Yar mahaukaciya hausa novels cmplt

 Compiled by Umar Dalha








*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM*





                 1


*Dukan yabo da godiya ya tabata ga ubangijin talikai , Wanda bai haifa ba kuma ba'a haifeshi ba , na godewa Allah da ya nuna min karshen novel DINA Duk karyar kada , ina rokonsa da ya bani ikon fara wanan cikin sa'a ya kauceni fadawa halaka dalilinsa, duk wani abin karuwa ya dorani saman sa abin ki ya kauce ni daga shi , wanan novel na kirkiri abina ne ina rokon Allah ya tayani isar da sakon dake cikinsa, masu karatu ina kara Mika sokon gaisuwata da kuma godiyata Allah ya barmu tare, Daukacin jama'ar gidan mu Exclusive Allah ya kara daukaka, marubuta baki daya ina jinjina na gode*









                 Labari


Kakarin amai take tana jan nunfashinta , ita kuwa ta daneta ta matse mata baki ala Dole sai ta dura mata danyen misan da ta tsinto a cikin bola , MAhaukaciya ce na hango ta dane wata yar budurwa tana kokarin dura mata mushe a bakinta ita kuwa ta gumtse bakin taki budewa , tana tsaka da kokowa da ita sai naga ta dakata , ta ja da baya kuma sai naga ta saka ihu ta shiga shure shure tana dafa cikinta da alama nakuda ce ta taso mata , yarinyar nan naga ta taso da gudu tana ta bibiyar wanan mahaukaciyar tana fadin , sanu haihuwar ce ? 


Ita dai Mahaukaciya ba bakin magana banda juya kai ba abinda take hakan yasa yarinyarnan fita da gudu daga cikin tsumakoran da suka saka suka dadaure sukayi dan dakinsu inda zapi , sanyi , damana ke riskarsu , tana FIta tayi ta gudu tana haki da kyar ta samu ta fito cikin layin domin a can cikin bola ne suke can karshen anguwa , tana fitowa ta tsaya tana waige waige ta rasa ina zata dosa domin neman taimako , wani gida ta hango tamkar kango ta nufa domin wani lokacin sunkan sakata kai shara gidansu wato bola , su bata dan kanzo da ruwan daurayarsu na kayan wankin su wani lokacin har barinta suke ta debi na rijiya taje su sha dadinsu ita da Mahaukaciya , 


Tana shiga ta rafka salama ta ja gefe ta rakube , wasu yara naga sun fito su kansu daudar jikinsu ta ishe su suna ta wasa suna ganin wanan yar budurwar saï naji sun fara wake suna fadin *Ke mai suna Yar Mahaukaciya yaya haukan ki Yar Mahaukaciya , shin ina babarki Mahaukaciya tana ta zuba haukan? Yar mahaukaciya* ita kuwa sai murmushi take aika musu bata ce komai ba , har suka gama daukar maganar su suka tafi abinsu , ta kusan rabin awa a tsaye sai ga uwar gidan ta fito ta sha damara da niyar yin surfe tana ganin Yar mahaukaciya tayi hamdallah ta yafitota 


Yar mahaukaciya ta matsa da Sauri ta zuguna a gabanta , 

Larai ta ce " idan abinci kike so zan baki da ruwan rijiya ke harma da zanin daurawata aman sai kin surfe min wanan dawar gaba dayanta 


Yar mahaukaciya ta juya inda aka nuna mata dawa ta hadiyi wani yawu mai daci ta ce " To uwar gida ran gida zan surfa yanzu kuwa 


Larai ta washe hakora ta kama mata buhun dawar suka tsayar da tirmin da tabaryar ta gyara yagegen zanin dake daure a jikinta ta shiga daka ba kakautawa , tun da rana ba ita ta gama ba sai yama lilis , Larai ta aiketa tayo mata cefane taje har cikin kasuwa a kafarta ita dai fama take ta gama ta koma wajen Mahaukaciya tasan yanzu ta dena iface ifacen domin takanyi hakan , 

Ba ita ta gama bautar gidan yawa ba sai da wajen shigar magariba , 

Larai ta harhado mata abinci harda na shekaran jiya ya gama yin tsami ta turo mata harda kanzo ta sauye mata shi a cikin wani bokici da ya gama yin tsatsa sanan ta ce ta jawo guga biyu ta isa gudun kar ruwan rijiyar ya kare ta je ta jawo guga biyun ta sauye a tsohuwar jarkarta ta dauka gaba daya tana tafe tana Sauri yara kuwa sai binta suke suna fadin yar Mahaukaciya ita kuwa bata kulasu famarta ta isa bola 



Tana zuwa ta hango dan karton da ta kara ta rufe an janye shi ta kara Sauri ta shige cikin kewayen nasu , jini jini ta fara gani a dashe a ko'ina ta yaye rufar da tayi da ledodi tana yayewa gabanta na faduwa don abinda idanuwanta suka gani bata san sanda ta saki bokicin abincin da ta wuni tana aiki dalilinsa ya zube a nan ba ta dauki hanunta ta dora saman kanta saman bakar ledar da tayi dan kwali da ita ta kurma ihu domin jariri ta gani konce cikin jini yashe a nan gashi ba Mahaukaciya ba alamarta da gudu ta karasa ta shiga dage dage da alama neman Mahaukaciyar take 










Shin ina mahaukaciya? Yaron nan wa ya haife shi? Su waye Mahaukaciya da Yar Mahaukaciya? Taku har kulun Sajida


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM*









                    2


Dadaga tarin tarikicen su take tana ihun kuka tana Kiran Mahaukaciyata ina kike ? Da kyar ta dena dage dagen ta matso kusa da jaririn nan ta tsura masa ido yaron sai kuka yake tun karfinsa wani tausayinsa ya kama ta ta Mika hanu a nitse ta dauko shi ta jawo ruwan nan ta wanke masa fuskarsa ta dorashi a bayanta ta dauki zanin nan da Larai ta bata ta goya shi ta fito ta fantsama neman Mahaukaciya ,





    Wai shin wacece Yar mahaukaciya?



Yar mahaukaciya ita kanta bata san sunanta ba bata san na mahaifiyarta ba , ita dai ta fara wayo ta ganta a gidansu bola kuma taji yara na kiranta da *Yar Mahaukaciya* ana kiran mahaifiyarta da *Mahaukaciya* duk da irin tarin daudar da suke ciki da cin abinci marar kyau da kwana a waje marar kyau idan ka kalesu zaka gane cewar fararen mutane ne rayuwa ce kawai ta mayar da su masu duhu , Yar Mahaukaciya ba arabi bale boko , bata da kowa sai Mahaukaciya , tarbiyarta tarbiyar Allah ce domin tanada nutsuwa tana masifar son Mahaifiyarta Mahaukaciya , bata son komai ya rabeta kulun cikin shan dukanta take domin idan ta kawo mata abu mushe taki ci sai kawai ta daneta wataran ta dura mata wataran kuwa ta samu ta gudu ,

Abincinsu gida gida take bi tayi aikace aikacen ragwayen mata ta samu abinda ta samu ta kai musu su ci abinsu kuma ruwa na kwata ne kadai basa sha domin tana yin iya kokarinta don ganin mahaukaciya ta kwana da ruwa a dakin , tun tana karama suke cikin bolar nan wataran ta wayi gari taga Mahaukaciya na dauke da ciki bata san KO na waye ba hasalima sai da taji yara na fada ta gane inda suka dosa tayi mamakin inda mahaukaciya ta samu cikin nan harma tayi tunanin KO hakan kawai ake wayar gari da shi , ita dai bata da mai bata amsa hakan yasa ta yi shiru abinta take lalaba mahaifiyarta cikin tsananin so da kauna iya labarin tarihin mahaukaciya Kenan 



Tafe take da dan yaro a bayanta tana girgizashi tana fadin kayi shiru dan Mahaukaciya muje mû nemo Mahaukaciyarmu mu kawota gidan mu ta goya sabon dan mu , kayi shiru Dan mahaukaciyana tana ta yawo gaba daya ta jigata sai jiri take na tsananin yunwa ga Dan mahaukaciya sai dai ta bashi ruwa yara kuwa banda tsokanarta ba abinda suke duk inda ta zaga sai an biyota ana fadin lah Yar mahaukaciya ta sato beby har ta ISO wajen wani police zata huce taji yace " ke yar mahaukaciya dan wa kika sato haka?


Tayi narai narai gabanta na mugun faduwa ta ce " Mahaukaciya ta haife shi kuma ta gudu 


Ya zabga mata mari har sai da ta dan fara sakin fitsari ya damketa sai police station , suna zuwa ya Nuna cewar ta sato yaro ne suka shiga tambayarta amsar dai data ce Dan Mahaukaciya ne hakan yasa suka kunce yaron suka shiga nadarta Dole sai ta fadi inda ta sato yaro banda kuka ba abinda take suna tsaka da dukanta sai ga tsohon daraja shima police din ne aman ya fisu mukami , yana zuwa ya tambayi mai tayi 



Ilyasu yayi masa bayanin ai ga abinda aka kamata da shi 


Tsohon daraja ya ce " tabas kwanakin baya naga Mahaukaciya da ciki a jikinta kuma yau na ganta wajen kasuwa ba cikin sanan saninta duk jini ne tabas wanan yaro *Dan Mahaukaciya ne* dan haka ku saki baiwar Allahn nan tayi tafiyarta 



Haka suka saketa ba dan ransu ya so ba domin sun so ta kwana a nan suyi anfani da ita ,sai dai kash tsoho ya kawo cikas 


Da kyar take takawa domin ta daku ta dauko dan Mahaukaciyar tayi wajen kasuwar don neman Mahaukaciya tana tafe tana kuka yaron na kuka tayi kasuwa neman duniyarnan ba Wanda bata yi ba ta juyo ta nufi wani layi tana tafe 'tana kugin sunan Mahaukaciya har ta isa wata makaranta ta zauna tayi tagumi almajirai sai shigi da fici suke suna ta sha'aninsu har akayi sallar isha'i bayan an gama sallah Malan ya fito daga masalaci ya hangi yatinyar nan zaune tana ta jijiga yaro a hanunta kawai sai wani tausayinta ya kama shi ya matso yayi mata salama 


Ta dago jajayan idanuwanta masy shige da na misa ta sauke su saman fuskar wanan Malan mai cike da Haiba ta amsa salamarsa 


Ya ce " Baiwar Allah lafiya kike zaune a nan? Ga yaronki da alama yunwa yake ji to ki bashi ya sha mana 


Yar Mahaulaciya ta kale shi tace " Malan ai ruwan ya kare babu kuma abincinsa 


Malan sai yaji tausayinta ya ce tashi mû shiga gidana a tatsa miki nonon akuya tayi sabuwar haihuwa sai ki bashi ya sha , ta mike har tana harde kafafuwanta ta bi bayansa suka shiga gidansa 


Matansa biyu dayar mai kirkin gaske DAyar kuwa tadi dafi zafi hakan yasa ya nufi dakin saratu ya fada mata ta fito ta taimaki yarinyar nan da danta ,


Saratu ta fito suka gaisa da yar Mahaukaciya tace miko yaron a bashi nonon akuya kema kije ga ruwan dumi kiyi wanka domin da alama sabuwar haihuwace 


Yar Mahaukaciya ta ce " nayi wanka? Da gaske?


Saratu ta ce " eh man ga bokici ki dauka ki zuba ruwan sai ki dan sirka da na rijiyar ki je kiyi wanka shima bara nayi masa sai a bashi nonon 


Sai washe hakora take domin itadai da wayonta har ta manta rabonta da tayi wanka ta jawo isashen ruwa ta kai bayi ta aje saratu ta bata soda ta dauko mata jacen kayanta ta mika mata har tana fadin ki wanka ruwan zafin da kyau fa saboda jego ita dai har lumshe ido take tana zuba ruwa a jikinta kafin ta fito Saratu ta wanke dan mahaukaciya ta bashi nonon akuya ya sha sosai har ya samu wani ni'imtacen baci mai dadi 


Wanka take tun karfinta wani bakin ruwa na zuba daga jikinta yana bin magudadar ruwan nan da nan sai gâta ta fara haske tamtar mai , ta cire ledar dake rufe a kanta ta dauki sodar nan ta ringa kwabata a cikin gashin kanta nan da nan naga wata irin dauda mai yauki tana zuba daga kanta ta kama kwarara ruwa gaba dayanta ta darwaye jikinta dagowar da zata yi na zaro ido domin gashin kanta ba baki bane kalar 🙍🏼 masara ne yelow gaba dayansa aman yalow mai haske ga shegen tsayi da gareshi na tambayi kaina wai Yar Mahaukaciya yar hausawa ce kuwa? Ta dauko ledarta ta daure kanta ta saka kayan da Saratu ta bata sai ajiyar zuciya take domin ta rabu da kashi 80 na daudar dake jikinta tana fitowa gaban Saratu ya fadi , duk irin kirkin saratu matsalarta daya ce kishi Allah yayi mata kishin mijinta tamkar mai , hakan yasa da Sauri ta daukowa Yar Mahaukaciya yan tsumakoron da ta dadauko mata ta bata ta hada mata da tuwon lamshi mai yawa ta ce " to yar uwa rufe gidan zamu yi kinsan Malan ba a nan yake kwana ba hakan yasa Mike rufe gida da wuri 


Yar Mahaukaciya ta kama godiya harda tsugunawa saratu ta ce ba komai ta dora mata dan Mahaukaciya ta goya ta dauki sauran kayan tayi gaba tana yiwa Allah godiya taci GABA da Neman Mahaukaciya 










                😌

.[8/11, 06:27] ‪+234 816 681 0364‬: *'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                    3

Tafiya take har karfe biyu na dare yayi mata ta gaji tamkar ta kife idanuwanta sai zugi suke yi mata na baci dan mahaukaciya kuwa sai bacinsa yake shekawa hankalinsa konce domin ya sha nonon akuyar nan ya koshi , wata bishiya ta hango a hankali ta isa ta samu ta rakube ta shinfide dan Mahaukaciya tayi konce a gefensa ta shiga tunanin duniya tana tunani tana share hawayenta ta mike da ruwan na yar jarkar ta zauna ta daura wata kalar alwalah gaba daya ba daidai bace ta juya Gabas tayi sallah Wace bata karanta komai sai dai tayi ta musmus da baki shima wajen Larai ta jiyo idan tana sallah tamkar koton kurciya nan da nan ta gama tana salamcewa ta konta kusa da dan kaninta tana adu'ar Allah ya jikanta ya ya fito mata da Mahaukaciya ,


Haka rayuwa tayi ta tafiyarwa yar mahaukaciya tun bata iya raino ba har ta kware ta iya goya yaron da zuwa wanki , shara a bata nera ashirin nera goma ta je ta siyowa Dan Mahaukaciya koko ta zo ta bashi ya sha , idan ya koshi itama ta samu ta sha , a tanzu yara sun koma tsokanar Yar Mahaukaciya da Dan shege ita dai ta kanta take tana nema musu dan abunda zasu saka a bakarsu har yanzu tana zuba ido ne taga ta inda Mahaukaciya zata bilo duk fitar da zata yi kuwa sai ta nemi Mahaukaciya har yanzu bata fida rai da ita ba , 




Konce take ta samu da kyar barci ya dauke Dan Mahaukaciya ita kuwa sai hama take ga wani uban sauro na damunta inuwa inuwar mutun ta fara gani ta mike zumbur ta fara kalon kofar wani katon mutun ne bakikirin mai murdaden jiki ya shigo kafin ta ankara tayi wani abu har ya watsa mata wata hoda a fuskarta ya kwasheta ya sakata cikin wata bakar mota ya dauko jaririn shima ya saka shi cikin motar wa'inda suke cikin motar suka figi motar , 


Tafiya suke tun karfinsu sai da sukayi tafiyar awa hudu sai gasu a garin jos suka karkata suka nufi wani tankamemen gida mai shegen kyau suna isa aka wangale musu porte din suka dana kai ciki , wata hanya naga sun dauka a cikin gidan sun nufi wani gate din aka kuma bude musu , suna isa ya diro ya bude ya dauko Yar Mahaukaciya a kafadarsa ya nufi wani daki da ita ya dauko yaron shima ya Mika shi wajen wata tsohuwa naga ta nufi ciki da shi , 


Dishi dishi ta fara gani sanan a gankali ta buda idanuwanta , wajen da ta ganta konce saman wani makeken gado Wanda tunda uwarta ta haifeta bata taba sanin akoyshi a nan cikin duniya ba ta Mike tsaye da Sauri ta fara dubedube can ta koma ta zauna ta tare fuskarta da hanayenta ta shiga tinani , watarana taji kishiyoyin Larai suna fadin idan aka mutu akoy wuta akoy aljana , ance a aljanar akoy manyan gadaje da manyan TV da komai da komai a wutar kuwa wutace kawai sunce ai idan Larai ta mutu tace ita aljanar zata zaba su kuwa a kaisu wuta dan sun aure mata miji ( to kaji Larai shawara Kenan za'ayi miki?) , ta kuma daga kanta ta hango babar TV din ta kali gadon da take zaune saman kansa a fili ta furta " Au Kenan mutuwa nayi aka kawoni aljana? To ina dan Mahaukaciya da Mahaukaciya ? Ku zo ku ga aljana ku zo muyi zaman mû a nan aljanar tafi duniyar dadi , tana tsaka da maganarta aka bude dakin wata mata ce ta  shigo rusheshiyarta ta ja ta tsaya da Sauri yar Mahaukaciya ta mike tana soshe soshe tana kalonta 


Matar nan ta ce " ke yarinya ki tashi nayi miki wanka na shirya ki na kaiki wajen hajiya 


Yar Mahaukaciya ta ce" baiwar Allah nan ina ne? Duniya ce KO lahira?


Matar nan ta ce " ke karki kawo min maganar banza ta kama Yar Mahaukaciya kiiii sai cikin bayi tana ji tana gani matar nan ta tube ta tamkar wata beby ta zirata cikin bahon wanka ta kama dirzarta  da wani soso mai shegen zafi , tun tana nonokewa har ta hakura matar nan dan rashin imani ta dauko wani tirare da detol ta zuba a ruwan har kanta ta kuma darje jikin Yar Mahaukaciya jikin har wani sulbi yake na wahala ruwan ya kuwa shigar mata ido ta rufe ruf tayi ta murzawa aman matar nan bata damu ba , tana gamawa ta jawo tawul ta nade jikin yar Mahaukaciya ta jawota tsakar dakin nan Yar mahaukaciya ji take tamkar sabuwa har wata iska ke daukan ta tayi fayau da ita farinta yayi mugun fitowa ,


Matar nan mai suna Mesi wato ba musulma bace ta dauko kayan bushe gashi da wani mahaukacin kaya doguwar riga mai daukan hankali ta jawo hanun Yar Mahaukaciya ta zaunar da ita ta shiga bushe mata gashin kanta ta dauko man shafawa ta shafa mata nan da nan kan nan mai kalar blonde ya fara sheki ta saka ribom ta daure aman har gadon bayanta ya zubo , ta mika mata sabon pant da breziya ta saka gaba daya aikin nan da take yi mata bata yi mata magana itama tayi shiru tana kikifta manyan idanuwanta ta rasa wanan wani irin Abu ne? Wanan wata irin masifa ce? Meye za'ayi mata ne? Ina za'a kaita? Ina Dan Mahaukaciya? Nan din ina ne?
















     Ni ma ban sani ba yar mahaukaciya sai dai mu bisu mu gani

[8/11, 06:28] ‪+234 816 681 0364‬: *'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*









                    4


Tana tsaka da sakar zuci taji Mesi cikin wata uwar muryarta tamkar namiji tace " ke tashi mu tapi 


Cikin Sauri Yar Mahaukaciya ta mike ta bi bayan Mesi suka ratsa wani falo baba , suna ratsa na biyu ta hango wata tsohuwa tana ta jijiga yaro a hanunta , 


Tsohuwar ta matso ta mika mata yaron ta ce " bashi ya sha 


Yar Mahaukaciya tayi shiru ta amshi Dan Mahaukaciya ta rungume shi yana ta bacinsa kawai sai taki cewa komai 


Mesi ta ce " yaronta ne kuma mahaulaciyar ce dan Haka kawai mû kaisu wajen Hajiya 



Tsohuwa ta washe hakoranta jajaye ta ce " kai aman hauka shi kadai yake wanan yarinyar mai kyau haka ya kamata? ( tsohuwa shin haukan ba kadarar Allah bane? Akoy Wanda ya isa ya kaucewa kadara ne? )



Messi ta ce " baki ma ga gashin kanta ba wani mai shegen kyau sai tambayar masifa ke malama mu je KO na ci ubanki a nan 


Yar Mahaukaciya tayi gaba da gudugudu suna biye a bayanta sunyi tafiya mai nisa sai gasu sun bilo dakin wata mata tana zaune bakin gadonta ta hakimce Matar zatayi shekara arba'in da biyar a duniya , 


Suna shigowa su duka suka tsuguna suna gaishe da ita banda yar Mahaukaciya 



Hajiya Falmata ta ce " ya zaku kwaso min yarinya karama haka nayi yaya da ita? 


Mesi ta ce " ai hajiya wanan ta dade cikin hauka yanzu haka da kokowa da komai muka samu muka fito da ita kinga sai da na sharara mata mari hudu sanan ta dena buge buge kuma kinga yaron nan danta ne ita ta haife shi bashida uba shege ne kuma ita din ma shegiyar 



Hajiya Falmata tayi shiru ta ce to ku zaunar da ita 


Suka zaunar da Yar Mahaukaciya ita dai binsu take da kalo bata ce komai ba , sai da suka zaunar da ita suka fice 


Hajiya falmata ta taso ta zauna nesa da yar Mahaukaciya ta kura mata ido ta ce " ba laifi kina da kyanki , kuma kinfi wancen Wanda nayi da ita kuma na kasheta da alama ke zaki fita iyawa kuma aikina zai fi ci sosai 


Gaban yar Mahaukaciya banda faduwa ba abinda yake tayi shiru tana ta kifta ido , ita dai har yanzu bata gane inda Hajiya Falmata ta dosa ba , wani aiki ? Mai zata yi da ita? Tana tsaka da tinani taga hajiya ta Mike tana famar tube kayan jikinta Yar Mahaukaciya ta sada kanta kasa taki dagowa , duk da mahaukaciya ta reneta bata ganin tsiraicin Babar mace haka ,  gabanta sai faduwa yake 


Hajiya falmata ta mika hanu ta dauke dan Mahaukaciya ta ja hanun Yar mahaukaciya ta kontar da ita saman bed din dakin ta yar mahaukaciya tayi zumbur ta Mike tana kalon kasa 


Hajiya falmata ta ce ' ke dan ubanki konta min ke badan boka yace na konta da mahaulaciya mai da ai da baki isa na konta dake ba sai manyan hajiyoyi to dan dai kawai ina gudun kar asirin da nayi shekara goma sha hudu da suka fice ne ya karye dan uwarki konta min KO na saka a daure min ke 



Yar Mahaukaciya ta zaro ido ta ce " Ni fa ba dana bane dan Mahaukaciya ne 



Hajiya Falmata ta zabura ta ce " kutumar ubancan to wacece mahaukaciyar ke kuwa wacece ? 



Yar Mahaukaciya ta ce " Ni Yar Mahaukaciya ce Kuma wanan ma dan Mahaukaciya ne Mahaukaciya ta tafi yawo bata dawo ba 


Hajiya falmata ta zaburo ta ce " ai kuwa yau sai na kasheki tsinaniya shine kika sakani a gaba har na tube miki ?  Yau sai na galabaitaki sanan nayi anfani da ke kuma na kashe ki tayo kan Yar Mahaukaciya ta shaketa 












    Wayo yar Mahaukaciya


🇳🇪 BElles écrivaines du Niger


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                    5


Wayo Kano ba wuta sai ingi 🙆🙆🙆🙆🙆🙆







Famar sumewa take domin Hajiya Falmata ta mugun shake mata wuya ta gaza tabuka komai domin karfin ba daya ba , tana kokarin ganin bayan Yar Mahaukaciya wayarta dake aje a gefen bed din ta shiga ringin kuma karar wayar wakar da ta sakawa mijinta ne hakan yasa cikin Sauri ta cikata ta dauki wayar 



Daga dayan bangaren Elhaj biloniya ya ce " Hajiya na fasa tafiyar gani na dawo bangarenki bakya nan shin kina ina ne?



Hajiya Falmata ta ce " what? Kana gida?


Elhaj biloniya ya ce" eh lafiya nake jin muryar taki a tsaitsaye? 


Hajiya Falmata ta ce " no ba komai dear gani nan zuwa yanzu yanzu 


Ta datse Kiran ta danawa Mesi kira tana kokarin mayar da kayanta , Mesi ta shigo da gudu tana amsawa 


Hajiya Falmata ta ce " ke sakaran banza da wofi zo ki san yanda zaki fitar min da wanan dabar domin honorable ya dawo gidan nan idan kika yarda aka kama ki da ita ke zaki kwana a ciki , bata samu damar fada mata cewar yarinyar ba mahaukaciya bace hakan yasa Mesi bata tsaya tambayar a kasheta KO kar a kasheta ba kawai ta jata ta bi ta hanyar baya da ita ta tura ta ta wata karamar kofa ta ingiza keyarta sai waje ita kuma ta juyo ta koma cikin gidan tana ta tsinewa halayar Falmata ta samu babar yarinya haka aman tana aikin mita ,



Yar Mahaukaciya da take rungume da Dan Mahaukaciya tana zabga Sauri bata ma san ina zata dosa ba gashi kafarta KO takalmi babu tana godewa Allah da ya kubutar da su daga hanun wa'inan bayahudan 


Tafiya take zabgawa tana haki ta rasa ina zata nufa hankalinta duk a tashe ta rasa mai zata yi , ina zasu kwana ga garin bata san shi ba tafe take tana  tunani idanuwanta sai zubar da hawaye suke , karar taka birki taji kiiiiiiiii aman ina duk da haka sai da ya buge kafafuwanta ta fadi dabas a kasa aman Dan Mahaukaciya na rike a hanunta , mutumin da ya kadeta ya fito daga cikin motarsa dan matsakaici ne , bashida kiba aman yanada dogon hanci yana cikin jalabiya fara da alama ba nesa zai je ba 


Ya ce " Malama lafiya kike tafiya bakya kalon gabanki? 


Yar Mahaukaciya ta dago kanta ta sauke idanuwanta a saman fuskarsa bata ce komai ba ta mike taci gaba da tafiya , yayi sororo yana kalonta kawai sai yaji a ransa wanan yarinyar da danta duk inda zata tafi tana cikin damuwa ne gashi kuma ya bigeta da mota kuma bata ce masa komai ba , cikin Sauri ya tayar da motar ya bi bayanta 



A hankali yake binta da motarsa yana fadin baiwar Allah lafiya? Mai yake damun ki? Ina zaki tafi? Ina takalman ki? Aman shiru bata bashi amsa ba hakan yasa ya ce to ki shigo na kaiki inda zaki tafi mana?



Tana jin haka ta waigo tana kalonsa ta ce " zaka kaini?



Wanan bawon Allah mai suna Idrissa ya ce " eh ki shigo na kaiki inda zaki je 


Ya Buda mata motar ta shiga tana jijiga Dan Mahaukaciya , shi kuwa ya koma ya shiga tuki ,


Tafiya suke ba mai yiwa dan uwansa magana shi jira yake ta fada masa ga kwanar da zai sha KO ga unguwar da zai kaita aman tayi masa shiru hakan yasa ya ce" baiwar Allah ina zamu nufa ne?



Cikin sarkakiyar murya Yar Magaukaciya ta ce " Bawon Allah ina ne nan?


Idrisse ya ce " Jos ne baki san sunan garin ba? Mai yake damunki ne?


Yar Mahaukaciya maimakun ta bashi amsa sai ta jefe shi da wata tambayar ta ce " menene jos? Sunan anguwa ne? 


Idrisse yayi tsai yanzu fa ya dan fara tsorata KO dai ya kwaso ruwan dafa kansa ne? Ya nisa ya ce " Dan Allah ya sunan ki?


Yar Mahaukaciya tayi tsam ta ce " ana kirana da sunan *YAR MAHAUKACIYA* 


Idrisse ya taka birki ya juyo yana kalonta rigar jikinta duk ta dame mata jiki tamkar karuwa (  yar bariki ) gashi batada dan kwali gashin kanta tamkar ba na bahaushiya ba kai fatar jikinta kanta tamkar na mai Jan kune nasara sai dai kwayar idanuwanta bakake ne sidik shine banbancinta da nasaru , 


Ya ce " ban gane ana kiranki da Yar Mahaukaciya ba , meye ainahin sunan ki na kirki? Wanda aka rada miki? Wanda dadynki ND momynki ke kiranki da shi?



A ranta tana mamakin yaransa meye dadynki ND momynki? Meye sunan da za'a kirayeta da shi wanda ya dara Yar Mahaukaciya? Ta juyo suka hada ido hudu da shi ta ce " haka ne suna na , haka suke kirana da shi kuma wanan sunan sa Dan mahaukaciya 


Idriss ya girgiza kai a ransa ya ce bazan iya barin wanan haka ba da alama ta gaji shi yasa take sakin zance ba tsari hakan yasa ya ce " zan kaiki gidan abokina yana da ma'aikata mata ki kwana a can gobe da safe idan Allah ya tashe mu lafiya zan zo muyi maganar abinda ke damun ki da kuma sunan ki aman ki sani bazan yarda cewar sunan ki Yar Mahaukaciya ba because ke din da alamar nutsuwa a tatare da ke so ki yarda da ni bazan cutar da ke tomorrow sai na kaiki gidan ku tunda yanzu kin gaji 



Ita dai kalon bakinsa take yanda yake magana ba tun karfi ba daman akoy maza masu magana a hankali? Sai kuma da taji yace tanada wani suna bayan yar Mahaulaciya tana son sanin sunan , sai kuma da yace zai mayar da ita gidansu wato bola hakan yasa hankalinta ya konta harma ta gyara konciyarta tana kalon titi ya tayar da motar ya harbata kan titi ,



Sun dan yi tafiya mai dan nisa suka isa wani gate shima tankamemen sa lokacin Yar Mahaukaciya tayi baci shi dai haka kawai yaji matar nan yana tausaya mata ya dana horm aka wangale masa gate din yana shiga daidai Umar abokinsa ya fito da computer sa zai je jardin ya huta yayi tsai yana kalon Idrisse , Idrisse yayi parking da motar har lokacin bata farka ba , ya fito ya nufi Umar yana isa suka tafa 


Umar ya ce " kai mutumina wanan bebyn fa?


Idrisse ya ce " kai karka yi min zakarancin naka wanan wata baiwar Allah ce na hadu da ita na kawota nan tunda kana da masu aiki mata ta kwana a wajen su tomorrow sai na kaita gidan su yeah?


Umar ya ce " wayo baiwar Allahn harda danku kai na tayaku murna abokina Allah ya raya bara na matsa na ga bebyn tamu 


Idrisse ya girgiza kai suka matsa tare shi da Umar , Umar ya Mika hanunsa a hankali yana konkwasa gilashin motar 


Yar Mahaukaciya dake barcinta ta Buda idanuwanta a hankali ta dago kanta suka yi ido hudu da Umar gabansa ya yanke ya fadi yayi Saurin ja da baya nan da nan jikinsa yayi wata muguwar mutuwa ya saki computer hanun NASA ,   ,,,,,,,,,     ,,,,,,,,,,






















To jama'a mai ya baiwa Umar tsoro? I don't know 🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀












I'm sorry ba wuta ba nepa 😭😭😭😭😭😭


  *'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                    6



Na sadaukar da wanan shapin gareki masoyiyar asali AMINA AMINU ina godiya da adu'o'in ki 





Umar ya saki computer hanunsa ji yayi duka gabobin jikinsa sunyi wata irin mutuwa 


Idrisse da Sauri ya matso ya dafa kafadar Umar ya ce " yayadai abokina lafiya mai ya faru? KO ka Santa ne?


Umar ya ce " abokina yarinyar nan na taba ganinta a turkey naje wani aiki na ganta ana tuka ta ita da kanta aman wanan tafi wacen fari kuma gashin wacen baki ne yarinyar nan aljana ce domin da nayi mata magana gurds dinta sai da suka kusan kashe ni , gaskiya bazan sauketa a gidana ba 😡



Idriss ya zuba masa ido yana sauraron sa ya ce " to aman mai zai kawo mutumin dake turkey saman titin jos ba KO takalmi? Kuma tafiyar nan taka duka duka yaushe ne ai bai kai har ta haihu ba KO? KO da tsohon ciki ka BArTA ne?



Umar ya daga kafada irin bai shafe shi ba ya ce " ni dai banga ciki a jikinta ba may be ta ajiye shi a gida ne  kafin ta fito na fada maka wly aljana ce ka rabu da ita tun wuri ,



Idris ya juya yana kalon Yar MaHaukaciya Wace itama su take kalo tana son fahimtar yaren su , abinda suke fada , Idris ya nufo motar jikinsa ba kwari ya Bude mazaunin direba ya tayar da motar ya kama hanyar fita yana tafe yana sakar zuci shi dai Allah baiyi masa tsoro ba kuma ya sani idan har Aljana ce wanan tofa zata bace ne koda tsakar dare ne hakan yasa yayi imani da Allah ya dauki hanyar gidansa da ita , a hanya ya tsaya wani butique ya siyo mata hijabai uku da dogayen riguna ya fito ya sayi kaji ya shigo motar ta koma barcinta hankalinta konce ya tada motar , sai da yayi tafiyar minti ashirin ya isa gidansa mai gadi ya bude masa ya zagaya ya shiga ta baya da ita gudun kar a kai tsegumin ya zo da mace harda yaro gidansa momynsa kuwa mai zafi ce 



Bayan ya gama daidaita tsayuwar motar ya rasa taya zai tayar da ita yayi tsai yana kalon fuskarta verry inoscente wanan yasan bazata fice wata shekara 15 a duniya ba , gashin idanuwanta ya tsurawa ido sai yaji sha'awar tabawa yaji KO nata ne domin bakinsu yayi over ga kuma tsayi ga sheki ya Mika hanu a hankali zai taba wani abu yace masa kai Idris matar aurece fa hakan yasa da Sauri ya janye hanunsa ya dan bubuga kujerar da take konce 


Firgigit ta farka ta tsura masa idanuwan nan nata masu matukar firgitar da mutun , ya kawar da kansa ya ce " ki fito mu tafi 



Ya bude motar ya fita ita dai da kalo take binsa ta rasa ina ne wajen bude motar ganin taki fitowa yasa ya bude mata ya kwashi kayan ta fito ta tura motar irin yanda taga yayi ta bi bayansa cikin gidan suna shiga ya Mika mata leda baka 

Ya ce " ga abincin ki da kuma hijabi ga daki can ki kwana ciki da safe idan Allah ya kaimu zamuyi magana kinji?



Yar Mahaukaciya ta gyada kanta tayi hanyar dakin da ya nuna mata , tana turawa taga dakin masha Allah ya sha kwaliya tayi tsai tana tunanin to wai daman haka suke gidajensu ko'ina ka shiga da shegen kyau haka? Ta samu nan kasa saman kafet din ta shinfide Dan Mahaukaciya ta rungume shi sai baci , KO abincin bata ci ba , baci yayi awon gaba da ita ( baiwar Allah )





Da sasafe taji ana dukan kofar tata ta farka ba shiri taje ta bude kofar tana budewa yayi saurin sunkuyar da kansa domin rigar ta jikinta ta dan yaye daga sama ya juya ya ce " Baba gatanan zan tafi kwana uku zanyi kinsan halin oga idan yana gari dan Allah ki kular min da lamarinta idan na dawo zan mayar da ita gidan su 



Baba ta ce " to yaron kirki Allah yasa a dace Allah ya bada sa'a ,


Yar Mahaukaciya dai kalonsu take bata ce komai ba , ya dan kalota ya ce " na tafi ogana ne ya dawo wajen aiki kuma yanada bukatana wajen aiki duk da cikin gari ne ya saba ya rike mu har sati , so kiyi zaman ki idan bukatar wani abin ya tashi ayi kirana Insha Allah zan samu yanda zanyi na fito 



Yar Mahaukaciya ta ce " zaka kaini bolar?


Yayi tsai yana kalonta can yace" sunan unguwarku bola?


Yar Mahaukaciya ta ce " aa gidan mu ne can bolar 


Idris yayi shiru a ransa ya ce " KO dai ta haukace ne yarinyar nan ?


Yar Mahaukaciya ta ce " kuma kaga ina neman Mahaukaciyata ban ganta ba 


Har zaiyi magana wayarsa ta hau ringin da Sauri ya daga yana furta ai na shigoma sir , ya kashe da Sauri ya juya yana fadin eh ki zauna idan na dawo zan kaiki bolar kinji?



Ta gyada kanta baba ta ce " Allah ya kiyaye hanya dan nan 


Yana amsawa ya tafi ya Buda motar sa ya tafi 



Baba ta juyo wajen Yar Mahaukaciya ta ce " Yarinya muje ki canja kayan nan KO? Ya sunan ki ne?



Yar Mahaukaciya ta ce " *Yar Mahaukaciya* sunana



Baba ta zaro ido ta ce,,,,,,,,,,










 Sorry masoyan yar mahaukaciya ina kara baku hakurin kadan in da nake yi hakan ya faru ne da 🏌🏼‍♀ nepa🏌🏼‍♀

🇳🇪 Belles écrivaines du Niger 



*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                    7

Na sadaukar da wanan gareki yar uwa masoyiya Maman manal matar oga lolz Allah ya barmin ke 


Baba ta zaro ido tace"  yar nan bana son neman magana wani irin yar mahaukaciya kuma? Ina babarki take ne?


Yar mahaukaciya tayi tsai ta tuna lokacin idan tana daka a gidan su Larai yayansu suna cewa babata babata nan ta gane Babar mutun tamkar uwa Wace ta haifi mutun hakan yasa ta watsa hanayanta irin bata sani ba 



Baba ta ce " mu je kiyi wanka ki ci abinci sai ki bani labari , 


Baba ta shige gaba yar Mahaukaciya na biye a bayanta ta buda bayin ta tara mata ruwa sai da ta nununa mata komai domin a yanda tayi mata tsaye da alama bata iya ba , ta juya ta dauki yaron harda pampos dinsa tun na jiya da suka saka masa ba'a cire ba , hasalima ita bata san menene ba tana tsaka da yiwa yaron wanka yana tsala kukansa Yar Mahaukaciya ta fito ta dauki rigar da Baba ta Nuna mata ta saka tayi tsaye tana kalon yanda Baba ke juya Dan Mahaukaciya tana yi masa wanka , a hankali ta zauna tana kalon fatar hanunta ta zama wata kala wai daman haka take?  Tana tsaka da tunanin irin rayuwar nan mai dadi ta ji baba tsohuwa na cewa to bude ki bashi ya sha 



Yar Mahaukaciya a ranta ta ce " wai meye ake cewa ta bude ta bashi ya sha ne? Ita fa bata san mai ake nufi da hakan,



Baba ta ce " ke yarinya ki dena yawon tunani kar ciwon nan mai suna totion ya kama ki , ai ina fada miki haka mukayi da sale ya shirishiri ya dankara min saki uku bayan ya dala min mari a gaban sabuwar amaryar sa kuma ya tunkudo ni waje aka yi mana taro jama'a na tambayar mai ya hadamu wai kinsan mai yace?


Yar Mahaukaciya ta girgiza kai tana sauraron baba 


Baba ta ci gaba da cewa wai wani cewa yayi fa na saci kudinsa murtala fa 


Yar Mahaukaciya ta ce " kai har Murtala ? To wa ya dauka ?


Baba ta karkace ta gyara zama tace" yar nan nera sha biyar ne na dauka aradu ni ba duka na dauka ba kuma wata hudu yayi bai bani kudin cefane ba shine fa na dauka kuma ai ba sata bace KO?


Yar Mahaukaciya ta gyada kanta tana mamakin wai dauka ne tayi ba sata bane tayi murmushi 


Baba ta ce " ke yarnan ai dukan da yayi min da kuma sakin ya saka na kumbure uwa hulawa ni kadai nake kara girma babar uban gidana ta kaini ganin likita a can ne yace min wai totion ( tension ) ce ta kamani kuma har kisa take kinga ki dena tunani dan miji ya sakeki kiyi hakuri Allah zai baki wani cikin ruwan sanyi balatana ke din nan mai kyan aljanu 


Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta ce " toh , domin ta lura Babar nan ba dai surutu ba 


Baba ta kama rigar Yar Mahaukaciya ta zuge zup din , ita dai kalonta take tana son ganin abinda zata aikata tana zugewa Yar Mahaukaciya ta saka hanayenta biyu ta rufe mamarta 


Baba ta ce " ke kuji mini yarinya da iyayi kunyar shayar da yaron ne kike a gaban idona na FITA?



Yar mahaukaciya ta ce " kunu yake sha 


Baba tayi tsai ta ce " dadina da yan gayu Kenan wai baza'a shayar da yaro ba kar nono ya fadi ,hum to Allah shi kyauta ta dauki yaron tayi kicin da shi sai wake take rera masa ta dora kunu ta kada domin shima mai gidan ma'abotin shan kunu ne hakan yasa ta hada ta baiwa yaron ya sha ya koshi sai baci ( bawon Allah )




Wasa wasa yau har sun cika kwana uku a gidan Idriss bata aikin fari bale na baki aman duk da hakan tana fitowa tana kalon yanda baba ke kula da harkokin gidan da irin kulawar da take basu ita da Dan Mahaukaciya , har mamaki take wani abin , 



Zaune take tana kalon TV baba ta zo ta zauna kusa da ita ta ce " yarinya baki fada min inda babarki take da kuma abanki ba fa abun da mamaki har yanzu basu neme ki ba lafiya kuwa?



Yar Mahaukaciya ta juyo tana kalon baba a hankali ta furta nima nemanta nake , Mahaukaciya ta bata ban san inda ta nufa ba , na rasa inda ta tafi ta barmu da Dan Mahaukaciya 



Baba ta gyara zama ta ce " ban gane ba


Yar mahaukaciya ta gyara zamanta ta baiwa baba labarin rayuwarta har Wanda bata san sunanta ba bata san kowa ba hasalima bata san sunan garin nan ba wai jos ita kuwa a tinaninta a kano take domin tana ji a bakin mutane 



Mai baba zatayi in ba kuka ba harda face majina tana karkata kai ta ce " kai duniya kai duniya ina zaki da mu ? Oh ni habiba ya ga murja jikar saude wayo duniya kana tunanin a kunci kake sai ka tsinci Wanda ya fika oh Allahna , ta juyo ta kali Yar Mahaukaciya ta ce " yarinya Ashe shi yasa da na tambayeki sunan ki kika ce min Yar Mahaukaciya?



Yar Mahaukaciya ta gyada kanta 


Baba ta ce " to ni zan ringa kiranki da Rahamu sunan yayi miki?


Yar Mahaukaciya tayi dariya ta ce " eh yayi min baba 


Suna tsaka da zance sai ji suka yi an banko kofar dakin an shigo , Baba ta mike tana dafe kirji ta ce " salalahu alaihi wasalam Tawa ta sameni ,



Kafin Yar Mahaukaciya ta fahimci inda baba ta dosa sai jin saukan duka tayi ta ko'ina dukanta ake ba kakautawa , mai dukan ta warto Dan Mahaukaciya ta jefa shi kasa ya rufe da kukan jarirai da gudu Yar Mahaukaciya ta nufi wajen da yake yashe ta rungume shi suna rusa kuka a tatare ,  


Mai dukan ta nuna su da yatsa ta ce "  """"' """""""" """""



Love u

🇳🇪 Belles écrivaines du Niger



 *'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                    8

Mai dukan ta nuna su da yatsa tana kunfar baki tace" ke karamar yar bariki shegiya mai shige da zabaya ( albinos ) a gidan ubanwa ma ya hadu da ke har ya dirka miki cikin nan kika haifo yaro mai kama da ke? Kaga yayan shegu sai dai suyi kama da uwar su to bara kiji na fada miki Idriss nawa ne ni kadai babu ubanda ya isa ya hada shi da wata matar sai dai bayan raina dan haka ki dauki shegen danki da ke ku bace min a gidan mijin da zan aura tun kafin na kontar da ku nayi muku yankan rago 



Yar Mahaukaciya dake goge jinin dake zuba a kan Dan Mahaukaciya ta dago idanuwanta ta sauke su a fuskar wanan matar wada da gani ta girmi idriss nesa ba kusa ba kuma tana ambatan mijin da zata aura cikin rashin kuzari ta dauki dan Mahaukaciya ta juya tana share hawayenta daidai zata bude kofa Idriss ya turo ya shigo ta dan ja da baya da sauri ya matso yana tambayar lafiya?



Hajiya Mariya ta taso tana fadin : my man ai na koreta ne kana ganin irin yanda ake zaginka a cikin family dina ana fadin ka ajiye karuwa yar bariki harda danku a cikin gidan ka ?


Idriss yayi gagawar daga mata hanu cikin daga murya yace ubanwa ya baki izinin korar a gidana? KO gidanki ne? An fada miki itama irinki ce? An fada miki itama ta samu yayane a waje irinki?



Hajiya Mariya tace" kai dakata Malan yayan ba da kai na samesu ba? KO an fada maka KO wani jaki nake mu'amala da shi ne? To wly KO ka kori yarinyar nan KO na kirayi mahaifiyarka na fada mata sanan na yada ka har a wajen uban gidan naka na samu na ganshi na fada masa irin abinda kake aikatawa ya koreka banza kawai , ta ficeshi ta ja rigar yar Mahaukaciya tayi waje da ita ta baiwa mudi mai tebur kudin mashin tace ya kaita inda yaga dama ,


Baba tsohuwa ta zauna tana ta hawaye ta fadawa idriss gaba daya abinda Yarinyar nan ta fada mata , harda sunan da tayi mata wato Rahamu ,


Idriss ya nisa ya ce" ban taba tinanin cewar watarana zan hadu da mace lokaci guda naji ta shige min a rai irin wanan yarinyar ya lumshe idanuwansa ya ce na kamu da sonta baba kuma insha Allah KO ina take zan nemota na aureta koda kuwa zan rabu da aikina ne , aman gaskiya ni bazan raka mata sunan Rahamu ba , bakya ganin yanayinta yanayin yayan larabawa ne ina wa laifin sunan Manal? 


Baba tsohuwa ta washe hakora tace ai kuwa kaga sunan yayi min dadi sosai wato Manil 


Yace aa Manal take baba ya Mike yayi dakinsa yana neman layin yaronsa ya kwatanta masa kamaninta da nufin maza ya zo anguwar su zai ganta da beby a hanunta ya dauketa kafin ya fito ( baka sans cewar a mashin aka dauketa ba ?)



Tafe suke yana papara gudu tun karfinsa ya ce " ke wace unguwa zan kaiki?



Yar Mahaukaciya tayi shiru can tace " Dan Allah ka kaini wajen magani kaga dan Mahaukaciya duk yayi wani iri



Mudi ya juyo kadan yaga yaron duk ya wani banbankare a ransa ya ce " kan uba kar aje ya mace min a rufe ni hakan yasa ya ja ya tsaya daidai wata katuwar asibitin kudi ta Yaron nan mai tashe wato Ibrahim Y Nazir ya ce " ke sauka ki shiga nan zasu warkar da ke kinji?



Yar Mahaukaciya ta sauka da sauri mayafinta har yana dan zamewa ta shige asibitin , tana zuwa ta nufi wajen da taga kamar nan ne wajen maganin , ta shiga layi , tun abin karfe goma sha daya har karfe 12 da yan mintuna sanan layinta ya ISO tana zuwa sai taga wata taga taji ance katin yan me kike so?


Ta dago dan Mahaukaciya ta nuna ta ce " dan Allah kiyi masa magani kina ganin jikinsa?


Matar ta dan bude windows din ta leko ta ce " ke dauke min jini mana karki bata min wajen aiki ki bayar da kudi a yanka miki katin ganin likitan yara 



Yar mahaukaciya ta ce " nawa ne kudin?


Matar ta ce " dubu hudu 


Yar Mahaukaciya ta ce " dan Allah ki yanka min a bashi zan kawo miki 


Matar nan na jin haka ta dana Kiran securitie yana zuwa ta ce masa yayi waje da wanan tana neman tsayar musu da aiki



Sécuriti din ya ce " madame mu je 


Haka tana ji tana gani yayi kokarin tura keyarta tana ta magiyar su saurareta , har ya kusan turota waje wata mata da wani a gefenta da alama sun zo dubiya ne ta tsayar da direban dake Jan su ta fito tana tambayar lafiya?


Securitie din ya fada mata abinda yake faruwa , 


Ta girgiza kai ta bude motar ta zaro kudi ta mikawa Yar Mahaukaciya tana fadin take kiyi maza ki kewaya urgence domin wanan ai urgence ne daga baya kwayi katin Allah ya bashi lafiya 



Yar Mahaukaciya tayi Saurin tsugunawa da dan Mahaukaciya a hanunta tana hawaye ta shiga godewa wanan mata har ta shige mota direba ya jasu sai cikin asibitin ita kuwa da gudu ta mike tayi inda aka nuna mata , tana isa aka tarota aka dorashi saman wani gado na yara suka tura shi 


Suna shiga akace wanan ai tamkar accident dan haka a kirawo Wanda ya kawoshi idan ba haka ba baza'a taba shi ba ( kuji fa )


Wata nurse da gudu ta fito ta yafito Yar Mahaukaciya ta biyo bayanta cikin Sauri 


Suna zuwa 

Docter mai sunan Abdallah ya ce " mai ya samu yaron ?


Yar Mahaukaciya ta ce " ban sani ba 


Ya dan dago idanuwansa ya sauke a samanta domin muryarta mai dadin gaske , a ransa ya ce yarinya ce hakan yasa yace" ina Mahaifiyar sa?


Yar Mahaukaciya ta nuna kanta ta ce " nice Mahaifiyar sa faduwa yayi dan Allah Malan kayi masa magani kar ya mutu 


Docter Abdallah ya ce " Malan ? Sai kuma ya basar ya mike domin gaba daya ji yayi ya kasa musa mata , ya nufi dakin da aka shinfidar da yaron ya ce a shiga dakin tiyata da shi , 


Nan da nan aka shirya shi akayi dakin tiyata da shi cikin gagawa domin yaron har wani shidewa yake , suna shiga docter Abdallah da sauran ma'aikatan suka dukufa don ceto rayuwar Dan Mahaukaciya Bawan Allah 


Gani nayi Docter Abdallah da Sauri ya cewa nurse ta bashi irin abin nan da idan mutun yayi doguwar suma ake dana masa a kirjinsa ,  da gudu ta dauko ta daidaita ya kara yage rigar Dan Mahaukaciya ya murza abin ya dora masa saman kirjin sa , aman shiru kake gani ya kara murzawa ya dora masa cikin karaji ya ce " no ,no  boy ka tashi mana kar ka yi min haka please ba'a taba mutuwa a hanuna ba ya kara murzawa ya dora masa yana kokarin kara murzawar da Sauri wata nurse ta rike hanunsa suka kama suka duba lokacin mutuwarsa 12h da minti 47 


Docter Abdallah ya yi shiru gaba daya jikinsa ya mutu maganar matar nan wato yar mahaukaciya ta fado masa a rai inda take cewa dan Allah ka yi masa magani kar ya mutu , a hankali ya furta i'm sorry , 


Ya fito yana layi yana fitowa Yar Mahaukaciya tayi kuri tana kalon kofar dakin tiyatar sai da gabansa ya fadi ta iso da Sauri tana fadin " Likita ya jikin Dan Mahaukaciya ? 


Da kyar ya tataro nutsuwar sa ya ce " Madame i'm sorry Allah ya amshi abinsa 



Yar Mahaukaciya ta ce " ban gane ba mai kake nufi?


Docter ya hadiyi wani yawu ya ce " ya rasu , 


Yar Magaukaciya gaba daya taji tana kokowa da nunfashinta da kyar ta iya furta ya mutu? Sai luuuuuuuu ta tafiiiiiiiii


     😭😭😭😭😭😭😭😭😭

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                         9



Luuuuuuuu ta tafi kafin ta fadi Docter Abdallah ya tarota ya dagata cimak yayi wani daki da ita ya shiga bata taimakon gagawa cikin kankanin lokaci ta dawo hayacinta tana farkawa ta shiga rusa kuka har muryarta na dishewa , shi kuwa yana zaune yana kalonta yana share zufa domin ji yayi kwatakwata baya iya wata magana , 


Tana tsakar kukanta ta daga kanta sama tana kalon pankar dake juyawa a dakin asibitin tana tunanin ya zatayi da rayuwarta ? Tana kalon Dan Mahaukaciya tamkar Tana tare da mahaukaciyarta , Yanzu ta sanadiyarta aka kashe mata dan Mahaukaciyarta? Ta nisa bata san cewar a fili taci gaba da fadin " shin ya zanyi? Wa gareni? Ina zan kai Dan Mahaukaciyana ayi masa sitira? Wayo Allah gani gareka



Docter Abdallah ya dago kansa yana kalonta ga dukan alamu zancen zuci ne ya fito fili ya lura tana boye wani abu a ranta da alama ta fiya zurfin ciki, to aman mai take nufi da ina zata kai Dan Mahaukaciya? Mai yiwuwa yaron nata ne mai suna hakanan domin da ya tambayeta sunan yaron hakan ta fada, to aman ina babansa? 


Cikin karfin hali ya ce " ina babansa yake ne?


Ta juyo idanuwanta wa'inda suka koma kalar ja tana kikifta ido ta ce " babansa ya mutu , bamu da kowa a garin nan kuma ban san hanyar bola ba 


Ya budi baki zaiyi magana sai yaji karar bude kofa yana juyawa yaga kakarsa ta shigo cikin shigarta ta alfarma ta sha glas na karin gani tana shigowa ta juya ta cewa direban da ya kawota " yaro Kagan shi a nan ai ka juya kawai idan na gama yi masa fadan ya maidani gida KO ya dorani mashin 😌



Shi dai dan ladi direba ya juya yana dariya domin lamarin hajiya Hawaou sai ita , ta shigo cikin nutsuwa ta tsaya ta ce" kai Abdallah ka kiyayeni yanzu dan nayi maka maganar aure shine zaka fice yau baka gaisheni ba? Ai Allah ya taimakeni nasan wajen aikin naka , to ka sani aure ba fashi au ka kawo KO na zabo maka yaro 😏


Docter Abdallah ya taso da sauri a ransa yana fadin wani dan duniyan ya gaya mata yau ga asibitin da yake ? A ransa ya ja dan karamin tsaki haka kawai iyayensa basu takura shi kan yayi aure ba ita tana faman shiga rayuwarsa , ya kamo hanunta ya zaunar saman kujerar da ya tashi sai a sanan taga Yar Mahaukaciya na kuka ta zaro ido ta ce " Ikon Allah yarinya mai akayi miki? KO alurar ce bakya so? Ko dai yaci zalin dinki yayi miki biyu irin yanda yayi min?



Docter Abdallah ya ce " iya dan Allah ki saurara kadan kinga nan fa asibiti ne yama akayi suka barki kika shigo?



Hajiya Hawaou ta ce " gidanku akayi suka barni na shigo, kuma na fada maka ka dena kirana da iya sai kace uwar kaji 


Ya girgiza kai ya ce " kinga wanan yarinyar marainiya ce batada kowa kuma yanzu ta kawo yaronta nan ya rasu shine take kuka domin bata san kowa a garin nan ba ,


Ai hajiya Hawaou na jin haka ta shiga salalami tana kuka ta Mike ta rungume Yar Mahaukaciya tana fadin" kiyi hakuri yarinya dukan mai rai mamacine , ai nima dan makociyata tana haihuwar shi ya rasu kai nayi kukan mutuwar yaron nan domin suna mugun neman haihuwa Allah ya basu kuma ya amshe abinsa kiyi hakuri Allah ya jikansa muje gidana ayi masa sitira idan kin huce sai asan yanda za'ayi aman bazan barki haka ba , kawai ta shiga tatara mayafin yar Mahaukaciya ta dagota KO takalmi babu a kafar Yar Mahaukaciya ta kamo hanunta tana kuka itama tana kukan suka shiga cikin mota Shi kuwa ya koma ciki dan ya dauko gawar dan Mahaukaciya 




Cikin mutunci aka yiwa dan Mahaukaciya sitira harda taro domin Hajiya Hawau mutuniyar mutane ce sosai aka yiwa dan Mahaukaciya adu'a inda mata ke shiga suna ta'aziya domin Hajiya Hawau tayi ruwa tayi tsaki tace jikanta ne daga kauye suka zo Allah yayi masa rasuwa ,


Ita dai Yar Mahaukaciya tana Zaune da zunbulelen hijabin Iya da tazbaha a hanunta tana ja astagfari kawai take ja itama Iya ta fada mata tace ki ringa hailala kina maimaita astagfrullah Allah ya jikansa ke kuwa ya sanyaya miki zuciyarki ya baki dangana, hakan yasa ta koma gefe daya irin yanda ta saba zamanta tayi shiru tana ta jan carbinta tana astgfari hawaye wani na korar wani ,



Konci tashi har an yi cikon satin Dan Mahaukaciya , aman har yanzu sakewa ta gagari Yar Mahaukaciya domin jira take a koreta ta kara gaba dan tasan hakan rayuwarta take KO an Nuna mata so to fa za'a kyamaceta ,



Dawowarsa Kenan daga asibiti ya nufi can cikin gidan su domin mahaifiyarsa tayi kiransa cewar tana son ganinsa , yana shiga ya tarar da ita zaune ta harde kafafuwanta ya karasa ya zauna yana kokarin gaisheta kamar yanda ya saba , cikin sauri ta katse shi ta ce " abdul wai wacece yarinyar nan? Ni dai a sanina dangin ku duk yawancinsu yan camaru ne ya akayi ita wanan na ganta a nan ? Wa ya kawota ne? Meye halakar kakarnan taka masifafiya da ita?



Abdallah ya rasa amsar da zai baiwa umansa domin ita a rayuwarta ta tsani taga an rabe su idan dai mutun ba mai arziki bane tofah ranta baya so , ya ce " am haba mom kinga nima tare na gansu bansan KO wacece bâ fa ,




Hajiya Marhaba tayi shiru can ta ce " naji can ita da jarabarta aman na haneka da shiga sabgar yarinyar nan idan kuwa ba haka ba wly sai na saba maka , kuma karka manta nayi maka mata dan haka ka mayar da hankalinka kanta kaji KO?



Abdallah ya dan Sosa keya ya ce " an gama mom please ki dena rayar da hankalinki ai itafa bazawara ce kingani ai sai bazawari KO?



Hajiya Marhaba ta daga kafadarta irin su ya shafa din nan ta Mike tana tafiya ciki gadara , 


Bayan ta tafi docter Abdallah ya kontar da kansa jikin baban kujerar dake tsakar dakin su ya lumshe idanuwansa ya ce" ina son sanin labarinki beauty ( wato Yar Mahaukaciya ina ruwanka da labarinta inji ni sajida 😏 ) 



Zaune take ta saka kwanon furar da Hajiya Hawau ta dama mata a gaba tana ta tunani , Hajiya Hawau ta dauko karamar kujera tayani tsegumi ta zauna ta ce " to yarinya bani labarinki kuma ki fada mini sunan ki 




Hankalin yar Mahaukaciya ya tashi a ranta ta ce " Nasan idan kema na fada miki sunana Yar Mahaukaciya zau gujeni ne, ni kuwa wani suna zan fadawa iya?






To jama'a ku taya Yar Mahaukaciya zabar sunanta don gujewa tsanar sabuwar family dinta 🤝🤝🤝🤝🤝


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                       10


Yar Mahaukaciya ta gama yanke hukuncin ba Wanda zai kuma sanin labarinta domin idan ta fada kyamarta ake gwara ta boye sirinta ta nemi Mahaukaciyarta a boye daga baya idan ta ganta sai ta gudu da ita ,



Ta dago kanta ta kali hajiya Hawau ta ce " Ni dai Marainiya ce bani da kowa sai Allah ,



Hajiya Hawau ta ce " to shi mijinkin rabuwa kuka yi KO mutuwa yayi?


Yar Mahaukaciya ta ce " mutuwa yayi hajiya , domin tasan idan ta ce rabuwa suka yi za'a nemi sanin KO shi waye dan a nemi yan uwanta ,


Hajiya hawau ta ce " eyah Allah ya jikansa kar ki damu yata kinga daman ni dana daya a duniya Allah ya bani ya aure mata marar mutunci kinga tana can ciki ba ruwanta da ni , yaron ma da yake kulani bakin ciki take kinga kuwa ohon mata Allah ya bani nima yar KO?


Yar Mahaukaciya tayi murmushi a ranta ta ce ki gafarceni hajiya ki gafarceni , 


Hajiya hawau ta Mika mata furar da ta dama ta sha nono mai kauri da cukui sai abin mai take ga siga ta ce " kinga damun Dan Aljana ne wanan kwana biyu bai shigo ba mahaifiyarsa ce bata da lafiya ai har Idrissu ya kamata a gadon asibiti yaki sakinta sai da akayi da gaske 



Yar mahaukaciya tayi murmushi ta ce " kai gaskiya bai kyauta ba sam 


Hajiya ta kara karkata daurin dan kwalinta tace " kyaji mai yi dan Allah kinga ai ke kinsan abinda kike yi aman sauran gaba dayan su sun goyi da bayan a BArta ta samu lafiya ji suke asibitin ci ce , ai sai sun ga uwar bari kafin su yarda da magana ta , 



Yar Mahaukaciya tayi dariya domin du yanda kaso kaucewa lamarin hajiya to fa sai ta saka ka dariyar , 


Hajiya ta ce " KO ke fa to baki fada min sunan naki ba ,



Yar Mahaukaciya ta ce " sunana RAHAMU domin bata manta sunan da Baba tayi mata ba 


Hajiya hawau ta ce " Rahama suna mai dadi To ni dai zan ringa kiranki da Ramatu domin Rahama haka sunan sirikata yake a gaban baban idrisu bazan iya fada ba 


Yar Mahaukaciya ta ce " to hajiya ba damuwa na gode , haka suka wuni suna dan tataunawa Yar Mahaukaciya ta dan fara sakewa da hajiya Hawau domin tana kara janta a jiki 




Washe gari da safe Hajiya Hawau ta shirya tacewa Yar Mahaukaciya ta tashi su je gidan su Dan Aljana su ga jikin babarsa an sakota daga asibitin, 


Haka kawai Yar Mahaukaciya taji bata ra'ayin fitan ta kali Hajiya ta ce " Hajiya ki je ni na karasa aikin mu KO?



Hajiya ta ce " kai Ramatu bakya son yawo kema ga son aiki to ni dai kinga tafiyata sai na dawo 



Yar Mahaukaciya ta ce " a dawo lafiya Allah ya tsare 


Hajiya ta ce " Amin tayi gaba abinta , 


Bayan tafiyarta Yar Mahaukaciya ta zage damtse ta shiga sharar gidan ta share tsaf ta dawo ta zuba cleam ta wanke da ruwa da tsintsiya ta koma ta harhada kayan wanke wanke ta dawo ta zauna ta cire  hijabinta ta kara gyara daurin zaninta ta zauna saman tayani tsegumi ta shiga wanke wankenta 


Ya jima tsaye yana kalonta tana ta wanke wanke yana mamakin kalar fatarta har wani yelow yelow yake sakawa faratunan kafarta dogaye ba kananuwan yatsutsai bane da ita a hankali yayi salama ya shiga 


Ta razana da jin salamarsa ta dago da Sauri tana konce hijab dinta daga kanta ta saka tana amsa salamar sa ,



Idriss ya karaso ya jawo kujera ya zauna kusa da tata , yana fadin sanu da aiki madame wanan aiki haka?


Yar Mahaukaciya tayi murmushi tana kara gyara zaman hijabinta 


Ya ce " ina masu aikin gidan ne?


Ta ce " ai an aiki biyun kasuwa dayar kuwa tana baya tana wanki 


Ya ce " ai kuwa sai an karo muku masu aiki KO?


Yar Mahaukaciya ta dago da Sauri suka yi ido hudu kuwa ta kawar da kanta ta ce " ina ma aikin gidan yake ai ni kadai ma na isa nayi shi 


Docter ya girgiza kansa ya ce " tap ikon Allah ai bazai taba yiwuwa ba hutawa kawai zakiyi 


Yar Mahaukaciya ta ce " hum , a ranta ta ce hutu fa lale KO a mafarki



Ya lura bata cika magana ba aman tana da girmama mutane yana son yi mata tambayoyi sosai aman sosai yake jin nauyin hakan bai san dalili ba haka yayi ta zama har ta gama wanke wanken ya dauke kondon kwanonin yayi kicin da su ita kuwa tayi murmushi ta dauko tabarma katuwa ta shinfida masa ta dauko kwarya da ludayi ta zauna ta a saman yar kujerar nan ta shiga dama furar , shima waje ya nema ya zauna yana kalon yanda take aiki bata da alamun gajiya tana gama damawar sai ga Hajiya hawau ta shigo gidan da salamarta 



Yar Mahaukaciya taje da Sauri ta amshi ledar dake hanunta tayi daki da ita fruits ne ta sauye ta wanke ta jera rabin a frij ta debo wasu saman tire da wuta ta fito tana fitowa taga Hajiyar na zaune saman kujerar tana kara dama wata furar a hanunta , gefenta Idriss ne zaune yana shan wada ta dama masa idanuwanta suka ga wata kafa fara kar cikin wani bakin takalmi mai shegen kyau takalmin uwa na sarakai domin kalar adon sa ji tayi bazata iya kalon mai takalmin nan ba hakan yasa a hankali ta ajiye fruits din a kusan Hajiya Hawau ta Mika hanu tana fadin Hajiya kawo na dama miki mana 



Hajiya hawau ta ce " aa yar gidana wanan damun sai ni da kaina kowa ya dama baya sha sai ni din nan da kike gani ai ta Dan aljana ce da nake baki labari , ta kuma kalon dan Aljana ta ce " Dan Aljana kaga yartawa da nake fada maka 


Bai dago ba bai kuma ce kanzil ba itama haka kawai ta kasa koda dago kanta bare ta kale shi , jin takun tafiyar hils da wani kalar tiraren yasa ta bada hankalinta kan kofar shigowa 



Wata budurwa ce ta shigo ta sha mahaukacin hils mai shegen kyau kai ita kanta abin kalon ce domin haduwa iya haduwa ta hadu ga kamshi tana zubawa batayi  salama ba kawai shigowa tayi sai da taga idriss na zaune sai naga ta saki murmushi ta ce " Brother daman kana nan har momys take neman ka?



Idriss ya dago kansa daga kwaryar furarsa ya dan kaleta yace " sauran kice mata ina nan 


Tayi murmushi bata gaida hajiya Hawau ba bare ta gaisar da Yar Mahaukaciya Wace take kalon takalmin kafarta tana mamakin yanda akayi ta hau saman sa , ta nufi wajen wanan mutumin mai cike da korjini tana zuwa ta saki murmushi ta ce " Honorable barka da warhaka 




Sai yanzu Wanda aka kira da honorable ya dago kansa ya zabga mata harara , da Sauri na furta ya Salam na fadi ba shiri ba ni kadai ba Yar Mahaukaciya kanta gani nayi ta zaro idanuwanta tana kalon wanan bawon Allahn 





Shin wanene Dan Aljanar da Hajiya Hawau ke fada tana karawa? Wacece wanan budurwar da ta shigo meye halakarta da Irdriss? Mai yasa bata gaishe da Iya ba? Muje zuwa daga Yar mutan niger


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                       11


Aunty Amnoor inai miki murnar gama novel dinki *Naga Rayuwa*



Aunty UMMIEXY barka da gama *HISABI* 


Allah ya kara kwarin ido da zakin hanu amin💋💋💋💋💋💋💋💋









Dagowar kan da yayi , yayi daidai da kalonsa da Yar Mahaukaciya tayi gabanta ne ya yanke ya fadi da Sauri ta sada kanta kasa a ranta ta ce " to shi kuwa wanan mutun ne KO aljan? Daman akoy mutane kalar haka? Shi kuwa wanene? 



Muryarsa ta tsinto ya furta kalma uku Wace bata san mai yake nufi da ita ba 


Yana kalon budurwar da ta shigo ya ce " are u crazy?



Ta girgiza kai gwuiwa a sace ta juyo wajen Hajia Hawau ta ce " hi grandma



Idriss ya ja tsaki ya mike da furar sa ya kali Yar Mahaukaciya Wace take ta al'ajabin maganar dan Aljanah  kamar yanda Hajiya ke kiransa da shi ya ce " sister taso ki ga sakon nawa na shige ance mom na kirana 


Yayi ciki Yar Mahaukaciya ta bi bayan sa 



Hajiya Hawau ta gama dama furar kai KO ni sai da ta ban sha'awa irin yanda take daukan ido ta mikowa Dan Aljanah ta kakabe zaninta sai tura baki take tayi cikin dakinta , 



A hankali wanan budurwa ta ja kujera tana fuskantar Dan Aljannah cikin raunananiyar murya ta ce " Mubasshir please manan kayi hakuri ai na gaisheta 



Sai da ya gama jujuya furar yana ta tinanin wanan sabuwar mai aikin ta Hajiya ce ta dauko kwaryar da aka dama masa furar a ciki shi fa yaki jinin yan aiki yana kyankyamin harkokinsu baya son KO kadan su rabi abincinsa gashi kuma furar sai fizgarsa take , maganar Budurwar nan ta maido shi daga tunanin da ya tafi ta ce " *Mubasshir* ka amsa min please  nace kayi hakuri 



A hankali ya dago idanuwansa ya sauke su a saman fuskarta suka yi ido cikin ido da Sauri ta kawar da kanta domin duk tsatsauran halinta bata san ya akayi take shakar hada ido da Mubasshir ba , 


Cikin fadafada ya ce " *Sahla* ki gane ni fa ba zan kwashi marar tarbiya ba , a kulun ina fada miki ki kiyayi rashin kunya , idan baki girmama macen da ta haifi mahaifin ki ba fada min zaki girmama tawa kakar kuwa? Da da ranta nasan har sai kin taka ta domin kince kina kyankyamin tsofafi, ki gane darajar tsohuwar nan da kika raina yasa har nake iya kalonki har nake kula ki kin fi kowa sanin KO wanene ni nafi karfin ajin ki aman ina jin kunyar wanan tsohuwa da nake kalo tamkar kakata ke kuwa Allah yayi miki rahama kina kaucewa , so bara kiji ni bazan lamunci shashancin nan naki ba idan har bakya mutunta manyan ki to fa tsakanina da ke horo ne kawai ba wani Abu 



Cikin tsoro da kalamansa ta ce " I'm sorry honorable nayi alkawarin mutunta ta kayi hakuri please karkayi fushi da ni 




Ya dago kansa yana kalonta gaskiya shima ya san yana son Sahla domin kyakyawa ce ajin karshe , sai dai abinda baya so a tatare da ita raina mutun sam ita ta raina mutane ta tsani ta shiga lamarin mutun indai ba ta yarda da shi ba hakan kuwa harda kakarta Wace ta haifi mahaifinta ,




    Wacece Sahla?????


Sahla itace auta a wajen hajiya Marhaba wato kanwar Idriss , Hajiya Marhaba tayi ta samun ciki tunda yarintarta sai dai cikin ikon Allah cikin yana barewa cikin haka Allah ya bata cikin idriss ta haifi abinta cikin koshin lafiya , bayan sa ma sai da tayi barin biyu kafin ta samu cikin Sahla , tun bayan haihuwar Sahla shikenan tamkar anyi ruwa an dauke Hajiya Marhaba bata kuma samun wani cikin ba hakan yasa suka dauki son duniya suka dorawa matar manya lakabin da Sahla tayiwa kanta Kenan , tarbiyar Sahla ba kwaba ba tsangwama , makarantar sai taga dama take zuwa , kawayenta duka yayan manya ne , Sahla ta kasance Doguwwar mace fara ga shegen kyau masHa Allah ga iya Jan aji ga yanga kai Sahla da ba dan halayenta ba sai nace goma ce cifffffff sai dai kashhh irin wanan gata da ta samu ya saka bata ganin kan kowa da gashi , baba KO karami zata takaka san ranta domin tasan abinda ta taka



Abinda ke hadasu fada da Hajiya Hawau irin yanayin shigarta da kuma sangartar ta idan fa hanya ta hado su sai dai ita ta rakube ta fice sanan ita ta fice hakan yasa sam basa jituwa suke yar tsama , hakan nayiwa Hajiya Marhaba dadi domin taki jinin sirikar tata abu ya hana tayi maganin ta Elahj domin yana matukar kaunar jangom lakabin da take kiranta da shi Kenan ( ya Allah ka tsare mu amin )


Abu daya yake saka Sahla dan sadakawa soyayar Mubasshir da ta wayi gari ta tsinci kanta a ciki tsundum hakan yasa take dan rage wasu abubuwan a cikin halayenta domin shi bazai lamunci rashin mutuncinta ba idan kuwa ta rasa shi tasan ta tafka asara ( tofah )





      Ci gaban  Labari



A hankali ya aje furar domin sai ya deba da niyar kaiwa bakinsa sai ya mayar da ludayin yana matukar son ya sha furar nan kyankyaminsa ya hana shi ya sauke ajiyar zuciya ya mike yana saita agogon hanunsa ya dan dubi Sahla kasa kasa ya ce " ki kaiwa hajaju furar nan ki fada mata na koshi , sai tomorrow ya juya ya saka kansa gaba yana tafiya cike da isa tamkar dan Sarki 



A hankali tana kalonsa har ya fice daga harabar gidan ta sauke nanauyar ajiyar zuciya ta lumshe idanuwanta ta ce " i love you My man i  really love u  ta kuma lumshe idanuwanta ta ce " zaka soni ne a hankali domin nasan dan ni kadai aka yi ka , ta Mike ta saka kafa ta shure furar harda hararan kwaryar tayi waje ta nufi motarta dan tasan a yanzu ya bar unguwar tana iya fita 










😌😌😌😌😌😌😌😌😌


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*










                       13


Karfe biyar da rabi Mai gadi yayi salama ya gaida Hajiya Hawau ya sheda mata ga Mutumin da Idriss yace a bari ya shigo idan ya zo ,



Hajiya hawau ta amsa masa ya juya inda aka yiwa Malan yunus shinfida a banban falon dakin Hajiya Hawau a nan za su ringa yin karatun kulun har ita hajiyar ,




Cikin ikon Allah kulun sai Malan Yunus Ya zo da yama sunyi karatun arabi da Yar Mahaukaciya yau har sati uku Kenan sosai take fahimtar hukunce hukunce na musulunci gaba daya , domin kowace rana akoy abinda zasu karanta sanan a kulun sai yayi mata wa'azi sosai sosai , sai yanzu ta san cewar itama mutun ce mai daraja domin an haliceta a jinsin bil'adama , idan yana bata tarihin manzanin mu da irin yanda suka sha gwogwormaya dan yada adinin musulunci sai taji wani irin shaukin adininta taji wata irin soyayar adininta taji haushin shekarun da ta shafe a bola bata zuwa ta saurari karatu koda yaran na tsokanar ta ,  



Bangaren Malan Yunus yana matukar jin dadin karatu da Yar Mahaukaciya domin idan yana koya mata karatu tana bada hankalinta gaba daya ga saukin daukan harda domin akoy tambayoyi sosai kan du abinda ya koyar da ita 



Yau ta kama alhamis tun da safe Yar Mahaukaciya tayi aikace aikacenta ta gama ta dora girkin su karfe biyu ta sauke komai har jus jus dinsu da suke hadawa ta gama ta saka a frij Hajiya Hawau sai aikin sanu take jera mata , sai da ta gama taje tayi wanka ta fito ta daura zaninta ta zira rigarta na atampa ta fito ta nufi falo wajen hajiya Hawau 



Tana shiga ta zauna kasa , saman kapet wanan na daya daga cikin al'adunta sam bazaka ganta saman kujera idan baban mutun na sama ita sai dai tayi zamanta a kasa koda kuwa ka tashi tana matukar jin kunyar hawa wajen da ka tashi 




Hajiya Hawau ta dago kanta daga kalon da take tace : taso maza yau na kunce miki kitson nan da na yi miki uwa mai takaba 



Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta matsa kusan Hajiya Hawau ta kunce daurin dan kwalin kanta Hajiya Hawau ta kama tsifa 


Suna tsaka da tsifar Docter Idriss yayi salama ya shigo cikin falon da Sauri Yar Mahaukaciya ta shiga kiciniyar kwace kanta don ta rufe domin KO hijab babu a jikinta gashi rigarma ba zumbuleliya bace 



Hajiya Hawau ta kama baki ta ce " ke zauna min kaji min yarinya to dan wanan dan neman ya shigo shine zakina kokarin ganin kin kwacen kanki? To ba yayanki bane shi din? 



Idriss ya zauna ya ajiye jakarsa baka da alama daga office yake , ya dago kansa ya ce " Iyancy mitar mai kike yi ne?



Hajiya Hawau ta turo daurin dan kwalinta gaba ta kankance idanuwa ta nuna masa yatsarta ta ce " Kai wanan yaro ka kiyayeni , ka FITA a idona na rufe aradu zan kai kararka wajen ubanka dan ni din nan da kake gani daidai nake da kai 




Idriss ya bushe da dariya har yana rike ciki ya ce " haba Madame haba madame mai yayi zafi kiyi hakuri kin sani sarai ke din ta kudin ce KO?




Ta kuma turo bakinta , Yar Mahaukaciya tayi murmushin diramar Hajiya da jikanta ta dan juyo fuskarta ta ce " Yaya ina yini ya aiki 



Idriss da sai yanzu ya lura da ita domin da ya shigo ya ji dai hajiya Hawau na mita aman bai san mitar mai take yi ba , ya amsa salamarta idanuwansa a saman tarin gashin kanta da ake kuncewa 


Ya ce " Hajiya wai atach ne yar taki tayi?



Hajiya Hawau ta ce " Allah ya kiyashemu da Karin gashi, ai gashinta ne ba wani atach 



Idriss ya zaro ido ya ce " Aman ya naga uwa na nasaru wanan kalar gashin ai ba na hausawa bane kinga fa ja ne ga tsayi aman kina yi masa shampo KO ? 




Yar Mahaukaciya ta dago kanta idanuwanta yana mage ta saukesu a fusfar idriss ta ce " YAYANA kuma mainene shampo?




Idriss ya hadiyi wani yau da ya tsaye masa a makogoronsa a ransa ya kara yarda tabas Ramat ba bahaushiya bace to aman wai ita wace yare ce?



Ya ce " hajaju ki bar kan nata mana na kaita saloon a wanke mata idan mun dawo sai ki dadaure mata 



Hajiya hawau da daman hanayenta sun gaji sosai ta ce " to dan Albarka Ramatutu tashi ki dauko hijabinki ku tafi a wanke miki da abin wankewa kinji ?




Yar Mahaukaciya ta mike tana dan jan rigarta dan ta rufe mata jikinta aman ina da Sauri Idriss ya kawar da kansa daga dubanta yana fadin a'uzubilah yana kawar da kansa ,




Ta dauko zumbulelen hijabinta ta zira Idriss ya bar jakar Ma'aikatan NASA a nan suka shiga mota 



Daidai zasu FITA daga harabar gidan sai ga Sahla da kawarta Alisha sun shigo suna shan kidan su ran Sahla ya gama baci domin wanan ai zubar mata da mutunci ne Idriss yayi niyar yi ya zai dauko wanan bagidajiyar a motarsa kuma gashi kawarta Alisha ta gani ga irin yanda Alishan ke maseefar son Idriss din 




Alisha ta waigo ranta a bace ta ce """"""""""




           Love u


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*











                       15



hajiya hawau cikin bacin rai ta nuna Sahla da hanu ta ce " ke yarinyar nan kin fiya neman magana , shin yaushe zaki fara mutuntani ne? Ki tuna ni fa na haufi mahaifinki aman kashinki yafini daraja , ta girgiza tana kama hanun Yar Mahaukaciya ta juya ta ce " Idrissu karka ce mata komai ka barta duniya ce , ta kuma juyawa wajen Mubasshir da ita ya kurawa ido bai taba ganinta a irin wanan halin ba tabas KO wacece wanan tanada baban mukami a wajen Hajiya , 



Hajiya ta hade hanayenta biyu tana kalon sa tace" Yarona dan Allah karka hukuntata dan ta batamin ka barta ta hukunta kanta da kanta , ka BArTA ta gane cewar mutun yafi kudin nan nasu daraja , ta ja hanun Yar Mahaukaciya suka nufi kicin 




Gaba daya jikin Sahla yayi sanyi aman fa batayi nadamar abinda ta aikata ba 



Idriss da tunda ya tare Yar Mahaukaciya ya shiga wani yanayi Wanda eh lale bazai ce bai taba shiga ba aman wanan kam yafi na kulun yana bukatar yin nesa da mutane dan ya dandance abinda ke kokarin damunsa ya mikawa Mubasshir Hanu ya ce " friend sai mun hadu nayi ciki 




Mubasshir ma ya mike ya ce " muje tare kasan inada abun yi 




Haka suka tafi suka bar Sahla nan zaune duk irin kwaliyar da ta sha da kanshin da take zubawa duka suka tashi a banza domin Wanda tayi dominsa KO kalon banza bata ishe shi ba , ranta ya kuma baci ta kara kudurtawa ranta sai tasan wacece wanan yarinyar mai kama da aljanu sai ta binciki lamarinta 




Shigar su Hajiya Hawau kicin Yar Mahaukaciya ta dakata 



Hajiya Hawau ta juyo tana kalonta , Yar Mahaukaciya ta duka gwuiwoyinta a kasa cikin shashekar kuka ta ce " Dan Allah kiyi Hakuri Hajiyata ki dena fushi dan an bata min ki sani fushinki na Konan raina kakata bani da kowa sai Allah sai ke kiyi hakuri ki yafe mata 




Hajiya hawau ta tsura mata ido ba komai ya birgeta ba sai kalmar kakarta da Yar Mahaukaciya ta furta a hankali ta saka hanayenta biyu ta dagota daga tsugunin da tayi ta ce " ba komai jikata na hakura na daina fushi , ki tayani da adu'a Allah ya karkato min da hankalin dana kaina 





Yar Mahaukaciya cikin fuskar tausayi ta ce " nayi alkawarin saka aban gidan nan a adu'a Allah ya ganar da shi 





Hajiya tayi murmushi ta ce " mû je kinga Dan Aljannah naji tashin motarsa bai sha fura ba , karbi ki saka min a frij nasan zai dawo gobe sai na dama masa 






Yau tunda safe gogo Fatima kawar Hajiya Hawau ta turo yaro a fada mata jikanta mai wata shida ya rasu , Hajiya Hawau harda kuka ta dauko hijabinta zumbulele ta zumbula ta dauko goronta da carbinta ta yiwa Yar Mahaukaciya salama tana fadin sai dare idan tana son ganinta mai gadi ya kaita , ta kama hanya ta shiga adaidaita sahu tayi tafiyarta 




   


Zaune yake a office yayi shiru yana nazari ya zama wajibi ya koyawa yarinyar nan hankali yana matukar sonta yana so ta san darajar mutane domin shi mutumin mutane ne , tabas zai kai kudin aurenta aman fa zaiyi iya yinsa dan ta gane cewar mutun rahama ne , yayi murmushi da ya tuna irin abinda zai hadata da shi abinda tafi tsana ne wato tsofafi , yayi nisa da tsare tsarensa a cikin zuciyar sa kawai fuskarsa ta hasko masa furar Hajaju ba shiri ya hadiyi yau ya mike ya shiga tatare wayoyinsa dan kuwa yayi missing din furar nan yau har kwana 24 bai sha ba da jiya ya sha aka bata masa rai yayi tafiyarsa , 







Tunda Hajiya Hawau ta tafi Yar Mahaukaciya bata zauna ba sai da ta wanke gaba daya kayansu masu dauda ta kai bayan gidan ta shanya , ta dawo ta dauki tsintsiya ta wanke tsakar gidan ta koma wajen shukar mangoron gidan ta share tas ta kwashe ta dawo ta kuna tiraren wuta mai dadin kanshi sanan ta shiga bayi ta kuma yin wani wankan ta dauko zani na sabuwar atamparta ta daura ta dauko jar Riga ta saka ta daura dan kwalin zanin ga Jan kunshinta da ta kunsa ya fito yayi shar da shi batayi wata kwaliya ba KO mai bata murza ba domin yanayin garin da dan zapi zapi ta fito ta saka silifas dinta ta shige kicin ta shiga kiciniyar hada dan jus a Kofi dan kuwa yau baza tayi girki ita kadai ba , ,, bayan ta hada ta dawo wajen da ta wanke ta shinfida tabarma baba ta zauna ta saka cokali a cikin kofin ta fara shan fruits salat dinta ,

 




Cikin takun kasaita ya shigo cikin gidan da salamarsa cikiciki yanda ya saba , Yar Mahaukaciya kam bata ji ba hakan yasa bata dago kanta ba aman hancinta ya jiyo mata kanshin Dan Aljannahn Hajiya , kasa kasa ta kali kafarsa ta ga cikin takalmi kafa ciki ne yake tafe gabanta ya fadi domin Hajiyar bata nan yanzu budurwar sa zata zo ta shifka mata rashin mutunci ,




Karasowa yayi yana dan kalonta a ransa ya ce " Ashe kunshi nayiwa wasu matan kyau , shi bai taba ganin kunshin da ya birge shi kamar wanan ba , Yar Mahaukaciya ta dago kanta da tsoro tsoro ta tsura masa ido , ita kawai mamakin gashin kansa take uwa mace 





Cikin fada fada ya ce " Meye




Yar Mahaukaciya tayi gagawar sada kanta kasa kunya ta rufeta a ranta ta ce " baki iya kalo ba , Yar Mahaukaciya baki iya kalo ba , aman a fili ta ce " Bata nan Hajiyar




Ya yatsina fuska ya ja kujera nesa da ita ya zauna , a ransa yana fadin melodius , kuma wani bangaren na zuciyarsa ya ce , ina ruwanki da ni 😌




Ya kusan minti ashirin a zaune bai ce mata ufan ba itama ta kama bawan Allahnta tayi shiru , can dai ta mike ta shige cikin falon ta dauko furar ta debo kindirmon mai zaki ta dauko cikui uku masu shegen laushi ta hado da yar madarar ta fito inda ta shinfida tabarmarta ta nemi waje ta zauna ta jera kayan a gabanta tayi zaman makaranta ta dauko kwaryar ta zuba furar da nonon ta maida hankali ta dameta sai da ta damu gaba dayanta ta zuba madarar nan sanan ta saka hanunta a ruwa da sabulun dake gefe ta wanke hanunta ta dauki cikui din nan gaba daya ta cicira shi a ciki ta zuba dan siga ta motsa , nan da nan man ya hayo sama furar ta fara sheki ,


Tunda ta fara dama furar ya kura ido yana kalonta kwarai ya gamsu da tsaftar yanda aka dama furar ganin ta mike yasa ya kawar da kansa , a hankali ta rufe kwaryar furar ta shiga kicin ta dauko karamar kujera ta fito tana taku cike da tsoro ta kawo kujerar gabansa ta ajiye ta juya ta dauko furar da wani ludayi wankake ta dora saman murfin furar ta karasa gabanta na faduwa ta ajiye saman kujerar sanan ta shige falo tana sauke ajiyar zuciya a ranta ta furta tasan ba sha zaiyi ba 





Tofah Mubasshir ya zubawa kwaryar furar ido abinka da idan Abu na birge mutun har kanshinta yake ji shawara yake da zuciyarsa shin zai iya sha kuwa? 






Ni zan sha 😋😋

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





*This Page Dedicated to Aunty QUEEN MERMUE, Aunty NAFEE ANKER and AUNTY HALILOSS*




                   16


Ya jima yana kallon kwaryar furar sai ya mika hannu zai dauka sai ya maido hannun nasa , ganin dai ta shige d'akin bata fito ba yasa ya Mika hannu ya bude furar ya saka ludayin cikin nutsuwa ya kara motsata ya debo a cikin ludayin yayi bismillah ya kai bakinsa , bai san sanda  ya lumshe idanuwansa ba , ya d'auko k'waryar gaba d'aya Kamar Wanda wani zai warce masa ya maida






    

  Wanene *MUBASshir* ?



D'a d'aya tilo ga Marigayi Elhaj Mubarak Balarabe Mai farin gida , Elhaj Mubarak bai ta6a siyasa ba babban d'an kasuwa ne yana harkar kayan larabawa abayoyi , siga kantu, tiraruka , zamzam inda ya gaji wanan sana'ar wajen mahaifinshi , Matarsa da'ya tilo Hajiya Fad'imatu ya ga sarkin chadi , sun kai shekara goma sha biyu da aure har ta kusa shiga ménopause Allah ya azirtasu da cikin Mubasshir , abin nema ya samu sarkin chadi gaba daya ya nemi alfarmar su koma kasar su har ta haihu irin ganin girman su da Elhaj Mubarak yake yasa bai musa ba suka tatara suka koma , cikin ikon Allah tana rainon cikinta cikin kulawa da d'umbin kauna ga mahaifinta da kuma mijinta harma da al'umar garin , cikinta ya kai wata tara da kwana bakwai ta haihu ta sami da namiji cikin tsananin murna da godiya ga Allah subahanahu wata'ala Elhaj Mubarak yayiwa Yaron huduba da sunan Mubasshir , sosai aka sha shagalin bikin haihuwar Mubashir inda Mahaifin Hajiya Fad'imatu yayi Kiran Elhaj Mubarak ya bashi wata akwati mai dan girma da wani katon kwad'o a jikinta yace masa wanan a bari sai Mubasshir ya girma a bashi sako ne daga kakansa ,



Cikin girmamawa Elhaj mubarak yayi godiya da fatan Alkhairi suka juya Nigeria yaci gaba da harkokinsa na neman kud'i da gine gine na gidaje da sunan D'ansa tilo Mubasshir , 


Mubashir nada shekara shida suka shirya da mahaifansa suka d'aga saudiya sukayi Sallah daga kasar saudiya Mahaifin Hajiya Fad'imatu tsoho mai ran karfe da mijin Hajiya Fadimatu wato Elhaj Mubarak suka shirya tafiya Chine daga nan su komo Nigeria ,


Ranar da zasu tafi sai da suka raba dare suna hira duk rabin hirar jawabi ne Mahaifin hajiya Fad'imatu ke yi musu ita da mijinta , haka kawai take jin wata irin kaunar mahaifin nata Wace bata taba ji ba , har lokacin tafiyarsu yayi , a filin jirgi ma sai yayi gaba sai ya dawo ya kuma d'ora hanunsa a saman kanta ya ce " Allah yayi miki albarka 



Itama tayi murmushi ta ce " amin Abu , haka mijinta ya d'auki yaronsa yayi ta sumbatar goshinsa yana saka masa albarka hardai aka fara Kiran sunaye ya ajiye shi yayi mata bankwana , 


Jirgin ya fara shawagin tashi sun dan daga sai ji kake bam wani irin kara Wanda duk jama'ar wajen suka tsorata wato jirgin da su Elhaj Mubarak ke ciki ne ya kama da wuta inda pilot din yayi yayi ya tsayar da jirgin abin ya faskara , gaba daya mutanen cikin jirgin Allah ya amshi ransu ,

Mutuwar nan ta girgiza Hajiya Fad'imatu ba ita kadai bama ta girgiza mutanen lagos da chad da kuma makah , Allah ya sa sun huta 


Bayan rasuwar su sarkin Makka ya rike Hajiya Fad'imatu sai da yaga ta zama normal ya gamsu da ta hakuran sanan ya yarje mata ta koma lagos domin chadin bata da kowa mahaifiyarta ta dade da rasuwa yan uwa ba wani jituwa suke ba haka kuwa mijinta maraya ne GABA da baya ita kuwa bazata iya rayuwa a kasar makah ba tafi son tazo ziyara , kuma tana son ta koma gida KO don ta kula da dukiyar dan Marayanta Mubasshir , Sarkin Makah yasa akayi kiranta ya shaida mata bai hanata tafiya ba aman ta bar Mubasshir ya sauke alkur'ani domin yayi nisa a karatun hakan yasa ta barshi a wajen uwar gidan sarki Abdulrahman ita kuwa ta juya gida 



Mubasshir nada shekara tara ya sauke alkur'ani mai girma , a shekara goma ya rubutashi da hanunsa , sanan litatafen musulunci ba wanda baya kokarin ganin ya hadace , kuma ga karatun boko sosai yana samun ci gaba 



Mubasshir nada shekara ashirin da hudu har ya kamala karatunsa na boko idan ka Ganshi sak sufar larabawa ce da shi ga yalwar gashi baki sidik ga tsayi gaskiya Mubasshir Allah yayi masa tsararen kyau 


Yar gidan sarki abdulrahmane ta mugun kamu da kaunar Mubasshir wato Mubinah Aman ina shi a yanzu yafi son ya koma gida domin Mahaifiyarsa yanzun ta fara gajiyawa kuma ga aboki da yayi Idriss yana mugun kwadaita masa rayuwa a Nigeria duk da Makah karshe Kenan aman garin mahaifiya yafi komai dadi hakan yasa ya tada Bali dole sai da aka shirya kaurowarsa Lagos unguwar dolar sunan unguwar tasa domin gaba daya gidajen unguwar gidajensa ne sai daya daya irin tsafin ginin nan na wasu aman sauran duk nasa ne inda gwomnati ke hayar su .



Dawowarsa Nigeria sosai yaji dadinsa domin yanayin kasar ya birge shi Mahaifiyarsa tayi murna sosai inda ya kama kasuwancinsa yaci gaba da yi , sanan yayi kaka wato Hajiya Hawau domin a rayuwa daga Hajiya Fadimatu sai wanan tsohuwa domin yana jinta sosai a ransa kuma a wajenta ya idasa kwarewa da hausa sanan dalilin girmanta da idanuwansa ke gani yasa yake kula jikarta Sahla don ba dan ita ba sam bazai saurari Sahlan ba don kuwa ita din bata cikin tsarin kalar matan da yake so , sam bata birgeshi sai dai dan dole don kuwa KO mubina da ta tafi tsere ta dan fita cikowa ( to fa 😳 )














           Ci gaban labarin




Taku har kulun ..........sajidah

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*




   





                     17

Dedicated to ♻ *EXCLUSIVE  Forum* ku gane ina yinku irin da yawa din nan , 


*Ummy xeey*

*Aishan umma*

*Ruksad*

*Nabilancy*

*Bébé'arth*

*Phertimer Umar Abdallah*

*Aishat À muhd*

*Réal khady*

*Meelart Ahk*

*Sardy bash*

*Ummu khady*

*Billy Ladan*  da da da ,,,,........,,,,,, da duk sauran da ban zano ba jinjina gareku *Muah* 







              Ci gaba




Yana tsaka da shan furarsa yaji takun takalmin Sahla ta nufo cikin gidan a ransa ya ce " oh Ashe taga zuwana KO wa ya fada mata , ? Wata zuciyar ta ce masa kanshin tiraranka manan tace ta shi take gane idan kazo ,, yana tsaka da tinanin yaji salamarta ya dago kansa a hankali ya ce " Amin wa'alaiki salam warahamatulah Sahla 



Tana mugun jin dadin idan ya kama sunanta domin ji take duk duniya ba Wanda ya kaishi iya furta *Sahla* har wani sanyi sanyi take ji idan ya furta , cikin nutsuwa ta dauko farar kujera ta aje kusan sa ta zauna , kasa kasa yake kalon shigarta doguwar Riga ce ta atampa da wani zungureren takalmi mai kyau a kafarta sai dai ta tafi zumbal ba kibar komai ba inda ya dan ciko ya sauke ajiyar zuciya da yayi arba da jagirar da ta ja baka a goshinta domin harga Allah sai da ya tsorata 



Cikin wata murya mai dadin sauraro ya ce " ki dena wanan abin a goshinki yayi yawa 




Sahla tayi murmushi ta ce " huby a saloon fa akayi min 




Cikin basarwa ya ce " basu iya ba 



Ta kuma yin wani murmushin a ranta tace mutun sai shegen kushe mutane aman a fili tace " to zan dena  




Yayi murmushi da yasa ta kuma narkewa ya ce " Masha Allah Allah yayi miki albarka 




Tayi far da ido ta ce " Amin , aman a ranta tana fadin sai kace ubana ka ringa saka min albarka duk sai na rabaka da wanan shegiyar akidar ta mahaifiyarka ta saka albarka duk motsin da za'ayi 




Mubasshir ya ce " ina son muyi magana da ke mai mahinmanci 




Sahla ta ce " toh muje cikin gidan mom mana ai yafi siri KO?




Mubasshir ya ce " no muje cikin falon Hajiya hankalina yafi konciya da nan din 



Ta mike cikin yanga tayi gaba har ta kusan shiga ta waigo ta Ganshi a zaunan ta juyo domin tasan abinda ya hana shi tashi ta dauki kwaryar furar tasa ta yi ciki , yayi bismillah ya mike yayi cikin shima 



Suna shiga ta kara kakabe masa wajen da zai zauna ya karaso ya zauna ta juya ta nufi dakin Yar Mahaukaciya Wace ta gama sallah kenan da zumbulelen hijabinta mai hanu kalar blue mai duhu fuskarta ta kara haskawa a cikin hijabin , tana shiga ta ja tayi tsaye tana yatsina , taso taga wani abin fada sai dai bata ga komai ba domin dakin tas a gyare ga kanshin turaren wuta da yake ta ja tsaki ta ce " Ke yar talakawa tashi maza ki kawowa mijina abin motsa baki domin shi baya kyankyanin tsohuwar nan kiyi maza ina jira , ta juya kwas kwas ta koma falon bata cire takalmin kafartata ba 



Yar Mahaukaciya ta mike tana fadin daman na sani yau tawace ta sameni , ta fito cikin nutsuwa ta nufi kicin din falon inda suke ajiye jus jus kalakala ta bude frij din ta ja ta tsaya , ita dai bata san wani kala yake sha ba ta rasa wane zata dauka kawai ta rintse ido ta dauko guda exotic karami dan naira dari uku ta dora saman faranti ta dauko abin zubawa ta juyo tana tafe tana adu'ar Allah ya taimaketa kar tayi laifi , ta kusan isowa cikin falon taji Sahla ta kwala wani ihu ta shiga rawa tana ta kakaba dariya Yar Mahaukaciya ta ja daidai kapet din ta tsaya ita bata karasa ba ita bata koma ba 




Sahla cikin murna ta ce " wai dan Allah da gaske kake zaka aure ni? Dan Allah yaushe ? Wayo dadi kasheni Ashe daman kana son nawa?




Mubasshir ya girgiza kai yana kalonta uwa zautata sai ihu take wai na murna ne  




Tana tsaka da murnar tata ta waigo ta ga Yar Mahaukaciya ta zuba mata manyen idanuwan nan nata ya na mage tana kalonta saida gabanta ya fadi dan kuwa ba karamin kyau taga tayi ba cikin bacin rai na ganin jus din da ta dauko ta nufeta ta kifeta da mari cikin fada ta ce " ke jakar ina ce? Ki rasa jus din da zaki daukowa Honorable sai wanan? To yayi mai da jus din dari uku? Ke dan kin saba shan sa sai ki kawowa mijina? To bari ki ji KO karena yafi karfin ya sha kalar jus din nan bale Honorable 




Yar Mahaukaciya da tunda ta mareta ta saki farantin gaba daya kayan saman suka zube kasa tayi Saurin tsugunawa tana kwashewa gaba daya jikinta na kyarma 



Muryar Mubashir ta sakata dago da kanta cikin gagawa domin bata taba jin muryarsa a haka ba 



Mubasshir ya ce """""""



😟😟😟😟😟😟😟😟😟😟

[9/20, 13:53] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





            18


Mubashir ya ce " ki guji batawa mutun rai a duk inda kike kiyi kokarin ganin kun wanye lafiya da mutun , ya juya wajen Sahla ya ce" ki je ki kawo min kalar Wanda kike si na sha din , Sahla ta juya tana matukar mamakin canjinsa na lokaci daya da  da ne Hasan sai yayi mata fada tayi murmushi ta ciro wayarta dan tayiwa kawarta albishir mai dadi 


Bayan tafiyarta ya dan kali wajen Yar Mahaukaciya Wace ta sala hanunta cikin kwalbar nan tana tsincewa tana ta hawaye domin ta tsorata da  fadan da Sahla da mijinta suka yi mata a fada mana wanan ai shine a dakeka a hana ka kuka yanzu da hajiya tana nan ai da bata bari sun yi mata wanan wulakancin ba , aman ba komai zata kara hakuri har Allah ya bayana mata Yar Mahaukaciyarta su tatars su nemi wata bolar su domin kuwa konciyar hankali yafi kudi , 


Mubashir ya sauke ajiyar zuciya ya danyi murmushin abinda yake sakawa a ransa daidai nan muryar Malan yana salama Yar Mahaukaciya tayi Saurin dago kanta tana kalon kofar ta amsa salamar tare da yin kicin da sauri ta fito tana goge hanunta da tsuma ta nufi kofar falon ta bude sai ga Malan yunus yana murmushin sa 


Yar Mahaukaciya cikin murnar ganinsa ta duka har kasa ta ce" Marhababika Malan ina yini an zo lafiya? Ya hanya?



Malan yunus yayi Murmushi ya ce" Lafiya lau Rahama ya na sameki ya kuma gida?


Ta ce" lafiya Alhamdulilah 


Ya ce Masha Allah , Masha Allah , daman nazo na shaida miki zamu mayar da karatun mu da dare domin mai gidan yayi kirana ya fada min ya sama miki wata makaranta ta boko ita kuwa wuni ake a can , kin san kowane yana da anfani dan haka sai a maida hankali Allah ya kama mana 



Yar Mahaukaciya cikin jin dadi domin harta manta marin da aka gaura mata ta ce" Alhamdulilah Allah abin godiya 


Suka yi salama da Malan Yunus ya juya KO cikin dakin bai shiga ba dan kuwa sunyi da idriss sai na dare kuma daga gobe zasu fara , 


Ta Mike ta rufo daki sai murmushi take dokawa kuncinta na lobawa suka yi ido hudu da Mubasshir Wanda tunda ta bude dakin ya tsura mata ido , suna hada ido ya kawar da kansa a ransa ya ce" who is she??????? (Entouka i don't know)


Cikin nutsuwarta ta raba ta gefensa tayi shigewarta dakin hajiya ta rufo tana adu'ar Allah ya kawo hajiya lafiya tayi mata albishir 


Sun jima shi da Sahla suna zance ba laifi yana observing dinta idan tayi tayi sai ta tambaye shi ya fahimceta? Shi kuwa sai ya gyada mata hakan kuwa sam baya damunta domin ta saba da rashin maganarsa ita dai ba aikin bokan mamarta ya ci bâ; maganar ma zai koya gaba gaba ( to fa )



Karfe shida da rabi ya mike domin yaga alamar Hajiya ba dawowa zata yi ba suka fito tayi masa rakiya har wajen motarsa ya shige ya tafi ita kuwa ta nufi wajen mahaifiyarta dake jiranta su tatauna

[9/20, 13:53] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*






                19


Tana shiga Hajiya Marhaba ta ce " tun dazu ina zaune ina zuba idon ganin kin dawo fada min nawa ya ce za'a kawo kudin tambayar 



Sahla ta ce " Momy bamu yi wanan maganar ba kin sani sarai tuwon girma miyarsa nama kin san abin mamaki za'a kawo mana ya ce fa a cikin satin nan yake so a kawo komai tunda na fada masa Dad zai dawo gobe kinga kawai sai ayi ayi a amshi kudin muma mu shiga shirye shiryen mu 



hajiya Marhaba ta ce" Ohk tohm ai ba damuwa sai muyi jiran dawowar Elhajn 



Ba Hajiya Hawau ta dawo ba sai karfe Takwas Idriss ya biya ya daukota suna tafe yana mitar ta bar yarinya ita kadai a gida tun tana kyale shi har tace" yo to kaji ubana ai sai ka kawo min duka , yanzu ayi mana mutuwar ka hana ni zaman makoki dan kin Allah? To KO ubanka bai isa ya hanani balatana kai ehe , nan da jikana ya rasu har kwana tayi a gidana tana tayani jaje dan ita ta isa da iyalanta ba Wanda ya bi sayunta ya titsiyota a gaba ya korota gida sai ni da aka raina , ni dai Idrissu ka fita a idona na rufe Aradu tohm 



Idriss yayi gum da bakinsa sai a lokacin yayi mata  maganar ya samawa Yar tata makaranta har an gama uniform dinta da komai sai dai direct secondry ya kaita aman da masu yi mata lesson dan dai kawai ta kara wayewa ne ta san wani abin 


Hajiya ta washe baki kamar ba itace yanzu take fadan an dameta ba ta ce" Allah yasa ka gama da duniya lafiya yanda kake kokarin faranta min ni da yata Allah ya baka mai faranta maka Allah ya jikan kakanka kuma sai hawaye aka ci gaba da fadin sak irin halayensa ne ka dauko Allah ya sa ya huta 



Idriss ya gumtse dariyarsa don kuwa lamarin na Hajiya yanzu dariya yanzu kuka kai Allah ya sa muyi tsufa mai anfani , ya Mike yayi mata salama ta rufo dakin nata ta kashe komai itama ta yasu sai barcin gajiya .



Tunda asuba bayan sunyi sallah Yar Mahaukaciya tati wanka Hajiya ta miko mata kayanta dogon wando ne da riga daidai gwuiwa da fararen safa kayan ma farare  ne tas sai bakin hijabi mai hanu da kuma bakin takalmi mai dan tudu mai igiya , makarantar ta yayan manya ce shima ta kan Mubasshir ya bi aka dauketa sanan aka daukar mata malaman da zasu kula da harkar karatun ta ya kasance tayi gagawar iya turanci KO test baza'ayi mata ba dan ya fadi gaskiya bata iya komai ba .


Cikin minti talatin ta gama shiryawa ta daure gashin kanta da kyar ta saka hijabin Wanda yake da tsayi sosai domin har ya fi rigar tsayi ta juyo cikin nutsuwa ta fito wajen Hajiya Hawau da ta gama mata abin kari da kuma zuba mata wani a kwano ta saka mata a jakar da kudin abinci idan ta cinye wanan abincin , tana fitowa ta gaisar da Hajiya 


Hajiya ta ce" kai kayan nan sun karbeki Ramatutu wly sunyi miki kyau nasan duka sai kinfi yaran kyau 



Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta ce" Hajiyata kings hijabin harda wajen fitar da hanu 



Hajiya ta ce " kema kya fada zamani , tashi mu je muyi jiransa kar ya tafi ya barki ga abincinki komai da komai harda kayan hada shayi idan kinje ki zauna ki karya sanan ki shiga ajin kinji KO?


Ta ce " toh suka fito kofa wajen mai gadi suka zauna suna jiran fitowar Idriss Wanda KO daga baci bai farka ba 


Sai karfe bakwai da rabi ya fito shima dan kar aje bata shirya ba suyi lati ranar zuwanta ta farko bai dace ba , yana fitowa ya hangosu Hajiya a zaune a yar tayani tsegumi ita kuwa a tsugune a gefenta ai besan sanda dariya ta kufce masa ba ya ce " aiki ga mai kare ka 


Haka ta Mike ta shiga ya tayar suka haura titi suna tafe yana yi mata bayanin yanda zata yi dan karta sha wahala sosai, ya ciro wani kati mai walwali ya Mika mata ya ce" wanan katin cin abincin ki ne na biya na shekarar gaba daya sanan na zabi na biya idan kinje kinada damar duk lokacin da kika ji yunwa ki shiga restaurant ne part VIP ki shiga can ki zabi kalar abinda kike sha'awar ci a kawo miki ki ci ki dan huta kiyi sallah sai ki huce wajen karatun ki , karkiyi wasa da karatun nan naki domin kafin ki fahimci lesson sai kin sha fama tunda baki iya rubutawa da karantawa ba aman da yardar Allah zaki iya harma ki koya min , ya karasa yana murmushi ' 


Tayi murmushin itama ta miko hanu ta karba tana godiya ta ce" ai kuwa kaga Hajiya har ta zuba min kayan abincina a jaka 


Ya kwalalo ido ya ce" to kaji yo ai baza'a barki ki shiga da wani abinci ba gudun karki zo da abinda zai bata miki ciki kuma a tsayar da karatun KO wani ya ci ya bata masa ciki a samu matsala , makarantar nan akoy shegen tsaro dan haka ki kiyaye ki dena zuwa da komai wanan din ma ki juye shi a nan idan kin shiga kya karya  , hakan kuwa akayi ta juye komai ya rakata har kofar shiga daidai nan aka tsayar da shi ita kuwa aka caje Jakarta aka rage litatafan aka ware na ranar abinda zasu yi sai  wani litafin aka saka mata dan saboda karatun da zata ringa dauka da wasu malaman bayan aji . 



                   ❤

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*






                    20


Haka Yar Mahaukaciya ta shiga cikin makarantar ta nufi office din da aka nuna mata taje ta ja ta tsaya ta shiga rapka salama ta kai wajen minti biyar a nan a tsaye sai da wani dalibi ya zo ya dana wani jan abu sai taga kofar ta bude ya shige ta kwalalo ido tana nan tsaye ya fito yayi tafiyarsa ta lumshe ido tayi bismillah hanunta na karkarwa ta dana jan abun kofar ta ce wani guiui ta bude ai uwa an hankadata ta fada sai zazare ido take tana kifkif da ido 



Mutumin dake zaune ya hakimce da shigar manyan kaya a jikinsa gefensa kuwa da wasu mutane sai dadana computer suke gaba kadan da shi kuma jerin wasu mutanen ne suna observing dalibai a computer ita dai tayi tsai tana kalon su yayi gyaran murya ya mika mata hanu da nufin ta bashi takardarta Wace idan tazo zata gabatar a kaita aji a nuna mata komai 


Ai gaba daya takardun hanun nata da litatafen da jakar ta ajiye masa saman table din nasa na glass ta ce" wly sun caje ni kosan ma yaya ya juya da shi KO karyawa banyi ba 



Nan da nan suka shiga kalon juna , banban na zaune Wanda ke hakimce ya ce" ur name?



Yar Mahaukaciya tayi Kifkif da ido tana kalonsa fuskarta bayane da tsoro kafin tayi magana téléphone din saman table din yayi ringin ya Mika hanu ya daga 



Daga dayan bangaren ya ce " tazo KO?


Abdallah mai kula da makarantar ya ce" aa dalibai dai suna ta shigowa har yanzu bamu ga mai sunanta ba aman ga wata tsaye inajin bata iya turanci ba ma 



Mubasshir ya ce" what? Na fada maka yar gidana ce kuma akoy abinda ya tsayar da ita ba'a kula da karatunta ba kayi mata hausa idan tazo shine zakana cewa baka sani ba ? Look idan kaga bazaku kula kan karatunta ba na tura a dauko mini ita , karatu KO a Wace kasa take so sai na kaita kuma KO wani kalar malami sai na sama mata ya koyar da ita




Abdallah ya ce " kayi hakuri abin du bai kai nan ba yaya sunanta ne?



Mubasshir ya zaro ido yayi Saurin rufe kan wayar ya kali idriss da ya saka shi a gaba kan a kula kar su banzatar da ita ya ce" kai sunanta fa?



Idriss ya dane dariyarsa ya ce" *RAHAMA IDRISS*




Mubasshir ya yatsina fuska ya kara a kunan sa ya ce" Rahama idriss 



Abdallah ya tambayi Yar Mahaukaciya dake tsaye da hausa ya ce" kece Rahama Idriss?



Da Sauri ta gyada kanta ta ce " eh Nice 



Abdallah ya ce" sir itace a kara hakuri zata samu kyakyawar kulawa 



Mubasshir ya ce " ohk thx ya datse Kiran 



Abdallah da kansa ya mike ya raka Yar Mahaukaciya aji Sanan yayiwa malamin bayanin idan ya gama ya nuna mata office din hajiya Amina , ya juya ita kuma ta samu waje ta zauna ta shiga kalon Malan yana ta gwaranci toh gwaranci mana domin ita dai ba abinda take ganewa a cikin abubuwan da yake fada tana dai kalonsa har ya gama ya kaita wajen Hajiya Amina inda ta kwashe awa uku tana koya mata A B C D ......Z, sanan taje wajen cin abinci inda ta sha mamaki kamar ba a cikin makarantar yake ba kuma gaba daya sai daukan ido wajen yake nan taga manya manyan yan mata da samari kowa yana harkokinsa wasu suna ta selfi wasu suna buga gem , wasu suna ta labari, wasu suna zance, wasu kuwa suna jiran abincin su kai wajen ba dai tsaruwa ba ,  



Cikin tsoro ta nufi wani table mai shegen kyau Wanda taga ba kowa samansa sanan harda wani rubutu a farar takarda ta nemi waje tayi zamanta da bismillah tana dan yarfe hanunta domin ba komai a hanun ta mugun gaji ne da rubuta A B C din nan , tana zama bata ma gama hutawa ba taji muryar wata cikin turanci na fadin tayi ta tashi ga princess nan zuwa table dinta ne , 



Abinka da Wanda bata san mai take cewa ba kawai sai ta dan sakin mata murmushi ta waiga dan taga inda zata kai katin ta a zuba mata abinci ta ci ta koma masalaci , 


Bata Ankara ba sai ji tayi an daki table din ta dago kanta da sauri tana kalon wace ta buga table din , wangalau tayi da idanuwanta tana kalonta batada KO dan kwali a kanta ta sha kananan kitso na atash sun mugun yi mata kyau , ta kara girar ido sunyi zako zako ta sha lips dinta mai sheki gwanin kyau gata fara kar ta budi baki cikin turanci ta ce " ke yar gidan uban waye harda zaki zo ki dora tsumakaran duwaiwanki a saman kujerarr da ni nake zama?



Yar Mahaukaciya bata kauce idanuwanta daga kalonta da take ba ita mamaki take Kenan ana zuwa makarantar babu hijabi KO dan kwali? 



Ita kuwa ganin kalon da take yi mata da idanuwanta kamar na mage kuma ta ki yi mata magana yasa cikin zafin rai ta saka hanu ta ja hijabin Yar Mahaukaciya tana fadin shegiya mai acuci bari na tona miki asirin abinda kike boyewa a hijabin yanzu haka wani kurji ne da ke daidai lokacin gaba daya daliban wajen sunyi ca suna kalonta dan kowa yasanta da rashin mutunci yar gidan embasader ce table dinta ba mai zama mutun daya take shayi shi kuwa yayi kwana uku bai zo makarantar ba shi yasa take taka rawarta yanda take so a makarantar, kuma taga bakuwar fuskar nan tana kokarin kawo mata raini dole tayi maganinta 


Da karfi ta idasa Jan hijabin Yar Mahaukaciya harda ribom din da ta daure kanta da shi ya biyo hijabin gaba daya gashinta ya barbazu har gadon bayanta cikin gigita ta Mike tsaye ai kaf wajen suka kwashi waouh domin sai da ta Mike dirinta ya fito ita kuwa baiwar Allah kokarin ganin ta kame kanta take suna tsaka da wanan rigimar chef din cafetariar ta fito itama ta sha ado da masarar Riga a daure a tsatsonta ta fito cikin turanci tana tambayar mai yake faruwa? 



Princess da gaba daya jikinta yayi sanyi domin sai da ta raina kanta duk irin tarin adon nan da ta sha kuwa sai taga tamkar wata banza a  Yar Mahaukaciya ga kalar gashinta kalar blonde kuma gashinta ne ba atash bane ga tsahi da gareshi ga shegen santsi ga yanayin jikinta da ka ganta ka san daga gidan hutu ta fito , 



Wani daga cikin daliban ya ce" aunty wanan mai kyau ce ta zauna a table din princesses shine princesses take fada 


Aunty ta kali Yar Mahaukaciya ta ce" ina katin ki yarinya ?



Yar Mahaukaciya jin an ce kati ta gane na cin abincinta ake tambaya ta juya nan kasa inda ya fadi ta dauko ta mikawa Auntyn ,


Aunty ta zaro ido ta ce" kai princesses kin san da wa kike magana kuwa? Kinsan du wanan gyaran da muke tunda safe na tarbanta ne ? Kinsan KO yar gidan wacece?



Gaba daya suka bada hankalinsu wajenta har Yar Mahaukaciya domin yanzun da Hausa tayi magana don kuwa ta tsorata kar wanan yar masefar princesses din ta ja musu asara dan an hau shegen table dinta , ita kuwa yar mahaukaciya tambayar kanta take to ita kuwa Yar gidan waye harda za'a yiwa yar gidan ambasader fada dan ta taka ta ???





Nima ina son sanin amsar wanan tambayar???????????????????????????????????


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    23

Tunda garin Allah ya waye jama'a ke kai kawo manya manyan mata masu ji da kansu kawayen Hajiya Marhaba , tayi wanan gayar ne dan kawai a tsayar da shagulgulan da za'ayi mawakan da za'a dauko har na wajen diner , da sauransu 



Sahla ce ta fito daga dakinta tana waya , Hajiya Marhaba ta ce" beby ina kuma zaki je haka?



Sahla ta juyo ta ce" mom zan je na zabo kalar Wanda zan dora , tayi kirana ta ce ta kawo su jiya 



Hajiya Marhaba ta ce " Ohk karfa ki yarda ki jima, sanan ki san da kinyi lulubi saboda kin san ya hane ki fita so ki kula 



Sahla ta amsa mata tayi gaba abinta



 


Idriss ya dago kansa ya kali mahaifinsa ya ce" ina yaro ban taba ganin mutun mai biyayar iyaye kamar ka ba abanah, aman tunda na kawo shekara goma sha uku a duniya sai naga ka fara janyewa da Hajiya , Abanah karka manta Hajiya kai kadai gareta danginku duk babu, Abanah yar uwarta daya ba mai aure a nan bace bata da labarinta ma , shin Abanah idan ka samu dan lokaci na ka zauna kadan da kakata bazaka je ka gaisheta ba ? Tana matukar nisa rashinka a cikin zuciyarta kuma nasan bata barci Haba Babana karka manta fadar Allah ce mu maza mu bi iyayenmu matayenmu kuwa su bimu dan samun tsira a gobe kiyama, a kulun idan muka zauna da ita sai na bata hakuri sai tayi murmushi ta ce ba komai ,  ya hade hanayensa ya ce" kayi min rai Abanah ka gyara koma meye tsakaninka da Hajiya ka koyar da mu kulawa da tamu mahaifiyar 😌



Mahaifin Idriss , Ilyas ya kare masa kalo gaba daya jikinsa ba kwari ya ce " Idriss please tashi ka bani guri ina bukatar tinani



Idriss ya mike yana adu'ar Allah ya sa mahaifin sa ya gane 


Bayan fitar Idriss Elhaj Ilyas ya mike ya har wani juwa yake yana mamakin kansa, mai yake sha'afar da shi da mahaifiyarsa? Yaushe rabonsa da ya kai mata abinci ya zauna ya bata ta ci yana yi mata hira? Mai ke damunsa? Cikin Sauri ya juya daga office dinsa ya shiga motarsa ya nufi gida , yana zuwa ya bar motar a kofar gida gudun kar Marhaba ta Ganshi ya dawo yanzu



Cikin Sauri ya fada bangaren Mahaifiyar sa , sai da ya lumshe ido domin Hajiya ba dai kanshi ba , kulun cikin zambada tiraren huta take na hayaki kalakala , ga tsakar gidanta sai ka yarda Abu ka dauka ka cinye, kai ba dai tsafta ba Allah ya bata abinta , 


Cikin faduwar gaba yake takawa a hankali yana dosar dakin bugun zuciyarsa na tsananta , kuma wani bangare na zuciyarsa na korarsa ya rasa meye wanan, aman a yau kaunar ya ga Hajiya ta rinjayi kin ya ganta, 

Sautin dariyarta ya tsinkaya tana fadin" kai aman akoy aiki kwabin fulawa wajen yan mata kadai ta isa ta saka bawa ciwon ciki dan dariya 



Yar Mahaukaciya da ta takarkare zaune a saman tabarma ta saka Roba baba tana kwaba fulawar da zasu yi fanke na mutanen hajiya tunda Hajiya ta zuba mata kilo biyu ta kasa kwabeta sai nishi take ita kuwa Hajiya ta ce ai kuwa sai ta koya 


Salama yayi inda cikin zabura Hajiya ta dago kanta ta zubawa fuskar gudan jininta ido , kasa amsa salamar tasa tayi dan tsananin mamaki ,

Suna yin ido hudu ya dauki sauki ya je da Sauri ya tsuguna ya dora kansa saman ciyoyinta ya rike kafafuwanta daga kasa ya saki kuka kamar karamin yaro 



Yar Mahaukaciya dake zaune ta waigo ta zaro ido , tunda tazo gidan nan yau kadai Allah ya taba hadata da mahaifin Idriss daga kamar ta gane cewar mahaifinsa ne , da Sauri ta Mike ta basu waje 


Ya kusan minti goma yana ta kuka a saman cinyar Hajiya Hawau , Wanda kukan ke ratsa duk wata gaba ta jikinta , ta rasa ya zata yi sai ta daga hanunta zata shafa kansa sai ta kasa , ji tayi an daga hanunta an dora saman kan Elhaj Ilyas ta dago kanta tayi ido hudu da *Mubasshir* ya sakar mata wani lalausan murmushi sanan yayi mata nuni da ta kula baban, baiyi magana ba gudun kar ya ganshi a haka ya shige a hankali dakin Hajiyar .


Cikin nutsuwa Hajiya ta ce" mai yake damunka Dan gidan Hajiya?


Da sauri ya dago kansa ya kuma rushewa da kuka yana fadin dan Allah ki yafe min , wly ban san abinda yake damuna ba , na rasa nutsuwata na rasa abinda ke damuna , na rasa farin cikina Hajiya ki yafe min



Hajiya Hawau ta share hawayenta ta ce" kulun cikin yi maka adu'a nake Dan gidan Hajiya , ka sani Allah yana tare da mai gaskiya kuma ka kara riko da adininka Allah ya baka lafiya 


Elhaj Ilyas ya ce" Amin na gode Allah ya kara tsawon kwana da lafiya , nan fa tsakani uwa da Da suka shiga hirar su 





Mubasshir na shiga ya tarda Yar Mahaukaciya zaune saman wata kujera mai tsayi tana kalon madubi da macaji ( masarci) a ganunta tana caje gashin kanta da kyar sai nishi take dan kuwa daga ta caje sai ya koma ya nanade kansa haushi ya kamata ta wurgar da macajin tana fadin wly sai na askeka gaba daya ma na huta , haka kawai 




Mubasshir dake tsaye yana kalonta yau dai yayi niyar sai ya san wai atach ne take sakawa KO kuwa haka kalar gashinta yake , 



Yayi gyaran murya , 


Da Sauri Yar Mahaukaciya ta kale shi , sam bata ji karar shigowarsa ba , kuma tirarensa da ya zama KO da yaushe yana gidan sai ya kasance kanshin tiraren KO yaushema jinsa take a hancinta hakan yasa KO yanzun da tana caje kanta ta dan ji kanshin bata wani kula ba , tana ganinsa ta shiga neman hijabinta da a tinaninta saman bed din Hajiya ta ajiye shi , da Sauri ta bude akwatinta ta dauko na makarantarta ta zumbula Sanan ta shiga kikifta ido,




Mubasshir shi abin nata dariya ma ya bashi wai kariya bayan bugu , aman sam bai daran ba  ya ce" menene kike kokarin rufewa tamkar naki bayan kin loda gashin doki KO na matacen mutun a kanki ?



Yar Mahaukaciya jin an ambaci ta loda gashin matacen mutun a kanta ya saka ta kwalalo ido waje ta ce" karde aje gashin nan na matacen mutun din ne?



Mubasshir ya kaleta a ransa ya ce zata raina min hankali , a fili ya ce" ya zanyi miki tambaya kiyi min ni ma?



Yar Mahaukaciya tayi kalar tausayi ta ce" wly kaga gashin mutane duk baki ne, gashin Fati ma baki ne, haka na princess da su Tina su Mariam duka baki ne, kaga kuma ance idan mutun ya mutu gashinsa fari yake zama, kuma ni tun ina yarinya yara idan suna bina sai suna cewa Yar Mahaukaciya mai farin gashi matata,      ......     Maganar ta tsaye mata a makogwaro lokacin da ta ambaci sunanta a gaban Dan Aljannah da Sauri ta rufe bakinta ta tura bayi tayi shigewarta 


Mubasshir dake tsaye yana sauraronta gaba daya zancen ya shige masa duhu mai take nufi da yara na kiranta da *Yar Mahaukaciya*? Mai hakan ke nufi?



Sahla dake labe tana sauraron su ta jiyo gaba daya abinda suke fada ranta ya gama baci ya mijin da zata aura ya zo yana magana da wanan banzar? Kuma taji Ashe ma ita din *Yar Mahaukaciya ce*, ai kuwa zata fadawa momy tun wuri ayi maganin wanan abin tun kafin a jaza mata bala'i 




Wayo Yar Mahaukaciyata

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    24

Sahla na fita ta ficewarta ta nufi cikin gidan su, tana zuwa ta shige dakin mahaifiyarta tana haki, 


Hajiya Marhaba na ganin yanayin yar Tata ta Mike ta nufi dakinta tana fadin tana zuwa, tana shiga ta tarar da Sahla tana ta haki ta ce" Beby lafiya?



Sahla na ganin mamarta ta fashe da kuka har tana  buga hanayenta jikin bed tun karfi 


Hajiya Marhaba ta je da gudu ta rike hanunta tana fadin Beby wa ya taba miki zuciya haka? Fada min uban wa ya taba min ke? Idriss ne KO? 



Sahla ta shiga sauke ajiyar zuciya ta ce" mom ni fa kawai a kori yarinyar nan daga gidan mu , gaskiya ta fara fice Gona da iri , 



Marhaba ta ce" wace yarinyar?


Sahla ta ce " wanan mai kalar fatar zabaya mana, 



Hajiya Marhaba ta ce" toh mai tayi ?



Sahla ta dago kanta ta ce" kinga irin yanda Yaya Idriss ke kashe mata kudi kuwa? Sanan yarinyar uwarta Mahaukaciya ce , tana nan tana hauka kina son samun sirika Yar Mahaukaciya ne? Kuma duk da Mubasshir ya tsaneta hakan baya hana shi zama inda take, kinga tun wuri kiyi maganinsu dan kuwa yau naga dad a wajen Hajiya .




Hajiya Marhaba ta zabura tana dafe kirji ta ce" what? Dadyn naki ne ya tafi wajen Hajiya? To mai yasa bai fada min ba? Mai yaje yi wajenta ? KO dai asirin nawa ya karye? Kam akoy matsala , 


Ta juya ta dauko wayarta ta dana kira tayi ciki ta bar Sahla zaune tana dariyar cin galaba , sanan tayi kwafa tace" da naso na barki ki dan gana da danki aman tunda kika fifita wata bare a kaina ni da ke sai dai sheri ba dai khairi ba ( Allah ya shirya mana yayanmu )



Mubasshir ya jima tsaye bata fito ba kuma yaji tafiyar Aban Sahla hakan yasa ya juyo ya fito ya yiwa Hajiya salama ya nufi gidansu zuciyarsa cunkushe da abubuwa kala daban daban, 



Yana shiga yaji sautin wakar larabawa hakan yasa cikin farin ciki ya dan kara Sauri ya isa baban falon mahaifiyarsa , ai kamar jira ake yana saka kafa yaji gaba daya an shiga watsa masa tirare , ta ko'ina wasu na fesawa sai hamdallah suke , daga gefe kuwa Ashe mawakiyar ce suka zo da ita takanas sai yi take tana juyin nan na larabawa, 


Mubasshir ya sada kansa kasa da kyar yake iya cira kafarsa yana dana sanin zuwansa a wanan lokacin gashi suna kokarin rikita masa lisafi , 



Hajiya Fareedah ce ta taso ta kama hanunsa ta karaso da shi kusa da mahaifiyarsa ta ce" yarona an girma, Alhamdulilah yau har zan wankeka , Allah mai kyauta da kari ,Mubasshir ya zama ango 



Mahaifiyar Mubasshir tayi murmushi da taga sai kawar da kai take , tasan baya son kida yayi yawa , baya son yawon hayaniya, inda ya sha banban da ita domin ita tana mugun son mutane tana son KO wani motsi zata yi ta jita kusa da mutane , 

Ta ce" nurul'ayne mai yake damunka?



Hajiya fareeda tayi caraf ta ce" ku shiga daga ciki mana sai ya fada miki aman a nan bazai yiwu ba tunda kinga akoy mutane da yawa 



Mubasshir na jin an bashi damar tashi ya Mike yayi sama , ya nufi dakin mahaifiyarsa ya konta ya lumshe idanuwansa yana fadin wacece ita? ( wai mai ya shafeka malan 😏 )



Cikin nutsuwa ta turo kofar ta shiga da salama aman bai ma san ta shigo ba , ya lula duniyar tinani , 


A nitse ta ISO ta tsaya a kansa tana mamakin abinda yake saka Mubasshir cikin tashin hankali haka tana mamakin abinda ke saka shi tinani haka , KO yana tina mahaifinsa ne? KO taron nan da yayi yawa ne yake damunsa? 


Ta kai minti ashirin a tsayen nan bai san tana wajen ba hakan yasa ta matsa ta zauna kusan sa ta dago kansa ta dora saman cinyarta ta ce" mai yake damun Mubasshir da har ya kasa fadawa mama?




Mubasshir ya dago kansa ya ce" maman Mubasshir al'amuranta na mugun daure min kai 



Mahaifiyarsa ta ce" Al'amiran wa fa? 



Sai a sanan ya Ankara da abinda yake fada ya dago idanuwansa da suka rine ya ce"""""""",,,,,,,,,,,""""""""""


[10/3, 13:50] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                      28


Wani ma yayi rawa balatana dan makadi, sisterna rabin jikina , ke din ta daban ce , wanan babin gaba daya naki ne Madame Abdul Kader *Maman Imran* love u so much












                 Labari


Ya dade yana wanka dan saboda sai da ya shiga ruwan zapi sosai ya wanke harda kansa ya dauro banban towel ya fito ,   yana fitowa ya ga Maman sa ta ajiye masa kayan da zai saka da komai saman bed 


A nitse ya zauna ya busar da gashin kansa uwa na mace dan santsi da shekin baki ,ya dauki mayukan gashi ya shafa 

Shi da kansa yake nanade kansa ya saka macaji ya daidaita shi yana jin haushin saurin taruwar gashin kansa kawai sai ya aske ya huta, kuma sai ya fito 



Cikin nutsuwa yayi shirinsa ya gama ya dauko kayan , yana dagawa yaga manyan kaya ne gari da yar ciki da hula sun sha wani mahaukacin zubi a jikinsu hular kanta wani irin aiki ne aka yi mata sosai ta hadu , abinka da mai son manyan kaya , yayi murmushi a fili ya ce " Maman Mubasshir Kenan 




Su Idriss na  suna ta labari suna dariya su uku daidai suma sun sha manyan kayan su sai anuri suke abinka da ranar fito na fito 


Mubasshir ya sauko cikin takun kasaita tamkar dan Sarki daidai da takalmin kafarsa na shadar nan ne haka agogonsa mai zubi ya sha hularsa , yana ganin su ya saki murmushi 



Nura ya ce " waouh , waouh , waouh , wata miyar sai a makota , wai dan Allah kaine kuwa?



Mubasshir ya Mika musu hanu daya bayan daya suna gaisawa sanan cikin murmushi ya ce " angoncewa ce




Idriss ya sha kunu ya ce " kai kasan gaban manya fa kake 



Mubasshir ya ce " meye manya? Yana wata yatsina 



Ramadan ya ce " ya ilahi sirikinka ne fa



Mubasshir ya mike yana fadin " kunga mu yanzu mun zama masu iyali ku tashi mu nufi gidan iyayena na gaisar da kakata sai iyayen matata a al'adar chadi 



Suka Mike suna murmushi , fitowarsu keda wuya wanan mawakiyar ta larabawa ta kwasa sai koda Mubasshir take , dago kansa da zai yi ya hango gimbiya Mubinah yar gidan sarkin Makah cikin shiga ta alfarma ta zuba zinari da wani mahaukacin lesh fari gata fara sai daukan ido take , 


Suna fitowa ta mike ta nufo Mubasshir Wanda sai da gabansa ya fadi a ransa ya ce " ya akayi mai martaba ya BArTA ta biyo su mai girma Barhan? 


Tana isowa ta rungume shi irin gaisuwar larabawan nan sanan daidai kunan sa ta rada masa " na zo na raka mijina gidan amaryarsa da tayi min shigar wuri kafin na shigo 




Mubasshir ya dan saketa ya lakaci habarta yayi murmushi sanan ya juya wajen iyayensa yayi Saurin tsugunawa yana gaisar da su 



Hajiya ta taso ta kama hanunsa ta daidaita masa hularsa ta ce " Alhamdulilah yarona ya girma , Allah ya kade baki ( kunsan larabawa suna mugun gudun baki shi yasa daga sunyi magana sai kaji sun ce Masha Allah , 😁 )



Haka sukayi ta saka masa Albarka sanan suka juya inda wasu motoci kwaya hudu a jere farare tas sai sheki suke , yau yau aka fitar da su da ka gani ka san an cashi kudi a nan , 


Karar tafiyar doki naji na waiga wani ne ya taho da dokina biyu  yana jaye da su da irin runfar nan ana jaye da su , sai karar kacaukacau suke sun mahaukacin sha ado na zinari sai kara suke 



Mubasshir ya juya ya sauke idanuwansa saman Mubinah dan kuwa ya san wanan aikinta ne ya gala mata harara dan ta sani sarai ya tsani hawa doki KO a can su biyu suke hawa KO da ita KO da wani a gefen sa , 


Tayi murmushi cikin harshen larabci ta ce" kar a yada al'ada ka sani sarai da a can ka yarda kayi aurenka da sai ka zaga gari a saman doki dan haka ya sa na shirya wanan KO ba komai ka girmama al'adar mai martaba uba a wajenka 




Da haushi haushi ya taka ya hau itama aka kama mata ta dare tamkar itace amaryar ,motocin nan suka saka su a tsakiya , mai girma Barhan ya karaso ya rufa masa alkyaba aka cire masa hular aka rufa masa ta alkyabar nan dan kuwa haka al'adarsu take 



Cikin nutsuwa suka kama hanyar gidan su Sahla 




Hajiya Hawau ta sha dinkinta na shada ta hade harda kafa daurin dan kwalinta sun malaya manyan tabarmi a tsakar gidansu da kawayenta tsofafi sai labari ake ana shan fura mai cukui sai kanshi take ga dadi abinka da tsohuwar da ta san darajar baki duk Wanda ya shigo Yar Mahaukaciya da kawarta Fati sai su zuba furar a cikin kwarya da ludayi su Mika masa , suma sun sha dinkinsu na shada duk da ba wata kwaliya suka yi ba dalilin ainkin da suke yi 



Suna tsaka da shan dariyarsu suka jiyo karar ganga da kuma muryar mace tana ta ISO da larabci tana wakarta , ga Wanda ya iya ya san dan gata ake wakewa ga Wanda bai iya ba kuwa sai dai ya gyada kai dan dadin wakar 



Fati  ta kama hanun Yar Mahaukaciya ta ce" kawata ai angwaye ne 




Yar mahaukaciya ta ce" mai ya kawo angwaye nan kuma a yanzu?



Fati ta ce " oho o mu dai mu shirya tarban su 



Hajiya Hawau ta fado kincin din ta ce" Ramatutu ai ga Dan Aljannah nan ya ISO da tawagarsa kinga wa'incan kwaryoyin masu zane su za'a dauko a zuba musu furar , aman ai ke kinsan yanda ake dama ta dan Aljannah dan haka a dauko duka cukuii din da nonon a dame musu yi maza yar Aljannah 



Yar Magaukaciya tayi murmushi Ganin irin yanda Hajiya ta rikice ta ce " Hajiya ai na dame ta tun dazu Idriss ya ce a aa zuwan su duk da nayi zaton ko wasa yake mun dai dame kuma yanda kike sonta , aman ciki zasu shigo kinga baza a bar Dan Aljannahn ki a wajeba KO?



Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Allah yayi miki Albarka bara na sauke su a baban falon , ku kuwa ku jera furar ku kawo musu 

Ta juya tana kara daure dunkunkumin dan kwalin da ta dunkuma 



Yar Mahaukaciya haka kawai ta tsinci kanta da tsoron hada ido da Dan Aljannah a wanan ranar , mutun a ranar da ba ta aurensa ba ma yana mugun daukan ido bare a yau?



Fati ta ce" Malama Hajiya garin kidima har kofina take ambato 😁




Yar Mahaukaciya ta ce" Dole Hajiya ta rikice dan kuwa dan gatanta ne 



Haka suka dauko kwaryoyin suka kara darwaye su , gasu kananuwa masu shegen kyau da ludayinsu masu kyan gaske suka jere a saman wani baban faranti na silba mai  shekin gaske , sanan suka ringa zuba furar nan suna saka ludayin a ciki , sai da suka gama 


Yar Mahaukaciya ta ce " plz my kawali ki dauko na Dan Aljannah dan Allah 




Fati ta zaro ido ta ce " mai kike nufi da hakan? Yayanki ne fa kuma kin sani sarai kar na fita na zubar garin kalonsa 



Yar Mahaukaciya ta san sarai zata aika hakan yasa ta dauko wani farantin dan madaidaici ta zuba furar a wata kwaryar mai murfi sanan ta dauko ludayi ta dora a gefe ta dauko mushoir ( hankici ) sabo fil fari kar ta dora shima a gefe ta gyara komai 


Fati dake kalonta ta ce" gaskiya al'adar Hajiyar gidan nan na mugun birgeni , koman ta daban ne sanan ta koyawa yar Jikanlen ta 



Yar Mahaukaciya tayi dariya tana dora farantin Dan aljannah a gefen sauran furar ta ce " kama mu tafi malama kar suyi tafiyarsu 




Suka kamo suka fito suna tafiya cikin nutsuwarsu suna fitowa kanshin ya daki hancinsu daga fatin Har Yar Mahaukaciya suka dago suka zubawa bakin dakin kalo 


Idriss da dan Aljannah sun saka Hajiya a tsakiya ita kuwa sai washe hakora take daga gefe guda kuwa Mubinnah ce sai fifitu ake yi mata ta sha kyau har ta gaji, sai su Ramadan da Nurah a wata kujerar abin gwanin ban sha'awa 



Fati ta juyo ta kali Yar Mahaukaciya Wace itama kamar ta fadi dan yanayin Mubasshir ya kidimata harda Idriss abin ya mugun haduwa kawai sai taji eh lale tana iya yin soyaya da shi dan kuwa ya mugun birgeta a yau 


Fati kuwa ta kidime ta haukace ta ce" kawata kina ganin zinaria ce fa a jikinsu dan Allah ki duba ki ga irin yanda AA ya zama uwa Kwaï dan daukan ido 




Yar Mahaukaciya cikin rada ta ce " ki nutsu mu basu juya tun kafin na kife a nan 



Su duka suka dan saki murmushi sanan sukayi salama 


Hajiya Hawau ta dago kanta ta amsa haka sauran jama'ar wajen 


Cikin nutsuwa su Yar Mahaukaciya suka ajiye wanan farantin a saman table din dake ajiye a tsakar dakin sanan suka shiga dauka suna mikawa mutanen dakin , har sai sun duka har kasa su Mika musu hakan ba karamin birge hajiya Hawau da kuma su idriss yayi ba 







                   🙆🏿

[10/3, 13:50] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                      29







Fati ta dauko ta nufi Mubinnah tana isowa ta dan risina ta Mika mata da Sauri mai yi mata fifitar nan zata karba Mubasshir ya daka mata tsawa " cikin harshen larabci ya ce" idan anzo waje ana anfani da al'adar su ce sanan nan gidan sirikai na kuma iyayena ne dan haka kar a kawo min batanci kin gane ?



Da sauri ta risina tana fadin Allah ya huci ran Dan Gattahn Mai Martaba mafi soyuwa ga gimbiya Mubinnah 



Mubinnah duk da bata ji dadin yanda ya sacewa kuyangarta gwuiwa aman bacin ransa yafi komai daga mata hankali hakan yasa ta mika hanu ta karbin wanan kwabin da bata san KO na menene ba ta dan gyara zamanta tana shawara da zuciyarta shin zata sha ne KO aa 



Su dai KO a ransu , Yar Mahaukaciya ta dauko farantin Mubasshir har a lokacin bata gama yi masa kalo ba tayi niyar bazata yarda tayi masa kalon kurula ba , 


A nitse ta nufi wajen da tafi jin kanshin sa , itama Fati ta dauko na Idriss ta nufe shi 



Yar Mahaukaciya na isawa ta tsuguna har Kasa ta dago hanayenta ta mikawa Mubasshir dan farantin mai kyan gaske 



Mubasshir ya zuba mata ido dan gashinta daga gaba ya dan leko kadan sanan bakinta sai sheki yake na mai mai maski da ta dan goga , 


Maganar idriss ya dawo da shi inda yake fadin" Malan kaga Karka wahalarmin da mata mana ka karba plz karka rama a kanta 



Firgogit yayi dan kuwa ya fada wata duniyar tinani ya Mika hanunsa wajen karba sai da hanayensu suka gogi juna , ita kuwa Allah Allah take ta bar wajen dan jikinta har karkarwa yake jin baranbaramar da Idriss ya afka mata a gaban Hajiya harda bakin kunya sai ma da taji Muryar Ramadan na fadin" au kace kaima taka a gidan take , gaskiya kunyi mana wayo , wanan wayo har ina ? Gaskiya muma a san yanda za'ayi da mu 



Da Sauri Yar Mahaukaciya ta janye hanunta ta Mike da gudu tayi dakinta tana haki 



Mubasshir da Idriss gaba dayansu da ido suka bita , Mubasshir yayi dan daman bai rike hanunta ba , ji irin yanda take gudu ana kalonta ( inada tambaya , ina ruwanka hon)



Shi kuwa Idriss wata irin faduwar gaba ce ta ziyarce shi ta haka kawai a ransa ya ce " wai a nan a cikin zulumbuwar riga take lale akoy aiki a gabana ( to kaji 😏 )



Hajiya ta katse dan shirun da ya gilma ta hanyar fadin " tayi maka kyau idrissu , nace tayi maka kyau ka firgita min ya 



Yayi murmushi ya ce " haba kakus ya zamu zo ki hada mû da fura ? 



Ta ce " to dan nema ita ce da ni ehe 😏



Mubasshir ya ce " kyale shi hajiyata ni kadai na san darajar wanan dan haka kowama kar ya sha idan yana so 




Haka sukayi ta barkoncinsu har dai Sahla ta gaji da Kiran mamanta tana fadan sun shiga wajen tsohuwar nan sun makale kar ayi mata abinda ba shi ba 



Sahla ta ce " mom kiyi Kiran Yaya Idriss plz 


Hakan kuwa akayi ta dana kiransa daidai zasu shigo falon nata ,


Salamarsu ta saka ta katse kiran jama'ar dakin na amsawa 



Marokiyar ta rangada guda ta kwashi kirari da kuma isowar angon auta wato Sahla 



Cikin nutsuwa suka tsuguna gaba dayansu kasa suka shiga gaisar da Su Hajiya Marhaba da kawayenta 


Hajiya Marhaba murna kamar mai , 

Suna tsaka da gaisawa wayarta ta fara ringin 


Ta dauka sai taga sunan bokanta ne inda ta rubuta hajiya bokatu , 


Tayi murmushi ta Mike ta dan matsa kadan ta daga 



Daga dayan bangaran ya ce " na gama aikinki na aikawa mijinki yanzu yanzu zai aikata abinda na saka shi tunda kince kina so a cikin jama'a yanda kowa zai ganta a rana yanda ba Wanda zai so ta rabe shi KO?


Hajiya Sahla ta ce " kwarai kuwa boka yanzu ne daidai dan kuwa gaba dayan mutanen da nake so su ganta a tozarce suna wajen nan so kawai ayi aiki na cika 



Boka ya ce " karfa ki manta kudin ki mai yawa ne 



Ta ce " kar ka manta aikinka mai kyau ne idan har yayi kyau din ai kuwa abinda zaka samu har sai ya fi wanan 



Ya bushe da wata mahaukaciyar dariya ya e " to bunsura sai na jiki , ya datse Kiran 










To fa , kaka kara kaka , shin waye za'a tozarta a cikin mutane? Waye za'a wulakanta har ma kowa ya gujeta? 🤷🏿‍♀🤷🏿‍♀🤷🏿‍♀🤷🏿‍♀🤷🏿‍♀🤷🏿‍♀ taku har kulun yar mutan Niger 😘😘😘😘

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                      30


*Jiki Alhamdulilah sisters na gode da adu'ar ku gareni love u*














          Cikin takunta tamkar ba ita ce ta gama wayar ba ta juyo ta zauna , tana zama idanuwanta suka sauka kan Mubinnah Wace ita har ga Allah da farko bata ganta ba , gabanta taji ya fadi abinka da mai sakin magana idan ta raya mata ta kali Mubasshir wanda ya kagauta su tashi su bar dakin irin yanda matan nan kowace ta zuba musu ido ga uban surutu an cika su da shi ga wasu hotuna uwa Wanda aka gayace su gidan TV shi kam duk a takure yake 



Hajiya Marhaba ta ce" Mubasshir wanan fa? Ban Santa ba 



Mubasshir ya kara sada kansa kasa dan kuwa KO bai dago ba ya san da Wace ake magana 



Idriss ya kaleta ya ce" Mom Wanan fa itace Mubinnah daya daga cikin yayan sarki 



Hajiya Marhabah ta ce" wani sarkin?



Idriss ya ce" na Makkah mana mom 



Hajiya Marhaba ta washe hakora ta shiga yiwa Mubinnah barka da zuwa jama'ar dakin ma haka , sanan kasa kasa sai surutu suke suna tambayar Kenan harda iyalan sarkin sun zo? Gaskiya Hajiya Marhaba ita tayi dace , 



Wani irin ihu suka jiyo , gaba dayansu suka yi tsit , suka kuma jiyo wani ihun da Sauri suka Mike Idriss ya ce " a nan ne 



Mubasshirr ya kama hanyar fita shi da Idriss inda matan suka yi cirko cirko suna raraba ido dan kuwa kowanen su tsoron FITA yake ayi ba shi 




Suna fitowa suke jin ihun daga wajen bangaren Hajiya Hawau ne Harda Alamar koke koke 


Idriss ya sha gaban Mubasshir ya ce cikin haki" Malan dakata , mu fara Kiran yan sanda kafin mu shiga cikin gidan nan wa ya san Abinda ke faruwa a ciki, idan fa yan boko haram ne?




Mubasshir ya gala masa harara ya ture hanunsa ya ce" KO yan a rayu haram ne Allah ya jikana ya juya ya nufi cikin gidan



Da shigarsa abin mamaki ya tarar Wanda ya kasa gaskatawa idanuwansa abinda suke gani , haka kunuwansa suka kasa yarje masa abinda suke jiyowa, nan da nan wata nadama da dana sani suka darsu a zuciyarsa domin wanan ba halin datako bane, sam wanan abin datijon kirki ba zai aikata shi ba 



Cikin sauri ya FITA ya saka akayi gida da Mubinnah domin idan ta ga wanan abin shi aka tonawa asiri ba kowa ba , 



Cikin mutuwar jiki ya juyo ya dawo inda wajen ya zamana tamkar ana kida dan kuwa har dan gewaye su aka yi ana kalo , ba kowa bane face *Elhaj Ilyass* sai Jan kafar *Yar Mahaukaciya* yake yana mugayen kalamai a kanta kamar haka 



    *Ashe Hajiya Mahaukaciya ce kika tare min a gida? Ashe kortuwa ce yarinyar nan ? Idan ka ganta luplup tamkar mutunuyar arziki ashe ita kuwa munafuka ce?*



Hajiya hawau cikin tashin hankali da kuka tana Jan Yar Mahaukaciya , Elhaj Ilyas na jan ta ta ce" Haba , haba Ilyasu dan girman Allah ka cika min yarinya ka cikata mu bar maka gidan ka domin wanan yarinyar ni shaida ce kan mutuniyar kirki ce , KO wa ya fada maka abinda ya fada maka karya ne domin wanan yarinyar marainiya ce sanan ni ni na daukota lokacin da danta ya rasu harma akayi masa sitira a nan , Haba Ilyasu wanan wulakanci har ina, ya kake so nayi da raina ne?





Elhaj Ilyass ya ce" Hajiya wly kinji na rantse ba inda zaki sanan yarinyar nan a yau yau din nan zata bar min gidana domin ni ba mazinaci bane sanan ba zan lamunci ta bata min suna ba da sunan iyalina , ke kuwa ni kika Haïfa ba ita ba dan haka ita kadai zata bar min gidana 





Hajiya Hawau ta juya wajen kawayenta tsofafin dake tsaye suna al'ajabin wanan lamarin da hanu daya ta fara rokon a taimaketa a tafin mata da Yar Mahaukaciya kafin danta ya gane yayi kuskure ta maidota 


Aman ina kowa sai ya silale domin da ace ma jinin hajiyar ce aman haka kawai haduwar rana tsaka a zo da wanan zancen gashi daga an ganta bata shigen yayan hausa ga ido irin na kyanwa aje tsakar dare ta farka ta cinye mutun,? Gaba daya kowa tsoron Yar Mahaukaciya ya darsu a zuciyarsa 



Mubasshir na rakube jikin garu yana kalon yanda da daya daya jama'ar suka fara fashewa suna tafiyarsu sai yan tsirirai su hajiya Marhaba da sauransu , muryar Idriss ta dawo da shi inda ya ce" Aba ka kontar da hankalinka ka cikata haka ni zan fitar da ita 




Da hajiya da Mubasshir a tare suka kali Idriss jin furucin bakinsa 



Elhaj Ilyass ya ce" Yawa yaron kirki fitar min da anoba daga gida 



Yar Mahaukaciya da ta zamto tamkar mutun mutuni , a da da farko tayi tinanin zuwan wanan ranar , aman ganin irin yanda ta samu zama sai tinanin ya kau daga ranta, tabas ta saba da wulakanci, da cin zarafi aman bata taba zaton a wanan ranar haka zata faru da ita ba , furutin Idriss shi ya fi komai daga mata hankali bata san lokacin da wani karfi ya zo mata ba ta Mike daga yashen da take cikin karaji ta ce " Ya isa ,



Ta juyo da idanuwanta da sauran farin ya koma ja, tsakiyar kuwa yake haske haske cikin dakakiyar murya ta ce" *Idriss ba sai ka fitar da ni ba , zan FITA da kaina, ta juya wajen Hajiya ta tsuguna ta kama kafafuwanta ta ce" Ni ba mazinaciya bace , aman kuma ban san ba KO ni mayiya ce KO aljana ce, abu daya na sani nima mutun ce, sanan ni YAR MAHAUKACIYA CE, kiyi hakurin rashina , karki damu da inda zan kwana na saba da wahala, kar kiyi fushi da danki haka Allah ya so , na gode sosai da tarbiyar da kika bani harma kika nuna min nima inada daraja*


Tana gama fadar haka ta jawo hijabinta na makaranta dake rataye saman igiya ta juya cikin nutsuwa ta fito daga gidan su Idriss inda take yi masa kalon karshe







To jama'a ina Yar Mahaukaciya zata nufa? Muje zuwa😁😁😁😁

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    31


Tafe take bata san inda take jefa kafarta ba , gata dai da ganinta ka san yar banban gida ce KO yanayin jikinta da yanda take haske sai dai fuskarta a mugun hade tamkar hadarin gabas 



Mutane sai kalonta suke suna al'ajabin wanan mai ke damunta? Wasun kuwa har tambayarta suke , aman ina ita ba ta tasu take ba 



Tun da ta fito yake biye da bayanta a hankali yana son sanin inda zata je , tafiyar yaga ba mai karewa bace hakan yasa ya samu ya shiga gabanta da motarsa daidai wani dan karamin gida na laka 


Kasa take kalo ganin mota ta shiga gabanta ya saka ta juya ta fada cikin kofar gidan nan ita duk a tunaninta hanya ce 


Da Sauri ya sauko yana kokarin cire Babar rigarsa domin ji yayi kwatakwata tayi masa nauyi , cikin nutsuwa ya kutsa cikin gidan nan inda ya tarar da Yar Mahaukaciya da wata mata tana yi mata tambayar wa take nema , ita kuwa kawai ta tsura mata ido tamkar sabuwar halita 



Cikin nutsuwa ya karasa yana fadin " salam kiyi hakuri kanwata ce bata tayi ne 



Matar nan ta ce" oyo sanu kinji kiyi hakuri ga yayanki 



Yar Mahaukaciya ta dago idanuwanta ta sauke su a fuskar *MUBASSHIR* Wanda shima a lokacin ita yake kalo , suka yi ido hudu da shi 


A hankali ya furta " mu tafi yana nuna mata kofa 


Tamkar wata karamar yarinya Yar Mahaukaciya ta make kafada tana nufin ba inda zata je 



Mubasshir ya hade rai yayi iya yinsa aman firr ta kafe ita fa ba inda zata tafi 


Matar nan ta fito itama ta saka baki ake baiwa Yar Mahaukaciya hakuri kan ta shige su tafi aman kamar da kurma suke magana 



Mubasshir ya hade rai tamkar bai taba yin dariya ba ya umarci Yar Mahaukaciya da ta fice su tafi , aman ina abinka da Wanda bai iya fushi ba , ita duk gani take idan fa ta bishi za'a koma ne a kuma ci mata mutunci kamar yanda akayi mata yanzu KO ma fin hakan , shi yasa sam ta kasa daga kafarta kuma bata ga abinda zai Sakata daga kafar tata 



Mubzsshir ya lumshe ido a ransa ya ce" Ya Allahna ka yafe min taimako zanyi ka fini sanin ba dan wani abin zan tabata ba ,

Kawai sai gani nayi yana tatare hanun rigarsa ya CIRA Yar Mahaukaciya sama ya nufi motarsa da ita , Wace ta zaro ido tana wutsil wutsil din ya sauketa tana yakushinsa tamkar sabon kamu







Shin ina Mubasshir honorable zai nufa da Yar Mahaukaciya? Zata amince ne KO aa?    ❤❤❤

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    32



Tunda ya sakata cikin motar ya zagaya ya shiga ya dauki hanya ita kuwa tsananin tsoro ya hanata dagowa ta kale shi balatana ta tambaye shi inda zai kaita dan haka kawai sai ta hade kanta da gwuiwar ta tana ta sheshekar kuka 



Tafiyar da sukayi ta kai ta minti talatin gaba dayanta ta hada zufa domin du ta dababaye jikin nata da katon hijab dinta na makaranta , 



Ji tayi ya ja ya tsaya ta kasa dago fuskarta kawai jiran jin duka take KO wulakanci dan tasan gidan su Idriss din ne kawai ya maidota , ta kai kamar minti biyar a zaune bayan tsayuwar motar tana ta sheshekar kukanta , wani sanyi kamar na busawar iskar Allah du da hijabinta sanan taji wani lalausan hanu wanda da ba dan taji yatsitsai ba da KO ya za'ayi da ita ba zata yarda cewar hanu ne ba , cikin Sauri ta dago kanta dan ganin wanda ya dora hanunsa saman kafadunta 


Hajiya Fatimatu Mahaifiyar Mubasshir ce tsaye sai kyali take , ga kwaliya ta sha ga sarka mai kyanli, ga farar fata ga kuma hasken gari hakan ya hadu ya haska fuskarta a idanuwan Yar Mahaukaciya Wace nan take ta gane wanan mata KO ya take ta hada alaka da Dan Aljannah da tsabar kamar da suka yi har ta baci , aman sam bata kawowa ranta cewar ta haife shi ba saboda ita bata da banban jiki sanan du da daga fuskarta zaka gane ta manyanta aman hutu ya hana a gane shekarunta , 



Hajiya Fadimatu ta katsewa Yar Mahaukaciya tinaninta ta hanyar sakar mata murmushi sanan ta kamo hanayenta cikin nutsuwa ta ce " Marhababiki yata , ta juya fuskarta cike da fara'ar da Mubasshir har ya fara kishi ta ce " Son kaga Adu'ata ta karbu KO Allah ya bani ya daidai lokacin da na aurar da dana , 



Mubasshir yayi Murmushin shima ya ce" Maman Mubasshir aure fa kika yiwa Mubasshir ba mutuwa yayi ba , dan haka kar a maye gurbin Mubasshir a zuciyar Maman Mubasshir dan kuwa ba zai taba yarda ba 




Mahaifiyar Mubasshir tayi murmushi ta lakaci Hancin Mubasshir ta ce " Kishi? Au kishi kake? To ka zage dantse dan kuwa aiki ya sameka jan aiki kuwa , ta kama Hanun Yar Mahaukaciya wace KO takalmi babu a kafarta sanan jikinta yayi busu busu da kura ta bi wani lungu da ita saboda taron jama'ar gidan ta nufi dakin Mubasshir da ita dan kuwa ita bangarenta jama'ar sunyi yawa sosai 




Suna shiga wayar dakin ta fara ringin ta daga tayi salama 



Mubasshir ya ce " Maman Mubasshir hajiya ce tayi kira na hadaku kuyi magana tace tana son sanin idan har da gaske kin karbi sha lelenta 



Hajiya Fadimatu tayi murmushi jin yanda ya karasa maganar sanan ta amsa Kiran Hajiya Hawau  ,   sun jima suna zantawa sanan hajiya Fadimatu cikin wani irin farin ciki ta ce" Haba , haba Hajiya ai yarda daya ce , da kuma na kowa , sanan tunda ta zamto musulma koda yayanta ashirin ai bai haramta ba , dan haka ina so insha Allah kiyi kokari nan da kwana uku ki zo mu hadu da shi Aban tun kafin ya juya sai ayi KO? 




Hajiya Hawau cikin Hamdallah da godiyar ubangiji ta ce " Allah ya saka miki da mafificin alkhairin dake nan gidan duniya da kuma na kiyama, Allah ya sa ki gama da duniya lafiya, Yanda kika kudurci aikata Alkhairi a kan marainiya Allah ya jibanci lamuranki 



Hajiya Fadimatu tayi saurin fadin" Amin hajiya aman plz ki dena Gode min na fada miki yiwa kai ne na yarda da ke da zuciya daya , haka suka datse Kiran su dukansu suna farin cikin abinda suka yanke Wanda a tinaninsu hakan shine banban gudumuwar da zasu yi dan taimakon marainiyar Allah wato Yar Mahaukaciya 




Cikin nutsuwa ta juyo wajen Yar Mahaukaciya Wace gaba dayanta take tsorace da wanan dakin, ita tunda ta wayi gari ta ganta a gidan duniya  bata taba , no bata taba kawowa kusan ranta cewar wai a nan gidan duniya za'a iya tsantsara wanan tsarin haka , Dakin ciki daya ne wani wawakeke sanan du madubi ne ya gewaye dakin sai gadon dake tsakiyar dakin kasan ba kafet jikin tils din kasan hoton Mubasshir ne aka zana da sajensa yana murmushi gaba daya wata kunya ta kamata gani take kawai kalonta ne yake ta kuwa tatare siket dinta ta matse ita kar yaga jikinta ( lol ) aman kuma mamakin da take Wai ina bayi? Sanan ina wajen kaya? Ita tsoroma ya mugun kamata da ace ita kadaice da ba abinda zai hanata ta zare a dakin nan 




Hajiya Fadimatu ta kamo hanunta cikin nutsuwa ta jata saman gadon Mubasshir suka zauna a gefen gadon sanan cikin sanyinta da kwarewa wajen kontarwa da mutun hankali ta ce" Rahma, Rahmatullah, mai yayi zafi da aka manta Kiran inalilahi wa'ina ilaihi raj'une ake kukan nan? Shin kin manta fadar Ma'aiki idan ka ga abinda ya kayar maka da gaba KO ya bata maka rai kayi ta maimaita sunayen Allah kana tazbihi kana kusanta da ubangijinka dan samun saukin zuciyar ka ? Domin kinsan ita zuciya a jikin dan Adam Mugun nama ce idan har zuciyar Dan Adam ta baci to fa ba mutun, sai ki ga mutun yana aikata abubuwa irin Wanda KO daba ba zai aikata ba dan kuwa cikin aikinsa tsabar kin Allah zaiyi yawa a ciki , shi kuwa wanan Halaka ne Rahma Tabas Halaka ne 




Cikin nutsuwa Yar Mahaukaciya ke kalon Bakin Mahaifiyar Mubasshir wata irin nutsuwa taji tana ratsata wace bata taba jinta cikinta ba hadi da kunya Wace ta rasa ta maicece, da sauri ta sada kanta kasa tana dan murza yatsuntsanta tana raurau da ido 




Hajiya Fadimatu tayi murmushi ganin Yar Mahaukaciya tana da kunya ta dago kanta ta ce" Ni sunana Nana Fadimatu sanan ni Mahaifiyar Mubasshir ce kuma ina son zama mahaifiyarki , shin zaki bani wanan damar?



Idanuwan Yar Mahaukaciya suka ciciko da kwallah tana kokarin zubar da hawayen shaukin wanan kalma ta Mahaifiyar Mubasshir 



Hajiya Fadimatu tayi Saurin girgiza mata kai ta ce " AF sanan idan abu ya faranta ranta kayi hamdallah ba kayi kuka ba 

Ta cire hijabin Yar Mahaukaciya ta dora kanta saman cinyarta a hankali tana yi mata labari har barci mai dadi yayi awon gaba da Yar Mahaukaciya cike da farin cikin wanan rayuwa sabuwa tare da adu'ar Allah ya  sa mai dorewa ce 









To fa shin mainene abinda su Hajiya Hawau suka yanke ne? Muje zuwa 😘

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    33



Sosai take bacin ta hankali konce harda ajiyar zuciya, Hajiya Fadimatu ta gyara mata konciya ta Mike a hankali gudun kar ta tashe ta ta koma wajen bakin ta 






Bayan wanan tarzomar kowa ya watse aka bar Hajiya Hawau ita kadai domin gaba daya bakin nata sunyi tafiyar su gudun kar a makala musu Yar Mahaukaciya 


A boye ta samu wayarta har tayi magana da mahaifiyar Mubasshir , bayan ta gama ne ta fito dan ta tatare tabarmin da ta shinfidawa bakin ta , tana fitowa ta tarar da Fati kawar Yar Mahaukaciya rakube kanta a kasa tana ta tinane tinane 



Hajiya Hawau ta karaso a hankali ta zauna kusa da ita ta ce" Fati tinanin mai kike?



Fati ta dago kanta ta kali hajiya sanan cikin gargadar murya ta ce" shin Hajiya ina sister ne? Hajiya dan Allah ki cireni daga cikin duhu cos ina cikin duhu ta karashe zancen da kuka 


A hankali hajiya Hawau ta dafa kafadarta ta ce" RAHMA ba mazinaciya bace , sanan mafaifiyarta ba mahaukaciya ba ce, kuma ita marainiya ce sanan ni kakarta ce, Kuma Dan Aljannah yayanta ne , wanene baki fahimta ba a ciki?



Fati ta ce" Kenan AA jikanki ne shima?



Hajiya Hawau kawai ta daga kanta alamar eh 


Fati ta sauke nanauyar ajiyar zuciya sanan ta ce" yanzu tana ina Ita din?



Hajiya Hawau ta ce" Tana gidan su Mubasshir dan haka ki mike kiyi wanka zan saka a rakaki wajenta , ki tafiyan mata da kayanta gaba daya kin ji?


Fati ta daga kanta tana farin cikin jin Rahma na gidan su AA Mubasshir , 

Hakan kuwa akayi Hajiya Hawau tayi kira ta shaidawa Mubasshir yayi Kiran securites ya shaida idan za'a kawo wata budurwa baka mai dan tsayi da kaya a shiga da ita ta baya , sanan ya shaidawa Mahaifiyarsa , ita kuwa sai murna ta karu dan Hajiya Fadimatu akoy son yaya mata shi yasa kulun adu'arta Allah ya bata kafin rasuwar mahaifin Mubasshir to bayan  rasuwar tasa ma bata daina ba tana fatan Allah ya baiwa Mubasshir sai a bata ta rike sai gashi yau Allah ya bata ya mai kyau haka tayi murmushi tana adu'ar Allah ya tayata riko 




Cikin bacinta taji an kankame mata  jiki firgigit ta farka tana zare ido domin bata san tayi baci har haka ba , idanuwanta ta shiga murzawa dan gaskatawa kanta Wanda take gani 



Fati tayi dariya ta ce" ni ce sis 


Yar Mahaukaciya tayi musrmushi ta ce" wa ya kawoki? Ya akayi kika zo ? Kinga abinda ya sameni ko ? A ina..........cikin sauri Fati ta ce" ke ki dan huta da tambayoyin mana , Hajiya ta fada min komai dena daga hankalinki haka kinji 



Yar mahaukaciya tayi shiru tana tinanin mai Hajiyar ta fada mata , aman sai ta share bata ce mata komai ba , 


Suna nan zaune Mahaifiyar Mubasshir ta kuma shigowa ta ce" Yar Fadimatu kin farka? A taso  ayi wanka domin yama tayi 



Yar Mahaukaciya ta ce " ohk mamana tana murmushi 



A hankali Mahaifiyar Mubasshir ta nufi daidai wani madubi ta mika hanunta a nitse ta dan shafa wani farin abu , abin mamaki kofa ta bude daga Yar Mahaukaciya har Fati da kalo suka bi Hajiya Fadimatu baki sake uwa zararu sanan ta kuma taba wani bayi biyu suka bude a cikin dakin cikin nutsuwa ta taho ta kuma taba wani abin sai dirowa ta bude ta zaro tapi ta nufi wajen tiraruka ta dauko kala uku du ta zube musu ta ce" kuyi wankan ga salaya, ga kuma wanan kafin ku gama kimtsawa za'a kawo muku kayanku ku saka 



Su duka suka amsa mata 


Har ta kusa FITA ta dawo ta ce" zaku tafi diner ne?



Fati ta ce" Eh 


Yar Mahaukaciya ta ce" aa 


Suka kali juna a tare 


Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" Kuyi shawara idan kun yanke shawarar sai na turo mai shirya ku 



Suka amsa mata da to ta juya ta fita 


Tana fita Fati ta zarowa Yar Mahaukaciya ido ta ce " hey😳, for what zaki ce ba zamu tafi ba?



Yar Mahaukaciya ta ce" ki gane sisi idan na tafi kinga abinda ya faru da safe bana so ya kuma faruwa 



Fati ta ce" auren yayanki ne , auren gidanku ne, dan kawai wata nonsence bata sonki a wajen sai ki ki tafiya? Sis harda mai shiryamu fa waouh har ina tinanin yanda zamu dawo idan aka shiryamu plz ki amince mu je muma 



Haka dai suka zauna suna ta musanyar yawu kan su je KO kar su je 









Eyah fans shin Su je din ne KO kar su je??????🤷🏿‍♀

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    34


Wanka suka shiga kowace ta dau lokacinta , ita dai Fati tana gamawa ta dauro alwalah ta zo ta gabatar da salar Magarib, tana nan zaune tana lazumi Yar Mahaukaciya ta fito ta nufi Jakarta ta buda ta dauki pad ta juya cikin bayin ta saka ta kuma fitowa kanta daure da tawul karami ta lulube jikinta da hijabinta 



Sai da Fati tayi sallar Isha sanan ta mike daga saman dardumar ta ninke ta ta tsaya ta zubawa hoton Mubasshir dake zane saman terrace din 



Yar Mahaukaciya ta ce" mai kike kalo?



Fati ta ce" sis kinsan Allah gaskiya banga laifin matan da suka yanyanka hanayensu lokacin annabi yusuf , ki duba ki ga irin kyan AA fa sis ni KO da AA kadai aka barni sai nayanyanke hanuna 



Yar Mahaukaciya ta bushe da dariya ganin yanda Fati tsakaninta da Allah take bayaninta har cikin zuciyarta yanayin yanda take fitar da zancen 


Ta ce" sisi kinsan wani Abu? Ni sam kyan mutun baya rudata wly ke wani lokacin nafi son mutun mai bakar fata cos yafi kyau 



Fati tayi mata kalon kin raina ni sanan ta ce" to tayaya kyau zai rude ki ? Ai dan kinsan kina da shi shi yasa , da baki da kyan nan da garin kalon mai kyau har sai kin fadi , sis dan AA yayanki ne shi yasa kyansa baya baki tsoro



Yar Mahaukaciya a ranta ta ce na fiki tsoron kyan bawan Allahn nan domin ina daya daga cikin wa'inda suka Ganshi yana zubawa mahaifiyarsa shagwaba , da a lokacin kika Ganshi da sai kin suma ma ina jin , aman a fili ta ce" idan kin gama ki zo mu kimtsa plz 



Suna tsaka da kimtsawa Fati ta dage ta gyara zama tana tsantsarawa Yar Mahaukaciya kwaliya mai shegen kyau da tsari ta caje mata girar ta domin girar kalar gashin kanta , ta dauko tana kokarin zabar mata jan bakin da zata shafa Hajiya Fadimatu ta shigo fuskarta dauke da murmushi 



Tayi musu salama 



Suka amsa suna gaishe da ita 


Ta amsa su tana ta zuba murmushi ta ce" kuyi hakuri yayana na barku ku kadai, kunsan bakin ne da yawa sai yanzu na samu na kufce 



Yar Mahaukaciya ta ce" lah ba komai mama 


Hajiya Fadimatu ta karasa tana fadin zaku tafi ne wajen dîner?



Fati ta ce" No mama ba zamu je ba 



Hajiya fadimatu ta ce ohk ba damuwa , daidai nan wata mata tayi salama da wata jaka a hanunta ta tsuguna har kasa tana gaishe da su fati , suka amsa suna kalonta 



Ta juya cikin murmushi ta ce" ma'am wacece kanwar ogan?



Hajiya Fadimatu ta nuna Yar Mahaukaciya ta ce" kin ganta nan baki ga kama ba?



Wace aka nunawa mai aikin bangaren Hajiya Fadimatu ce ta ce" kai masha Allah , Ashe ta warware ma , Allah ya raya mana ita ( uwa wata beby? )



Hajiya Fadimatu ta amsa da Amin Ya Allah sanan ta karbi jakar ita kuwa ta juya ta bar dakin 



Hajiya Fadimatu ta bude jakar  wasu abayoyi ne a ciki da kuma wasu mahaukatan less farare tas anyi dogayen riguna da su gwanin ban sha'awa da ribon na less  din ta ce" kunga wajen ango ga abinda zasu saka nan wanan less din , tunda bazaku tafi ba sai kuyi shigan arabian ku fito dan saboda hotuna da za'ayi mana da ango kafin ya tafi diner 



Yar Mahaukaciya ta ce" An gode mama,,,,,.....kafin ta karasa Hajiya Fadimatu ta rufe mata bakinta tana fadin no kar naji godiyar nan , dan mamanki tayi miki kyauta sai ki kama gode mata? No kiyi hamdallah ya wadatas sanan ta Mika hanu ta dauko wani Jan baki kalar pink ta Mika mata ta ce" wanan shine daidai da kwaliyarki 



Yar Mahaukaciya tana murmushi ta karba ta dan goga pink ne Wanda bai ciza ba sanan bashida man lebe a hade da shi ta fito tsaf da ita 


Hajiya Fadimatu a ranta ta ce" Allah yayi halita a nan , Allah ya kade hau da bakin duniya , a fili kuwa ta ce" Yar Fadimatu kinyi kyau har kin gaji masha Allah 



Yar Mahaukaciya tayi murmushi sanan ta sada kanta , Hajiya Fadimatu ta kali Fati ta ce" takwara kuyi Sauri ku fito fa kunsan al'adar mu da banbanci 



Fati ta ce " toh mama i'a gamu nan fitowa 



Ta juya ta fita ,  tana FITA Yar Mahaukaciya ta cire tawul din dake nanade da gashinta ta saka macaji baba ta caje kanta sanan ta dauko ribom ta daidaita gashin tsakiyar kanta ta daure ta warware abayar bata san lokacin da ta furta masha Allah ba ta juyo dan nunawa Fati sai taga ita har ta saka 



Fati ta ce" kawai ki rage mamaki yan Mata dan kuwa haduwa mun hadu saka nayi miki roling mu tafi ,



Yar Mahaukaciya ta saka tata Fati ta nada mata mayafin Abayar ta fito tamkar balaraba ga hasken da idanuwanta ke bayarwa idan ta kaleka abin ba'a cewa komai ,suka dauki takalmansu mai shegen kyau suka saka , Fati ta dauko wayarta ita kuwa ta kama hanyar fita cikin takunta na nutsuwa da daukan hankali 



Fitowa suka yi suka tarar da matar nan ta dazu tana tsaye tana jiran su , ta ce " Hajiya mu je na kaiku falon da ake salamar angon



Yar Mahaukaciya ta ce" salamar ango kamar yaya?



Amina ta waigo ta ce" Eh ai haka al'adarsu take yanzu angon ya fito tun dazu ana ta hotuna tamkar baza'a daina ba , idan aka gama sai a barku ku uku tunda Hajiya ce yar uwarsa ta jini da Mahaifiyarsa , Mahaifiyarsa tayi masa nasiha sosai da sosai shi Kenan sai ya tafi daga wajen dinern gidansa zai fice da matarsa shi Kenan sai jibi da auren zamu ganshi shima gasuwa zata kawo shi idan ya koma sai bayan sati guda kuma shikenan ya zama magidanci shima 



Fati ta ce " waouh wanan tsarin ya tsaru ya birge ni sosai tsarin nan , ta juya kan Yar Mahaukaciya ta ce " sister al'adar ku tana birge ni 




Yar Mahaukaciya tayi murmushi tamkar wata sakara ta dan juya kanta a ranta ta ce " nima yanzu na ji ,


Daidai nan suka karaso wani falo Wanda fadin haduwarsa bata lokaci ne , ya hadu ya hadu yayi karshen haduwa , cikin nutsuwa Yar Mahaukaciya ta saka hanunta ta bude tana kalon Fati dake yi mata magana , sai gani tayi Fati ta zama tamkar robo kikam tana kalon ciki 



Cikin faduwar gaba ta juyo a hankali idanuwanta sukayi arba da jama'ar dakin ta furta ya salam ta lumshe idanuwanta dan faduwar da gabanta yayi 


Hajiya Fadimatu ta mike cike da murmushi ta tarota ta kamo hanun Yar Mahaukaciya da Fati ta ISO har tsakiyar jama'ar dake hahakimce ana ta daukan hoto domin Mubasshir a zaune yake saman wata kujera mai ruwan ash da baki baba gaba daya idanu aka zuba mata ganin wanan yarinyar mai shegen kyau a tare da ita , 



Hajiya Fadimatu cikin Murmushi ta ce" Asalamu alaikum 


Gaba dayansu suka amsa mata salamarta kanan ta ce " Ina mai gabatar muku da Yarinyata Rahma , da kuma kawarta mai sunana , Kanwar Mubasshir ce she is my daughter my lovely Girl ta karashe tana sakarwa Yar Mahaukaciya Murmushi 




Gaba daya dakin suka kwashi dan surutu suna fadin waouh, 


Hajiya Halima ta taso ta karaso gaban kawarta tana murmushi ta Mika hanayenta ta kamo na Yar Mahaukaciya tana murmushi ta jata jikinta suka yi irin gaisuwar nan ta larabawa sanan ta jata gaban sauran kawayen Hajiya Fadimatu suna gaisawa cikin raha kowa yana mamakin daman yayanta biyu? 



Bangaren Mubasshir Hajiya Fadimatu ta nufa tana nazartar yanayinsa , lokaci guda du ya wani dan daburce yana kalon kasa gashi Mubinna ta rumgume shi ana daukan su hoto aman sam hankalinsa baya kan daukan hoton 



Hajiya Fadimatu na isa ita ma ta shiga aka dauke su da Mubinnat sanan ta yafito Yar Mahaukaciya , sai da gabanta ya fadi ta mike kamar wace Kwaï ya fashewa kaza a ciki ta nufe su , Allah ya taimaketa kafin ta isa Mubinnat ta daga waya tayi waje , 



Cikin nutsuwa ta isa abin mamaki kanshin tiraren da ta fesa shi ne a jikin Mubasshir , shima yana jin kanshin ya dago suka hada ido daidai ta ISO kusa da shi 


Cikin Sauri ya kawar da kansa yana ajiyar zuciyar da bai san KO na mainene ba , 


Hajiya Fadimatu ta kara matsota sosai jikin kujerar kamar yanda itama take ta ce " Yar Fadimatu ki saki jikinki mana sanan kiyi murmushi ayi mana hotunan mu 


Mubasshir ya dago kansa ya kali Mahaifiyarsa da alamar shagwaba a fuskarsa ya ce" Yar ?????🙁





Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce " yes 


Mai hoton ya dauke su ya kai kala biyar sanan Hajiya Fadimatu ta ja Yar Mahaukaciya ta zaunar da ita a gefen kujerar sanan ta dora hanunta na dama saman kafadarsa kasa kasa ta ce" wai ba zaku saki jikinku ba ana kalonku fa 



Mubasshir da yayi sumar zaune ya kuma dago da kansa da cikin muguwar kasala ya bi dayan hanun nata da kalo Wanda ya sha kunshi yayi mugun kyau a ransa ya ce Au Ashe sai da tayi kunshin , a fili kuwa ya sakar mata murmushi itama ta mayar masa inda mai hoto ya dauki abinsa tamkar itace amaryar yanda take wani annuri 


Haka dai akayi ta hotunan nan har lokacin nasiha yayi , gaba daya mutanen suka bar dakin harda Fati kawar Yar Mahaukaciya , 


Hajiya Fatima ta nemi waje ta zauna ta kali Yar Mahaukaciya dake kalon kofa tana son fita kuma ta rasa ya zata yi 


Hajiya Fadimatu ta ce" Yar Fadimatu zo nan ki zauna mu yiwa Yayanki gargadi KO?



Mubasshir ya zaro ido Yar Mahaukaciya ma ta zaro ido nima haka cos wanan gargadi harda abinda yaro ba zai ji ba , ita kuwa Mahaifiyar Mubasshir an fada mata Yar Mahaukaciya bazawara ce , shi yasa zatayi maganar ta a gabanta , shi kuwa gani yake sam bai dace ba karta raina shi dan kuwa KO da ta taba aure har ta haihu hakan ba yana nufin za'a yi masa galgadi a gabanta ba dan yarinya ce , ita kuwa mugun tsoron sa ne ya Sakata firgici jin za'a yi masa gargadi a gabanta 




Hajiya Fadimatu ta ce"""""""""""''''"'''''"""""""""""""""'






           Muah

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    35




Hajiya Fadimatu ta kare musu kalo sunyi wani cirko cirko suna kalon ta ta ce " yar Fadimatu matso kusa da ni ki zauna KO kema kina jure tsayuwa ne?



Yar Mahaukaciya ta kifta ido tamkar ta juya ta fice take ji aman kuma bazata iya yin hakan ba , cikin nutsuwa ta karasa ta zauna a kasa daidai kafar Hajiya Fadimatu , inda shima ya karaso ya zaunan 



Gyaran murya tayi sanan ta fara da adu'a , wato haka al'adar su take idan kayiwa yaron ka aure sai ka zaunar da shi ka tinatar da shi cewar da da yanzu ba daya bane , ka kara jadada masa irin nauyin dake kansa a yanzu Wanda idan yayi wasa da su tabas gobe kiyama yana cikin garari tsirar sa sai wani ikon Allah , hakan Hajiya Fadimatu ta dage wajen kawowa danta kwaya daya misalai da ayoyin da suka zo mana da mahinmancin iyali da yanda zaka kula da su , tana tsaka da yi masa wanan jawabin gaba daya ya nutsu maganganunta na ratsashi duk da ya san duk abinda take fada masa kamar ana kara yi masa bita ne aman kwarai yana ratsa shi kuma yana ji a jikinsa cewar dole ne ya kula da iyalinsa, jin mahaigiyarsa tayi shiru ne ya saka shi dago da kansa , aman mai zai gani *Hawaye* take sharewa daga idanuwanta 



Cikin kidima ya mike tsaye ya dare saman kujerar da take zaune har hanunsa na rawa ya dan karkato fuskarta , kwarai hawaye Mamanda ke zubarwa , cikin wata irin murya ya ce " Kuka? Hawaye daga idanuwan Maman Mubasshir? Shin mai ya batawa Maman Mubsshir rai haka? Mai ya daga mata hankali haka? 



Hajiya Fadimatu tayi lalausan murmushi a ranta ta ce' ina kaico da rashin sa'ar mata da kayi shi ya saka ni kuka aman a fili ta ce" Ina mamakin girman Mubasshir ne , yau da gobe sai Allah 



Yar Mahaukaciya ma da ta mike tana kalonta sai taji hawayen maman Mubasshir na shigar mata zuciya tamkar Mahaukaciyarta , haka kawai taji zuciyarta ta tsinke wani irin kuka yana kokarin zuwar mata tayi iya yinta ta dane shi aman sai da hawaye ya zubo mata tayi saurin sharewa 


Hajiya Fadimatu ta Mika mata hanu ta matso itama ta zauna suka Sakata a tsakiya a hankali taci gaba da jawabinta Wanda wani har kunya yake baiwa Yar Mahaukaciya , wasu abubuwan sai yau ta taba jin wai a aure akoy su kuma Dole a kiyaye , ita kam tata ta sameta koda yake Wanda ya nuna yana son nata ya fasa son nata kenan bata da wata damuwar tinanin idan fa bata yi biyaya ba itama zata hadu da fushin ubangijinta 


Sosai ta kwashe lokaci tana ta kara jadadawa har abokan Mubasshir suka fara dana masa kira ba kakautawa domin can wajen diner an taru sosai har amarya ta zo tana jiran karasowar ango su shige tare , nan Mahaifiyarsa ta salame shi ya mike suma suka mike dan su yi masa rakiya ta kama hanun Yar Mahaukaciya da hanunta na dama shima ta kama hanunsa da na hagu suka Sakata a tsakiya suna dan taba hira suna dan murmushi idan har ba saninsu kayi ba to lale zaka rantse cewar su duka yayanta 




Sai da suka rakoshi har daidai motar da tarin mutanen gidan da jama'ar sa suka cicika , daidai wata yar madaidaiciya fara mai shegen kyau Hajiya Fadimatu ta Bude masa gidan baya dan kuwa a yau ta hane shi tuki da kansa , 


Ya rungume ta suka yi irin gaisuwar larabawa ya juyo kan Yar Mahaukaciya suka kali juna tayi dan murmushi ta daga masa hanu alamar byby ya juya ya shige cikin motar tare da faduwar gabar da baisan KO ta meye ba 





Wajen diner ,casu ake sosai kowa yana kwasar gara inda Mubasshir yayi shiru yana kalon mutane hankalinsa a rabe yake wajen gida da yawa daman shi ba ma'abocin son kida ba ga kuma abinda ke nukurkusar sa Wanda yake matukar jin haushin kansa da kuma kunyar kansa dan kuwa wanan tabas abin kunya ne a gareshi ( to kaji )



Sahla ta juyo tana kalonsa taga hankalinsa a wani wajen cikin kisa ta matso daidai kunansa ta ce" Mijina tunanin mai kake?



Mubasshir yayi murmushi ya kaleta ya ce" ba komai wifey 



Ta ce " taso muyi rawa manan 


Yayi dan murmushi ya ce" kinsan su Maman Mubasshir suna kalo daga can fa 


Tayi far da ido ta dora kanta a kafadarsa ta wani lumshe ido , su kuwa masu daukan hoto da yan uwa sai yi suke 



Mubinnat dake hakimce tana kalo a ranta ta ce , wai a kan wanan skelet din ce zaka kasa zama a can , lale zaku dandana kudarku , tayi murmushi 



Zaune suke su uku da dan abin ciye ciye a gefen su suna kalon abinda ke faruwa sai suna ta yabawa haskowar da za'ayi aka hasko Sahla ta manawa Mubasshir kis a kuncinsa  su Yar Mahaukaciya suka zaro ido a tare nan da nan wata kunya ta kama Yar Mahaukaciya ta rufe idanuwanta 


Hajiya Fadimatu dake zaune   itama ta lura da yanayin Yar Mahaukaciya a ranta ta ce " BIYU Kenan domin tana wani wasi wasi a ranta aman ba komai lokaci  


[11/7, 07:51] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    36




Haka dai ta kawar da tinanin suka ci gaba da kalonsu har wani lokacin inda baci ya fara kama idanuwan su 


Hajiya Fadimatu ta ce " Baci KO?



Yar Mahaukaciya tayi murmushi tana murza ido 



Hajiya Fadimatu ta ce " ai sun gyara miki dakin naki ( wato dakin na wajen Mubasshir ita ta zaune shi dan kuwa yafi kusa da dakin Hajiya Fafimatun )



Yar Mahaukaciya a ranta ta ce " dakina? Waouh , a fili kuwa ta ce " an gode mamana 



Hajiya Fadimatu na matukar jin dadin sunan da Yar Mahaukaciya ke kiranta da shi wato *Mamana* 


Suka mike da niyar zuwa yin bacin suka yi mata sai da safe suka haura saman benen 


Suna shiga suka tarar an canza zanin gadon , an saka tirare mai kanshi an gogoge ko'ina sanan kayansu an jere su tsaf 



Fati ta kali Yar Mahaukaciya ta ce " ke princess ce ashe shi yasa kike luwai luwai da ke 



Yar mahaukaciya tayi murmushi tana cire kayanta ta zaro na baci ta saka tayi konciyarta 



Fati ma ta saka ta haura saman gadon ta lumshe ido can ta ce " yau za'a kwashi gara , duk da kashi ce Zala 



Yar Mahaukaciya ta bude idanuwanta ta ce " gara ? Ta me fa?



Fati ta karkato ta ce " ta angoncewa mana yau su AA za'a fada wata duniyar 



Yar Mahaukaciya ta zaro ido ta cije lebenta ta daga filo ta kwalawa Fati suka shiga kokowa uwa wasu kananun yara sai kyakyata dariya suke , can Yar Mahaukaciya ta nisa ta ce " Allah ya shirye ki 



Fati ta ce " ya shirye mu baki daya 




Washe gari tunda asuba Yar Mahaukaciya ta farka , ta saba gidan Hajiya Hawau idan suka Farka sai aikace aikacen su Hakan Yasa ta kasa hantsewa tana baci sanan zaman dakin ya ishe ta , cikin nutsuwa ta bude dakin ta fito daure da Zani na atampa da rigarta daidai ita da dan kwalin atampar ta sauko kasa ba kowa a falon duk da ba wata dauda gare shi ba ta zage ta shiga aiki kakabe can goge nan share can gaba daya har inda Yan Aikin basa tabawa dan wani abin sai mutun da kansa dan kuwa dan aiki bazai tsaya ya yi maka aikinka yanda ya kamata ba , kafin karfe takwas Yar Mahaukaciya ta gama gyare falon nan , sanan ta je bangaren masu aikin ta tambaye su ina tiraren gidan 


Cikin rawar jiki hanne ta fito tana mamakin Hajiyar ce da kanta take shara , lale wanan ta daban ce , ta fito ta buda wani dan daki Yar Mahaukaciya ta shiga , haba zo laga kalo tamkar dan shago ne aka Buda na tiraruka kanshi ta ko'ina tashi yake kai kace kasuwar tiraruka ta shiga , wangalau tayi da baki tana kama sunayen Allah tana mamakin rayuwa , bolarsu ta fado mata a rai da Mahaifiyarta ta lumshe ido tana adu'ar Allah ya sa bata cikin wata bolar , ganin zata fara sana'ar tata yasa ta shiga bubudawa can wani mai sikari ya mugun birge ta , kanshinsa yayi mata sosai hakan yasa ta dauko shi ta dauki abin kunawar ta fito ta rufo ta je ta kuna sanan tayi kicin wajen masu aiki 



Da salama ta shiga cikin kicin din gaba dayansu su hudu suka shiga gaishe da ita da harshen turanci , sarai hausawa ne aman kowace da iliminta kuma sunyi karatun girki , su duk a tinaninsu Yar Mahaukaciya bata iya hausa ba dan yanayin tsarin halitarta , 



Tayi murmushi sanan cikin kwarariyar hausarta ta ce " kun tashi lafiya? Ya aiki ?



Gaba dayansu mamaki ne ya kama su har hada baki suke wajen fadin " hajiya ashe kin iya hausa?



Yar Mahaukaciya ta kuma yin wani murmushin ta ce" plz ku dena kirana da hajiya , ya Za'a kira mamana da Hajiya Kuma nima a kiraye ni da Hajiya ? No ku ringa kirana da Rahma



Daya daga cikin su mai suna Aisha ta ce" kiyi Hakuri Hajiya ai ita Hajiya Baba ta gidan nan muna kiranta da Maman Rahma da can sunanta Maman Mubasshir to a jiya ta canza kinga ke sai dai mu ce aunty 



Yar Mahaukaciya tayi murmushi a ranta tana matukar kaunar Maman Mubasshir Wace ta dawo Maman Rahma wato ita sosai take girmama darajar matar , ta ce" to naji, yanzu mai kuke dafa mana yau?



Nan suka bubuda mata gaba daya abincin na yan gayu ne , wanin na larabawa ne ma mai yiwuwa na al'walin Mubasshir ne dan kuwa shi kadai ya dan dakata sai daga baya zai koma 


Yar Mahaukaciya ta ce " fanin jus fa?


Suka amsa mata da ai na kwali kawai suke sha 



Yar Mahaukaciya ta ce" am , fura zan hada da kuma jus na gargajiya 



Kalon kalo suka shiga yiwa juna Mariam ta ce" Fura? Fura ma tamu?



Yar Mahaukaciya ta ce " Yes KO babu kayan hadata ne?



Aisha ta ce" akoy sosai akoy komai da komai dan kuwa elhaj ma muna hada masa aman sai yace bata da taushi aman har hatsin a surfe Yake 



Yar Mahaukaciya ta ce " baya son Wace ba ta hanu ba shi yasa , dauko min komai harda baban turmi 



Mamakinsu dada karuwa yake balatana da suka ga Yar Mahaukaciya ta dage tana kirbar fura a turmi , sai da tayi mata lilis ta kuma maida ta a tukunya sosai furar ta hade kanta tayi wani irin taushi ga uban cikui ga kayan daka , Yar Mahaukaciya ta kwashe ta cicibra kayanta sanan ta raba gida biyu ta bar musu rabi , ta shiga hada jus na hausa sai da ta hada na gyada , da zobo, da kuma na abarba ta markadeta 



Su dai kalonta suke suna mamakin yanda yarinya mai gata haka har ta iya daka 



Karfe tara ta gama komai ta kwashe tayi frij da su sanan ta haura sama dan yin wanka 




Daidai lokacin Hajiya Fadimatu ta sauko , 

Tunda ta sauko falonta take mamakin gyaran dakin tayi murmushi ta ce" Lale yau Hanne tayi abin kanta , itace da tashi da wuri haka KO dai wani wajen zata tafi?



Tana zama ta dana Kiran dakin su nan da nan sai ga hanen ta duka har kasa tana gaisar da hajiya Fadimatu 



Hajiya Fadimatu ta amsa mata da fara'a sanan ta ce " yau su hanne anyi abin kai anyi aiki da wuri 



Hanne ta Sosa kai cike da kunya ta ce " Maman Rahma ai aunty Rahma ce tayi gaba daya aikin nan 



Hajiya Fadimatu ta zaro ido ta ce " Wace rahamr ? Tawa?



Hanne da tsoro ya  kamata ta ce" eh ita Maman Rahma ai harda fura tayi a kicin 



Mamakin Hajiya Fadimatu ya kasa boyuwa sai ga su Yar Mahaukaciya suna saukowa. Fati Harda akwatinta 



Suka tsuguna suna gaisar da Hajiya Fadimatu 

Ta amsa fuskarta cike da Murmushi ta ce" Fati ya haka kardai ki ce min sai tafiya 



Fati ta sada kanta tana murmushi ta ce " wly mama yanzu yayana yayi kirana ya ce ya kwana a Lagos nayi masa kwatance ya biyo ya dauke ni dan yanzu zai fice gida 


Hajiya Fadimatu ta ce " Eyah to ai sai kin karya KO?



Fati ta ce" Mama ai ya dade da isowa tana dan Murmushi 



Hajiya Fadimatu ta Mike tana fadin maza a hada mata kayan kari a kwano ita kuwa ta haura sama ta hadawa Fati sha tara ta arziki ma'aikatan gidan suka kwasa suka yi waje da  su 



Yar Mahaukaciya  tayi mata rakiya har waje suna yiwa juna byby cike da kewar juna ,



Ta juyo zata shiga falo Kenan taga wata mota mai mahaukacin kyau ta shigo da wani irin gudu tamkar za'a tashi sama 


Gabanta ne yayi mugun faduwa ganin Wanda ke cikin motar





,,,           morning ,,,,,,,,,,,😘

[11/7, 07:51] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    37



Gabanta ne ya fadi ganin wanda ke kokarin fitowa daga cikin motar , ta kara maida hankalinta tana kalonsa , shadar jiya ce a jikinsa a dan yamutse kadan daga sama ,sanan fuskar nan a mugun hade tamkar ba shine jiya yake son kin murmushi ba , bata Ankara ba sai gani tayi ya kifta ta ya shige falo , haka kawai ta tsinci kanta da kasa komawa dan kuwa yanayinsa zai nuna maka cewar yana cikin bacin rai sanan yana yana bukatar ganawa da Mahaifiyarsa *Mubasshir* Kenan 



Yana shiga sanyin kanshin falon da dadadan tiraran da aka kuna suka daki hancinsa ya lumshe idanuwansa ya saki ajiyar zuciya 



Hajiya Fadimatu dake zaune ta baiwa kofa baya ta ji alamar an shigo aman bata waigo ba ta ce" Yar Fadimatu kin dawo daga rakiyar? Sai ki zo ki fada min a ina kika iya daka fura mai kyau haka 



Cikin nutsuwa da karayar zuciya yake takawa har kusan mahaifiyarsa , a hankali ya zagaya gabanta ya tsuguna ya dora kansa a saman cinyarta 



Hajiya Fadimatu da tayi mutuwar zaune ganin Mubasshir a wanan rana shi da ya kamata sai a gobe a ganshi , gashi yau ya zo karfe goma na safe sanan ba a cikin hayacinsa ba , a hankali ta dora hanunta na dama tana shafar sumar kansa wace da dan ruwa ruwa a cikinta shaidar yayi ta wanke kansa dan yaji saukin abinda ke damun sa 



A hankali yake samun nutsuwa yana sakin ajiyar zuciya sanan yana godewa Allah da jama'ar gidan duk sun juya sun bi jirgin karfe biyu na dare zuwa kasa mai tsarki wasun kuwa yan chadi na karfe biyar suka bi , 



Hajiya Fadimatu ta dan dakata da adu'ar da take tofa masa ta ce " Mai ya fito da angon jiya yau? Mai ya fito da saurayi yau? Shin ya yarda al'adar mu ne KO yaya?




Mubasshir ya dago da kansa bayan ya daidaita muryar sa ya kali mahaifiyarsa sanan cikin raunin murya ya ce " Maman mubasshir KO daya Mubasshir bai yarda al'adar sa ba , no ina matukar jin kunya maman Mubasshir cos nayi alkawarin bin al'adata shi yasa dole na dawo gidan nan a yau dan nayi biyaya , Mamana i'm sorry 



Rintse ido Hajiya Fadimatu tayi domin sarai ta gane inda zancen ya nufa wato Sahla ba cikakiyar budurwa bace shi yasa ya dawo a yau , wata kunya ce ta kama ta da kuma godiyar Allah da ya Sanya duk basa nan , sai tausayin danta a ranta ta ce mai yiwuwa zuwa gaba ya samu cikakiyar , a fili kuwa tayi gagawar kawar da zancen ta mike ta kama hanunsa tayi wajen table da shi tana fadin albishirinka 



Ya ce " goro yana biye da ita 



Ta ce " Yau sistern ka tayi maka mutuniyar taka tun da safe ta farka ta daka ta da kanta , ta KO yi laushi sosai da gani zata birge ka 




Mubasshir ya dan yatsina fuska duk da horon Hajiya Hawau ce aman tata ta daban ce sam bazata iya hada furar Hajiya ba 



Zaunar da shi tayi sanan ta leka dan ganin rakiyar tayi ni sa da yawa 


Tana lekawa ta ganta zaune tana kalon fulawowin gidan , a hankali ta ce " Yar Fadimatu 



Firgigit ta waigo tana amsawa ta mike a nitse ta karaso 


Hajiya Fadimatu ta ce " yayanki ne ya zo , ki zo ki bashi mutuniyar tasa , kinga kuwa kamar kinsan zai zo ta karashe tana yi mata murmushi 



Yar Mahaukaciya ta shige itama tana murmushin , direct kicin din ta shige ta shiga dama furar da harhada komai da komai , ta dauko katon faranti ta jera kayan a saman sa harda jus jus din da ta hada ta dauko gabanta na faduwa tana tsoron kar aje har yanzu yana yanayin da ya shigo wato cikin bacin rai 



Tana tunkarar table din taji Hajiya Fadimatu na aikin nata wato gargadi da ban baki , nitse tayi salama saï da ta ajiye farantin tsakiyar table din sanan ta tsuguna har kasa ta ce " barka da safiya , an tashi lafiya?



Ciki ciki ya amsa mata da lafiya lau sanan ta Mike da niyar juyawa , Hajiya Fadimatu ta ce" yaya dai , a zo a karya KO? 



Yar Mahaukaciya ta juyo a nitse ta ce " No mama ai bana jin yunwa na sha jus din nan ta nuna jus na ayabar 



Hajiya Fadimatu tayi murmushi dan a zaman da Yar Mahaukaciya tayi a gabanta jiya zuwa yau ta lura bata son hayewa abinci ta ce " ai fa jiya ma abinda kika sha Kenan jus , aman yau da rana ni da kaina zan baki abinci ki ci 



Yar Mahaukaciya tayi gaba tana dan murmushi , Mubasshir yayatsina fuska a ransa ya ce" iya yi duk haka suke shegen kin son abinci ga shegen boyayen mugun hali a tatare da su ya mika hanu ya bude furar bayan tafiyarta 






Sahla ce konce tana kuka dan kuwa zuwa tayi aka yi mata dinki aka kara matseta sosai har doctern na fadin KO Aljani ne shi bazai gane cewar a bude take ba , sai dai kash bata san cewar duk inda take tunanin Mubasshir to ya zarce tinaninta sai gashi tun kafin ya idasa manufarsa ya gane cewar a bude fa take wani ya rigaye shi 


Wayarta dake ajiye saman bed din ta dauki tsuwa ta Mika hanu ta dauko sunan mahaifiyarta ne ke yawo a Saman screen din ta dana ta kara tare da fadin hello cikin shakakiyar muryarta 



Hajiya Marhaba ta ce" beby ya kika kwana? Ina fatan dai lafiya lau 



Sahla ta ce" lafiya lau mama



Hajiya Marhaba taji muryar tata wata iri ta ce" kin tabata? Muryar taki nake ji wata iri 



Sahla ta fashe da kuka tana fadin na shiga ukuna Mama wly yayi tafiyarsa , shin yaya zanyi?



Hajiya Marhaba ta kwashi di kira da salamewa ta ce" ya tafi gidan uban wa? Taya zai FITA ya barki a haka? Ba cewa akayi su ga yanda al'adar su take ba ? Kardai aje irin mazan nan ne an mori ganga an yar da sauran , ? Can tana tsakar fadanta wani Abu ya fado mata a rai ta dan dakata 


Ta ce " Sahla 


Sahla ta amsa 


Ta ce" ki fada min gaskiya u'r NT Virgin?



Gaban Sahla ya fadi ta shiga kame kame da inda inda 



Hajiya Marhaba ta ce" Dan ubanki ki fada min gaskiya idan kin san a bude kika je masa gida ki fada min tun da wuri mu nemi mafita mu gayawa boka tun kafin ya dankara miki saki dan ubanki 




Sahla cikin tashin hankali ta ce " eh a bude 



Hajiya Marhaba ta datse Kiran tana babalawa Sahla zagi da sakacin da tayi tun wuri bata sanar mata ba ayiwa bakin zaren tufka nan da nan tayi Kiran bokanta ta sanar masa komai abinda yake faruwa harda fadin a daure shi sai yanda suka yi da shi 



Bokan ya bata amanar za'a fara aiki a lokacin ma aman Dole ta je da kanta 



Hajiya Marhaba ta ce " ba damuwa gatanan zuwa





To fah shin wanan boka zai iya kara daure AA Mubasshir??????? Muje zuwa😘😘😘😘😘


[11/19, 9:34 AM] ‪+234 909 534 8504‬: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    38


*I'm sorry please ayuka ne sunyi yawa aman bi'izinillah zanyi kokarin ganin na gama shi love u*











Hakan kuwa akayi ta shirya da kanta ta je gidan bokan ya gama tsafe tsafen sa ya bata magungun nan da Sahla zatayi aiki da su dan ganin Mubasshir ya haukace a kanta 


Daga gidan bokan ma direct gidan sahlan ta zarce tana isa aka tsare ta da tambayoyin Wace ita , sai da suka yi Kiran Sahla cikin fada ta ce" Mahaifiyar tawa zaku tsare a kofa?



Cikin Sauri ya bata hakuri ya bude mata 


Hajiya Marhaba baki ta wangale tana kalon wanan gida , ita mamaki take da Mubasshir ke tuka kansa da kansa alhalin ya malaki arzikin da koda a jirgi ne sai ayi yawo da shi a tsakar garin Lagos aman may be bai yarda da kowa ba ne , su dai ta fado masu gasasa , haka har ta samu ta karasa cikin falon Sahlan inda take tsaye tana jiranta 



Sahla da kyar ta mike ta daukowa Mahaifiyarta jus dan bata son mai aiki ta gani aje Mubasshir ya sani 



Hajiya Marhaba ta bita da kalo har ta dawo , abinka da uwar zamani kuma sam kunya ba a tsarinta yake ba ta ce " ke da kika ce ga a yanda kika zo kuma wanan tafiyar fa ?




Sahla ta tabe baki ta ce" hm momy ba'a cewa komai ni fa gaskiya du na Sare, na tsorata gaskiya momy wly tsoronsa nake kamar raina 



Hajiya Marhaba ta zaro ido ta ce " tap to bara kiji abinda zan fada miki , haka zakiyi ta hakuri har ki saba , sanan ga sakon Boka nan kiyi tayi har mu kule masa bakin gaba daya kawai sai yanda muka yi da shi,  dan kuwa KO da wasa bana ra'ayi jin makamancin cewar ba zaki iya ba dan KO wanan gidan kadai ya malaka miki to fa mun haye balatana ina hango mana nesa 



Sahla ta amsa tana kara yatsina suka ci gaba da hirarsu ba ita ta bar gidan ba sai da ta ci abincin rana karfe uku tayi sanan ta fito ta shiga motarta ta ficewarta ( to kaji )





Bayan tafiyarta Sahla ta Mike ta shiga aikata gaba daya abinda mahaifiyarta ta saka ta sanan ta darmi aniyar shiga ta daga hankali dan ta lura da mutumin ya FIya fadawa hanu 




Tunda ta haura sama tayi konciyarta ta lumshe ido ta fada duniyar tinanin mai ya kawoshi gidan a yau shi da akace sai gobe? Aman mai yiwuwa yazo ganin mama ne dan a irin yanda ya shaku da ita daman da wuya ya iya kwanaki ba tare da ya ganta ba , tana cikin tinaninta baci yayi awon GABA da ita , ba ita ta farka ba sai da salar la'asar ta mike a firgice tana salati tana mamakin bacin da tayi a nitse ta nufi bayi ta sakarwa jikinta ruwa tayi wankanta tsaf Sanan ta fito daure da tawul dinta ta zauna ta bude Jakarta ta makaranta ta kama karatunta tamkar suna tsaka da karatun, sai da taji ta gaji sanan tana dan jin yunwa sanan ta mike ta bude Jakarta mai kayanta na sakawa , abin mamaki Hajiya Hawau sabin kayanta kawai ta zubo mata a jakar tayi shiru tana kalon wa'inda ta cire har wani dan wari suke dan kuwa da su tayi bacinta ta farka bayan ta ci aikace aikacen nan da su , ta kara dadagawa a zuciyarta ta ce , gaskiya bazan iya saka sabin kayan nan ba uwa wata amarya , to naje ina da su , gaskiya aa , ta koma ta dauko zaninta da rigarta ta mayar da kayanta hankalinta konce ta daure kanta da dan kwalinta ta nufi waje daidai ana kiran magarib , 



Mubasshir ne zaune suna ta kara tataunawa da mahaifiyarsa bayan adu'o'in da ta kara masa sanan ta bashi hakuri harda neman alfarmar ya zauna lafiya da matarsa kar ya nuna mata komai , yayi hakuri tunda ga abinda yasa ya aure ta to kawai ya jure kar ya goge aikin ladan da yayi niya 



Mubasshir kansa a kasa ya ce " Insha Allah maman Mubasshir zanyi biyaya sanan zanyi kokarin ganin na bi abinda kika ce i promise ,




Tayi murmushi ta ce " Allah yayi maka albarka , Allah ya baka yaya masu biyaya 



Ya ce " Amin yana murmushi domin a rayuwarsa yana matukar kaunar yaya , yana son yaya sosai duk da yanzu wani tinanin ya fara darsuwa a zuciyarsa 


Mikewa yayi ya rungume mahaifiyarsa yayi mata salama da niyar tafiya gidansa daidai nan Yar Mahaukaciya ta sauko ta tsuguna har kasa tana gaishe su 



Hajiya Fadimatu ta kamo hanunta ta ce" kin sha baci sau uku ina shiga sai na tarar baki farka ba , yunwa bata tayar da ke ba ?



Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta ce" Ai mama ni ma yau nayi mamakin bacin nan nawa ya jima sosai 



Mubasshir dake tsaye yana kalonsu suna birgeshi tamkar Mamanshi ta haifeta dan dai farin wanan aljanar ya fi na mamanshi , a hankali ya ce " zan fice sai na dawo maman mubasshir 




Hajiya Fadimatu ta ce " am Yarona nace ba , ina son saka yata makarantar islamiya kasan karatu da jama'a yafi shiga , kuma ina son ka fadawa kaf masu tsaron gidan nan cewar idan akayi baki da sunan ita suke nema to a barsu su shigo dan kaga akoy yan makarantarsu sanan yarinyata ta isa aure idan nayi siriki kar a tsayar min da shi a waje 


Da Sauri mubasshir ya kaleta harda zaro ido gabansa yayi wani mugun faduwa idanuwansa suka wani firfito waje , ita kuwa wata irin kunya ta rufeta ta mike da sauri har tana hade kafafuwa wajen sauri ta shige kicin 


Ya bita da kalo gabansa ya kara faduwa 


Hajiya Fadimatu dake kalonsa tana nazarinsa ta ce " kana ji ?



Mubasshir ya juyo da Sauri ya ce " ohk toh zzzzan fada harda wata sabuwar inda inda da ta same shi , ya juya da Sauri ya fita ya nufi motarsa still gabansa bai dena faduwa ba 



Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta lumshe idanuwanta ita kadai ta san abinda take tinani sanan ta kuma yin wani murmushin ta mike ta nufi kicin dan ta dawo da yarta da taji kunyarta ta tsere 






.



.






........................... . . . . . . . . . . . . . . . . . .  . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . . .

[11/19, 9:35 AM] ‪+234 909 534 8504‬: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                    39



Yana fita ya fada motarsa ya tayar ya kama hanya tafe yake kwakwaluwarsa tana cikin caji sai maimaita kalmar inalilahi wa'ina ilaihi raj'une yake ya rasa wanan wani irin tashin hankali ne ke tunkarar sa 


Tun kafin ya isa kofar gidansa yake horn da gudu aka bude masa ya fada gidansa ya ajiye motar a nan ba tare da ya daidaita ta ba ya fito ya bar wayoyinsa a nan cikin motar ya nufi cikin gidan 



Sahla dake zaune ta sha kananan kaya Wanda ilahirin jikinta a waje yake tana jin karar motarsa domin daman hankalinta gaba daya a wajen yake , 


Cikin yanga da karairaya ta Mike ta nufo kofar dan ta taro sa , kafin ta karasa har ya bude ya fado falon ja tayi ta tsaya gabanta na faduwa tana tinanin ta karasa ne KO ta juya ,balatana a irin yanda ya shigo 



Tsayuwa Mubasshir yayi yana karewa Sahla kalo tun daga kitson atach din da aka yarfa mata kananuwa masu shegen kyau da yanayin tsarin halitarta da Allah yayi mata , sam Sahla a shafe take tun daga saman har kasan sanan abin haushin mamarta har sun dan fara faduwa daman gasu kananuwa hakan na nufin au haka halitarta take KO kuwa an zubar da su ne , yayi saurin rintse ido da ya Tina wai yayi taraya da matar da wani ya fara taraya da ita , 


Cikin bacin rai ya raba ta gefenta wani tirare mai karfin tsiya ya bige masa hanci take ya furta a'uzubilahi minan shaidanin rajim , yaci gaba da tafiyars ya nufi dakinsa 


Da gudu Sahla ta bi bayan sa tana rungume shi ta baya ta saki wani irin kuka mai tsuma zuciyar duk wani mai saurare , 

Ta kai wajen minti biyar a haka sanan ya juyo da ita a gabansa cikin kakausar murya ya ce " Kuka? Sahla kina kukan jin kunyar halayenki ne, kina kukan irin dabi'unki ne, kina kukan kin banzatar da kanki ne KO kukan na share ki kike?



Cikin shashekar kuka Sahla ta ce " Haba Yaya Mubasshir mai yasa zaka yanke min irin hukuncin nan ba tare da kayi bincike ba ? Ka sani wly ba laifina bane kadara ce Wace ba Wanda yafi karfin ta afka masa, Haba Yaya Mubasshir dan Allah kai fa musulmi ne taya zaka yanke hukunci haka ba tare da bincike ba?




Mubasshir yayi tsai yana kalonta a ransa ya ce lale KO shekarunta nawa? Yarinyar da har tasan ita ba budurwa bace har ta san ta je wajen wani katon ya kara wangaleta yayi mata aiki dan ya mayar mata da abinda ta kau a titi wai itace zata yi tsaye ta kirayi kanta da kadara ? Tabas akoy na kadara kuma akoy na ra'ayi, ya lumshe idanuwansa a fili ya ce " Kadara? To Allah ya kare mu da mumunar kadara ya juya dan kwata kwata baya son wanan yawan dumin 



Sahla ta kara shan gabansa ta ce " Dan Girman Allah , Dan Soyayarka da fiyayen Halita, Dan Darajar mahaifanka ka yafe min ka manta da komai muyi rayuwar mu cikin aminci dan Allah 



Gaba daya ji yayi tamkar an dadaure masa gabobin jikinsa irin yanda ta hada shi da Allah , cikin kasalaliyar murya ya ce " Tabas ni musulmi ne , bazan so na kwana da haushin ki a raina ba , sanan du mai yafiya Allah yana yafe masa kurakuransa shi ma , ya dafa daidai zuciyarsa ya ce " Na Yafe miki , sanan zan ci gaba da rayuwar aure da ke aman fa bisa sharadi biyu zuwa uku idan kin amince 



Cikin sauri Sahla ta ce " na amince koma mainene 



Ya danyi murmushi ya ce " a yanzu na farko ina son ki dan nisanta kanki da ni na dan lokaci kadan dan na samu nutsuwa kafin na dawo gareki , a cikin gidan nake ba wani waje zan je ba , aman ina son nayi rayuwa da ibada har naji na ware da wanan , sai dai idan kin san kina da muguwar sha'awar da zata hanaki yin hakan 



Wata irin kunya ta kama Sahla da dana sanin tarboshi a haka cikin sine kai ta ce" no aa ba komai Insha Allah zanyi iya yina dan ganin na kiyaye , mainene sauran sharadin?




Ya dan cije lebensa ya ce " idan lokacin ki san su yayi zan sanar da ke , sanan ya juya cikin nutsuwa ya fada tankememen dakinsa yana sakin ajiyar zuciya 



Sahla ta bishi da kalo tana cije lebe domin ta dirki magunguna gudun yau ma kar ta sha wahalar da ta sha jiya sai dai a banza  ga kuma maganin da aagaifiyarta ta ce shi kadai ma dubu ashirin ta baiwa boka sunansa malaka idan ya sadu da ita shikenan ta saye shi , haka ta juya tana mutsumutsutu ta nufi dakinta itama 





Yana shiga dakin nasa ya nufi bayi ya dauro alwala ya fito ya kama nafillah yana karawa duk idan ya kai sujada sai yayi ta adu'a yana rokon sasaucin abinda ke damunsa , da ya gama ma ya mike ya cire kayansa ya saka na baci ya juya ya konta 



Lumshe idanuwansa yayi yana adu'ar baci aman ina hotonta ya fado masa a idanuwansa ya mike tsaye ba shiri ya shiga zirga zirga a fili ya ce " anya kuwa Mubasshir baka sayarwa kanka tashin hankali ba?



Ya koma ya fada ya jawo filo ya rukumkume yana sakin ajiyar zuciya aman sam bacin ya kauracewa idanuwansa banda juyi ba abinda yake yana kokarin cire hotonta daga idanuwansa dan kuwa sam basu dace ba , wanan zancen idan ya fito ai kowa ma sai ya debe masa albarka dan wanan ai cin amana ne







To fah mai ya hana honorable baci? Hoton wacece yake kokarin cirewa daga zuciyarsa????????????????????????????????????????????????????????????????????


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*





                      40




Da kyar baci barawo yayi awon gaba da shi , baci marar dadi dan kuwa cike yake da mafarkai marasa dadi , a ganinsa domin mafarkinta ya kwana yi Wanda har wani zazabi ya zubo masa dalilin hakan dan kuwa damuwa bata daga cikin abinda ya sani , ba dai irin wanan damuwar ba 






Konci tashi yau har kwana uku daidai da auren Mubasshir Da Sahla inda rabonsa da gidan mamarsa tun washe garin auren sa bai koma ba yana gidansa sanan shi da kansa ya cire dokar da ya dorawa Sahla KO ya rage tinanin abinda bazai fishe shi ba,






Kamar yanda ta saba ta farka da wuri tayi aikace aikacenta Wanda Hajiya Fadimatu tayi tayi ta rabata da su aman ina sai ta farka ta ga ta gama komai hakan yasa ta kawo ido ta zuba mata sanan tana matukar farin cikin irin yanda sam Yar mahaukaciya bata da ragonta sanan ga biyaya sosai take jin dadin yanda take kafakafa da duk abinda ya shafeta , 


Bayan ta gama aikinta ta koma dakinta ta tsala wankanta tana fitowa Hajiya Fadimatu ta fito cikin bakar abayarta ta sha nadinta tsaf masha Allah 


Yar Mahaukaciya ta duka ta ce" barka da safiya mama



Hajiya Fadimatu ta amsa tana mikar da ita ta ce" yata zan fita , may be na dan jima , daga nan zan biya makarantar ku dan hutu kinga ya kusa karewa na ga abinda ya dace ayi KO?



Yar Mahaukaciya ta ce" to mama Allah ya kaiki lafiya ya maido ki lafiya 



Hajiya Fadimatu ta amsa da amin ya Allah sanan ta juya tana mai adu'ar Allah ya sa wanan hadi da sukayi niyar yi alkhairi ne 





Hajiya Hawau na hango cikin mota tana zaune da hijabinta zumbulele Hajiya Fadimatu ta karasa direba ya bude mata ta shiga sanan ta ce" unguwar yan baiwa zaka kaimu inda wakili ya sauka 



Direba ya ce " toh Hajiya sanan ya harba motar bakin titi ya kama hanyar gidan wakili Elhaj Muhammad 



Hajiya Fadimatu ta gaisar da Hajiya Hawau cikin mutunci sanan ta ce " tabas nima na yarda da tarbiyar yarinyar nan domin camera na laka a dakinta duk abinda take aikatawa ina kalonta sanan ina saurare , sai dai abu guda dake daure min kai , 



Hajiya Hawau ta ce " mai yake daure miki kai?



Hajiya Fadimatu ta ce " am akoy abinda ke damun Rahma domin ta fiya tinani KO haka Allah ya halice ta?




Hajiya Hawau ta ce " tabas nima na sha ritsata da tambayar shin tinanin mai take saï tace ba komai , sai nafi mayar da hakan kan KO dan yaronta ya rasu ne ?




Hajiya Fadimatu tayi shiru sanan ta nisa ta ce" hakane , Allah ya sa abinda zamu aikata alkhairi ne dan ni kam nayi ta rokon Allah kan isan har ba alkhairi bane to ya cire min wanan tinanin daga zuciyata aman cikin ikonsa a kulum kara sha'awar hakan nake 




Hajiya Hawau ta ce" tabas alkhairin Kenan Allah ya biya mana burin mu sanan ya kade shetan 



Daidai nan direban ya bubude musu kofa suka fito suka nufi falon inda wakili Elhaj Muhammad ke zaune yana jiran karasowar su 





Bayan sun gaisa Elhaj Muhammad ya dago kansa ya gama nazartar Hajiya Hawau tabas daga ganinta ka ga tsohuwa mai kamala , sai dai ba a nan gizo ke sakar ba , shin da gaske ne abinda ta fada ?



A nitse ya ce " baba tabas na gamsu da bayananki sai dai wani hanzari ba gudu ba ,mai zai nunan shedar eh lale yarinyar nan mutuniyar kirki ce? Sanan shi yaron nan baba jininki ne kuwa?



Hajiya Fadimatu ta dauko wayarta ta ciro wata memori ta jona jikin TV daram sai ga vidion Yar Mahaukaciya tun zuwanta gidan da yawancin maganarta harda idan tana tare da kawarta Fati , da komai sanan ta ce " Yaya ka yarda da maganata ka jagoranci daurin auren nan domin yarinyar nan yar Amana ce ceton rai zamu yi , Allah shi zai bamu ladan mu 




Elhaj Muhammad ya aa numfashi ya sauke Sanan ya ce " toh babu damuwa Allah ya sa alkhairi ne , yanzu su liman din suna can dakin bakin KO?




Hajiya Hawau ta amsa da eh suna can 



Ya ce " sunan yarinyar Rahma wa?



Hajiya Hawau ta ce " lokacin da tazo daidai da sunanta ta manta hakan ya sa mukayi duk yanda ya dace a musulunce muka saka mata Rahma 



Elhaj Muhammad ya kuma kalonta shi dai yana dan kokonto aman bashi da wani iko a nan Dole ya aiwatar da umarnin hajiya fadimatu haka ya mike ya tafi wajen su liman din da niyar daura auren Rahma da agonta ..................................................................................🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀



           

🇳🇪Belles écrivaines du Niger



*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                    41


Sun jima zaune sunyi shiru kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa jiran vilowar Elhaj Muhammad suke , 


Bayan kamar minti arba'in sai gashi ya shigo da damin goro a hanunsa yayi salama 


Suka amsa masa a tare suna kalonsa 


Waje ya samu ya zauna ya fuskance su ya ce " cikin ikon Allah an daura aure a gaban shedu sanan kuma ga goro na samu Kiran sarki na shaida masa ya ce eh aure taya shi ake Allah ya sanya alkhairi, 


Hajiya Hawau ta ce" kana nufin *Rahma* ta zama matar *Dan Aljannah*?


Elhaj Muhammad ya ce " Kwarai kuwa ni na wakilce ta liman ishak ya wakilci Mubasshir Allah ya sa alkhairi aka hada 


Hajiya Hawau ta ce " Alhamdulilah Allah abin godiya tabas alkhairi aka hada Allah ubangiji ya fi karfin su Allah ya kare duk wani mugun abin da za'a jefa dan a bata wanan taraya sanan Allah ya hada Hankalinsu 


Hajiya Fadimatu ta amsa da Amin ya Allah


Haka suka gama suka tatara suka nufi gidan Hajiya fadimatu 


Suna shiga suka tarar da Yar Mahaukaciya konce saman doguwar kujera tana bacinta  , cikin nitsuwa Hajiya Hawau ta karasa ta tataro gashin kanta ta daidaita mata shi sanan ta dora mata dan kwalinta da ya fadi a hankali ta ce " ina ji a jikina ke Yar Halak ce, sanan ke ba mutuniyar banza bace , hakan yasa na gommaci ki auri bawan Allahn nan tun kafin su saka rayuwarsa a garari, jinina ne Idriss sai dai kash bashida mahaifiyar kirki , sam bai yi dace da uwa ba , haka yar uwarsa tayo halayar mahaifiyarta Wace ta raba soyayar da da uwa,

Ni na san Ilyasu baya cikin hankalinsa shi yasa nake yi masa uzuri Allah ya yaye masa abinda ke damun sa ya haskaka rayuwarsa, kema Allah ya baki hakuri da juriya kan rayuwar da zaki tsinci kanki nan gaba 


Hajiya Fadimatu dake zaune tana kalon Hajiya Hawau tayi Murmushi ta ce " Baba tabas ance zamani ya canza kana iya haihuwar yaro ka kasa tankwasa shi , na sani ne bi'izinillah gata muka yiwa Mubasshir l'a zai gode mana kan hakan , aman fa ina neman wata alfarma 


Hajiya Hawau ta kaleta ta ce" Alfarmarki KO maicece fada min ita insha Allah zanyi kokarin ganin na cika miki 


Hajiya Fadimatu ta ce " bana son su san an aura musu juna nafi son na kara wanke yata ta goge da ilimi ta yanda zata kwaci kanta koda za'a cutar da ita, ina son yaronki da kansa ya nuna yana so dan kar yaga an bashi kyauta yayi kokarin banbanta darajarta da ta Sahla du da ita bazawara ce aman itama mutun ce so plz hajiya ki taya ni mu boye musu 


Hajiya Hawau tayi shiru ta ce " to aman hajiya kar mu taka dokar musulunci fa , kar aje ta kula wasu samarin bayan ita ga mijinta 


Hajiya Fadimatu ta ce  " tabas wanan shi na fara tinawa aman kuma zan saka ido sosai a al'amuran ta , l'a komai zai tafi daidai 


Habiya Hawau ta ce " Toh Allah ya kama mana 


Sun kusan minti talatin sanan Yar Mahaukaciya dake sheka bacinta ta farka da adu'a a bakinta tana rike dan kwalinta dake kokarin koncewa , 


Ido ta zaro ganin Hajiya Hawau zaune , ta mitsika idanuwanta ai bata san lokacin da ta tashi da Sauri ta fada jikin Hajiya Hawau ta saki kuka ta rukunkumeta 


Itama kukan take na yaushe gamo sai da Hajiya Fadimatu ta ce " ya isa hakanan sanan suka sasauta 


Hajiya Hawau ta talafo fuskar Yar Mahaukaciya ta ce " kiyi hakuri yata , kiyi hakuri 


Yar Mahaukaciya ta girgiza kai ta ce " Haba hajiyata ki dena bani hakuri kan laifin da ba naki ba sanan wly ni na yafe har cikin zuciyata , 


Hajiya Hawau tayi murmushi ta ce " Allah yayi miki albarka ,


Ta amsa da amin sanan ta juya wajen Hajiya Fadimatu ta ce " Mamana tun yaushe kika dawo? KO tare kuka zo?


Hajiya Fadimatu cikin murmushi ta ce " Mun dan jima da shigowa kina dan hutawa shi yasa naki na tashe ki dan na san halinki sarkin aiki ta karasa tana murmushi 


Haka sukayi ta labarin su har yama tayi direban Hajiya Fadimatu ya mayar Da Hajiya Hawau gida cike da kewarsu Yar Mahaukaciya 


Gidan Mubasshir ,


Zaune suke saman diner suna cin abinci Sahla ta sha ado sai zuba kamshi take tana iyayi shi kuwa gangar jikinsa kawai ke tare da ita aman zuciyarsa ta tafi aikinta tinani wata can daban 


Sahla ta ce " konci tashi yau har munyi kwana biyar da aure , husby yaushe zaka kaini na ga momyna?


Mubasshir ya kaleta ya ce " au har kinyi kewar gidan ne?


Sahla tayi fari da idanuwanta ta ce " eh to ba sosai ba aman momyna nafi kewa 


Mubasshir ya ce " Sahla ba fa mu kadai bane a cikin gidan nan 


Sahla ta tsayar da cin abincinta ta ce" eh man husby akoy masu aiki KO?


Mubasshir ya ce " no banda masu aikin akoy iyayena a cikin gidan nan


Sahla ta ce wasu iyayen naka bayan Hajiya


Mubasshir ya kaleta a ransa ya ce *Hajiya* au bazata ce mata mama ba? A fili ya ce " eh banda maman Mubasshir inada iyaye da nake kyautatawa suna saka min albarka dan gamawa da duniya lafiya kuma ina son matata ta koyi halayana na kirki 


Sahla ta dan yatsina fuska a ranta ta ce lale ma har wasu bare Kenan ka yayubo min a gida tabas zanyi août da koma su waye su , aman a fili ta ce " oh ohk toh kuma a wajen ina suke?


Yayi murmushi ganin yanda bata iya boye damuwarta ya ce " ai ki gama cin abincin sai mu tafi ki Gansu KO?


Sahla ta ce " ba damuwa 


To fa Sahla shin kin sans abinda mijinki ke tanadar miki?  ..........'

[

*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                    42


Bayan ta gama cin abincinta yana zaune saman baban kujerar tsakar falon yana kalon TV ta fito da wandon nata da rigar ta ce " mu tafi husby


Mubasshir ya dago kansa yana kalonta shi bai san ana konbo da rama ba sai a kan Sahla ya girgiza kansa ya mike ya dauko mata abaya baka da mayafinta ta karba ta saka tana yatsina suka kama hanya , ita dai burinta ta ga su waye a cikin gidanta 


Tafiya ta kai ta minti goma da suka yi a tsakar gidan sanan suka ISO wani wajen mai shegen kyau , abinda ya bata mamaki yanayin ginin wajen ya fi nata kyau , haka dai ta zuba ido tana biye da shi har ya tura ya shiga da salama , ta biyo bayansa itama tana wara idanuwanta 


Wata irin zabura tayi abinda idanuwanta suka gane mata , wasu tsafi ne yangom a zaune a saman cafet suna cin abinci wata tsanwar miya mai warin dadawa ta doki hancinta idanuwanta suka sauka a saman miyar gogo wace sam ba hakora a bakinta abincin ma sai ta dame shi sanan take iya hadiyewa ga bakin nata gaba daya ta jamula shi da miyar wata irin tashin zuciyar ba gyaira ba dalili ta tasowa Sahla da sauri ta saka hanunta ta toshe bakinta da hancinta ta zaro ido ganin Mubasshir ya saka hanu yana sakawa wata tsohuwar abinci a bakinta sanan ya juyo ya nuno mata sahla , Abinka da tsafi aikuwa ta Mike da kyar tana fadin Yau ga matar Yaron mu har cikin gidan mu 


Sahla ta shiga baya baya dan ta lura dukan su fama suke su taba mata jiki , bata Ankara ba taji wata ta taba ta tana juyowa ta ga Gogo ce ai bata san lokacin da ta saki ihu ba ta juya da gudu ta nufi bangarenta tana rusa kuka wiwi 


Mubasshir ya zaro ido ya san a rina aman bai taba tinanin abin zai kai haka ba , wai a nan ta tardo su an kimtsa su ne , da irin kafin ya tafi aiki da yake biyowan nan ne da ta suma ma dan a lokacin suka farka wasu har kashi a nan suke yin kayansu dan kuwa tsafi ne sosai ya tara yake ciyarwa da shayarwa bisa yardar hukuma da saka hanunta harma masu gatan dan kuwa irin kulawar da yake basu tafi wace zasu samu a gidan nasu 


Sai da ya zazaunar da su yayi Kiran masu kula da su sanan ya juya ya nufi bangarensa 


Yana shiga kakarin amai ya fara ji ya girgiza kansa ya nufi dakinsa yayi konciyarsa ya dauki waya yayi Kiran mahaifiyarsa 


Daidai lokacin suna zaune Hajiya Fadimatu na gyarawa Yar Mahaukaciya gashinta dan gobe zata fara zuwa makaranta wayar dakin tayi ringin 


Yar Magaukaciya ta mike ta dauko dan wayar jikinta da doguwar waya Wace za'a iya janta 


Hajiya Fadimatu ta ce" daga maga mu ji kowaye?


Yar Lahaukaciya ta daga ta yi salama


Daga dayan bangaren Mubasshir ya ja wani dogon nunfashi ya kasa amsa salamar muryar nan duk da sanin mahinmancin salama haka kawai ya tsinci kansa da wani irin yaunin baki 


Yar Mahaukaciya ta ce " hello , heloooooooo?


Ta mikawa Hajiya Fadimatu tana fadin Mama ai ba'a magana KO an datse Kiran ne ban sani ba ?


Hajiya Fadimatu ta karbi wayar daga hanun Yar Mahaukaciya ta kara a kunanta tayi salama 


Daga dayan bangaren Mubasshir ya amsa salamar a kasalance sanan ya ce " Maman Mubsshir ina yini 


Hajiya Fadimatu ta saki murmushi dan ta gane ya kasa amsa salamar ne jin muryar Rahma , ta amsa gaisuwar sa sanan ta ce " lafiya nake jin muryar taka kamar maran lafiya?


Mubasshir ya shiga kame kame ya ce" am daman aa baci ne nake ji shine nayi kira nayi miki sai da safe 


Hajiya Fadimatu ta ce " To Allah ya tashe mu lafiya , am daman insha Allah tomorrow yarinyata zata fara zuwa makarantar islamiyar fa 


Mubasshir ya danyi Jim sanan ya ce " Maman mubasshir plz a kula da tsaronta direba ya ringa kaita yana jira har ta fito ya daukota ya dawo da ita saboda kinga ba'a so a san inda take , sanan malaman nasu mata ne kadai?


Hajiya Fadimatu ta ce " da mata da maza ne 


Yayi Jim sanan ya ce " To maman Mubasshir plz ta kula 


Hajiya Fadimatu ta ce " kai ni fa na haifeka zakana kokarin koyar da ni yanda zan kula da yata? Aman ai batayi baci ba KO na baka ita kayi mata hudubar?


Da Sauri ya ce " no maman Mubasshir kiyi hakuri ba haka nake nufi ba , love u , good night 


Hajiya Fadimatu tayi Murmushi a ranta ta ce zama kayi nufin hakanan din aman a fili ta ce " ohk by a gaishe min da Sahlan ta datse Kiran 


Mikewa yayi zaune daga koncen da yayi ya shiga kikifta idanuwa ya ce " Maman Mubasshir plz da hakuri kika yi KO wani irin malami take da bukata sai na dauko ya ringa koyar da ita saboda kar aje rana ta baci ldriss ya hadu da ita alura ta tono garma ( to fa ka tabatar dan haka kake gudun fitarta? )


Haka yayi ta tinane tinane hardai ya yanke shawarar da shi kadai ya san kayansa ya gyara konciyarsa yana adu'ar baci ya lumshe ido yana fatan zakara ya bashi sa'a 🤔 


Karfe bakwai ta gama abinda ta saba sanan ta shiga wanka tana fitowa ta zauna ta shafa mai ta daga kayan makarantar tata ta islamiya doguwar riga ce har kasa sanan hijabi shima har kasa da nikaf na matan aure da budurwar dake bukatar saka shi 


Ta saka rigar Kenan tana kokarin konce hijabin dan an daure shi ne da wata yar igiya wayar dakinta tayi kara ta matsa a hankali ta daga tare da salama 


Hajiya fadimatu ta ce " yar Fadimatu sauko ina jiranki yanzu 


Yar Mahaukaciya ta ce" to mama 


Ta ajiye wayar ta sauko da hijabin dan Hajiya Fadimatu ta konce mata daurin tana zuwa ta tarar da Hajiya Fadimatun zaune tana zuba abinci cikin faranti , ta duka tana gaisheta 


Hajiya Fadimatu ta amsa tana murmushi daidai nan aka turo kofar falon aka shigo 


AA ne cikin wata dakakiyar shada fara kar sai zuba kamshi yake ya shigo da salamarsa 


Hajiya Fadimatu ta zaro ido ta ce " lafiya da safiyarnan? Mai ya fito da kai yau? Ka manta al'adar mu ne?


Mubasshir ya karaso yana murmushi ya kama hanayen mahaifiyarsa ya ce" Maman mubasshir i really miss u , kinga abokina ya gayaceni yau shine na biyo na ganki kafin na fice 


Hajiya Fadimatu ta ce " Kenan ka karya dokar?


Mubsshir ya ce " Maman Mubasshir Al'ada ba adini ba , kinfi kowa sani , so please ki bar maganar nan kiyi murnar ganina 


Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" to sanunka da zuwa 


Yar Mahaukaciya dake tsugune ta ce" barka da safiya yaya 


Mubasshir ya juyo ya zuba mata ido ba wata kwaliya tayi ba aman har wani fizga yanayinta yake, ya ce " Barkan ki 


Yar Mahaukaciya ta Mike ta mikawa Hajiya Fadimatu hijabin na hanunta ta ce " Mama na kasa kunce wanan daurin gashi lokaci ya kusan yi 


Mubasshir bai san ta ina maganar ta fito ba saï ji yayi bakinsa na fadin" halan wanan rigar da ita zaki tafi makarantar ?


Hajiya Fadimatu da Yar Mahaukaciya suka kale shi a tare , da tambaya a fuskar su 


Sai a lokacin ya gane cewar yana fa son ya kwafsa kansa hakan yasa cikin basarwa ya dana wayarsa yana kalon kofa ya ce" am naga kamar tayi kadan ne , am manta ,


Ya mike yana fadin Maman Mubasshir tayi sauri dan hanyata ne na sauke ta sai na fice yayi waje yana karasa zancen 


To fa Malan yayadai???????

[

*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                    43


Ya kai minti ashirin a zaune cikin mota yana jira , abinda bai taba yi ba a rayuwarsa wato zaman jiran mutun ya fito koma waye dan koda mahaifiyarsa zai fita ta san halinsa bata barin sa zaman jira dan kuwa yanzu zai fara shiga yana fita yana takurata da Maman Mubasshir ki fito plz, aman wai yau shine zaune yana jiran fitowar wanan yarinyar da ba komansa bace , haka kawai ya ja tsaki a fili ya ce " dan na kula da amanar da na daukowa kaina ne da ba dan hakan ba da ba Wanda zai fito da ni a yau daga gidana , 


Yana tsaka da mita ya hango fitowarta ya tsura mata ido nan da nan ya ji wani sanyin dadi na ratsa shi ganin hijabinta har kasa sai dai fuskarta a bude kuma da alama da nikaf a hanunta , 


Horn ya dana hakan ya sa ta nufi motar dan kuwa ita a tinaninta ai yayi tafiyarsa tana isa ta Buda baya ta shiga tana furta barka da warhaka Musa direba 

Maganar ta tsaya mata a makogwaro sanadiyar hada idanuwa da suka yi ita da Dan Aljannah 


Ido ta zaro tayi Saurin dora hanunta a saman bakinta tana kikifta ido ta ce " yaya yaya kayi hakuri nayi tinanin Musa ne yake yi min horn i'm sorry  ta karasa tana kokarin bude motar ta fita sai karkarwa hanunta yake sanan motar taki buduwa 


Sai da ya gama kalonta a yanayin tsoro son ransa sanan cikin dakakiyar mirya ya ce " ba'a tsayar da ni jira , wanan ya zama na farko kuma na karshe cos hakan na bata min rai ba kadan ba , ki dawo gaba dan ni ba Musa direba bane 


Wani iri yake saukan mata a jiki yanayin maganarsa gaba daya tamkar tayi tsere haka take jin zuciyarta nayi mata lugude da kyar ta samu ta bude motar ta fito tana ta adu'a ta bude gidan gaba ta shiga kanta a kasa sanan ta kama yar karamar yatsarta tana ta murzawa da karfi tamkar ita tayi mata wani laifin


Tafiyar kurame ne suke domin ba Wanda ke cewa dan uwansa ufan sanan KO saukar numfashin su ba mai ji sai yatsarta da ta koma jajawur dan azabar murzata da take tunda suka fito tsawon tafiyar minti arba'in Kenan dalilin gosulo , suna isowa makarantar ya shiga direct har cikin kofar baban office din malamin mai suna ustaz Mu'azu ya faka 


Cikin nutsuwa ta dago kanta sai taji ya ce " ina zuwa 


Fita yayi ya shiga office din bai wani jima ba sai gashi ya fito da wata malama a bayansa ta karaso wajen Yar Mahaukaciya ta bude motar ta fito 


Tana fitowa ta tsuguna ta gaisar da ita , ita kuwa sai washe hakora take ta kamata ta mike sanan ta ce " muje madame 


Sai da ta sada Yar Mahaukaciya da ajinta sanan ta dawo wajen Mubasshir AA 


Tana zuwa ta ce " an gwada mata kuma insha Allah za'a kiyaye , aman fa dalilin bazata zaman jiran malaman mu maza ba zatana sauka a lokaci daban daban dan haka dole mu dauki nimber wayar ka idan ta tashi da wuri muyi kira kazo ko ka turo a mayar da ita gida 


Mubasshir ya ce" wanan duka ba damuwa idan dai har za'a kiyaye wanan , sanan komai akeda bukata ni za'a kira ba ita ba so ya mika mata takarda ya ce ganumberna personnel koda yaushe kika kira zan daga 


Malamar mai suna Husnah ta karba tana godiya ya juya ya shige motarsa yana hamdallah a cikin zuciyarsa 


Tafiya yake wayarsa ta fara ringin sai da tayi har sau uku sanan ya mika hanu ya dauko dan ganin KO waye ke kiransa da safe haka 


Number Hajiya Marhaba ya gani hakan ya sa ya nemi waje yayi parking ya daga tare da salama 


Hajiya Marhaba dake haki ko tsayawa amsa salamarsa bata yi ba ta ce " Mubasshir ina gidanka ina jiranka yanzu 


Mubasshir ya ce " am Hajiya Gidana kuma? Ni ai ina gidan Maman Mubasshir fa 


Hajiya Marhaba ta ce " ohk mu hadu a can din 


Kafin ya bata amsa har ta datse kiran a hankali ya furta ya Salam sanan ya tada motarsa ya juya kanta ya nufi gidan mahaifiyarsa 


😘😘😘😘😘😘😘😘😘


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                      45

Kamar yanda suka zo haka suka koma tafiyar kurame suna isowa ta kama kofar zata bude ta fita 


Mubasshir da ya kasa hana kansa magana ya ce ji mana 


Yar Mahaukaciya ta jiyo tana kalon kasa dan koda wasa bata iya kalonsa cikin ido 


Mubasshir ya mika hanunsa ya karbi nikaf din dake hanunta ya daga yaga eh lale nikaf din ne


Ya ce " mai yasa ke bakya saka shi ne?


Yar Mahaukaciya ta dago ta kale shi , idan bata manta ba wataran ta taba riskar hirar su da Hajiya Hawau yana fada mata cewar ya tsani yan matan nan masu saka nikaf din munafurci dan abinda suke aikatawa gonda gagarumar karuwa da su yawancinsu aman yau kuma ya tambayeta mai yasa ita bata saka ba?


Tambayarki nake , Muryar Mubasshir ta dawo da ita daga duniyar da ta fada ta ce " Am daman ance na matan aure ne , yan mata sai idan mutun yana da ra'ayi ne zai saka idan kuwa baka ra'ayi to karka saka 


Mubasshir yana sauraronta sam bai so maganar ta tsaya daga nan ba ya lumshe ido ya ce " aman ai zawarawa ma na iya sakawa KO?


Yar Mahaukaciya ta dago idonta suka yi ido hudu ta kawar da kanta ta ce " eh 


Ya Mika mata ya ce " toh ki ringa rakawa duk inda zaki je tunda zawarawa ma na iya sakawa kinga kina layi KO?


Yar Mahaukaciya ta karba ta daura a fuskarta idanuwanta kadai ake gani ba'a ganin sauran fuskarta , ta dago ta sauke idanuwanta cikin nasa ,


Wani irin yar yaji a jikinsa harma yayi nadamar Sakata daura nikaf din , dan da ta daura kawai sai kyan idanuwanta suka fito ba kadan ba har wani walkiya suke balatana na tsakiyar nan mai kama da na mage , Saurin kawar da kansa yayi yana fadin kina iya tafiya 


Yar Mahaukaciya ta kama ta bude kafin ta fita a hankali ta ce " Allah ya saka da mafificin alkhairi sanan ta fice tana tafiyarta da ta saba


Ba shi ya bar wajen ba sai da yaga eh lale ta shiga falon sanan ya ja yayi gaba yana mai jin haushin kansa irin yanda yake mantawa da ayukansa masu mahinmanci wajen tinanin gyara rayiwar yarinyar nan , dan ba dan ya daukarwa kansa alkawarin kulawa da ita da bazai tsaya batawa kansa lokaci a kanta ba , aman insha Allah zai nema mata miji Wanda ya san zai kula da ita domin Allah a daura musu aure KO yayi abinda zai fishe shi ( toh fa )


Tana shiga Hajiya Fadimatu na amsa waya ta zauna sai da ta gama ta gaishe ta 


Cikin murmushi take amsawa ta ce" ah Yar Fadimatu ya akayi kika saka nikaf din?


Yar Mahaukaciya tana cirewa ta ce" Mama ai yaya ne yace na saka kar na kuma fita babu shi 


Hajiya Fadimatu a ranta ta ce toh kaji shi da ya tsani saka nikaf yau kuma shine da kansa yake cewa a saka ? Lale yau kam ta gama yarda da abinda take zargi aman zata gwada shi tayi murmushi ta ce " toh ki ke kiyi wanka sai ki sauko mu ci abinci 


Yar Mahaukaciya ta amsa tana mikewa ta nufi dakinta 


Konci tashi har Hutun su Yar Mahaukaciya ya kare sun koma makaranta inda wanan karin da wani irin gata take tafiya wanda wataran direba ya kaita wataran Maman Mubasshir kanta kawai sai ta shirya wai rakiya zata yi mata har cikin makarantar ba wanda bai Santa ba sanan yanzu idan bata son zuwa ta ci abinci har inda take ake kawo mata cikin mutuntawa 


Yau ta tashi a lati dan kuwa mura ta hanata baci sai daidai asuba ta samu ta rintsa jikinta zafi rau da zazabi 


Hajiya Fadimatu ta fito karfe bakwai da rabi ta zauna tana jiran saukowar Yar Mahaukaciya abin mamaki har karfe takwas tayi bata sauko ba , a fili ta ce" lafiyar Yata kuwa? KO ta tafi ne? No bazata tafi bata sanar da ni ba dan ba dabi'arta bace 


Hakan yasa ta mike ta nufi dakin Yar Mahaukaciya tana fatan Allah yasa lafiyarta lau 


Tana shiga ta hangota konce lulube cikin bargo tana karkarwa , Da sauri ta karasa ta dan yaye mata bargon tana fadin Yar Fadimatu lafiya?


Yar Mahaukaciya dake barin sanyi har hakoranta haduwa suke da kyar ta iya furta mama can cikin kasan makoshinta sanan ta maida idanuwanta ta rufe 


Ai da gudu Hajiya Fadimatu ta juya tana rarumar wayarta ta danawa doctern su kira ta fada masa yarinyarta ba lafiya kuma sosai ne jikinta yayi zafi sosai 


Doctern ya ce " To Hajiya Zan karaso nan da Awa biyu dan makocina ya rasu muna wajen jana'iza 


Hajiya Fadimatu ta ce " Eyah Allah ya jikansa ta datse Kiran ta shiga neman lambar Mubasshir dan kuwa bazata iya zubawa yarta ido a haka ba har tsawon wani lokacin 


Lambarsa ta wajen aiki take kira dan tasan a wanan lokacin yana office aman secreteria dinsa ta dauka tace bai karaso ba 


Tana kokarin Kiran numbersa ta gida duk ta rude taji takun hayowa matatakalar dakin nasu 


Da Sauri ta leka ta ga Mubasshir ne ya shigo ai bata san lokacin da tace " Yarona maza karaso Yarinyata ba lafiya plz 


Wani irin faduwar gaba ya tsinci kansa da ita ya kara Sauri ya haye saman ya nufi dakinsa na da Wanda Yar Mahaukaciya ta zaune shi ya tura ya shiga ya karasa saman gadon da Hajiya Fadimatu ta yaye mata rufar tana kokarin daure mata gashin kanta ta kamata ta mikar da ita daga koncen da take 


Saurin kawar da kansa yayi dan kuwa irin doguwar rigar barcin nan ce mai sulbin gaske duk da tsayinta aman lafewa take a jikin mutun , idanuwansa ana mike ta suka sauka saman mamarta dake tsaye tsai tamkar su tsole ido hakan ya mugun kayar masa da gaba da dana sanin kalonta 


Hajiya Fafimatu ta ce" wai zaka kama min ita ne na saka mata hijab mu kaita asibiti KO kalon kasa zaka tsaya yi yarinya na galabaita?


Mubasshir cikin inda indar da bai san yana da ita ba ya ce" mmmmamar Mubasshir bara na dauko docteur Halima a haka bazata iya jiran harkar asibiti bâ


Kafin ta bashi amsa ya fita ya figi mota ya nufi office din Docter Halima tana tsaka da aikinta ya daukota ya kawota 


Tana zuwa ta shiga gwaje gwaje nan ta gano mura ce ke damun Yar Mahaukaciya ta rubuta magunguna suka Fito da AA dan ya Mayar da Ita wajen aikinta 


Bayan ya ajiyeta ya nugi pharmacie dan siyan magungunan da aka rubuta 


Bayan ya siya ya kaiwa Hajiya Fadimatu ya dawo falo ya zauna ya kuna TV aman ina hoton dazu ya fado masa a idanuwansa a fili ya furta " A cikin nan yaro ya konta kuwa? Dan cikin gonda nashi na namiji dake shafe da nata , a shafe yake tamkar bata cin abinci KO haka halitarta take???


I dn kw

[

*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                      46


Shi kadai yana zaune tamkar sabon kamu yana magana da kansa daidai Hajiya Fadimatu ta sauko daidai ya ce" To kai Mubasshir mai ya shafeka idan ma ba nata bane?


Hajiya Fadimatu ta ce" Lafiya kake magana kai kadai? 


Mubasshir ya mike yana dan murmushi ya ce" No maman Mubasshir ba komai ina dai tinanin wani abin ne, 


Hajiya Fadimatu ta ce" toh Allah shi kyauta 


Mubasshir ya ce" Maman Mubasshir ya jikin Yar taki?


Hajiya Fadimatu ta ce" ah yanzu da sauki har baci ya dauke ta  


Ajiyar zuciya ya sauke  sanan ya ce Allah ya kara lafiya


Hajiya Fadimatu ta amsa da amin 


Ba ita ta farka ba sai gabanin la'asar domin maganin nata na mura mai saka barci ne , tana farkawa cikin ikon Allah da karfin jikinta ta farka ta shiga bayi ta wanke jikinta ta wanke bakinta ta dauro alwalah ta fito ta dauko Zani da Riga na atampa ta saka ta kabarta sallah 


Tana gama salolinta ta mike ta cire hijabin ta koma dan kuwa har a lokacin barcin bai saketa ba ta ja zif dinta tayi konciyarta dan bata son saka rigar da ta dan kama ta kuma ta konta da ita  , baci yayi awon gaba da ita 


Cikin nutsuwa ya turo kofar ya shigo da yar salamarsa shirun da yaji ne ya saka shi idasa shiga dan ya san kawai tana barci 


Hangota yayi ta hade kafafuwanta tana bacinta rigingine aman gashin kanta gaba daya ya rufe mata fuska , 


Gaba daya ya tataro courag dinsa ya nufi gadon yana adu'ar Allah ya sa bacin take dan ya ga ta canza kayanta ne ma ya saka shi nufar inda take ,    


Yana zuwa ya dan dakata daga nesa da ita yana kalonta , jikinta daidai da ita , fuskarta ta yara ce , yanayin jikinta bata sha fama ba , to aman wacece ita? Yaron da ya rasu wanene shi? Mai dinta ne ? A ina ta samo shi? KO dai sato shi tayi? Idan ba sato shi tayi ba to dan waye ? Da ita ta haife shi da jikinta ya nuna duk da akoy matan da idan sun haihu cikinsu na komawa ya lafe aman wanan ai a shafe ne yake daga ganinsa 


A fili Ya furta no bazan iya ba , bazan ci gaba da zuba miki ido a haka ba aje ki cutar da ni, a yanzu haka na gaji da irin cutar da ni din da kike dan haka hakurina yazo karshe yau bazan kuma hakura da hakan ba 


Gadan gadan ya nufeta yana tatare kafar wandonsa 


Hanayensa biyu ya saka ya tayar da ita daga konce 


Cikin tsoro ta buda idanuwanta ta sauke su cikin nasa wanda yayi iya yinsa dan ya hada idanuwan da ita 


Bakinta ta buda cikin karkarwar baki ta ce " Yaya mai akayi? Lafiya?


Mubasshir ya ce " who are u?


Yar Mahaukaciya ta zuba masa ido jikinta ya fara karkarwa gabanta na dukan uku uku tsoro ya darsu a zuciyarta 


Cikin karaji Mubasshir ya ce " da ke fa nake bazaki bani amsa ba ?


Yar Mahaukaciya tayi Saurin fadin wayo Mahaukaciyata  ta fashe da kuka ta hade kanta da gwuiwarta , sosai take kuka har jijiyoyin wuyanta sunyi rako rako 


Wani irin tausayinta ya darsu a zuciyar Mubasshir a hankali ya sauke hanunsa daga kafadunta cikin dakakiyar muryarsa ya ce " wacece Mahaukaciya?


Yar Mahaukaciya ta dago kanta ta sako daga Saman bed din cikin sarkakiyar murya ta ce" Mahaukaciya itace Mahaifiyata , bansan kowa ba ban san komai ba , Mahaukaciya da ita na fara bude idanuwana , ita na fara gani , mu ci abincin mu mai tsami , mu sha ruwa a bola , Mahaukaciya tana cikin Hauka aman tana nemo abinda zamu ci da cikin mu , Mahaukaciya koda an taba ta tayi min duka tana dawowa ta rungume ni muyi baci, 

Ta silale kasa cikin kukan mai tsuma zuciya ta dago ta hade idanuwanta da Na Mubasshir Wanda ya zamto tamkar mutun mtuni ta kwashe gaba daya labarin rayuwarta ta fadawa Mubasshir dake zaune yana kalonta 


Bayan ta gama bashi labarin Hajiya Fadimatu dake rabe tana sauraron su ta kara kasa kunenta 


Mubasshir ya kare mata kalo ya ce " Karya kike Rahma, Karya ne , shin taya zan yarda da ke? rahma kina nufin neman mahaifiyarki ne ya saka kika baro bolarku? Taya ma zan yarda da ke duk irin yanda Hajiya ta kula da ke ta daukeki tamkar yar cikinta aman kika watsa mata kasa a ido kika yi mata karya? Ni wanene da bazaki yi mini ba ? Ki fada min gaskiya Rahma wacece ke ?


Yar Mahaukaciya ta lumshe idanuwanta , tabas ta san akoy ranar kin dilaci aman ta so sai ta hadu da mahaifiyarta sanan hakan ta faru , mikewa tayi a hankali ta nufi saman drewernta ta dauko alkur'aninta ta zo ta zauna gaban Mubasshir ta lumshe idanuwanta ta dora hanunta a saman kur'anin ta ce " Na Rantse da ,,,,,......  Kafin ta karasa fadin abinda yake bakinta Mubasshir ya Mike ya karbe kur'anin cikin zaro ido ya ce " *Baki da hankali ne?*


Yar Mahaukaciya ta Mike itama cikin karajin ta ce " *Ka  barni na rantse Mubasshir , ka barni na rantse maka da alkur'ani mai girma duk da irin yanda mutun da gaskiyarsa yayi rantsuwa da shi yake samunsa ka san duk jahilcina na san idan bakada gaskiya ka rantse da shi ka halaka*


Ta kuma fuskantar sa ido cikin ido ta ce " *Tabas ni Mahaukaciya ce dan kuwa Mahaukaciya ta haife ni* sanan na boyewa Hajiya ne dan ina mace , macen ma mai rauni marar gata , ina gudun idan hajiya ta koreni ina zan dosa, ina gudun wani abin ya kuma tunkarata, ina gudun fadawa wata halakar , aman a kulun cikin bakin cikin biyewa Mama ta gidan nan nake , domin a kulun na kali darajarta da kimarta sai nayi kuka na karyar da nake yi mata , aman a yanzu alhamdulilah tunda Allah yayi kafin na bar gidan nan kun san KO wacece ni , na gode da kulawarku gareni Allah ubangiji ya biya ku ranar gobe kiyama 


To fah , shin Yar Mahaukaciya zata kara GABA ne ? Ya aurenta da Mubasshir zai kasance? Zata ga mahaifanta ne KO yaya?


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                      47


*Happy Juma'at, Allah ya karbi ibadun mu, Ya kyautata karshen mu, ya sa Aljana ta zama makomar mu dan nabiyin Rahamati*


  Tana gama fadar haka ta juya cikin mutuwar jiki ta nufi akwatinta dake ajiye sai a lokacin ta tina zip din rigarta a kunce ta kama ta ja sama , ta buda akwatin ta zaro hijab dinta fari kar tana dagowa ta ga Hajiya Fadimatu ta harde hanayenta tana kalonta shima Mubasshir din ita yake kalo inda ta kasa fasara kalon kyama ne KO na ki ne yake jifanta da shi? 


Hankalinta ya kai kololuwar tashi da ta ga harda Fadimatu a wajen Kenan ta ji abinda ya faru ? A fili ta furta ya salam 


Hajiya Fadimatu ta matso tana kalonta fuskarta cike da tausayi idanuwanta jajir jikinta ba kwari a hankali ta furta" *Tafiyar ce?*


Yar Mahaukaciya ta kara sada kanta kasa tana ta zubar da hawaye 


Hajiya Fadimatu ta kara matsowa ta dago Fuskar Yar Mahaukaciya ta ce " Rahma, ki dubi girman Allah ki fada min a mai kika daukeni? Matsayina a wajen ki


Yar Mahaukaciya ta sada idanuwanta ta ce " Ke uwa ce a wajena , Wace ta karbe ni ta kula da ni ina alfahari da ke sanan zanci gaba da yi miki adu'a duniya da kiyama 


Hajiya Fadimatu ta jayota ta rungume ta tsam a jikinta , haka yar Mahaukaciya ma ta rungume ta tana kuka mai tsuma zuciya tana ji tamkar ta rungume Mahaukaciyarta ne a haka 


Sun kusan minti uku a haka sanan ta saketa ta juyo wajen Mubasshir dake tsaye da kur'anin a hanun sa yayi Sakai yana kalon su , ta ce " Yarona , na yarda da abinda Rahma ta fada, tabas bata taba haihuwa ba , sanan kwarai ta taba yin rayuwar bola, kuma eh lale yawan tinanin da take yi harda kuka wani likacin na tinanin mahaifiyarta ne , haka zalika yarinyar nan bata sato dan kowa ba kaninta ne dan kuwa dan mi ake satar yayan mutane? Ai dan tsafi ne da kudi a gidan nan da gangan na sha zubar da kudi dan na gwadata ta wanan fanin aman KO gyara take sai dai ta dage ta share ta mayar koma ta gewaye, sanan kafi kowa sanin a yanzu tanada ilimin yin aiki da card dinka dake wajenta ta kwashi abinda taga dama tayi tafiyarta aman bata taba kawowa a tinaninta ba , a vidion nan nasha jin ta furta Mahaukaciya aman ban san inda ta nufa ba , na yarda da ita dan baka san rayuwar titi bace , duk tsafi , duk sanyi, duk ruwa a wajen nan a nan suke, ba KO tabarma bale ayi tinanin katifa, Allah kadai ya san irin warin da suke ciki sai su kansu, dan haka ni Mahaifiyarka na karbi Rahma da hanu bibiyu zan Rayu da ita a matsayin yata koda an samu mahaifiyarta sanan ni Fadimatu ni zan aurar da ita da yardar Allah a inda zata huta dan kuwa hutu shi yafi dacewa da yata..


Mubasshir dake tsaye shi ya rasa ma mai yake ji a cikin zuciyarsa, ya rasa ta inda zai fara fuskantar wanan damuwar taya zaiyi da rayuwarsa ne ?(😳),    cikin sanyin jiki ya juya ba tare da ya tofa ufan ba ya shige motarsa ya kama hanya ya nufi gidansa 


Yana zuwa yau bai KO leka mutanen nasa ba , ya fice direct sai dakinsa


Yana shiga ya ajiye kur'anin a gefen gadonsa ya tsuguna a nan ya saka hanunsa ya  barbaza gashin kansa ya rufe idanuwansa cikin firgici ya bude ya mike da wata irin kara ya shiga watsi da kayan dakin yana fadin no , no ,no , Mubasshir kaifa ba mahaukaci bane , kaifa ba Mahaukaci bane , mai ya hadaka kuma da wanan? Tabas duk abinda ta fada gaskiya ne, to aman idan har gaskiyar Kenan ta boye wani abin , dan kuwa bazai yiwu ta ce wai ta zauna a gidan kato har tsawon sati daya wai ya bar mata gidan a nan kasar Nigeria? Wasu mazan da kamar su warto matan a gari shi ya samu wanan santaleliyar a gidan sa shi ba ustaz ba ,ba komai ba kuma ya zuba mata ido? No wanan ai bazan yarda ba kawai ya ciyar da ita ne ita kuwa ta biya shi, ya kaiwa table din daki duka da hanunsa 


Gabansa ya kara faduwa da ta tuna harda mace ta nemi ta nemeta wai ta gudu , a yanda ya san gidan nan da matakan tsaro ita ta isa ta gudu ba tare da an Ankara da ita ba ? No bazan shanye wanan ba , kawai ta yi abinda ake so da ita ne ta samu hanyar FITA, ya rufe idanuwansa wasu zafafan hawaye suka zubo masa daga idanuwansa Wanda rabon *Honorable AA Mubasshir* da ya zubda su har ya manta wai yau gashi yana zubar da su ya furta *Ludu* Kenan ???? Inalilahi wa'ina ilaihi raj'une ya silale nan kasa yana hawaye tun karfinsa yana fadin oh my god , Ya Allah ka kawo min dauki domin wanan ciwon yafi karfina , wanan ciwon bazan iya magancewa kaina shi ba , wanan ciwon ya zarce da tinanina ya fi karfin karfina 


To fah shin wani ciWo ne wanan? Sanan maiye damuwar honorable da idan ma Yar Mahaukaciya ta gamu da abinda yake zato? Zato zunubi ne koda ya kasance gaskiya ne , shin honorable ya manta da wanan ne???????????????


Happy juma'at daga Yar Buzuwa yar Mutan Niger Sajida❤❤❤❤❤



*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                      48


A nan kasa ya yasu cikin wani irin hali marar musaltuwa ance idan mutun na mawuyacin hali baya jin sha'awar komai aman yana rufe idanuwansa hotonta da rigar barcin nan ta fado masa a idanuwansa firgigit ya kuma bude idanuwansa yana maimaita A'uzubilahi mina shaidanin rajim yana rufe ido 


Daidai nan *Sahla* ta shigo dakin da salamarta ganin AA a zaune a kasa ya sakata karasawa da Sauri tana fadin *Hubby* lafiya ?


*Mubasshir* ya dago kansa ya zuba mata idanuwa yana kalonta a ransa yayi hamdallah dan kuwa da bata zo din bama tabas da shi ya je ya fitar da abinda ke damunsa 


Hanu ya Mika ya jawota nan kasan inda yake zaune ya shiga yamutsata da haushi haushi abin kamar hauka tun tana ganin zata iya jurewa har ta fara kuka tun karfinta daman abin da har a lokacin ta kasa sabawa da shi kulun sai ta jure ta kai zuciyarta nesa duk irin jarabarta gashi yau tamkar ba a hayacinsa yake ba 


Shi kuwa gaba daya rikide masa tayi ta koma masa macen da yafi kyankyami a rayuwarsa sanan yafi bukatar kasancewa da ita hakan yasa ya zage yayi mata horo na abinda tayi masa ( tofa sowie Sahla) bashi ya barta ba sai da yayi mata jinajina ya kai sai ta ja nunfashinta da karfi take iya fitar da shi , ya Mike a hankali ya nufi bayi ya sakarwa kansa ruwa sai da ya jima kana ya fito ya taimakawa Sahla Wace take takawa tamkar sabuwar amarya


Yana gama shiryawa ya zauna saman gadonsa ya bude kur'anin Rahma inda ya karanta sunanta *Rahma Idriss* ya dauko biro ya goge sunan Idriss din ya fara rubuta *M* kuma sai ya rufe ya ajiye ya mike ya fice daga gidan GABA daya


 Wasa wasa sai da Yar Mahaukaciya tayi jinyar sati guda a gida jinya mai kama da hutu domin har dan kiba ta kara jikinta yayi wani irin freich domin wani hadin sabulai da Hajiya Fadimatu ta hada mata da kanta ga manta da take shafawa mai kara sulbin fata da kuma sheki , Hajiya Fadimatu kanta da tayi yawon kasa kasa tana sarawa kyan Yar Mahaukaciya kuma tana ji a jikinta cewar Mahaukaciya Mahaifiyarta ba Mahaukaciya bace tun haihuwa dan kuwa alamu da yawa suna nuna hakan , kulun cikin adu'a suke Allah ya bayana ta a duk inda take .


Zaune take da wata doguwar riga baka mai duwatsu jajaye da fari a jikinta kanta ba dan kwali ta saka ribom ja ta daure shi ta buda litafinta tana bitar karatun da akayi bata nan 


Salama aka yi daga kofar shigowa ta daga kanta ta amsa  tare da mikewa tana dafa kirjinta 


Wanda ya shigo shima hakan ya zaro ido ya shigo da Sauri yana fadin beautyna kece KO idanuwana ne? 


Yar Mahaukaciya ta ce " Yaya Abdallah kaine?


Abdallah yayi wata dariyar Farin ciki daidai nan Hajiya Fadimatu ta fito tana fadin tamkar salama nake ji 


Abdallah yayi Saurin tsugunawa yana gaisheta 


Hajiya Fadimatu ta amsa cike da sakin fuska sanan ta ce " Kun san juna ne Yar Fadimatu?


Yar Mahaukaciya ta kaleta ta ce " Lah Mama ai shine Wanda ya kaini gidansa nayi sati a can din nan


Hajiya Fadimatu ta ce " kai masha Allah na gode sosai da irin rikon da kayiwa yata Allah ya saka da alkhairi 


Abdallah ya kara sine kai yana Sosa kansa ya ce " aa mama ai yiwa kai ne 


Bayan sun zauna Abdallah ya dubi Maman Mubasshir ya ce " Mama daman Karin albashi muka samu gaba daya mutanen kanfanin sanan ni an kara min matsayi shine nazo nayiwa elhaj din godiya dan ban san gidansa ba kuma a office din ma sunce yayi hani da aje gidansa ya ce idan ana neman sa a zo nan kuma sai Allah yayi na taki sa'a na tardo sister a nan 


Hajiya Fadimatu ta ce" eh hakane kaga yarinyata ce kwanakin baya ta samu wata jarabawar ubangiji aman Allah ya tsawatarwa abin sai dai yarona kaninta bai rayu ba 


Abdallah ya zaro ido yana fadin Allahu akhbar Allah ya jikansa da rahama 


Hajiya Fadimatu ta ce" amin , ya Allah , aman matar taka tayi aure?


Abdallah yayi jim yace " ai mama itama ta rasu , hatsarin mota tayi sai tokarta aka bine 


Yar Mahaukaciya ta zaro ido a tare suka furta inalilahi wa'ina ilaihi raj'une 


Hajiya Fadimatu ta ce" haka ne rayuwa kowa da abunda zai zamto ajalinsa sai dai muyi fatan kyakyawan karshe da kuma samun rabo mai kyau a kiyama 


Gaba daya suka amsa da amin , 


Suna tsaka da labari Mubasshir yayi salama dan kuwa rabonsa da gidan tun ranar da ya koma gida yayi tafiya Australi da niyar yayi wata aman hakan ya gagara Dole ya juyo ya dawo gida 


Hajiya Fadimatu ta dago kanta tana fadin ga bakin Australi sun sauko 


Abdallah ya Mike da Sauri yana fadin barka da zuwa Elhaj har yana dan risinawa ya Mika masa hanu dan girmamawa 


Mubasshir ma ya Mika masa suka gaisa yana fadin kaine a gidan na Maman Mubasshir?


Abdallah ya ce " Eh wly Elhaj daman zuwa nayi na kara godiya ashe baka garin ma 


Mubasshir ya ce" Haka , yau na dawo , no yiwa kaine ba komai 


Abdallah ya kara risinawa yana fadin " to mama zan fice sai na dawo 


Hajiya Fadimatu ta ce"" sanu da kokari a sauka lafiya Abdallah , ta dubi Yar Mahaukaciya dake kalon kasa ta ce " Yar Fadimatu tashi ki yiwa dan uwan naki rakiya KO?


Yar Mahaukaciya ta mike ta dauki dan kwalin rigarta ta yafa a kanta ta nufi kofa dan rakiyar Abdallah 


Hajiya Fadimatu ta juyo bayan fitar Yar Mahaukaciya daga falon ta kali AA da yayi mutuwar zaune yana kalon kofar da ta bi ta fita yana tinanin sabon al'amarin nan , ita kuwa ina ta san shi? Meye hadinta da shi? KO shima yana cikin mutanenta ne ??????????????


Hajiya Fadimatu ta ce " baka jina ne ina magana?


Mubasdhir ya juyo yana kalonta ya ce " ina zuwa Maman Mubasshir nayi mantuwa a mota ya Mike ya fice har yana kokarin bige kyauran madubin dake falon 


Yana FITA gabansa ya fadi hangota da yayi jingine jikin motar Abdallah ta rufe fuskarta tana murmushi


Wani irin dumdumdum yaji a ransa idanuwansa suka rufe ya fara ganin duhu duhu ya sauko daga matatakalar kofar dakin gadan gadan ya nufo su ya................


Muje zuwa taku ce Yar gidanku ce Sajida😘😘😘



*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*


                      49


🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻hhh i'm sorry fans, i'm sorry na dawo 


Yana isowa da alamar basarwa ya ce" au rakiyar bata kare ba?


Abdallah ya dan risina yana fadin 


Ai ni na dan tsayar da ita Elhaj, yana fadi yana dan Sosa keya irin yaji kunyar sirikin nan 


Mubasshir ya hadiye wani daci a ransa sukayi salama Abdallah ya shiga motarsa ya juya cike da murnar ganin Yar Mahaukaciya duk da bata bashi amanar zata iya soyaya da shi ba yana ji a jikinsa zata amince masa 


Mai dinki ne?


Yar Mahaukaciya ta dago ta kali Mubasshir sai taga tamkar ba shine yayi maganar ba hakan yasa ta juya a hankali ta nufi ciki shi kuwa ya kasa tsayar da ita gudun raini 


Yana dawowa ya zauna kusa da mahaifiyarsa ya ce " Maman Munasshir yarinyar nan ta fara zuwa makaranta ne?


Hajiya Fadatu ta ce" Wace yarinya kuma?


Mubasshir ya yatsina fuska ya ce " ta gidan nan


Hajiya Fadimatu ta girgiza kai ta ce" aa sai tomorrow l'a , please kirawota ma ka kaimin ita saloon dan saboda a gyara mata gashinta saboda school


Mubasshir ya dago kansa ya kali mahaifiyarsa bai san lokacin da bakinsa ya furta Yaya kyan kura bare tayi hauka?


Hajiya Fadimatu ta ce" mai kake nufi da hakanan?


Mubasshir ya ce " Maman Mubasshir manan ki dena cewa taje saloon kar aje a gamu da ita aje a fadawa su Abdul kinga wata matsalar ce


Hajuya Fadimatu ta girgiza kai ta ce " naji ba damuwa 


Haka suka wuni tare har yama tayi ya nufi gidansa ba tare da ya kuma Sakata a idanuwansa ba 


Yau ta kama litinin tun karfe bakwai da rabi ta gama shiryawa ta fito fes da ita ,  har bakin mota Hajiya Fadimatu tayi mata rakiya tana kara jadada mata cin abinci a kan lokaci sanan banda cin abu mai sanyi 


Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta rungume Hajiya Fadimatu ta ce" Mama karki damu zan kiyaye 


Hajiya Fadimatu tayi murmushin itama tana kara gyara mata hijab dinta ta shige suka tafi 


Tunda ta iso Fati ke murna haka sauran yan ajinsu banda princesses Wace gaba daya wani irin haushi ya turnuke ta na ganin kanwar AA ta dawo 


Zaune yake cikin office dinsa , wayar sa ta dau kukan neman agaji , wanan Kiran na biyar ne hakan ya sa ya mika hanu ya daga 


Daga dayan bangaren akayi salama 


Mubasshir ya amsa yana fadin ya akayi ne kabir?


Kabir ya ce " Elhaj daman yau naga Hajiya ta dawo makaranta aman dalilin kokarinta aka canza mata aji aka mayar da ita ajin wanan saurayin dan gidan minister dake sonta , nayi nayi a maido ta sun kiya sun ce wajen yafi dacewa da ita , ni kuma sunki maida ni can din shine yasa nace bara na fada maka a san yanda za'ayi 


Mubasshir ya ce " What? Shi din wanene shi? Dan ubansa na minister shine zai sota ? 


Kabir ya ce " ayi Hakuri Elhaj yanzu haka ina zaune ina hangenta a ajin  , shi kuwa ya dawo da kujerar sa kusanta sanan yau bata saka likaf ba 


Ai Mubasshir bai san sanda ya kashe Kiran ba ya mike ya kwashi makulan motarsa ya nufi kofa KO sanar da su baiyi ba inda zai nufa 


Tafe yake yana nanata Mubasshir Yar Amana ce a wajenka dan haka Dole kayi takatsantsan  da al'amuran ta , bazai yiwu kana ji kana gani wani dan iska ya kara lalata mata tarbiya bayan ta titi daman da ta samu, Dole ka kawo canji a rayuwarta ka fada mata karta yarda ta kula KO wani saurayi kai zaka sama mata miji idan har bata iya zama sai da namijin a kusanta ( to kaji fa Mubasshir haka ta fada maka)


Haka yayi tayiwa kansa zance tamkar sabon kamu har ya iso makarantar su Yar Mahaukaciya 


Masu tsaron kofar Makarantar kansu sunyi mamakin ganin AA da kansa a makarantar gashi ba wani abu ake ba balatana suyi tinanin an gayato shi ne , KO kanwar tasa dake makarantar ce ba lafiya KO wani Abin? Haka dai suka bude masa ya nufi ciki 


Yana isa ya tsayar da motarsa ya fito cikin shigarsa ta alfarma ya nufi office din director din fuskarsa da glass na rana baki , 


Yana isa sau daya ya konkwasa 


Director din ya amsa da com in 


Mubasshir AA ya tura ya shiga yana kokarin zare gilas din idonsa 


Director ya Mike da Sauri yana fadin "kai kai kai yau baki ne damu haka?


Mubasshir ya kale shi ya ce " Asalamu alaikum, i'm sorry director kafin mu gaisa ka fito ka fito min da sisterna daga ajin da aka kaita 


Director ya kale shi ya ce" AA ni kasan na san mahaifinka kafin ya rasu , Nasan kai daya ya malaka, kuma mahaifiyarka bata kara aure ba , to taya ta zama kanwarka? Ni fa abin nan na daure min kai kuma kaga dokar makarantar nan fa AA ku da kanku kuka dorata bai dace daga kanku a samu wata matsalar ba fa 


Jikin Mubasshir yayi sanyi tabas ya taka doka har biyu a wanan makarantar , ta farko ya saka an karbi Rahma ba tare da takardar haihuwarta ba , a zuwan dan kawai kwakwaluwarta ta bude sai na biyu ya kawo Wanda zai kula da dukan abinda take aikatawa a cikin makarantar a matsayin dalibi shima an yarje masa, to idan yaci gaba da haka za'a samu tangardar dokar 


Director ya katse masa tinaninsa ya ce " Aman fa kayi hakuri AA daman dan a dan daidaita al'amarin ne dan ganin komai ya tafi daidai 


She is my wife 


Director ya zaro ido yana kalon AA dake tsaye yana dan kakauda kai yana nadamar abinda bakinsa ya fada wata karyar Kenan , director ya ce " what?


Mubasshir ya dan duko ya dora hanayensa biyu saman table din ya ce " *yes , She Is My WIFE* director shi yasa kaga inai maka kwana kwana, dan ajin da zatayi ba matan aure ni kuwa da nan na yarda na san baza'a samu malaman banza a nan ba 


Director ya ce " Kai masha Allah , ai da tunda wuri ka fada min haka ai da ba'a soma hadata bama da mazan dan haka muje a maiyar da ita wancen ajin 


Mubasshir ya fito daidai an fidosu cin abincin rana nan fa kalo ya koma sama shaho ya dau giwa duk sai masu kalon AA a jarida da kuma TV sukayi arba da shi a fili 


Yar Mahaukaciya da Kawarta Fati sun fito suna tafiya da niyar dosar wajen cin abinci suka ji ana yi musu magana 


Fati ta fara juyawa tayi arba da AA da director sun nufo su ,ai bata san lokacin da ta furta masha Allah irin kyan da yayi mata a fuskarta ta juyo da Yar Mahaukaciya tana Fadin wayo AA ne 


Kalon kalo suka yiwa juna inda yana isowa ya ciro nikaf daga aljihunsa ya Mika mata 


Cikin rawar hanu ta mika hanunta zata karba inda garin karkarwar ya kufce ya fadin ,nima na ajiye wayar dan caji😘😘😘😘😘😘😘😘


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      48




A nan kasa ya yasu cikin wani irin hali marar musaltuwa ance idan mutun na mawuyacin hali baya jin sha'awar komai aman yana rufe idanuwansa hotonta da rigar barcin nan ta fado masa a idanuwansa firgigit ya kuma bude idanuwansa yana maimaita A'uzubilahi mina shaidanin rajim yana rufe ido 


Daidai nan *Sahla* ta shigo dakin da salamarta ganin AA a zaune a kasa ya sakata karasawa da Sauri tana fadin *Hubby* lafiya ?




*Mubasshir* ya dago kansa ya zuba mata idanuwa yana kalonta a ransa yayi hamdallah dan kuwa da bata zo din bama tabas da shi ya je ya fitar da abinda ke damunsa 


Hanu ya Mika ya jawota nan kasan inda yake zaune ya shiga yamutsata da haushi haushi abin kamar hauka tun tana ganin zata iya jurewa har ta fara kuka tun karfinta daman abin da har a lokacin ta kasa sabawa da shi kulun sai ta jure ta kai zuciyarta nesa duk irin jarabarta gashi yau tamkar ba a hayacinsa yake ba 


Shi kuwa gaba daya rikide masa tayi ta koma masa macen da yafi kyankyami a rayuwarsa sanan yafi bukatar kasancewa da ita hakan yasa ya zage yayi mata horo na abinda tayi masa ( tofa sowie Sahla) bashi ya barta ba sai da yayi mata jinajina ya kai sai ta ja nunfashinta da karfi take iya fitar da shi , ya Mike a hankali ya nufi bayi ya sakarwa kansa ruwa sai da ya jima kana ya fito ya taimakawa Sahla Wace take takawa tamkar sabuwar amarya



Yana gama shiryawa ya zauna saman gadonsa ya bude kur'anin Rahma inda ya karanta sunanta *Rahma Idriss* ya dauko biro ya goge sunan Idriss din ya fara rubuta *M* kuma sai ya rufe ya ajiye ya mike ya fice daga gidan GABA daya






 Wasa wasa sai da Yar Mahaukaciya tayi jinyar sati guda a gida jinya mai kama da hutu domin har dan kiba ta kara jikinta yayi wani irin freich domin wani hadin sabulai da Hajiya Fadimatu ta hada mata da kanta ga manta da take shafawa mai kara sulbin fata da kuma sheki , Hajiya Fadimatu kanta da tayi yawon kasa kasa tana sarawa kyan Yar Mahaukaciya kuma tana ji a jikinta cewar Mahaukaciya Mahaifiyarta ba Mahaukaciya bace tun haihuwa dan kuwa alamu da yawa suna nuna hakan , kulun cikin adu'a suke Allah ya bayana ta a duk inda take .




Zaune take da wata doguwar riga baka mai duwatsu jajaye da fari a jikinta kanta ba dan kwali ta saka ribom ja ta daure shi ta buda litafinta tana bitar karatun da akayi bata nan 



Salama aka yi daga kofar shigowa ta daga kanta ta amsa  tare da mikewa tana dafa kirjinta 



Wanda ya shigo shima hakan ya zaro ido ya shigo da Sauri yana fadin beautyna kece KO idanuwana ne? 



Yar Mahaukaciya ta ce " Yaya Abdallah kaine?



Abdallah yayi wata dariyar Farin ciki daidai nan Hajiya Fadimatu ta fito tana fadin tamkar salama nake ji 



Abdallah yayi Saurin tsugunawa yana gaisheta 



Hajiya Fadimatu ta amsa cike da sakin fuska sanan ta ce " Kun san juna ne Yar Fadimatu?



Yar Mahaukaciya ta kaleta ta ce " Lah Mama ai shine Wanda ya kaini gidansa nayi sati a can din nan



Hajiya Fadimatu ta ce " kai masha Allah na gode sosai da irin rikon da kayiwa yata Allah ya saka da alkhairi 



Abdallah ya kara sine kai yana Sosa kansa ya ce " aa mama ai yiwa kai ne 



Bayan sun zauna Abdallah ya dubi Maman Mubasshir ya ce " Mama daman Karin albashi muka samu gaba daya mutanen kanfanin sanan ni an kara min matsayi shine nazo nayiwa elhaj din godiya dan ban san gidansa ba kuma a office din ma sunce yayi hani da aje gidansa ya ce idan ana neman sa a zo nan kuma sai Allah yayi na taki sa'a na tardo sister a nan 



Hajiya Fadimatu ta ce" eh hakane kaga yarinyata ce kwanakin baya ta samu wata jarabawar ubangiji aman Allah ya tsawatarwa abin sai dai yarona kaninta bai rayu ba 



Abdallah ya zaro ido yana fadin Allahu akhbar Allah ya jikansa da rahama 



Hajiya Fadimatu ta ce" amin , ya Allah , aman matar taka tayi aure?




Abdallah yayi jim yace " ai mama itama ta rasu , hatsarin mota tayi sai tokarta aka bine 



Yar Mahaukaciya ta zaro ido a tare suka furta inalilahi wa'ina ilaihi raj'une 



Hajiya Fadimatu ta ce" haka ne rayuwa kowa da abunda zai zamto ajalinsa sai dai muyi fatan kyakyawan karshe da kuma samun rabo mai kyau a kiyama 



Gaba daya suka amsa da amin , 


Suna tsaka da labari Mubasshir yayi salama dan kuwa rabonsa da gidan tun ranar da ya koma gida yayi tafiya Australi da niyar yayi wata aman hakan ya gagara Dole ya juyo ya dawo gida 



Hajiya Fadimatu ta dago kanta tana fadin ga bakin Australi sun sauko 



Abdallah ya Mike da Sauri yana fadin barka da zuwa Elhaj har yana dan risinawa ya Mika masa hanu dan girmamawa 



Mubasshir ma ya Mika masa suka gaisa yana fadin kaine a gidan na Maman Mubasshir?



Abdallah ya ce " Eh wly Elhaj daman zuwa nayi na kara godiya ashe baka garin ma 



Mubasshir ya ce" Haka , yau na dawo , no yiwa kaine ba komai 



Abdallah ya kara risinawa yana fadin " to mama zan fice sai na dawo 



Hajiya Fadimatu ta ce"" sanu da kokari a sauka lafiya Abdallah , ta dubi Yar Mahaukaciya dake kalon kasa ta ce " Yar Fadimatu tashi ki yiwa dan uwan naki rakiya KO?


Yar Mahaukaciya ta mike ta dauki dan kwalin rigarta ta yafa a kanta ta nufi kofa dan rakiyar Abdallah 



Hajiya Fadimatu ta juyo bayan fitar Yar Mahaukaciya daga falon ta kali AA da yayi mutuwar zaune yana kalon kofar da ta bi ta fita yana tinanin sabon al'amarin nan , ita kuwa ina ta san shi? Meye hadinta da shi? KO shima yana cikin mutanenta ne ??????????????



Hajiya Fadimatu ta ce " baka jina ne ina magana?



Mubasdhir ya juyo yana kalonta ya ce " ina zuwa Maman Mubasshir nayi mantuwa a mota ya Mike ya fice har yana kokarin bige kyauran madubin dake falon 



Yana FITA gabansa ya fadi hangota da yayi jingine jikin motar Abdallah ta rufe fuskarta tana murmushi


Wani irin dumdumdum yaji a ransa idanuwansa suka rufe ya fara ganin duhu duhu ya sauko daga matatakalar kofar dakin gadan gadan ya nufo su ya................














Muje zuwa taku ce Yar gidanku ce Sajida😘😘😘

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      49


🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻hhh i'm sorry fans, i'm sorry na dawo 





Yana isowa da alamar basarwa ya ce" au rakiyar bata kare ba?



Abdallah ya dan risina yana fadin 




Ai ni na dan tsayar da ita Elhaj, yana fadi yana dan Sosa keya irin yaji kunyar sirikin nan 


Mubasshir ya hadiye wani daci a ransa sukayi salama Abdallah ya shiga motarsa ya juya cike da murnar ganin Yar Mahaukaciya duk da bata bashi amanar zata iya soyaya da shi ba yana ji a jikinsa zata amince masa 



Mai dinki ne?


Yar Mahaukaciya ta dago ta kali Mubasshir sai taga tamkar ba shine yayi maganar ba hakan yasa ta juya a hankali ta nufi ciki shi kuwa ya kasa tsayar da ita gudun raini 


Yana dawowa ya zauna kusa da mahaifiyarsa ya ce " Maman Munasshir yarinyar nan ta fara zuwa makaranta ne?



Hajiya Fadatu ta ce" Wace yarinya kuma?



Mubasshir ya yatsina fuska ya ce " ta gidan nan



Hajiya Fadimatu ta girgiza kai ta ce" aa sai tomorrow l'a , please kirawota ma ka kaimin ita saloon dan saboda a gyara mata gashinta saboda school


Mubasshir ya dago kansa ya kali mahaifiyarsa bai san lokacin da bakinsa ya furta Yaya kyan kura bare tayi hauka?


Hajiya Fadimatu ta ce" mai kake nufi da hakanan?



Mubasshir ya ce " Maman Mubasshir manan ki dena cewa taje saloon kar aje a gamu da ita aje a fadawa su Abdul kinga wata matsalar ce



Hajuya Fadimatu ta girgiza kai ta ce " naji ba damuwa 


Haka suka wuni tare har yama tayi ya nufi gidansa ba tare da ya kuma Sakata a idanuwansa ba 



Yau ta kama litinin tun karfe bakwai da rabi ta gama shiryawa ta fito fes da ita ,  har bakin mota Hajiya Fadimatu tayi mata rakiya tana kara jadada mata cin abinci a kan lokaci sanan banda cin abu mai sanyi 



Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta rungume Hajiya Fadimatu ta ce" Mama karki damu zan kiyaye 



Hajiya Fadimatu tayi murmushin itama tana kara gyara mata hijab dinta ta shige suka tafi 



Tunda ta iso Fati ke murna haka sauran yan ajinsu banda princesses Wace gaba daya wani irin haushi ya turnuke ta na ganin kanwar AA ta dawo 





Zaune yake cikin office dinsa , wayar sa ta dau kukan neman agaji , wanan Kiran na biyar ne hakan ya sa ya mika hanu ya daga 



Daga dayan bangaren akayi salama 


Mubasshir ya amsa yana fadin ya akayi ne kabir?



Kabir ya ce " Elhaj daman yau naga Hajiya ta dawo makaranta aman dalilin kokarinta aka canza mata aji aka mayar da ita ajin wanan saurayin dan gidan minister dake sonta , nayi nayi a maido ta sun kiya sun ce wajen yafi dacewa da ita , ni kuma sunki maida ni can din shine yasa nace bara na fada maka a san yanda za'ayi 



Mubasshir ya ce " What? Shi din wanene shi? Dan ubansa na minister shine zai sota ? 



Kabir ya ce " ayi Hakuri Elhaj yanzu haka ina zaune ina hangenta a ajin  , shi kuwa ya dawo da kujerar sa kusanta sanan yau bata saka likaf ba 



Ai Mubasshir bai san sanda ya kashe Kiran ba ya mike ya kwashi makulan motarsa ya nufi kofa KO sanar da su baiyi ba inda zai nufa 



Tafe yake yana nanata Mubasshir Yar Amana ce a wajenka dan haka Dole kayi takatsantsan  da al'amuran ta , bazai yiwu kana ji kana gani wani dan iska ya kara lalata mata tarbiya bayan ta titi daman da ta samu, Dole ka kawo canji a rayuwarta ka fada mata karta yarda ta kula KO wani saurayi kai zaka sama mata miji idan har bata iya zama sai da namijin a kusanta ( to kaji fa Mubasshir haka ta fada maka)


Haka yayi tayiwa kansa zance tamkar sabon kamu har ya iso makarantar su Yar Mahaukaciya 



Masu tsaron kofar Makarantar kansu sunyi mamakin ganin AA da kansa a makarantar gashi ba wani abu ake ba balatana suyi tinanin an gayato shi ne , KO kanwar tasa dake makarantar ce ba lafiya KO wani Abin? Haka dai suka bude masa ya nufi ciki 



Yana isa ya tsayar da motarsa ya fito cikin shigarsa ta alfarma ya nufi office din director din fuskarsa da glass na rana baki , 



Yana isa sau daya ya konkwasa 


Director din ya amsa da com in 



Mubasshir AA ya tura ya shiga yana kokarin zare gilas din idonsa 



Director ya Mike da Sauri yana fadin "kai kai kai yau baki ne damu haka?



Mubasshir ya kale shi ya ce " Asalamu alaikum, i'm sorry director kafin mu gaisa ka fito ka fito min da sisterna daga ajin da aka kaita 



Director ya kale shi ya ce" AA ni kasan na san mahaifinka kafin ya rasu , Nasan kai daya ya malaka, kuma mahaifiyarka bata kara aure ba , to taya ta zama kanwarka? Ni fa abin nan na daure min kai kuma kaga dokar makarantar nan fa AA ku da kanku kuka dorata bai dace daga kanku a samu wata matsalar ba fa 



Jikin Mubasshir yayi sanyi tabas ya taka doka har biyu a wanan makarantar , ta farko ya saka an karbi Rahma ba tare da takardar haihuwarta ba , a zuwan dan kawai kwakwaluwarta ta bude sai na biyu ya kawo Wanda zai kula da dukan abinda take aikatawa a cikin makarantar a matsayin dalibi shima an yarje masa, to idan yaci gaba da haka za'a samu tangardar dokar 



Director ya katse masa tinaninsa ya ce " Aman fa kayi hakuri AA daman dan a dan daidaita al'amarin ne dan ganin komai ya tafi daidai 



She is my wife 



Director ya zaro ido yana kalon AA dake tsaye yana dan kakauda kai yana nadamar abinda bakinsa ya fada wata karyar Kenan , director ya ce " what?



Mubasshir ya dan duko ya dora hanayensa biyu saman table din ya ce " *yes , She Is My WIFE* director shi yasa kaga inai maka kwana kwana, dan ajin da zatayi ba matan aure ni kuwa da nan na yarda na san baza'a samu malaman banza a nan ba 



Director ya ce " Kai masha Allah , ai da tunda wuri ka fada min haka ai da ba'a soma hadata bama da mazan dan haka muje a maiyar da ita wancen ajin 



Mubasshir ya fito daidai an fidosu cin abincin rana nan fa kalo ya koma sama shaho ya dau giwa duk sai masu kalon AA a jarida da kuma TV sukayi arba da shi a fili 



Yar Mahaukaciya da Kawarta Fati sun fito suna tafiya da niyar dosar wajen cin abinci suka ji ana yi musu magana 



Fati ta fara juyawa tayi arba da AA da director sun nufo su ,ai bata san lokacin da ta furta masha Allah irin kyan da yayi mata a fuskarta ta juyo da Yar Mahaukaciya tana Fadin wayo AA ne 



Kalon kalo suka yiwa juna inda yana isowa ya ciro nikaf daga aljihunsa ya Mika mata 



Cikin rawar hanu ta mika hanunta zata karba inda garin karkarwar ya kufce ya fadin ,nima na ajiye wayar dan caji😘😘😘😘😘😘😘😘

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      50



Mamyna my blood sister *Mariam maman Imran love u*


Mamyna *Khadija ni ma ina sonki irin da yawa din nan*


Jinjina gareki sis *Muneera* ina yinki sosai




A tare suka duka da niyar dauko nikaf din da ya fadi , sai dai ya rigayeta dora hanunsa a sama hakan yasa ta kasa karasa nata hanun sanan ta kasa dagowa 



A nitse ya dago fuskarsa cikin sa'a kuwa suka hada ido hudu da shi da sauri ta sada kanta suka kuma mikewa a tare , 


Kara matsawa yayi kusanta ya gyara nikaf din sai gani tayi yana nufo fuskarta da niyar ya daura mata 


Abin mamaki KO motsi kasawa tayi ya kama ya daura mata nikaf din a fuskarta , abinda tunda yake bai taba ba domin yana dage mata nikaf din suka kuma yin ido hudu da yayi saurin lumshe idanuwansa wa'inda tini suka fara karbar sakonnin idanuwan *Yar Mahaukaciya*



Cikin mutuwar jiki ya ce " mu tafi Maman Mubasshir na kiranki 



Yar Mahaukaciya ta zaro ido ta ce " Lafiyarta? Mai ya samu Maman Rahma? Bata jin dadi ne?



Mubasshir ya zuba mata ido irin yanda ta rikice take maimaita masa tambayar dake nufin abu daya a karo uku, wai kuma shi ya ce mata *Maman Mubasshir* ita kuwa tace masa wani *Maman Rahma* 


Tabo hanunsa da tayi ne ya tunatar da shi fa ya shiga tinani , firgigit yayi yana fadin " No lafiyarta lau tana dai kiranki 



Yar Mahaukaciya ta juya tayi salama da Fati kawarta suka juya suka shiga mota ya kama hanya ya harbata titi 



Tafe yake yana tinani kala daban daban a zuciyarsa , haka bangaren Yar Mahaukaciya domin taga ba hanyar zuwa gida ya kama ba , aman bazata iya yi masa tambayar inda zai kaita ba , ta yarda da shi 



Sun kusan minti arba'in a hanyar sanan suka iso wata babar unguwa Wace da gani ka san wanan unguwa ta manya ce,   zama ta gyara ta kara buda idanuwanta tana karewa wanan unguwa kalo a ranta ta ce " Kai Lagos da abin mamaki take 




Tsayuwar motar ne ya fargar da ita ta zubawa kofar gidan da suka tsaya ido , har wani kara murza idanuwanta take 




Cikin dakakiyar Murya ya ce" fito 



Yar Mahaukaciya gabanta ya fadi ta kali Gabas da yama , kudu da arewa ba kowa irin unguwar nan ce ta yan gayu KO ihu kayi iya kai zai tsaya , ta kuma kalon kasa taga ba kasa bace ta ajiye wata nanauyar ajiyar zuciya a ranta tace" Maman Rahma baga irinta ba , yanzu KO wani abin ya sameni a wajen nan ai bazan iya guduwa dan kuwa wanan takalman da kika sakani sakawa yayi min nauyi 



" *Wai bazaki fito ba?* " Mubasshir ya  fuskarsa a daure 



Gaba daya jikinta bari yake , haka ta kokarta ta fito tana Jan kafa ta bi bayansa domin bai shiga gidan da mota ba , 



Kofa kanta sai da suka shiga uku a ta hudun ce ya dora hanunsa kana ta bude , itadai binsa take kawai bata ce komai ba har suka ISO wani banban waje mai kyan gaske , sai a nan ta fara ganin mutane kuma abin mamaki harda tsofafi 




Wata tsohuwa ta hango tana kokarin tashi sai dai kusanta ta zubar da ruwa ga yanayin wajen shi kansa santsin ne da shi , ga santsin ruwan , Ai bata san lokacin da ta shige gaban AA Mubasshir dake tafiyar kasaita ta nufi wanan tsohuwa da gudu ta tarota gaba daya ta rungumota a jikinta tana fadin " Mama dan tsaya na taimaka miki karki fadi 



Cikin ikon Allah tsohuwar bata kai kasa ba Yar Mahaukaciya ta kamata ta canza mata wajen zaman ta ciro dan kwalin kayan makarantarta ta gogewa tsohuwar nan hanu da baki sanan ta kakabe mata jikinta ta kara gyara mata zamanta 



Tunda ta shige gabansa da gudu ya tsaya yana kalon KO itama irin na Shalan ne wato taji tsoron tsofafin mutane koma yace kyankyami 



Abinda ya gani ne ya saka shi maida hankalinsa a kanta , mamakinta bai gama gushewa ba sai da yaga tana gogewa gogo fuskarta harda majina ,  ya kara maida hankalinsa ganin sai labari take bata ita kuwa ta dage sai dariya take baki ba hakori ,   ji yayi gaba daya zuciyarsa tayi sanyi , wata nutsuwa ta sauko masa a cikin ransa Wace ya rasa ta maicece , wani farin cikin ganin gogo na dariya ya sakashi shima yin dariyar sanan ya matsa kusan su ya dan tsuguna yana kalonsu cike da sha'awar yanayinsu 




Yar Mahaukaciya gaba daya ta ma manta da shi tana kokarin ganin gogo ta daina yi mata labarin akoy aljana a cikin gidan ,,  


Juyowa tayi a hankali tana nuni da hanunta tana fadin kinga Gogo gidan nan ba wata aljana sanan koda akoy aljanar akoy adu'ar da mamana ta koya min idan kinyita to fa aljanar nan zata kone ,    ido hudu suka kuma yi da Mubasshir dake kalonsu a tsugune domin sam bata san yazo gurin ba 



Hadiye maganarta tayi tana kokarin daura nikaf dinta dan gudun baiwa gogo tsoro har cire shi tayi 



Mubasshir ya Mike a hankali yana fadin mu tafi ya nufi hanyar fita itama ta kama nikaf din ta daura sanan ta biyo bayansa 





Tafe suke a mota yana yi mata gargadi KO nace kashedi kan ta kiyaye harkar maza , ta fita a harkar maza ta cire maza daga ranta 



Yar Mahaukaciya ta dago kanta ta kale shi 



Ya ce " Yes ki cire maza a ranki , idan har mazan ne kin damu da su har haka kawai ki fitar da miji guda aman fa na hane ki da zance na hane ki da sauraron maza a titi ba ruwanki da mazan makarantar ku 



Ta kuma kalonsa a ranta ta ce" to mai yake nufi da na saka maza a raina? Kuma na fitar da miji aman ya hanani kula su to ta yaya zasu  soni ma a haka?



Mubasshir ya ce" Malama ki kali gabanki gindaya miki sharuda ne nake dan gudun gobe kiyama Allah ya tambayeni kan amanar da aka bani domin ni din nan ni ne tamkar *Mahaifi* a wajen ki a yanzu dan ni nake da ikon aurar da ke  dan haka ki kiyaye bana son na kuma yi miki magana kan harkar Maza ( Toh fa kaji ikon Allah , sai Baba Mubasshir )



Har suka iso yana haikar baki Wanda ta gaji ta kontar da kanta jikin madubin motar cikin ikon Allah baci yayi awon gaba da ita 





Suna isowa Wace Maman Mubasshir ta saka ta zo takanas tun daga maroco dan siyan kayan dakin Yar Mahaukaciya da kuma gama shiryata ta fito daga cikin falon ita da wata mata a kusanta Wace ta dan darata da tsayi ga wani irin fari da gareta idanuwanta da farin glas 



Har bakin motar ta rakosu sanan tayi nuni da motar Mubasshir Wanda ya fito ya nufesu dan su gaisa 



Yana isa ya dan risina dan duk da bata wani tsufa ba ya san zata haife shi hakan yasa ya risina ya gaishe su 



Hajiya Fadimatu ta ce " yawa dan Fadimatu kaga Hafsat matar da ta hadawa yar gidan Mr President dakinta , tazo Nigeria ne na nemeta nima 



Mubasshir ya  ce" Masha Allah Maman Mubasshir , sanan ya ci gaba da fadin" yarinyarki tayi min  baci a mota bara na dauko sakona na koma office ,   



Yana gama fada ya juya ya nufi cikin falon inda Hajiya Fadimatu tayiwa su Hajiya *Rafi'at* salama kan sai tayi mata dabara ta zaba sai ta sanarwa *Hafsat*  ta nufi motar *AA* dan ta tashe da yarinyarta su kuwa suka shiga wuleliyar motarsu suka kama hanyar tafiya.








Wai shin wacece *Hafsat da Hajiya Rafi'at?*  



I don't kwnow ,   LV u asosai

[11/16, 21:18] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      51



Cikin nutsuwa ta mika hannunta tana tashin Yar Mahaukaciya Wace tayi nisa cikin baccinta na gajiyar fadan AA Wanda bata san abinda tayi masa ba 



Firgigit ta farka da adu'ar tashi daga baci a bakinta tana fadin " kayi hakuri 


Hajiya Fadimatu ta zaro ido ta ce " Yayi hakuri? Mai yayi miki yarinyata? 



Yar Mahaukaciya ta saki ajiyar zuciya Sanan tayi murmushi ta ce " Mamana Ashe mun karaso , bacine ya dauke ni nayi zaton Yaya ne ke tashina,  




Hajiya Fadimatu ta ce " eyah, lafiya yau aka sauko da wuri haka?"




Yar Mahaukaciya ta ce " no bamu sauka ba , yaya ne yace kina son ganina"




Hajiya Fadimatu tayi jim , itadai tasan bata tura shi ba aman kuma bazata karyata shi ba gudun kar ta raina shi KO zuwa gaba hakan yasa ta share tana fadin " fito mu tafi ki huta kafin yama tayi yata"




Daidai sun fito shima ya fito ya karasa yayiwa mahaifiyarsa salama ya juya akalar motarsa dan komawa office 



Yana isa secretariar sa ta tarbe shi da dumbin takardu ta fara zano masa jama'ar da suka zo baya nan da sakon'nin da aka badar , tana tsaka da zanawa ya ce " Mariam kije gida ki huta 




Mariam ta zaro ido cike da mamaki tana kalon bayansa da ya juya ya shige office dinsa domin tunda suke ba'a taba tashi kasa da karfe biyar ba , don kuwa AA akoy son aiki sai gashi yau tun kafin shi ya tafi ita ya salameta kuma da alama lafiyarsa lau , tayi ajiyar zuciya a fili ta ce" alhamdulilah ni ma sai naje na kula da gidana da wuri yau 






Bayan shigarsa da kamar minti ashirin sai ga Abdul abokinsa yayan Sahla ya shigo office din da salama 



Mubasshir ya dago kansa yana amsa salamarsa sanan ya sauke kafafuwansa ya Mika masa hanu sukayi musabaha 




Abdul ya nemi waje ya zauna yana mai ajiyar zuciya 



AA ya kare karantarsa ya lura duk ransa a jagule yake ya ce" freind yaya dai?




Abdul ya kale shi cikin yanayin tausayi ya ce" Hajiya ta koreni na koma ta kuma korata da kyar na samu ta yafe min aman tace kawai na manta da yarinyar nan domin tayi min nisa, ni na kasa gane wani irin nisa tayi min indai ba auren wani tayi ba KO mutuwa tayi bata duniyar? Nayi nayi ta fada min inda yarinyar nan take aman fafur Hajiya ta kiya taki ta saurareni please freind ka saka baki wly ni ban san mai nayi mata ba 




Mubasshir ya yatsina fuska yana matukar mamakin Abdul kan mace ne yake kokarin yin kuka? Ya ce" wai wace kake nufi? 




Abdul ya nisa ya ce" *Rahma* nake nufi freind , kuma da ta wani takarkare take hanani sanin inda hasken idaniyata take ta manta ta sanadiyata ta santa ne????





Mubasshir ya gyara zama ya ce" oh yarinyar nan , Au bata gidan? Toh ban gane ta sanadiyarka ta Santa ba , shin ba ka fada min cewar jikar Hajiyar bace?????

[11/16, 21:18] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      52


Abdul ya dago kansa ya dubi Mubasshir ya tuna eh fa ga abinda suka fadawa Mubasshir aman gaskiya shi zai fada masa gaskiyar zancen KO ya kama masa Hajiya ta fada masa inda Ta boye masa Rahmarsa , cikin alamar dan jin kunya ya ce " No ba jikarta bace, hasalima bata hada komai da ita ba , ranar da na fara yin tiyata a rasun nan ranar da bazan taba mantawa da ita ba a ranan na hadu da ita , sanan a ranar hajiya ta ganta , yaron da ya rasun danta ne ,,,..............''''''''''''',,,,,,,,,,,,,nan ya kwashe duka yanda akayi har daukanta da sukayi shi da Hajiya Hawau ya fadawa Mubasshir Wanda yake sauraronsa kamar ana kara yi masa bita ne kan abinda aka karanta masa 




Mubasshir ya ce " kuma haka kuka dauki yarinyar da baku san KO wacece ba , wada ta shigo maka asibiti da yaro jiki a farfashe? Shin idan fa wata muguwa ce KO sato dan tayi?



Abdul ya kawar da kansa ya ce" she is innocent, tabas Rahma ba muguwa bace, sanan kamila ce, kuma nitsatsiya ce, domin da muguwa ce a zaman mu da ita da KO ta yaya sai halinta ya fito 




Mubasshir ya kuma jefo masa tambayar " kana sonta ne?



Abdul ya gyara zama yace" ina sonta tamkar yar uwata ta jini, ina jinta a jinin jikina, 



Mubasshir ya ce" ya akayi ka gane cewar kana sonta? Mai kake ji har ka gane cewar sonta ne kake? 



Abdul ya dago ya kuma kalon Mubasshir Wanda daman shi yake kalo, da alamar mamakin tambayoyinsa ya ce" kafi kowa sani domin kai har kayi aure KO?




Mubasshir ya koma ya jongina da kujerar da yake zaune ya lumshe idanuwansa ya ce" kafi kowa sanin KO auren mai nayi,kafi kowa sanin amintaka ta ci karfina har na kasa yin musu da abinda ya zamto tamkar a cikin duhu nake,  ya kuma dago kansa ya ce " freind tell me dan Allah mai ake ji? May be na dade da fara son matata rashin sanin inda so din soyaya ya nufa ya hana ni ganewa 




Abdul ya ja ajiyar zuciya ya ce" tabas kai namiji ne mai kokari, jarumta, na yarda da jarumtar ka , sanan na gode da abinda kayi domin ni, nima Allah ya bani ikon yi maka abin alkhairi ,  ya nisa ya dora da cewa" idan kaga abin sonka kafin ka furta masa kalmar so zakana ji gabanka na faduwa,   koya ka nisanta da shi burinka ka dawo ka gansa,  koda mumuna ne tofa zaka Ganshi ba Wanda ya kaishi kyau, da zarar kun hada idanuwa sai gabanka ya fadi, baka gajiya da kalonsa, ka tsani wani ya rabe sa balatana namiji, ka tsani wani ya kale shi, ka tsani....




Cikin Sauri Mubasshir ya furta wait wait wait yana daga hanunsa sanan dayan hanun yana laluba gashin kansa ya mike da sauri ya debi ruwa ya rufe ido ya shanye tas sanan ya ajiye kofin ya juyo yana kalon Abdul Wanda yayi tsamanin KO kwaruwa yayi ya ce" aman ai idan amanarka ne ma kana iya jin irin haka KO?




Abdul ya ce" koda kanwarka ce bazaka ji irin hakan ba , ina tsaka da zana maka ka katse ni , naci gaba ne?



Mubasshir ya shiga girgiza kai uwa karamin yaro ya ce" No barshi haka is OK




Abdul ya ce" gaba daya abinda na zana maka ba Wanda bana ji a tatare da yarinyarnan , dan haka ya hade hanayensa ya ce" ka taimakeni ka taya ni ta fada min inda take 





Mubasshir ya rintse idanuwansa ya bude ya ce" zanyi kiranka zanje na ganta karka damu 




Abdul ya taso cikin jin dadi ya rungume Mubasshir yana yi masa godiya sanan yayi masa salama ya fita 



Yana tafiya Mubasshir ya shiga zaro ido tamkar sabon kamu ya fada saman kujera jagob ya tatara gashin kansa ya cakula ya rufe ido yana furta inalilahi wa'ina ilaihi raj'une , inalilahi wa'ina ilaihi raj'une , ya buga hanunsa saman table ji kake taratsatsa domin kolba ce ta fashe 


Zumbur ya kuma mikewa ya dauki ky din motarsa hanunsa na digar jini aman bai damu ba ya fito ya shiga motarsa ma'aikatan sai kalonsa suke kowa na mamakinsa aman ba Wanda ya nufe shi dan ba fuskar hakan ,



Tuki yake na ganganci kansa ba hula sanan ba Babar rigarsa a jikinsa farar Riga ce kawa ta ciki,  sai dogon wandonsa na shada , idanuwansa sunyi jajajir haka fuskarsa a murtuke , bai san inda zai nufa ba hasalima burin sa ya ganta a gabansa ya kali fuskarta sanan ya furta mata cewar shi fa sam baya sonta yana kokarin kare mutuncinta ne , 



Wani irin burki ya taka aman ina sai da ya bigi Babar motar da ta kwaso kaya take gabansa ji kake piiiiiiiiit karar  oda inda kansa ya fada , jama'a duk suka fifito hanu a saman kai suna furta inalilahi wa'ina ilaihi raj'une 


Da Sauri direban babar motar ya taka birki duk suka firfito suka nufe shi 






Zaune suke suna cin abinci wayar dakin ta dauki kara , haka kawai ta ji gabanta ya fadi ta mike da Sauri ta nufi wayar ta daga , sakin wayar tayi sanan ta tafi luuu zata fadi tana fadin inalilahi wa'ina ilaihi raj'une 



Da Gudu Yar Mahaukaciya ta tareta tana fadin mama lafiya??????????????????????????????????????????????????????????????????












      😱😱😱😱😱😱

🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      53

Da gudu Yar Mahaukaciya ta tareta tana faman fadin " Mama lafiya? Aman ina sai da suka kai kasa dan kuwa karfin ba daya ba, cikin Sauri ta rarumo wayar ta kanga a kunanta tayi salama 



Daga dayan bangaran likitar take shaida mata anga numberta da kuma ta gida a cikin wani litafi a motarsa yana asibitin Jarumai aman bai ji ciwo sosai ba 



Yar Mahaukaciya cikin sarkewar harshe ta ce" wa .....wane yayi hatsarin?"



Matar ta ce" *AA MUBASHIR* "




Yar Mahaukaciya ta furta inalilahi wa'ina ilaihi raj'une sanan ta FITA da sauri tayi Kiran direban gidan kafin ya fitar da motar ta haye sama ta dauko hijabin Hajiya Fadimatu da nata sanan ta sauko cikin gudu gudu ta tsuguna kusan Hajiya Fadimatu ta ce" Mamana yaya bai ji ciwo sosai ba , please ki tashi mu tafi wajensa plz mamana" 



Hajiya Fadimatu da sai a lokacin ta dawo daga sumar tsoratar da tayi na jin gidan jininta a asibiti ta mike da kyar ta zura hijabin suka fito suka kama hanyar asibitin 





Suna isa aka kaisu dakin da aka kontar da shi cikin girmamawa 



Tsayuwa tayi tana kalonsa tana tofa masa adu'a tana yiwa Allah godiya da hatsarin nasa bai zo da tsanani ba , waigowa tayi ta kali doctern ta ce" docter bacin nan na lafiya ne?"



Docter ya ce" eh ma'am alurar baci muka yi masa dan ya huta domin da alama tinani yayi masa yawa dan kuwa shi kadai ya zo ya bigi motar sanan an duba motar lafiyarta lau, kuma shi ba shan wani abin maye yayi ba, ba earpice a kunan sa, kuma kwakwaluwarsa lafiyarta lau kawai dai cikin biyu ne KO wani abin ya taba masa ransa KO yana Sauri ya je wani wajen ne hakan yasa ya kasa control din kansa"



Hajiya Fadimatu ta shafa fuskarsa ta ce" Ya jima yana barcin ne?"




Docter ya ce" eh toh sai da muka daidaita komai ya samu kamar awa uku muna ta neman yanda zamu sanar muku, zuwa yanzu yaci ace ya farka ma sai dai da alama yana jin dadin bacin, Muje ma'am na baku takardun da ake bukatar a cike da kuma na maganin sa"





Hajiya Fadimatu ta kali Yar Mahaukaciya dake tsaye itama tana sauraron bayanan likitan ta ce" Yata bara na dawo" ta juya ta bi bayan doctern 





Da tafiyarsu Yar Mahaukaciya tayi tsai tana kalonsa sai bacinsa yake gashin idon nan nasa yayi zagar zagar a konce baki yayi lufluf da shi , bakin nan nasa tamkar ya shafa man lebe sai sheki yake namiji da shekin lebe, a hankali ta jawo kujera ta zauna daf da shi ta dago hanayenta ta dora saman cinyoyinta ta tokare habarta ta zuba masa ido tana kare masa kalo a ranta tana matukar mamakin mumurdewar hanunsa shi kuwa ba karfe yake ci ba a saninta bata taba ganinsa yana irin daga karfen nan aman hanunsa yana yan dambe da ake nunowa a tashar TL9 , 



Tana haka har wani irin baci ya kama idanuwanta ta karewa dakin kalo ba wajen konciya hakan yasa ta dan dora kanta daga bakibakin gadon baci yayi awon gaba da ita ( toh fa ke da aka barwa marar lafiya?)





Cikin nutsuwa ta turo kofar ta shiga da salamar ta , murmushi ne ya subuce mata ganin Mubasshir ya farka yana kalon Yar Mahaukaciya dake baci duk da bai ga fuskarta ba yana son sanin KO wacece ke konce kusan sa ,



Shima Murmushin ya sakar mata ya dago hanunsa irin ta karaso 



Hajiya Fadimatu ta karasa suka gaisa da gudan jininta ta ce" Dan Fadimatu yaya saukin jikin?




Mubasshir yayi murmushi cikin muryar maran lafiya ya ce" maman Mubasshir i'm sorry"




Ta girgiza kai ta dora yatsarta a saman lebensa ta ce" no dan gidan Fadimatu dena bani hakuri yarona, Allah ya baka lafiya "



Yayi murmushi yana kalon hanunta magunguna ne ya dan yatsina fuska a ransa ya ce " tap gaskiya ni bazan sha maganin nan ba" 




Bayan ta ajiye ledar maganin ta zo a nitse ta tana murmushi ta ce" oh Yar Fadimatu nasan bacin nan na jiya daman bai wani isheta ba , baiwar Allah gashi yanzu mun kado KO abinci bata ci ba 





Gaban mubasshir ya fadi ya lumshe idanuwansa yana kalon mahaifiyarsa na kokarin cirewa Yar Mahaukaciya hijabinta dan ya shake mata wuya , yayi gagawar kawar da kansa yana kara rintse idanuwansa a ransa yana ta adu'o'i kan Allah ya kare masa idanuwansa da kalon banban muradin sa 




Idanuwanta ta bude suka yi ido hudu da Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" Mama kin dawo? Baci ne ke damuna 




Hajiya Fadimatu ta ce" ai Dole yar Fadimatu, Konta ki hutawarki , ai likitan yace zai mabu salama aman sai dai mu tafi gida da yayanki dan nayi Kiran number matarsa ta yiwa mahaifiyarta rakiya bata nan shi kuwa baya son shan magani sai dai mu tafiyarmu gida da shi 




Yar Mahaukaciya ta gyada kanta tana leken fuskarsa ta ce" Allah ya kara afuwa 




Hajiya Fadimatu ta ce" Amin , sanan taci gaba da hada masa yan magungunan da likita ya ce ya sha idan ya farka sai a basu salama su je gida ya ci gaba da sha 





Cikin ikon Allah likita ya salame su suka nufi gida da magungunan su, aman tunda ya farka bai yarda sun hada ido da Yar Mahaulaciya ba , koda tayi masa sanu da jiki hanunsa kawai ya daga mata a hakan har suka isa gida , inda Hajiya Fadimatu ta rasa décision din da zata dauka domin shi dai ba lafiya ne da shi ba, bazata yarda ya kwana a dakunan kasa ba , kuma dakin nasa shine Yar Mahaukaciya ta zauna, sanan tana ganin lokacin ta fada musu gaskiya yayi KO dan su dan saba da juna 










😳😳😳😳😳😳🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻😳😳😳😳😳😳😳😳

.



🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      54


Tana zaunen nan falon tana waya da Hajiya Hawau Yar Mahaukaciya ta fito da kwaryar fura a hanunta ta sha damu sai kanshin kayan daka da cikwui take, cikin nutsuwa ta dan zauna har Hajiya fadimatu ta gama wayar 




Ganinta ta karaso ya saka Hajiya Fadimatu fadin "toh Hajiya sai kin zo zuwa yamar, sanan kar fa ki daga hankalinki da sauki jikin"



Tana gamawa ta juyo da murmushin nan nata mai tsada ta kali Yar Mahaukaciya 



Yar Mahaukaciya ta taso ta nufota ta ce" Mamana ga furar yayan nan na dama nasan zai sha"



Hajiya Fadimatu ta ce" Sanu da kokari Yar Fadimatu, aman tafi ki kai masa furar yana dakina"



Yar Mahaukaciya ta juya ba dan taso hakan ba dan kuwa tunda yayi hatsarin nan tamkar ya wani tsaneta ne KO baya ji idan tayi magana dan kuwa sai dai kawai ta ga yana hararanta 




Cikin nutsuwa da faduwar gaban da bata san KO ta maicece ba ta tura dakin bakinta dauke da sallama , 




Idanuwa ta zaro ganin AA Mubasshir jingine da bed ya dafe zuciyarsa ya mike kafafuwansa yana kallon kasa sanan ga wani hawaye na bin fuskarsa , bata san lokacin da ta yar da kwaryar furar ta nufe shi har tana harde kafa 



Tana isa ta dire gwuiwoyinta a kasa ta saka yatsarta ta lakato hawayen kuncinsa dan tabatarwa kanta kuka yake, cikin sarkakiyar murya ta ce" Yaya Mubasshir jikin ne? Ina ke yi maka ciwo? Ka sha maganinka? Dan Allah ka dena kuka, bara na kirawo Mamana" 



Ta mike da niyar FITA ta kirawo Hajiya Fadimatu sai taji an riko mata hannunta riko ba na wasa ba , riko na keta da zafi sannan aka fisgota 



Dabash ta zauna domin sauran kadan ta kifo a kansa Allah ya sota, ta shiga zazare ido tana tsoron abinda ya saka ya rike mata hanu haka sanan irin yanda ya hada fuska ka rantse cewar ba AA bane , gaba daya ya zama wani abin tsoro






Nunfashi ya ja ya sauke ya zuba mata ido yana ayana abubuwa da dama a ransa sannan ya bude bakinsa yayi iya kokarinsa wajen furtawa mai raya tinaninsa mugayen kalamai inda ya ce" *I hate you* "




Da Sauri Yar Mahaukaciya ta dago idanuwanta wa'inda suka fara canza launi sai hasken mai kama da na magen da ya fara fitowa ta zuba masa su 




Hakan ba karamin karayar da shi yayi ba amman sam baya jin zai iya lamuncewa zuciyarsa abinda take so ya ci gaba da fadin" *Yes i hate you, na tsani na hadu da ke, na tsani na zauna tinaninki sanan rashin lafiyata ta dalilinki ne, ke ke din nan dai ke ba zawara ba aman kinfi zawara sanin hanunki dan har kin iya yanda zakiyi ki rikitar da maza, Abdul na sonki, Abdallah na sonki, jama'a da yawa na harin cewar suna sonki , Ni....ya ja nunfashi yaci gaba karyarki ta sha karya a kaina, Ni nafi karfin nace wai ina sonki abin ba dadin ji dan haka ina mai umartar ki da kiyi gagawar tsayar da daya a cikinsu wa'inda suka zubar da girman nasu na aura miki ki kara gaba dan kuwa bana son na ringa cin karo da ke a cikin gidan nan* "





Yar Mahaukaciya dake kalonsa cikin matsanancin faduwar gaba da tarin hawayen dake zuba daga idanuwanta ta ce" *Mai yasa ka tsaneni? Shin wani laifi na aikata?* "




Mubasshir ya kawar da kansa dan kuwa hawayen nan nata ji yake tamkar ya jawota jikinsa ya saka harshen sa ya lashe su sanan ya rukunkumeta dan kar Wanda ya kalan masa ita, yayi gagawar watsar da tinanin ya ce" *kwarai kuwa kina da laifi, kin fi kowa laifi ke laifinki yafi karfin na kawar da kaina kansa dan haka ki kiyayi abinda na fada miki* "




Yar Mahaukaciya ta Mike da kyar ta juya tana tafiya , har ta kusa fita ta juyo ta dawo inda duk takun tafiyarta bugawar zuciyar Mubasshir ne, 



Tana dawowa ta tsuguna kanta a kasa ta ce" *shin tsanar da kayi min ta yan'uwantakar ce KO mai?*



Kwarai tambayar ta zo masa a bazata kuma sai a sanan y'a gane ilimi ne da ita , ya kawar da kansa cikin kame kame ya ce" *ai musulmi baya tsanar musulmi banza haka, ina yi miki son yan'uwantaka wanda koda Maman Mubasshir bata yarda da ke ba dalilinki na musulma zan taimaka miki aman banda wanan son ba wani* "



Yar Mahaukaciya ta kuma cewa " *Son soyaya ne na aure baka yi min?* "





Mubasshir ya gyada kansa da alamar gajiyawa da tambayoyinta 




Da mamakinsa sai gani yayi ta saki murmushi ta ce" *Har ka bani tsoro yaya, daman ni? Wacece ni? Ilimin me gare ni? Mahaifiyata Mahaukaciya ni yar bola har nayi tsamanin soyaya daga namiji kamarka? Ta yi dariya irin da mamaki ta ci gaba" ai dan gata sai Yar Gata, i'a zan fadawa Abdallah idan da gaske yake ya fito inji yayana* " 


Tana gama fadar haka ta mike tayi waje da gudu da alamar jin kunyar nan , 



Mubashir yayi gagawar rike daidai zuciyarsa yana sakin wata irin ajiyar zuciya tamkar yayi tsere, ya silale nan ya konta yana kalmar shahada domin a yanda zuciyarsa ke bugawa shi yasan kawai lokacinsa ne yayi, yasan kawai shi tashi ta kare domin bai san ciwon *So* ba, ta kafa masa wuka ta barshi da tsiyayar jini a kahon zuciya,








Toh fa AA ai gwara karka bige plz ku tayani da adu'ar kar ya tafi🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻



🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      55


Tana fita d'akinta ta fad'a, ta ja ta rufe ta silale jikin kofar tana mai da numfashi, a hankali ta furta" *Ya Allah , kai kayi talaka kayi mai kud'i, kai kayi mai gata da marar gata, ALLAH da kai na dogara domin kaine gatana, Allah kayi min zab'i ba zabina ba, ALLAH ka zaba mini abinda yafi zama alkhairi a rayuwata, Ya Allah* " ta rintse idanuwanta hoton Bakin AA na furta mata kalmar *I HATE YOU* tayi Saurin bude idanuwanta ta mik'e tana fadin A'uzubilahi mina shaidanin'rajim ta fada bayi ta sakarwa kanta ruwa 





Bayan sallar Magarib Yar Mahaukaciya ta sauko amsa Kiran Hajiya Fadimatu a falo, ta sha Riga da Zani na atamfa ta zaya mayafi ja tayi kyau tamkar Yar Tsana duk da ba wata kwaliya ta zana ba , tana isowa ta tsuguna ta gaishe da Hajiya Fadimatu 




Hajiya Fadimatu ta amsa cikin sakin fuska sanan ta ce" Yar Fadimatu ana salama da ke ina jin Abdallah ne 




Yar Mahaukaciya ta sine kai ta mike ba tare da ta amsawa Hajiya Fadimatu ba dan wani irin nauyinta da take ji, ta nufi kofa 



Tana FITA Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya a fili ta ce" astaghfrullah ya Allah ka yafe min wanan abin da nayi , Allah ka san abinda ke zuciyata Allah ka shige min gaba, sanan ta kama hanyar dakinta 



Tana shiga dakinta ta tarar da Mubasshir yana zaune saman darduma yana Jan carbi , a nitse ta nufi windown dakin ta bude madubin tana lekawa 




Mubasshir dake zaune yana hailala yana neman sauki wajen Ubangijin sa yayi fatiya ya juyo yana kalon Mahaifiyarsa ya ce "Maman Mubasshir ina yini? "



Hajiya Fadimatu ta juyo da murmushinta ta ce " Lafiya lau Dan Fadimatu, kaga Mamarka da tsegumi KO? Ina kalon yata ne "




Mubasshir ya ce "Yarki?"



Hajiya Fadimatu ta ce" yes zance ake kaga yanda ta ja gefe tamkar Wanda take tsoron saurayin"




Mubasshir ya zaro ido bai san sanda ya ce" What? Zance ? Kuma ita da wa?




Hajiya Fadimatu tayi masa kalon lafiyarka? Domin tambayoyin nasa a jere sanan ya mike lokaci guda har mazari jikinsa yake , 



Da Sauri ya juya ya fada bayi yana tari ya kuna pampo ya sha ruwa da kyar tarin ya sake shi ya juyo ya fito, yana fitowa ya tarar da Hajiya Fadimatu tsaye hankalinta tashe ta ce" Son jikin ne?"




AA ya girgiza kansa da yake Sara masa ya nufi bed ya konta yana rinrintse ido 




Hajiya Fadimatu ta bi bayansa ta dafa shi ta ce" KO mu tafi asibitin ne? "




Mubasshir ya girgiza kai sanan da kyar ya ce" maman Mubasshir ba komai karki damu"




Zata yi magana taji ana konkwasa dakin ta taso ta bude a tinaninta Yar Mahaukaciya ce sai ta ga Hajiya Hawau 




Murmushi ta saki tana fadin" Hajiya barka da warhaka , sanan ta bata guri ta shige cikin dakin



Hajiya Hawau ta kali Hajiya Fadimatu ta ce" Hajiya da wa yar tawa ke zance ? KO dai shine sirikin namu?




Hajiya Fadimatu ta ce" shine kina gani sai wani kawar da kai take," ta karashe tana kokarin kawar da fuskarta gefe dan kar ya dagota 




Hajiya Hawau ta ce" ai kuwa idan ya shirya ai sai ya fito kawai ayi da shi"




Mubasshir dake sauraron zancen su a ransa ya ce" tazo ganina ne KO tazo ta karasa ni, ? A fili kuwa da kyar ya samu ya tashi ya juyo yana kalon su ya ce" Barka da zuwa Hajaju"




Hajiya Hawau ta karasa tayi tamkar yanzu ta Ganshi ta ce" Dan Aljannah ya jikin? 




Mubasshir ya ce" Jiki yayi sauki Alhamdulilah, daman ina son zuwa wajen ki sai gaki kin zo"




Hajiya Hawau ta gyara zama ta ce" toh bani na sha" 




Ya dan furzar da iskar bakinsa cikin kawar da kai ya ce" *Abdul ya sameni kan zancen nazo na sameki ki fadan inda Rahma take yana son aurenta , plz ki taimaka ki fada masa na yarda da son da yake mata* "




Hajiya Hawau ta kali Hajiya Fadimatu itama ta kale ta irin kalon aikin banza din nan sanan ta ce" *Ai yata anyi mata miji sai dai kuyi hakuri* "




Irin kwaruwar ta dazu ya kuma yi wanan Karin yama kasa tashi balatana ya shiga bayin ya samu sasaucin kwaruwar da yayi ta hanyar shan ruwa, 



Wasa wasa tari ya tirnike shi tun yana rike daidai zuciyarsa har ya saka yana kokarin faduwa, 



Da gudu Hajiya Hawau tayi bayi ta dibo ruwa inda Hajiya Fadimatu ta zauna tana rike da shi suka bashi ruwan ya sha, suka kuma bashi ya sha yana ta ajiyar zuciya 




Hajiya Fadimatu ta dora kansa saman cinyarta tana shafa bayansa a hankali ta kali Hajiya Hawau da ido tayi mata maganar da su kadai suka gane abinda suke nufi sanan cikin muryar nutsuwa da kontarwa mai sauraro hankali ta ce" *Ya zakayi kokarin boyewa Wanda ta dauki cikinka ta raine ka ta shayar da kai ta juri rigimarka ta ga girman ka damuwarka? Ya zakayi kokarin yin gardama da abinda na hango a kwayar idanuwanka? Shin ka manta alkawarin mu na bazaka boye min sirinka ba?* "




Mubasshir cikin Mutuwar jiki ya dago da kansa daga cinyar Hajiya Fadimatu gabansa na ci gaba da faduwa a ransa ya ce" Kardai Maman Mubasshir ta rigayi Mubasshir sanin abinda ke zuciyarsa? Kar dai Maman Mubasshir ta gane cewar Mubasshir ya kamu da son Yar Gidan Fadimatu? Son da yake kokarin zautar da shi? Kaunar da tayi masa shigar bazata?



Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta kawar da kanta ta ce" *Idanuwanka sun nuna tsantsar tsoro da fargabar abinda na karanta a tare da kai* "



Ta Juyo ta kama kafadunsa ta ce " *YA KAKE KOKARIN KASHE KANKA KAN HALALIN KA , IYALINKA, MATARKA? SHE IS UR WIFE MUBASSHIR* "



wani irin dum dum dum maganar ke yiwa Mubasshir a kunansa , wasu tambayoyi ya juyo yayi min Wanda nima nace AO🤷🏻‍♀








Tambaya yake shin Maman Mubasshir ta kuwa san sunan wa ta kama tace matarsa? Shin ta gane KO wanene a gabanta? Idan ta gane yaushe aka aura masa ita? Yaya zai yi da Abdul amininsa? Yaya zaiyi da ita kanta Rahmar?????????????????????????????????muje zuwa 😲


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      56

adu'ar samun sasaucin kunci da tashin hankali


*ALLAHUMA, LA SAHLA ILLAMA JA'ALTAHU SAHLAN, WA'ANTA TAJ'ANUL HAZNA, IZA SHI'ITA SAHLA*


Hajiya Hawau ya tsurawa ido yaga itama shi take kalo, ya juyo ya kali mahaifiyarsa a fuskarta ya karanci sam ba wasa a cikin bayanin ta,  



Wani lalatacen murmushi ya saka yana dan juya kai cikin muryar tausayi ya ce" Eyah maman Mubasshir ba fa ni nake nufi ba, ina nufin *ABDUL* yayan Sahla ne ke son Rahma fa, "




Hajiya Fadimatu ta ce" look son, Rahma matarka ce, taya zakana hada ta da wani kuma? "




Cikin wani yanayi ya juyo ya kale su ya ce" *ku yiwa Allah ku dena hada maganar nan cos ni kunuwana suna jiyo mini wani abin daban, Wanda kuma yake impossible, Rahma dake kofa tsaye tana zance da wani saurayin, gardi, Rahamar da aminina abokina yake matukar so, sai kuma kunuwana su rinka jiyo mini cewar matata ce? Ni ?* "



Hajiya Fadimatu ta mike cikin kakausar murya ta ce" *akoy wasa tsakanin uwa d'a da , sannan akoy zancen gaskiya, Ni Mahaifiyarka ni na samu alwalinka a matsayina na mahaifiyarka da kuma Hajiya Wace ta zamto sheda kuma ta bada amanarta muka yanke wanan hukuncin, ranar juma'a ya daura aurenka da shaidu a gidansa na nan, idan kana musu kayi Kiran sa, idan kuma baka yarda da hukuncina ba to ka watsa min kasa a ido* " ta karasa cikin yanayin bacin rai, dan a ganinta Mubasshir yama raina ta ne yana so yana basarwa




Mubasshir jikinsa yayi sanyi jin furucin mahaifiyarsa da yanayin bacin rai a tatare da ita duk dan shi, da Sauri ya karasa ya tsugunna kasa gabansa na faduwa ya kama kafafuwanta ya ce" Maman Mubasshir kiyi hakuri please, ba ina nufin ban yarda da maganarki bane, KO ban yarda da zabinki ba, no abin ne ya zo min a bazata, Dan Allah kiyi hakuri"


Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya ta kali Hajiya Hawau dake murmushin jin dadi, a nitse ta kamo shi ta dago shi suka koma bakin gadon , cikin nutsuwa ta ce" Dan Fadimatu, zaka yi min biyaya ka rike min yata tsakaninka da Allah?? "




A ransa ya ce  tamkar yanda zan rike raina da mahinmanci , a fili kuwa yayi murmushi ya ce" Maman Mubasshir koda aljana ce kika aura min dole nayi biyaya ba zancen musu " ( ehem ) ya ce GABA da fadin " damuwata biyu ce Maman Mubasshir, Abokina da kuma ita yar taki"




Hajiya Hawau ta dafa kafadarsa ta ce" abokinka ba yanda ya iya domin matar mutun kabarinsa, sanan inada kwakwaran dalili na yin hakan, dan haka kayi fatan alkhairi kawai, "



Hajiya Fadimatu ta dora da " to aman mai yasa kace da y'a ta?"




Mubasshir ya dan kawar da kai yayi kokarin kauda kishinsa sanan ya ce" kinga hanzu ma fa da igiyar aurena tana zance Maman Mubasshir , kuma kina kalo kika barta "




Hajiya Fadimatu da murmushi ta ce " Gidan ku , ta je tayi zancen"



Hajiya Hawau ta ce" aa Hajiya baza'ayi haka ba , an soke zancen"




Mubasshir ya sauke ajiyar zuciya a nitse ya Mike ya nufi bayi ya kuna ruwa ya wanke fuskarsa ya dago kansa yana kalon miror, wani murmushi ya subuce masa a saman lebensa a hankali ya furta " *Matata ce* , ya lumshe ido yana kalon kasa , sanan ya kashe pampo ya fito a ransa yana fadin "wly idan bata shigo ba zan je na dawo da ita dan kuwa ba zai yiwu ba "





Yana fitowa ya tarar basa dakin, ya sauke ajiyar zuciya sai a lokacin ya samu ya nufi window ya bude yana ta hangawa,  ajiyar zuciya ya sauke ganin basa nan, ya juyo a nitse ya tada Salah saman salaya dan ya kara godewa ubangijin sa da wanan kyautar da yayi masa ba tare da wayon sa KO tashin hankalin sa ba,






Tana shigowa ta tarar da su Hajiya Hawau zaune , direct jikin Hajiya Hawaun ta je ta lafe tana dora kanta a saman cinyarta



Hajiya Fadimatu ta ce" Yar Fadimatu bakon ya tafi?"




Yar Mahaukaciya ta dan sine kanta irin jin kunyar nan bata ce komai ba ,



Hajiya Hawau ta shafa kanta cikin nutsuwa ta ce" Yar Gidana muna son yin magana da ke" , 



Yar Mahaukaciya ta dago gabanta na faduwa , badan komai ba sai dan tsoron kar ace ta koma gidan su Abdul, don kuwa KO da anyiwa Sahla aure mahaifiyarta na nan shi ma Abdul din yanzu tsoronsa take .............





Hajiya Fadimatu ta gyara zama ta ce""""""""",,,,,,,,,,,,,"""""""""""







[truncated by WhatsApp]



🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*_Na SAJIDA_*








                      57




Hajiya Fadimatu ta gyara zama tayi gyaran murya ta ce" Yar Fadimatu shin na isa na sakaki abu kiyi , KO na hana ki ki guji yinsa?"




Yar Magaukaciya ta yi gaggawar daga kanta jikinta na rawa dan haka kawai ta tsinci faduwar gaba a tatare da ita ,




Hajiya Fadimatu ta kawar da kanta domin sai yanzu wani nauyin tunkarar Rahma da zancen nan ya darsu a zuciyarta , ta kuma juyowa daidai Lokacin da Mubasshir ke saukowa ya canza kayan jikinsa sai zuba kanshi yake ya fesa tiraren Hajiya Fadimatu , ja yayi ya dakata yana kalon su , shi kansa a yanzu gabansa faduwa yake bai san dalili ba ( zaka sani )




Hajiya Hawau ta ci  gaba da fadin " shin kin dauke mu a matsayin iyaye? Wa'inda suka isa da ke , wa'inda zasu iya yanke hukunci dan inganta rayuwar ki? Wa'inda zasu guji ganin kin halaka sai inda karfin su ya kare? Shin a yau idan muka zo miki da wani hukunci da muka yanke a kanki zaki yarda da shi? "




Zuwa wanan lokacin Yar Mahaukaciya ta gama jika da gumi, domin KO ba komai ta san wanan zancen mai matukar mahinmanci ne, tabas wanan zancen mai mahinmanci ne tana rokon Allah ya sa alkhairi ne, idanuwanta ta dago wa'inda suka kara girma na tashin hankalin da ta shiga ta sauke su a fuskokin su hajiya , wani irin kwarjinin su ya daki kwayar idanuwanta da Sauri ta sada kanta kasa cikin gargadar murya ta ce" Mamana,  hajiyata, iyayena, kun yanke hukunci a kaina shine kuma kuke yi min shawara? Wacece ni? No a duniya banda mahaifiyata sai ku gareni , kun isa da ni , Ko mai kuka yanke a kaina ni na san alkhairi na ne dan haka bani da musu KO ja da maganar ku"




Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyoyin su, kaunarta da Karin ganin darajarta da kunyarta suka darsu a zuciyoyin nan uku, 



Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya da ido ta yiwa Hajiya Hawau nuni da ta fadawa Yar Mahaukaciya abinda suka yi ,




Hajiya Hawau ta kara gyara zama ta ce" *Daman ranar juma'ar can da ta shige aka daura miki aure ke da Dan Aljannah* "



Bugawar zuciyar Yar Mahaukaciya daidai da kiftawar idanuwanta, domin kwatakwata idanuwan ta kasa tsayar da su sai kikifta su take, jikinta gaba daya rawa yake, kafafuwanta dake tankwashe ta samu ta hau saman su ta yi tamkar zaman rakumi a hankali cikin rawar jiki ta dauko hanunta guda ta tokare habarta , hawaye wani na bin wani 




Jikin Hajiya Fadimatu yayi sanyi, ta taso a nitse ta kamo Yar Mahaukaciya ta dora kanta a saman cinyar ta tana shafawa tana gyara mata gashin kanta da shi kansa ya jike wajen hudodin, har a lokacin jikinta rawa yake sanan bata furta komai ba,




Ta kai minti goma a haka , zuwa wanan lokacin shi kansa ji yake kafarsa ta kasa daukar sa, a hankali ya cire hular kansa ya jinginu da jikin abin hawa benen, ya dora hanunsa na dama daidai zuciyarsa yana irga bugawarta ,



Can kamar an tsikare ta ta zabura ta sauko kasa ta hada hanayenta biyu kamar ta zo neman gafara ta ce" *Mamana ki yi min rai, kar ki saka ya kore ni daga inuwarki, shi ya fada min da bakinsa cewar na fitar da miji cikin satin nan ya aurar da ni ya huta da gani na, yanzu idan ya ji cewar an aura masa ni ai har ya hadiyi zuciya ya mutu daman ba lafiya gare shi ba , dan Allah dan Annabi a kashe auren nan tun kafin ya ji ya kore ni mama Dan Allah, kinga sai Abdallahn yayi ya fito daman yanzu ya gama fadar hakan* " ta karashe zancen tana rushewa da kuka , ta mike da gudu ta nufi hanyar dakinta 




Daidai zata hau ta ganshi nan tsaye gabanta ya yanke ya fadi ganin irin yanda yake da kyau haka gashi da alama fuskar sa tamkar ransa a bace, gabanta ya kuma yankewa ya fadi , a ranta ta furta *wutsiyar rakumi tayi kadan ta taba kasa* 



Shi ma gabansa ya yanke ya fadi domin idanuwansa sai suka hango masa tsanarsa a kwayar idon Yar Mahaukaciya, nan take kalmar *I HATE YOU* da ya furta mata nan da yan awanni suka dawo masa , ya bi bayanta da kalo har ta shige dakin ta rufo 




Hajiya Fadimatu ta mike da niyar bin bayan yarinyarta , Hajiya Hawau ta dakatar da ita ta ce" kar ki bita a yanzu, ki barta ta gama shawara da zuciyarta , "




Hajiya Fadimatu ta koma ta zauna jiki bâ kwari ta ce" tabas idan Yar Fadimatu ta ce bata son Dan Fadimatu zan raba auren nan , dan kuwa bazai yiwu ni da kaina na aurawa yar Amana abinda bata so,




Muryar Mubasshir suka tsinta yana fadin" *NO MAMAN MUBASSHIR BAZA'A RABA AUREN DA BA'A TARE SHI BA MA , BA KYAU* "




Hajiya Hawau da Hajiya Fadimatu suka zuba masa ido irin yanda jijiyoyin hannun sa suka mimike, 



Hajiya Hawau ta kawar da kanta tana kokarin danne dariyarta dan kuwa da ka kali fuskar Mubasshir zaka karanto tsantsar tsoron kada a raba shi da abinda yake matukar so, ta kali Hajiya Fadimatu ta ce" *wanan aure mun hada shi ne da niya mai kyau, sanan shi aure raine da shi, kuma wanan karamin dalili ba zai saka mu raba auren nan ba saï da kwakwaran dalili, Rahma na cikin tsoro ne da fargabar yanda Dan Aljannah zai karbi maganar, bayan shi ban karanci tsanarsa a kalamanta ba, ki barsu su sasanta kansu ya nemi soyayar matarsa da kansa ki zira ido hakan shi zai kawo alkhairi ba wai a raba auren ba* " 



Mubasshir ya gyada kai uwa shi ake fadawa ya ce " yawa Hajiya , ai shi kansa sakin ba kyau ana yinsa"



Hajiya Fadimatu ta zabga masa harara ta ce" ai Dole ka fadi haka bayan ka gama fada mata tayi ta fitar da miji kai ka gaji da ganinta KO?  Kai ga dadynta, to sai kayi kokarin fahimtar da ita kaine mijin idan ba haka ba kuwa ,i'm sorry sai dai ka sakar min y'a "



Tana gama fadar haka ta Mike ta nufi kicin dan samawa Hajiya Hawau wani abin Marar nauyi ta ci...



Da ido suka bita sanan a tatare suka sauke ajiyar zuciya , Mubasshir ya kali Hajiya Hawau ya ce""""""""__,,,,,,,"""""""""""""""",,,,_______"""""""""""""





🇳🇪BELLES écrivaines Nigériennes 



'YAR 👧🏻 




 MAHAUKACIYA👹 na 




    



                    58






*Tabas soyaya ita ke sakawa a damu da mutun idan an ga shiru, idan na ce zan tsaya zano ku wly sai mu cika page din bamu gama bâ, Alhamdulilah Allah na gode da ka bani ikon rubutu tabas alkhairin rubutu shi na samu ba sharin sa ba, sisters godiya marar addadi , tsakanina da ku sai fatan alkhairi, daga taku yar Mutan Niger*







Mubasshir ya zubawa Hajiya Hawau ido , yana matukar son ya kara fada mata kar ta yarda Maman sa ta raba auren sa , aman ina ai da kunya KO ba komai kakar Sahla ce, Dole ya ji kunyar wani abin, Hakan ya sa ya Mike yana kokkarin FITA daga dakin dan bai ga ana marhabun da shi a cikin gidan ba 





Cikin murmushi irin nasu na Manya ta ce" dawo ka zauna Dan aljannah,"




Mubasdhir ya juyo yana tafiya kansa a kassa ya dosanu ya zauna stil yana kalon kassa




Cikin nutsuwa ta ce" ni na jajirce da taimakon ubangiji aka daura maka aure da Marainiyar Allah,




Cikin firgicci ya dago yana kalon ta, 


Hajiya Hawau ta ci gaba" kwarai kuwa , abinda ya saka ni aikata hakan dan ina tsoron aurawa wani yarinyar amanna ya cutar min da ita, tabas na san bazawarra ce aman idan kayi hakuri ta fi budurwar dadin zama ,"



Mubasshir ya kuma dagowa ya kara kalon ta a ransa ya ce " Ai fa ni ba dadin zamanta nake so ba, dan kuwa na sani Sahla ta FITA dan ta FITA kama kai,duk da haka ga yanda na same ta ballatana Wace ta waye a harkar? Ni kawai hutu na aura sai kuma ina dan tausaya mata,  




Hajiya Hawau ta ce" ka bani amsa, shin zaka iya kular min da yarinyata? "




Mubasshir ya danyi murmushi ya ce " ai KO da ban sanki ba girman ki ya isa na girmama abinda kika hango ballatana na yarda da zabin ki, insha Allah zan yi kokarin adalci a tsakaninsu




Hajiya Hawau ta amsa sa cikin farin cikin girmamata da darajata da Dan Aljannah yayi 







Bayan ta salamce salar walahar ta ta juyo a nitse ta karasa inda Gajiya Fadimatu ke zaune da abinci a cikin assiete tana jiran ta gama sallar, tsugunnawa tayi har kassa fuskarta da dan murmushi ta ce" Mamana ina kwana, an tashi lafiya? "




Wani sanyin dadi ne ya ratsa zuciyar Hajiya Fadimatu ta ajiye plat din abincin ta kamo Yar Mahaukaciya ta zaunar da ita saman bed din tana kalon ta, can ta ce" jiya kinyi baci baki ci abinci ba Yar Fadimatu,"




Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta ce" kawai sai da na farka na ganni ina baci kuma sai tsoro ya Hanna ni FITA na debo abinci, "




Hajiya Fadimatu ta ce" Tsoron mai?"



Yar Mahaukaciya tayi gagawar dukar da kanta ta ce " ba komai mama"



Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta dago habar Yar Mahaukaciya ta ce" idan na ga auren nan cutuwa ne a gare ki believe me ba inda zai  da izinin Allah, sanan a yanzu haka idan kika kafe kan bakya so zai sawake miki duk da shi din yana so"




Yar Mahaukaciya ta zaro idannuwanta bata san sanda ta ce " Yana so?




Hajiya Fadimatu ta ce " Yes,  yana so"




Yar Mahaukaciya ta dan sadda kanta da matsanaiciyar kunya tana tir da wanan baki nata, a zuciyarta kuwa tasan wacece ita harda AA Mubasshir zai so auren ta? (Haka)





Mikewa Hajiya Fadimatu tayi ta bude werdrob din Yar Mahaukaciya ta ciro wata doguwar riga ta atamfa, rigar taji dinki daga sama ta matse sai ta bude daga kasa, da dan tsaga tsaga a sama daidai kirjin rigar sannan zub din bai hau har sama ba, hanun rigar daya dogo ne daya gajere , jar atamfa ce mai ratsin baki baki kalar fararen fata 😅🤷🏻‍♀, 


Ta mikowa Yar Mahaukaciya dake zaune sannan ta ciro mata dan kwalin rigar ta miko mata ta ce" tashi Yar Fadimatu ki shirya mu tafi amsar kaya na nadiya nan makota,"



Yar Mahaukaciya ta dago atamfar, dinki ya hadu iya haduwa sai dai kunyar dinki ta saka ta kasa sakawa, sai dai a yanzu bazata taba iya musantawa Hajiya Fadimatu ba , Hakan ya sa ta dauka ta nufi gaban mirror dan ta dan gyara fuskar ta dan Hajiya bata son ta FITA bata saka kwali ba ,




Zama tayi ta yi dan adonta iya lips dinta da idanuwanta ta Mike ta dauki bras dinta ta saka ta saka pant dinta sannan ta dauko rigar har wani kara karan zub din take dan KO tafiya kake zub din na motsi suna Jan hankalin mutun, , cikin nutsuwa ta saka ta ja zub din sannan ta dauko dan abin hannunta baki siriri ta saka , ta dauko dan kwalinta zata daura Hajiya Fadimatu ta shigo tana fadin " Yar Fadimatu ki fito sai su dauko miki wa'inan bol din , hajiya Karima ce ta ce a zo mata da su saboda wajen mijin Nadiya gidan sarauta ne ita kuwa bata tanadi wanan ba , dan haka bara nayi gaba sai ki biyo ni da sauran 




Yar Mahaukaciya ta ce " To mamana , ki bata kar ta manta"




Hajiya Fadimatu  ta ajiye ta karbi bakin ribom din ta tatara gashin kan Yar Mahaukaciya ta hade waje guda ta saka mata ribom din sai gaba daya ya zubo ya rufe mata wajen da rigar bata rufe ba daga baya sanan ta dauko bololin ta nufi hanyar gidan Hajiya Karima makociyar su,





Bayan ta gama shiryawa ta dauko tirarukan dake saman table din dakin ta yiwa jikinta barin sa ta bude wajen takalman ta ta dauko wani plat mai igiya baki ta daura a kafafuwanta sannan ta fito cikin nutsuwa da mayafinta baki mai shara shara irin mai dan duwatsun nan tamkar sange , 




Cikin nutsuwa ta sauko direct ta nufi kicin tana kwalawa ma'aikatan gidan kira dan ta ga an fitar da kayan ita kawai suke jira 



Da ido ya bita sauran kadan ya kware , yana waya da Sahla tana ta magiyar ya amsata yayi mata shiru , cikin sarkewar murya ya ce" Sahla ina zuwa ,"


Kafin ta bashi amsa ya katse Kiran ta kali mahaifiyarta dake zaune tana sauraron labarin nasu ta ce " Mama kinji fa ya kashe, ni gaskiya sai na kara kwana biyu na kara hutawa dan wly so yake ya kashe ni sam bai san gajiya ba a rayuwarsa "




Hajiya Marhaba ta ce " ai shiyasa na amso miki magungunan nan sai kiyi ta anfani da su yanzu haka Wanda kika matsan nan kinga dubu hamsin na siyo shi dan karfi ne da shi, sai dai yayi ya gama har ya gaji ba dai ke ki gaji da shi ba "




Sahla ta dan yatsina fuska dan tunda ta matsa maganin nan cikinta ke yi mata wani irin ciwo kokari ne dai kawai take dan Mahaifiyarta ta fada mata anfannin maganin yawa ne da shi , ita fa a gaskiya a yanzu tsoron mazan ma take tun karfinta cause Mubasshir tamkar machine yake shi dai burinsa ya ji sa a birnin nan Wanda jirgin sa mai wuyar sauka ne (😲). " tayi kwafa kasa kasa ta ce" Ashe dai ana gajiya da ita"






Fitowa ta kuma yi da wata Babar leda a hanunta tana kokarin gyara rikonta kwalabe ne a ciki na shan ruwa masu nauyin tsiya ga tsada ga kyau , sam bata lura da mutun a falon ba tana juyowa ta gamshi zaune yana kalonta , gabanta yayi wani mugun faduwa bata san lokacin da ta saki ledar ta fada mata a kafa ba , 



Ido suka rintse a tare dan kuwa yanda ta ji azabar faduwar wanan kofofin haka ya ji a jikin sa , , wani ihu ta saki na azaba da firgici domin ta firgita kwarai da ganin ba zatan da tayi masa a falo ga kuma faduwar wanan abubuwa masu masifar nauyi murafen su masu dan kaifi har daya ya yanke ta, wani wahalalan kuka ta saki gaba daya jikinta na rawa ..






Mikewa yayi cikin zafin nama ya isa wajen ta , yayi gagawar janye ledar ya cire Wanda ya dan yankun mata , yanda jikinta ke rawa haka NASA ke yi, cikin dauriya ya Mika hanu ya daukota cimak ya nufi Babar kujerar dake tsakar falon ya shinfida ta , sai wani kakauda kai yake




Wayarsa ya janyo yayi Kiran Umairah docter matar général kadre makociyarsu dan yanda take karkarwa sai yake jin tamkar wani abin ne ya shige mata kafar, 



Minti sha biyar tsakani sai gata ta shigo ta karaso tana fadin "Oh yar gidan momynta ce ba lafiya? Oya cuta baki yi mana adalci ba " 





Mubasshir ya dan Mike yana fada mata ga abinda ya faru,




Umairah tayi murmushi ta kama kafar ta Yar Mahaukaciya tana dubawa ba karaya ba gocewa , jin ciwon nan dai ne , hakan ya sa ta dauko compress ta goge mata da alcool ta rubuta mata amoxi ta mikawa AA sanan ta juya ta tafi ,





Mikewa tayi a hankali tana dan rintse idanuwanta ta mika hannu zata kuma daukar ledar ta je ta kaiwa Hajiya Fadimatu ,




Mubasshir ya zubawa kirjinta ido ta tsagogin dinkin nan, gabansa ya fadi yayi gagawar hadiyar wani yawu mai wuya , ya kuma zubawa dogon wuyanta da bayanta ido ba shiri ya kawar da kansa tun kafin ya bada kansa, cikin muryar tasa ta yana hanu ya ce" ina zaki je?"



Gaban Yar mahaukaciya ya Fadi ta dago tana kalonsa cikin gargadar murya ta ce" am daman mamana ce ta ce na kai mata wa'inan wajen amsan kayan Nadiya" 





Ya juyo yayi mata kalon kinyi kadan ki fita sanan ya mike a nutse ya nufo ta, 




Takunsa take ji sai ji tayi ya kure mata waje, a hankali ya Mika hanunsa daya ya dan rankwafa daidai wuyanta har lumfashin sa na sauka a saman wuyan ta ya kama zub dinta ya .......  ......................... ................ ........(😅😅 oh my Hawee kinyi shiru ki ji yayi mai da zub din KO? Har kin diro, to alhana bazan fada ba 😲🤒🤒🤒🤒💃💃💃💃)



🇳🇪BELLES écrivaines Nigériennes 



👹 YAR MAHAUKACIYA👹 na SAJIDA



    



                    59


Lumfashinsa na sauka a saman wuyan ta, da gangan ya kara jawota kadan hakan ya Sakata jin bugawar zuciyarsa da Sauri da Sauri, Zip din ya kama da niyar ya ja shi ya rufe sauran wajen da bai rufe bayanta ba , hakan ya baiwa hancinsa damar sauke numfashinsa a kunnanta , 



Jin wanan bakon al'amarin ya saka jikin Yar Mahaukaciya mutuwa, gaba daya jikinta ya saka ta furta " *Wayo Allahna* " tayi luuuu zata fadi 




Cikin mutuwar jikin shima ya tarota suka fada saman Babar kujerar, da Sauri ya mike yana kakabe jikinsa ya dan gyara tsayuwarsa ya saita muryarsa ya ce " Kai Bariki, idan mutun ya saba da abu hakane, na tabo miki wajen dake miki kaikayi KO? Yayi kwafa ya dan duko cikin rada rada ya ce " i'm sorry da na katse miki jin dadin ki dan ba kyau bin maza a waje may be ni kadai zan iya gamsar da ke , aman da alama sai nayi da gaske dan kin fiya zalama" yana gama fadar haka ya juya yana taka mattatakalar dakin ya nufi dakin mahaifiyarsa 





Da kalo ta bi bayan sa har ya shige, nanauyar ajiyar zuciya ta sauke , tabas da da ne bazata damu da maganganunsa ba , a lokacin da idan ya yi su ma bata san inda suka dosa ba , sanan da a shekaran jiya ne ma ba zasu wani mugun damun ta ba cos ba'a fada mata cewar miji yake a gareta ba , aman a yau sai ta ji ba dadi, gaba daya sai ta ji ta muzanta, shin ina laifinta dan ta wayi gari ta tsinci kanta a bola? Menene laifinta dan ta rayu a cikin bola? Ta rintse ido a fili ta furta " *Shin mijina yana yi min kalon fasika ne?* ,





Lami dake tsugune tana maganna ta ce" na'am hajiya?




Yar Mahaukaciya tayi gagawar kallon ta , sannan ta ce" Au Lami kin fito?, kinga bara na saka hijab dina mu tafi mu kaiwa mamana nassan tana ta jira"







Lami ta ce" Ai hajiya Elhaj ya ce a fada miki karki fita, mu mu tafi mu kai kayan"



Yar Mahaukaciya ta ji zancen wani iri ta dago ta ce" Elhajin ne ya fadi haka?"



Lami ta amsata cikin biyaya 




Yar Mahaukaciya ta ce " ohk tohm ki dauka ku kai mata , aman kar ku ce shi ya hana ni zuwa kunji? "





Lami ta ce" to Hajiyata a huta lafiya" suka dauki kayan suka tafi abinsu 










Birgima take tana ihun cikinta , fitowa tayi daga bayi ta nufota da Sauri tana fadin Sahla ke kam akoy ragwonci , matsin maganin matan ne kike yiwa wanan ihun? To da a gabansa ne sai ya san abinda kika matsa KO? "





Sahla dake rusar kuka ta cusa hannunta kasanta ta shafo lemar da take ji na binta ta dagowa Hajiya Marhaba dan kuwa bakinta ya kasa magana bale har ta furta kalmar jinnin dake binta 





Idannuwa Hajiya Marhaba ta zaro sannan ta juya da gudu tana ihun a zo a taimake ta dan ta kai Sahla Asibiti. ,






Bayan kamar awa uku likitici biyu maza suka fito da nurses sun hada gumi sosai , Hajiya Marhaba ta mike tana karkarwa ta nufe su ta ce" Ya jikin y'a ta docter?




Docter Aliyu yayi gagawar fadin ki biyo ni office dina , yayi gaba inda docter Usman ya bishi da kalo yana jin haushin wanan halaya na docter Aliyu Wanda a da bai san shi da  su ba ,




Suna shiga ya ja kujera ya zauna inda Hajiya Marhaba ma ta nemi waje ta zauna tana sauraron sa cikin bugawar zuciya , 






Docter Aliyu ya ce" wa ya zubar mata? "






Hajiya Marhaba ta dago tana kalonsa da alamar tambaya ta ce" ban gane inda ka dosa bâ?"


Docter Aliyu yayi murmushin rainin hankali ya ce" cikin jikinta wa ya zubar mata?"






Hajiya Marhaba ta zabura tana dafe kirjinta ta ce " ci.....ciki????? Inalilahi wa'ina ilaihi raj'une, ciki ne da Sahla ? Kuma ya zube?" 



Gaba daya cikin firgici take da tashin hankali dan KO an fada mata ba zata yarda cewar Sahla har ta dauko ciki ba , abinda suke nema tamkar ransu gashi sun samu kuma sun barar da shi garin a kara mata kokarin juriyar yawan sha'awar sa , wannan ai shine kaga samu ka ga rashi, ta kuma rushewa da kuka





Docter Aliyu yayi zuru yana son sanin kukan na mainene , can ya nisa ya ce " tana da aure ne?"




Hajiya Marhaba cikin share Hawaye ta ce" da aurenta mana"




Docter Aliyu cikin jin haushin Kenan ba zai samu kudin da ya hango ba zai samu ba ya ce" Toh dole sai mijinta ya zo wajen nan dan kuwa cikin mun gano cewar matsa wani abin ne akayi dan a zubar da shi, dan haka sai ya zo KO an kawo mana takardun da likita ya saka ayi hakan saboda lafiyarta"





Hajiya Marhaba ta zaro ido ta ce" uban mai mijinta zai yi a nan? Tap KO daya ai KO mai za'ayi ayi shi iya nan docter"





Docter Aliyu ya zuba mata ido shi daman da ganinta ya san ba gaskiya a al'amuran ta shi ya sa ya gano ci a tare da ita hakan ya sa ya gabatar mata da uzurin sa inda Hajiya Marhaba cikin karkarwar jiki ta biya masa muradinsa ta baro offishin sa cike da jin haushin kanta na asarorin da suka sameta a dan kankanin lokutan nan ( wannan Kenan)








Cikin bacinta take jiyo waya na ringin ta Mika hanu ta kashe kafin ta maida hannunta ta kuma kwasan kuka hakan ya sa ta Mike tana murza idannuwanta ta nufi kofa dan bude kofar shigowar,






Tana budewa idannuwanta suka sauka kan fuskar mutanen dake Dana cl din shigowa falon nasu , kirjinta ta dafe ta kurma ihu daidai da daukewar nunfashinta tayi baya yim ta fadi kass inda suka nufota cikin kidima da tashin hankali.................'''











Shin su wa Yar Mahaukaciya ta gani????????????????????????????????





🇳🇪Belles écrivaines du Niger


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*Na*

             *Sajida*


                      70


Adu'a suke tun karfin su, aman jikinsa sai kara daukan zafi yake, 

Hajiya Fadimatu ta daga hannunsa ta saki hannun wani irin nauyi, tayi saurin kawar da kanta ta rintse idannuwanta gabanta na mugun faduwa 


Yar mahaukaciya ta ce" mama Lafiya ?  Ba alamun sauki ? 


Hajiya Fadimatu ta tataro dukan KOkarinta ta ce" ba komai y'ar Fadimatu, 


Yar Mahaukaciya ta ce" KO na Kira Yaya Idriss ne ? 


Hajiya Rafi'at ta Gyada mata kai, hakan yasa ta ajiye kansa à hankali ta nufi wayar falon ta danawa ofice dinsa Kira domin ta san kawai yana ofice 


Jin abinda ke faruwa ya saka shi barin Ofice dinsa ya kwaso yan kayan aikinsa ya nufi gidan su abokinsa domin ceto ransa 


Yana zuwa ya tarar still sun dukufa sai adu'a suke masa zuwa lokacin Yar Mahaukaciya kam ta fara zubar da hawaye domin hannun sa baya KO karyuwa


Yana zuwa ya shiga tambayar abinda ya faru, inda hajiya Fadimatu ta fada masa komai na idan yayi irin haka harda na Karshe da yayi bai kai hakan ba


Idriss ya ce" Mama na karshen da yayi mai akai masa yaki yin nisa ? 


saï à lokacin suka tuno jawabin mahaifin Fadimatul islam (Yar Mahaukaciya)  kan idan hakan ta faru à tabatar da an saka shi à ruwan kankara sosai cikin ikon ALLAH zai kawo hankali


Nan ta kwashe ta fada masa yanda Elhaj Muhammad ya fada, 


Idriss ya ce" to wankan za'a yi masa ai mama 


Hajiya Fadimatu, Aunty Habiba, Hajiya Rafi'at da Islam gaba daya suka zuba masa ido suna kalon sa


Hajiya Fadimatu tayi karfin hali ta ce" wankan KO ?  To ya zamu iya kai shi dakin ? 


Idriss ya Mike gannin yanda duk suka wani tsure ya nufi kofa yayi Kiran securitiesn suka taho suka cicibi AA suka yi dakin Yar Mahaukaciya da shi inda ta Mike ta bi bayan su domin hada ruwan wankan 


Baban bokici ta cika da kankara ta shiga bayin ta zagine tana sauyewa à cikin bahon wankan Daidai nan Hajiya Fadimatu ta shigo ta kama mata suka juye kankarar, 


Suna gamawa su Idriss suka shigo da shi à talafe da dan gajeren Wando à jikinsa Yar Mahaukaciya tayi gagawar lafewa à bayan Hajiya Fadimatu , suka saka shi à cikin bahon ruwan da yayi mahaukacin sanyi


Suna saka shi securities suka juya suka fita inda su Hajiya Fadimatu ma suka yi niyar fitar dan barin Idriss da AA ya zuba masa ruwan à jikin sa


Idriss ya ce" Mama ku dakata ku matso mu yi masa tare 


cikin sagewar gwuiwa suka juyo islam na biye da ita tamkar jela kanta à kasa suka shiga daban ruwan suna zuba masa har à cikin sumar kansa


Basu dau wani lokaci suna hakan ba ya ja wani dogon numfashi ya bude idanuwansa tamkar gauta dan ja à fuskar mahaifiyarsa domin ita kawai ya fara tozali


ido ya rintse yana Jin yanda kankarar nan ke ratsa masa jijiyoyin jikinsa, kokarin zama yake aman sulbin abin wankan ya hana shi, 


Ya damki hannun mamansa ya kafe ta da ido saï ga hawaye wasu na korar wasu


hajiya Fadimatu ta kasa jurar ganin hawayen yaronta Bata san sanda ta jawo shi jikinta ba du da tsananin sanyin ruwan nan ta ce" Hasbunnalahu Wa ni'imal wakim, Ya Salam, shin yaushe dan Fadimatu zai daina daukan bacin rai da zapi haka ?  Shin yaushe zai lazumci fadin Inalilahi Wa'ina ilaihir'raj'une à duk lokacin da yaji ransa ba Daidai ba ?  Dan Fadimatu irin wannan zuciya ba'asan musulmi da ita, Tunda ka yarda da kalmar La'ila ha ilalahu MUHAMMADU'rasululah salalahu alaihi Wa Salam ka gama komai, Tunda ka yarda da shi kadai ya Isa yayi kuma shi kadai ya Isa ya hana mai yasa zaka kuma saka damuwar wani à ranka ?  haba dan Fadimatu yanzu fa girma ya hau kanka, Dan mai bazaka gyara shi ba ? 


Kalaman mahaifiyarsa na sauka à kunan sa tamkar warware masa kalmomin bakinsa ake cikin ikon ALLAH ya fashe da kuka mai tsanani ya kara rike mahaifiyarsa yana tunanin da mugun nufin su sahala ya kasance da an halaka masa mahaifiyarsa dan kuwa bazata juri hakan ba, 


yana kuka tana hamdallar Jin muryar sa domin Bata sakawa ranta zata ji muryar sa a kusa kusan nan ba,  hakan yasa ta barshi yayi mai isarsa sannan ya shiga ajiyar zuciya, du wannan abin bai lura da Idriss da Yar Mahaukaciya dake zaune dirshen à cikin bayi suna nasu hawayen ba 


Cikin yanayin tausayi ta ce" fada min Wanda ya bata maka haka ? 


AA ya lumshe Idannuwansa, da ace zai iya da ya boyewa mamarsa wannan lamarin, saï dai Ina bashida sama da ita, damuwarsa damuwarta ce,  Dan haka ya bude bakinsa yana hawaye yana fada mata gaba daya abinda kunuwansa suka jiyo masa à gidan sa wato tataunawar Matarsa ta suna da Sirikarsa


Idriss dake saurare yafi kowa firgita inda ya rushe da kuka tamkar mace ya hada kansa da garun bayin ya shiga buga kansa da garun yana tir da halayen mahaifiyarsa da Kanwar sa


sai à lokacin AA ya lura da mutane à bayin bayan mahaifiyarsa,  da sauri ya Mike ya nufi Idriss ya jawo shi da hanu guda ya ce " Idriss, baka da hankali ne ? 


Idriss cikin kuka ya ce" banga anfanin rayuwata ba Mubasshir, Ba yau ba nake yiwa su mama à kan duniya aman abin har ya tsalake baiwar ALLAH (Hajiya hawau) ya fito kai ? Shin Mamana Bata kaunar saduwarta da rahamar ubangiji ne ?  Ta raba d'a da mahaifiyarsa, ta kyamaci nakasasu, ta wulakanci talaka, yanzu tana kokarin halaka rayuwar jama'a da dama dan kudi?


why ?  

Hajiya Fadimatu ta karaso gabansu ta ce" ya ku yayana ku saurara, ku kasance masu yiwa iyayen ku adu'ar alkhairi à duk halin da kuka tsince su, Idriss tsananin ka da mahaifiyarka adu'ar shiriya da ita da kanwar ka, 


Ta juyo wajen AA ta ce" ka Sani da 1 ALLAH ya kawo ka har ka tsinci wannan tataunawar ya saka da Rahama, abinda nake SO da kai shine kayi ta adu'a ba dare ba rana à duk halin da ka tsinci kanka à ciki kan ALLAH yayi maka jagora, sannan idan ta baka karka sha, ta kali Idriss ta ce" Kayi hakuri Idriss kayi hakuri Haka Taka Kadarar take, yanzu Baban abinda ya dace muyi shine mu kwatanta musu cikin nutsuwa idan da halin kubutar su cikin ikon ALLAH zaku ga sun kubuta 


Idriss ya sada kansa, shi yanzu wata irin kunyar su yake ji ya zaiyi da iyayen sa ne ?  Ina zai saka ransa ? 


Hajiya Fadimatu ta juya jikinta à matukar mace ta nufi waje tana mamakin wannan lamari 


Yar mahaukaciya ma ta juya da sauri zata fita AA ya ce" Islam dakata 


Cak ta tsaya tana kalon kasa inda Idriss ya juya à nitse ya silale daga bayin ya fito matatakalar benen ya zauna yana kalon kasa


Aunty Habiba Y'ar sokoto ta kali Hajiya Rafi'at ta ce " sister banga fitowar amarya ba fa, kar aikina ya koma baya, ta karashe tana murmushi


Hajiya Fadimatu da gaba daya jikinta yayi mata nauyi ta ce" au ai mantawa Nayi na barota à dakin, please sister tashi maza ki sauko min da ita domin yaron nan sai adu'a


Hajiya Rafi'at ta Mike tana murmushi ta nufi matatakalar benen tana hawa kunuwanta na jiyo mata sheshekar numfashi inda tayi tsai gabanta na faduwa tana son gane kukan waye ? 


 

😳 Amarya à dakin ango😳, Idriss ma yana wajen, shin kukan waye ????????????? 😄😄😄😄😄😄😄🤒


🇳🇪Belles écrivaines du Niger


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*Na*

             *Sajida*


                          71


*Wannan page Ina rokon duk wani mai rauni karya karantawo 🤷🏻‍♀*


Cikin sasarfa ta karasa daga kusan mai kukan gaba daya jikinta ya mutu cikin wata irin murya ta ce" komai yayi zapi ka barwa sarki ALLAH, shi zai sanyaya maka Idriss,  kadarar ka mai sauki ce Idriss domin da ranka da lafiyarka to sai ka barwa ALLAH komai shi zai warware maka damuwar ka


Tunda ta fara magana ya tsayar da kukan da ya Zo masa yana sauraron duk wata Kalma da zata furta Har ta dasa Aya, ji yayi inama Bata rufe bakinta ba domin wata iriyar nutsuwa da take sauko masa lokacin da Take maganar, dago kansa yayi ya zuba mata ido, tana maganar ashe Bama shi take kalo ba, tana kalon kasa, saurin kawar da kansa yayi daga kalon kurular da ya kafeta da shi yana furta a'uzubillah haka kawai ya kare matar mutane da kalo, cikin yanayin sauri ya Mike yana gagawar magana ya ce " na na na gode, 

Da sauri ya raba ta gefenta ya fice tamkar tana biye da shi dan ta kama shi, 


Hajiya Rafi'at ta lumshe idannuwanta maimakun ta nufi dakin AA sai ta shige dakin Hajiya Fadimatu ta Konta à gefen bed ta rufe idannuwanta tana tunanin irin rudanin wannan family da kuma shi Idriss Da Allah ya tsame daga halayen mahaifiyarsa


Kalon bayanta yake yana takowa à hankali har ya ISO Daidai inda take tsaye Tunda ya kama sunan ta, a nitse ya dan rage tsawon sa ya dora kansa à wuyanta yana sinsinawa 


Yar Mahaukaciya tayi saurin juyowa tana kikifta ido cikin inda inda ta ce" Yaya  Lafiya ?  Mainene kuma hakan ? 


Mubasshir ya rintse Idannuwansa ya kuma budewa gaba daya jikinta wani irin santsi da wani shegen kanshi yake, kara janyota yayi ba tare da ya Bata amsar tambayoyinta ba ya hadata da jikinsa, 


Gaba daya jikinta Bari yake domin har à lokacin jikin AA banda gajeran Wandan nan ba komai, Yar Mahaukaciya ta dimauce ta rasa  mai yasa yake sha'awar hada jikinta da nasa, 


Katse mata tinaninta yayi sanadiyar jan dan kwalin kanta Wanda à dole aunty Habiba ta konce mata shi dan al'adarta ta dauke dole ta wanke mata shi tayi wankan sallar Azahar, hakan ne ma ya saka aunty habiba sakawa a kirawo Yar Mahaukaciyar dan tana gudun kilu ta jawo bam, 


Yana jan dan kwalin ya fadi kasa gashin ya zubo da dan danyatar sa ta mayukan wankin kan da aka yi anfani da su wajen wanke kan, Hancinsa ya kai à hankali ya sisina ya lumshe Idannuwansa cikin nutsuwa ya shiga cusa hannunsa à cikin gashin yana kara lumshe ido


yar mahaukaciya ta zaro ido da sauri ta dago idannuwanta tayi arba da fafadan kirjin sa Wanda à Yau ne ta fara ganinsa à fili haka, gabanta ya fadi ganin irin baiwar ni'imar da Allah yayi masa gashine konce yayi sidik da shi s kyalin ruwa yake,  dago da kanta tayi dan Jin bugawar zuciyarsa ya tsananta kan na da, 


Tana dago da kanta tamkar Jira yake ya hade bakinsa da nata ya shiga kissing, 


Yar Mahaukaciya ta zaro idonta ta shiga kokarin kwacewa, aman Ina karfin ba daya ba, ganin zata Bata masa lokaci ya saka shi yayi sama da ita ya fito daga bayin yayi saman bed da ita


wutar dakin ya mika Hannu ya kashe sannan ya ci gaba da kissing din Fadimatul islam wace daidai wannan lokacin tana kokarin fita daga hayacinta dan ita kanta à Yau tana Jin dadin tabatan da yake sakamakon tsumin Aunty Habiba  Mai Abin Mamaki Y'ar sokoto, 


Zuwa wani lokaci AA yayi fatali da Rigar Yar Mahaukaciya wace ita kadai ce à jikinta sai zani da ta Daura, 


Arba yayi da yan biyu sunai masa hello, bai san  sanda ya kai bakinsa domin kawo musu agaji ba, 


Su duka nunfashin wahala suke saukewa Daidai nan AA ya ce fa yana bukatar isar da sakonsa banban birnin, 


Saï à wannan lokacin Y'ar Mahaukaciya ta bude idannuwanta ta zuba masa ido inda ta lura da gaske fa yake, 

Tura shi ta shiga yi tana Kiran sunansa aman Ina aikinsa yake ba sasautawa, kukan wahala ta saki tana tura shi tun karfinta aman Ina baya Jin duniyarta bale ya saurara mata, 

Kuka take tana yakushinsa domin ji take tamkar zata bar duniyar, tun tana yi da karfinta har ya kasance KO hannunta ta kasa dagawa tana ta zubar da hawaye saï da bukatarsa ta biya dan kansa sannan ya kyaleta ya koma gefe yana sauke ajiyar zuciya( 😳 Leila ba ruwana) 


Ganin shirun yayi yawa gashi wayarsa saï ringin take Sahla na kiransa mai yiwuwa dan taga dare yayi ne bai dawo ba take kiransa ya saka Hajiya Fadimatu ta Mike ta haura sama dan ganin tataunawar mai suke haka da yar aiken, da Fadimatul islam din, da kuma Oga AA din da suka shantake suka kasa fitowa har magariba ta kawo kai ( Jama'a ku mu taro Maman Mubasshir karta sume mana🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻😄😄😄😄😄😄?


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*






                          73



*Manzan Allah sallallahu alaihi wasallam ya ce wanda ya karanta subhanallahi wabi hamdihi subhanallahil azim,,, sau dari a rana za'a yafe masa zunubansa koda sun kai yawan kumfar kogi*





Yana karasowa ya tsareta da ido ya ce" Sahla mai kike à nan gidan da tsohon daren nan ? 




Sahla ta yatsina fuska ta ce" wajen Mom na Zo, 

Ta raba ta gefensa tayi shigewarta 


Idriss ya sauke ajiyar zuciya ya ce akoy ALLAH, 



Tana shiga ta ce" Mom Ina ta Kiran wayarsa tana ringin baya dagawa 



Daidai zata yi magana Mubasshir ya Kira ta, cikin rawar jiki ta daga ta kara à kunenta 


Mubasshir bisa umarnin elhaj Muhammad da ya tsare shi da ido ya ce" Wifey, kiyi hakuri Ina wajen aiki wata gagarumar kongila ce ta sameni daga wajen sarki,  so ki kular min da kanki, sannan ki tanadar min Abu mai dadi ki tsumayi tukuicin ki



Sahla da tayi Shiru tana sauraron zazakar muryar mijinta ta rausayar da kai ta ce" i miss u my man sai ka sauko 



Mubasshir yayi murmushin yake ya ce" miss u too wife, bye-bye, kit ya kashe Kiran ya dora kansa saman kujerar da yake zaune 



Elhaj Muhammad ya yunkura ya ce" Saki, Saki ?  No saki ba shine solution ba, ka tsunduma matar ka à tsananin kaunarka, idan har da rabon ta tsira da ita da mahaifiyarta to zasu daina mumunan nufin su, idan kuwa basu da rabo ne, To ka Sani ALLAH baya baci, shi ya san yanda zaiyi da su, 



Mubasshir ya Gyada kansa irin ya gamsu da bayanan mahaifin matar sa, 



Elhaj Muhammad ya ce" ka huta son bara na leko madame 



Mubasshir ya yi murrmushi, yanayin soyayar Sirikan nasa yana matukar birge shi, yana son yin koyi da su, à hankali ya lumshe Idannuwansa yana tuna moment dinsa da Islam, islam cikakiyar budurwa ce, yarinyar da tayi rayuwa à bola, gardawan maza suka sauketa, lale ya yarda Allahn nan shi ne mai karewa, domin ita Yar gatan ta shigo à bude ita kuwa Yar bolar ta shigo à rufe, à hankali ya furta da banbanci tsananin ku à zuciyata, Zanyi iya yini dan ki ringa jina à jinin jikin ki my Islam



Maman Mubasshir ce zaune tana Jiran Aunty Habiba ta gama hada ruwan dumin da zata kuma gasa Yar mahaukaciya, gefe guda su Hajiya Rafi'at ne zaune suna labarin tafiyar su, 



Maman Mubasshir ta juya ta kale su ta ce" na kula ba mai kama min y'a ta KO ? 



Hajiya Rafi'at da ta san ita ce da Laifi tayi saurin tasowa ta ce" Eyah maman islam ai na Zo na kama miki kika kiya kuna fushi kan dan Aljannah, 



Hajiya Fadimatu ta kawar da kai ta ce " lale fa dan Alhannah, Ai yau KO Aljani yake idan ya shigo sai na hadu da shi



aunty habiba ta fito ta ce" Aunty na hada aman kiyi hakuri mu yi mata aikin ni da Rafi'at 



Hajiya Fadimatu ta dago ta kan Yar mahaukaciya wace du tana Jin su, su basu san abinda ya sameta bane zasu ci gaba da sakata à ruwan tiraren nan ?  (Wa ya fada miki ?) 



Da sauri ta Mike tana kakawar da kanta ta ce" Mama zan iya fa, 

Ta juya tana kokarin yin sauri idannuwanta sai rufe su take tana cije lebenta, har ta shige bayin suka Mara mata baya



hajiya Fadimatu ta zauna Kusa da Hajiya hafsat ta ce " sister ya zakina nunawa y'ata halin KO in kula ne haka ?  Kin ga fa irin wahalar da ta sha na rashin ki aman sai Ina ga bakya Bata kulawar da ya dace da ita



hajiya hafsat ta zaro ido ta ce" Lah aunty, wace kulawa kuma zan baiwa islam wace ta fice Wada kike Bata ?  Kin tarbeta à lokacin da kowa yake hantarar ta, kin zauna da ita ba tare da kyama ba, kin sakata à hanyar samun ilimi, kin koyar da ita girki, kin koyar da ita tsaya, kin aurar da ita ga miji mafi daukaka à rayuwarta mai kuma zanyi mata ?  Aunty ki Sani wly wly islam kece mahaifiyarta domin ni haihuwarta kawai Nayi, har kunyarta nake ji a zuciyata, Ina Jin dacin irin rayuwar da na gana mata, 

Ta karashe zancen tana kokarin mayar da hawayenta




hajiya Fadimatu ta ce " karki ringa tuna baya, abinda kika aikata ba à cikin hankalinki ba kike yiwa nadama ?  Haba sister ai bai dace irin haka ba, na Sani sarai islam Ina bata kulawa aman ki Sani ya zama wajibi kema ki ringa sakata à jikinki domin ba komai zata iya fada min ba, KO daman can islam akoy zurfin ciki bale yanzu da yaron nan ya yi mana haka, kina gani fa irin saurin da ta kwasa du dan kar à gane baiwar ALLAH, Dan haka muna barar hakan



hajiya hafsat ta kawar da kanta tana murmushi à fili ta ce" korafinku ya karbu 







à gaskiya na san Ina jinkiri wajen posting, aman Ina neman afuwarku kun san yau da gobe sai ALLAH, abubuwan ne sai à slow, thanx à lot


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*






                          74




*Uwa Tana Iya Kula Da 'ya'ya Sama Da Goma Amma A Wasu Lokutan Sai Ka Tara 'ya'ya Goma Sun Kasa Kulawa Da Uwarsu Guda Daya!!! Yakamata Musan Cewa Abubuwa Masu Mahimmanci Da Daraja Basu Cika Maimaituwa A Rayuwar Mutum Ba... Shi Yasa Kowanne Mutun Uwa Daya Kacal Gareshi!!! 

Kuma Watarana Zamu Wayi Gari Babu Ita A Duniyar Nan... Dan ALLAH Mu Kara Kulawa Da Mahaifanmu Musamman Ma Uwa Wacce Babu Kamarta A Duniyan Nan!!!

Ya ALLAH Ka Bamu Ikon Yiwa Mahaifan Mu Biyayya Ka Jikan Iyayenmu, Ka Basu Aljannatul Firdausi, Allah Ya Sakawa Iyayenmu Da Mafificin Alkhairinsa Duniya Da Lahira*





bayan ta ajiye wayar ta shaidawa mahaifiyarta aiki ne ya rike shi ashe



Hajiya Marhaba ta ce" jibi ne tsinaniyar yarinyar zata tare KO ? 



Sahla ta ce"Eh mama



Hajiya Marhaba ta ce" toh duk yanda zanyi zanyi na kawo miki hadin maganin kinji ? 


Sahla ta amsa mata ta Mike tana fadin bara ta juya kar aje yayi safiyar dawowa gidan Bata nan



Hakan kuwa hajiya Marhaba ta barta cikin tsohon daren nan ta juya ta koma gidanta tare da dumbin muguwar hudubar mahaifiyarta




Tunda ya juya ya fita bai sake saka Islam à Idannuwansa ba, domin Hajiya Fadimatu ta kasa ta tsare ta hana shi hawa saman balatana ya ganta, duk irin yanda yake fakewa da Bara ya dauko wani abin sai ta tare shi ta ce lala ba zai hau ba, hakan na matukar mahalar da shi, 


Da kansa ya je gidan su Fati kawar islam ya shaida mata Auren islam aman ya boye mata mijin domin ya fi son ya zame mata surprise, auren kansa tayi mamakin sa domin Bata taba kawowa à ranta rashin zuwan islam school na kwana biyun nan haka ne ba, kuma ai suna waya Bata taba Shaida mata ba, Jin ya ce à washe gari zata tare ya sanya ta shirya da yama ta nufi gidan su AA Mubasshir, 




Konce take tana baci, wannan bacin ya zame mata tamkar na rashin Lafiya, ta fiya baci à yan kwanakin nan, 


Hajiya Hafsat ta shigo dakin ta Nemi gefen gadon ta zauna ta rasa ta Ina zata fara, à hankali ta saka Hannu tana dadaba bayanta 


Firgigit Yar mahaukaciya ta farka tana adu'ar tashi daga baci, idannuwanta ta sauke à fuskar mahaifiyarta, da sauri ta zauna tana kalonta



Hajiya hafsat ta kawar da kanta à ranta tace " wannan ido na mahaifinki ai sai mutun ya tsorata, à fili ta ce" ni islam bacin Lafiya kike ? 



Yar mahaukaciya ta ce " *Mahaukaciyata* da sauri ta rike baki ta gwalalo ido tana dan girgiza kai



Hajiya Hafsat ta jawota jikinta ta rungume ta tsam, kawai sai suka fashe da kuka irin mai tsananin nan, Wanda KO ranar da suka hadu basu yi shi ba,


Sai da suka yi mai isarsu sannan hajiya hafsat ta fara tsagaitawa tana shafa gashin kan Yar mahaukaciya, à hankali ta ce" sunan da kike kirana da shi ne à da KO ? 



Yar mahaukaciya ta dago kanta ta ce " Eh, sunan da yara suke fada miki ne, nima da na tashi sai nake kiranki da shi



hajiya Hafsat tayi murmushi tana share mata hawaye ta ce" shin Ina dukan ki à cikin hauka KO ? 



Yar mahaukaciya ta lumshe idannuwanta ta bude ta ce" duk da à cikin hauka kike à lokacin mama, idan zaki yi baci sai Kin jini à jikinki idan kuwa bana nan na tafi nemo mana abinci har na dawo kina zaune kina duba hanyata 



Hajiya Hafsat ta rintse idannuwanta ta ce " ki yafe min *Islam*



Da sauri Yar mahaukaciya ta ce " Mama, karki nemi gafarar abinda baki da laifi, ba abinda kika yi min, Dan ALLAH ki dena tinawa 



Hajiya hafsat tayi tsai tana kalonta, can ta ce " tell me, kina Son sa ? 



Yar mahaukaciya ta zaro ido tana kalon mamarta 



Hajiya hafsat ta ce " eh fada min, 


Yar mahaukaciya ta e" wane ? 



Hajiya hafsat ta girgiza kai tana murmushi ta ce" mijinki nake nuFi, kina son sa ? 



Yar mahaukaciya tayi saurin rufe idannuwanta gabanta na faduwa, tabas idan ta buda makaryacin bakinta ta furta cewar Bata son Dan Aljannah sai à nada mata sarauniyar makaryatan duniya baki daya, Dan haka gwara tayi shiru shine mafi aala à gareta, sai dai tana mugun Jin tsoronsa, tana Jin tsoron haduwarta da shi, sannan tabas idan abinda ya faru da ita da shi ne Aure ta san zata wahala, Karshe ma ta mace domin ta ji azabar da Bata san akoy irinta à nan gidan duniya ba



hajiya hafsat ta katse mata tunanin da ta afka ta ce" my islam, ki buda kunuwanki da kyau ki saurare ni, ki dago muyi zancen fahimta da ke à matsayina na wace tafi kowa sanin sirinki, shin kina son Mubasshir ??? 




Yar mahaukaciya ta dago kanta still idannuwanta à rufe kanta à Sade kasa cikin wani irin yanayi ta gyadawa mahaifiyarta kai tana nufin eh



hajiya hafsat ta ce " Alhamdulilah, kin san mai zan fada miki ?  Aljannarki zaki je nema, ki Sani islam akoy da babu mijinki shugabanki ne, Lafiya da rashinta kyautatawa à gare shi ya zame miki wajibi, da fara'a KO babu kokarin kwontar masa da hankali na rataye à wuyan ki, yi Nayi Bari na Bari islam, à yanzu yanda mijinki yake da iko à saman ki KO mu da muka haife ki Bamu da shi, ki Sani idan kin gyara auren ki kin gyara lahirarki, shi kuwa gyara aure shine biyaya ga mijinki, Islam baki da sama da mijinki duk abinda ya saka ki yi kiyi shi banda Wanda ya sabawa adinin musulunci, Tsafta, girki, tsaftar gidanki, komai ki rike da hanu bibiyu, tsananin ki da kishiyarki kyautatawa, *Islam,  Islam,  Islam* sai da ta kirayi sunan sau uku taci gaba *Islam* duk ranar da kika je gaban boka KO malan kika durkusa da bukatar kan mugun nufi ga abokiyar zaman ki KO à kawar da hankalin mijinku à kanta KO wani mugun nufi ni mahaifiyarki ban yafe miki ba, ki Sani babu wani makami KO kariyar da ta fi kiyi alwallah ki tsarkake kanki ki fadawa ubangijin ki, ke kece shaidar abinda ya faru à kanki kinga à yanzu Allahn nan shi dai ya ga bayan ta, sannan yaci gaba da kare ki, kiyi ta hakuri da zaman gidan miji domin yau da gobe sai ALLAH, 


haka mahaifiyar islam tayi ta Bata shawarwari kan rayuwar aurenta, da mahinmancin hakuri da barnar shirka, har lokacin jikonta yayi, da kanta ta karba ta jika islam tana kara koyar da ita yanda zata kula da kanta tun tana Jin kunya har ta sake sai dai tayi dariya KO ta rufe idannuwanta 



suna fitowa suka zauna tana caje mata kai Fati kawarta ta shigo da gudu tamkar karamar yarinya


rumgume juna suka yi suna ta murnar ganin juna, 


fati ta ce" kawata yanzu mamanki take fada min wata magana, Dan ALLAH yanzu AA ne mijinki ?  Daman ba yayanki bane kika ce yayanki ne ? 



Yar mahaukaciya ta ce" ke hajiya bakya zama sai tambayoyi ?  Kinga mamana nan tayi mata nuni da Hajiya hafsat dake murmushi tana kalon su



Fati ta ce" Lah kinga kuwa kuna kama wallah, ta duka ta ce" mama Ina yini



Hajiya hafsat ta amsa fuskarta cike da fara'a, Daidai nan Elhaj Muhammad ya shigo da salamarsa yana fadin jama'a Ina cigiyar My princesse nd my wife



Hajiya hafsat ta dago kanta ta ce" du sun bata


da sauri ya ce" ALLAH ya kiyaye, plz koda wasa kar ki kuma ambatar sunan Bata à gabana plz, koda wani abina ne ba'a gani ba ki ce" aban islam wannan abin ka sayi wani plz maman islam


Hajiya hafsat cikin murmushi ta ce" Aban islam kaga kawarta fa, 



sai à lokacin ya juya yana kalon su ya Mika hanu ya kamo islam Ya jawota yana gyara mata gashin kanta ya kali Fati da tayi sharan tana bukatar karin haske à sunan *Islam* da kuma wannan mutumin da farin su iri daya shi da *Rahma* harda kwayar idannuwansu, 









🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈🙈


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*






                          75



*Watarana manzon Allah S.A.W. ya gama ibada yana addu'a Yana cewa Allah ka yafema sayyada Aisha R. A. zunubbanta da wanda ta sani da wanda bata saniba Da wanda tayi yanzu da wanda zataiyi nan gaba duk Allah ka yafemata ashe sayyada Aisha tana ji sai taji wani irin dadi sai tace: Ya RASUULULLAHI (S.A.W.) na gode sai Manzon Allah yace wannan addu'ar dana yimaki. Itace nake yiwa AL 'UMMATA A kowace Sallah. Allah ya karawa ANNABI daraja tare da wasila da farila à aljanar firdausss*





Ganin kalon na fati ya saka shi yin dariya ya ce" i'm Muhammad, nine aban islam, yayi nuni da Yar mahaukaciya 



Fati ta ce" abanta fa ? Sis ???  Ta kali Yar mahaukaciya 



Islam tayi murmushi ta ce" yeah, ni ba marainiya bace, wannan shine abanna, sannan wannan momyna,  ni kuma sunana na gaskiya Fadimatul islam, 



Fati ta ce" waouh, kenan hakane, waouh sister inai miki murnar ganin iyayenki, yanzu maman AA ta fada min komai to du sai nake Jin zancen tamkar wani Sabon zance, 



Islam tayi murmushi ta kama hannun fati ta ce" haka Allah ya tsara, kinga Zo ki ga



Suka yi gaba, inda su Hajiya hafsat da mijinta suka ci gaba da tataunawa kan tarewar y'arsu kwaya daya da suka malaka à gidan duniya




Tunda garin ALLAH ya waye ake ta shige da fice a cikin gidan, masu gyaran dakin amarya na kanfanin Imran spécial aka dauko suke gyaran bangaran Islam, gado uku akayi mata kowani daki da nasa, kujerunta seti biyu na arabian da kalar na sarakai, adon ash da fari ne ake tsara dakin da shi, komai ya ji zanzan, 



Tunda yama tayi mahaifiyar Sahla ta Zo à sadade ta kawo mata maganin wajen bokan inda suka hada hadaden j'yaourt mai cike da na'a na'a sai kanshi yake ta dauko sabon caraf mai kyan gaske suka zuba dan madaidaici ta zuba maganin ta girgiza ta saka à firij Hajiya Marhaba ta juya bayan ta kara jadada mata ta tabatar ya sha fa, 





Bayan salar magarib gaba daya familyn na zaune inda na hango wani a

hasken yadi fari kar sai Sheki yake, sheshekar kuka na tashi sai muryar namiji na adu'a , Yar mahaukaciya ce tsugune à tsakiyar falon inda Hajiya hafsat, hajiya Fadimatu, hajiya hawau, hajiya Rafi'at, Aunty habiba, Sai Elhaj Muhammad dake adu'o'in neman tsari ga Y'arsa, wace zai sadata da gidan mijinta à wannan lokacin, 



sosai sukai mata nasiha, suka kuma nuna mata mahinmancin Hakuri da kuma ilar rashinsa, 



Kuka suke su uku à bayane wato *Fadimatul islam, Fati, da kuma hajiya Rafi'at* su kuwa iyayen suna share hawayen su, 



Makota da abokan arziki suka fara cicika motoci inda mahaifin Islam ya murje Idannuwansa ya dauko sabuwar motarsa ya kama hannun y'arsa tana kuka ya nufi mota da ita akayi amaryar koko da Fati kawarta, 






Su suka fara isowa inda Elhaj Muhammad ya damka mata alkur'ani mai Girma ya kama hannunta ta shiga Gidanta da adu'a à bakinta, 


Sai da ya sadata da dakinta ya kuma yi mata gargadin karta yi sake da adu'a sannan ya juya ya baro gidan zuciyarsa cike da raunin kukan Islam




duk irin azarbabin masu rakiyar amarya Hajiya Rafi'at ta kasa ta tsare ta hana kowa shiga bangaren islam, haka kowa ya hakura ya juya da santin falonta da sauran dakunan da suka leka,  aka bar islam da fati da hajiya Rafi'at kanwar mamarta 






konce yake saman makeken bed din dakinsa yayi rigingine Idannuwansa a lumshe, yana matukar mamakin irin yanda zuciyarsa ke azalzalarsa da ya je wajen islam tun kafin yan rakiyarta su juya, yana mamakin dokin da yake, cijewa yake tun karfinsa 



Cikin takun yanga take takowa cikin dakin takalman kafarta na fitar da sauti kwos kwos kwos, uwargida kenan wato Sahla sai zuba kanshi take ta sha make up din yaudara, 



Tafiyar tsutsa ta shiga yi masa tun daga wuyansa har kirjinsa, sosai sakonta ya fara caza shi domin daman à dane yake, 



Idannuwansa ya buda ya sauke su à fuskar Sahla gabansa ya fadi, domin à lokacin mumunan aikin da ta shirya masa ya fado masa à ransa, 



Murmushi ta sakar masa sannan cikin yatsina ta ce " wani irin ango ne mai baci karfe takwos bayan an kawo masa amarya à dakinta ? 



Mubasshir ya tataro dukan kokarinsa dan ganin ya ja Sahla à sabon salon barikin da ta fido dan tunkuda shi à rami, 


Jawota yayi ya hade bakinsa da nata ya shiga tsotsa Idannuwansa à lumshe 


Gaba daya ya kashe mata jiki, ita kanta ta san à wannan fanin ita din ba kowa bace wajen AA, 


Hudubar mahaifiyarta ta fado mata à ranta, hakan yasa ta zare bakinta da sauri tana fadin" Ya Salam, huby plz tashi na raka ka bangaren matar ka bana son ka shiga hakinta KO kadan 



Mubasshir ya kuma jawota ya ce" mai yasa zaki katse min rabar jikinki ne ? I need u, plz matso gareni 



Sahla ta Mike da sauri tana fadin kai Hiby baza'ayi haka da ni ba, so plz bara na kawo mata dan yaourt din na tarban amarya da na Adana maka rabonka ka sha ka Isa ga amarya domin yau darenta ne, 


Tana gama fadar haka ta juya da murmushin yaudara à fuskarta



Mubasshir ya rintse Idannuwansa ya ce "tabas yau daren amaryana ne, sai dai kin cuce ni Sahla 


Bata dauki wani lokaci ba sai gata dauke da caraf din da kuma kofi kwaya daya


tana zuwa ta cika kofin ta zauna ta mika masa tana fadin" oya daga bakinka na baka ka koshi mu tafi na raka ka



mubasshir ya sakar mata murmushi ya daga bakinsa yayi bismillah ya rufe Idannuwansa ya ya................................😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳



🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*





                    76



*Ya UBANGIJI ALLAH ka karbi tubanmu,Ka wanke zunubanmu,ka amsa addu'o inmu,ka tabbatar da hujjojinmu,Ka shiryar da zukatanmu,Ka tsayar da harshenmu akan gaskiya,kuma Ka cire duk wani mugun tunani daga zukatanmu.Mun sani, kuma munyi imani, shiriya, kariya da rahama duka naKa ne.Ya Allah,Ka samu acikin inuwarka alokacin da babu wata Inuwa sai taKa, Ya Allah Amin,summa Amin*













    Rintse Idannuwansa yayi tare da yin bismillah ya fara shan yaourt din da Sahla ta kawo masa yana tunanin yanzu koda gubar ce haka zata didika masa ya sha, 


Har ya kusan shanyewa sai ya gumtse à bakinsa ya tare da hannunsa ya cire kofin ya jawota jikinsa ya hade bakinsa tamkar zaiyi kissing dinta 


Idannuwanta ta zaro Jin ya zuba mata yaourt din da nufin itama ta sha, 

Da sauri ta janye kanta tayi bayi da gudu tana kokarin amai domin har ta hadiye wani, 


Murmushi ya saki ya Mike a nitse ya bi bayanta ya jingina kansa da jikin bayin sai da ta gama amanta sannan ta juyo, 


Gabanta ne ya fadi ganninsa à tsaye yana kalonta 


Mubasshir yayi yannayin damuwa ya ce" Sahla Lafiya ?  Kyankyamina ne kike ? 



Da sauri Sahla ta zaro ido ta ce" kyankyaminka fa ?  No wly KO daya



Mubasshir ya tsareta da ido ya ce" to ya akayi kike kakari haka ?  KO dai kin hadiye wani Abu à ciki ne ?  KO da wani abin à ciki ? 



Sahla ta kuma zaro idannuwanta tamkar mujiya ta ce" wani irin da wani abin à ciki ?  Kana nufin zan saka maka wani Abu da zai cutar da kai ne ? ( abinka da marar gaskiya) 



Mubasshir ya yatsina fuska ya matso kusanta, sai da ta dan ja da baya domin duk ta tsargu da kanta, hakan ya sa ya wayance ya kamota gaban miror din bayin ya dora kansa saman wuyanta da wata murya ciki ciki yana shafa mararta ya ce" relax, relax, nifa du ba can nayi va, Ina dai mamakin yanda à Yau kike guduna,  Ina mamakin daga na zuba miki abin bakina Kin zabura Kin tofar, dole tsoro ya shige ni kar aje KO kin rage sona ne, KO kuwa bakina yake wari ban Sani ba ? 




Sahla da wata irin kasala ta gama rufeta har lumshe idannuwanta take ta ce" bana son shiga hakin Yar uwata ne,  husband ita ce da kai, bana son ka tashi da shanyayen jiki gobe kiyama



Mubasshir ya lumshe Idannuwansa yana sauraron tatsuniyar munafukar matarsa, à hankali ya ce" are u prégnant ? 



Da sauri ta bude idannuwanta domin tamkar ya buga mata guduma ne, Yau du wani iri take ganinsa tamkar ya san abinda ta aikata sai faman kawo mata sirin da daga ita sai mahaifiyarta suka Sani, cikin wani irin yanayi ta janye jikinta sannan ta kakaro murmushi ta ce" bafa zan biye maka ba, mu shiga hakin baiwar ALLAH, dan haka mu tafi Nayi maka rakiya kar lokaci ya kure



Mubasshir shima ya mayar mata da murmushin ya ce" ban taba gani KO Jin labarin matar da aka yiwa kishiya take zumudin raka mijinta dakin amaryar tamkar Wanda take fatan ta rabu da su ?   My baby kiyi kokari ki samo cikin bebyna Nayi miki alkawarin gaba daya dukiyata da na malaka ta nan Lagos da sunan ki, kafin yarona ya Zo sai na dawo da dukiyata ta makah nan



Sahla ta zaro ido ta ce" Da gaske ??  Sai kuma ta wayance ta ce" ai yanzu ni bazan yarda ayi haka ba Tunda mu biyu ne, dan haka muje Nayi maka rakiya, sannan Ina son raka angona ne dan na samu rabauta sannan na kafa tarihi




Mubasshir yayi murmushin yake ya taba kuncinta ya ce" Tabas kin kafa tarihi, sannan ya shige Sahla na biye da shi tana ta yauki 




suna shiga bangeren Yar mahaukaciya sai da gaban Sahla ya fadi, domin fadin tsaruwar falon ma Bata baki ne, 


Mubasshir ya mika hannunsa ya kamo na Sahla domin sai wani dari dari take, haka suka ratsa falon na farko suka nufi dakunnan, daki na uku ne nata ya saka hannunsa à hankali ya bude kofar 



abin mamaki maimakun su tardo amarya à lulube cikin rufa na amare, à tare suka wangame baki Wanda ya saka nima na waiga wayan nawa ya kufce ya fadi kasa da sauri na rarumo wayar don na dauko muku dalilin firgitarmu



Fadimatul Islam ce tsaye tana dadage tana faman sai ta dauko wani Abu à saman werdrob dinta  , ta sha damamen bakin wando sidik mai santsi sai daukar ido yake, da Riga mai kamar jikin mage gashishikan jikin rigar sai kyali suke, gashin kanta à sake yake har gadan bayanta sai kyali yake ya sha gyaran Amare, du burar da zata yi sai mazaunanta sun motsa tamkar an cika balanbalan da ruwa ana girgizawa, haka na shanunta idan ta bura dai sunyi sama domin ba abinda ta saka daga ciki, ai tana Jin sun shigo din nan bisa hudubar auntynta wato Hajiya Rafi'at tayi wata irin juyowa ta nufo su tana buga kafa aman abin mamakin tamkar Bata ga da Sahla à wajen ba, 


tana isowa ta shiga dire kafafuwanta tamkar Yar baby karama tana juya idannuwanta nan nata tamkar na mage tana dan kikifta su haka sai yarfe hanu guda take ta mika hannunta ta kamo hannun Mubasshir da ya zama tamkar gunki nunfashi kawai yake fitarwa aman komai na jikinsa ya tsaya ya daina anfani, kalonta yake kwakwaluwarsa ta tafi caji domin Tunda yake da ita bai taba ganinta da shigar kakanan kaya ba, KO ranar da ya bareta à Léa a duhu komai ya wakana , du ganin da zai yi mata da doguwar rigarta KO zani da atamfa aman koda atamfa bai taba ganinta ba, 



Yan hannunsa da Yar mahaukaciya tayi ne ya fargar da shi cikin shagwaba ta ce"nurulkalbi plz kazo ka dauko min CD na Gaza daukowa, yayi min nisa gashi Ina son Nayi kalo 




Sahla dake tsaye Bata san sanda ta ce" tap, tun karfinta ba



à tare suka juyo suka kaleta,  Islam ta ce" Lah auntyna yaushe kika shigo ?  Kinga Ina ta my one ban lura da ke ba i'm SO sorry yayi mantuwar tasa ne kafin ya fito KO ??? 




Sahla ji tayi uwa ta make bakin Yar mahaukaciya dan Haushi , ita zata nunawa bariki ?  Aman zata fada,  ta danyi murmushi ta ce" ikon ALLAH,  amaryar nan anya kuwa ?  Kai kanwata ba KO irin kukan za'a rabu da su mama din nan du da ba'a jima da haduwa da su ba,  ba'a wani shaku ba, aman ai amarya koda zawara ce ranar tarewarta ya dace à bude mata lulubinta ba ta bude ba




Yar mahaukaciya tayi dariya harda dan rike cikinta ta ce" Lah yanzu aunty à tinaninki yaune tarewar ? Ai an dade da sanin wannan hanyar yauma Nayi niyar na dawo kusa da mijina ne dan na ringa dama masa dakan hanu na fura cike da ada'ar soyaya 



Sahla ta juya da sauri ta kali AA dake tsaye yana kalon ikon ALLAH, irin yanda islam ke mayar da du bakar maganar da Sahla ta yaba mata, maganganun da take Ramawa haussa ne cikin haussa,  Sahla ta ce cikin bacin rai" Daman ka dade da tarawa da ita ?  Toh à matsayin matarka KO dadiro ? 



Yar mahaukaciya ta ce " matarsa ai dadiron sa ce, sai dai mata suna suka tara sanan akoy dadiron mijinta bayan Aure kuma akoy dadiro kafin Aure da kuma bayan Aure,   ta juya wajen wata akwati Karama mai shegen kyau ta ce" Aunty kinga kyautar budurcina Wanda yayi min ni tawa kirar Dubaï ce harda dan gwal à ciki,  taki ma irin haka ya baki ???????? 




Sahla tayi tsit ta kasa Bata amsa kawai sai ta juya da gudu ta fita daga dakin inda suka rakata da ido,  Islam ta dan saki murmushi ta juya tana kokarin saka Baban hijabinta dan ta kwonta baci




AA  yayi tsam yana kalonta ya juyo yana tambayar kansa mai kenan ?  Mai hakan ke nufi ?  Wai shin duka wannan abin da Islam tayi wasan kwakwayo ne ????????? No  bazai yiwu ba ba zai yiwu ba









zai yiwu kai AA 😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄😄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*







                          77





*Manzan Allah tsira da amincin Allah su kara tabbata agareshi yace: duk wanda yai min salati a rana sau dubu {1000} to bazai mutu ba har sai nai masa bishara da Aljanna. Wanda ya yada wannan hadisin to hakika yana sona, wanda kuma ya boye to hakika yayi nadama*









Kalonta yake cike da al'ajabinta, wai daman tana magana haka ? Toh Wa ya koya mata irin hakan ?  Au yanzu fa wuta ce ta kuna masa KO ? Yayi murmushi ya zauna bakin bed din yana kalon yanda take kiriniyar daure gashin kanta 


À hankali ya ce " baki ci nasara ba, domin fushin bai dameni ba



Yar mahaukaciya ta waigo ta dan kale shi ta juya ta ci gaba da shirin bacinta, 


Shima kyaletan yayi yana nan zaune har ta gama ta juyo tana kalonsa, domin à saman bed din yake ya tankwashe kafafuwansa 



Juyawa tayi tana kalon tsakar dakin nata sai lalausan kafet à shinfide, ta nufe shi da niyar konci



Mubasshir ya ce" Islam


Cak ta tsaya Bata waigo ba, ya lumshe Idannuwansa ya ce "ki dawo saman bed dinki ni zan kwana à kasan, yana gama fadar haka ya buda jerin kayansa da aka zuba à dakinta ya dauko tawol ya nufi bayi 


Yana shiga ta juya harda dan gudunta ta haye bed dinta ta ja lalausan bargonta ta rufa ta tofe jikinta da ada'o'i ta lumshe idannuwanta sai barci 



Can cikin dare ta farka dan gyara konciyarta ta jita à jikin mutun, hakan ya matukar firgitata ta mika hanu à hankali ta kuna fitilar jikin bed din mai dan duhu 


Fuskar Mubasshir ta tsurawa ido da kontacen sajensa Idannuwansa a rufe sai bacinsa yake hankali konce, à nutse ta tsurawa kirjinsa ido yanda gashin ya konkonta alamun nutsuwa à tare da shi, 



"idan kin gama kalon ki kashe fitilar my islam, haka kawai kalo da tsakar daren nan ?  


Muryar Mubasshir ta tsinta Idannuwansa a rufen nan aman yana fadin haka, da sauri ta shiga zare ido tana kokarin tashi daga kirjinsa ta ce" ni, ni ba wani kalo da nake nini 



Kara jawota yayi sannan cikin muryar mai baci ya ce" shiiiiiiiiiit, Ina bukatar ki à jikina SO kiyi min hakurin hakan, ya kara rumgumeta da kyau à jikinsa



Luf tayi cike da kunya tana kara sine kanta à kirjin nasa nan da nan kuwa baci yayi awon gaba da su




Karan wayarsa ta tayar da su à tare ya mike à hankali ya lalubo wayar, sunan umina ya gani à jikin screen wato Hajiya Fadimatu cikin Bari ya daga ya kara à kunansa ya ce" Maman islam Lafiya ?  



Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" Dan Fadimatu Ina yarinyata ?  Hop lafiyarta lau ?  



Mubasshir yayi murmushi ya juya yana kalon Yar mahaukaciya da tayi tsuru cike da tsoron Jin ba'asin Kiran domin karfe biyar ma Bata cika ba, ya ce" ga yarinyarki zaune ta tankwashe kafa tana zare idon tsoron Jin kiranki à karfe Hudu maman Mubasshir, 



Hajiya Fadimatu ta kali hajiya hafsat dake ta murmushi ta ce" bani yarinyata kaji ko



Mubasshir ya mikawa Yar mahaukaciya wayar sannan ya tsareta da ido, 


Tana amsa tayi salama 


Hajiya Fadimatu ta ce " my Daughter lafiyanki lau ?  Ba abinda yayi miki ? 



Islam kunya ta cika ta, kawai sai ta kasa magana ta shiga sisine kai, ganin haka ya karbi wayar ya ce" Maman Mubasshir ki kontar da hankalinki plz, y'arki tana cikin koshin Lafiya, kunya ta hanata baki amsa, 



Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" na kasa baci ne, du da Elhaj Muhammad ya fada min yanda kuka yi, aman sai nake jina bana tare da nutsuwata, plz karka cutar min da yarinya 



Mubasshir ya ce" Maman Mubasshir kin san wani Abu ? 



Hajiya Fadimatu ta ce " aa 


ya ce" Maman Mubasshir Ina tsananin son Y'arki, 



Hajiya Fadimatu ta zaro ido, hajiya hafsat ma ta zaro ido ai ba shiri ta datse Kiran, Hajiya hafsat kuwa ta bushe da dariya domin yanda hajiya Fadimatu take dan zazaro ido abin à daran ne, hajiya hafsat ta ce " aunty plz ki konta ki huta ni kam kinga Nayi nan, ta shige bargo tana ta dariyar Mubasshir da islam da mamansu 



Mubasshir ya saki murmushi Jin ta datse Kiran, ya juya ya kali islam yanda ta dukunkune à cikin bargo ya san kunyar abinda ya fada ne ya saka tayi hakan, ya matso à hankali yayi mata kis à kuncinta sanan ya ce" kinsan mamanki tana tsoron kar à maimaita abinda ya faru ne kar à jima yarta ciwo



Yar mahaukaciya ta zaro ido ta kara matsowa can karshen bed din à ranta tana tunanin daman haka yake Sam kunya Bata ishe shi ba, 



Ya Mike yana murmushi ya nufi bayi ya dauro alwallah ya shiga nafilfili 



Karfe takwas na safe wayar hajiya Marhaba ta tayar da Sahla daga baci, 



Hajiya Marhaba ta ce " baby Ki tashi haka mana da barcin nan naki kiyi ki leka ki ga yanda suke ciki




Sahla ta diro daga bed dinta ta ce" bara na wanke idannuwana na leka kinga abin nan na jiya ya kona min rai zinariyar nan ba karamin kudi aka kashe mata ba, abinda ni bai ban ba ita ya Bata, aman su suka ja ma kansu, nasan yanzu ta dade da mutuwa Bara na hanzarta na kwashe su zinariyar kafin yan sanda su zo





Hajiya Marhaba ta ce " yawa Yar Gari maza hanzarta




Sahla idannuwanta kadai ta wanke ba KO tunanin Wanka KO alwallah dan rama sallar asuba haka ta hanzarta wanke fuskarta ta bude bangarenta ta nufi na Yar mahaukaciya har tana harde kafafuwa wajen sauri



tana isowa Bata yi tunanin yin salama ko wani abin ba kawai ta tura kofar Baban falon ta shige 


Gabanta ne yayi mugun faduwa inda kafafuwanta suka Gaza daukarta ta zube nan tana kare musu kalo su Mubasshir da islam sun sha wata farar Shadda bugagiya ta sha aiki kala daya, saï Aunty Rafi'at da fati suna zaune saman table suna cin abinci sai anuri ke fita daga fuskarsu



wani ihu ta saki ta ce..............................,,,,,,,,,,,,,.............


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*







                          78



*Yaya Hayat Admin na hayat haussa novel, haussa novel nd fashion cool novel..... Patati nd patata sako zuwa gareka, kayiwa girman ALLAH ka barmin novel dina yanda ka ganshi cos nawa ne ba naka ba, haba taya zakana hada document da novel dina da numbobin wayarka da sunayen Grup dinka kuma ba tare da izinina ba ?  Ka manta y'ar mutan Niger da na nemi alfarmar ka saka ni à grup Ina bin novel din auntyna matan Ali ka bukaci kudin shiga ni da nake Niger Ina zan ga naira hakan yasa kaki sakani sai yanzu zaka yi anfani da naya novel din ?  Kai walahi idan ka kuma anfani da novel dina dan kayi document da shi ban yafe ba ka barshi yanda yake idan na gama abina zan hada abina à document na gode*


Wani ihu ta saki da ya saka suka Mike a tatare, da hanayenta ta daga tana nuna su tana kokarin yin magana da gudu ta Mike ta fice ta nufi dakinta tana zuwa ta danna Kiran mahaifiyarta, 


Hajiya Marhaba na daga wayar Sahla ta rushe da matsanancin kuka



Hajiya Marhaba ta ce " ke pretending kike KO kukan gaske ne ? 



Sahla ta ce "mama lafiyansu lau, suna zaune suna karyawa cikin annuri, KO dan ta saba da shine ya sa Bata gaji da shi ba, ya sa bai halakata ba, mama mai yake faruwa da ni ne ?  Daga wannan sai wannan, KO duba fa ki gani tun kafin ta tare yake like mata kenan yafi sonta da ni KO ? 




Hajiya Marhaba cikin tashin hankali ta ce" wani irin mutun ne kika aura Sahla ?  Shi asiri baya cinsa ne ? Bara Nayi Kiran tsinanan bokan nan Naci kutumar..... Don kuwa bazai yiwu na barshi ya cinye min kudi kuma aiki bai ci ba, KO kontar da hankalinki kiyi musu basaja tamkar ta kirki, ni na fisu zama hatsabibiya,  zasu ga abin mamaki, da ni suke zancen



Sahla ta saki ajiyar zuciya ta ce" à da Ina tunanin sasauta masa aman à yanzu na tsane shi mama, dalili kontawa da yayi da wannan yarinyar har ta kare min kalo ta gwada min abinda ya siya mata, 



Hajiya Marhaba ta ce "barni da su, Tunda kika gane hakan ai da kyau



Suna katse wayar hajiya Marhaba cikin bacin rai ta danawa bokanta kira


Cikin magagin baci na mutumin da bai tashi ba har karfe tara boka ya daga wayar hajiya Marhaba, 


Rufe shi tayi da fada tana fadin ita zaya yaudara aikinta yaki ci


Wata uwar ashar ya dura mata sannan cikin yannayin mashaya ya ce" ke kika Bata aikinki Yar akuya, dan haka li jirayi sakamakonki na zagin aljannu da kika yi,  dif ya kashe Kiran 


Hajiya Marhaba ta bi wayar da kalo ta Mike tayi Kiran kawarta azumi, 

Tana dagawa ta shiga zayane mata abinda ya faru, ta dora da fadin" kinga kuwa shine yayi min aikin Elhaj na daga bayan nan da ya fara warwarewa, yanzu haka yanzu zanyi Kiran uwar tasa Ina kuka idan ta taho ta tsalako shikenan hauka har kabarinta, sai sauran tsinanun, To aman na fara kokonto 



 Ji tayi an warce wayar daga hannunta ta dago da kanta da sauri idannuwanta suka sauka à fuskar mijinta da lokaci daya kamaninsa na tsare gida tun suna samartaka ya dawo masa, daga bakin kofa kuwa Baban danta ne ya dora hannu biyu à kai yana rusa wani matsanancin kuka, fitowa yayi ya jawo dansa suka zauna suna Jiran isowar su Sahla domin su hajiya Fadimatu har sun karaso inda yayi Kiran Mubasshir ya bashi umarnin KO à daure ne ya kawo Sahla wace ya yana shiga ya tsorata ta ta hanyar fadin mamarta ba Lafiya 


Ai da Gudu ta fito suka kama hanyar gidan mahaifinta gaba dayansu banda fati 



Suna karasawa ta fita da gudu tayi falon umanta, tana zuwa ta tarar da jama'a à falon inda suka taru kowa yayi jigum, shi kuwa Idriss sai rusar kuka yake 


Ihu ta saki ta dora hannayenta biyu à kanta ta nufi Idriss tana tambayar ta mutu ne ? Mai ya sameta ? Wani ne ya kashe min uwa ? Ina maman a..... 


Dim kake ji ta hadiye sauran maganar à bakinta, sanadiyar wani wawan mari da abanta ya zabga mata, kafin ta dago ta kali mai marin nan nata ya kwasheta ji kake kush karar faduwarta à kasa, kafin ta gama dandace abinda ke faruwa da ita ya bita kasa ya shiga nausarta



da gudu suka ririke shi suna fadin haba Elhaj, idan rai ya baci ai hankali baya gushewa, 


Sahla dake zubar da jini ta goshinta ta kasa daga hanunta da alama ya karye fuskarta kuwa har ta canza kala, ta ja jiki ta rike kafar Idriss tama kasa kukan du irin azabar dake tsigarta, idannuwanta ta dago har jini ya dan konta ta zuba masa su ta ce" mai ke faruwa Yaya Idriss ? 



Idriss shima ido cikin ido ya ce" Sahla asirinku ne ya tonu, 



Sahla ta zaro ido ta ce" wani asirin mu ?  Ni da Wa ? 



Idriss ya ce" asirinku na shirin ku na halaka rayuwar bayin ALLAH da suka yi muku rana dan ku malake abinda ba naku ba, ke harta asirin da mama ke yiwa dady na ta juya shi yanda ta ga dama ya karye Sahla, yanzu haka ta bine wani à kofar dakin dad Bata tsoron yayi dawowar bazata dan kawai ta tsoratar da Hajiya (hawau)  cewar dad ya mutu yana dakinsa idan ta tsalaka ta haukace à cewar bokanku, Allah ya taimaka muna shigowa dakinta muka nufa dad cike da mamakin za'ayiwa mama sherin bin bokaye sai gashi yaga haza domin shaida ta kirarin mutun da kansa KO ta Zina ta shaidu,



Sahla zuwa wannan lokacin ta gama tsurewa,  tsoro da fargaba da tashin hankali da kunya suka mugun lulubeta, cikin nauyin harshe ta ce"  Wa ya fada muku ? 



Abanta cikin wata irin murya mai cike da kunci ya ce" Wanda ya boye mana dan ya kare mu, Wanda ya zuba muku ido dan yaga imanin ku, Wanda à cikin ruwan sanyi ya dago ku à fili *ALLAH* kenan, Wanda baya baci, 



Sahla ta waigo ta zubawa fuskar Mubasshir ido a ranta tana tunanin ashe ya ji komai shi yasa yayi tayi mata tambayoyin nan ? 



Idriss ya Mike ya nufi kofar dakin mahaifiyarsa ya bude dakin, tana jingine da kofar tana sauraron komai, ta dora hannunta à kai tana tunanin yanda aka yi hakan ta faru ai kuwa Bara ta kirayi boka ta fada masa ta bashi hakuri ya kuma shirya mata wani sihirin ( oh wai Kin manta rana dubu ta barawo, rana daya ta mai kaya ?) 


Budewar da yayi tana tsaye, ya zuba mata ido itama shi take kalo, ai kuwa ta shiga zaro ido hango mutanen falon, ta fito tana inda inda ta ce" aa fa, aa fa, wannan duka karya ne, ni ban aikata ba, aban Sahla karka yarda à hadani da kai, kai kasan à yanda

Nake kula da hajiya bazan iya cutar da ita ba, kai kafi kowa sanin hakan KO ? Ta juya wajen Idriss ta ce" Docter kaima ai shaida ne matso nan ka furta mahaifiyarka ba abinda tayi kowa ya tashi ya fice gidansa, 



Sahla ta ce" mama. 


Hajiya Marhaba ta juyo gabanta ne yayi wani irin faduwa, fuskar Sahla ta Haye tayi sindim, jini ya shigar mata ido ga hannunta ta kasa daga shi


Hajiya Marhaba ta ce " ubanwa ya taba lafiyar jikinki ? Fada min ubanwa ya dake ki ? 



Mahaifin Sahla ya ce" ni ne, ni na daki y'ar da nake tir da...... Da sauri Elhaj Muhammad ya ce" kul na haneka da yin mumunan furuci Wa y'arka, SO kake ta shiryu KO ta baude ?  Rashin tunani dana sani, kaucewa hanya ya tabata ga iyayen da zasu aibata y'ayansu dan sun kaucewa hanya, To mai zaka yi kenan ? Mala'iku suna gagawar amsar adu'ar iyaye Wa y'ayansu da amin KO wace kala ce dan haka ka kiyaye kar danasani yayi yawa rayuwarka



Hajiya Marhaba ta karewa Elhaj Muhammad kalo cikin kunan rai ta ce" ai dole ka fadi haka, kai ka kilace taka sakaryar y'ar zaka yi mana bariki à nan, toh wly baka Isa ba



Mahaifin Idriss ya juya dan yiwa Idriss magana sai dai abin mamaki bai ganshi à inda yake tsaye ba


Kiriniyar bude dakinsa yake domin idan za'a bude dakinsa sai an sha fama da kofar


Da sauri suka nufe shi aman kafin su Isa har ya bude kofar da gudu hajiya Marhaba ta rike shi aman da yake karfin ba daya ba zai kufce mata Mubasshir ya damko shi, kokowa suka shiga suna kokarin turo shi, garin ta tura shi karya shiga dakin da ta bine abinda zata haukata  hajiya hawau da shi, ita kafafuwanta suka shiga, abin ikon ALLAH kawai sai ji suka yi ta kwashe da wata muguwar dariya



À tare suka furta inalilahi Wa'ina ilaihi raj'une, hanayensu à saman kansu 


Mubasshir ya saki Idriss Wanda ya juyo jiri na kwasarsa ya zube à nan sumame 



Ita kuwa sai dariya take babakawa, haukan dariya hauka mai wuyar warkewa, haka suka yi jigum jigum inda suna waigowa itama Sahla ta suma ( to fa wanzam baka SO à jikinka) 



To fans tambayana à nan shin Sahla zata ci gaba da zama à matsayin matar AA ?  Haukan hajiya Marhaba ya dace da ita duba da irin abinda ta aikata ?  Bawan ALLAH Idriss ya tasa makomar ba masoyiya mahaifiya ta haukace, kanwa ta kauce hanya ?  Shin labarin Yar mahaukaciya na kayatar da ku ?  Cos ance wai banida masoya 😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩😩


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*







                          79



*Wayo dadi, daukaka abar gudu abar nema, ni kam na rasa bakin magana sai jazakumlah,*





da gudu ya nufe shi yana jijigashi, inda Yar mahaukaciya ta nufi Sahla saï kuka take dan kuwa ita abi kankani ke rikita mata lisafi, tana kuka ta dago kanta ta kale su zata yi magana kenan sai ga abanta ya shigo da gudu yace " ku kama su mu je asibiti



Mahaifin Idriss wato Ilyas ya dago da kansa ya ce" baza'a kaita asibiti ba, sannan ba zan bisu asibiti à yanzu ba, kawai zan rufeta à daki ne naje wajen tawa mahaifiyar, 



Elhaj Muhammad ya zuba masa ido ya SO ya takura sa sai dai yayi wani tunanin kawai ya kamawa Mubasshir suka dauki Idriss suka shiga motar da shi, 


Elhaj Muhammad ya kali Mubasshir ya ce" kaje ka dauko matar ka domin kaine muharaminta



Mubasshir ya dago Idannuwansa cike da hawaye ya ce" ka yafe min aba, na saki Sahla saki daya



Elhaj Muhammad ya zaro ido ya ce" why Mubasshir  zaka yanke danyan hukunci haka saki cikin fushi ? 



Mubasshir ya kawar da kansa ya ce" banyi saki cikin fushi ba, na gama nazarina kafin Nayi sakin nan domin da à lokacin da nake walafawa Sahla soyayata gareta ta canza tunani Bata bani yaourt din nan ba da lale lale bazan saketa ba, aman à cikin zuciyar Sahla kiyayata tafi soyayata yawa dan haka ka yafe min, 



Elhaj Muhammad ya rasa ma mai zai ce masa kawai sai ya kada kai ya koma dakin inda ya tarda Elhaj Inyass ya fitar da du abinda ya san zata iya raunata kanta ya rufeta à dakin sai falasa irin aika aikar da tayi take tana busasa dariya, 

Elhaj Muhammad yayi gagawar kawar da kansa dan kuwa sai yaji ba dadi, 


Su hajiya Rafi'at da hajiya hafsat suka kama suka dauko Sahla wace kitsonta na atch sai yawo yake tsananin tsayinsa a kanta, 


Suna sakata irin motar nan ce jeka da iyalinka, lxus suma suka shiga Mubasshir ya tayar ya kama hanyar asibitin idriss


Suna zuwa da gudu aka karbesu BQ tare da tambayoyin abinda ya faru ba suka dukufa domin ceto ransu, 



Zaune suke Yar mahaukaciya ta dora kanta saman cinyar auntynta tana ta sauke ajiyar zuciya, itama Rafi'at din du tayi wani iri da ita sai tunani take na rayuwa, 


Hajiya hafsat ta kasa zama sai kai kawo take tana dan leka hanyar dakin da aka shiga da su,  kuma sai ta kali AA da yayi wani irin ja na Wahala, kansa à kasa yana kalon yatsun kafarsa, 


Elhaj Muhammad ya zuba mata ido yana kalonta, wani irin tausayinta da kaunarta suka kara darsun masa à zuciyarsa, ya kuma kali y'arsa dake konce q cinyar Rafi'at, ya juya ga Mubasshir dake kalon kasa, ya girgiza kai à hankali ya Mike ya kamo hannun hajiya hafsat, har yanzu abin nan bai barta ba na idan hankalinta ya tashi ta kasa zama, yayi murmushi ya jawota jikinsa ya Bata kyakyawar runguma, hakan ya saba yi mata idan har yana son ta shiga cikin nutsuwarta, hakan kuwa aka yi sai ta dora kanta à kirjinsa tana sauke ajiyar zuciya, tana karawa, 


Ta kusan minti biyu à haka ta tuna su Mubasshir fa na wajen da sauri ta kufce daga rikon da yayi mata tana kara jan zumbulelen hijabinta tana kokarin rufe fuskarta, 


Mubasshir ya kawar da kansa yana girmama soyayar sirikansa 



Docter Halima ce ta fito ta nufo su 


da sauri suka Mike har suna hada baki wajen tambayar ya jikin su, 

Mubasshir ya kali Yar mahaukaciya da ta ce" ya jikinsa ? Gabansa ya fadi, Muryar docter ta dawo da su inda ta ce" alhamdulilah jikinsu da sauki cikin ikon ALLAH, 


An daidaita lunfashinsu, shi an saka masa ruwa aman munyi masa alurar baci wace tana iya daukan awa uku zuwa Hudu yana baci dan ya samu hutu, sai ita an dora hannun, aman tana bukatar kulawa KO ku dauki nurses masu kula da wannan harkar KO ku dauko Wanda zata tsaya tsayin daka dan lafiyarta ta samu cikin sauki da yardar ALLAH 



Mubasshir ya ce" docter muna iya shiga mu ganshi KO ? 



docter ta ce" eh sosai ma, kuna iya zama ma ai docter ne, ba wata damuwa, 


Elhaj Muhammad ya girgiza kai Jin bai damu da rashin Lafiyar sahlan ba, ya ce" docter Ina bukatar à daukarwa kanwar Idriss nurses uku da mai kula da tsaftarta, da mai kula da abincinta, da mai kula da addininta à kan lokaci, du wata kulawa Ina son à Bata kafin ta dan warware 


Docter ta ce" Elhaj akoy tsada fa


Elhaj Muhammad ya kaleta ya ce" ba wannan ba, aikinsu shine biyan bukatarmu



Mubasshir suka yi gaba su hudun suka nufi dakin Yar mahaukaciya kafin ya gama ya tarda su, 


suna shiga suka tarar yana konce hanunsa jone da karin ruwa, yana baci aman da ka kale shi sai ka ga ya fada, 


hajiya hafsat ta nufi gadon Sahla tayi mata ada'ar samun sauki, 


Elhaj Muhammad suka shigo da nurse aka ja gadon Sahla dan à canza mata daki domin jinyar namiji da mace bazai yiwu à daki daya ba



Elhaj Muhammad ya kare yi masa kalo ya ce" da ace inada wata y'ar da na Isa da ita da na aurawa Idriss bisa sharadin idan ta Bata masa ban yafe mata ba


hajiya hafsat itama ta zura masa idon ta ce" ya ALLAH yanda ka yaye mana damuwarmu bisa Imani da muka yi da kai ka yayewa wannan Bawa naka cikin ruwan sanyi sannan ka bashi ikon cinye jarabawar


gaba daya suka amsa da amin, Mubasshir dai na kalonsa kuma sai ya saci kalon Yar mahaukaciya da ta zuba masa idon itama ba tare da wani tunani ba sai tsantsar tausayawa gare shi balatana idan ta tuna Tata rayuwar da ta shude ba'a dade ba



Elhaj Muhammad suka yiwa su hajiya Rafi'at da Mubasshir da Yar mahaukaciya Salama suka nufi gidan su Idriss dan su tarda hajiya Fadimatu dake wajen hajiya hawau suna ta jajantawa da kuma murnar dawowar tunanin Elhaj ilyassssss



bayan tafiyarsu Mubasshir sai ya daina kalon Idriss din gaba daya sai ya dawo da tunaninsa wajen islam da tayi zuru ita da aunty Rafi'at suna ta kalon lumfashin Idriss, wani haushi da mugun kishi ya rufe shi, à ransa ya ce, Tunda ta zura masa ido Bata dauke ba, mai hakan ke nufi ? Tana tsoron ta kawar da kanta ne wani abin ya sami masoyinta ( toh fa eh din Inji ni ) 


Gani yayi bazai iya jure wannan abin ba, ya Mike yana dan sosa keya ya ce" auntyn mu plz mana bara mu samo muku dan abin matsa baki kafin ya farka 



hajiya Rafi'at ta kale shi ta ce" haba freind (domin shekarunsu daya abinka da yan gayu shima idan yana bukatar wata alfarmar ce yake kiranta da aunty)  ya zaku barni à nan ni kadai kuma ?  Idan ya farka fa ya Zanyi da shi ? 



Mubasshir ya ce " ai ba zamu jima ba


hajiya Rafi'at ta ce " toh ka je kai kadai mana



Mubasshir ya zaro ido ya ce" Ina bazai yiwu ba fa hajiya kinga tafiyar mu dan Ina dan yi miki Yar murya aa bye,  

Ya ja hannun Yar mahaukaciya wace tayi murmushi diramar auntynta da mijinta na birgeta matuka 



Bayan fitar su aikin nata da ta saba ta ci gaba wato kalon sa, Kiran salar da aka yi ne ya saka ta Mike ta cire hijabinta dan taga yana baci kuma zata shiga bayi, ta ajiye à saman kujerar da ta tashi ta nufi bayin 


alwallah ta dauro ta fito,  tana fitowa ya mayar da Idannuwansa ya rufe ta dauki hijabinta ta dora saman Riga da siket dinta ta jawo dardumar da docter ta Miko ta kabarta sallar la'asar, 


Bayan ta gama sallah tayi ta adu'o'inta da ta saba sannan ta daga hannunta sama cikin bayananiyar murya ta fara yiwa ALLAH kirari da shi da fiyayen halinta, ta nemawa iyayenta gafara da Wa'inda suka rigaye mu gidan gaskiya, ta kara nemawa y'ar uwarta kariyar ubangiji da ahalinta baki daya, ta roki gamawa da duniya Lafiya, sannan ta gangaro kan Idriss ta ce" Ya  ALLAH  alhamdulilah,  Allah mun gode maka da wannan rana ALLAH muna rokon ka ka sanya ta zamto alhairi à gare mu, ya ALLAH ga bawon ka nan, kafi kowa sanin dalilinka na ciro kamili daga tsatson Wanda ba kamili ba, ya ALLAH kafi kowa sanin abinda ya dace da wannan Bawa naka domin kai kadai ka san gaibu, ya ALLAH ka sanyaya masa damuwarsa, ka yaye masa kuncin sa, ka bashi ikon kula da mahaifiyarsa da kuma kanwarsa, ka bashi juriyar cinye wannan jarabawar, ka shiryar da kanwarsa, ka baiwa mahaifiyarsa Lafiya, kai kayi komai kai kake da komai ya ALLAH, 


*sai da ta gama yiwa kowa adu'a sannan ta fashe da kuka mai tsanani, ta kara daga hannunta sama ta ce" ya ALLAH ka kawo min abokin rayuwana koda da an daura min aure zan koma gareka, ya ALLAH idan wani abin na aikata KO nake aikatawa ka nusar da ni ka yafe min ka bani miji na gari komai talaucinsa, ya ALLAH idan kuwa lokacin Nayi auren ne baiyi ba ALLAH ka kara min hakurin jiran lokacin domin na san da mutuwa da arziki da Aure lokaci ne, ya ALLAH idan..... Ta kuma fashewa da wani kukan ta ci gaba idan kuwa banida raban yin auren ne har na koma gareka ka saka min dangana ka kuma kare ni da sharin Zina ka kara nutsa ni à kogin tsoronka ya ALLAH ka cika min burina amin*



bayan ta gama adu'ar ma sai da ta ci kukanta sannan ta Mike a nutse ta nade salayar ta juyo dan ta ajiyeta 


Gabanta ne yayi mumunar faduwa sanadiyar ido Hudu da suka yi , wato Tunda ta fashe da kuka ya zabura ya zauna yana kalon ta kuma yana sauraronta, 


wayancewa tayi tana dan murza ido kamar wani abin ya fada mata à ciki ta nufi dan kusa da gadon tana dan inda inda ta ce" """""""""""""







garigajin ganin ji ganjin kara Kaka kara 🙄🙄🙄🙄🙄🙄


🇳🇪Belles écrivaines du Niger


*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*


*Na*

             *Sajida*


                          80


Tana murza ido ta ce" au ka farka ?  Yaushe ka farka ?  Ya jikin ? 


Shiru Taji yayi bai ce komai ba hakan yasa ta dago da kanta suka yi ido Hudu, gabanta ne taji ya yanke ya fadi ta shiga kikifta ido


Idriss dake kalonta yana kokontan anya kuwa shekarun da aka ce ta kai kuwa ?  Kamar wata Yar budurwa mai shekara 25 haka, ya lumshe Idannuwansa ya ce" shekarunki nawa ? 


Hajiya Rafi'at ta dago kanta ta zuba masa ido tana mamakin tambayar sa, yaro karami da shi yana tambayar shekarunta ita tayi imanin ta bashi wata shekara biyu KO uku, ta kawar da kanta ta ce" ban gane shekaruna ba ? 


Zaiyi magana kenan Mubasshir ya turo kofar ya shigo da ledodi manya bakake à hannunsa, Yar mahaukaciya na rike da wayoyinsa, 


Suna shigowa ya saki murmushi Ya ce" marar lafiyana ya farka ? 


Idriss yayi murmushin shima ya ce" ALLAH ya tashe ni broth


Mubasshir ya Mika masa hanu suka gaisa ya zauna yana kokarin bude dan abin motsa bakin, 


Idriss kuwa banda kalon hajiya Rafi'at ba abinda yake, gaba daya ta tsargu, tana tsoron karfa aje yaron nan ya saurari adu'arta, ta girgiza kai à ranta ta ce " da kuWa ya cuce ni sosai, 

Muryarsa ta katse mata tunani inda ya ce" tashi ki dauko min kofi na sha magani 


À tare suka dago, Yar mahaukaciya ta Mike domin dai ta san bazai aiki auntynta ba duda bashi da Lafiya, ga mamakinsu sai ji suka yi ya ce " No ba ke ba,  da *Yarinyar* nan nake


À tare suka zaro ido harda Mubasshir, Hajiya Rafi'at ta waiga ta kali Mubasshir ta ce" Freind KO kwakwaluwar yaron nan ta tabu ne ?  Cos yana Farkawa ya shiga tambayana shekaruna, ni kuwa anya ba za'a Kira docter ta duba lafiyarsa ba ? 


Mubasshir ya ajiye abarbar da ya wanke ya matsa kusan gadon ya ce" broth are u OK ??????? 


Idriss yayi murmushi ya ce" tabass lafiyana lau broth, i'm Idriss Ilyass, i'm 31 old, ni Docter ne, sannan à wannan lokacin Ina cikin tashin hankalin mamana mai suna Hajiya Marhaba da ta samu tabin hankali da kuma sisterna mai suna Sahla da ta karye sannadiyar son zuciya da kuma son abin duniya, kuma alhamdulilah na yarda da kadara 


Mubasshir ya ce " hajiya Rafi'at ce fa kake Kira da yarinya,  to mai zaka yi da shekarunta ?  Mai ke damunka ? 


Idriss ya lumshe Idannuwansa ya bude ya leko fuskar Rafi'at dake kalonsa tana jiran Jin amsar bakinsa, ya dawo da Idannuwansa wajen Mubasshir ya ce" nima Ina son sanin abinda yake damuna broth, Ina son sanin rigimar dake kokarin dosoni à wannan lokacin, ina rokon ALLAH ya kama mini domin wannan tashin hankalin zai fi rikitani, zai kara kawar min da nutsuwata


daidai wannan lokacin gaba dayansu sun sare du sun kara matsowa kusan sa, harda islam sun zuba masa ido, Mubasshir ya riko hannunsa ya ce" what happen, mai ke damunka broth ka fada min da yardar ALLAH zamu samo mafita 


Idriss ya tsare shi da ido ya ce" kayi min alkawarin zaka samo min mafita ? 


Mubasshir ya ce " bi'izinillah Zanyi iya yina idan har hakan bai kaucewa hanya ba, 


Idriss ya sauke ajiyar zuciya ya zuyo ya kali Rafi'at da tayi tsuru tana kalon sa, ba zato ba tsamani ta ji ya ce" Ina son auren Rafi'at, Ina son Rafi'at, Rafi'at tayi min ita nake son rayuwar Aure da ita, sai dai Ina fargabar KO zata ki *Dan Mahaukaciya ?*


Yar mahaukaciya ta zaro ido ta rike baki, Mubasshir ya saki murmushi ya juyo yana kalon Rafi'at da ta zama tamkar mutun mutuni tana kalon sa, Mubasshir ya ce " shikenan sai ayi tuwona maina


Hajiya Rafi'at ta kuma zaro ido ta ce " Da Wa za'ayi tuwanka manka ?  Au KO kunya baka ji ka kali idona ka ce Ni Rafi'at kake SO ? Ni KO auren ne ai sai Wanda ya girme ni nesa ba kusa ba, idan kaji adu'ana ne ka tausaya min to ka tayani da ada'ar ALLAH ya bani Daidai ni ba wai yaro karami ba, ka shiga Ina da ni ka fada min mai ?  Ai Nafi karfin Auren kanina 


Idriss ya rintse Idannuwansa ya ce " stop, ya Isa haka, Ki dena kalon tsabar idona kina fada min zancen nan, Ki Sani *Namiji baya kadan* kuma da kike maganar wai kin girme ni fada min shekarar biyu da kika bani ne zaki fadi haka ? To ya kike kalon tarihin auren fiyayan halita Wanda akayi duniyar dominsa ? Aure suna ne, ba tausayinki da naji kawai sonki nake, sai dai idan kalmar nan daya zata hannaki aurena wato *Dan Mahaukaciya*


hajiya Rafi'at jikinta yayi sanyi tsoronsa ya darsun mata à zuciyarta ta zuba masa ido tana sauraron duk wata kalma tasa, wai shekara biyu ta bashi, no shekara uku ne, to aman taya zata yarda da wannan abin kunyar ai har Sahla ta goranta mata, itafa har yanzu gani take Idriss baya cikin nutsuwarsa, domin wannan abin da ya dage yana fadi, ta juya ta kali Mubasshir ta ce" ka saka à caje kwakwaluwar kanina kuma abokinka, idan kuwa à cikin hankalinsa yake ka fada masa lale ya cika dan dirama, aman Ina rokonsa ya tsayar da diramarsa haka domin ni kam na cika rauni, tana gama fadar hakan ta juya zata bar dakin da gudu sai ga kofar ta bude an shigo *Elhaj ilyass ne da Elhaj Muhammad* suka dawo da kwondon abinci, gaba daya abinda suka fada à kunayensu, 


hajiya Rafi'at tayi saurin sada kanta kasa dan kar su gane hawayenta


Elhaj Muhammad ya ce" where are u going ? 


Rafi'at ta ce" zan Kira docter ne ya ya farka 


Elhaj Muhammad ya gyada kansa ta juya tana tuna fita ta tari Adaidaita tayi gidan su Mubasshir, 


bayan yan gaishe gaishe da karin jawabi kan Idriss yayi hakuri da kadararsa ya ce " ba komai ALLAH ya bani ikon cinyewa

suka amsa da amin, shiru ya biyo baya na dan dakiku 


A

Elhaj ilyass ya dago kansa ya ce" son abinda na saurara à kofa kana fada da gaske kake KO kuwa maganar ta Rafi'at ce baka cikin nutsuwarka ? 


Idriss ya sada kansa ya ce" dad, Ina cikin nutsuwata, tun ranar da na je gidan su Mubasshir ta bude min kofa na tsinci kaina à wannan yanayin, Rafi'at ita ake Kira da matar rufin asiri domin du irin abinda ya faru tana yi min adu'a da kuma iyayena, nan ya kwashe adu'ar da ya saurara daga bakinta, ya ci gaba" idan har zata juri zama da ni à halin da na tsinci kaina à ciki à yanzu tabas da sai Nafi kowa murnar hakan


Elhaj Muhammad ya ce" Alhamdulilah, barni da ita, ni nasan yanda zan bilowa al'amarin da yardar ALLAH,


Bayan wani dan lokacin Elhaj Idriss ya kali Mubasshir ya ce" yarona tashi ku tafi gidanku kaji, 


Mubasshir ya dan sada kansa ya ce" ai aba Bazan iya barinsa haka shi kadai ba


Idriss yayi murmushi ya ce" broth tashi ka tafi da sister baiwar ALLAH ta gaji da yawa, ai nima yanzu zan tashi mu koma gidan


Mubasshir ya ce" tohm sai munyi waya, suka Mike suka yi musu salama 


Tafiyar minti talatin da dan dori ne suka yi kafin su Isa gidan su, kowanen su da abinda yake sakawa à ransa, ita dai Yar mahaukaciya tana fatan auren nan ya tabata domin Idriss mutunan kirki ne, shi kuwa yana tunanin gaskiya an shiga hakinsa da yawa, 


Tsayar da motar yayi ta bude ta fice, ya bita da kalo à ransa yana tunanin Bata san tafiyar kawarta fati ba, 


Yar mahaukaciya ta tura falonta ta shiga da ada'a à bakinta, karo tayi da farar takarda ta buda ta karanta sakon fati ne na ta tafi gida sai an kwana biyu zata dawo da yardar ALLAH 


Yar mahaukaciya tayi murmushi ta ce" My fati, 


Dakin ya sha gyara sai kanshi yake ta shige dakinta tana ta murnar yanda fati ta gyara mata dakin kafin ta tafi 


Wanka ta fada, kafin tayi sai da ta shiga ruwan dumi ta fito ta sala Wanka ta dauro alwallah ta fito daure da tawul, ta zumbula doguwar Riga ta kabarta sallar magariba, bayan ta gama ta cire ta bude cikin kayanta ta saka wasu Riga da wando masu shegen kyau ta daure gashin kanta Bata tsaya yin Wata kwaliya ba ta nufi dan karamin frij dinta ta bude ta dauko jikon kabewa da madara no sugar da mamanta ta dadafa ta cicika biduduna aka jera mata à frij, guda ta dauko ta girgiza ta shanye tana tande baki, haka ta bude zumuwar da aka yi mata Hadin amarya aka ce ta ringa sha kadan kadan, ta kuwa zauna ta aniya sha sai da taji ta koshi ta rufe sauran ta Mike ta ajiye, sannan ta fito ta nufi Baban falonta ta kuna TV, 


Kalonta take hankali konce ba abinda yake damunta, ta jawo wayarta ta danawa fati Kira, suka shiga labari sai kyakyata dariya suke


Cikin farar jalabiyarsa ya turo kofar ya shigo da salama aman Bata ji ba dalilin hankalinta ya dauku wajen wayar da take, 


Ajiye ledar hanunsa yayi ya zuba mata ido yanda take labari tana dariya, ita Sam ba abinda ya dameta, ya lumshe Idannuwansa yana tunanin first night dinsa da ita du da yana cikin halin bacin rai aman abin nan yaki fita à ransa, ya sada kansa à ransa ya ce" anya kuwa zan iya hakura har sai ta yarda dan kanta, 


Ya girgiza kai à hankali ya furta " Islam


Dago kanta tayi da sauri sai à lokacin wata kunya ta dirar mata, to yaushe ya shigo dakin ma ?  Da sauri ta kali kayan jikinta ai kuwa ta diro da gudu zata nufi dakinta


Mubasshir ya saka hannunsa ya kamota ya janyota jikinsa ya rungumeta


Yar mahaukaciya ta shiga sisine kanta, aman kanshin turarensa na mugun birgeta, haka kawai ta shiga cusa kanta à jikinsa tana shakar kanshin turaran


Hakan ba karamin rikita shi ba yayi, domin sai yake Jin hakan tamkar tafiyar tsutsa take yi masa à kirji, à hankali ya dago da kanta ya zuba mata ido, 


Yar mahaukaciya ta bude idannuwanta Jin an rabata da kanshin nan mai dadi ta kale sa, gabanta ne ya fadi wata irin soyayar mijinta ta kara tsarga mata jikinta, da sauri ta sada kanta kasa 


Mubasshir ya saki murmushi ya kuma rungumeta, à hankali ya ce" kaunar Mubasshir ne nake hange à kwayar idanuwan islam ??? 


Yar mahaukaciya tayi shiru Bata bashi amsa ba, to mai zata ce masa ? Ita Kam lamarinsa ya girmimi tunaninta, gashi tun karfi ya koya mata kaunar kasancewa à kirjinsa 


Mubasshir ya  dauki ledar hannunsa ya ja hannunta suka nufi dakinta, ya ce " dauro alwallah muyi nafila 


Jin yace nafila ta nufi bayi ta kuma yin Wata alwallar ta dawo, ta zumbula hijabinta na sallah, Mubasshir ya ja su suka yi raka'a biyu


Bayan sun gama ya dafa kanta da harshen larabci ya rufe Idannuwansa yana ta kwararo mata ada'a, sai da ya gama yayi mata yan tambayoyi bisa kan adinin musulunci Wanda cikin ikon ALLAH ta bashi amsoshi gamsasu, har zuwa wannan lokacin Yar mahaukaciya Bata dago inda Mubasshir ya nufa ba, 


Mubasshir ya ce " AM dauko plate mu ci abinci KO ? 


Yar mahaukaciya ta ce" ai na sha jus din nan bana Jin yunwa KO kadan bara na dauko maka dai, tana gama fada ta nufi kicin ta fito da Baban plato ta ajiye ta bude gasasun zabi har Hudu ta juye ta ajiye masa jus din biyu ta zuba sauran à frij ta fitar da ledodin ta dawo ta shige bayi tayi brosh, ta dawo ta bude kayanta ta dauki wata Yar rigar baci ta dauki hijabinta ta nufi bayi ta saka ta zumbula hijabinta ta dawo ta dauki turarukanta na humrar ne, na fesawar ne, har ta juya zata konta ta ga turaren da aunty habiba ta Bata ta ce mata ta tabatar da ta zama mata cikakiya à gidan mijinta ta shafa shi, ta bude ta bulbula à hanunta ta shashafa à kowani sashe na jikinta tana Jin dadinsa à ranta, ta juya tayi bismillah ta gyara shinfidar gadon duda ba wani abin tayi ba, ta Haye tayi konciyarta


Du abinda take yana kalonta, mamakinsa ne ya karu ganin ta Konta da wannan katon hijabin dan yana dakin KO ?  Yayi mrmushi ya Mike ya dauki sabon tawul ya nufi bayinta dan yin wanka 


Ya dauki lokaci kafin ya fito daure da tawul ya fita ya rurufo kofofin ya dawo ya rufe dakinta ya nufi gaban miroir ya fefesa tarare,


Yana gamawa ya kashe fitilar dakin ya Haye gadon 


Yar mahaukaciya ta tashi da sauri tana zazaro ido ta ce" Yaya Mubasshir ka kuna fitilar nan mana, kana ganin duhu, Yaya Mubasshir mai zaka yi à dakina kuma bayan sun tafi su aunty ka koma naka dakin mana, y a ta y y y y y y y y y y y y y y y y y   hadiye sauran maganarta tayi sakamakon janyota da yayi ya hade bakinsa da nata ya shiga aika mata zazafan kisssss


Cikin kankanin lokaci Mubasshir ya wular da hijabin Islam yayi mata runfa yana sarafa harshenta, sakin harshen yayi yayo kasa da kansa inda ya shinshino abinda ya fitar da shi daga hayacinsa bai san lokacin da ya cafke na................... Ya shiga sarafasu cikin kwarewa


Abinda da Wanda ta sha tsumi ta sha jiko ta bulbula tarare nan da nan ta maida hankali tana karbar sakon AA cikin na'am da sakon da yake Bata, Jin dadin hakan take, shi kuwa banda Bari ba abinda jikinsa yake, adu'ar saduwa da iyali ya yi hakan yasa Nayi baya Inaiwa Yar mahaukaciya adu'ar juriyar mijinta


I'm sorry iya hakan nake iya rubutawa☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹☹ sauran na samu mazga😄😄😄😄😄😄😜


🇳🇪Belles écrivaines du Niger




*'YAR 👧🏻*     


         *MAHAUKACIYA👹*




*Na*

             *Sajida*







                          81


*Aunty Zainab kiyi ki gama min Docter deejart plz 😩*



*Sister Dee ya haka ? Gaskiya page daya yayi mana kadan, kawai ki karo mana page din bintalo domin ya dauko sugar😋* 








wayarsa dake ajiye kasa ta kwashi ruri, à tare suka zabura, Mubasshir ya diro daga bed din Yar mahaukaciya tayi saurin mayar da kanta cikin bargon, yayi murmushi yana daga wayar 



Idriss ya ce" kai wai ya haka Tunda safe Ina kiranka har karfe tara tayi  mai kake ne ? 



Mubasshir ya zaro ido yana fadin " what karfe 9 fa ?  Ya Salam abokina bara muyi sallah 



Idriss ya zaro ido ya ce" Ina gidanka 



Mubasshir ya ce" gidana fa ?  Haba bawan ALLAH da safiyar nan ?  



Idriss ya ce " kasan ALLAH ka bude min KO Nayi maka aika aika à cikin gida



Mubasshir ya ce" aa yi hakuri, Bara na wurgo maka ky din falon kafin na sauko 


Hakan kuwa akayi Mubasshir ya wulowa Idriss ky din falonsa ya bude ya zauna ya kuna TV domin yayi niyar fa bazai bar gidan nan ba sai da shi



Cikin nutsuwa ya dauki matarsa yayi bayi da ita inda ta dan sake da shi domin ta lura idan da taci gaba da nonokewa Mubasshir sai ta rame irin yanda yakeda takuran nan da son komai sai yayi mata,gashi ya mayar da lips dinta filin saukarsa du motsinsa sai ya mana mata kis



Haka suka gama ya jasu sallar asuba à karfe 9🤔, 



Bayan sun gama Yar mahaukaciya ta duka gabansa cikin muryarta uwa ta yara ta ce" morning yayana



Mubasshir ya zuba mata ido yana kalonta yaki amsa gaisuwar tata, 


Dago da kanta tayi tana kalon sa, yanayin kalon da yake mata sai da taji kunya, hudubar aunty habiba ce ta fado mata cikin ranta inda take fadin" karki baiwa mijinki damar wata ta waje ta birge sa, kiyi iya yinki dan ganin kin Wadata mijinki da dukan abinda yake bukata idan dai bai kaucewa hanya ba, sannan ki Kula da yannayin fuskar mijinki, Idannuwansa lebensa komai nasa yana iya yi miki magana da su, ki kasance mai gane kurmancin mijinki, 



Yar mahaukaciya ta Mike ta cire dogon hijabinta, ta kuma cire abayar da ta dora saman Yar karamar rigarta fara tasss,  tana sane ta duka kamar zata cire wani Abu à akaifunta, 


Mubasshir dake zaune ido ya zaro yana kalonta, kafin yayi wani yunkurin ta Mike,, ta juyo gabansa, cikin dabara ta dan ja rigar tata kasa, saman mamarta suka dan bayana à fili, nufo shi take, shi kuwa ya tsura mata ido yana son ganin abinda zata aikata


tana isowa daidai shi ta mika hannayenta biyu ta zagaye wuyansa da su,  ta Haye saman cinyoyinsa ta hade idannuwanta da nasa tana kashe shi da wani Shu'umin kalo, à hankali take matso fuskarta da tasa har ta ISO Daidai lebensa, inda Idannuwansa ke rawa ya kali idannuwanta ya kuma kali lebenta, gaba daya ya kunce ya zama wani sususu, maimakun ta mana masa Kiss sai ta fitar da harshenta ta lashi gefen fuskarsa wajen sajensa sannan ta Isa Daidai kunnansa ta hura masa iska cikin wata murya wace ni kaina sai da na zaro ido domin ban san Islam da ita ba ta furta" *Morning My Blood*



Mubasshir bai san lokacin da ya rintse Idannuwansa yana Jin saukar leben islam à kunansa da kuma sunan da ta nada masa, gaba daya tsikar jikinsa tayi wani irin tashi, bai san sanda yayi saurin jawo ta gaba dayanta jikinsa, jikinsa na mugun Bari ya lalubi lips dinta ya shiga kissing dinsu cikin zafafan Kiss, 


wayarsa ta Kuma kwasan ruru tamkar an kara mata sautin kidan 


 

Bai saki bakinta ba ya lalubo wayar sannan ya saki cikin kasalaliyar murya ya ce" Haba Idriss, haba Idriss ya zaka yi min haka, haba mana, shin mai Nayi maka da farar safiyar nan kazo kana shigar min haki haka ?  Ka tausaya min mana kana katseni 



Idriss ya ce" la la la,  lale ma Mubasshir jarabarka tafi karfinka, toh wly au ka bude kofar nan ka fito ka raka ni zance au na hanaka koma meye kake bazaka yi shi ba wly



Yar mahaukaciya banda dariya kasa kasa ba abinda take, ta Mike a hankali daga jikinsa tayi gaba abinta 


Mubasshir ya ce " baby plz karki tafi 



Idriss d'à bai katse wayar ba ya ce" tafi ke karki kula shi



haka dai à dole ba dan ya SO ba ya bude kofar bayan ya saka shadarsa maroon ya sauko inda ya bar Yar mahaukaciya tana shafa mai



yana saukowa ya nufe Idriss d'à maseefar taya zai adabi rayuwar amare, ba'a yiwa ango sauko haka



Idriss yayi murmushi ya ce" nawan wly ban rintsa ba, dama na samu Nayi hajiya traitement dinta na dawo dakina dan yin baci abin ya gagara, dole na tashi na shiga fadawa ALLAH kan ya kwata min zuciyar Rafi'at 



Mubasshir ya ce " abokina baka da dama, yanzu dan iya shege ka tsalake ka diro kan auntyna ? 


Idriss ya ce" au yaushe kuma ka yarda da auntynka ce ? 



Mubasshir ya ce" Tunda ta haifi My Islam



Idriss yayi dariya ya ce" ai kuwa nima na zama uncle dinka daga yau 


zaiyi magana wayar Idriss ta kwashi kara,  ya daga da sauri yana salama 


Elhaj Ilyass  ya ce" kaga fa abin arziki Idriss insha ALLAH yau za'a daura aurenka, yanzu haka zancen da nake maka muna gidan à zaune, ga su elhaj da mamana, da su hajiyar, Elhaj ya ce Tunda yau juma'a ne kawai mu je gidan liman mu shaida masa sai à daura idan an gama sallah 



Idriss ya Mike da sauri yana ta wara ido murna ta cika masa ciki ya rasa ma mai zai ce hakan yasa ya mikawa Mubasshir wayar yana ta hamdallah, 


Mubasshir yayi godiya ya ce" su din ma gasu nan tafe gidan



hakan kuwa akayi islam banda murna ba abinda take 


Suna Isa ta bude ta fice da gudu inda Mubasshir ya zaro ido ya ce" ya Salam, islam no karkiyi ki fadi


Ina bata ma jinsa ta tura kofar ta shige tana ta murna sai dai Bata kai ga karasawa ba ta ja ta tsaya tana kalon ikon ALLAH, Aunty Rafi'at ce sai kuka take shekawa an kewaye ta



Turo kofar suka yi suka shigo inda suma suka ja suka tsaya suna kalon ikon ALLAH 


Rafi'at ta ce" haba aunty, haba hajiya, kawai dan yaro ya ce " ga abinda yake SO sai à biye masa, haba dan Allah yanzu da girmana à hada ni Aure da yaro karami ?  Nafa girme masa fa kuma wly tausayina ne yake ba wani sona ba


hajiya hafsat ta ce " sister wai meye haka ne ?  Haba taya za'a zauna ana nuna miki gabas kina kalon yama ?  Sunar ce bakya SO ?  Idan har baki godewa ALLAH kan ni'imar da yayi miki à yanzu mai zaki yi ?  Taya zaki fasara kyautar da Allah yayi miki adu'arki da ya amsa da wata fasarar ? Rafi'at à da inai miki kalon kinyi hankali ashe dai da sauran ki, 



hajiya hawau ta ce " aa hajiya ku tashi ku barni da y'ata mu zanta kun ji ? 


Hakan kuwa akayi sai da suka tashi suka ga su Mubasshir sunyi cirko cirko da hanu suka yi musu nunin su fice karta gansu 


hakan kuwa suka shige inda hajiya hawau ta dage wajen kontarwa da hajiya Rafi'at hankalinta kan auren ta da idriss



ya kasa tsaye ya kasa zaune, du labarin da suke yana dai jinsu ne aman baya fahimtar abinda suke fada, 


Hajiya hafsat ce ta fito da faranti da abinci à ciki,  ta ajiye ta dauko ta shiga zubawa kuskus ce ta sha muryar jan nama sai kanshin kayan yaji ke tashi, ta mimika musu,, har ta kai kan Idriss ta mika masa ta ce" Idriss ka dawo cikin hayacin ka mana, 


Idriss ya juya à hankali ya shiga cacakar abincin 


Yar mahaukaciya ta shigo da jus jus ta ajiyewa kowa à gabansa, ta juya ta dauko nata farantin ta zauna Kusa da hajiya Fadimatu tayi bismillah ta debo ta kai bakinta 


Wani irin Abu taji ya bigeta à hancinta na kanshin kayan yajin nan da tafarnuwa, kafin ta Ankara tayi wani abin sai kawai taji cikinta ya fara hautsina mata sai ga amai


da gudu ta mike zata nufi Bayi aman Ina dole ta duka à nan tana kwara amai tun karfinta, dan kwalin kanta ya fadi kasa haka mayafinta domin wani irin tukota aman yake


da gudu Mubasshir ya rigayi kowa isawa wajenta ya kamata yana tambayarta Lafiya ?  Mai ya sameta ?  Wani abin ta hadiye ? 



Da kyar ta samu ta gama aman du ta galabaita ya dauketa yayi bayi da ita dan ya wanke mata wajen da ya baci à jikinta, ita kuwa hajiya Fadimatu sai sintiri take tana tambayar ta shigo ne bayin ? inda hajiya hafsat ta shiga gyara wajen


Idriss ya Mike ya fice dan dauko kayan aikinsa domin yana Docter gida har uku hakan ya sa baya tafiya ba malet dinsa mai dauke da yan abubuwan da ya dace domin aikinsa 



Daidai zai fita suka yi karo da Hajiya Rafi'at, da sauri ta zaro ido tana yi masa kalon mamaki domin Bata san shigowarsu ba, ido Hudu suka yi inda gabanta ya fadi, tayi saurin sada kanta kasa shi kuwa yaki dakin hanyar balatana ta fice, 


Hajiya hawau ta taho tana fadin lafiyarku kuwa yayanan ?  Naga kun tsare hanyar ficewa



hajiya Rafi'at ta ce " hajiya shine ai ya tsare hanyar fa


Idriss ya ce" to hajiya ta shige mana ? 



Hajiya hawau tayi murmushi ta juya tama daina shigan balatana su fake da ita



Rafi'at ta juya itama zata bar wajen da saurinsa ya riko hannunta ya jawota tamkar wata beby ya hadeta da garun dakin


Idannuwanta ta rintse tana mutsukmutsuk da baki, Idriss ya tsurawa bakin nata ido Yana kalonta 


Jin yayi shiru ne t'a bude idannuwanta ta sauke su à cikin Idannuwansa, ta kasa janye idonta daga NASA 


Idriss ya saki murmushi à hankali ya ce" hei *I Love u*


Aunty Rafi'at ta zaro ido ta kasa dauke idannuwanta daga fuskarsa gabanta na dukan uku uku 


Idriss ya kashe mata ido daya ya ce" Yaya dai madame, kalon fa ????? 



Da sauri ta sada kanta tabi ta kasa hannun NASA tayi dakin da gudu tana ajiyar zuciya 


Yayi murmushi y'a ce " she love me too,  yayi gaba abinsa



Yana dawowa dauke da kayan aikinsa ya shiga aune aunensa inda ya bukaci fitsarinta, bayan tayi ta bayar ya kuma daukan jininta ya fice, ita kuwa tayi lamo à cinyar hajiya Fadimatu, inda Mubasshir yake zaune rike da hannunta daya yana dan murzawa, hajiya Rafi'at tana dan shafa gashin kanta ita kuwa hajiya hafsat sai cin abincinta take domin juna biyu ne da ita mai shegen sakata kwadayi du da ba Wanda ta fadawa har shi kansa mai abin, 


Hajiya hawau ta kare mata kalo ta ce" wai y'ata watansa nawa ? 



Hajiya hafsat ta zaro ido domin ta san da ita hajiya hawau take, ba shiri ta Mike tana fadin " Wa ?,  tayi gaba ba tare da ta tsaya an fada mata Wa din ba, 


ai kuwa hajiya Fadimatu tayi dariya ta ce" haba kin rigani à fili na rigaki à badini hajiya, Allah ya raraba Lafiya 


Yar mahaukaciya ta zaro ido zata Mike Idriss ya shigo da result yana ta murna ya ce" an daura auren 



Hajiya Fadimatu ta ce" oh yaren zamani idriss to barka



Idriss ya dan sine kai yana mikewa Mubasshir takardar gwajinsa yana hangen Rafi'at da ta sada kanta kasa tana share hawaye, wannan karen kam kukan dadi take( Wa ya fada miki) 


Hajiya hawau ta shigo tana fadin" an daura Aure ba ango, ya akayi baku je masalaci ba ? 



Mubasshir da ya buda takardar bayan ya yiwa Idriss barka yayi saurin cewa what ?  Yana zaro ido ya kali Idriss yace"docter baka fasara min abinda nake gani ba ? 



Idriss ya ce" congratulation, abinda ka gani hakane 


Mubasshir yayi saurin kai kansa kasa yayi sujada yana ta murna, yana dagowa ya dagota ya rungume à gaban su hajiya Fadimatu wace itama murnar ta hanata zama, à tare suka yi gaba suka bar masa dakin domin kara rungumeta yake yana lalubar cikinta dake shafe yana fadin"beby boy or girl hi, dadyne, how are u ?  Kana cin abinci ?  Kana jina ? 



Yar mahaukaciya sai sine kai take a ranta tana mamakin rashin kunyar AA 













Alhamdulilah , Alhamdulilah, dukan godiya ta tabata ga ALLAH buwayi gagara misali da ya bani ikon ganin Karshen novel dina *Yar Mahaukaciya* Ina fatan du Wanda ya karantashi ya karu da abin karuwar dake ciki sannan Ina neman gafarar du Wanda na batawa sanadiyar wannan novel nawa na biyu bayan *Duk karyar kada na ruwa ne* , Allah ya hada mu à novel dina na gaba mai suna *Daga tafiya daukan soja* Na gode taku y'arku, kanwar ku, yayarku *Sajida* Y'ar mutan Niger,...




Post a Comment

0 Comments