matar lameer hausa novels cmplt

 [6/23, 8:20 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

*1*

_____________________________

Pay before read, recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________




Miqewa tayi da sauri ta daga kanta tana kallon me shigowar ya tafa hannu tare da tuntsirewa da dariya yace “kin dauka wannan raggon mijin nakine ko? Nifa ina mamakin yanda mace kamarki zaki tsaya kina auren wannan sullutun mutumin da baya iya biya miki buqatarki itafa mace tafi kowa yanci kuma tanada zabin daya dace da ita namiji dai har namiji a riga Amma a gado babu fuss sai jinkai da izza a waje, koda yake hakanma ni yayimin ya auromin mata babu ko sisina nayi mata ban ruwa kuma ta cikamin aljihuna da kudi hhhhhhhh!" 

Suka kwashe da dariya ita kuma ta tsuke fuska tace “amma kasan nace maka kada kazo gdannan yau yayanka zai dawo kuma kasan cewa banason ya fahimci akwai alaqa tsakaninmu mu zauna a matsayin abokan gaba haka nakeso shirin ya kasance.




Dara² idanunsa ya sauke akan me tallan furar da ya tsayar ta dago da hardaddiyar hausarta tace “Kado ka hiya niman magana wallah in zaka shiya jaka hudu ka shiya in bakka shiya kuma ka bareshi dama kai ka cika son araha toni komi nawa mi tsadane kajima in hwadi maka"

Yanda take mgnr ne yayi bala'in bawa pillot Lameer dariya yayi murmushi yace “komanki me tsadane nikuwa idan babu damuwa mu buga wani wasa mana ki fadamin komai kikeso zanyi miki zan aureki kawai dan ki rinqa bani dariya ko sau daya kika bari nazo gurinki baki bani dariya ba zan sanya karnukan gdana su cijeki idanfa kin yarda" 

Wani murguda baki Jiddoh tayi tace “hohoho aura kado mi akai akayika da har zan kasa baka dariya yo ko innarka da baffanka ai nabawa dariya kai bura ma kaji wani abu kwanaki da naje burni har wani me qaton ciki nabawa dariya bare kai dan tatsitsi dakai amma fah tsaya kaji ni bani auren kado kado bashi riqon aure saki a jininku shike yawwa kuma jauro Madi ma ya fika kyau gashi dan gayu har agogo fah yake sawa🤣🤣🤣




_Somin tabi_





*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/23, 8:23 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

*2*

_____________________________




Sake gyara zaman hularsa yayi ya zuba mata maganadisun idanunsa yana qare mata kallo sama da qasa yace “nononki baiyi tsami ba ko?" Turo baki gaba tayi ta qara tura cokalelen dankwalinta gaba tace “yo nonon shanuwa idan yayi tsami ai saidai akai juji" dariya yayi da ganin bata fahimci me yake cewa ba yace “amma akwai ranar da nonon naki zaiyi tsami fah" wani tsalle tayi tace “ariyyy hege Kaɗo da muguwar alkaba'i kake idan nonona yayi tsami ai goggo kasheni takayi kai barima kaji ranar nan da mukaje dandali ana ajon auren me yar butta da tsalha da nashiga ina rawa kowa saida ya liqamin takarda"



Ɗan ƙaramin bakinta ya zubawa ido yana kallonta yarinyar kyakkyawa sai bambadanci daya dami rayuwarta miqewa yayi tare dayin miqa yace "kisamu leda ki juyemin a ciki zan baki jaka uku da rabi" miƙewa tayi ta zari qwaryarta zata tafi ya riqo hnnunta da sauri yace "tsaya mana Hauwa" sakin ƙwayar tayi jikinta ya dauki rawa ta zube a gurin ta fasa uban ihu ya saki bottle  ɗin hannunsa yayo kanta yayi saurin rufe mata baki yace "ke kinada hsnkali kuwa JIDDAH uwar me nayi miki da zaki zunduma wannan uban ihun salon kisa yan uwanki su bugeni"  



sake rintse idonta tayi ta zunduma ihu tana fadin "shikenan na mutu na lalace jiyannan goggo ta gama hwaɗi mami cewa idan kaɗo ya tabaka mutuwa kakeyi yanzu nima shikenan mutuwata tazo zan tafi inda Allah wayyoh ni goggo wayyoh ni baffa wayyoh ni Madi dan burni kaɗo ya cutamin shikenan walakiri zaya kasheni..."




Tsayawa yayi kawai ya zuba mata ido haushi baƙin ciki da takaici kamar su kasheshi baisan sanda ya fincikota ya hadata da jikinsa yace "badai tabaki nayi kike haukannan ba to na rungumeki na tsotsi bakinki ma yarinya sai ki jira mutuwarki kowanne lkc daga yanzu" 




Bai damu da yanda ta bata jikinta da nono ba ya sake mannata da jikin motar ya matseta yanda ko hangenta baayi ya manna mata kiss a goshinta da lebenta ya sauke numfashi ya saketa ta kuwa zube a gurin shikuma ya zaro dubu biyu ya ɗora mata a cinyarta ya shige motarsa yaja yabar gurin itakam jiddah sake neman guri tayi ta kwanta bayan ta soke kudinta tana jiran mutuwarta don tayi imanin a yau kaɗó ya cusheta babu abinda zai hanata mutuwa.




Numfashinta ma ɗaukewa takeyi wai ta mutu idan ta bude idonta saita sunsuna rigar jikinta sai taji ƙamshin jikin kaɗo a jikin rigarta sai ta sake mutuwa taji ko zata dainajin ƙamshin turaren kaɗonta😄😃





*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/23, 8:25 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________


Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

 *Free*3*

_____________________________




________📚Tananan kwance har masu kiwon shanun rugarsu suka fara dawowa idan taji tafiyar mutane sai ta qara kwanciya tayi luf ita a dole ta mutu idan suka wucce sai ta bude idonta tayi ajiyar zuciya tace “hege walakiri ya wucce baiganni ba"🤣

Kai harfa dare ya fara shiga Jiddoh ana kwance jikin ta qaura yayi la'asar qarshe dai ta tashi zaune ta takure a jikin wata bishiya tanata dan kukanta.




Baffanta ne yazo wuccewa yaci karo da qwarya yayi saurin ja da baya tare da ciro touch light dinsa ya fara haske haske can ya hangota a takure ya matsa da sanda gabanta yana ware Mata kallo Saida ya tabbatar itace sannan ya matsa kusa da ita ya hasketa tayi saurin dagowa tare da qanqame jikinta tana karkarwa tace “na tuba azara'ilu mazarin rai alqur'an   bansan ya taba hannuna ba kuma ma har rungumeni yayi sumbaceni nidai yau mutuwa kala uku zanyi wayyohh Baffa zan tafi nabar ko harda Madi dan burni aradun Allah kado ka cuceni..." 




Naushin da taji taji an sakar Mata a bakinta shine ya dawo da ita hayyacinta ta bude idonta ta saukeshi akan baffanta aisai ta zabura ta miqe da sabuwar rawar jiki tace “kaima Baffa ka mutu ne ashe zanci gaba da ganinka a lahira amma baffa ance a lahira baa zalumci meye yasa ka bugemin baki" fincikarta yayi yace “dama Yadammu ta hwadi mani cewa akwai wani kado da yake zuwa yake siye nononki kullum har yana qara miki kudi yanzu har takai ya hwara rungumarki yana sumbarki to alqur'an baki jamin abin hwadi a duniya ba a rinqa nunani da lebe muje wuro nijiyya ubanda yace ki rinqa hutta kina neman maza mazanma asararru irin kadawa su shusheki su tai su barki"




Figarta yakeyi da dukkan qarfinsu suna shiga ya watsata tsakar gdan fadi yake “Laure Ladi ku fito kuji abunda almurar diyar nan take aikatawa nan fa duk gida aka fito akayi cirko² ita kuma ta qara bajewa a dole itafa mutuwa take jira.

Gyaran murya Baffa wuro yayi yace “wato Laure kene kika lalata yarki da kanki yanzu gatanan ta hwadi miki abinda suke aikatawa da kado" salati aka hau yi ana tafa hannuwa fadi suke sun banu sun lalace wani uwar maqura da goggo tayi Mata ne yasata sake shiga hayyacinta tace “qur'anin ubangiji bani nace yayimin shine yayimin kuma nima har mutuwa nayi walakiri yaqi zuwa ya tafi dani da tuni na huta" 




Buge bakinta goggo tayi tace zakici uwariyonki yar qaniya" Baffa ne ya daga murya yace “Tani kaje kace da Jauro mudi anjima inason ganeshi aradun Allah aure zanyi miki tunda ke bakyajin magana yau ki tsokano masunta gone ki tsokano manoma yanzu kin fara biyewa shiriritar kado to gara kowa ma da kado donni ko gaisuwa banso ta hadani da kado shashashan kawai" 



___________Qarfe tara na dare ya shiga cikin garin Kano saboda tsakanin Kano da qauyen Alqalawa da nisa sosai don't qallah yakai kilometer 94.




Gdan iyayensa dake cikin unguwar Tarauni ya fara zuwa yayi parking ya fito ya qwanqwasa bayan yan mintina yaji ana zare saqatar gdan suka gaisa da maigadin yace “Alh kuwa yananan?" Shafa kansa yayi yace “Sai Hajiya dama tace idan kazo ince tanason ganinka" 

Saida gabansa ya fadi don yasan Kiran mahaifiyar tasu ba alkhairi bane, hakanan yasa aka budensa get din ya shiga da motarsa yayi parking ya fita ya dauki ledojin da yasa aka yanko masa zabbi manya guda ashirin ya raba biyu zaikai gidansa daya daya kuma ya taho dashi gdan iyayen nasa ya shiga.




Da sallama aka amsa masa ya miqawa me aikin da take yankan apple ledojin guda biyu days zabbi daya qwansu ta tafi shikuma ya zauna tare da rusunawa yace “hajiya barka da hutawa"..........






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/23, 8:28 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

4

_____________________________





__________📚Wani mugun kallo ta watsa masa tare da yatsina fuska ta qara cokalo dankwalinta gaba tacr “wato kai Lameer bakajin mgn ko ban isa dakai ba jiya jiyannan mukayi muku sulhu da wannan yarinyar arziqin Mubaraka amma yau ma dake kai dan tsiyane Saida ka qara towai meye matsalarka ne kullum ku kenan a sulhu kamar qananun yara?" 




Tattare girar sama data qasa yayi yace “yanzu dai qarata ta kawo miki kenan towai ita yaushe zata fahimceni ne yanzu ace matarka ta sunna ta kasa gane matsalarka to waye zai gane kuwa" daquwa ta watsa masa ta gyara zaman mazaunanta tace “qaniyarka dan kusun uwa taya zata gane baka yi Mata ban ruwa yanda ya dace har cemin tayi fah sai kayi wata baka nemeta ba idan kuma ka nemeta din saidai kabarta da ciwon mara dakayi kuruf kuruf na minti biyar ka gama oni Kandala qanwar maza anya wannan da ba mace zaayi ba kuwa aka manta akayima abin maza kai komai naka a sanyaye"




Wata uwar kunyace ta kama Lameer kamar qasa ta tsage ya shige shikam ya shiga uku da barbada a dangi tun yana boyewa iyayensa matsalarsa yau gashi Mubaraka ta tona masa asiri ta yaye masa zani a kasuwa shiwai wacce irin mace yake aure mara sirri bata riqe nata bama bare ta riqe na wani to waima yaushe ma sukayi auren ne duka duka har yanzu basu rufa shekara uku ba da yarsu daya amma duk ta tallatashi a dangi bayan shima bashi yayi kansa a hakaba hakanan ya tashi yaganshi bashida qarfin sha'awa.




Ruwa yaji Hajiya ta watso masa tace “soko sakarai tashi ka bacemin a guri nikam na haihi Ladidi da hula har mace take kawo qararta dubi jikinka duk wani farin abu ya bushe kamar wani Fadwah yar cikinka ma tahika natsuwa" 

Kallon jikinsa yayi da sauri yana tunanin to meye a jikin nasa tunawa yayi da yanda suka rabu da Hauwa yar fillo dutse a hannun riga baisan sanda yayi murmushi ba tare da shafa kansa yace “nono naje siyo mana rugar Sambajo a garin Alqalawa wlh wata sokuwar yarinya Hauwa tayimin barinsa a jikina wai kawai saboda by mistake na taba hannunta a shirmenta wai goggonta tace idan kado ya tabata mutuwa zatayi" 




Dariya sosai Hajiya takeyi tace “dada fillo bazai waye ba batasan kaima hakan take ba" fara'ar fuskarsa ce ta dauke ya tsuke fuska idanunsa ya kada yayi jajir yace “zan daina zuwa gidan nan Hajiya tunda nayi aure bantaba zuwa gdannan na tafi da farin ciki ba kullum sai kin fadamin kalma mara dadi akan lalurata Hajiya idan ban samu tausayi dajin qai a gurinki ba a gurin wa zan samu?" 

Binsa tayi da kallo cike da sanyin jiki kuma fa mgnr dan nata haka take kamata yayi take kwantar masa da hankali tabe baki tayi tace “hotiho kawai" 




__________Horn yaketa dokawa a gidan nasa kafin maigadin yazo ya bude masa ya shiga yayi parking ya dauki kayan dayazo dasu ya bude qofar parlourn ya shiga TV tanata aiki ga yarsa nan Fadwah tanata baccinta a saman kujera ita kuma uwar bata parlourn.

Iska ya furzar ya nufi qofar dakin ya kama jarmlock din amma sai yajishi a kulle yayi Knocking ya juya ya shiga kitchen ya nade hannun rigarsa ya fara jera naman da yazo dashi a ciki ya koma kan kayan miyan Suma yaji an bude qofar parlourn an mayar an rufe, to be kawo komai a ransa ba saboda zuciyarsa ta tafi tunanin Hauwa wanda ya addabi zuciyarsa cikin kwanakin nan ko kwanciya yayi itace da sakarcinta sukeyi masa yawo a kwanya saidai yayita zuba murmushi shi kadai gashi gobe zaiyi tafiya zuwa sounth Africa zaiyi missing dinta sosai.





Baiji shigowarta ba sai ji yayi ta bugeshi ta baya ta wucce ya dago manyan maganansa ya kalleta ta daga masa hannu tace “oh sorry mistake ashe ka dawo" murmushin kawai yayi ya matsa gabanta yace “naji saqonki na gode waike Mubaraka yaushe zakiyi hankali ne ki riqe mana sirrinmu kinsani fah nafi kowa son naga na zama jarumin namiji wanda bakeba zan iya gamsar da wasu matan ma amma ban samu wannan damar ba ya kikeso nayi don Allah kina gani kullum cikin neman magani nake kuma kin sani ko banyi sex ba Ina iyakar qoqarina naga na cire miki kewa amma komai nayi miki bakya gani saboda kawai wannan matsalar  Mubaraka mata da yawa irin damarki suke nema sun rasa kinga ke ba rashin ci ba ba rashin sutura ba duk abinda kikace shine nakeyi miki Toni meye ya hana ki karbeni a yanda nake bayan kin sani abubuwa da yawa naki bayimin sukayi ba Amma saboda kada tawayar tayi yawa nake qyaleki yanzu idan baki rufa asirinmu ba a duniya waye zai rufa?"




Tabe baki tayi ta juye indomie dinta a flat sai yanzu ma ya lura da yanda gashinta yake a hargitse shi dama ba kirki ba, kafin yayi mgn tace “dallah malam kauce na wucce" matsawa yayi ta wucce har takai bakin qofar yace “yinin yau banci abinci ba Ina abinci na?" Ko kallon arziqi bai samu ba tayi ficewarta.

Ajiyar numfashi yayi ya dauki yourghut da cake ya fita ya nufi dakinsa dake sama abin takaici da mamaki dakin kaca²  gadon harda danshi alamun baa dade da tashi akai ba ya ajiye yourghut din ya fara gyara dakin ya gama ya shimfida sallaya yaci abinda zaici ya miqe yayi wanka ya dawo ya dauki laptop dinsa ya fara aikace²nsa sai wajen daya sannan ya kwanta saime?




Zuciyarsa taqi hutawa da tunanin Hauwa da zarar ya rintse idonsa kallonta yakeyi matse jikin mota ya hade jikinsa da nata yana sauke mata kiss a kuncinta jikinta na rawa tunaninsa gabadaya ya karkata ya koma Rugar Sambajo qauyen su Jiddoh yasan dai bai barta da matsala ba tunda ya biyata kudin nononta da wautarta tasa ya zubar da haka ya kwana ko cikin baccinsa itace wai tana shafa gemunsa tana cemasa “I LOVE U My Lameer" shikadai yaketa zuba murmushi yana qara qanqame pillow.






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/23, 8:29 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

*Free 5*

_____________________________




 


____________📚Hodijam Jiddoh baiwar Allah wannan dare ta daku gurin goggonta har saida ta kumbura mata jiki saboda duka da muburgi fadi takeyi “ni zaki kunyata ki jawa abin hwadi a gari dan ubanki ki rasa wa zakike kulawa kuna shiga duhun dawa dashi yana lalubeki sai kado ashe da gaskene da Madi dan burni yashe yana ganinki kina kaiwa wani dan yankon kayi nono yanayi miki juyensa ya baki kudi da yawa, to daɗa Allah ya nunamin kuɗi har jaka goma a jikinki ɓingel wato kuɗi yake baki yake ƙwaƙuleki ko?"


  


Girgiza kai takeyi kamar zata tsinkeshi tana kuka jikinta na rawa goggo ta sake nufota tana cewa “kina yimun bayani ko sai nasha aradu ani gaton uwarki"

Jiddoh bata iya qaryaba cikin kuka ta zayyane musu komai suka rinqa sallalami da tafa hannaye suna hwadin “aradun Allah Jiddoh kin riqa qugunki ya isa daukan bindira tunda har kado ya hwara hwadi maki batun aure to kuwa ai dole baffanki yayi miki aure da Madi dan burni tunda ke shegiyar ya ce" 




Wata wawura goggonta ta kumayi mata ta zauneta ta bare qafafunta tana kuka tana ihu ta dauki danyan tasshi ta murza Mata ta dagata tace “gobema ki qara bari Kado ya tabaki har ya dambusheki dau uwariyonki aurakiya kawai almura me idon agwagwa"

Habawa me Jiddoh zatayi banda kuka tumami da ihun azaba danyan barkono a gatonta sai tsuku yakeyi Mata ita kuma tanata dara tana tumami tana ihu da kuka me ban tausayi.




A haka goggonta ta cillo Mata bokatin qarfe tace “tashi dan ubanki kije rafi ki daukomin ruwa kizo kiyi wanka kiyimin wankin daudata ki sukole wadannan kayan naki bazan kwanta dake bukka dai ba babu tsarki yau sai kin qarar da ruwa buta goma" 

Hakanan tana tafe tana talewa tana kuka taje rafin ta zauna a bakin rafi tanata rera kukanta taji an warce bokitin nata ta dago da sauri zatayi bala'i sai taga Madi a tsaye sai washe baki yakeyi yana turo harshe gaba yace “hegiya Jiddoh yau nayi miki burni ai ya nine nazo nace naganki da Kado a cikin duhun dawa kuna cicin tsuli kuma aradun Allah gobema na ganki kin qara kai mushi nono sai nayi miki sharri da yahi haka tunda ke bakyaji kuma kin rainani aradun Allah bindira ta tahi ta Kado qarhi kuma kizo muje bayan rafi a gwada ki gan...."





Qumm yaji an buga masa Abu a goshinsa jini ya balle ita kuma taja da baya da sauri tace “alqur'anin Allah kai tsinanne ne Innan qotai tayi asarar aihuwa shege dan durun uwa danma ka samu nace da Kado ka iya sa agogo to tunda kai Dan iskane na daina sonka ma na tsaneka na tsaneka hege bindirar ka din uwarka an hwadi muka di diyat iskace"

Damqota yakai hannu zaiyi ta qara jifansa da bokatin ta kwasa da gudu ta shige cikin duhun dawa tanata bubbuda qafa saboda zafin tasshin da takeji a qasanta har yanzu ta jima a gurin sannan taga yabar gurin ta fito da sanda ta kandami ruwanta ta dora akanta ta nufi cikin rugarsu takai tayi wanka ta wanke gidan dadin sosai Amma har lkcn zafi yakeyi Mata ta shafa versilin a gurin ta rinqa fifitawa har Allah yasa taji relief ta koma daki tayi sallah ta kwanta  tanata juyi qasan zuciyarta cike da tunanin Kado tare dajin haushinsa na jamata dukan da yayi a fili tayi tsaki tace “Kado hege ne harda wani hmwah yayimin qaton kawai saikace Bandirawo Iro"............





_Ina neman afuwarku na jin *DHOOM ISHAQ* shiru wannan ya farune sakamakon wani uzuri da yasha kaina amma gobe insha Allah zanyi qoqarin yin abinda ya dace_






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/25, 11:41 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

*Free Page*


_____________________________

*Free 6*

_____________________________




__________📚 Washegari tun asuba ya tashi ya fara shirya kayansa cikin trouble bag dinsa kasancewar yasan Koda ya tashi Mubaraka ba lallai ta tashi ba zatace yayi wuri da yawa to shima baiyi yunqurin tashin nataba ya gama shirinsa tsaf ya hada tea dinsa yasha ya kira drivern office dinsa ya daukeshi zuwa airport kasancewar tafiyar bashi daya bane da sauran abokan aikinsa zasuje training din.




Yana zuwa babu bata lkc suka daga zuwa South Africa zuciyarsa cike da kewar parents dinsa da yar fulaninsa Hauwa da kewarta take neman zame masa jiki a wannan lkcn haka ya wanzu cikin wata irin rayuwa daya kasa gane wacce iri ce kullum zasuyi waya sau biyu da Mubaraka ya tambayeta lfyrta data yarsa Fadwah amma ya kasa daina kewar qasarsa ta gado musamman Rugar Sambajo.



____________Kwananta uku bata dauki tallan nono ba ko dandali ta daina fita duk a qoqarinta na karsu hadu da Madi dan burni yace zai sanya mata bindara tunda taji Indo qawarta da akayi Mata aure tana cewa bindira lubebiyace idan ta shiga bata iya fita saidai ta yayyaga mutum kuma idan ta tashi dane yake tunkudota waje.

Shiyasa take masifar tsoron bindira ita har kuka takeyi da tumami idan akace zaa kaita asa mata bindira, tana tafi tana yan waqoqinta taci uwar dammara abinka tayi kwalliya ta rambada kanta kile harda digon india a goshinta da kumatunta tasa kayansu na fulani shudaye tana tafe tana waqar  “lula lulaye aluliya zani bikin andi aluliya" batasan binta akeyi ba saida tazo jikin wata bishiya kawai taji an dumbular mata nono an kwasa da gudu.





Aikuwa ta dora hannunta akan nononta tana ihu tana burgima tana hwadin “shikenan na mitu na lalashe dan innini na sun tabamin wayyoh Goggo wayyohhhh Baffa wlh bazan yarda ba saina taba nonon uwarsa nima" wasu yanmata ne guda uku sukazo wuccewa suka ganta a kwance duk tayi birgima tayi tumu² suka tsaya suna kallonta tare da tafa hannu sukace “Hamdi imboni Jiddoh meye hakadin?" 

Miqewa tayi zaune tana karkade qasar data shiga cikin dogo baqin gashinta da ya mulku da manshanu tace “Qur'ani saina mulmulawa uwar Wanda ya dumbularmin Inninina Fura a gatonta"🤣🤣


 



Dariya suka kwashe da ita Lantana ta kalli Jummai tace “kiji doluwa to yau aka fara dumbular inninin naki naga cewa akayi har Kado kike bawa yakesha shiyasa sukayi girma sukayi ruguza ruguza haka" 

Zabura tayi tace “kutmar dumadu naci hagu naci dama naci tattabatsinin kantalin baqoramar inyaniyar marurun tsohon gwailon uban wanda ya hwadi haka" kafin suyi wani aune ta hade kansu guri guda ta kama jibgarsu hagu da dama tana wani tsalle tana naushi ta ko Ina.





Suna ganin haka kowa yaci na kare ta kuwa rufa musu baya a guje fadi take.

 Yau har bayan tsoho da tsohuwa suna doki doki sai nabi ƴa naci uwar galken ubanta Kaɗon dako mgn bata dameshi ba ina ya iya wannan iskancin shi banda sumba da qaquba babu abinda ya iya kuma qur'ani saina hwaɗí muhi bashi kawo lantarki gidanku"

Yanda suka rinqa gudun a daji abin abin dariya kuma sai qara rungume qirjinta takeyi wai kada a qara dumbular mata nono😁




Jitayi an riƙeta ta baya taja ta tsaya tana huci tare da waiwayowa zatayi bala'i sai tayi ƙasa luuuu saboda ganin yayanta lawan tasan ta kaɗe har rassanta rirriƙeshi tayi tana kuka tana cewa.

"Alqur'an bani na tsokalesu ba sune kawai ina kukana da burgimar tuba sukazo suka tambayeni meye yasani kuka nace adumbili akayimin shine sukace wai ai dama ance ina bawa Kaɗo nono na wannan na jikina bana shanuwa ba yanasha kuma aradun Allah ƙarya sukeyi barima na fito maka dashi ka gani"😂😂😂






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/25, 8:31 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

*Free Page*


_____________________________

*Free 7*

_____________________________




_________📚Hannu ya dora aka yace “honi lawwali ni zaki nunawa dan qaniyarki yar  ja'ira tashi muje wuro kiyi bayani" yanayin gaba ta miqe da sauri ta nade zanenta ta kuma kwasa da gudu ta nufi gdan yana kiranta yana komai amma bata tsayaba saida ta isa gdan ta shige dakin kishiyar Goggonta tana mazari Inna Jummah ta miqe da sauri tace.

“Wanne niya meye hakadin ubanwa kika taokano" sake qanqameta tayi tana kuka tana girgiza kai yana zuwa ya cake yace “zakici qaniyarki yar kusun uwa"




Yana fita ta zube a tsakar dakin tana mayar da numfashi tace “wlh sai nayi qulla ciki akan wanda yayimin adumbuli" tafa hannu jummah tayi tace “gide shiyasa nice da baffanki yayi miki aure" 

Saurin rufe Mata baki tayi tace qur'ani baniso ance idan akayi wai...Wai...." Saurin daga mata hannu tayi tace “aradu ya isa kuma dole baffanki ya aurar dake shekara sha hudu qawayenki harda yayansu ke kinanan kina bambadanci a gari" 




Miqewa tayi tace “ai saiki aurar dani din yo aradun Allah guduwa zanyi kamar yanda Ladin Moddibo ta gudu nima na rinqa shigowa daga maraya Ina taunar danqo Ina tafiya qwasqwas.

Binta tayi da kallo har ta fice daga dakin ta nufi dakinsu ta kwanta tare dajan mayani ta lullube jikinta dashi yau goggonta da kanta ta fita tallan nono, zuciyarta ce ta tafi tunanin Lameer ta dallawa kanta mari tare da jan tsaki tace “aikin banza ma ko meye gamina dashi.





___________Lkc yanata tafiyarwa Lameer ya kasa sukuni kullum da tunanin Hauwah yake kwana yake tashi idan ya kwanta bashida mafarki sai nata wannan mafarki shine yake dauke masa kewar abubuwa da yawa saboda idan yayishi yakan yini cikin walwala da farin ciki.

Watansu biyu suka gama abinda sukaje yi suka fara haramar tahowa gida shidai farin ciki gurinsa baa cewa komai ya rasa meye yakeji game da Hauwah amma yafi alaqanta abin da soyayya to kuma shi wanne irin so yakeyi mata ya zaiyi ma ya tunkari iyayenta yace yana son yarsu?




Ya fahimci sudin irin fulanin nan ne masu tsauri sosai a dan shiga cikinsu din da yakeyi ya fahimci sun tsani Bahaushe musamman ta fanni auratayya zaiyi walaha kaji mutanen rugar Sambajo sun aurar a waje ko sun auro.

“To wai nima da nake wannan lissafin ta Yaya zan auri mace sama da daya bayan dayar ma bana iya sauke nauyinta dake kaina dari bisa dari?" 

Ya tambayi kansa yana shafa qasumbarsa tare da lumshe idonsa ya hadiye wani yawu me ciwo shikam yanason Hauwah matsayin Mata to amma ya zaiyi ya riqeta ya sauke mata dukkan haqqoqinta sannan ya zaiyi da Hajiyarsa data tsani ko mgnr kishiya taji wani yayi balleshi da dama kamar ta tsaneshi cikin yayanta ya lura har tafison Mubaraka akansa saboda indai abi ya shafi Mubaraka to yanzu zata rufe ido taci mutuncin sa, "Ni wai ya zanyi ne?" ya fada yana dafe qirjinsa da yakeyi masa zafi saboda ba yau ya fara wannan tunanin ba.





 

*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/26, 10:23 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

*Free Page*


_____________________________

*Free 8*

_____________________________



_________📝Ya jima yana saqawa da warwarewa domin samun mafita amma ya kasa jin Hauwah yakeyi a duk wata kusurwa ta jikinsa.  

Ji yakeyi dama ace zai sameta batare da yasha wahala ba shikam koma meye zai faru saidai ya faru Hauwah itace muradinsa a yanzu baya fatan ya rasata a rayuwarsa jima yakeyi kamar idan ya rasa Jiddah bazai rayu ba.





____________Abubuwa da dama sun faru a cikin watanni biyun ciki harda tsayar da ranar  aurenta da Madi wannan abu ba qaramin dagula lissafin Jiddoh yayi ba ta tashi hankalin kowa akan cewa itafa bazata aure Madi ba dan iskane har cewa yayi suzo su zagaya duhun dawa ya gwada mata bindira.

Duk yanda tayi tunanin abin zaizo Mata da sauqi ta kasa samun wannan gatan hakan yasa kullum cikin kuka take da damuwa ko zaman gidan ta daina duk da sun hanata fita amma suna fita tallan nono zata haure dangar karar da suka kewaye gidansu da ita ta shiga cikin duhun daji.




Sau tari sai baffanta yaje gindin magwaron data mayar gurin zamanta ya korota sannan take tafiya hatta abinci ta dainaci saidai idan taji yunwa Tasha madarar shanu ta kwanta sukam iyayen ko a jikinsu hidimarsu kawai sukeyi.

Ana haka ta fara rashin lfy sosai kamar bazatayi ba nanfa hankalin baffanta ya tashi sosai ya shiga damuwa dan baiyi tunanin qiyayyar da takewa dakai har ta kwanta jinya ba.




Yaso ya canza raayi amma yayarsa Yadammu tazo har gida ta rinqa sababin bala'i wai ai iskokine da Jiddoh dama haukanta ba irin na masu hankali bane wauta tsokana da rashin kunya duk ta tattara kuma a gurin uwarta ta kwashe komai.

Shiga gdan yayi yana fadin “Hari! Hari!! Ke Hari dake nake wannan ja'irar yar taki bazata jamin abin fadaba maza fito Yadammu tace yau Boka bawa yake hawa bori fito da Jiddoh muje yau duk uban aljanin dake kanta saiya sauka kuma aure tsakaninta da Madile babu fashi saidai idan bana raye"




Dukkan matan gdan fitowa sukayi suka fara sallalami suna fadin “oya maigida Moddibo Dalha ma yana maganin iskoki basai kaje gurin Boka Bawa ba" 

Daquwa ya watsa musu yace “kunfini ko kunfi Yadammu sanin abinda ya dashe ne to aradun Allah duk Wanda shi qara buda baki sai ta koma gdan tsohonta almuran banza almuran wofi ai dama nasan kune kuke daurewa Jiddoh gindi takeyin abinda taga dama nan har gda akazo aka yimin gorin nabarta ta gandame ta zama uwar mata a gda tunda rugannan take babu yar data tabayin shakara sha hudu a gdan iyayenta sai ita kunsani yarinya tun tanada shekara tara ake dauranta aure a rugannan amma ita saboda bakin jininta da mugun halinta gatanan daqyar ta samu Madilen ma ya tsaya yo banda sharrin iskoki inane zatashe batasonshi har tani jinya yo kwarankwatsa saidai tayi bunga"




Shiga daki goggonta tayi tana tashinta amma fir taqi tashi saida sukakai ruwa rana sannan da taga Baffa ya dauko kokara zai sabeta yasata tashi ta fice da gudu tayi bayan gdan gudu takeyi sosai bata tsayaba saida tayi nisa da rugarsu ta shiga wata fadama ta samu gindin bishiyar kashu ta zauna tana haki dafe da qirjinta saida tayi me isarta sannan ta hade kanta da gwiwa taci gaba da rera kukanta zuciyarta na tuno mata da Kado tana tuna rana ta farko da suka fara haduwa dashi.




_*WAWAYE*_



_________Goggonta ta dora Mata tallan nono su Idin Tasha suka shanye Mata harda sanyata ta siyo musu sukari ta zuba musu suka tashi zasu tafi tace su bata kudinta suka kama zaginta harda dungure mata kai Mati ya zare Wuqa yace zai yankata idan bata tafiba babu arziqi ta tashi ta dauki qorenta ta nufi hanyar rugarsu tana tafi tana waiwaye batayi auneba kawai taji ta bugi mutum tayi baya da sauri jikinta na rawa ta dago ta kalleshi kyakkyawan Saurayi me cikar zati dago kakkaura wankan tarwada sanye da kayan turawa injita da fada.

Shima kallonta yakeyi cikin hasala yace “ke wacce irin yarinya ce kina tafe kamar makauniya kalla yanda kika batamin jiki da nono...."




Daga hannunta tayi tana ajiyar zuciya da niyyar bashi haƙuri bata iya buɗe bakinta ba saboda kukan da yaci ƙarfinta kawai sai ta kama ƙafarsa ta fashe da kuka.

Jikinsa ne yayi sanyi tunaninsa mgnr daya fada mata ce tasata kuka shima durƙushewa yayi ya sanya hannunsa ya ɗago fuskarta ya zuba mata kyawawan manyan idanunsa ƙirjinsa na bugawa da sauri da sauri  yace "meye dalilin kukan?"

Cikin in...ina tace "su... su Idi da Mati suka shanyemin nono har sukashe ni siyo masu sukari da ciniki na kuma suka hanani kuɗin kuma sukashe idan nace sune sai sun kasheni kullum sai sunsa Goggona ta bugeni idan kuma na hanasu su shunamin karnukansu suyita yimin haushi kwanaki wani har cizona yayi" ta zauna sosai ta bude masa gurin saman santala santalan sangalalin qafarta farare tas da suka cika da suma kwantacciya lufluf dashi ya sauke idonsa a gurin da karen ya cijeta gurin har yayi rami sai ruwa yake zubarwa...........





 

*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/26, 2:21 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

*Free 9*

_____________________________






_________📝Rintse idonsa yayi da sauri yace “subhanallahi meye yasa bakije an wanke miki gurin ba?" Shiru tayi tana sharar hawaye kafin ya miqe yace “zo na wanke miki nasa miki magani" batayi jayayya dashi ba ta miqe tabishi yasa ta zauna a gefen motarsa shikuma ya dauko hydrogen da corton ya fara wanke Mata tana kuka tana ciccije leɓe yanayi Mata sannu lkc zuwa lkc yana ɗagowa yana kallon kyakkyawar fuskarta data jiqe sharƙaf da hawaye yanajin wani tausayinta yana kwarara a sassan jikinsa.

Koda ya gama yayi mata plasting ɗin zama yayi ya zuba mata ido yana kallon kyakkyawar halittar bafulanar yanajin wani shauqi na taso masa, a hankali cikin dashewar murya yace





 "Ya sunanki?" haɗiye kukanta tayi tace "Jiddoh Arɗo Jibir" iska ya furzar ya miƙe yace "ok gobe kizonan idan kin ɗauko nonon ki kawo min zan siya zan taho da likita yayi miki allura kinsan cizo kare dafine dashi ƙafarki zata iya ruɓewa idan baayi miki allura ba, na nawane nonon dasu Idin suka shanye miki"

Shiru tayi kamar bazatayi mgn ba ta fara haɗe kayanta bayan ta gama ta miƙe zata tafi ya riƙe hijjab dinta fuskarsa murtuk ya zaro dubu biyu ya bata yace "ki ajiyemin canji na gobe zan karba kada Goggo ta dakarmin ke" ƙememe taƙi karɓar kudin wai dukanta zaayi nononta na jaka huɗu da rabi ne.




Kama gefen kallabinta yayi ya ɗaure mata dubu daya ya bata ɗaya a hannunta yace "kice da goggo wani ne ya siyi nono babu canji shine yace gobe kibashi na rabin jakar"

Dariya tayi tace "aradun Allah kaɗo kanada wayo sosai zaka tai dani burni na ƙaro wayo?"

dariya ta bashi ya shiga motarsa ya kunna tana tsaye har yayi kwana zai tafi ta bude baki tace "Kaɗo" juyowa yayi ya tsaya wai kaɗo sai kuma yayi murmushi ya daga mata hannu itama ta daga masa hannu ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo yana ajiyar zuciya a hankali yace "Hauwa'u kulu Maijiddah.

Figar motar yayi a guje ya fice daga lungun tundaga wannan lkc ya kasance kullum shine yake siye nononta idan ta dauko idan kuma zaiyi tafiya bazaizo ba to yakan bawa manajan gdan gonarsa kudin ya rinƙa bata kullum hakanne ya wanzar da shaƙuwa me ƙarfi tsakaninsu.




_*ASALIN LBR*_



___________Tananan zaune a wannan guri har duhun magaruba ya fara sawo kai ta miƙe a hankali ta fara fita daga saƙaƙiyar har ta fito titi sosai ta fara tafiya cikin rashin kuzari har ta isa rugarsu takuwa yi saa Allah bai haɗata da ƴan dumbule ba don ta lura nononta da Allah ya wadatata dasu suna mugun jan hankalin maza duk da cewa kullum cikin taresu takeyi da hannunta kasancewar ba bra suke sanyawa ba haka suke yawo da abunsu a tsaye cako cako wannan dalilin yasa kullum take taresu saboda kunya takeji taga sunyi cokal cokal dinnan.





Isarta gda kenan taga gilmawar wata baqar LAND GRUSSER ta bayan bukkokinsu a guje hakanan taji gabanta ya fadi tanason ganin waye a ciki amma babu dama da alamun na cikin ma a fusace yake.

Ƙwafa tayi ta shiga gdan nasu taja tayi turus ganin ƴan gidan nasu gabaɗaya tun daga kan baffansu har zuwa kakansu mahaifin baffansu kowa yayi cirko cirko suntada gemu da alamun wani abune mara daɗi ya hwaru batasan hawa ba balle sauka taji an fincikota tsakiyar filin da mutane sama da talatin sukayiwa da'ira wanda ko gutsuttsurata akayi ƙila wani bazai samu ba anyi cilli da ita an hau bugunta ta ko'ina suna haki kamar waɗanda aka sanyasu dole.




Itakuwa baiwar Allah Jiddoh sai ihu takeyi tana roƙonsu su bar dukanta zata mutu amma babu wanda yaji tausayinta ya ƙyaleta ita kuwa goggo tashi tayi tabar gurin saboda tanayin mgn kanta zaa dawo ace tayi rashin kunya.

Basu bar jibgar Jiddoh ba saida sukaga ta daina numfashi sannan kowa ya koma gefe yayi duru duru suna kallon kallo wannan yana faɗin kaine ka daketa a makasa wannsn yana faɗin aa kaine, baffane ya ƙuta yace "yo ba gwara a kashetan ba a huta da wannan abin kunyar da ta janyo mamu, wai ni Arɗo Jibo nine Kaɗo ya iya tarar cikin idona yace yanason irin mutum daga gareni wannan wanne irin tozarci ne Jiddoh tajamin a duniya"...............








*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/26, 9:14 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

*Last Free 10*

_____________________________






*Last Free Page!*

  


_Naso nayi muku free kamar yanda na saba amma yanayin labarin bazai bani damar hakan ba saboda tsoron kada a maimaita irinta *GIDAN UNCLE.*_



_Ku biya mu kasance tare zanyi alfahari daku masoyana na gaske wanda kuke burin kasancewa Dani a Koda yaushe UMMUH HAIRAN CE dai takunnan me nishadantar daku da dauko muku abubuwan da suke addabar rayuwarmu ta yau da kullum._ 



*_MARUBUCIYAR_*

_Jagoran rayuwa_

_Aminiya ko kishiya_

_Fadimatul zahrah_

_Habibullah_

_Queen Farha_

_Gidan Uncle_

_Adandi_

_Waceceni_

_Auran bazawara_

_Dhoom Ishaq_

_And now Matar Lameer_


_____________________________




__________📝Kuka sosai Baffa yakeyi yana kwaso kwashewar albarkar duniya yana jibgawa Jiddoh dake kwance a qasa magashiyan rai a hannun Allah.

Goggo dake bayan danga tana hangen halin da ƴqr tata take ciki ta share hawaye ta koma ta zauna tana tunanin ko meye yasa baffa yake tsangwamar ɗiyar tata tilo wadda duk cikin ƴaƴansa babu meyi masa biyayya kamarta.




Allah ya sani har ranta itama bataji zata iya bawa kaɗo auren ɗaya ɗayar ɗiyar tata ba amma wannan dukan yayi yawa dole ne tasan abinyi saboda ta lura rayuwar Jiddoh ake nema a rugar tasu, da wanne zataji da auren dolen da ake shirin yi mata da ɗan shaye shaye ko kuwa da mangarin da akeyi mata ko kuwa da mugayen alkaba'ain da akeyi mata?

Bata koma cikin gdanba saida kowa ya fashe sannan ta shiga ta tarar da jummai akan Jiddoh tanayi mata surkullensu na fulani tana shafa mata ruwa a fuskarta.




Miƙa tayi tare da jan zuciya suka miƙar da ita zaune ta zauna tana bude idonta daya kumbura saboda bugu tana kallonsu gwaggo da Inna Jumme tana matsar kwallah ta buɗe bakinta daqyar tace.

"Meye nayiwa Su Moddibo da Arɗo suke buguna wlh bansan komai da nayi musu ba wayyoh bayana Gwaggo wayyoh ƙuguna zani mutu wayyoh kaico...." tana mgnr ne cikin zubar hawaye kamata sukayi suka shiga da ita bukkarsu Inna Jumme ta ɗora sanwar ruwan zafi ta dawo ta zauna kusa da ita tace.




"Kema Jiddoh bakyaji kinsani cewa a wannan rugar tamu bamu bawa kaɗo aure meye yakaiki soyayya da kaɗo kaɗon ma maƙiyi irin jinin sarkin noma Mudansir na alƙalawa kinsan har abada babu jituwa tsakaninmu da irin sarkin noma nikam saidai hande jiddoh wai har kika turoshi shikuma ya ɗauko tsayi kamar daren mutuwa yazo wai yana neman izinin aurenki"

Kallonsu takeyi da rashin fahimta tace "ni bani bace ɓatan burtali yayi ya shigo jejinmu amma ni ban saneshi ba aradun Allah..."




Buge mata baki tayi tace "kusun uwarki ya kawoshi bakece kika faɗi mashi sunanki Hauwa ba yar gidar Arɗo jibo ko kuwa ƙarya yayi miki to nidai shawari zan baki in kinƙi kisha wahala garama ki nemai inda kuke haɗuwa ki hwaɗi masa yabi tsawanyarsa daban kibi taki saboda mudai ko mazan rugarmu sun qare bamu daukan subarjo kamarki mu bawa kaɗo kaɗon ma jinin Sarkin noma"

Miƙewa Inna jumme tayi taje ta juye ruwan zafin ta surka tazo ta kamata ta kaita makewayi ta rinƙa gasa mata jiki ita kuma tana kuka tana ciccijewa tana rufe ƙirjinta a cewarta da tsirarar  nono gara ta gindi.🙈




__________Shigar dare Lameer yayi cikin garin saboda yana tafiya yana hutawa kasantuwar irin suyar da zuciyarsa takeyi masa tunda yake a rayuwarsa bai taba ganin wulaƙanci irin wanda yau ya fuskanta a rugar sambajo ba.

Ikon Allah ne kawai ya kawoshi gdan yana shiga baibi takan komai ba ya haye samansa ya cire kayansa ya faɗa bathroom  ya sakarwa kansa ruwan sanyi duk da sanyin damunar da yake garin badon komai ba saidon ya samu sauqin abinda yake masa tuƙuƙi a ƙalbinsa amma ina kamar turi ma haka yaji.





Fitowa yayi ya zauna a saman resting chair din ya dafe kansa yana furzar da iska me zafi cikin ƙunar zuciya, zabura yayi ya miƙe ya fara safa da marwa yana tunanin mataki na gaba maganganun Arɗo Jibo suna dawo masa inda  yake cewa "kai kaɗo dubeni nan ni ba ɗan iska bane mu ba asararru bane ba rakiya mukayowa bayin Allah duniya ba idanma kana tunanin haɗa zuri'a dani to ka daina aradun Allah dana baka auren ɗiyata Jiddoh ƙwamma ni tsireta na cinye namanta"

 wannan Kalami sun daki zuciyar Lameer fiye da dukan dorina sosai suke zaga masa a kwanyarsa kuma suka sashi cikin tunani da son sanin meye dalilin da yasa Arɗo Jibo yayi wannan furucin tare da ƙara ɗaura ɗambar neman auren Jiddoh.

"Kuma munyiwa Jiddoh miji dama mun daɗe da samun lbrn kaine kake hure mata kunne har kanayi mata juyen nono kana janta ku shiga duhun dawa kasata ta fito innininta ta baka kasha..." "meye innini ya tambayi kansa tare da miƙewa ya buɗe ƙofar ya shiga kitchen ɗin dake saman ya dafa tea ya dawo parlourn nasa ya zauna ya tusa kofin a gaba ya kasa shan ko kurɓa daya saboda Hauwah kawai yake gani a idonsa dukan kansa yayi tare da tambayar kansa wai yaushe ya shiga wannan cakwakiyar rayuwar ne wacce ƙaddara ta kaishi Alƙalawa har ya ƙarasa Rugar Sambajo ya haɗu da Jiddoh ya fara yimata wannan son na mutuwa da rayuwa................








*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/27, 9:11 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.




_____________________________

*11*

_____________________________




__________📝Wannan rana bacci ya gagari Lameer kwana yayi yana tufka da warwara zuciyarsa tana guri biyu kaso tamanin yanaga Hauwah kaso ashirin yana gurin Mubaraka.

Wayewar garin kamar danshi akayita ya shirya tun shidda na safe ya zauna yana kallon tagar da take nuna mishi lkc yana sauke numfashi lkc zuwa lkc yanakai idonsa ga agogo har bakwai ta cika ya miqe ya dauki key din motarsa ya dauki wayoyinsa ya sauko qasan.




A tsakiyar parlourn sukayi clear da matar gdan ta fito daga kitchen dauke da cup a hannunta  ta tsaya turus tana kallonsa cike da tsoro a hankali tace “Lameer yaushe ka dawo?" 

Shafa sumarsa yayi yace “na shigo naji dakinki a kulle da alamun kinyi bacci shiyasa ban tasheki ba ya kike ya baby Fadwah" iska ta furzar cike da godewa Allah don tasan shima ya fada ne saboda ya kare kansa amma baije ba dakinta a bude ya kwana suna sha'aninsu ita da Muneef amma a fili sai tace.




"Ayyah sannu ya hanya"

Yana tafe yake bata amsa har yakai bakin qofar ta tabe baki qasan maqoshi tace “a tafe kamar namijin qwarai tsautsayi auren me dandaqaqqen azzakari" 

Tunaninta baiji me tace ba shikuma yajita sarai saboda Allah yayi masa baiwar jin sauti kamar maciji a zuci kawai zakayi magana ya kasa jinka, ajiyar zuciya yayi ya fita ya shiga motarsa zuciyarsa babu dadi yanaso Allah ya nuna masa ranar da zaiyiwa Mubaraka cin kaca wanda zata daina caba mishi mgn har irin haka amma ya kasa samun wannan damar.




Office dinsa ya fara zuwa ya zauna zuciyarsa cunkushe da tunani damuwar daya kwana da ita ta danne damuwar da Mubaraka take tunanin ta cusa masa, ya kasa hassala komai a gurin aikin sai juya biro da kallon takarda kawai da yakeyi.

Miqewa yayi kamar Wanda aka tsikara ya fara hada takardunsa yana zubawa a jaka wadanda zai bari kuma ya mayar dasu loccar ya dauki kayansa ya fice.




A guje yabar harabar office din nasu ya nufi hanyar da zata kaishi qauyen Alqalawa zuciyarsa cike da zulumi da tunanin wanne irin cin mutunci zai fuskanta yau.

Daga garin Alqalawa zuwa rugar Sambajo tafiyar kilo mitter 6 ce tunda ya isa garin Alqalawa zuciyarsa ke bugawa da qarfi hakan yasashi nufar gidan gonarsa dake kilo mitter 2 da rugar Sambajo yayi parking anan saboda cewar da Arɗo Jibo yayi duk ranar da suka ƙara ganin motarsa sai sunsa anyi masa rotse.




Ya jima a motar yana tunanin ta ina zai fara kafin ya samu ƙwarin gwiwar fitowa ya fara ratsa kalgo da sabara yana kakkarcewa amma burinsa kawai yaje ya qara roqonsu su amince masa da auren diyar tasu saboda baijin zuciyarsa zata iya hqr da Hauwah.

Tafiya yayi sosai a cikin duhun bishiyun da amfanin gona da yayi tsayi sabida ni'imar damuna, 

Yazo giftawa jikin wani lambu ya rinqa jiyo shassheqar kukan mace, da sauri yaja ya tsaya tare da qara baza kunnuwa gabansa yana faduwa saboda jin sautin yake kamar na Jiddoh.




Da hanzarinsa ya fara laluben inda sautin yake fitowa har ya matsi gurin sosai, yadan tsaya cike da faduwar gaba da gaske kunnuwansa basuyi masa qarya ba itance zaune  sanyi da wasu kayan saqi koraye irin nasu na fulani, ta sanya kanta cikin cinyarta tanata gursheqen kuka.

Abinka da farar mace fatarta duk tayi taruwar jini alamun duka akayi Mata ta nade jelar gashinta da akayi Mata kitson doka ta daure ya sauka har qasan mazaunanta.





Matsawa yayi da sauri gabanta ya tsugunna ya sanya hanunsa ya shafa damtsenta da yayi burdin burdin, a mugun tsorace ta dago kanta tare da bude baki zata qwallah qara yayi saurin rufe Mata bakin da bakinsa ya tura harshensa cikin nata yaja ajiyar zuciya me qarfi tare da zama dirshan a qasan ya fara qoqarin janyota jikinsa ta janye da qarfi ta miqe ya ruqo hannuta da sauri yace.

“Tsaya Hauwah saurareni ki fadamin waye ya dakeki haka?" Zama tayi ta qara rushewa da kuka tace “baffa Ardo dasu baffa Laminu harda Hamma Lawal kuma... Kuma ni bansan me nayi musu ba"




Cikin muguwar hasala yace “akanme suka dakeki har suka tara miki jini a jiki haka?" Kukanta ne ya qara qarfi tana girgiza kai yace “stop crying Hauwah ki fadamin meye yasa suka dakeki?" Cikin kuka tace “ni bansanshi ba yazo yace yanason aurena kuma shidin ya kasance Kado ne mu kuma a rugarmu bama bawa Kado aure kuma muma bama auro irinsu...." 

Cikin tsananin tashin hankali da sanyin jiki yace “meye dalilin da yasa baku bawa Kado aure Hauwah idan kuma qaddararku ce Kadon ya zakuyi nidai inasonki kuma zan aureki koda ace rabon da ya qaddaramin sonki zaiyi kisa wlh saina mallakeki Hauwah wayar gari kawai nayi naji inayi miki so irin na bada rai fansa wlh ko duniya zata taru nidai inanan akan bakana zan aureki ko duniya zata qini saboda kece farin cikina....."





Tunda ya fara mgnr jikinta yake rawa har kawo lkcn daya gama ta zabura ta miqe zata warta a guje shima ya miqe da sauri ya fincikota ya hadata da qirjinsa yace “kada ki sabarwa kanki da tsoro da gudun mijinki kinji yar fillo na, nasani zan fuskanci qalubale ta kowanne bangare akan aurenki amma na shiryawa karbar hakan matsalata kawai danginki su aminta dani wlh idan suka yarda ko a yau sai an daura aurena dake"..................






*UMMUH HAIRAN CE*

[6/28, 8:15 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.




_____________________________

*12*

_____________________________




___________📝Kama hannunsa tayi ta gasa masa cizo Amma memakon ya saketa saima ya qara matseta yana ajiyar zuciya yace “dadi nakeji idan najiki a jikina.

Daqyar ta kwace ya sake kama hannunta ya fita da ita daga gurin ya nufi jikin wata idaniyar ruwa da ruwa yake bulbulowa ya zaunar da ita saman kujerar dake gurin shima ya zauna a kusa da ita ya zuba Mata ido.




Duk da dama Hauwah batada qiba amma wannan karon tayi rama sosai, numfashi ya sauke  yace “kin rame sosai meye ya kawo hakan?" 

Qasa tayi da kanta tana wasa da yatsun qafarta ya zuba mata ido.

Komai nata burgeshi yakeyi, a hankali ya rinqa janta da hira harta saki jiki dashi suka rinqa hirarsu da dariya sun manta da duk wata damuwa a haka har yamma tayi liqis yace ta tashi ya rakata gda.




Saurin kada masa kai tayi tace “aa kayi zamanka ni zan tafi ni daya" murmushi yayi yace “bazan iya barin ke kadaiba kince anayi miki adumbuli" 

Rufe fuskarta tayi tana dariya shima dariyar yayi yace “haushi naji sosai da wani ya rigani taba dukiyata...." 

Ai kafin ya gama rufe bakinsa ta ranta ana kare ya zuba mata ido yana dariya a ransa yace "zanyi aiki kafin ki nutsu Hauwah"




___________Da sanda ta shiga gdan ta shige dakin Gwaggonta ta fada saman gadon karan dake  dakin tana murmushi ta rungume pillow tanajin wani nishadi na musammam.

“Muhammadu Lameer ta maimaita sunan tare da sake rufe fuskarta da hannunta tana murmushi tace “dan gayu me qamshi muah muah muah bakinsa kamar yasha zuma dadi"🤣🤣




Rufe idonta tayi tana qyalqyala dariya tace “komai nasa na yan gayune bari ma na gwada tafiyarsa na gani ko zan iya" 

Miqewa tayi tana wani gyarawa wai zatayi irin tafiyar Lameer, ta jima tana training sannan ta koma ta kwanta ta lumshe idonta tana haskosu wai gasunan a birni ya kaita makarantar bokoko irin wacce yayan gdan sarkun noma sukeyi.





Tashi tayi zaune da sauri tace “to Wai dama shi jikan sarkin nomane amma meyesa yafi su Jamilu da Daheer kyau?" Komawa ta kumayi ta kwanta tana shafa inda yayi Mata kiss tace “bakinsa qamshi ba irin na Madi ba da kullum yake warin daddawa da kuka ko asuwaki bayayi hege me qaton baki kamar wani rami" 

Duk abinda takeyi Gwaggo na tsaye ta bayan taga tana kallonta har saida taga ta gama sannan ta shigo dakin ta zauna tace “ina kikaje kikakai yamma liqis haka Ardo yanata nemanki zakuje gurin Boka Bawa" 




Turo baki gaba tayi tace “nifa bazani gurin wani Boka Bawa ba Kado yacemin shirkace kuma shirka batace kuma wlh yace yana Sona zai kaini burni yasani a makaranta  ya rinqa bani shayi da burodi....."





Sallalami Gwaggo ta fara tace “nikam naga boni da  dannan ni Hari anya wa'e Kado ba maye bane" sake turo baki gaba tayi tace “aradun Allah ba maye bane shifa kullum qamshi yakeyi kinga ma har turare yabani sannan yace idan yazo gobe zai tahomin da kayan kwalliya na yan burni harda wannan abin nan na wanke gashi irin nasu na aljanu da muke gani a majigi a Alqalawa idan munje tallan nono bakiji wani abubama Gwaggo da zan taho yace zai rakoni nace aa shine yace saiya rakoni tunda nace anayimin adumbuli kuma yace haushi yaji da wani ya rigashi tabawa.







*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/28, 8:15 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.




_____________________________

*13*

_____________________________




___________📝Wata uwar gwarza da Gwaggo tayi Mata a baki itace tasata tsuke bakinta ta dauki sandar korar shanu ta shimfida Mata a bayanta tana sababi ita kuma ta shige qarqashin gado ta buya yanda Gwaggo take fada tana zage zage yayi mugun firgita Jiddoh ta sake shiga taitayinta.




Daqyar Inna jumme ta qwaceta ta fice tana kuka ta koma bayan gida ita bata taba ganin aibin abinda ta fadaba kawai daga bada lbr sai a rufeta da mazga itakam taga ta kanta.

Daganan data gama zamanta ta gaji dandali ta nufa take sukayi tsalle tsallensu kowacce saurayinta ya kirata aka fara hirar masoya itakam da Madi ya aiko Kira cuccuwa dan aiken zagi tayi kafin ya iso gurin tabi zugar qwailayen yan matan sunbar dandalin batama nufi rugarsu ba gidan yayarta laminde ta nufa.




Mamaki ya cika laminde na ganin qanwar tata kasancewar rabonta da zuwa gidan tun kafin a fara rikicin aurenta da Madi.

Zama tayi tana bata lbrn Kado itanma fada ta rufeta dashi wai me zatayi da Kado matsiyaci ma irin na birni babu shanu babu gona sai iskanci da auri saki.




Nanfa rigima ta harqe Jiddoh babu hqr an zagar Mata Kado har fadi takeyi kuma idan Kado ya aureta kada wanda yaje gidanta tunda basa sonshi.

Tana tafe tana fada tana sababi har take gida ta shige dakin Gwaggonta taja bargo ta rufe jikinta sallar ma cewa tayi bazatayi ba tunda kowa ya tsani Kadonta 🤣




Washegari Gwaggonta batajin dadi baffanta dole ya qyaleta ta dauki tallan nono ta nufi garin Alqalawa tun kafin ta isa inuwar da suke zama ta hangeshi tsaye yana danne danne da wayarsa cikin farin uniform dinsa da yayi masifar amsar jikinsa.

Tsayawa itama tayi tana qare masa kallo har ya iso gabanta bata saniba sai ji tayi ya sauke qwaryan nonon kanta ya ajiye ya karbi bokitin hannunta yace.





“Kince bakya sona baki iya aurena amma sai kallona kikeyi why?" Turo baki tayi tace “kuma dan naga kayi kyau na kalleka shine zaka zageni da arnanci to ai nima inajin arnancin"

Murmushi yayi yace “Allah ya baki hqr fulani na ni kam ban isa ba na daina yau kinsan me nakeson ki koyamin?" 




Kada masa kai tayi ya shafa siririn sajensa yace “fullanci nakeso ki koyamin naga rugarku duka bakwa Hausa kada naje cikin surukaina na zama bare" 

Dariya tayi tace “yore lale ananin ba ananin ba ananin yore laye ananin yore..."dariyarsa ce ta sanyata yin shiru ta zubawa dan qaramin bakinsa ido har ya tsuke ta sauke ajiyar zuciya ta nemi guri ta zauna tace.





“Jiyama saida Gwaggo ta bugeni saboda Ina bata labarinka nikam dai inason nayita kallonka kanayimin kyau amma su sunce Basu sonka kawai oye ka tafi ka auri kaduwa yar uwarka kaga jiyama saida Baffa yace zamuje gurin Boka Bawa"

Kallonta yayi tare da motsa bakinsa yace “waye Boka Bawa ne?" Wasa ta farayi da yatsun qafarsa daya miqe tace “shi gani yake har hanji indai yace maka zaka mutu to mutuwa zakayi wai sunce iskokine dani shiyasa nakeqin Madi ni kuma iskanci ne banaso ranan nan fah cemin yayi my zagaya duhun dawa tasamin bindira bayan ance wai wai bindira qatuwace Indon Moddibo  Dalha tunda akasa Mata bindira kawai sai tayi ciki aka rinqa yawo da ita turba turba ana nunata anayi Mata waqa wai ansa Mata bindara tayi cikin shege qarshe sai barin Rugarmu tayi ta koma birni"




Yanda take zaro masa zancen ne yasashi fahimtar inda zancen ya dosa yayi murmushi yace “kuma ke tsoronta kikeji Toni yanzu in munyi aure ya zakiyi dani nima inason kiyi ciki ai" 

Harararsa tayi ta miqe tana qunquni ya miqe ya riqe faffadan hips dinta dabai gama fashewa ba yace “duk ranar dana zama mijinki zan nuna miki bindira ta kinason gani?" 

Saurin daga kai tayi ta kalleshi tace “au kaima kanada ita?" Murmushi yayi ya shafa qasan mararsa yace “inada ita Amma ni tawa bs kamar ta kowa bace batada qarfi kamar yanda ake fada miki ba"..............






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/28, 9:30 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.




_____________________________

*14*

_____________________________




_________📝Tabe baki tayi ta dauki qwaryarta tace “nikam Baffana da yan gdanmu ba yar iska bane basuda bindira ni kadama ka qara cewa kasanni banasonka kuma......" 

Rufe mata baki yayi yace “ni kuma inasonki zan aureki idanma bakiso bazanyi miki ba kawai kallonki zantayi kiyita sani nishadi ko?" Daqa masa kai tayi tace “amma ka yarda zaka nunamin din ko?" Murmushi yayi yace “har wasa zakiyi da ita ma" 




Dariya tayi ta fara juye masa nonon saida ta gama dure masa a jarka sannan ta qulle masa furar a leda tasa masa a but sannan ta dawo ta tsaya kusa dashi tace.

 “Kayyy wannan mutum oye kwai shirgege kalla fah a saitin qugunka nike" matsawa yayi yace “aa kalla sosai a saitin qirjina dai ko? Murmushi tayi tace “yawwa Ina abuna da kace zaka siyamin?"




Jan hanunta yayi ya zagaya ya sanyata a mota shima ya shiga ya zauna yace “na siyo miki amma ban gaji da ganinki ba so nake nayi miki wata tambaya inaso cikin satinnan zan turo iyayena su nemamin auranki, a yau nakeso idan na koma gda na sanar da mahaifina inason qara aure amma idan munyi aure Lagos zaa kaimin ke fah"

Wata uwar harara ta galla masa tace “tabdi kaje ka saidani kwarankwatsa dubu bazanje ko inaba"




Kallonta yakeyi da mamaki shikam tunda yake bai taba ganin sakaryar yarinya irin Jiddoh ba bude mata qofa yayi yace “naji jeki" wata leda ya dauko ya miqo mata yace.

“Ga alqawarin da nayi miki jiya ki kula da kanki zanje Lagos May be zanyi sati daya kafin na dawo kome ke akwai zanji gurin Alhajinmu.





Hannu ya sa a aljihunsa ya zaro yan dari biyar bayar da baisan adadinsu ba ya kama hannunta yasa mata tare da kissing dinta yace “ki bawa Gwaggo Koda yake muje kawai inganta da kaina banson tallan nan naki"

A fari taso qin yarda suje wuronsu dashi amma yanda yayi kicin² yasata dole ta yarda sujedin bisa sharadin saidai su tafi a qafa haka kuwa akayi suna tafe yana janta da hira yana dauke da qorain nonon nata har suka iso bayan gdan cikin saa kuwa sukaci karo da Gwaggo ta debo ruwa a rafi ta tsaya tana kallonsu cike da tsoro hadi da kunya irin tasu ta fulani ta saki bokitin ta juya da sauri.




Binta yayi shima yana fadin “Gwaggo ki tsaya bafa wani abu bane don Allah ki tsaya ki saurareni"a wata kwana suka hadu da Inna Jumme ta tsaya itama ta tsaya tasan halin abokiyar zaman nata duk da Jiddoh ba ita kadai bace amma itace mace ta fari to a al'adarsu ta fulani bazata taba tsayawa tayi mgn da duk wanda yace yanason Jiddoh ba balle Lameer da dama ba qaunarsa sukeyi ba.





Inna Jumme ce ta tareshi tace “oye miye yake hwaruwa kaiko bazaka samawa kanka lfy ka fita harkar diyarnan ba tunda sunce bazasu baka ba" 

Shafa sumarsa yayi ya durqushe yace “Wlh nima nayi qoqarin hakan amma na kasa Inna nabawa Hauwah kudi ta kula da kanta sannan na bata ta kawo muku a daina dora mata tallan nono saboda bata gari Inna Hauwah tanada garin jiki kuma halittarta tana daukan hankalin maza komai zai iya faruwa ta fadamin komai da dalilin da yasa batason aurenta da Mahadi don Allah kada kuyi Mata dole kada kuja da ikon Allah wlh zan aureta kuma zan riqe muku ita amana fiye da abinda kuke tsammani"




Kallonshi Inna Jumme takeyi cikin tausayawa tanaji a ranta dama Ladingon ta ce ta samu wannan dan gayun da kota tsiya² sai anyi auren tace.

“amma ta yaya zaayi kace ta daina tallan nono bayan dashi muka saba?" 

Qasa ya sakeyi da kansa yace “eh nasani amma nasan kunayi ne domin ku samu kudin cefane to ga dubu hamsin nan ku rinqa cefane har na dawo sannan a fadawa Baffa yayi hqr yau talata to rana i ta yau magabatana zasuzo don Allah ya taimakeni ya amsheni a matsayin zabin ubangiji"………………….





*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/28, 8:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: _____________________________



*MATAR LAMEER*

_30% TRUE LIFE FICTIONAL STORY 30%_ _AND COMEDIANS STORY 40%_



*_LATEST HAUSA NOVEL FOR 2020_*

_____________________________

*Fauziyya Tasi'u Umar*

_____________________________

Pay before read 300 single section VIP 500  recharge card MTN ta  WhatssApp  a wannan number 09013718241 ko wannan 09031307566, ko ta account number:  0255526235: Fauziyya Tasi'u Umar

GTBank.


_____________________________

*15*

_____________________________


*LAST FREE PAGE*





________📝Cikin tausayawa Inna Jumme tayi masa gdy ta nufi hanyar da zata isar da ita gda tana zuwa ta tarar da Jiddoh tsaye tana leqensu ta cafketa ta.

Juyowa  tayi cikin muguwar kidima tana ganin Inna Jumme ta sauke ajiyar zuciya tace “inna Kado tausayi yake bani wlh kamar nayi masa kuka yau har qwallah naga yanayi dazun fah"





Kamata tayi tare da daukar ledar kayan suka shiga suka bajeshi a tsakar daki Jiddoh ta rinqa bin kayan da kallo kayane bana wasa ba ya hado Mata harda dogayen ruguna turaruka hijjabai da takalma sannan kayan kwalliya hatda relacxer ta manya guda biyu.

Wani tsalle tayi tace “Aradun Allah wannan shi zan rinqa shafawa nima jikina ya koma irin nasa ya daina kaushi da kirci Inna Jumme jikinsa fa shi har wani danshi yakeyi kuma duk jikinsa gashine irin na yan majigi"




Daquwa Jumme tayi mata tace “ke ar wannan ai saidai abawa Gwaggonki amma yayi miki yawa a man shafawa irin nasa farin nan nefa ke kuwa ai farace" 

Turo baki gaba tayi tace “aa ne yaseen shi meye yasa baiyi farin ba nidai kibani abuna na bude na gani" mangari takai mata tace “uwariyonki ko sille baki tabawa cikin kayan nan nasan baffanki bazai bari ki karba ba ki bari mu boye sai mu nunawa Gwaggnki  kudin kinsan su bakinsu daya da Ardo fah"




Shiru tayi kamar me nazari kafin ta kunto kudin daya bata kel kel dasu yan dari bibbiyu har na dubu ashirin ta zaro ido tace “Inna jaka dari ce mun shiga uku siyemu zaiyi fah"

Karba Inna tayi ta qirga jikinta na rawa tace “mun boni Jiddoh jaka dari uku da hamsin ya bamu Ina zamu kaisu?...."

“Ku kawo nan sukaji an ambata tare da bude labulen Ardo ya shigo a fusace yace “wato na lura kema kina daya daga cikin masu budewa yarinyar nan ido da kudi ko to bari kiji Jumme aradun Allah ko Moddibo ubana daya kawoni dunniya zan iya dagawa sanda akan wannan shegen yaron me idon agwagwa"





Wartar kudin yayi da qarfi a hannun Inna ya fita da sauri duka suka miqe suka bisa ya nufi madafi da aka balbala wutar kashin shanu ana girki ya cusa kudin.

Inna Jumme tace “Ardo sheden ka qona da wuta oye Ardo kanada hankali kuwa jaka dari uku da hamsin fah Ardo"

Itakuwa Jiddoh durqushewa tayi a gurin ta rusa ihu tace “na shiga ukuna Baffa ka qona masa kudinsa wayyohh Kado dama ban karbar maka kudinka ba Baffa me zance masa...." 




Sanda ya daga zai maka mata Gwaggo ta tareshi tace “oye  Ardo diyagga da gaskiyarta wannan qiyayya taka da yaron nan Lameeru tayi yawa koma meye ai bai kamata ka huce akan kudi ba yanzu idan yazo yace a biyashi me zaka bashi"

Hayayyaqo Mata yayi yace “ya kada galkena ya tafi dasu ai dama ba yau suka saba kashe mana shanu da hada baki da barayin burtali su kada mana shanu ba aradun Allah Hari da Jumme kowacce ta sake sakan baki akan mgnr makirin yaron nan jikan sarkin noma qur'anin Allah saita tafi gdan tsohonta"





Yana fadin haka ya juya ya shiga dakin ya dauko kayan kwalliyar ya fita dasu Jiddoh ta bishi da sauri cikin tashin hankali tana kuka tana fadin “ayyah Baffa kada ka rabani da kayan kwalliya na nima so yake nayi kyau na zama yar gayu...." 

Bai tsaya sauraronta ba ya zubasu a wata tsohuwar rijiya ta qarasa da gudu ta leqa rijiyar ko hango batayi saijin zubarsu ciki tayi ta zube a gurin ta dora hannunta akanta ta runtuma wani ihu tare da fizgar ledar ta rungume a qirjinta shi kuwa Ardo ya angijeta ya wucce abinsa ya barta rungume da leda tana kuka tana kirar “shikenan kayan kwalliya na sun tafi rijiya Kado yaushe zaka dawo ka kawomin wasu..................






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/29, 10:01 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*16*

_____________________________




________📝Tajima kafin taga zaman bazai kaitaba ta tashi ta nufi gidan tana haɗa hanya ta shiga ɗakin gwaggonta ta kwanta tanata sauke ajiyar zuciya zazzabi me zafi ya rufeta zuciyarta cike da tunanin Lameer da maganganunsa da suketa yimata yawo a ƙwanya.




___________Kada ya shiga gari kai tsaye gdansu yanufa yayi saa kuw ya tarar da Alh a falon ƙasa yana hutawa ya zauna suka gaisa dashi sannan suka gaisa da hajiya yayi shiru gabansa na faduwa yana tunanin ta inda zai fara.

Alh ne ya katseshi da cewa "Magaji meye yake faruwa ne kamar bakinka akwai magana ince dai ba matsala bace a gdan naka?"

Girgiza kai yayi yace "ba wannan matsalar bace Alh don allah alfarma nake nema a gurinka"




Da mamaki Alh ya dubesa yace "tame babana?" shafa sumarsa yayi yanason faɗar sirrin ransa yanajin tsoron tujarar hajiya.

Yanda yake kallonta ne yasa alh cewa hajiya abamu guri yaron nan tsoron masifarki yakeji" taɓe baki tayi tace "bashida gsky ne shiyasa yake tsoron faɗa a gabana" tana faɗin haka ta miƙe tayi shigewarta ɗakinta shikuma alh ya zubawa Lameer ido yana nazarin damuwa kwance saman fuskarsa yace "kai nake sauraro magaji Allahu yasa dai lfy"




Sumarsa ya shafa yace "lfy lau Alh dama inason na sanar dakai ne...." sai kuma yayi shiru bakinsa ya sarƙe murmushi Alh yayi yace "kamar ba namiji ba  kana mgn kana fargaba ita faɗuwar gaba asarar namiji ce ai Lameer ka fito kayi mgn darect mana"

Cikin in...ina yace "in...inason zanyi au...r...e ne dama..." zuba masa ido uban yayi cikin naƙaltar yanayi da mamaki yace "aure wanne irin aure Lameer kana zaune ƙalau zaka tashi hankalinka ƙanƙaninka dakai zaka tarawa kanka iyali meye damuwarka da matarka ta gda?"




"Bashida wata damuwa da ita saima ita da yake tatawa rashin mutumci kullum cikin ƙorafi take alh kai shaida ne basa wata guda baayi musu sulhu ba wani sabon tashin hankali ma watnnin nan daya sawo kai kaga yaron nan sai suyi watada watanni bai sauke mata haƙƙin aureba kuma wlh ba yau aka fara ba dama duk gdan da kaji an fiya samun saɓani to ɗaya yayi watsi da haƙƙin ɗaya, yo bandama iskancinsa Alh da tsabar ya raina mutane Lameer har nawa yake da zaice zai auri mace sama da ɗaya kuma bayqn ɗayar bata ƙoshi ba, eh mana bata ƙoshi ba mana Alh ci da sha ai duk mace tana samu a gdan iyayenta kwanciyar aure itace aure ai"




Tuda ta fara faɗan jikin Lameer yayi matuƙar sanyi baisan sanda hawaye ya fara fita a idanunsa ba tsoronsa Allah tsoronsa suce zasu hanashi auren Hauwah ya tabbatar rayuwarsa ta shiga kwale-kwalen masifa da tashin hankali saboda yanzu hakan jinsa yake kamar ransa hade yake dana Hauwah.

Muryar Alh ce ta katseshi da cewa "wai hakane Magaji?" ɗagowa yayi da manyan idanunsa da suka kaɗa sukayi jah cikin sanyin jiki yace "eh hakane Alh amma don Allah kada ka yankemin ƙauna da samun dawwamammen farin ciki Alh Hauwah yarinya ce ƙarama batasan komai ba kafin lkcn da zata fara buƙatata insha Allahu nasamu lfy tunda ina neman magani"

_Kuji fa wata gwari_




Ajiyar numfashi Alh yayi yace "Wannan falsafar taka akan qarya kayita ka nemi maganin kafin ka buƙaci ƙara aure shi aure meye yakesa ayisa ne Lameer anya ma kuwa kasan sharruɗan aurevoir? To bari kaji wani abu Magaji ko matarka ta gida wato Mubaraka indai kayi wata shidda baka kusanceta ba warware aurenku ya kamata ayi saboda hasashen masana halayyar ƴa mace na duniya ya tabbatar mace lafiyayiya watanni uku take iya jure rashin namiji a tare da ita wannan dalilin yasa kaga addini ma ya sassauta musu yace suyi iddah watanni uku idan rabuwar aure ta gifta"





Ɗagowa yayi yace "amma Alh..." katseshi yayi da cewa kaje ka Lameer banson shirme fah" hawayene ya zubo a idanunsa sharrrr ya miƙe a matuƙar sanyaye ya nufi ƙofar ya buɗeya fita ya shiga motarsa ya zauna tare da buga kansa da sitiyari yace "innanillahi wa innah ilaihir raji'un"

Daƙyar ya iya yima motar key ya nufi gdansa cikin wani yanayi dashi kaɗai yasan ya yakeji a zuciyarsa yana shiga ya buɗe motar ya fita ya buɗe ƙofar falon ya shiga daƙyar ya iya sallama ya hangi Mubaraka zaune da apple a hannunta Fadwah nata wasanta ta nufoshi da tafiyarta da batayi ƙwari ba ta riƙe masa ƙafafu ya ɗagota a hankali yana amsa sannu da zuwan da Mubaraka takeyi masa ya nufi sama da ƴartasu a hannunsa ya sauketa a saman gado ya dauko choculate ya bata ya shiga bathroom  ya sakarwa kansa ruwa sannan ya dawo ya zauna a ƙasa dirshen yana kallon yarinyar jikinsa yana rawa saboda a rayuwarsa bai iyasa abu a ransa ba.





Tunda yake bai taɓajin ciwo da takaicin rashin mazantaka ba sai yau wannan wacce irin masifa ce, shidai yasan yace zai hƙr da Hauwah ma zance ne bazai iyaba yanzu meye abinda ya dace yayi?.................






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[6/30, 8:31 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*17*

_____________________________




________📝Daqyar ya tashi ya haura gadon ya kwanta yana tufka da warwara zuciyarsa cunkushe da abubuwa kala².

Wannan dare shidai bai rintsa ba asubar fari yayiwa gdansu tsinke mahaifinsa yana dawowa daga masallaci ya tarar dashi zaune tare da maigadi ya tashi da sauri ta tareshi.




Shikam Alh saida gabansa ya fadi ya zubawa dan nasa ido yana ayyana wanne irin abune wannan me yake damunsa haka da zai baro gdansa cikin duhun asubar nan.

Shiga gdan sukayi yajashi har dakinsa yace “babana meye ya fito dakai da sanyin safiyar nan" shafa kansa yayi ya durqushe yace “Alh na kasa jurewa jiya ban iya rintsawa ba don Allah ka taimakeni ka amince da aurena da Hauwah wlh zuciyata ta kamu da qaunar yarinyar fiye da inda kake tunani Alh komai zai iya faruwa dani idan ka hanani auren Hauwa"




Mamaki ne ya cika zuciyar Alh Lameer dinsa me kunya wai shine yake roqonsa ya amince yayi aure to yanzu idan ya amince da wannan aure me yayi kenan? Da ace baisan matsalar Dan nasa ba dasai ya shige masa gaba yayi aure amma yasan matsalarsa.

Towai meyema ya dauki hankalinsa haka har ya damu da auren? Katseshi yayi da cewa “kace wani abu don Allah Alh wlh aure suke shirin yimata kuma itama ni takeso zata zauna dani a duk yanda nake nasan bazan samu matsala da itaba tunda yarinya ce wlh nayi maka alqawarin daganan hsr bangon duniya zanci gaba da neman magani kuma duk yanda zanyi naga na sauke haqqinsu duka zanyi insha Allah"



 

Kada kai yayi yace “naji magaji kaje zanyi tunani akai yauwa ya maganar tafiyarka Lagos?" Numfashi ya sauke yace “sunyi posting dina tun sati daya daya wucce wannan mgnr ta hanani tafiya nafiso a gama komai kafin na tafi inyaso tunda Mubaraka tana aiki idan aka daura sai kawai na wucce da Hauwah can"

Shiru Alh yayi kuma fa a mgnr dannasa akwai abin dubawa duk lalacewar namiji mace kusa dashi garkuwa ce ko banza sayi hira yace bani kaza ta bashi" ajiyar numfashi Alh yayi yace “kaje idan nayi nazari zan nemeka" 





Gdy yayi tare da miqewa ya fito sukayi kicibis ds Hajiya itama ta fito saida gabansa yayi wata muguwar faduwa ya tsugunna yace “ina kwana Hajiya" tabe baki tayi tace “lfy meye ya kawoka gidannan da asubar nan?" 

Shafa kansa yayi yace “nazo naga Alh ne" tsaki tayi tace “au dama mgnr nan tun jiya baa barta ba to wlh tallahi kaji na rantse wannan auren bazaayishi ba indai nice na haifeka bazan yarda da wannan kwadon hatsin barar ba ta gdanma baka iya da itaba balle ka kawo wata" 





A hassale ya kalleta yace “wai waye yace miki bana iyawada da iyalina ne meye na ragesu dashi ci ko sha ko sutura? Me takeyiwa kanta a rayuwarta to nidai don Allah ki cire bakinki a mgnr aurena Hajiya ni namiji ne kuma tsayayye a gdansa sannan nakai lkcn da yakamata ace nasan daidai nasan akasin daidai"

Tafa hannu tayi cikin salati tace “ehhh lallai Lameer kakai harma ka isa wato ni kake fadawa cewa kai namiji ne ko tabdi lallai da aiki a gabana dannan tunda nake dakai baka taba tsallake mgnta ba sai yau saboda kaso qara aure har kake yimin tsawa"




Kallonta yayi yana mamaki wai yayi mata tsawa shikam ya rasa wacce irin uwa Allah hadashi da ita da kullum burinta taga kasawarsa tayi masa gori akai.

Miqewa yayi ya fice tanata sababin bala'inta ya nufi gdan wan babansa don yasan tunda Hajiya taqi mgnr idan bata sama ya biyowa Alh ba to baza ayiba.

Bai boye masa komai ba ya zayyane masa harda takun saqar da suke fuskanta da dangin Hauwah Mal Yahaya yayi qwafa yace “aikuwa ka taro March bakada fili Lameer shi aure nufin Allah ne amma fa zaakai ruwa rana saboda Rugar Sambajo munsansu sanin gaske tun duniya na kwance basa bawa Kado aure ni kaina na nemi aure a rugar amma daga qarshe cin mutunci ya biyo baya da qage hadi da qazafi sufa sun tsani Bahaushe musamman wanda ya hada alaqa da garin Alqalawa Lameer abubuwa da yawa sukaja wannan gabar fah saboda haka indai zakaji shawara ka janyewa auren yar gdan Ardo Jibbo saboda tujararren bafulatani ne fiye da kwatance shi duk cikin yayan Moddibo Durange shine baudadde har ya baudar da yan uwansa wlh ni kaina tsoronsu nakeji sau uku suna fasamin glass din motata saboda wani dalili nasu mara kan gado...............







*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[7/1, 8:46 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*18*

_____________________________




________📝Ɗagowa yayi cikin yanayin tashin hankali yace "amma Mal itafa yarinyar tana sona don Allah kuje ku nemamin aurenta idan suka ganku ƙila su yarda da gaske nakeyi ba yaudarar yarsu nakeyi kamar yanda suke zato ba da gaske Mal inason yarinyar wlh jinta nake a ƙarƙashin zuciyata"

Shiru Mal Yahaya yayi kana yace "shikenan kaje insha Allahu zaayi abinda ya dace amma kaima ka dage da addu'a don wlh tsoron sharri da kaidin waɗannan fulanin nakeyi"




Godiya yayi sosai ya miƙe ya tafi gdansa zuciyarsa taɗan sake yayi parking ya nufi cikin gdan da sallamarsa suna zaune a dinning suna break, gabansa ba ƙaramin faduwa yayi ba da ganin irin kallon da Mubaraka takeyi masa ya dake ya sanyawa kansa ƙarfin hali da juriya ya matsa kusa da ita yayi kissing kuncinta yace "wife kin tashi lfy"

Ajiyar zuciya tayi tare da kwantowa jikinsa tace "aa Lameer feel dinka nakeji kusan wata uku an tafi huɗu baka kulani nikam don Allah yau kayi wani abu"

Zama yayi kusa da ita yana wasa da hannunta yace "gashi ina sauri zan tafi Lagos ki bini bashi idan na dawo zanyi miki yanda kikeso kinji tawan?"




Miƙewa tayi a mugun hassale tace "kullum abinda ka iya faɗa kenan kullum kai a cikin kawo uzuri kake Lameer waini kai kafi kowa uzuri ne a duniya ko kuwa me kamayar dani babufa dole a cikin auren nsn matsawar bazaka iyaba nikam dai na gaji Lameer dolene wlh a yau dolene kodai ka saukemin haƙƙina ko kuma duk abinda zai faru ya faru"

Hannu ta ɗora aka ta rushe da kuka tare da sakin Fadwah dake hannunta tace "nikam nashiga ukuna wai wanne irin miji nake aurene Lameer na gaji gaskiya na gaji"




Yanda take mgnr yayi matuƙar sanyaya masa jiki a ransa yake raya abubuwa da yawa miƙewa yayi ya isa gareta yasa hannu ya ɗauketa cak ya nufi ɗakin baccinsa dake sama ya azata bisa gado ya sake fita ya ɗauki Fadwah ya kaiwa nannyn ta ya koma saman gabansa na faɗuwa saboda sometimes idan tayi masa wannan tujarar dasun fara zatace ita kawai jagwalgwalata yakeyi baya iya gamsar da ita, wannan ne yasa yakejan jikinsa daga gareta.




Juriya ya aro yasawa kansa ya nufi dakin ya cire rigarsa ta wani kafesa da ido har wani lasar lebe takeyi saboda a buƙace take dashi, kyawun surar mijin nata yana mugun ɗaukar hankalinta takanji dama shine Allah ya bashi ƙarfin ƙaninsa da tafi kowacce mace saa.

Haurawa yayi gadon ya janyota jikinsa abin mamakinsa hatta cire komai nata tasa hannunta a gabanta sai wasa takeyi dashi, shima sanya hannunsa yayi akan nata ya tura yatsansa ciki yana juyawa a hankali yana matsa nononta tare da murzawa yana hura mata  iska a kunnenta.




Haka ya rinƙa sarrafata da ƴan dabarunsa har saida yaga ta fice daga hayyacinta alamun gaf take da release sannan ya buɗata ya shigeta taja wani numfashi tanajin wutsiyarsa har ƙirjinta komansa na jarumai ne hatta joystick  ɗinsa itama ta jaruman maza akayi masa amma ina babu fus.

To wannan karon yayiwa Mubaraka abin arziƙi tunda yayi nasarar sata tayi release a cikin minti biyar ɗin daya takura kansa yayita saboda ƙarshen gejin daɗewarsa kenan akan network.

Ƙamƙameshin da yaji tayine ya sanyaya masa rai yasan yau ya ciri tuta yau babu tujara.




Miƙewa yayi ya koma gefe jikinsa na rawa ya lumshe idanunsa yana ayyana abubuwa da yawa a ransa mafarkinsa kawai ranar da zasu kasance haka da Hauwansa ranar da zai shayar da ita daga ruwan jikinsa itama ta shayar dashi ranar da zai bare dal a kwali shikam wannan rana wanne irin farin ciki zai kasance a ciki?

Abinda yaketa saƙawa kenan a ransa har zuwa wani lkc daya gama hutawa ya matsa jikinta yace "bakicemin kin gode ba" wani takaici ta shaƙa tace "dan kanabin mutum bashin million ɗaya ya dauki dubu ɗaya ya baka shine zakayi masa godiya?"............





_Ƴan VIP kuyi hƙr dani inada patient ne shiyasa baku jina yanda ya kamata amma idan na zama normal zaku jini insha Allahu._



_Kuma mgn ta Allah ma kun rage comments daga VIP din har single din saboda haka zaku iya jina nima nayi muku shiru gsky kowanne sashi Ina kallonsu mutane ƙalilan keyin comments🤷🏻‍♀️_






*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[7/1, 11:00 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*19*

_____________________________




________📝Kwanan Jiddoh uku tana kwance batada lfy saboda baƙin cikin abinda Baffa yayi mata sannan ta fara murmurewa, ranar data fara samun sauqin ranar baffanta yace saita dauki nono ta fita talla.

Babu yanda zatayi haka ta dauka tana tafiya tana hutawa har ta isa inda ta saba zama ta zauna cikin saa kuwa tana zama wani driver yazo ya siye nonon nata ta sake daukar hanyar komawa gdan yanzun ma hutawa takeyi.




A qofar gdan ta tarar da wasu manyan mutane su hudu jikin wata mota, Dan tsayawa tayi daga nesa tana qare musu kallo itadai bata hango wani idon sani ba don haka ta nufi qofar gdan a tsorace.

Har taje zata shiga taji an Kira sunanta ta tsaya cikin faduwar gaba tare da juyawa, ajiyar zuciya ta sauke tace “Kabiru ya kwana biyu bana ganinka a tasha?" 

Murmushi yayi yace “qlau wlh Ina birni ne yau din ma rakiya nayowa wadannan iyayen nawa gurin baffanki kuma tun dazu muna jiranshi bai fito ba" 

Kada kai tayi tace “Allah sarki sannunku da zuwa shanuwa zaku siya?" Muneef ne ya zuba mata ido yana kallonta tun daga sama har qasa yanajin wani abu na sukar zuciyarsa game da yarinyar.





Ganin yanda ya kafeta da ido ne yasata saurin janyo dankwalin kallabin dake kanta ta rufe qirjinta itama tana kallonsa yana fuzgar kama da Kadonta saidai yafi Kado hasken fata shi farine Kado kuwa wankan tarwada ne.

Numfashi ta sauke tace “Bari na kira muku shi qila yana galke ne" juyawa tayi ta shiga ciki tana juya jikinta daya zama halittar ta Alh Ali mahaifin Lameer yayi murmushi yace “Banda fitina irinta Lameer duk matan birni ya rasa wacce tayi masa sai wannan yar mitsitsiyar yarinyar wannan shekara nawa zaiyi yana rainonta kafin gidadanci ya saketa"

Murmushi Alh Yahya yayi yace “amma ai yarinyar takai asota din ta qeru sosai nikam zanyiwa dana murnar samunta" lkcn da Baffa ya fito yana muzurai lkcn muneef ya hadiye wani yawu me daci saboda samu da rashin daya gani a take qiri² ga kayan dadi yagani amma babu damar ci tunani yakeyi wai meye yasa guy dinnan yakeyi masa shigar sauri haka shi duk wani abu me kyau nasane?





Kamar abin arziqi baffa ya saukesu a bukkar baqinsa harda damo musu fura suka shiga suka gaisa suna kallon kallo tsakaninsa da Alh Yahya duk da Baffa yana kokwanto kan kasancewar shine ko akasin hakan.

Gaisuwa sukayi ta mutunci kafin daga bisani Mal Yahaya ya nutsu yace “Ardo Jibo nasan ni ba boyayye bane a gurinka kasantuwar kasanni tunda jajayen sawu lkcn da na nemi auren qanwarka kuka hanani to alhmdllh mun yarda matar mutum kabarinsa ba tuntuntunin bayane ya kawomu ba,

Yanzun ma wata alfarma mukazo nema ta gaisuwa gami da roqon iri, wato Allah cikin ikonsa ya hada danmu Muhammad Lameer da Yar wajenka Hauwah har soyayya ta qullu sukaji suna buqatar zama da juna a matsayin ma'aurata wannan dalilin yasa yaron nan Lameer yaje ya samemu akan muzo mu sameku idan Allah yasa bakuyiwa Hauwah miji ba kuma yanada rabo to a yarda ya shiga sahun masu neman aurenta mudai a shirye muke damu bawa danmu damar auren yarku badon komai ba saidon yauqaqa zumunci da kawo qarshen wannan sa'insa da taki ci taqi cinyewa"





Wani mugun murmushi Ardo yayi ya murza gashin bakinsa ya furzar da iska yace “kambale amma kukam kwai yan neman tsiya to daɗa ɗannaku bai faɗi muku abinda yakeyi da ɗiyata ba? Nikam naga bala'i to bari kuji nidai bani bawa watsattsen yaro kamar ɗanku yata hasali ma nayi mata miji ɗan asali kuma idan birnin ma takeso shima ɗan birnin ne tunda acan yake neman kuɗinsa, ba irin ɗanku watsattseba daya lalatamin ɗiya ba saboda  janta da yake yana lalubeta yana koya mata iskanci gashinan kuna gani yarinya ƙarama me shekaru goma sha huɗuta ganɗame ta zama uwar mata dubi uban nonuwa kamar a tatsa a siyar dubi iyayen mazaune"🤔





Kuka ya farayi harda sanya hannu ya tare idanunsa yana fullanci yana faɗin "daɗa Allah ya isa tsakanina da wannan yaro kuma aradun Allah ku hwaɗi masa babushi babu Jiddoh idan ba haka ba zaiyi ta ransa tarnatsa bakwai wai yaron nan har kuɗi ya bawa yarinyar na jaka dari uku da hamsin nidai kam aradu ya cuceni dayace yanason irina kuma ku ƙara fada masa matsawar bai haƙura ya ƙyalen ɗiya ba to zan haɗashi da hukuma nariga nayiwa yarinya miji yazo duk ya dagulam komi...."

Yanda yake mgnr ya lalata masa yarinya yayi bala'in ɗaurewa iyayen Lameer ɗin kai harma da ƙaninsa Muneef musamman Muneef da yasan gwaramar dake tsakaninshi da matar ɗan uwan nasa, shima mahaifinsu Alh Ali mamakine ya hanashi mgn kasancewar shekaran jiyan nan hajiya take cewa dashi ya nemawa ɗansa magani indai zai ɗaure masa gindin ya ƙara aure saboda shiɗin ba namiji bane.





Ficewar da Baffa yayi ne yana faɗin idan kun gama ku rufo nikam nayi nan innah tagaida assha.

Suma miƙewa sukayi kowa zuciyarsa babu daɗi amma banda Muneef da yakejin kamar sallah saboda murna yana ayyana ta yanda zai fara zuwarwa Jiddoh shima ya kwashi nasa rabon, mota ɗaya Kabiru da Muneef suka hau Mal Yahya da ƙaninsa Alh Ali suma daya suna tafe suna tattaunawa Alh Ali yace.

"Amma nayi mamaki matuƙa da wannan bawan Allan yace Lameer ya lalata masa yarinya naga shi ba yarone me kwarafniya ba dama Muneef ne toda bazan jaba duk da baa shaidar ɗan yau amma zaka iya gane halin kowa "




__________Shikam baffa yana fita gidansu Madi ya nufa yayi saa ya tarar dashi a ƙofar gida yana ganinsa ya ɗaure fuska amma ko a jikin baffa ya matsa ya zauna kusa dashi yace "yaro kayi hqr a rufawa juna asiri ka auri Jiddoh har shanuwa zan baka da bujumin sa kada ka tsaya duba cewa idanta ya buɗe kaima ai idonka a buɗe yake ince kaine kayiwa indodo ciki ta gudu burni har kake binta canɗin ince ɗanda ta haifa kaine ka shaƙeshi ya mutu saboda yayi kama dakai"




Miƙewa madi yayi cikin hassala yace "to seme idan nine ƴarkace aradun Allah bazan aura ba duk mazan garin nan sun santa sun dumbuli nononta gashi ta girma ta ganɗame a gabanku tasan komai sannan wannan ɗan burnin ya gama ƙwaƙuleta kwanaki a gabana ya rinƙa sumbarta yana mulmula nononta sannan kuma ni a kwaso a liƙamin ragowar wani wama ya sani ko yanad ƙanjamau ya liƙa mata nima ta mannamin"

Miƙewa Arɗo yayi yace "ba zuwa nayi kacimin mutunci ba koda yake Jiddoh ce tajamin kada ka damu madile zanje na samu Arɗo Bukar nasan shi dama yafison auren irin waɗannan yaran ina faɗi masa zai saki wata cikin matansa ya bawa Jiddoh ɗakin"







*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[7/1, 8:50 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*



_____________________________

*20*

_____________________________




____________📝Tunda suka dawo gda Lameer yake Kiran Alh yaji yanda sukayi da Ardo jibo amma sai yakeyi masa hanya hanya yake cewa dashi ya bari ya dawo tukunna sai suyi mgn.

Todai yana zaune ne a Lagos amma bayajin dadin komai zuciya taqi nutsuwa.




Shikuwa Muneef duniya ta samu Yaya bayanan yana yaye matar Yaya dashi da Mubaraka duniya sabuwa, ko aiki ta daina zuwa saidai idan gari ya waye a shirya Fadwah akaita gurin Hajiya aja labule a zuge ita da qanin mijinta yaita aikatata yana aika Mata da wutsiya.

Idan ya gama ta zai tafi kuma ta cika masa aljihu da kudi, mafi yawan lkc ma a gidan yake kwana su kwana suna ihun dadi sy kadai a gda sai yanda sukayi.




Yauma suna falo sun baje babu komai a jikin Mubaraka sunata lashe lashensu suna zuba soyayya kamar baza  mutu ba suck dinta yakeyi na tashin hankali tana nishi tana qara bude masa shikuma yana qara tura kai yana mulmula nononta ya dago kansa yace.

“Baby kinsan wani Abu?" Kada masa Kai tayi da shigar rashin mayar da hankali yayi murmushi yace “ashe bamu kadai mukasan dadin harka ba shima mijinki yana tabawa shiyasa baya kulaki"




'Dagowa tayi da sauri tace “me kakeso kacemin Muneef?" Hannunsa yasa ya qara kwma nipples dinta yace “wai bai fada miki yana neman aure ba?" 

Zaro ido tayi da sauri tace “What?" Murmushi yayi yace “tabdi Amma mijin nan naki yakai maci amana to wallahi aure yake nema wata kucakar yarinya yar fulani baki gantaba yar shila da ita da kadan tafi Fadwah shekararta 14 babanta yace amma ya gama da ita ya budata bakiga manya kaya ba nononta daya yayi naki biyu ga duwawu ga hips gata kamar ita tayi kanta ke nifa da naganta wlh penis dina wani tsalle tayi ta miqe nafi awa biyu bata kwanta ba....."




Hankade tayi ta miqe zatabar gurin yayi saurin janyota jikinsa yace “haba beb kada muyi haka dake keda kike Dani meye na damuwa da wannan ragon mijin naki....." Daga masa hannu tayi zuciyarta na tafasa tace “ya isa haka Muneef ni dama na dade Ina zargin haka na dade Ina tunanin Lameer cin amanata yakeyi shiyasa bai damu dani ba musamman yan watannin nan" 

Sake riqota yayi yace “to kema ai cin amanarsa kikeyi sai me yayi kiyi kadai ki manta dashi muci gaba da shagali itama waccan qaramar alhaki. Idan ya kawota nasan ni ya aurowa saboda da ganinta zata kawo fire" 




Wannan rana dai Muneef kasa samun kan hajiyansa yayi sai daqyar ta yarda sukayi sau daya saboda kishin mata ya motsa shikuma yana qara zugata akan tayi masa rashin mutunci kada ta yarda da wannan cin amanar abinka da wanzami baison jarfa take tadau saiti harda daukar waya ta Kira Lameer.

Bugu uku tayi ya daga tace “hello Lameer yaushe zaka dawo?" Cikin yarda da kuma sanyin jiki na alamun damuwa taci rabin jikinsa ya sauke numfashi yace “gobe Insha Allahu Hauwah me kikeso na taho miki dashi? Gurinki zan fara zuwa wlh nayi missing dinki fiye da tunaninki" 




Tashin hankalin da bata taba shigaba taji ta shiga batasan sanda tayi jifa da wayar ba tace “Hauwah kuma wace Hauwah Muneef?" Cikin nuna rashin damuwa yace “bafulatanar karuwarsa mana kinga hakan ya isa ya tabbatar miki bakya gabansa itace a qasan qalbinsa ko yarku bai tambaya ba Hauwah yake tambaya gsky matarnan kina ruwa har saman goshi"

Miqewa tayi ta shiga safa da marwa tanajin wani tuquqin baqin ciki yana taso mata “komawa tayi ta rushe da kuka tace “Muneef akwai matsala aure Lameer zaiyi amma Hajiya ta munafurceni bata fadamin ba saboda ba ita ta haifeni ba ashe soyayyar da take nunamin ta banza ce hqrn da take cewa nayi duk naa cuceni ne ina bazai taba yuwuwa ba Muneef dole asan abinyi idan yayi auren nan asirinmu tonuwa zaiyi...."




 Rufe mata baki yayi yana murmushin gidan boss yace “saidai naki ya tonu amma ina tabbatar miki ni nawa a rufe yake kuma murna zanyi idan kin tafi gantalun bin mazanki shi kuma ya tafi nemomin kudi ni inada wata a gdan zanzo kota qarfi nayi ban ruwa"

Yana gama fada mata haka ya miqe ya sake cafkota kafin tace zata kwaci kanta ya fara caccakarta babu yanda zatayi haka ta biye masa sukayi aikinsu suka gama.

Sukayi wanka ya dauketa a mota saboda cewar da tayi zataje taga Hajiya, har harabar gdan suka shiga yayi parking ta fito shima ya fito suka jera kamar shine mijin suka shigo ciki Hajiya na ganin haka ta daure fuska don batason shigewa junan da sukeyi gudun abin Allah wadarai saboda sarai tasan halin Muneef yanzu ma fama takeyi dashi akan neman Mata.





Zama sukayi yace “bansan meye yasa Hajiya bakya sona ba babu dama ki ganni da matar Yaya sai kin kawo wani Abu a ranki an fada miki ni Dan akuya ne da yayana zaiyi fito nima nayi haba haba Hajiya meyesa kika gurbata tunaninki akaina ne?"

Shafa fuskarta tayi tace.

“Autana kai dinne rawar kanka tayi yawa nikam kafidda mace mu killace ka" dariya yayi yace “wa waini? Haba Hajiya aini saidai a auro min" bata gane me yake nufi ba ta tafi ta kama Ina ka saka Ina ka aje da Mubaraka ta cika Mata gabanta taf da kayan ciye² sannan ta zauna tace.




“Ashe kina tafe yanzu mukayi waya da ja'irin yaron nan me neman mgnr tsiya baicemin zakizo ba?" Turo baki gaba tayi tace “dama ya zaayi yace miki zanzo yayimin laifi" rushewa tayi da kuka nandanan hankalin hajiya ya tashi ta shiga sallalami tace “meye ya faru yarnan na shiga uku ni jikar me sabulu" 

Karkacewa Mubaraka tayi tace “ashe Hajiya wulaqancin da Lameer yakeyimin ba banza bane ashe mace ya ajiye a duk inda yake zuwa jiya Muneef yake fadamin sunje nema masa auren wata yar fulani babanta yana cewa ya lalata masa ya da dare na kirashi muryarsa cikin wani yanayi yakw cemin Hauwah abin qasanki da dadi wlh saina aureki babu uban daya Isa ya hanani yana nishi yana cakal² dazu kuma na kirashi wata ta daga take cemin bacci yakeyi Hajiya Yaya zanyi me nayiwa Lameer yakeyimin wannan izayar....."





Ta qarasa mgnr cikin gunjin kuka na son ita sai an gasqatata, sallalami Hajiya takeyi tare da Dora hannu aka tace “naga takaina ni jikar me sabulu dama biri yayi kama da mutum ashe abinda yakeyi kenan shiyasa ya massheke TV abar adon gida kawai yanzu abinda Lameer ya koma kenan"

Shiru ce ta ratsa kafin daga bisani Hajiya tace “to yarnan kodai bakida dadine"😂 saurin dagowa sukayi tace “eh kinsan akwai abinda idan dandano bayi masa ba baya miqewa nidai naga abar Lameer da kaurinta da tsayinta to bayan ya girma ta lalace ne ko kuwa a gurinki ne qur'anin Allah kota auta batakai tashi ba balle ta yayansu dake England shikam tashi yar quininiyace"…………….







*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[7/2, 8:05 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*21*

_____________________________






___________📝Da sauri Mubaraka da Muneef suka kalli juna Muneef yace “haba Hajiya ba wannan zancen kawai dai kiyiwa danki fada yasan darajar iyalinsa kuma yasan girmansu yamayar da hankalinsa kansu ya daina leqe²"

Numfashi Hajiya ta sauke tace “shikenan ki tashi kije idan yazo zai gamu dani har ubannasa da yake daure masa gindin iskanci zaizo ya samene ba bagulatana ba ko rugace sai taci ubanta a gurina"




Miqewa Mubaraka tayi ta shige dakin Hajiya ta dauko yarta ta fito ko sallama batayiwa Hajiya ba saboda takaici itakam ta rasa wacce irin uwar miji ce da ita da indai ka kawo Mata qarar danta sai ta dawo da laifin kanka “wai ko bakya da dadine 😂”

Tana fita Muneef ya miqe ya bita daqyar ta shiga motarsa suka fantsama gari sune gurin shan ice cream da guraren shaqatawa.





Basu dawo ba sai wajen goma na dare suna zuwa suka zube a falon suka fara cin abinci bayan sun gama suka shiga wanka tare suka fito aka kira Nanny aka jorner ta da ita suka tafi dakinsu sukuma suka shige dakin Mubaraka.

Da farko taso tayi gardama amma yanda ya rinqa bi da ita yana shiga jikinta yana wani nishi yana kiran sunanta yasata miqa kai bori ya hau wadannan mutane akwai jarababbu Mubaraka haka takeso a kwana ana haqarta shikuwa Muneef dama hakan shine burinsa aikuwa aka kwana ana bawa shuka ruwa.




______________Da safe jirgin qarfe shidda Lameer ya biyo zuwa birnin dabo da farko yayi kamar yaje gda kawai sai ya wucce office ya had a reports na abinda ya kaishi Lagos yabada takardarshi ta transfer sannan yayi wanka anan ya huta.

Sha biyu ya dauki hanyar Rugar Sambajo zuciyarsa cike da nishadi zaiga farin cikinsa, saboda gudun da yakeyi tafiyar awa daya da rabi ce ta kaishi Alqalawa daga Alqalawa ya yanke burji ya nufi garinsu Jiddoh.




Nesa da gidansu yayi parking lkcn tana bayi tana wanka ta dawo daga tallan nono taji qugin motar, ta danga ta leqo taga motar cikin saa kuwa yana bude motar zai fito aikuwa tayi maza ta zari zaninta ta daura a qirjinta ta zura rigarta ta ta kama dangar ta tsalllake saboda tasan idan tace zata fita ta qofa bazaa barta ba.

Yana tsaye ya bawa gurin baya kawai yaji an masa cakulkuli ya dago da sauri suka hada ido taja da baya tare da qyalqyalewa da dariya tace.





“Na bashi tsoro Ina wanka naji tsayuwar motarka shine nayiwa su Baffa wayo na fito dama na matsu na matsu kazo ranan nan wani me kama dakai sukazo gdan nan yayita kallone nima nayita kallonsa amma fah kafishi kyau shi kodaddene kamar jan qosai"

Murmushi yayi a hankali ya sanya hannunsa ya riqo nata yace “Baffa ya yarda da mgnr aurenmu Hauwah?" Dagowa tayi tare da girgiza masa kai tace “ni bansani ba kawai dai naji yace wai gobe Ardo Garbati zai kawo shanuwar aurena....."





Rufe mata baki yayi da sauri jikinsa na bari ya jata yasata a mota shima ya shiga ya kulle ya zuge glass din yace “waye Ardo Garbati?" Kukan da take hadiyewa ne ya kwace Mata yayi saurin janyota jikinsa ta janye tace “ka kadaina tabani banaso iskanci ne" 

Kada Mata kai yayi saboda ya matsu yaji waye Ardo Garbati yace “ki fadamin waye Ardo Garbati?" Cikin kuka tace “baban su qawata larai ne  da Zahira da nayiwa duka karon wacca saboda sunce kai Dan iskane wai wai saboda Madi yace bazai aureni ba shine baffa yaje yace yabashi ni sadaka yabada shanuwa daya a daura aurena dashi"




Wata zabura yayi yace “kina nufin idan yabada shanuwa gobe shikenan zaa daura miki aure dashi?" Kukanta ta qarawa qarfi tace “kuma auri saki yakeyi matansa goma sha bakwai duka ya sakesu saura hudu a gdan to ya kuma sakin daya saboda zai aureni yayansa kuwa sun kusa hamsin bakaga kuma baya basu abinci kowa saidai ta nemi nata da kanta, jiyama da yazo wai yazo gurina tadi nikuwa nayi masa atule shine wai yace Allah yakai damo ga harawa wai sai yasa anyi mini dinkin qwary......"



Daga mata hannu yayi yace “ya isa jiddah muje ki rakani gurinsa" zaro ido tayi tace “kutqel tarnatsa bani zuwa Gwaggo ta hanani tace fyade yake yiwa yara" girgiza mata kai yayi yace “muje ki rakani babu me tabaki a gabana koda kuwa Baffa ne"

Dariya tayi tace “yaushe zamu tafi birni tare kasamin irin haqorin bakinka?" 

Yarfa hannu yayi tare da dukan kansa yace “oh my God luv kina wahalar dani muje na gama da wancan tsohon banzan tukunna sai muyi mgnr zuwanmu birni Hauwah naga alama sai na shigo da hukuma cikin mgnr nan sannan Baffa zai bani ke"




Wani murguda masa baki tayi tace “idan suka kamamin Baffana kuma fah?" Shidai bai kuma ce Mata komai ba saboda surutunta ya fara sashi ciwon kai yaja motar zaiyi ribbers tace “aa Tasha zamuje acan yake zama matsiyaci ne shanunsa uku duk ya siyar yayi aure"

Yanda yakejan motar cikin nutsuwa yafi komai bata sha'awa tace “kado itama zaka koyamin?" Shiru yayi Mata suna tafe tanata surutun ta har sukaje tashar Alqalawa sukayi parking ya fito itama ta fita abinka da qauye duk sai suka zama abin kallo.




Fusgo hannunta yayi ta wani tsaya ita a dole sai tayi abin yan birni sai kwarkwasa takeyi yace “dallah ki ware kiyi tafiya banson shirme" yanda yayi mata tsawar yasa ta nutsu har suka isa inda Ardo Garbati yake zama suka tambaya yananan akace eh ya zagaya.

Neman guri sukayi suka zauna bayan kamar minti goma ya fito yazo zai hucce caraf idonsa ya fada cikin na Jiddoh da taketa harararsa da murguda masa baki, murmushi yayi yace “oye amaryata aradun Allah Ina son tsiwar nan taki nan da jibi ma bazakiyimin itaba gishiri ya hau kan kaza"




Wani abune ya caki zuciyar Lameer amma sai ya dake ya miqa masa hannu suka gaisa yace “Mal Garba gurinka mukazo" shafa kansa yayi yace “to ai gani" kallon Jiddoh Lameer yayi yace “tashi kije ki jirani jikin mota" 

Sumsumsum ta miqe ta koma jikin motar tana ganinsu suna magana an yamutsa hazo sosai kafin haqan Lameer ya cimma ruwa sannan suka taso tare da Ardo Garbati Lameer ya kalli Hauwah yayi Mata murmushi ya bude mota ya dauko dumbujen kudi da shi kansa baisan nawa bane ya bawa Ardo Garbati yasa hannu ya karba da sauri yayi dariya yace “dama Kaine ka dace da ita Allah ya baka Jiddoh yarinya kyakkyawa me zamani".…………






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/2, 6:48 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*22*

_____________________________




____________📝Kama hannunta yayi yasata a mota ya shiga yaja suka tafi tanata zuba masa hira bata ankara da cewa sun fito daga garin ba saida taga sun dauki kwalta sosai sannan tayi shiru cikinta ya fara qugi ganin tafiya taqi qarewa yasata dago manyan fararen idanunta tace.

“Kado Ina zaka kaini nan hanyar inane?" Shiru yayi Mata baice Mata qala ba saima wani kallo da yayi Mata yayi ya kawar dakai.

Tafiya sai miqawa takeyi Jiddoh na qara tsurewa ganin sun yanke sun fita daga yankinsu yasata Dora hannu aka zata zunduma ihu yayi saurin kallonta tare da Dora hannunsa akan  bakinsa yace.




“Shitttt" dole ta hadiye kukanta ta rinqa jan zuciya tana rawar jiki saboda tsoro tariga ta ta saddaqar yau angama cinikin kanta dama Baffa yasha fada mata kanta zaiyi tsada.

Qwallah takeyi tana sharewa saboda gudun kada ya qara daka mata tsawa irinta dazun, batasan inda sukazo ba saida taji yayi horn ta dago firgigit kamar me bacci ta zubawa qofar ido cikinta na qara yawan kukan da yakeyi yana wani qulululuuuuu.

Juyowa yayi ya kalleta yayi murmushi yanda yaga alamun tsoro a fuskarta yayi bala'in qayatar dashi yace “gobe zaa yanka kannan naki jibi asha dabge"



Ai kafin ya gama mgnr ta fara kuka tana mammatse cinya saboda tsoron kada ta sakar masa fitsari a mota, Jan motar yayi da mugun gudu ya shiga cikin gdan gonar da gabaki daya dogayan bishiyun turare ne suka kewaye ko Ina na sai mangoro da gwaiba da zaitun gefe kuma dashen bishiyun zogale ne da auduga.

Bude qofar yayi ya fito itama ya bude Mata a zummar ta fito amma Ina ta tafi duniyar tsoro jikinta sai kyarma yakeyi, hannu yasa ya tabata yace “sauri nakeyi fito muje na kaiki inda zaki zauna kafin na dawo"



Kuka ta rushe masa dashi ta fado daga motar ta riqe qafarsa tace “don Allah Kado kayimin rai mutuwa mutuwa wayyohhhh mutuwa idan aka yankani a cinye naman jikina dama ance ku yan birni cinye naman mutane kukeyi shikenan Baffa shikenan Gwaggo......"

Dagata yayi cak yayi mata daukar jarirai ya nufi wata yar siririyar hanya da ita ya tura qofar ya shiga ya mayar ya rufe ya direta a saman kujera ya zauna a kusa da ita ya dago kanta yace “bakyaso nasa a yankamin ke?" Saurin daga kai tayi ya hadiye dariyarsa yace “ok tashi ki shiga dakin can kiyi wanka akwai kayan tsarabar da nazo miki dasu a mota zan kawo miki kisa idan kin fito kuma kici abinci kafin na dawo idan kikaqi ci aradun Allah sai nasa anyi gunduwa gunduwa dake da fatan kin gane?"




Saurin daga masa kai tayi ya miqe ya kama hannunta yace “ok muje na nuna miki bathroom din" miqar da ita yayi ya kama hannunta ya bude wani daki ya shiga tana rakube a bakin qofar har yakai bakin bathroom din yana Mata bayanin komai ya juyo yaganta tana mutsuniya a cikin labulen ta kasa budeshi wai ta shigo.🤣

Tsayawa yayi yana kallon ikon Allah yace “meyene kikeyi anan?" Shassheqar kukanta ta qara ya girgiza kai ya qaraso ya bude Mata tare da janyo hannunta yace “na fada miki banson kuka fah ko?"



Daga masa kai tayi yace “ok oya aje ayi wanka idan na dawo insha Allah komai ya daidaita da kaina zan wanke miki gashin nan" ajiyar zuciya ta sauke taja baya ta riqe qugu tace “cabdi kaji wani iskaro kuma kawai sai ka kama kaina ka wankemin aa yaseen nikam bazaayi iskancin nan daniba kuma ma aradu bazaka tafi ka barni a gdan yankan kaiba saidai mu tafi tare idan ba hakaba nayi arwala na hau ksn buzu nayi maka addu'a idan ka fita karka dawo ka makance ka kasa gane hanya"




Tunda ta fara mgnr ya qura Mata ido yana kallonta har saida tasa aya yaja numfashi yace “to je kiyi ina jirankin" neman guri tayi ta zauna tace “ni yar iskace da zanyi wanka dagani saikai a gdan salon ka rinqa leqoni..." 

Dariya yakeso yayi amma takaici ya hanashi dariyar sai daga wayarsa da yayi yace “eh nayiwa Baba Mai unguwa magana yace zaayi abinda ya dace yanzu nasan hisba sunje nima yanzu nake shirin komawa"



Kashe wayar yayi ya fita tabisa da sauri tana kiransa ko juyowa baiyi ba ya fice da sauri ya kulle qofar yaja motarsa ya fice ta zube a gurin tana shure² tana kuka tana jijjiga qofar Amma ta kasa budeshi hakanan ta miqe ta koma can gefe ta rakube tanata kukanta tana Kiran Baffa Gwaggo Inna Jumme.🤣

Kuka tayi sosai tare da kifa kanta a kujera a haka har bacci ya kwasheta itadai batasan meye ya faruba Jiddoh anji baqon guri A.C na ratsata sai juyi takeyi harta bingire a qasa tanata baccinta.




__________Yana fita a kwanar komawa garin yaci karo da motar Hukumar Hisbah tana fitowa daga lungun yayi parking Suma sukayi suka gaisa ya tambayesu ya akayi nan fa suka fara bashi lbr wani cikinsu yace “Ai ranka ya dade munsha fama da tsohon nan taurin kaine dashi saida mukayi dan qaramin yaqi don cewa yayi babu ubanda zai hanashi daurawa yarsa aure da  Barau dan jaji a cewarsa daya baka aure gara ya kashe yar tasa, duk wani bayani da kake tunanin zamuyi masa munyi masa qarshe saida muka gwada masa qarfi muka kirawo abokan aikinmu police wlh yana daura auren yana kuka wai an shusheshi an qwace masa yarsa zaa siyar da it's a birni, hmm waifa bayan angama mun qirga sadakin mun bashi munce ya riqe cewa yayi shi Allah ya tsareshi riqewa kuma itama yar ya sallamata tunda ance kaine ka saceta ka gudu da ita"




Ajiyar zuciya yayi cikin sanyin jiki yace “alhmdllh na gode sosai Allah yabar zumunci na gode sosai" komawa motar yayi ya dauko wani envelope ya suka karba sukayi masa gdy tare da qara jaddada masa cewa Ardo yace indai yaganshi ko yaga Jiddoh a saiya radesu da sanda.

Murmushi yayi yace “karku damu komai zaizo da sauqi insha Allahu burina kawai tseratar da yarinyar daga fadawa muguwar rayuwar da jahilci yake neman jefata insha Allahu zanyi qoqarin daidaita tsakaninta da iyayenta a lkcn da suka fahimci wacece ita suka gane kurensu na baya"



Juyawa sukayi suka nufi gdan daya killaceta suka shiga yanata washe baki kamar anyi masa busharar rahamar ubangiji.

Bude qofar sukayi suka shiga harda Amininsa Salees tare da sallama tana kwance tanata sharar baccinta, ya matsa gabanta ya tsugunna ya sanya hanunsa ya shafa fuskarta kasancewar batada nauyin bacci tayi miqa tare da banqarewa tana salati yayi saurin qara rufeta saboda riqarsu ce ta fulani iya cibiya a jikinta hatta cibiyarta a waje take.

Bude idonta tayi ta kalleshi Salees yace “Captain zamu iya tafiya tunda mun gama aikinmu? Ai bata jira yabada amsaba ta zabura zata miqe ya fincikota jikinsa kasancewar bazai iya bari aganta a haka ba yace “ke meye hakan ki nutsu kefa matar aure ce....." Wata bangaza tayi masa ta miqe kamar walqiya ta tsalllakeshi ta shige dakin ta kulle, ba Salees ba hatta yan hisbar saida abin ya basu dariya Salees yace “sunan wani littafi wai mijin qwaila kai yanzu duk izzarka akan mace wannan qaramar alhakin ce ta ruda duniyarka?"




Miqewa yayi yace “wlh itace har nakejin kamar bazan iya rayuwa ba in babu ita Salees cikin wata uku son Hauwah ya haukata duniyata ni yanzu banmasan ya zanyi da itaba shegen tsokana ta yasa nace gidan yankan kai na kawota"

Dariya sukayi sukace “haka zaka sauko ka zama daidai da ita ka rinqa yimata mu'amala irin ta shekarunta saiku daidaita kassan yaro abokin yaro ne" 

Miqewa yayi yaje bakin qofar ya murda ya shiga tana zaune nata kuka tana juya kai hatta kallabin data daure kanta ta cire ya matsa gabanta tanajin dumin jikinsa ta zabura ta miqe tayi baya a guje tana girgiza masa kai cikin sarkewar murya ta wanda yayi kuka ya gaji tace “nidai kada kabasu ni su yankani yanzu idan na mutu na dena ganinka na daina ganin Baffa na daina ganin Gwaggo na daina ganin Inna Jumme har Lamunde na daina gani"............





*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*

[7/2, 11:16 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*23*

_____________________________

_*BY*_

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________


Ajiyar zuciya yaja ya miqe ya matsa gabanta yace “ki nutsu kizo kiyi sallama dasu abokai nane tafiya zasuyi"

Noqe kafada tayi tare da qarayin baya yayi murmushin takaici yace “kedai bazaki daina shirme ba" juyawa yayi ya fita ta sake zama tana kukanta tana Kiran “wayyohhhh Gwaggota ya saceni barawon mutane ne Kado aradu bazan qara yarda na shiga motarka ba tunda kai azzalumi ne....."😂 




Turo qofar da yayi ya shigo da kayan abinci a hannunsa shine yasata qara miqewa ta tattare zaninta ta tura tsakanin cinyoyinta zuciyarta tana bugawa da qarfi saboda mugun tsoronsa da takeji.

Ajiye kayan yayi ya nufeta ta janye ya qara nufarta ta janye ya tsaya yana kallonta yace.

“Dagani saike zamu kwana a gidannan idan kika wahalar dani nima zan wahalar dake" yana fadin haka ya janyota ya mannata da jikinsa.





Ta cure tare da dungulewa guri daya tana tureshi tana kuka na fitar rai mai gunji tana yaqushinsa tana cizonsa, sakinta yayi da sauri yana fuzgo numfashi daqyar saboda gashinta daya nadi manshanu babu abinda yakeyi sai qarni da tsamin dauda.

Sake fuzgota yayi ya daga hannunta da qarfi zai zare Mata riga ta qamqame tana kuka tana girgiza masa kai amma baiko kulata ba ya hade qarfinsa ya cire rigar ya koma zai kunce zanin tayi saurin durqushewa ta qara qanqame qirjinta tana kuka tana fadin “Allah ya isana mugu azzalumi bazan taba yafewa ba indai ka qara kallonmin Inninina"





Dafe kansa yayi yace “oh God Hauwah damuwa ce ke gabadayanki nace kiyi wanka bakiyi ba kinmaji yanda kanki yake qarnin manshanu kuwa nace miki banasonsa shiyasa na siyo miki shampoo da mayukan gashi Amma baki daina shafawa ba to wlh yau ko ki bari na tayaki ki wanke kanki ta dadi ko kuma na gwada miki qwanji kinsan dai zan iya"

Murguda masa baki tayi tace “tarnatsa muliyan bazaka wankemin kayina ba saidai kasani a turmi ka kwakwatsa ka niqa ka soya kayi dambun nama Dani...."




Wata uwar wawura da yayi Mata yasata wani juyi a tsakar dakin ta shige qarqashin resting chair abinta da yake dakin babu gado katifa ce number one maigida sauko mu gaisa sai wardrobe ta jikin bango sai tv da lamp kawai.

Takaici ne yasashi zama kawai dirshan yana kallonta shi yama rasa ya zaiyi da gidadancin yarinyar, miqewa ya sakeyi ya bude qofar ya fita ya koma wani dakin ya dauko belt ya dawo har yanzu tana qarqashin resting chair din sai uban gumi take hadawa.





Matsar da kujerar yayi sai gata shanye gaho a qarqashi tanata faman muzurai rungume da qirjinta yayi saurin kashe fitilar ta miqe da sauri tana shassheqar kuka tana wawuren inda zata kama kawai sai jinta tayi a jikinsa.

Dama hakan yakeso aikuwa ya dagata cak ya nufi bathroom din da ita ya bude ya shiga nan din haskene sosai ya sauke idonsa akan lallausar fatarta me santsi da sheqi yaja numfashi ya direta yace “cire zanin nan kafin na zaneki" 




Bude idonta tayi zatayi rashin kunya taga zabgegiyar bulalar dake hannunsa aisai ta nutsu tana kuka jikinta na rawa ta kunce zanin ya rage daga ita sai dan kamfe kawai saita durqushe tace.

“Wayyoh ni Allah ka ceceni Allah ka ceceni hannun wannan mugun bawan ko Gwaggo na bata taba ganina a hak......"





Tsawa ya daka Mata data sata sakin fitsari a zaune ta sakeyin zaman yan bori ya matso ya tsugunna gabanta yace “tashi ki cire wannan munafukin wandon na jikinki" 

Saurin kada masa Kai tayi tace “aa nidai Kado bazan iya ba kaje kawai ni ka fitama zanyi wankana" murmushi yayi yace “kin makara yari ya tun sanda nace ki tashi kiyi da kinyi da ba wannan zancen akeyi ba nifa yanzu zabi zan baki dama na gama cinikin kanki har nabawa Gwaggo da Baffa kudin kina cika yimin musu zan Kira mutanen nanna dazu du fedemin ke..."🤣




Ai bai ida rufe bakinsa ba ta miqe ta zare wandon tayi qasa zata zauna yayi saurin tarota yanajin faduwar gabansa na qaruwa, by mistake hannunsa ya dunguri nononta ai sai ta qwallah qara tace.

“Wayyohhh zaiyimin adumbuli nashiga ukuna shima ashe irinsu Rubado ne wayyohhhh mutuwa shikenan ni nasan tunda ma bakabadani an yankani ba mutuwar ma dolene garama a yankani a gasani a cinye amma nidai wasiyyah ta idan an yankani akaiwa su Gwaggo kai da qafa.........🤣🤣🤣🤣






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/3, 8:13 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M L*

_____________________________

*24*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________




__________📝Wani irin haushi ne ya cikansa zuciya ya kamota ya dagata cak tana zillewa tana koke kokenta shikuma yaqi sakinta saida ya kaita cikin bowl din yana shirin sanyata ta qanqameshi tana cewa “wayyoh Kado ruwan gudu yakeyi kada ya tafi dani ya cinyeni"

Hannunsa yasa saman bakinsa yace “kada ki qara yimin mgn idan ba hakaba da kaina zan hukuntaki" aikuwa kamar ya dinke bakinta haka tayi masa shiru ya sanya hanunsa ya ware gashinta me mugun tsayi da santsi gashi baqi wuluk sai rashin gyara ya dauka shampoo conditioner ya matsa Mata akai ya sa ruwa kadan ya rinqa wankewa.





Wani mugun datti me kauri ya rinqa fita ita kuma tana qara shigewa jikinsa saboda yanda yake cakuda gashin nata da hannunsa wani irin yanayi takeji a jikinta.

Bai qyale kanba saida yaga digon datti ya daina fita kumfar ta koma fara sol sannan ya dauraye Mata ya dauko turaren gashi ya fesa Mata ya bude hanyar ruwan ya fita ya sake hada mata wani yace “shiga" noqe kafada tayi ya zare mata ido ta sake ja da baya ya matsa ya cafki hannunta da qarfi ta saki qara yace “zakiyimin bayani ne wai ni kikecewa dan iska ko zan nuna miki kalar nawa iskancin"





Yana fadin haka ya dagata yasata a ruwan ya dauki soso da sabulu me mugum qamshi ya fara wanke mata fuskarta ya fara saba mata jikinta ta hade cinyoyinta sannan ta maqale nononta da hannunta.

Shikam abin ma dariya yake bashi wai abinda ya biya sadaki da shaidu aka daura aure aka shaida halalinsa ne shine ake hanashi tabawa.

Murmushi yayi ya sanya hannunsa ya bude hannunta ya zubawa manyan boobs dinta ido yana hadiyar yawu a hankali yanajan zuciya cikakku tsayayyun nonuwanta suna sanyashi yanajin wani yanayi a jikinsa a hankali ya furta 14 years"





Miqewa yayi saboda tsoron kada ya zaqe yace “ki qarasa wankan ga towel ne ki tsane jikinki ki fito kizo muci abinci" harara ta galla masa ya girgiza kai ya fice, wasa² tafi minti talatin tana wankan sannan ta dauki towel din tana juyashi a jikinsa ganinsa fari tas yasa taqi sashi a jikinta a haukanta wai kada yayi datti yace ta bata masashi.

Kusan minti biyar ta qara kafin jikinta ya bushe ta dauki zaninta ta daura ta sake neman guri ta tsaya wai a dole kunyar fita takeyi a haka Shiru din yaji tayi yawa ya miqe ya nufi bathroom din ya bude furzar da iska yayi ya kamota ya janyota jikinsa ya hadata da qirjinsa ya zare zanin a hankali.




Ya sauke numfashi yace “meye yasa kika daura zanin nan Mai datti?" Sake lafewa tayi a jikinsa yayi kissing tsakiyar kanta yace “kinason dole saikin doramin damuwa ko?" Sakeyin Shiru tayi tana shassheqar kukanta, ya Kuma cewa muje nariga na zaba miki kayanda zakisa ki shirya muyi sallah  muci abinci mu kwanta dare ya fara kinga har goma ta wucce"

Dagata yati kamar jinjira ya fito da ita ya zaunar da ita saman wata stool ya fita da sauri ya bude motarsa ya dauko wata qatuwar akwati da daya hado mata tsaraba ya koma cikin gdan.





Tananan zaune inda ya ajiyeta kamar an girkata yayi Mata murmushi yace “nonon nan mallakina ne amma sai rufeshi kikeyi Hauwah meye yasa kinsan dai komai dake jikin mace  halal ne a gurin mijinta ko?" 

Turo baki gaba tayi tace “aikai barawo ne satoni kayi daga Rugarmu kuma aradun Allah bazan rufa maka asiri ba saina fadawa kowa satoni kayi"

Tsuke fuska yayi ya bude akwatin ya dauko hand drayer ya ajiye ya sake dauko tarkacen ribbons ya daukar mata wasu qananu biyu ya dauka Mata turaruka da man shafawar da yake ganin zai dauki fatarta bayan ya gama da wannan ya dauko mata wata yalolowar rigar bacci yaluwa ya ajiye Mata ya rufe akwatin ya jingineshi a gefe.





Matsawa yayi ya jorner hand drayer din a sucked ya nufota ta miqe da gudu zata bar gurin yace “dallah koma ki zauna banson qauyanci" komawa tayi ta zauna jikinta yana rawa yasa drayer din ya fara busar Mata da gashinta ita kanta iskar jikin drayer din me zafi zafi dariya ta rinqa bata ta rinqa qanqameshi tana shigewa jikinsa.

Shima dariyar yake tayata nan suka shagala da shirmensu tanayi yana biye Mata hardai ya samu ya gama gyara Mata gashin yasa ribbon ya daure matashi a qasa ya sauka har qasan duwawunta yaja numfashi tare da fadin “Masha Allah" 





Mai ya dauka ya fara shafa Mata daga qafafunta ya faro kamar abin arziqi har yazo tsakiyar cinyoyinta batace qala ba ya tura hannunsa tsakanin cinyarta ya fara shafa Mata har zuwa tudun pupsy dinta ta kuwa ture hannunsa ta bata fuska tace.

“Wato oye abin yayi maka yawa bayan satar mutane harda kwartanci kakeyi ko tabdi aradu dani gyatumarka ce irin yanda ake yiwa Dan akuya dandaqa haka zansa wanzamai su dandaqeka" sosai ransa ya baci da kalaman yarinyar amma ya zaiyi kowa yasai rariya yasan zatayi yoyo shidai addu'arsa shirmenta da wautarta ya tsaya iyakar shi kadai.





Hakanan yayi banza da ita tanata surutanta bai tanka mataba saida yazo saitin qirjinta sannan ya dago idanunsa da suka kada sukayi ja ya zuba Mata tare da dora hannunsa akan duka biyun ya kama ya fara shafawa a hankali yana sauke numfashi.

Zari ido tayi waje yayi saurin janye hannunsa yana sauke numfashinsa daqyar saboda wani baqon abu da yakeji a jikinsa yace “sorry tashi kisa kayanki" 





Noqe kafada tayi tana qoqarin yimasa kuka yace “wlh kikayimin kuka saina buda gindinki nasa miki bindira" saurin hadiye kukan tayi yace “oya tashi kisa riga muyi sallah ko isha banyi ba gashi har 11:00pm"

Yana fadin haka ya miqar da ita ya dauki rigar ya sanya mata rigar ta kuwa kwanta a jikinta tayi luf da ita iyakarta cinyoyinta yaja numfashi a hankali cikin saukar kasala yace “barakallahu ahsanal khaliqil"

Zunburo baki tayi tace “ni kada ka zageni da yaren da banaji qur'anin Allah ramawa zanyi kaji in fada maka eheeee"




Kallonta yayi da mugun sanyin jiki yace “ke wai bakya tsoro nane duk girman Mubaraka tana tsoron fadamin wata mgnr amma bandake?" Tabe baki tayi tace “wace Mubaraka?" 

Janyota yayi jikinsa yace “yayarki ce Ina nufin uwargidanki"zaro ido tayi waje tace “kutqel uba dama kanada mata?" Murmushi yayi yace “inada Mata harda yarinya ta daya gobe insha Allahu zan kaiki kigansu har gurin mamana da yayata ta qanwata zan kaiki ku gaisa kafin mu wucce Lagos nan da sati daya"





Hijjab yasa Mata yace “muje muyi sallah" sallah sukayi kamar abin arziqi bayan sunyi isha sukayi nafila raka'a biyu yayi musu addu'a sosai ta neman albarkar auren nasu tare da kama kanta yayi mata addu'o'in zaman lfy da samun kwanciyar hankali me dorewa sannan sukayi shafa'i da wuturi.

Hijjab din ya cire Mata ya ya janyo ledojin daya shigo dasu ya bude ta zaro ido tace “lahhhh Kado kazace wannan kaga harda cinyarta kuma naga ansa Mata kayan miya? To Ina Kai da qafar? Allah sarki kaza baiwar Allah itama zalincinku bai barta ba an mayar da ita gurguwa".................🤣🤣🤣🤣😂😂😂😂





*UMMUH HAIRAN CE...✍️*




[7/3, 3:40 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*25*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________





_________📝Cire hannunsa yayi daga abinda yakeyi ya zuba Mata ido duk wannan uban surutun da takeyi idonta ruwa yake zubarwa, girgiza kai yayi ya gyara zama ya yago naman yakai mata bakinta ta kawar dakai ya Kira sunanta ta dago yayi ajiyar zuciya yace.

“Duka zanyi miki idan bakici abinci ba banson qananun iskanci" ai kamar ya zugata ta sake rushewa da kuka taja da baya tace “ni wlh bazanci ba ni tausayinta nakeji"

Wani takaici ne ya sashi zama kawai yayi watsi da iskarta yaci namansa sosai saida yayi hani'an sannan ya miqe ya shiga bathroom yayi brush.





Dawowa yayi ya debe kayan dake gurin ya fita dasu ya shiga dayan dakin ya cire kayansa ya rage dagashi sai boxes ya nufo dakin hannunsa dauke ta bottle na ruwan swan ya bude qofar ya shiga.

Tana zaune inda ya barta ta ta dunqule guri daya tanata rawar sanyi ya kalli A.C yaga a qure take ya matsa ya rageta ya kashe glub ya kunna deem ya matso gabanta ya sanya hannunsa ya dagata ya dorata a katifar yana shirin kwanciya ta wuntsilo daga katifar tana wani haki kamar wacce tayi gudu, fasa kwanciyarta yayi ya zuba Mata ido.





Miqa Mata hannun yayi taja da baya yace “kizo mu kwanta dare yayi" wata alkafura tayi taja baya tace “waye zashi kwana dakai? Tabdi kai kanama rainamin hankali godode dakai na kwanta tare dakai ni kama fita daga dakin nan bazan kwanta da qato a daki daya ba salon tambarin iskanci ya fitomin a goshina.

Wannan karon yarinyar ta kaishe qarshe saboda haka ya matsa zai kamota ta janye ya qara matsawa ta janye har saida sukakai qarshen katifar ya tunkudata kai yabita zai danne ta mirgine gefe jikinta na rawa ta rushe da kuka tace.





 “Ni kada ka fado kaina ka karyamin kwankwaso don Allah ka tashi ka fita bazan iya kwana tare dakaiba" miqa yayi ya gyara kwanciyarsa yace “babu inda zani in kinga dama kiyita tsaiwa a gurin amma ki sani kuma ki rubuta ki aje duk wayon amarya watarana sai ansha manta Hauwah bazan takura miki ba amma akwai ranar qin  dillanci"

 Daga haka bai kuma cewa da ita komai ba yaja duvet ya rufe jikinsa  ita kuma ta zauna a qasa idan tayi kukanta me isarta saita dago ta kalleshi da haka har bacci ya dauketa ya tashi ya dauketa a hankali ya kwantar da ita.





Shima kwanciya yayi ya hada jikinsa da nata yana shafa kanta a hankali zuwa  cikin gashinta yana shaqar kamshin jikinta da haka yayi musu addu'a bacci me dadi ya daukesa tattare da wani matsanancin farin ciki yau Allah ya cika masa burinsa gashi ga Hauwan sa shimfida daya a kwance.

Yana manne da ita hannun daya sanya cikin gashinta ya mayar dashi gasan mararta ya rungumeta hannu biyu a haka suka kwana, Kiran assalatu ya farkar dashi ya janye jikinsa a hankali ya shiga bathroom yayi wanka yayi alwala ya dawo ya tasheta daqyar yana shafa fuskarta tayi miqa tare da bude idonta.




Ai a zabure ta miqe tace “waye ya dawo dani nan?" Murmushi yayi yace “nima tambayar da nakeyi kenan waye ya dawo dake nan kikazo kika naniqeni harda wani rungumeni ke dadi miji" murguda baki tayi tace “a tsinewa me qarya" zaro ido yayi tare da kwashewa da dariya yace.

“Idan kika tsine kanki zaki tsinewa kiqi albarka yarinya ni tashi kije kiyi alwala kizo muyi sallah" bathroom din ta shiga ta tsaya tana kallo can ta tuna inda taga ya taba jiya itama ta tabashi ruwa yazo tayi alwala ta miqe ta fito.





Tana fitowa ta tarar dashi ya idar da raka'atainul fajr yace “kinyi wanka kuwa" yatsina fuska tayi tace “to ba jiya nayi wanka ba kuma yauma sai nayi" daga Mata kai yayi yace “eh kullum ma sai kinyi zo muyi sallah sai kije kiyi" 

Noqe kafada tayi bai kulata ba balle suyi tazo sukayi sallar suna idarwa yace “tashi kije kiyi wanka" ita kuwa ta zame ta kwanta ta tace “nifa bazai yuwu ka takuramin ba naga jiya da dare ka matsamin saida nayi wankan nan sannan yauma kace sai nayi ni ka mayar dani gurin su Baffa na ma na huta da jarabarka"





*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/4, 2:07 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*


*26*




Miqewa yayi ya sunkuceta ya azata a gadon yabita ya danne da dukkan qarfinsa ta saki qara tare da qanqameshi hakan ya bashi damar qara sakar Mata nauyi tare da cafkar gashin kanta ya hade bakinsa da nata ya fara sauke mata wani salo da yayi mugun gigita duniyar Jiddoh ta dauke wuta gaba daya ta daina motsi.

Lkcn daya sauke hannunsa a qirjinta ne tayi saurin jan numfashi tare da tureshi ta fasa masa kuka saboda irin kamun da yayiwa nipples dinta taji a jikinta sake murza kansu yayi yaja ajiyar zuciya yanajin yanda jikinta ke rawa yace.




“Banason yimiki komai a yanzu inaso na baki lkc ki nutsu amma na lura so kike saina gurje miki rainin da yake damunki a game dani gara na gwada miki bambamcin tsakaninmu kafin ki qarasa rainani.

Kuka takeyi sosai jikinta na wata irin muguwar rawa gashi ta hada qarfin mutanen rugarsu gabadaya ta kasa tureshi shikuma sai qara murza nononta yakeyi da mugunta itan kuwa ta kasa daina kuka saboda azabar zafin da takeji, janyewa yayi a hankali tunaninta dagata zaiyi harta fara sauke ajiyar zuciya taji ya cafki boobs dinta da bakinsa, ta kuwa taqarqare ta kwallah qara.





Saurin rufe Mata bakin yayi yaci gaba da lasar boobs dinta yana sauke numfashi ajiyar zuciya yake saki ita kuma tana kuka dukkan wata gaba ta jikinta na rawa, tana jijjigashi tana gunji tace “Kado don...don Allah kabari wannan iskancin haramun ne nikam kaima ashe haka kake kaima ashe dan iskan...."

Rufe Mata bakin yayi yana kallon fuskarta ya cika hannunsa da bakinsa da boobs dinta yana wani lumshe ido, ta dage da gasa masa mintsini a bayansa tana ganin ta gama qure muguntarta amma ga mamakinta ko gezau baiyi ba saima qara narkewa da yayi a jikinta yana murzata.




Tun tana tureshi tana ihu wai a haukanta na neman daukine har tayi shiru sai mutsuniya da takeyi shikuma yaci gaba da shafeta yana lalubarta har yayi amfani da hikimarsa ya rabata da komai nata ya sanya hannunsa yana shafa cibiyarta zuwa mararta zuwa saman pupsy dinta ita kuma sai qara matsewa takeyi tana gunjin kuka tana girgiza masa kai.

Dagowa yayi ya zuba mata ido tausayinta ya cikata tace “kak....kayi hqr bazan qara ba Allah bazan kumayi maki musu ba duk abinda kacemin zanyi Inninina ciwo yakeyi wayyohhhh Allah Gwaggona zan mutu wayyohhhh anshari na k...."





Tura hannunsa yayi a gabanta ya wani lumshe ido saboda yanda yaji ta karbi saqonsa vulvo dinta ya cika da ruwa lumtsum kamar ya diba ya saki wani numfashi ya sake kwanciya yana tura yatsan nasa yana wasa da gindinta a hankali, ta tsuke qafarta ta sake rushewa da kuka tana dukansa tace.

“Kabari Kado baniso...." Ai bata ida rufe bakin ba ta saki wani razanannen ihu saboda hannunsa daya tura cikin tsukakken farjinta ta qanqameshi tana qarawa kukanta qarfi jikinta na wata azababbiyar rawa saboda azaba ya lumshe idonsa tare da zare hannunsa a hankali daya cika da ruwan ni'imarta.




Sanyawa yayi a bakinsa ya lashe ya sauke wani masifaffen numfashi ya sake tande yatsan nasa ya kwantar da kansa a qirjinta yana qoqarin hadiye sha'awarsa dabai taba tsintar kansa a cikin irinta ba ya zare boxes dinsa ya ya kama penis dinsa ya miqe ya buda qafarta sosai ya sunkuyar da kansa ya sanya hannunsa ya buda gurin sosai ya zura harshensa ciki yana lasa ta riqe kansa jikinta na rawa tana furzar da iska me zafi.

Shikuwa ko a jikinsa yaci gaba da sucking dinta yana rawar gabobi ya cire bakinsa yana karkarwa ya kwanta tare da riqe penis dinsa ya saki wata yar siririyar qara jikinsa ya dauki tsuma can zuwa wani lkc ya zubar da ruwansa a hannunsa ya koma ya kwanta luf a katifar yana hada gumi.




Yana dagata ta miqe a wahalce ta mirgina qasa tana qarawa jiniyarta qarfi tace “kuma wlh sai Allah ya sakamin cutar da kayimin mugu dashi kwart..." 

Dirowar da yayice tasata zabura ta miqe ta shige bandaki a guje yabita ta shige bayan qofa yabita ya janyota ya dagata cak yasata a cikin bowl ya hada musu ruwan wanka idanunta a rintse haka sukayi wankan ya dirjeta sosai suka fito yayi kissing nata tare da rada mata “I love you muah muah muah” 



Rufe idonta tayi cikin shassheqa tace “kuma saina fadawa Baffana kai har kafi su Rubado ma su iya adumbuli sukeyi kai kuwa harda shama kakey...." Rufe Mata baki yayi da qirjinsa da yake cike da suma yace “idan nasha abinda na rage sai yayana suzo Suma susha"

Bata qara yimasa mgn ba ya ajiyeta har yanzu taqi bude idonta kamar yanda bata daina kuka ba haka bata daina murguda masa baki ba shikuma bai daina shafa bayanta ba yana yabawa halittar da ubangiji yayi Mata a zuciyarsa yace “kyawawan Mata suna Rugage"





Fita yayi ya shiga kitchen ya dafo musu tea ya dumamo musu naman jiyan da taqici sai break da yasa wani yaronsa ya kawo masa jiya ya dauka ya shiga dakin ya ajiye ya matsa gabanta ya kwantar da kansa a saman cinyarta yace.

“Rana ta farayi mu karya mu tafi banason zamanmu anan gara muje na gabatar dake a gurin parents dina" yasha fama kafin ta karbi abincin amma fa fir taqicin nama wai ita tausayin kaza takeji wannan abu yana mugun bashi dariya haka ya hqr tasha tea me kauri da bread shima dankali cewa tayi bazataci ba cin kayan dadi rashin imani yake sawa😆😃..........






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/4, 2:07 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*27*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________




Bayan sun gama break din ya sake janta suka kwanta saboda bacci yakeji sosai don daren jiya kusan cinye lkcnsa yayi a kallon kyakkyawar surarta, fir taqi yarda ta kanta a jikinsa da taga ma yana neman takura Mata sai tace ita ta fasa baccin.

Dole ya qyaleta ta sauka ta koma falon ta kwanta anan baccin ya dauketa, har 12:00pm ya tashi ya sake wanka ya fito ya isheta tana bacci yayi murmushi tare dazama kusa da ita ya shafa fuskarta ta fara qifqifta idanu kafin ta budeshi tar akan sa.




Qaramin bakinsa ya sauke akan nata yace “kinyi baccin safe nasan qila baki tabayinsa ba bakisan dadinsa ba ko?" Kada masa kai tayi yayi murmushi yace “ina addu'ar duk ranar dazan bareki Allah ya aramin qarfin dokuna goma na barjeki yanda sai kinkai uku na rana baki tashi a baccin safe ba.

Da yake babu hausa sosai bata gane meyene yace ba sai miqewa da tayi zaune tayi miqa tare da tashi tsaye ya ruqo qugunta ta dawo jikinsa ta zauna ta yunqura zata tashi ya qara matseta da jikinsa tayi tsaki, dago kanta yayi da sauri yace “nikikewa tsaki?"





Daure fuska tayi tace “to inma banyi maki tsaka ba mi zanyi miki bakida aike sai iskanci ni wlh na gaji ka kaini Rugarmu mu rugarmu baa irin wannan iskoncin aradu daa Rugarmu kake da yanzu ka mitu kowa ya huta kuma ma idan naje saina hwadiwa innarka aradun Allah...."

Sake matseta yayi a jikinsa yana sunsunar wuyanta tare dasa harshensa yana lasa a hankali yana sauke numfashi yana tura hannunsa cikin rigarta yana shafa qasan cibiyarta a hankali zuwa qasan breast dinta yace “ahhhh Hauwah inajin feel dinki over ki barni nadan huta dake kadan kinji"





Ture hannunsa tayi ta miqe tace “Kado wannan sunsune sunsunen naka ya isheni fah aradun Allah zanyi maka asurka a hanci mutum saikace mayye kaita baman lasheni ni wannan ai baitace ko mutanen zangon mayu banji labarin suna lashe mutum ba saikai saboda mug...."

Buge mata baki yayi yace “zan fara dinke miki bakin rashin kunya tukunna kafin kiyimin asirka sakarya da batasan komai ba wannan dolene ma na nema miki malama take koyar dake a gida" 

Gatsine tayi masa tace “ehdin ehdin ai dama alqawari kayimin kuma alqawari kayane ni badon ma inaso in zama yar burni ba ai kasan bazan taba biyoka ba"






Wucceta yayi zai shige daki tasha gabansa tace “dubeni kagani mace har mace qirar Amurka qinqisar faransa rainon Ingilishi" yanda take wani karkada jiki tana banqaro qirji yayi bala'in bashi dariya ya rabata ya wucce tace “ohodai ai kasan zaren ba kalar yadin bane wani mummuna dakai kamar gwaggon biri"

Duk wulaqancin da takeyi yanajinta har ta gama ta koma ta zauna shikuma ya gama shirinsa tsaf ya fito ya abin mamaki kawai yaganta tanata kuka ya matsa ya dago kanta fuskarnan tasa babu alamun rahma yace “tashi kije kisa kayanki kizo mu tafi" murguda masa baki tayi.





Ya miqar da ita yace “idan kika sake na cire kayana wlh sai nayi miki abinda yafi na dazu zansha nononki harsai kan ya cire sannan zan....." Toshe masa baki tayi tace “uffararan aradu baka qarashan nonona saidai kasha na shanuwa" hannu yasa ya shafo gabanta yace “harnan zansha irin shan da nayi masa dazu ya rinqa bulbular da ruwan dadi Hauwah dama dama dama dazu na kwashi gara kinji yanda ruwan gindinki yakeda gardi kuwa"

Toshe kunnenta tayi tana zare ido tana fadin “sabo sabo baa bakina ba abakin wani Kado Shedan a gdan Kado Shedan a dakin Kado Shedan a gadon Kado"😂





Murmushi yakeyi ya figi hannunta ya shiga da ita dakin ya nuna Mata wata baqar doguwar riga yace “kiyi kisa kina batamin lkc" ta jima tana juya rigar yana kallonta kafin ta juyo tace to a fita a bani guri zansa kayana"

 Yasan idan ya biye Mata sai sukai sha dare basu tafiba dalilin da yasa ya fita kenan ta dauki rigar tasa tana ganin bra din ta sanya hannu ta rufe idonta tana qyalqyala dariya idan ta bude idonta tayi arba da qoqon bra din saita qara rufe idonta tana dariya.





Tsayawa yayi yana kallonta rigar tayi Mata kyau matuqa ta karbi farar fatarta amma yagano gyara ya matsa gabanta, ya dauki bra and panties din ya kalleta ya kamota ya daga rigar zai cire Mata tayi saurin qanqameshi tace “kabari... Kado kabari banaso kake ganemin jikina"

Murmushi yayi yace “na nawa kuma Hauwa cire kisa pant da bra banso jikinki yana rawa haka indai ba me and you bane" noqe kafada tayi tace “ai karuwai ne suke sanyawa nikqm ba karuwa bace bazan sanya ba salon in munje gdanku Innarka tace ni yar iskace" 







Fincikota yayi ya dagata ya cire Mata rigar ya dauki bra din yasa mata daqyar da kokawa sannan yasa Mata pant din ya dauki rigar ya mayar Mata ya dauki hankici ya goge Mata dige digen da tayi da maskara a fuskarta ya  shafa Mata powder ya matsa ya kalleta yayi murmushi yace.

“Kinfiki kyau a haka ki daina diga abinnan a fuskarki muni yake sanyaki juya ki kalli kanki a madubi ki gani" 

Juyawa tayi ta zubawa mudubin ido tace “lahhh wannan ba mudubi bane ai Kado majigi ne da muke ganin mutane a ciki a tasha idan munje tallan fura" 





Shikam ya gaji da wautarta ya juya ya fice yace “ki sameni a mota ina jirankin" 

Yana fita tabisa da gudu ya bude Mata motar ta shiga yaja suka tafi bayan ya zuba Mata kayan daya siyo Mata a mota ya kira me gyaran fulawar gdansa a waya yace ya shiga parlourn ya bude daya upstairs din da basa amfani da ita ya gyara ya canza komai   zaisa amaryarsa a ciki.

Suna tafe tanata kalle kallenta har wani maqale windown takeyi ganin hakan yasa ya danna pin din yaci gaba da tuqinsa sauqinsa kawai dake matar baqin glass ne.





Kai tsaye gdansu ya nufa gabansa na faduwa saboda tunanin abinda zai tarar gurin Hajiyarsa duk da yasan aikin gama ya gama, parking yayi ya bude qofar ya fito ya zagaya ya bude Mata ya tarar da ita shanye da baki tana kallon tsayin benen har wani karkata baki takeyi.

Tabota yayi yace “fito mu shiga saura kiyimin rashin hankali a gaban parents dina" oho shi yasan meye parents dama yace iyaye qila ta gane.

Kamata yayi hannunsa na cikin nata tanata kalle²nta tana mamaki harda riqe haba oho bai lura da abinda takeyi ba saboda wayar da yake amsawa ya murda qofar ya shiga yana rige da hannunta tare da sallama.





Wani birki da taci ta saki hannunsa ta tsaya tana dage kai tana kallon falon cikin mamaki tana daga hannunta sama, tsayawa yayi yana kallonta tana murmushi tace “aradun Allah wannan irinsa ne Moddibo Gambaje yake hwadi mana zaa bamu a aljanna nikam naga aljanna ido da ido"

Yana Shirin yin mgn ta sake warcewa ta shiga cikin parlourn ta zauna a gaban plazma TV din da taketa aiki ana haska wani film waishi rudin zuciya a wata tashar hausa.





 Uban tagumi ta zuba tana qara matsawa jikin TV har saida ta dunguri TV stand din sannan ta tsaya tana dage kai tana kallo tana qyalqyala dariya, ta juya ta kalleshi tace “lahhhhh zo ka zauna muyi kallo kaji Kado aradu nikam anan zan zauna Ina kallon aljanna Ina kallon Mata da mazan yan Aljannah da suka rigamu gidan gaskiya, rushewa tayi da kuka tace “ashema aketa tsoratani akace idan nabari Kado ya tabani mutuwa zanyi ishe irin rayuwar da akeyi kenan idan an mutu" daga Kai tayi taga jarumin film din ya rungume matarsa suna kissing din juna aikuwa saita miqe tayi tsalle ta rungumeshi tace “hege kado ashe duk a Aljannah ka koyo irin wadannan abubuwan to amma shi banga  yasha Mata Innininta ba"............🤣🤣🤣😂





_hhhhhhhh ango Lameer Allah ya qara maka hqr_






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/4, 9:17 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

__________________________

*28*

__________________________

*UMMUH HAIRAN*

__________________________



Hajiya dake fitowa ta tsaya ta zubawa sarautar Allah ido Muneef ma dake dinning yanayin lunch ya juyo da sauri ya zuba musu ido, ta zame  jikinta daga nasa ta matsa gefe saboda ganin Hajiya dake nufosu taja baya itama ta matso gabanta ta janyota da qarfi.

Ta kwada mata mari tace “dama kece farkar wannan mahaukacin? Ashe kece yar tatsitsiya dake kika gama da sangamemen qato irin wannan sai yanda kikayi da zuciyarsa" 




Matsawa tayi gabansa kansa yana qasa tace “ka bani mamaki Lameer bantaba tunanin haka daga gareka ba uwarme zaka tsinta a jikin wannan ficiciyar yarinyar da ka kasa samu a gurin matarka har kuke ha'intarta ka watsar da haqqoqinta akan wannan aljanar yarinyar?"

Dagowa yayi da sauri gabansa na faduwa saboda yanda Jiddoh ta maqalqalesa tana wani mugun kuka saboda sosai marin na Hajiya ya shigeta kamar yanda shima yaji marin a qasan qahon zuciyarsa yace.




“Amma Hajiya meye Hauwah tayi miki daga shigowarta cikin family dinmu a fara yimata wannan tarbar Hajiya matatace fah kuma sonta nakeyi na biya sadaki na aureta iyayenta suka dauketa basaso suka bani ita ta amince kuma zatayi rayuwa dani duk da kasancewar iyayenta sun sallamamin ita, meye yasa Hajiya zakiyimin haka meye yasa ni baki taba tayani so da tattalin abinda nakeso ba?"




“Matsawa tayi gabansa ta sanya hannu ta shaqosa tace “kutmar ubanka ne yasa bazan tayaka sonta ba Lameer nace durun uwarka, ni zaka titsiye kace sai na fada maka meye yasa banason abinda kakeso to bari kaji in fada maka ba Hauwah ba ko makka ce banasonta bakuma zan taba sonta ba aurene kayi hankalinka Dana ubanka ya kwanta ka nunamin ban isa dakai ba, to naji kaje ka zauna da matarka amma kashedi kuma umarni daga yau idan ka qara dauko kucaka baqauyiyar bagidajiyar yarinyar nan ka kawomin gdan sai nayi maka abinda baka taba tunaniba.




Tunda ta fara mgnr Hauwah ta qara shigewa jikinsa ta lafe jikinta na rawa tana kuka me gunji tunda take a rayuwarta bata taba ganin abinda ya tsoratata kamar Hajiyan Lameer ba yanda ta haqiqance tana fada yafi komai ruguza lissafinta.

Numfashi yaja me huci yace “kiyi hq....." Duka takaiwa bakinsa Jiddoh ta sake maqaleshi tana kuka rawar jikinta na qaruwa tace “nikam banason wannan masifaffiyar matar Ingarido ce ka fice dani daga gdannan wlh bani qara zuwa..."




Ranqwashi Hajiya takai Mata tace “tsohuwa ta ruga me tallan nono da fura itace Ingarido bani ba Koda yake kicemin abinda yafi Ingarido ma ba laifinki bane laifin wannan sabitu sallamammen ne shegiya yar gadon saida fura nikam duk yanda akayi ku mayune shiyasa daga siyan nono kika lashen kurwar Dana".

Ganin haukan na Hajiya babbane yasashi janye Hauwah da baya da baya zasu fice Muneef ya taso yace “haba Hajiya meye hakan wannan ai ba girmanki bane ki tsaya kina fadar maganganu irin wannan a gaban surukarki matar danki meye laifin Yaya don ya farantawa zuciyarsa ya auro farin cikinsa wlh nikam ya burgeni 100%...."





Hannu ta daga masa tace “kauce ka bani guri auta ko inci ubanka to ko Abulle yayarku da taji wannan gamin gambizar auren na shashashannan saida ta sallame daga sallar magrib waccan shashashar Zaliha yar uwar dayan itace kawai harda murna to dakai da ita dashi da ita wannan bagidajiyar wlh tallahi uban maqerin babanku zanci nidai wannan mugun irin baiyimin ba inda na shukane ma bazan siya nakai gonataba"




Yanda zuciyarsa ke tafasa da kukan Jiddoh din idan ya tsaya zai iya fadawa uwartasa maganar da zata jefashi cikin fushin ubangiji saboda haka ya figi hannun matarsa tana kuka tana komai ya jefata a mota yayiwa motar key ya fice daga gdan a guje.

Gidansa ya nufa zuciyarsa a tafashe yana tuqin zuciyarsa na qara kumbura kukan nata shi yafi komai dukan zuciyarsa baisan sanda yaci wani uban birki ba yace “Hauwah ya isa hakaaaa" yanda yayi mgnr da qaraji yasata saurin hadiye kukan taja wata qaqqarfar ajiyar zuciya.




Sake taka motar yayi ya shiga unguwar ya taka burki yayi horn me gadin yazo ya bude masa ya shiga yayi parking ya kifa kansa a saman sitiyarin yace “innanillahi wa innah ilaihirraji'un Hauwah idan baki daina kukannan ba zaki tarwatsamin zuciya mu shiga kiyimin wani hukuncin banda wannan" 

Dagowa tayi idonta sharkaf da hawaye tace “inane nan din Kad..." Rufe Mata baki yayi yace “gdanki ne nan ne gidana da iyalina anan zaki zauna kafin mu tafi Lagos amma banason sunan nan daga yau kidaina cemin Kado sunana Muhammad Lameer" rufe idonta tayi tace “shabdi rahin kunya kenan mu a Rugarmu baa fadar sunan babba" murmushi yayi yace “to kawai ki rinqa cemin babe kinji" batare data damu da abinda hakan yake nufi ba ta fara maimata “babi babe bebe bebi" dariya sosai tasashi wato ita a gurinta komai har ya wucce ta samu abin maimaitawa “babi babe bebe bebi  tana nufin duka da haka zatake kirana nikam naga ta kaina" ya fada a ransa tare da bude motar............






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/5, 8:33 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*30*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________





A fusace ya juya zai fita ta kamo kwalar rigarsa ta baya tace “wlh bazaka fita ba saika fadamin matsayina a gurinka nagaji da wannan rayuwar quncin dakai Lameer kai banji dadi dakai ta fanni mu'amala ta aure ba kai banji dadin zama dakai ta fannin rayuwa ba kai bansamu lkcnka ba wannan wanne irin jahilin aure ne mara ma'ana da rashi albarka ta baibayeshi ta ko ina Lameer na tsaneka na tsani jininka na tsani zama dakai na tsani komai naka ka rabu dani don Allah Lameer nidai nace ka sakeni kazauna da kucakar matarka"





Murmushi yayi Mata tare da dago kanta yace “saurin me kikeyi mmn Fadwah kin dade kina roqona saki naqi yi mikishi saboda abubuwa biyu da nake dubawa amma kidan qara hqr indai zakici gaba da fadamin duk abinda yazo bakinki to inayi miki albishir da saura qiris"

Yana fadin haka ya juya ya fice da sauri ya nufi kitchen ya dauki duk abinda yasan zai buqata ya fita ya koma part din Jiddoh ya shiga ya tarar da ita a tsaye tanata kalle kallenta ya shiga kitchen din tabishi ta tsaya tana kallon yanda yake hada komai.






Taliya ce ya dafa musu sai tomato soup da taji bushasshen kifi sai qamshi yakeyi ya zuba musu a flat daya ya dauka abin na arziqi ne suka fito ya jata dinning suka zauna ya dauki cokali ya juya ya debi yakai Mata bakinta ta kawar dakai ta wanke hannunta tasa ta juya ta diba takai bakinta.

Lumshe ido tayi tana tauna abincin a hankali yana kallonta harta hadiye na bakinga ta bude idonta taga ya diba a cokali zaikai bakinsa tayi saurin riqe cokalin ta janye flat din ta tashi ta sauka qasa ta juya masa baya.






Ajiye cokalin yayi ya zubawa sarautar Allah ido abincin da yawa amma ko a jikinta ta rinqa cin abinta tana kadakai, tashi yayi ya matsa gurinta yace “bazaki iya cinyewa ba ki bani na tayaki" wani mugun kallo ta watsa masa ta tureshi tace “aa mugunta zakayimin ka cinye nikam ka qyaleni wannan qaton bakin naka mugun lauma zaiyi.

Damuwarsa yaji ta gushe gabadaya yayi dariya yace “is ok amma wlh sai kin cinyeshi tas kin yarda?" Daga masa kai tayi taci gaba dacin abincinta, ya miqe ya shiga kitchen din ya zubo wani ya zauna a dinning din yanaci yana kallonta.






Cikinta fah ya cika gashi ko rabin abincin bataci ba abinka dame qaramin tanki, juyowa tayi ta kalleshi ya daure girar sama data qasa babu alamun Wasa fuskarsa yanacin abincinsa a nutse yana danna wayarsa, sakeyin qasa tayi da kanta tana cakalar abincin shikuma yana satar kallonta, idan taci abinda zata iya saita dago ta kalleshi.

Hardai tagaji ta dago tace “Kado na qosh....." Hannunsa ya daura a bakinsa yace “sheeeeeet!" Sannan ya miqe ya dauki lemo da ruwa ya tsiyaya a cup ya tsugunna gabanta yakai Mata bakinta ta karba tasha sannan ya sake tura nata abincin yace.





“Alqawari mukayi dake zaki cinye saboda haka saikin cinyeshi tass" ai baigama rufe bakinsa ba sai hawaye sharrrr ya miqe ya koma ya zauna saman stool din dinning din yace “oya kiyi ki cinye kiyi wanka zanje masallaci na dawo an fara kiran magrib" miqewa yayi ya shiga daki ta kuma tusa abincin a gaba.

Turawa takeyi tana kuka cikinta kamar zai fashe har wani yunqurin amai takeyi tanata jan zuciya, fitowa yayi da sauri baiko kalli inda take a yana daura agogo yace “idan na dawo naga baki cinye abincin nan ba sainayi gunduwa gunduwa da sassan jikinki"





Wawuyarku takuwa sake rushewa da kuka dataji yace zaiyi gunduwa gunduwa da ita har tana auna gabobinta yau tasan idan bata cinye abincin nan ba dafgenta zasuyi, Kai abu tun kamar zai yuwu harta kai qarshe kawai ta tusa abincin a gaba ta hade kai da gwiwa ta kurma uban ihu.

Daidai lkcn da yake haurowa saman ya qaraso da sauri ganin yanda ta riqe ciki tana kuka wiwi yasashi komawa ya zauna yace “me kikeyiwa ihun bayan kince zaki iya cinyewa?" Cikin shassheqar kuka tace “Qur'anin Allah na dauka abincin kadanne ashe dayawa kuma ai kaine mugu ka zubo da yawa"





Wata cafka yayiwa gashinta yace “nine mugu?" Kuka ta rushe dashi tace “eh mana mugun mugaye na saicin alhakina kakeyi ka tsotsemin Inninina kayimin wanka sannan kasani na cinye abincin da kasan yafi qarfina wlh sai munyi hisabi a lahira kai gidansu Ingarido zaa kaika idan ka mutu nikuwa gidansu Hamana"🤣

Dariya ce tasashi qarasa zama yace “waye Hamana?" Shiru tayi tace “wazirin Fir'aunu ne kuma babban babbansu a gidansu😃 Murmushi yayi yace “kintaba zuwa islamiyya?" Turo baki tayi tace “Modibbo Gambaje yana koya mana idan ya dawo daga rani"





Murmushi yayi yace “makaranta hudu zansaki ta islamiyya data boko zan dauko masu koya miki a gida sannan ta koyon girki zan kaiki Catherine school sai ta koyan kwalliya da zama da miji" numfashi ta sauke tace “nidai bazani b..." Rufe mata baki yayi yace “aikuwa sai kinje karma ki qara cewa bazaki ba banason musu"

Shiru tayi tana riqe cikinta tace “wayyohh cikina" da sauri ya dagota yace “meyene kuma?" Kuka tasa masa tace “kaga kasani naci wannan taliyar yar leda kuma....." Rufe bakin tayi taqara riqe cikin tana kuka yace “dallah kiyi mgn mene?" Kuka ta Kuma rushewa dashi ta kwanta a jikinsa tace “kashi nakeji kuma babu jejin da zan zagaya a kusa yanzu yaya zanyi"🙈🤣





_Jama'a nifa sakarcin Hauwah ya fara isata aradun Allah_






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/5, 8:33 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

____________________________

*29*

____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________





___________📝Riqota yayi jikinsa suka nufi qofar shiga gidan ya bude ya shiga da sallamarsa Mubaraka dake fitowa daga kitchen ta dago domin amsa sallamar ai batasan sanda ta saki flat din hannunta ba saboda tsananin firgici da mamaki.

Janye Hauwah yayi a jikinsa ya zaunar da ita saman daya cikin kujerun falon yace “sannu da gda uwargida sarautar Mata ya kadaici" bata iya amsawa ba saboda wani yawu me daci data hadiye daqyar ta matso gabansa cikin macewar gabobi tace “Lameer wacece wannan"





Tayi maganar tana kallon Jiddoh wadda itama ita take kallo qurrr tanata zuba santi a ranta na kyawun Mubaraka tayi ajiyar numfashi a ranta tana fadin “dama nice"

Miqewa yayi yana cewa “qanwarki ce  Ina fatan Isa ya gyara wannan bangaren?" 

Bata iya cewa dashi qala ba saboda wani baqin ciki da yake turnuqar zuciyarta yaja hannun Hauwah domin su hau saman Amma sai ta noqe tace “tabdi salon naje na taka na fado nikam ka barni anan"





Itadai bazata rabu da abin mgn  ba ya fada yana figar hannunta da qarfi ta fada jikinsa ya dagata cak tana ihu ya haura saman ya direta a tsakiyar parlourn yayi shigewarsa daki.

Tsayawa tayi tana kallon gurin ta zube a gurin tana kallon  kowacce kusurwa ta falon cike tsoro da mamaki komai juya Mata yakeyi saboda ko a mafarki bata taba tunanin tsintar kanta a irin wannan gurin ba.

Miqewa tayi tana latsa kujerun tana dariya tana cewa “laha'ilallah Kado zo zokaji wlh wanan gumakan na gurin nan duk laushine dasu kamar jikinka" 

Fitowa yayi ya tsaya jikin qofar ya zuba Mata ido yana kallon inda taken komai na parlourn tana shafawa tana dariya





Murmushi yayi ya matsa ya sha gabanta ta dago ta kalleshi ta nuna masa standard A.C dake tsaye a kusurwar hagu ta parlourn tace “wannan kuma meyene Dana taba naji yanata kwararar da sanyi?" 

Ajiyar numfashi yayi yajata suka zauna yace “A.C ce" kallonsa tayi tace “tohhh sunanshi kenan ic meyesa bana ganinsa a rugarmu?" Dariya yayi  yace “ai bakuda wutar lantarki shiyasa baki ganinsa a rugarku yarinya" 





“Miqewa tayi tace “aa Kado in zaayi wasa ai wasa banda tsikarin uwar miji da tabarya kada ka qara cemin yarinya danni ba yarinya bace na fada maka..."

Bata ida fadin abinda ke bakinta ba taji yayi sama da ita bai direta ko inaba sai kitchen din dake cikin parlourn saman yace “shirmenki yayi yawa Hauwah yunwa nakeji me zamuci?" Turo baki tayi tace “nan kuma dakin wayene?" Janyota yayi jikinsa yace “kitchen ne anan akeyin girkin duk abinda zaaci" 





Dariya tayi sosai tace “amma Kado kai dan rainin hankali ne yanzu nan duk jeran nan kana nufin madafi ne to inma banda ka rainani Ina zaa girka murhu?" 

Haɗiye dariyarsa yayi yace “aiga murhun nan zo kiga inda ake kunnawa" matsawa tayi ya dauki abin kunna gass ya danna ta saki qara tare da cewa “wayyohh kunne na wayyohh zai qonani!" dariya sosai yace “zo kiyi mana girkin abinda zamuci yunwa nakeji" 





Turo baki tayi tace “chabdi nidai aa bazan iya girki ba ni ko kunu ban taba damawa ba balle wannan jagwalgwalon naku na yan birni" murmushi yayi ya dauko tukunya sabuwa dal a cikin kitchen cabinet ya zuba ruwa ya dora ya goge hannunsa ya jata suka fito yace.

“Zauna Ina zuwa" baijira cewarta ba ya nufi downstairs din ya sauka ya nufi matattakalar da zata kaishi part din Mubaraka ya haura ya tarar da ita a tsaye da waya a hannunta tana yafa mayafi yace “ina Zaki?" Cikin kallo irin na tsantsar tuhuma tace.





“Zanje na tambayi tsohuwarka ne da saninta ka kawomin wannan kucakar karuwar taka gidana har kayi Mata bangare a cikinsa ka shige daki da ita sama da awa guda" Murmushinsa ya fadada yace

 “Abinne yazo a bazata wlh shiyasa ban sanar dake ba kiyi hqr nasan nayi miki laifi duk da qila kinsamu lbrn dama Ina neman aure, Mmn Fadwah wannan yarinyar da kike gani matatace ta sunnah da aure yabani matsayinku daya a gurina babu wacce tafi wata sai wacce tafi kwantarmin da hankali"





Numfashi yaja yaci gaba da cewa “Mubaraka Hauwah yarinya ce qarama qanwar bayanki ta qarshe gaba daya bazata wucce saar Zainab qanwarki ta hudu ba, haka Allah ya nufa kuma ya qaddara batasan komai ba dani dake mune zamu sanar da ita idan mukayi Mata mugun karatu dashi zata tashi idan muka bata sahihin karatu da babu mugunta ko sonkai a cikinsa to shine zaita zagawa tsakaninmu alkhairi zai wanzu cikin zamantakewarmu ya bamu kyakkyawar alaqa da fahimtar juna wanda hakan zaiyi tasirin bibiyarmu har qarshen rayuwarmu....."





Daga masa hannu tayi tace “kayyy dakata munafukin Allah ta'ala kana nufin wadannan matsiyatan kalaman naka sune zasuyi tasiri a kaina? Hmmm wai qanwa wlh kayi tsararo Allah ya kiyasheni tabewa yin qanwa da wannan bagidajiyar yarinyar kaidai daka kwaso ta kware maka can Amma badani ba" 

Yanda take mgnr tana nufoshi kamar zata dakeshi yasashi sakin baki yana kallon ikon Allah har ta iso gabanshi tace “wannan itace sakayyar halaccin da nayi maka ko Lameer kaje ka ajiye karuwa a Lagos sannan ka tashi dawowa ka dawomin da kishiya kishiyar ma wannan qazamar kucakar yarinyar da bazata taba wayewa ba a rayuwarta, to wlh saidai ka zaba koni ko ita nikam bazan taba zama da ita a matsayin kishiya ba Wai muna amsa suna daya gurin mijinmu.

Ka cuceni a abubuwa da yawa Lameer baka damu da saukemin haqqina ba wata da watanni kana qwarata kana barina da damuwar da banida me yimin maganinta saikai sannan yanzu ace kayi aure wannan ma ai cin fuskane da wulaqanci da wanne kuzarin zaka riqemu mu biyu har ka biyawa kowa buqatarta?"





Shafa sumarsa yayi yace “duk wannan ba damuwarki bace abinda ya shafeki kuma haqqi a gareki shine na sanar dake matsayin Hauwah a gurina kuma na sanar dake ruwa nane na kusanceta kullum ruwa nane na shekara ban kusanceta ba kamar yanda nakeyi miki wannan ba matsalarka bace, amma dai ki sani kuma kisa a ranki aurena da Hauwah yin Allah ne kuma ya qullu babu wanda ya Isa ya hanashi kamar yanda mahaifinta da danginta suka qi kuma suka qyale akayishi yaka duk wani dan baqin ciki zaiyi quncinsa ya qyalemu, idan kuma mutum yana ganin bazai iya hqra ba to ya hadiyi zuciya ya mutu kowa ya huta"






Wani mugun tashin hankali ta tsinci kanta a ciki da bata taba tunanin Lameer zai sata a ciki ba tunda sukayi aure tsayin shekara uku baitaba daga muryarsa sama da tata ba sai akan wata mace macen ma wannan qazamar kucakar bafulatanar dako yar cikinsa inda yayi auren wuri batakai ba, lallai da aiki ja a gabanta dole ta tashi hankalinsa dana zuri'arsa, babban tashin hankalinta yanzu cikin da take dauke dashi na watanni biyu wanda a lissafe idan zaiyi lissafi watansu hudu rabon da wani harka ta auratayya ta shiga tsakaninsu sai kwanaki takwas daya wucce ranar da tayi masa tujarar nan, yanzu ta yaya zata fara liqa masa cikin kamar yanda ta liqa masa na Fadwah?..…………...





_Hmmmmmmm tabdi wannan shine tsaka me wuya su Mubaraka ana ruwa_






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/7, 8:03 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

____________________________

*31*

____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________





Miqewa yayi yace “kewai komai ma baki iya ba bakiga toilet a bathroom ba dazu da kikayi wanka zakicemin wani kashi kikeji" sakeyin raurau da ido tayi tace “ni wlh banga juji ba" ya lura itafa komai bata ganewa sai anyi mata gwari gwari hakan yasa ya kama hannunta suka shiga bandakin ya bude seet toilet din yace “ga gurinda akeyin kashi nan idan kika gama sai ki murda wannan ki zaro tissues ki goge saiki sake danna nan ruwa zai zubo saikisa sabulu ki wanke idan kin gama kuma ki danna nan zakiga ruwa yazo yayi flurshing"





Fita yayi yabarta a tsaye tana leqen cikin toilet din tana kallon ruwan ciki gare gare tace “to aini dazu a wannan randar na debi ruwan alwala"🤣

Har yaja qofar yace “ehh!" Tare da zaro ido yace “kika debi ruwan alwala anan?" Daga masa kai tayi tace “eh aradun Allah kuma ruwan dumine dashi danasashi a bakina har wani zaqi yakeyi" ai baisan sanda yayi qasa ba yace “kinsha fitsarina Hauwah kewai wacce irin shashashar yarinya ce bakiga inda nayi tawa alwalar ba" turo baki tayi tace “toni Ina ruwana bakaine kace nazo nayi alwala ba"





Takaici ne yasashi miqewa ya fice daga toilet din ita kuma tahau kan masan, memakon ta zauna aa saita tsuguna akai qafafunta nakan gurin zaman idan tayi kashin ya fada tsulum saita qyalqyale da dariya tace “danwake daya ya fada" haka harta gama tayi duk yanda yace.

Ta wanke hannunta ta fito baya cikin dakin hakan ya bata damar yin sallar magrib da Isha ta kwanta a qasan.

Ya turo qofar ya shigo ya hangeta a qasa ya matsa da sauri ya dagota yace “kekam baki gudun mgn kin mayi wanka kuwa?" 





Kada masa Kai tayi ya dagata yace “ok muje kiyi wankan mu kwanta gobe litinin jirgin asuba zamu bi mu wucce Lagos" itadai batace masa komai ba ya dagota suka shiga bathroom din to yanzun ma a bataso tana zillewa shine yayi mata wanka ya fito da ita shima yayi suka kwanta bayqn yayi musu addu'a.

Kiran sallar farko akan kunnensa ya tashi yayi wanka ya tasheta ya fito Mata da wata doguwar rigar atamfa cikin kayan da ya bayar tunkan yatafi a dinka mata yasata ta sanya ya bata mayafi da takalmi da jaka ya koma yana kallonta tayi masifar kyau kamar ba itaba.





Murmushi yayi yace “dama kada kiyi shirmenki ki nuna kanki idan mun tafi banason qauyancinki ki ajiyeshi anan idan mun dawo kya dauka ki saka kinajina ko? Daga masa kai tayi ya fita ya hado musu tea ya bata tasha daqyar kasancewar asubace biyar ma bata qarasaba ya kama hannunta su fito zuwa qasan.

Ya saki hannunta yace “ki jirani anan bari nayiwa yar uwarki sallama" batace qala ba ta nemi guri ta zauna shikuma ya haura saman ya kwankwasa dakin Mubaraka, ta miqe zumbur shima farkan nata ya miqe tace “mun shiga uku gashinan wlh shine bugun qofarsa ne"





Cikin kadawar ciki Muneef yace “yanzu ya zamuyi" kafin tabashi amsa ya tashi ya shige bayan manyan labulen ta qasa ya kwanta luf, ta sauke ajiyar zuciya ta bude masa qofar tana miqa ya shigo dakin yana rarraba ido yace “na tasheki ko? Zamu wucce Lagos shiyasa nayi miki transfer kudi a account dinki nasan zasu isheki duk da ba dadewa zamuyi ba"

Kallonsa takeyi sake da baki kafin tayi mgn ya juya yace “Ina Fadwah ne ko tana gdan Hajiya"  nan ma bata bashi amsa ba ya sauka yace da Jiddoh taso mu tafi kinga har rana ta fara fitowa"






Suna fita drivensa yaja suka tafi yakaisu airport to dayake yayi mata federal warning yadan samu sauqin shirmenta kuma dadin dadawa taga babu fuska hakanan duk da tsoron da take ciki na hawa jirgin ta haqura saidai qanqameshi da tayi jirgin ya  tashi ita kuma ta kama bacci a jikinsa.

Lkcn da suka isa Lagos din tanata sharar baccinta ya sabata a kafadarsa har mota yasata a ciki suka nufi Quarters din tasu saida driven ya shiga har ciki sannan ya tsaya a daidai qofar bangarensa ya bude ya fito itama ta tashi yace ta fito ta fito suka shiga ciki.





Wayyohhhh Allah nan Hauwah taga qarshen haduwa bawai fin sauran gidajen da tashiga kayan qawa yayi ba aa saidai kawai yafisu tsaruwa ga wasu manyan hotunansa guda biyu da yayiwa parlourn ado dasu sai nata Suma guda biyu daya dauketa wata rana a bakin qoramar da suke zama suna fira farkon haduwarsu.

An wanke hoton ya fito sosai kamar a kirata ta amsa, kallonsa tayi shima ita yake kallo yayi murmushi yace “kina mamaki ne?" Daga masa kai tayi ya fadada fara'arsa ya matso gabanta ya dago fuskarta ya sauke Mata lebbansa biyu yace “to ki daina yanzu wasan zai fara, yanzu zamu fara sabuwar rayuwa dagani saike, ki dauka bakida kowa sanin nima zan dauka banida kowa sai ke kadai"






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/7, 8:03 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*32*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________




Qasa tayi da kanta cike da kunya ya sanya hannunsa ya dagata cak ya bude wani daki ya shiga da ita ya kwantar da ita yace “ki kwanta bari naje na nemo mana abinda zamuci" juyawa yayi ya fita bai jima ba ya dawo.

Ledoji ne a hannunsa ya ajiye ya matsa ya dagota yace “tashi kici abinci sai kiyi baccin" tashi tayi ta sauko ya bude farfesun bindin saniya da kunun gyada sai wani hadadden cake, da kansa ya rinqa ciyar da ita Saida ya tabbatar ta qoshi sannan ya tashi ya fice.






Office dinsa ya wucce bai shigo gidan ba sai biyar na yamma abincin rana na aikowa yayi aka kawo mata, yanda ya tafi ya barta haka ya dawo ya tarar da ita tana zaune a falon ya zuba mata ido yana kada kai a ransa yace “ita komai bata iyaba"

Matsawa yayi ya kamo hannunta ta miqe firgigit tace “sannu da dawowa" murmushi yayi yace “yawwa amma bakiyi wanka ba meye yasa?" Shiru tayi saida ya qara cewa magana nakeyi miki ko babu halin amsawa?" Kada kanta tayi tace “ai baka nunamin bayin ba ni kuma bansan inda yakeba"






Miqar da ita yayi suka shiga ciki ya manna da jikinsa sosai yace “ina feels naki sosai babe" batace komai ba suka shiga bathroom din ya hada mata ruwan yace “maza kiyi wankanki bari na shiga kitchen na nema maki abinda zakici da dare gobe dai insha Allah zan nemo miki mai aiki da zata rinqa koya miki abubuwa"

Dariya tayi tace “me zata koyamin?" Shafa fuskarta yayi yace “girki da kula da gda" yana fadin haka ta kwanta a jikinsa tace “ni...ni saidai kayimin wankan hannuna ciwo yakeyi kuma ai dama Kaine kakeyimin dai ko" 






Bashi da yanda zaiyi haka ya cire kayansa ta zubawa faffadan qirjinsa Mai cike da gashi ido cikin shagala takai hannunta ta shafa qirjinsa tare da kama nipples dinsa tace “lahhhh Kado ashe kaima kanada nono?" Kallonta yayi cikin mutuwar jiki yace “kada ki jiqamin aiki Hauwah yau inajin wani yanayi a jikina" 

Dauke hannunta tayi tace “to naji muje kayimin wankana" da haka suka shiga bathroom din din ya hada ruwan wankan ya cire Mata kayanta gabansa na faduwa yakai hannunsa ya kama boobs dinta tayi saurin ture hannunsa tace “na fada maka ka daina tabamin abubuwana Allah idan ka qara ko hmmm"





Kallonta yayi da runannun idanunsa yace “zo kiji wani abu fa" matsawa tayi ya zame wandonsa batare daya bare ta lura ba ya dauki hannunsa ya dora saman penis dinsa tayi saurin kallon inta hannunta yake tare da kallonsa gabanta na faduwa tace “wayyohhh Allah na Kado wannan sukukun fah?" 

Mannata yayi da qirjinsa jikinsa na rawa yace “dama nayi miki alqawarin zan nuna miki bindira ta duk ranar da mukayi aure ko?" Daga kanta tayi cike da firgici yace “to itane wannan take buqatar taimakonki kiyimin wasa da ita har na kawo ko kuma nasamiki ita a farjinki"





Saurin qanqameshi tayi ta fashe da kuka jikinta da komanta na rawa wanda shikuma hakan ya zama kamar turashi takeyi wani dadi yakeji yanda dukiyar fulaninta ke gugar gashin qirjinsa tace “wlh Allah tsoro nakeji don Allah kada kace zaka sakamin ita ni tsoronta nakeji kado idan kasamin wannan zindariyar mutuwa zanyi..."

Rufe Mata baki yayi yace “bazaki mutu ba sai kwananki ya qare nima son samuna na barki ki girma ki nema da kanki amma yau kamar bazan iyaba" yana fadin hakan ya dagata cak yasata cikin ruwan yana fuszo numfashi yana yana rirriqe cikinsa da haka aka gama.





Ya dauketa ya azata a gadon yabita ya danne tare da kama nipples dinta yana murzawa ta fashe da kuka shikuma yayi saurin rufe mata baki yaci gaba da sarrafata da kukanta da komai bai kulata ba saida ya samu nutsuwa ya fitar da abinda ya damesa a matse matsin cinyarta.

Yaja numfashi ya shafa kanta yace “matsoraciya duk tsoronki watarana sai ta shigeki har tasa qwai kin qyanqyashe Mata abunta" turo baki tayi tanaci gaba da kukanta tace “ni ka gogemin wannan majinar daka zubamin a cinyata me shegen zafi kamar ruwan zafi kuma... Kuma Allah ya saka min"





Sake cafkarta yayi ya buda qafarta ya nutsa yatsansa cikin vulvo dinta ta saki ihu yayi ajiyar zuciya yanda yarinyar take da ruwa yana burgeshi bakamar jarababbiyarsa Mubaraka ba dasai ya hada da yan dabaru ruwan yake taruwa, kusan baisan meye yakeyi Mata ba shidai yanata juya hannunsa cikin ramin vulvo dinta.

Ya kama penis dinsa ya kwanta yayi Mata rumfa ya rinqa wasa da ita yana karkadata a saman tsankankanin gurin baidai shiga gabadaya ba amma ya tura kadan kuma tanajin zafi tanayi masa kuka tare da tureshi tanayi masa ihu kamar ranta zai fita saboda baqon gashin azabar da take karba.






Rufe mata bakinta yayi jikinsa yana mazari ya fara dannawa a hankali yana matsa nononta yana budata da yatsansa don ya samu damar shiga sosai, itakuma tana turjewa tana qanqameshi tana yaqushinsa tana gunji shikuma yana qara dannawa yana nishi yanda jikinsa yake rawa abin gwanin tsoro.

Dannawa yake amma ya kasa shigeta saboda qanqantar gurin abinka damai qarancin jarumta a tantanin farko na budurcinta kafin haqansa yakai ga cimma ruwa ya keta na biyun yakai qarshenta, shi nashi ruwan ya tsiyayo ya saki wani ihu tare da matseta a jikinsa dukkan gabobinsa hatta haqoransa rawa sukeyi ya shafa kanta yace “ki...kiyi hqr Hauwah banida kuzari kamar kowanne namiji amma duk ranar da na motsa bana iya controlling kaina"





Kuka takeyi itama tanata zuba masa Allah ya isa wuta balbal bazata yafe mishi ba har kabarinsa yayita balbala da wuta, murmushi yayi yayi kissing dan qaramin bakinta a ransa yace “kina da sauran Allah ya isa yarinya.

Wani dadi da farin ciki ke ratsa zuciyarsa na murna duk da bai samu damar budata gabadaya ba Amma ko yanzu yasan ya dandana abinda ake dandanawa gskyr Salees da yake fada masa kullum cewa aishi ba aure yayi ba tunda bai bare file leda ba, “ashe irin nishadin da ake samu ma a daren farko damutum ta fara sanin budurwa daban ne da kowanne dare?" 





Ya  tambayi kansa yana zare jikinsa daga nata ta saki qara saboda azaba yadan dakata a hankali yace “sannu ashe na shigeki sosai" yana mgnr yana qara janyewa ita kuma tans yarfa hannun tana kuka me gunji.

Allah ya bashi saa ya zare jikinsa ya dagata ya nufi bathroom ya hada mata ruwan zafi yazo ya dauketa ya sanyata a ciki har yanzu kuka takeyi na azaba tace “kuma wlh saina fadawa Baffana kai dan isk............”

Rufe mata baki yayi ya daure fuska yace “kada ki qara cemin dan iska zan fasa bakinki bantabayin iskanci ba sunnah ce nake qoqarin rayawa na lura idan ba kawar miki da gigin budurci nayi akanki ba bazakisan kin girma ba"……………






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/7, 7:56 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*33*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________






Kukanta takeyi yanaci gaba da gasa mata jikinta tana rirriqeshi har ya gama ya tayata tayi wanka ya koya mata yanda zata tsaftace jikinta sannan sukayi alwala suka fito tanata sauke ajiyar zuciya, a haka sukayi sallar magrib da Isha ya tashi yayi shafa'i da wuturi.

Itakam kwanciya tayi saboda wani zazzabi da ya saukar mata, bayan ya idar ya dagata ya dorata a gadon yana yimata sannu itakuma sai qara langwabewa takeyi tana rawar sanyi, hankalinsa ya tashi matuqa babu shiri ya kira likitan office dinsu ya sanar dashi yana buqatar pen relief.






Yana gama wayar ya fita ya samo mata abinda zataci s kitchen, daqyar ya rinqa bata tana hadiya daqyar tana narkewa a jikinsa tana kuka shikuwa duk ya rude tsoro ya kamashi a ransa yace “dama ashe haka duk wata mace takeshan wahala a darenta na farko amma wasu suke sarayar dashi a titi?"

Bayan ya gama bata abincin ya miqe ya fita saboda jin da yayi ana taba qofar, ya bude suka shigo da likitan yayi masa jagora har dakin cikin harshen turanci yayi masa bayanin komai ya dubata sosai yace “kawai rashin sabone shiyasa Amma zata ware insha Allahu"






Magunguna ya bata tare da shawara sannan yace masa idan ya samu lkc yaje zai hadashi da wani likitan gargajiya, gdy yayi masa ya rakashi ya dawo suka shata filin dambe akan itafa bazatasha maganin bature ba saidai yaje rugarsu gurin Boka Bawa ya karbo Mata magani.

Kai abufa tun anayin na hankali har abu ya gagari kwandila ta rikice masa babu abinda takeyi sai kuka da surutai tana wani mimmiqewa, shikam wannan rana yayi danasanin tabata da yasan haka zata zame masa dama bai fara ba ya qyaleta yayita kallonta.






Ganin dai abin bana hankali bane yasashi fara yimata addu'a yana tofa mata tanata buge bugenta ya riqeta gam a jikinsa sun dauki tsayin lkc a haka sannan yaji ta fara keta gumi tana sauke numfashi ya kwantar da ita ya qara qarfin A.C ya zauna ya zuba Mata ido yana kallon kyawun surarta mace har mace sai gidadanci.

A ransa yana cewa wannan da ace kuma shidin wani cikakken namiji ne qila sai tayi sati tana aljanu, shima kwanciya yayi a gefenta ya rungumeta tsam a jikinsa da haka bacci ya daukesu, washegari lfy Lau suka tashi sai zazzabin dabai saukaba da kuma wani mugun tsoronsa da takeji.






Excuse ya bayar a gurin aiki ya tsaya kula da ita takuwa narke ko miqewa yace tayi sai tayita kuka wai ita ciwo ya faffarkata ya yayyagata🤣

Kayy Lameer yana ganin tujara ko tabata bai isa yayiba saita rushe da kuka haka ya rinqa binta.

Kwanansu biyu a Lagos ya daukar Mata malama Salmah babbar macece mijinta ya rasu anan gaban quarters dinsu kadan to tanada ilimi sosai dan koyarwa ma take a wata secondary itace zata zama malamarta, duk wani Abu da yasan zaa buqata ya siya suka fara karatun addini dagashi har Malama Salma sunsha mamakin yanda ta iya tundaga izu daya har zuwa izu biyar duk wata aya da aka datso Mata saita cafe.





Gata Allah yayi Mata baiwar saurin fahimta ko a na bokon ma da wuri take gane abubuwa, bayan malamar ta gama ma ta tafi zama sukayi dashi yana qara koya mata.

Cikin abinda bai wucce wata gudaba ta iya rubutun hausa da karantawa duk abinda aka rubuta zata karanta, nan suka koma koya Mata turanci shima babu wata wahala ta fara iyawa ga karatun addinin shima shiga yake dake fresh brain dinta take gata gifted aikuwa yanajin dadin hakan sosai.





Gwanin dadi suke tafiyar da rayuwarsu da malamarta ta dauketa tamkar yarta ko girkin ma dayace zai kaita chattering school ta koya cewa tayi ya bari zatake koya Mata, idan suka gama karatun boko sai su shiga kitchen suyi girki kala daya da lemo shima don kada su cika ta kasa ganewa.

Duk bayan wata guda yake zuwa kano   yayi sati ya dawo cikin wata ukun abubuwa da yawa sun faru Jiddoh ta fara wayewa ta gegije ta fara zama babbar mace saboda bayayi mata kiwon mugunta kuma bai qara yunqurin kusantarta ba ko wasannin ma da yake dan koya Mata har yanzu kuka takeyi tanace masa iskanci ne.






Daqyar da taimakon Malamarta ta daina ce masa Kado ta koma kiransa da babe aikuwa tunda babe ta zauna a gabanta a gaban uban kowa kiransa takeyi da babe shima yace mata babe.

A bangaren Mubaraka ma Abu da dama sun faru harga Allah ita  mantawa ma takeyi da cewar mijinta yanada wata Matar bayan ita saidai idan farkanta daya kwallafa rai akan Baben yayan nasa yayi Mata mgn kasancewar shi yakan kirashi haka video call to wani lkcn idan yana gda zanganshi rungume da Hauwah din ko kuma yaji yana Kiran babe.





Hakance tasa kullum yake qara kwadaituwa da amaryar yayan nasa yakeso shima yaji abinda yayan nasa yakeji a jikinta.

Itakuwa Jiddoh harkan gabanta kawai takeyi Koda ya siya mata waya ma babbar gaske bata wani damu da itaba garama idan Zaliha qanwarsa ta kirata takan dade suna waya kasancewar bayan Lameer din da Alh Ali mahaifinsa sai Zalihan sune kadai suke sonta sauran duk yan partyn Mubaraka ne garama babban yanansu Hamza shikam babu ruwansa duk da Mubaraka ta kasance qanwar Matarsa.





Wata dawowa da zaiyi lkcn sunada wata bakwai da aure yace ta shirya su tafi tare aikuwa tayita murna harda kissing dinsa kasancewar malamarta ta koya mata kissa da kisisina sinka sinka Lameer yanashan shagwaba a gurinta kaya kuwa batasa manya saidai idan fita zasuyi.

Ranar juma'a bayan ya tashi daga aiki suka shirya suka tafi qauyanci da gidadanci duk babu sai wani yauqi takeyi tana narkewa a jikinsa shikuma sai tarairayarta yakeyi yana biye mata ko a mota drivern yasha kallo yanda suketa rungumar juna suna tsotse bakin junansu yana wani shafeta abin kamar a amurka, haka da suka hau jirgi ma ta lafe a jikinsa har yanzu mugun tsoron hawa jirgi takeyi shi kuwa ko a jikinsa kodan aikinsa ne tuqa jirgin oho.






*UMMUH HAIRAN CE*...✍️

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_______________________________

*34*

_______________________________

*UMMUH HAIRAN*

_______________________________






Tun kafin su sauka kasancewar shigowar dare sukayi ya turawa Muneef saqon zuwansu yace yazo ya daukesa a airport, lkcn suna tare da Mubaraka suna qullah yanda zasuyi su dauke hankalin Lameer din dagakan cikin Mubaraka daya shiga wata na tara.

Kuka takeyi masa tana fada masa ta lura kamar Lameer bayason cikin nata kamar yanda yaso na Fadwah nan take bashi lbrn yanda sukayi tace “ranar dana fada masa inada ciki wata hudu a kwance yake amma zabura yayi ya miqe yace “yaushe na samu ciki da har yakai wata hudu?





Saida na tubure masa na rinqa kuka nace masa ashe duk zaman da mukeyi zargina yakeyi, to ganin na tashi hankalina Ina Shirin kiran Hajiya na fada Mata yasashi cewa shifa ba wani abu yaje zargi ba kawai dai mamaki yayi, to da qarya da qarairayi nace masa ai kwanciya yayi yanzu shine ya tashi"

Sauke numfashi Muneef yayi yace “dadina dake kinada kwanya sai ki tashi ki gyara gashinan isowa yanzu ya turomin saqon naje na daukosa a airport" a tsorace ta dafe qirji tace “na shiga uku yanzu jin dadina zai yanke kai nifa yanzu ko sha'awarsa banayi Allah"






Tafawa sukayi ya qifta mata ido yace “karki wani damu muna jorner" da haka ya fice itakuma ta tashi ta fara dauke duk wani abu dazai iya bashi damar gane wani abu, saida ta gama komai sannan ta shiga wanka ta fito ta zauna ta sheqa kwalliyarta ta fito parlourn ta harde.



____________Ya dauki kamar 30 minutes sannan jirginsu ya sauka mutane suka fara fitowa yana tsaye yana kallon masu saukowar can ya hango yayan nashi riqe da hannun wata balarabiyar yarinya yayi tawassali ga ubangijin daya halicci wannan kyakkyawar baiwa tasa, karkatar dakai yayi ya zuba musu ido shima Lameer din tunda ya hangishi ya lura da inda hankalin qanin nasa yafi karkata.

Nan danan wani mugun kishi ya taso masa ya janyota jikinsa hakan da yayi ya tabbatarwa da Muneef cewa Hauwah ce.

Numfashi yaja ya sauke ya zuba musu ido sunyi wani fresh dasu ba qaramin dacewa sukayi da juna ba kamar dama domin junansu aka haliccesu ga wani qara narkewa da takeyi a jikinsa tana shigewa shikuma sai biye Mata yakeyi.





Nandanan Muneef yaji wani shauqi ya shigeshi na ace shine take yiwa haka ba wannan rabin mutum din mijin nata ba, har suka iso baisani ba saida Lameer din ya mareshi yace “ubanme kake kallo ne?" Firgigit yayi ya dawo nutsuwarsa yace “oh sorry bansan kun iso ashe da gdan kake tafe gabadaya" 

Murmushi yayi ya kalleta yace “kin ganeshi?" Yatsina fuska tayi kamar taga kashi haka kawai takejin haushinsa da tsanarsa tun ranar da sukaje neman aurenta taga ya kafawa nononta ido, girgiza kai tayi tace da cewa “Notthing"🤣





Sakin baki Muneef yayi shikuwa gogan ko a jikinsa yayi kissing dan qaramin bakinta yace “ok muje gida nayi miki wanka ki huta sai nayi miki bayaninsa Amma ai kin gane Zaliha ko?"

Murmushi tayi wani isasshe ta sake kwanciya a jikinsa daidai lkcn da suke zama a mota tace masa “tamace idan muka dawo zatayimin gyaran amare zata tsumani wai meye tsumi babe ni bangane hausarba?" Kallonta yayi da sauri yace “aa kada ki sake kisha tsumin nan zai iya zame mana matsala kinji?" 





Turo baki gaba tayi tace “aa wlh nikam sai nasha tsumi ai magani ne nasan bai wucce maganin rana da basir ba" ya lura wauta a jinin Hauwah take shiyasa yayi mata Shiru ya qyaleta daga kan da zaiyi yaga Muneef ya saita mirrow yana qare musu kallo ya kuwa daka masa tsawa yace.

“Ka juya mirrow din nan bansan sa ido" da sauri ya juyashi yaci gaba da tuqinsa zuciyarsa na karanta masa wasiqar jaki har suka isa gidan yayi parking ya fito ya bude musu qofar suka fito ta kalleshi sheqeqe ta kawar dakai ya cije lebe yana tuno sanda yaganta a rugarsu kamar wata mahaukaciya amma yanzu yayansa ya wayar da ita iskancinta da wulaqancinta takansa ya biyo lallai kuwa sai yayi maganinta daga ita har mijin nata da yake daure mata gindi.






Kafin ya gama wannan tunanin sun bude qofar parlourn ya juyo yace dashi “ka debo kayan nan ka shigo dasu ka hauro dasu bangaren babe" bai iya cewa komai ba saboda baqin ciki suka shiga parlourn Mubaraka dake zaune tana jiran dawowarsa ta miqe da saurinta zata nufeshi wani mulmulelen abu yazo ya tokare mata qahon zuciya lkcn da tayi arba da Hauwah dake ta zuba mata murmushi tayi saurin daukar Fadwah data nufosu da gudu tana kiran “Dad yoyoyo" ta fara juyawa da ita tana dariya itama yarinyar tanayi suna hajijiya.





Tsayawa zatayi jiri ya debesu suka kuwayi baya luuuuuu zasu fadi yayi saurin taresu suka fada jikinsa ta rungumeshi sosai da hannunta daya dayan kuma tana rungume da Fadwah tace “pls help me Babe jiri nakeji kaini dakina" ai kafin ta rufe bakinta ya hadasu ita da yarinyar ya dagasu cak yayi sama dasu sunata dariya ita da Fadwah shima yana tayasu saboda sabon abune a gurinsa ganin yartasa cikin farin ciki haka shi zai iya cewa tunda yake Bai taba ganin Fadwah tana dariya irinta yau ba.

Daga Mubaraka har Muneef da yake shigowa sakin baki sukayi suka zubawa sarautar Allah ido shikam kusan akwatin hannunsa subucewa ya kusayi saboda mamakin yayan nasa “wai dama haka Yaya Lameer yasan darajar soyayya?" 





Ya tambayi kansa tare da kallon Mubaraka data zube a qasa ta dora hannu aka zata rusa ihu, saukowar Lameer dince tasa Muneef saita nutsuwarshi ya kalleshi yace “ka kaimata kayanta sama" 

Kamar Mai jiran umarni ya nufi saman ya bude qofar ya shiga suna baje a tsakiyar parlourn ta fuzge dankwalin da tayi rolling dashi ta ajiye a gefe suna after momy ita da Fadwah.

Ajiye  akwatin yayi ya kwantar da kansa jiki molu din qofar parlourn ya zuba mata ido, jin kamar ana kallonta ne yasata dagowa itama Fadwah ta dago aikuwa sai yarinyar ta rushe da kuka tana shigewa jikinta ta miqe da sauri cikin masifa tace “dallah malam ubanme ka tsaya kana kallo anan ka wani kafemu da ido saikace maye harka tsoratamin yarinya aikin banza aikin wofi to wlh yau yata bazata kwana gurin waccen matarba a gurina zata kwana kuma ko ciwon kai naga tayi kaima ka kuka da kanka stupid kawai"🤔






_Hmmmm Jiddoh masifa Jiddoh bala'i Muneef dai jininku yasha bambam da Jiddoh_😆





*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*



*41*




A hankali ya rinqa bi da ita har ta haqura ta sallama masa yaji dadinsa yadda ya kamata cikin ransa yanajin dama wannan farin cikin ya dore musu shida babensa, itakam bayan ya zare jikinsa daga nata kwanciya tayi luf a jikinsa tana mayar da numfashi yanata zuba mata ruwan albarka.

Sun huta sosai sannan ya dauketa sukayo wanka ya rinqa lallabata saboda shikam yana tsoron ta botsare masa musammam yanzu da gdan nasu yake a cike da baqi, da dabara ya jata yana janta da hira har ta saki jiki sosai dashi suka shiga kitchen suka samawa kansu abinda zasuci.





Amma fah raki yananan tunda halittane shine yake daqusheta da yaji tace “washhh" sai yace “idan kika cika qorafi komawa zanyi nafiso ki horu sosai" hakanan takeyin Shiru bacci ya dauketa a jikinsa ya dauketa cak yakaita dakinta ya kwantar da ita ya shiga nasan ya gyara ya sake cire bedsheet din da suka bata.

Da kansa ya wankeshi yanajin nishadi da soyayyarta na qaruwa a zuciyarsa ko Ina saida ya gyara Mata ya shirya ya fita zuwa qasan lkcn takwas da kwata gaisawa sukayi da kakar mubaraka da taketa binsa da kallon mamaki.






Shafa kansa yayi yace “ban fito da wuri ba Kaka inada mara lfy ne yar uwartata itama ba lfy ta isheta ba shiyasa ban samu fitowa da wuri ba" itadai tsohuwa batace komai ba saboda ba huruminta bane dama Mubaraka ce ta dameta da mitar yanacan yana shan soyayya da matarsa ya manta dasu.

Shassheqar kukan da Lameer yaji a can qarshen gadon yasashi juyawa ya kalleta ya haura gadon ya karbi Muftahu a hannunta ya zuba masa ido gabansa na faduwa yace “bansan meye yake damunki ba kinsa kishi a ranki wanda idan kikayi wasa zai zama sanadin rabaki da duk wani walwala naki"






Ajiyar zuciya tayi tace “dama dolene kake daukata mahaukaciya mana dolene kake daukata bansan abinda nakeyi ba"

Shidai bai bari mgnr tayi qarfi ba ya tashi ya fice yace “zance gurin wani me magani a Doguwa don Allah ki kula da Hauwah yarinya ce Koda yake nasan Zulaiha ma zatazo.

Ficewa yayi ya sake komawa bangaren Hauwah ya zauna a gefenta ya kamo hannunta yace “zanje Doguwa insha Allahu bazan dadeba magani zan karbo gurin wani mutum da Salees ya samomin lbrnsa, bata jaba tayi masa addu'ar dawowa lfy yayi kissing nata ya fice yana daga mata hannu.





Daqyar ta tashi saboda ciwon da jikinta yakeyi ta dan gyara parlourn sama sama duk da dama ya riga ya gyara ta dauki mayafinta ta yafa ta sauka qasan a wahalce tayi saa sun dawo parlourn qasa ta zauna suka gaisa da kaka Fadwah ta taho gurinta.

Daukarta tayi ta dubi Mubaraka ta gaisheta daqyar ta amsa ta miqa hannu zata dauki jaririn tayi saurin riqe abinta tace “ah haba yarinya ki jira lkcnki yazo kema ki dauki naki ai naga ya dage so yake sai yayi miki cikin Koda yake na gaba ai yariga yayi gaba banza dake"





Itadai jiddah bata iya kulata ba saboda zazzabin da takeji a jikinta sunanan zaune zaman kurame sai Hauwah da Kaka suke Dan taba Hira lkc zuwa lkc Kaka tana mamakin mugun halin jikar tata ita bataga laifin namiji ba idan yanada halin ajiye mace sama da daya ba don ya ajiye amma Mubaraka ta dauki qunci ta dorawa kanta.

Sai wajen 11:00am Hajiya ta iso gdan ita da autanta tunda taji tsayawar motarsu gabanta ya fadi, hakadai ta zauna har suka iso anata gaisawa shikuwa hankalinsa yanakan matar yayan nasa da kullum yake kwana da tunaninta.






Zamewa Hauwah tayi daga kujerar ta gaida Hajiya ta kalleta a qasqance tace “me kuma wannan takeyi anan?" Tabe baki Mubaraka tayi tace “uhm inaji zaman sa ido tazo" dariya Hajiya tayi Zainab tace “lallai fah sa ido to atashi abamu guri tunda ba fadar tsoho bace.

Jikin Hauwah yayi matuqar sanyi ta miqe a gajiye idanunta ya ciko da qwallah ta nufi qofar da zata shigar da ita bangarenta sukaja tsaki a tare tare da qwashewa da dariya Hajiya tace “don Allah jibi yanda take tafiya a wani tattale wai ita miji ya kwanta da ita ko uban waye baiji abinda tajiba"






Duk da haushinta da muneef yakeji Saida yaji babu dadi akan abinda akayi Mata yace “haba Hajiya kullum sai ki rinqa abu kamar wata yarinya wannan bafa girmanki bane zaki zubarwa da kanki mutunci ne a banza kisa yarinya qarama ta rainaki inama ruwanki da tsakaninta da mijinta ne wai don Allah"

Daquwa ta watsa masa tace “kaima saina sallama mata tunda duk sallamammu na haifawa duniya nifa kawai tsanar yarinyar nan a jinina take bazan taba sonta ba har abada" 






Itakuwa Jiddoh dakinta ta shiga ta fada saman gadon ta fashe da kuka sosai kalaman na surukarta suka kashe Mata jiki ta rasa meye yasa kullum Hajiyan Lameer bata fadan alkhairi akanta kullum cikin jifanta da mugayen kalamai take.

Yini tayi surr a kwance zazzabinta ya tsananta har wajen magrib tana kwance, daqyar ta iya miqewa tayi sallah sannan ta dawo parlourn ta kwanta ta rufe jikinta da hijjab dinta tanajin sanyi yana ratsata bude qofarsa taji ta sauke numfashi tare da dagowa ya tako da sauri yace “lfy meye kuma Babe?" Fashewa tayi da kuka tace “tun tunda ka tafi kaina da cikina yake ciwo inajin kamar zan mutu" 





A gigice yace “amma bakida lfy gidan nan cike da dangina a rasa wanda zai kirani ya fadamin" fita yayi yana masifa ya sauka qasan ransa bai taba baci irin na yau ba ya rinqa qwala musu kira yana bala'i fadi yake “saboda tsabar an rainani an mayar dani dan iska ban isa na kafa doka a gdana a bita ba to wlh anyi kadan ayimin wannan iskancin a gdana, itama fa matatace kuma sonta nake fiye da yanda kuke zato da kowa zan iya keta riga akan lamarin daya shafi Hauwah tsabar wulaqanci jiya batada lfy bata fito ba kun rinqa kirana Kuna fadamin matata munafuka ce taqi fitowa cikin dangina ayi Hira da ita, yau taji dama dama ta fito kun koreta har kuna caccaba mata magana, kuma a rasa wanda zai bita yaganemin lfyrta hardake Hajiya bayan kinsan yarinyar nan amanace a gurina to wlh bazan dauki wannan iskancin ba daga yau kada wanda ya qara takomin gidana tunda zuwa kuke domin ku rabamin kan matana kun zabi wacce kukeso a ciki, saboda haka ku dauketa ku tafi da ita bana buqata wannan din da bakwaso ni ita nakeso" 






Duk wani wanda yake gurin saida cikinsa ya karta lallai ran maza ya baci yau ankai Lameer bango, miqewa sukayi sumsum suka fara ficewa bai jima ba ya dawo da gudu gudu ya haura saman ya daukota cak sai rawar sanyi takeyi ya fito da ita yasata a mota hajiya tabisa jikin motar ta Kira sunansa yayi saurin daga mata hannu yace “kiyi hqr Hajiya wlh bazan saurareki ba kece kike sabbabamin duk wani Abu da yake damuna a matsayinki na uwa kin dauki lalurata abar yayatawa a duniya kamar kaina aka fara nasani bantaba cemiki komai ba sannan kin fifita matar da take qarqashin ikona ni danki fiye dani still kina daure Mata gindi abinda takeso shi takeyi kin nuna mata banada wata daraja a gurinta haka qanne na saboda haka ki dauketa ku tafi da ita wlh a yau dai bazata kwana a gidana ba kiyi Mata daki a gidanki ki kula da ita samada wacce nakeyi mata" yana gama fadin haka ya figi motarsa a guje ya fice daga gdan...........







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*

____________________________

*38*

____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________






Daqyar ta lallaba da rarrafe ta sauka daga step din banen ta zauna a tsakiyar parlourn tanata juyi azaba ta isheta tanata murqususun azaba ga neman agaji babu me agaza mata.

Lameer bai samu kansa ba sai bayan dogon wani lkc ya fara dawowa hayyacinsa ya kwanta luf a jikinta yana shafa sumar kanta.

A hankali ya janye jikinsa daga nata ya koma ya kwanta yana mayar da numfashi har yanzu jikinsa bai daina rawa ba saida ya kusa 30 minutes sannan ya dawo normal ya tashi zaune yakai hannunsa ya kunna sweech.





Zuba mata ido yayi yana tunanin abinda ya kamata ma yayi mata yasani ko baa fada masa ba yayi Mata barna, miqewa yayi ya shiga bathroom ya hada ruwa me dumi ya zuba magani a ciki ya koma ya daukota cak kamar gawa yazo ya sanyata cikin ruwan.

Motsi bai samu arzikin tayi ba balle yasa ran zata farfado hankalinsa bai qara tashi ba saida yaga ya gama gasata ya fita ya gyara gadon ya canye bedsheet din da ya baci kaca² ya share hawayen tausayinta ya shimfida wani ya koma ya daukota ya sanya mata wata rigar ya kwantar da ita.






Shima wankan yayi ya dawo ya zauna ya rinqa danna mata qirjinta can yasamu yaji numfashinta ya fara dawowa a sannu har ya daidaita ta sauke numfashi a hankali ta bude idonta sukayi ido biyu dashi zaune a gefenta, hannu ya kawo zai tabata ta kuwayi saurin rintse idonta jikinta na rawa.

A hankali cikin sanyin jiki yace mata “sannu kiyi hqr kinji" kada masa Kai tayi cikin kuka ta rinqa nuna masa qofa ya sunkuyo daidai kanta yace “me kikeso nayi miki?" Qofa ta nuna yayi ajiyar zuciya yace “in fita hakan yayi miki?" 





Daga masa kai tayi yace “ok kiyi baccinki gobe zankira likita ya dubaki" batace masa qalaba yaja Mata duvet ya rufeta ya kashe mata fitilar ya fice, tunda ya fita ta keson miqewa takasa sai aikin kuka tanaja masa Allah ya isa aranta da haka har bacci ya sake dauketa.

Yana fita qasa ya sauka domin dauko system dinsa a dakinsa na bangaren Mubaraka me zai gani, a kwance ya ganta male male a qasa tanata riqe ciki tana ihu, gabansa ya fadi ya matsa da sauri yace “subhanallahi meye hakan ke kuma?" Matsawa yayi ya dagota ta riqeshi tana kuka tana cewa.







“Wayyohh Allah Lameer cikina zan mutu na shiga uku na" roqeta yayi da qarfi yana kallon qasanta yanda jini ke zuba yace “me jini Mubaraka" ya fada cikin tashin hankali tare da direta da sauri ya nufi inda ya baro ya bude qofar ya shiga ya dauko wayarsa ya fito da sauri.

Kinkimarta yayi yasa a mota suka fice daga gidan asibiti ya nufa da ita yana zuwa sukazo suka shiga da ita ya dauki wayarsa ya kira Hajiyansa, saida tayi ringing sau uku sannan aka daga ya sanar da ita abinda yake faruwa, a gigice tace “ok gamunan"






Hankalinsa ya kasu kashi biyu ga jiddah daya baro itama tana buqatar tallafi ga wannan me labour din, duk ya matsu ya koma gurin Hauwah.

Su Hajiya zasuzo zasuzo basuzo ba sai bayan anyi sallar asuba suna isowa tana haihuwar danta namiji.

 Suna gaisawa nurse din ta fito tayi musu albishir fara'arsa ta fadada yayiwa Allah godiya shikuwa Muneef daya kawo su Hajiya banda yaqe babu abinda yakeyi lkcn da Nurse din ta fito da jaririn Lameer yayi saurin karbarsa ya yaye towel din da aka nadesa.






Gabansa ne yayi wata muguwar faduwa ya dago da sauri ya kalli Muneef ya sake kallon yaron ya sake kallon Muneef shima Muneef din shi yake kallo nasa gaban yana faduwa suka sauke numfashi lkc daya ya taka a hankali yace “hajiya gashinan Muneef yayi masa huduba zanje gida na baro Babe itama babu lfy" 

Su kansu iyayen mamakin tsananin kamar sukeyi duk da kasancewar ba abin mamaki bane amma kamar tayi yawa hasken idanun yatsun da komai na yaron na Muneef ne babu ta inda ya dauko kama da Lameer Hajiya ce ta sauke numfashi wani abu yana dawo mata amma sai tayi saurin kawar da tunanin da cewa “au dama da tamu dakai dan ubanka jeka zanzo gidan na sameka gaka gata tayimin bayanin dalilinta na zagin Muneef Kaine ka bata damar yiwa kowa rashin kunya ko kuwa halinsu na haye zata nuna mana"





Alh ne yace “wai meye ya faru ne?" Juyawa Hajiya tayi tace “wai fitsararriyar yarinyar nan ce jiya ta qarewa auta tanadi a gaban sullutun yaron nan amma ya kasa cewa da ita komai" 

Murmushi Alh yayi yace “Kema dai Hajiya da shiga shirgin da babu ruwanki kike banda abinku Hauwah ai yarinya ce rainonta Magaji yakeyi har yanzu kuma ma banda son dorawa kai damuwa irin naki Muneef ai qaninta ne tunda qanin mijinta ne" 





 

Shidai Lameer gaba yayi ya qyaleta tanata sababinta saboda hankalinsa yanakan Hauwah baisan halin da take ciki yanzun ba, mota yaja ya nufi gdan zuciyarsa cike da zullumin tujararta.

A yanda ya tafi yabarta haka yaje ya tarar da ita gabansa ya fadi ya haura gadon da sauri ya yaye bargon ya dagota ta bude idonta da suka kumbura sosai saboda kukan da  tasha ta qoshi ga jikinta da ya dauki mugun zafi yace “zazzabi Babe sannu" wayarsa ya daga ya kira number Salees ya sanar dashi abinda ke faruwa.






 Aje wayar yayi ya kwantar da ita ya cire mata komai na jikinta ya jiqa towel ya fara danna mata jikinta a hankali tana sauke numfashi tana binsa da kallo idonta nata shararar hawaye.

Jiddoh bakin tsiwa ya mutu ba baka sai kunne tayi danasanin cewa saiya siyo mata abinda zataci ta samu babe sai yanzu maganar qawarta indo take fado Mata da dake fada mata ashe tanan ake samun ciki har a haihu da kanta ta tsinewa gidadancinta daya kada barinta ta waye ta gane abubuwa dabata yarda wannan tsautsayin ya fada Mata ba.............






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

___________________________

*37*

___________________________

*UMMUH HAIRAN*

___________________________





Daqyar ya iya kai kansa gdan yayi parking ya shiga babu kowa a parlourn kasancewar dare yayi sosai kusan shabiyu da kwata, part din Mubaraka ya shiga yana shiga kuwa ta miqe tace “ina yata?" Zama yayi yace “zan kawo miki yarki amma da sharadi itama dole ayi Mata abinda takeso dama tunda kuke baku taba zama tare ba saboda haka kiyi hqr yau da gobe ta zama ranarta qila Allah yasa na bata nata sai na huta tunda kema girmanki iya jikinki ne"

Tabe baki tayi tace “nifa duk wannan bai dameni ba idan kaga dama ma inka tafi karka dawo Amma dai a kawo yata wlh"






Ajiyar zuciya yayi yace “ok bakida matsala ya fice da sauri ya nufi part din Hauwah ya bude sakin ya shiga ya kunna lamp din dakin tana kwance hankalinta kwance tana baccinta rungume da Fadwah ya sauke numfashi yanajin yanda mararsa ke daurewa ya sanya hannu ya bambare yarinyar a jikinta takuwa bude idonta da sauri yayi mata murmushi yace.

Ai kince idan na siyo miki abinda zakici kiyi ciki zaki bata yarta to na siyo miki ki jira nakai mata ita sai nazo nabaki a nutse, da farko qin yarda tayi saida ya hada mata da dabara ya nuna Mata magungunan yace sune yanzu zai dawo ya bata, aikuwa sakaryar saita yarda tana kallo ya fice da yarinyar itama ta fito parlourn ta tsaya tana jiran shigowarsa.






Bai bata lkc ba ya dawo ya kama hannunta yace “muje dakina na baki haqqinki tunda kin buqaci abinki" zugwi² tabisa suna shiga ya dannawa qofar key ya zaunar da ita a saman gadon yace “jirani nayi wanka na dawo" takuwa zunburo baki tace “wai sakayita jawa mutum aji saboda ya nemi haqqinsa ni wlh banason irin haka"

Dariya ta bashi sosai yaji tausayinta saboda ya fahimci ita inda ta dosa ma daban da inda ya dosa, bathroom ya shiga ya cire kayansa ya jima yana qarewa dick dinsa kallo shi kansa ya tsorata da yanda yaga ta miqe sambal dama gata babu ta inda ta samu tawaya kota wajen kaciya a miqe take cak.






Wanka yayi yanajin wani mahaukacin feel dabai tabaji ba tunda yake a rayuwarsa shi da kansa tausayin kansa yakeji da baisan irin wannan yanayin ba a ransa yana cewa “yanzu fah akai Wanda shi kullum a haka yake kasancewa cikin shauqi"

Wasu hawaye suka zubo masa ya daura towel ya fita yana tsane jikinsa, tagumi tayi ta zuba masa ido har ya gama ya dauki turare ya fesa ya take sumarsa ya matsa gabanta ya riqo hannunta jikinsa yana rawa yace “me kikeso kici kafin mu kwanta?" 






Shiru tayi ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa ta shige jikinsa tana shafa nipples dinsa da yariga ya sabar Mata da shansu da wasa dasu tace “ni kawai abun zaka bani matarka ta daina yimin gori ai dama nasan ba sona kakeyi ba shiyasa kaqi bani har saida aka fara yimin gori..."

Maganarce ta maqale saboda wani irin tsuma da taga jikinsa yanayi yana  danna kanta saitin nipples dinsa ta kama da sauri ta fara tsotsa ya saki qara tare da zamar da ita saman gadon ya fara lalubar qirjinta yana shafawa a hankali yana sauke numfashi ita kuma tana qara narkewa a jikinsa saboda zuwa yanzu tasan dadin wannan harkar duk gidadancinta saida yayi nasarar koya mata romance da wasu abubuwan.






Sun jima suna wasanninsu saida yaji ta cika bamdam da ruwa sannan ya zare towel din jikinsa saboda sanin halinta yasa bai bari ta fahimci meye yake shirin yi ba ya dora bakinsa akan nata yasa hannunsa yana wasa da gabanta ita sauke masa nishi tana sake tura masa yayi dabarar zarewa tare da maye gurbin yatsan nasa da joystick dinsa.

Tayi saurin zaro ido tare da qoqarin tsuke qafarta amma babu dama shikuwa jikinsa rawa yakeyi yana dannawa a hankali yana zarewa yanajin yanda mararsa ta jiqe jagaf da ruwan dadinta me dumin gaske baisan santa ya danna dick dinsa da qarfi ba ta kuwa cije lebansa saboda azaba yayi saurin janye bakinsa daga nata yanajin yanda penis dinsa take kutsawa hawa hawa kamar step din bene.






Tureshi takeyi tana qara datse haqoranta saboda azabar da tunda uwarta ta haifeta bata taba riskarta ba tana jijjiga kai jikinta na rawa amma ta kasa motsa komai na jikinta kasancewar qarfin ba daya ba.

Wata zungura da yayi matace tasata sakin wani ihu tare da kakarin amai, shikuwa gogan yayi nisa sai nishi yake yana Kiran “wa... wayyohhhh Babe dam... Haka akeji haka dadinki yake ohhhhhhh babe dadi wayyohhhh Hajiya ta ahhhhhhh Alh na...." Baisan babe tuni ta dade da nisa da duniyar da yake ciki ba ranta yana tsakanin sama da qasa yana lilo ko ya fado qasa taci gaba da rayuwa ko kuma yayi sama gobe a tashi da jana'izarta.





Sosai yayi qara'in rayuwa a wannan dare yayi budurinsa son ransa inda ita kuma Mubaraka ta kasa tsaye ta kasa zaune har bangaren Hauwan ta hauro daidai lkcn Hauwah ta saki ihun nan ta matsa gaban qofar taji yanda yake gurnani yana kiran Babe dadi yanata faman ambaton Hajiya Alhaji.

Tunda ta zube a gurin mararta ta riqe saboda tashin hankali da baqin kishi tafi awa daya tana fama da azabar zuciya data fili bayanta da mararta ciwo kamar ranta zai fita ga ihun mijin nasu da take jiyowa yana ta fadin dadi zai kasheshi sosai tayi data sanin haurowa domin jin qwaqwaf din.





 Tabbas yau zarginta yakau ashe itace baya buqata baya sauke mata haqqinta saboda qiyayya ashe kamar yanda qaninsa yasha fada mata sharholiyarsa yakeyi tun kafin yayi aure, ashe gaske ne mata yake rabawa kuzarinsa, yau gashi taji zahiri da kunnenta a cikin gdanta rashin hqrnta yaja Mata jiyowa kanta bala'i.

Tun tana tunanin ciwon zai lafa ta rarrafa ta koma bangarenta harta fawwalawa Allah komai tasan yau kashinta ya bushe gashi talatainin dare bare tace zata Kira wani ya kawo mata dauki.................







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*36*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

_____________________________





Ihun ya rinqa jiyowa sama sama ya tashi ya fito da sauri ya kasa kunnensa ya jiyo muryar Mubaraka ce taketa zunduma ihu tana neman dauki da gudu ya nufi bangaren Hauwah yyana shiga yatarar da Hauwah tanata nadarta duk ta yaqushe mata fuska da faratanta.

Da sauri ya matsa ya janye Hauwah daga kanta yace “ya salam Hauwah meye hakan me kikeson yi bakiga abinda kikayi mata ba bakida hankali ashe Zaki kama dukan me tsohon ciki...." 





Rushewa tayi da kuka ta zame daga jikinsa ya matsa ya daga Mubaraka takaici kamar ya kasheshi wai duk girmanta ta tsaya Hauwah ta yimata wannan mugun dukan ko kunya babu sai kuka takeyi, takaicine yasashi daka mata tsawa yace “dallah malama fice mata daga daki godai godai dake ki tsaya wannan yarinyar ta kama dukanki kina ihu har masu gadi sunajinki don abin kunya"

Miqewa tayi ta matsa zata dauki Fadwah Hauwah tayi saurin miqewa ta  dauke yarinyar tace “wlh bakeba ko ubanta bai Isa ya rabani da itaba a yau indai irin wannan yarinyar ce zakiyimin gori akanta ai nima macece  saurin me kikeyi abinci ne inaci saboda haka kowanne lkc nima zan iya haihuwa ko babe?"





Harararta yayi ya nunawa Mubaraka hanya yace “fita muje kekuma bata yarta" qanqame Fadwah tayi ta dauki zani ta goyata tana kuka tace “wlh bazan bayar da itaba nima sai kayimin alqawarin zakayimin ciki na haifi nawa a daina yimin gori gashinan saboda bakasona ka tsaneni ita har kakuma bata wani babyn amma ni kaqi bani abinda zanci na samu ciki"🤔

Wani gumine ya karyo masa ya kalli Mubaraka da take tsaye qiqam yace “muje Mmn Fadwah ke kina da hankali wannan kiyi mata uzuri yarinya ce..." Tsalle tayi ta dire a gefe tace “tabdi wai yarinya ai wlh ko digon maniyyi ce saita bani yata" kanta Hauwah tayi yayi saurin riqeta tace “nikuma yau naga ubanda zai rabani da ita"






Dafe kansa yayi tare da cewa “ya salam wai duk cikinku babu wacce zan fadawa taji ne" tabe baki Hauwah tayi tace “wlh kuwa nidai baji zanyi ba idan anaso nabada yarinyata to aje  a siyomin abinda zanci nima cikina yayi qatoto na haihu idan ba hakaba kuwa na fara fashin yara a unguwar nan"

Haukan Hauwah fah yafi qarfin sanin Lameer ya rasa yanda zaiyi dasu dukkansu ga wata muguwar gajiya dake damunsa agogo ya kalla yaga goma harda rabi dabara ta fado masa ya matsa kusa da Hauwah ya tsugunna yace “don Allah badon niba ki bata yarta insha Allahu kema a daren nan zan baki naki babyn" 






Murguda masa baki tayi tace “cabdi ni zaka yaudara ka mayar dani lusara ai wlh yau indai kaga nabada yarinyar nan to naga ka fita kaje ka siyomin nima naci cikina ya fara zama qato dama ai kwanaki Dana tambayeka cemin kayi saina fara period kuma naga wata uku kenan da fara period dina..."

Dora hannu aka yayi yace “nikam na shiga uku da tonon silili naji ki bari gobe zan siyo miki" wani murmushi da tayi ta matsa ta kashe sweech din dakin tace “dan Allah babe idan kun fita ku rufe mana daki kuma gobe ko mutum yaqi ko yaso dole ya hadomin kayan yata, hmmmm uhmmm kama rainamin hankali baqin wayonka wanne ne bansani ba"





Juyawa yayi ya kalli Mubaraka yace “kije zan kawo miki yarki" takaici ne yasata fita taja qofar da qarfi tace “oho dai ta baya ta rako nikam nayi gaba" matsawa yayi ya zauna a kusa da ita yace “naji zan baki baby wlh nayi miki alqawarin a daren nan kome zanyi insha Allahu saina baki babe kin yarda?" 

Kada masa Kai tayi ta kwantar da kanta a jikinsa tace “ni Ina ruwana nidai kawai abani a huta" murmushin tausayin kansa yayi ya miqe yace okay   jirani Ina zuwa" fita yayi ya nufi gidan abokinsa Salees a motarsa dake darene babu yawan abin hawa yasa nandanan ya isa gdan ya kirashi a waya ya fito.






Gumi yake sharewa sosai duk da A.C motar amma ya jiqe, Salees ya dubeshi yace “na tsorata da kiranka a wannan lkcn Captain" gumi ya sake gogewa yace “akwai matsala ne Saleesu wlh rigima ce ta kacame a gidana na rasa ya zanyi nayi maganinta" nan ya zayyane masa komai.

Mamaki ne ya cikashi yace “au kai dama kawai rabosu kayi da yarsu dan kasata a gaba kayita kallo? Waikai Lameer yaushe zaka zage ka nemi magani ne babu wani ciwo fah da bashi da magani ace kana zaune namiji har namiji amma matanka suke kawo maka irin wannan qananun rainin?" 





Shafa sumarsa yayi ya dauke qwallar idonsa yace “bazaka ganeba Salees Ina neman magani wlh amma kullum abin kamar gaba yakeyi nifa nafi alaqanta hakan da halitta tace a haka kawai nidai yanzu idan kanada wani taimako kayimin don Allah na raba raini da yarinyar nan wlh tunda ta kafe idan ba bala taji ba bazata bata yarta ba"

Shiru Salees yayi nadan lkc sannan yace muje Sokoto road akwai wani coursing dina da yake da irin wannan case din baya rabo da magunguna saboda abin ya zame masa jiki" suna tafe suna hira har suka isa cikin saa kuwa suka sameshi yana gari sukayi masa bayani aikuwa ya bashi wasu qwayoyi uku yace ya hadiya kafin yaje gda zaiga aikinsu sannan ya basa wasu package guda da wani syrup yace ya rinqa sha kullum da safe zai taimaka masa sai wani cream shima da zaike shafawa dick dinsa kudin kayan kawai dubu dari da talatin a take ya caketa cike da farin ciki ya juya gida, ai tunkafin yaje gida ya farajin wani yam² a jikinsa nandanan yaji makaman yaqinsa sun fara wani zabura.................







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*

____________________________

*39*

____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________





Paid before read pls,for this  Account number

0255526235 Fauziyya Tasi'u Umar GTB

Ko card ta  WhatsApp number: 09013718241:




Kuka takeyi sosai yana yi mata could na jikin nata, knowking din qofar da yaji anayi ne yasashi mayar Mata da rigarta yaja duvet ya rufe Mata jikinta ya fita suka shigo da Salees din ya dubata sosai yace.

“Kawai dai rashin sabone a hankali zata ware insha Allahu magunguna yabasa yace “ka bata wadannan kuma ka rinqa yimata sitbath godiya yayi masa suka fita suna fitowar sukuma su Mubaraka suna dawowa ganin Hajiya riqe da jaririn yasa Salees fahimtar meye yake faruwa yace.





“Dama madam ta haihu baka fadamin ba?" Murmushi yaqe yayi yace “na shafa'a ne hankalina yanakan babe" kallonsa Salees yayi yace “kamar akwai abinda yake damunka Lameer?" 

Girgiza kai yayi yace kada ka wani damu kawai jikin yarinyar cannne ya dameni gashi wani aiki ya tasomin zan sake komawa U.S.A nanda sati biyu inason tafiya da Hauwah saboda zuciyata ta kasa nutsuwa da zamanta anan" murmushi yayi yace “a cikin iyalinka kace ka kasa nutsuwa to a inane zaka nutsu? Yadai kamata ka zama adali a tsakanin iyalanka saboda hadin kansu kaima shine farin cikinsu kabarta ta saba da matarka da yaranka kafin itama Allah ya bata nata hakan shine zai dawwamar da zaman lafiya tsakaninsu"





Jinjina kai yayi cikin alamun yarda da  shawarar abokin nasa yace “kuma fah hakane na saba da yarinyar nan fiye da yanda kake tunani banason ko kadan tayi nesa dani Amma zan kwatanta insha Allahu" 

Murmushi yayi yace “aboki wannan yarinyar ta shigeka da yawa" dariya sukayi sukayi sallama ya tafi shikuma ya koma cikin gidan yan uwansa duk sun hallara a parlourn a gurguje ya tsaya suka gaisa ya haura saman gurin petain dinsa yana shiga ta ganshi ta kuwa rushe da kuka tace “ni ka fice mugu kawai mara tausayin yaro kawai wlh Allah saiya sak...."






Rufe Mata baki yayi yace “sheeeet banason surutu yanzu saina qara miki gajiya" rufe bakinta tayi tana shassheqar kukanta ya fita ya shiga kitchen ya hado mata tea me kauri ya soyo mata qwai ya dawo ya tasheta tana rirriqeshi yace.

“Kin cika raki wlh saikace kanki aka fara dama kikayi saa banja miki dinki ba" turo baki tayi zatayi masa tsiwa ya kama hannunta ya dora a saitin dick dinsa yace “tun jiya har yanzu bata kwanta ba" ai babu arziqi tayi shiru saidai Jan zuciya da qwafa da takeyi.






Shi abinma dariya yake bashi haka ya rinqa bata shayin tanasha kamar  magani komai ba dadinsa takeji ba suma magungunan daqyar tasha aikuwa tanasha ta fara kwara amai daidai lkcn yaji muryar qanwarsa Zulaiha ya matsa ya bude Mata tace.

“Ina Aunty na gurinta nazo naga bata sauko ba tun dazu..." Haɗiye mgnr tayi tace “subhanallahi me zan gani Yaya wata ta sauka wata ta kamu kenan to Allah ya raba lfy" harara ya watsa Mata yace “banson shegen surutunki zakizo ki dameta tana fama da kanta"miqar da ita yayi tana bubbude qafarta tana kuka ya rungumota jikinsa ya dagata cak yana cewa.






“Kiyi hqr bansan haka zakisha wahala ba da bazan yi miki ba amma bazan qaraba daga yau kinji" daga masa kai tayi tace “kuma ma ni banason babyn ka riqe kayanka shegen babyn dama sai ansha wuya kan asameshi nikam bazanma haihuba to indai hakane.

Murmushi yayi yace “inmadai Zaki haihun ba yanzu ba sai kinzama yar hannu qugunki ya qara qwari ko?" Turo baki tayi tana qara lafewa a jikinsa tace “nidai banaso mutuwa zanyi yanzun ma saura kadan har Windows na gani sun bude ta saman dakin nan"





Ba Shiba hatta Zulaiha da suka manta da zamanta saida tayi dariya cike da mamakin lamarin Yayan nasu wata kusan takwas sai yanzu yasanta ya mace lallai ba qaramin lusari baneshi ya zauna da wannan zillaziyar matar gda daya su kwana daki daya amma saidai su kalli juna.

Koda ya shiga da ita bathroom din ruwa ya sake hada mata yasata a ciki ta qanqameshi kuwa tana kuka tare da karkarwar haqori saboda shigar ruwan ba qaramin azaba yake bataba a hankali ya rinqa rarrashinta har ta haqura ta zauba.





Saida ruwan ya salamce sannan ya sake yimata wanka takuwa danji qarfin jikinta ya nadota a towel suka fito ya dauko mata doguwar riga mara nauyi wacce bazata takurata ba ya zura Mata ya shafa Mata Mai da powder sannan ya dauketa cak ya fito da ita parlourn.

Turus yaja ya tsaya ganin Hajiya da yayarsu Zainab wacce suke Kira da Abulle a tsaye a parlourn kunyace ta kamashi ya matsa ya direta saman kujerar yace “yanzu nake shirin  saukowa mu gaisa itama batada lfy ne so wanka nayi Mata na bata magani shiyasa ya babyn yanadai lfy ko?"






Wani takaici Abulle ta hadiya itako Hajiya daquwa ta watsa masa tace “soko lusari shashasha kazo ka lalace a gurin wannan aljanar yarinyar danka na cikinka ma da yazo duniya yau bakada lkcnsa balle uwarsa to bazan yarda da wannan iskancin ba bazaayishi a kinina ba rashin adalci qiri² har kana kallo wannan yar tatsitsiyar yarinyar ta kama Mubaraka  ta daka ta yaqushe mata jiki haka ammaka kasa daukar mataki qarshe ma ka dauki kwananta ka kawowa wannan rabin mutum din har fadimun take tanajinka kana ihu kana Kiran dadi kana zunduma min kira to ubanka zan maka bakai kaje ka dauko abinda zai karka ba"






A matuqar kunyace yace “haba Hajiya wannan mgnr ba taki bace tsakanina da matanane don Allah kada ki shiga munfi kusa tunda tare zaki tafi ki barmu...." Daquwa ta watsa masa tace “zan barkun ubanka ai yau qafata qafar Mubaraka yarinyar nan batacin maka ba batasha maka ba ka uzzura mata ka hanata sakat ga tauye haqqi yanzu kai inkaine akayi maka haka zakaji dadi kaji matarka da wani qato tana ihu tana Kiran a taimaka Mata dadi zai kasheta dadin ubanka wannan jemammiyar fatar har wani gardi zatayi saidai santsin quruciya sakarai kawai"






Haushi ne ya cika Lameer yace “to waima labe tayi mana ne?"  Da sauri Hajiya tace “Eh labe tayi tana zaman zamanta ta taso ta hauro tajiyoku kuna bawa sama hayaqi ni har kunya naji da tana fadamin yanzu ma sai kuka takeyi saika saki wannan yarinyar wai ta rabaka da ita baka ko son ganinta"🤣

Tabe baki yayi yace “tunda kin zama yar aikenta kice Mata bazan sakiba sai naji kan Bindiga a maqoshina, da jibi ma zamu wucce amma yanzu dole sai anyi suna" dakinsa ya shiga ya fito da kudi yabata yace “gashinan kikai mata suyi duk abinda ya dace"..............






_Ko a lbr bantabajin sakaryar uwa irin Hajiya ba_🤣🤣






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*

____________________________

*40*

____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________


Paid before read pls,for this  Account number

0255526235 Fauziyya Tasi'u Umar GTB

Ko card ta  WhatsApp number: 09013718241:





Hauwah ce tace “Hajiya zanzo inga jaririn" harara ta watsa mata tace tunda uwarki ta haifa mata ai saikizo ki gani shegiya me qirar samudawa..." Daga mata hannu yayi yace “ya isa haka don Allah kada ki dorawa yarinyar nan damuwa"

Juyawa tayi tace “eh ita aita dorawa wani ai komai takeyi Kaine ka daure mata gindi da anyi mgn sai kace yarinya ce Ina wata yarinya tunda har ta iya qacen kwana ta kwana da miji" shidai bai qara cewa qala ba sai Zulaiha ce tace “don Allah Hajiya kije wannan ba girmanki bane ita wacce kuke surutun nan ma akanta in kuka nutsu zakuga ba abinda ke gabanta kenan ba"





Abulle ce ta daga Mata hannu tace “kekuma rasa kunya waye yasa dake nifa wlh kawai na tsani yarinyar nan" cafewa Hajiya tayi da cewa “ni dama bantaba son mayyar yarinyar nan ba dandai kawai Alh yafi qarfi nane qur'anin Allah da sai ya saketa"

Murmushin takaici yayi ya kalli Hauwah da itama ta kalleshi da sauri idonta ya ceko da qwallah ya kamota jikinsa ya rungumeta yana shafa bayanta yace “saidai hqr kuma ba ke Zainab wlh ki fita daga harkar matata kada kema kijawa kanki raini"






Daga haka bai qara cewa komai ba ya mayar da hankalinsa wa wasa da gashin Hauwah ita kuma tayi luf a jikinsa tana lumshe ido ganin daga ita harshi babu me kulasu ne yasasu fucewa daga part din yayi ajiyar zuciya yace.

“don Allah ki meye zasuyi miki kada ki kilasu kinga duk sun haifeki kina kulasu zaace kinyi musu rashin kunya musammam Hajiya" gyara kwanciyarta tayi a jikinsa tace “toni kuma Ina ruwana dasu nifa na fahimci ma duk danginka Aunty Zulaiha kawai ke Sona saboda haka Nima nasan zaman da zanyi dasu Allah babu ruwana da kowa sai Alhajinka sai Aunty Zulaiha kuma ko gdanku bazanke zuwa ba"





Shafa qirjinta yayi yace “amma ni ai da ruwanki dani ko?" Zabura tayi ta tashi zaune da sauri tana cije lebe tace “ai kaikam sai mun tsaya hisabi gaban Allah na muguntar da kayimin kawai dan nace maka inason baby sai kazo ka sakamin wannan abin naka har maqoshina najishi bansan sanda na mutu na dawo ba"

Sumsumsum Zulaiha ta juya ta fice musu daga parlourn ta shiga kitchen din Hauwan ta fara hada musu abincin rana tunda tasan yanda take rakin nan yana biye mata ba abin arziqi zasu tsinana ba ga kuma baqi anatayi tasani sarai duk wanda yazo barka yaji sunanan zaice zaizo bangaren amarya to ga kuma amarya ta gamu da aikin maza ko tafiyar ma ita bata gwadawa daukar abarsa yakeyi duk inda zata.






Ranar gidan yini yayi da mutane shima Muneef anan ya yini dauke da boyayyen dansa yana qare masa kallo yanajin dama ace dansane na sunnah, gefe kuma yanata fakon fitowar Hauwah amma shiru gashi jiya yayan nasa yayi masa tsakani da bangarenta yace tunda tasu batazo dayaba to ya daina zuwa inda take.

Hakanan ya yini sukuku babu wani kuzari a jikinsa har zuwa yamma da ya gaji da jiran tsammani ya tafi.

Itakuwa Zulaiha tayi guri tanacan sunata hirarsu da Hauwah tanata kwasar dariya labari take bata na abinda ya hadasu da mubaraka tayi mata duka har tsautsayi yasa tace “itama saiya bata baby" 





Dariya sosai takeyi tace “kedai bazaki rabu da quruciya ba Aunty Hauwah dake waye yace miki da sauqi ake samun baby ai san ansha wuya gurin haihuwar ma jidali ne abuda kake kusan mutuwa qafarka daya a lahira daya a duniya" 

Cikin tsoro tace “nashiga uku na irin wahalar da nasha jiya kenan?" Dariya tayi tace “tabdi yarinya ai ta jiya shafar mai ce yanzu kinga kin gamashan wahalar wannan sauranki dadinsa shima kwananan Zaki fara kwasheshi anayi kina cewa ohhhhh babe qara yi da qarfi dadi Babe" kunyace ta kamata ta rufe idonta tace.






“Kayyy Allah Aunty Zulaiha babu dadi fah nikam bama zaa qara ba banaso ya riqe kayansa" murmushi tayi tace “aa baza ayi hakaba ki more amarcinki yarinya kiji dadinki da mijinki" wasu tarkace ta hada mata ta bata tace “bari na hada miki wadannan kisha Zaki dainajin zafin gurin zai washe yanzu"

Kofi ta dauko da nono a freegde ta zuba maganin a ciki ta karkada tabata tace “ki shanyeshi sannan ki sha wannan tsumin zakiji dadin jikinki sosai" shashashar ku ta bude ciki ta dirke magani tas ta koma ta zauna sukaci gaba da hirarsu.





Sai biyar mijin Zulaiha yazo ya dauketa sukayi sallama Hauwah me hannun kyauta turarukan da malamarta ta hada Mata ta bata cikin wadanda ta taho dasu sukayi sallama akan sai jibi zata dawo, sai lkcn ta samu damar sauka qasan Lameer na zaune a parlourn qasan yanata yiwa Fadwah wasa yaga fitowarta ya zuba mata ido yana mata murmushi.

Itakam qasa tayi da kanta Fadwah ta zame ta nufota ta washe baki tace “babena nayi missing naki bakije mun gaisaba yau" kwanciya yarinyar tayi a kafadarta shikuma ya janyota ta fado jikinsa ya sauke numfashi yace “kinyi kyau fiye da kullum babe sperm dina ya karbeki Allah yabani ikon bakishi kullum Allah yasa ke bazamu samu matsala dakeba"





Janyewa tayi a jikinsa ta dosana mazaunanta a kujerar tace “tabdi qatuwar matsala ma ai wlh ka dameni guduwa zanyi danma dai Aunty Zulaiha tace daga na jiya an dainajin zafi yanzu saura dadi" 

Mubaraka dake zaune ta hadiyi wani baqin ciki shikuwa gogan ya sake matsowa jikinta yace “ni dama dadi naji wai ashe har ihu na rinqayi Ina Kiran dadi zai kasheni oh su gulma anyi asara kuma kinsan ashe Hajiya na taji sanda nake ihun dadi gsky Babe na keta dabance" miqewa tayi a qufule tace “eh naji Lameer ai and dade ana ruwa qasa na shanyewa ba yau ka bara zalumtata ba ba yau ka fara cin amanata ba ince har Mata kake ajiyewa a garin da kake ko an fada maka bansani bane"






Ko kallonta baiyi ba ya dauke Fadwah ya sauketa a qasa yace “jeki kwanta Luvly" miqar da Hauwah yayi yace “muje ki tayani nayi wanka muyi sallah mu dora daga inda muka tsaya"Kama hannunta yayi suka shige suka barta tsaye da sakakken baki.

Zama tayi a kujerar dabas tana kallon jaririn hannunta tsoronta na qaruwa tunda ta haihu bayan daukar da yayiwa yaron a asibiti baiko qara kallonsa ba ko dazu data miqa masashi cewa yayi ta kwantar dashi, tsoronta yana qara nunkuwa a ranta tace “kardai fah ya fahimci wani abu"






Shima a bangarensa ya kasa nutsuwa zuciyarsa cike take da tunane tunane tana ayyana masa abubuwa da yasa game da matar tasa da dan da ta haifa masa ya rasa meye yasa daya kalli yaron gabansa ke faduwa, ya rasa meye yasa bayajin digon son yaron a cikin zuciyarsa kamar yanda yakejin na Fadwah.

Zubewa yayi a gadon yana saqale da babensa yace “ki kwantarmin da hankali Babe bansan meye yake damuna ba na tashi da farin ciki ya rikide ya koma damuwar da bansan meye asalinta ba" shafa qirjinsa tayi a hankali tace “could down babe dama wani lkcn ana samun haka fah"






Bakinsa ya dora saman chest dinta yayi kissing nata yace “yaushe Zaki bani babyn da zanyi farin cikin zuwansa duniya inason ranar da zanganki da cikina kina zama da yan dabaru, a lkcn ne zan kaiki rugarku su Baffa suganki da jinin Kado a cikinki naga yaya zasuyi da ikon buwayi"

Shiru tayi ta lafe a jikinsa tace “inason ganin Gwaggona nasan itama tanason ganina" numfashi ya sauke yace “kin tabbata?" Daga masa kai tayi yace “ok zakije very soon amma sai mun dawo daga U.S.A da naso barinki anan zuciyata taqi nutsuwa gara duk inda nake mu kasance tare"





Miqewa yayi ya fara rage kayan jikinsa ya rage dagashi sai boxes ya kashe musu hasken dakin ya kunna lamp ya shige bargon tare da janyota jikinsa ta fara zillewa yace “don Allah kada kiyimin haka nayi miki qoqari 8 mouths kina hutawarki haba Hauwah" 

Kuka ta saka masa tace “zafi fah har yanzu nakeji a gurin kuma gurin kamar ciwo dazu da naje zanyi fitsari..." Kwantar da ita kawai yayi a jikinsa yace “ok shikenan yi baccinki kawai" yanajinta tana sauke ajiyar zuciya har bacci ya dauketa yayi musu addu'a yaja musu bargo"





Shikam ba bacci yayi ba saboda wata muguwar sha'awa dake cinsa mararsa tanayi masa ciwo sosai maganin da yasha daren jiya bai sakesa ba har yanzu daqyar a daddafe asuba tayi yanayin sallah ya dawo ya rinqa lallabata da kalamai yana fada mata bazataji zafin ba.

Daqyar yayi nasarar shawo kanta ta yarda jikinta na rawa ya fara romance nata bai dauki wani lkc ba yaga ta sakar masa jiki har tana tayashi yaji dadin hakan sosai shima ya rinqa kunnata saidai ya tabbatar yakaita qarshe sannan ya fara shigarta da dabara da farko bataji zafin ba saida ya saita kansa a ciki ta qanqameshi cikin rawar jiki tace “wai.... wayyoh Lameer zaz...zafi wayyohhh Allah na........" 







_Yau bazaku jini da rana ba sai dare insha Allahu_






*UMMUH HAIRAN CE...*✍️

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *M.L*

_____________________________

*35*

_____________________________

*UMMUH HAIRAN*

____________________________





Lameer dake shigowa ya tsaya ya zuba musu ido tace “yawwa babe wlh kajawa wannan wawan qanin naka kunne ya fita daga harkata banason gulma da munafurci yazo ya wani kafeni da ido dubi yanda ya tsoratamin yarinya nifa banason shisshigi wlh rashin mutum babu ruwana ni"

Figar Fadwah tayi taja uban tsaki tayi shigewarta dakinta ta ajiyeta a saman gado tace “aikin banza mutum sai shegen sa ido" wasansu sukaci gaba dayi.

Duban Muneef Lameer yayi yace “meye ya hadoku da itane?" Wani takaici ya hadiye yace “nima ban sani ba wlh"





Murmushi yayi yace “kayi hqr kasan yarinya ce" wani nunkin takaici muneef yaji ya taso masa wai wannan yar mitsitsiyar yarinyar data waye a gabansa itace take caccaba masa mgn saboda tasamu daurin gindi gurin mijinta bai Isa yace komai ba hakanan ya juya ya nufi upstairs din.

Koda ya sauka bai tsaya ya saurari Mubaraka da ta hade kai da gwiwa taketa sharbar kuka ba yayi ficewarsa daga gdan saboda tafasar da zuciyarsa takeyi, tanaganin ya fito ta sake rushewa da tana dafe inda Lameer ya mareta saboda kawai tace saidai yabar gidan da Hauwah bazata iya ganin wannan iskancin nataba.






Ta jima a zaune a gurin komai ya rikice mata daqyar ta tashi ta shiga dakinta ta cire kayanta ta kwanta tanata rera kukanta, kiran wayarta yasata tashi zaune daqyar ta daga tana ganin sunan Muneef ta kara a kunnenta yace “yarinyar nan taci uwar rashin mutunci waini tacewa wawa a gaban yaya amma bai iya cewa komai ba harma tana cemin zatayimin rashin mutunci wai nine maye kuma Yaya yana kallo qarshe ma dariya yayi yacemin nayi hqr yarinyace" 

Haɗiye kukanta tayi tace “nifa dukana yayi abinda Bai taba yiminba mari har uku saboda na zageta nace Mata qazama kucaka baqauyiya" hawaye ta share tace “wlh bantaba tunanin Lameer yanada zafi haka ba har cemin yayi indai bazan zauna da matarsa ba saidai ni nabar masa gdansa wai baitaba farin ciki da aurena ba kullum baqin ciki nake qunsa masa"






Haka suka rinqa gulmarsu daga qarshe suka fara video sex saida suka gamsar da junansu.

Tana shirin ajiye wayar ya bude qofar ya shigo ya zuba mata ido tube haihuwar uwarta tayi saurin rufe wayar ta turata cikin shirginta, nazarinta yakeyi sosai yana mamakin yanayin daya tarar da ita a ciki juyawa yayi yace “idan kin gama abinda kikeyi ki kawomin coffee dakina" 

Batace masa qalaba ya juya ya fice ya shiga dakinsa ya shiga wanka ya kwanta yana danne²nsa da wayarsa.





Ta jima kafin ta shigo cikin shirinta na bacci dauke da qaramin set na coffee ta ajiye masa a saman table din ta zauna ta zuba masa ido ko kallonta baiyi ba ya ya miqe ta zuba coffee din a cup ya dauka har yakai bakinsa ya kurba ya zuba mata ido yana nazarinta gabadaya batada walwala tasa kishi a ranta duk ta zuge.

Tasowa yayi ya zauna kusa da ita ya shafa cikinta yace “ya bby na?" Haɗiye wani yawu tayi cike da fargaba tace “la...lafiy....." Kukane ya qwace mata ya kalleta yayi murmushi yace “kin dorawa kanki kishin babe aranki ita batama san kinayi ba bata damu dakeba kin damu da ita meye yasane?"





Kuka ta sake rushewa dashi tace “marina fah kayi saboda ita kaje ka daukomin yata Lameer ban yarda da zamanta a gurin makirar yarinyar nan b..." 

Saurin dakatar da ita yayi yace “karki shiga tsakanin yata da matata itama uwarta ce kulawar da zata samu a gurinta bazata samu irinta a gurinki ba saboda haka ki tsaya a matsayinki keba abin alfaharine a gurinki ba ta kama yarki ta riqe miki kullum Babe batada mgnr data wucce Fadwah nasan ba saboda kowa ta baro makarantarta ta biyoni Kano ba sai saboda Fadwah"





Tabe baki tayi tace “aidai nice na haifi abata ba uwar wani ta haifamin ba saboda haka dole abani abata wlh" miqewa tayi zata fita yabita da ido harta fice ya koma ya kwanta don yasan halin Hauwah duk bala'inta tafita.

Haurawa tayi cikin saa kuwa ta tarar da qofar a bude ta shiga parlourn ta zubawa parlourn ido abinda tunda take dashi bai tabayi musu ba shi tagani a parlourn manyan hotunansu shida Hauwah batasan sanda ta dauki cup ta jefi hoton dashi ba fuuuuuu ta nufi qofar dakin ta bude suna kwance tana rungume da Fadwah suna baccinsu cikin kwanciyar hankali sanye da baqar yalolowar rigar bacci ta baje gashinta a saman pillow.






Zuba mata ido tayi ko ita da take mace saida taji wani yarrr a jikinta balle kuma namiji, matsawa tayi tasa hannu zata janye Fadwah tayi saurin qanqameta ta fara shure² da qafa tace “nifa ka qyaleni nace ka tafi gurin matarka bazakazo ka dameni ba na gaji"

Fincikarta tayi da qarfi tace “ba tsinnanen mijin naki bane uwace tazo karbar yarta idan ba tsohon bafulacce ne ko tsohuwa me tallan nono da fura ta haifamin ba abani yata...." Ai bata gama rufe bakinta ba taji an shaqeta ta suka kama kokawa kafin kici wane wannan Jiddoh ta hada Mubaraka da bango ta hau kirbarta kamar Allah ya aikota babu kunya Mubaraka da taji wuya ta kama zunduma ihu.






*UMMUH HAIRAN CE...*✍️

[7/12, 4:44 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*



*42*





Yana fita asibitin su Salees ya nufa yakaita aka shiga da ita aka fara bata taimakon gaggawa cikin ikon Allah ta fara samun sauqi ranar anan suka kwana yana jinyarta tun a daren ya gama shirya musu komawarsu Lagos saboda ya fahimci sai yayi da gaske akan lamarin Mubaraka da Hajiyarsa.

Washegari sai goma aka sallameta suka tafi gida dayake sunsan tujararsa idan aka kaishi qarshe bai tarar da kowa ba hakan ya bashi damar sakewa sosai da matarsa ya rinqa bata kulawa sai washegari da yaga taji sauki sannan suka wucce Lagos.






Tunda suka koma Lagos yake riritata babu abinda ya sake shiga tsakaninsu yana maganinsa a hankali saida sukayi sati biyu sannan ya sake nemanta da kukanta da komai haka ya rinqa lallabata suka raya daren bai wani dadeba kamar karonsu na farko dana biyu gaba daya baifi minti uku ba yayi release.

Baiso hakan ba amma hakan ma yaji dadi sosai yana ganin alamun nasara haka rayuwar taci gaba da tafiya a hankali Hauwah ta fara sabawa da yanayin mijinta itama bata wani damu ba idan yazo miji idan baizoba salamun sukanyi sati biyu uku har wata wani abu bai shiga tsakaninsu ba duk ranar da zai nemeta kuwa to yini yakeyi a kwance da zazzabi da ciwon mara.






Shekararsu daya da rabi da aure soyayya babu irin wacce bata gani a gurinsa duk wani burinsa akan iyalansa yake, zuwa lkcn daqyar Alhajinsu yasa ya komar da Mubaraka dakinta hakan yasa ta dan nutsu bata nuna zafin kishinta akan Hauwah.

Ko dawowa sukayi bata fiye shiga harkarta ba saidai habaici da take jefar mawa da Hauwan ita kuma wata nutsuwa ta shigeta bata biyewa suyi saidai tayi murmushi, Abu daya da yake damunta shine gorin da dangin mijin sukeyi Mata wai baayi kyau ayi yado ba.






Akwai lkcn da ya matsa mata sukaje gaida Hajiya ya shiga gurin Alhnsa yabarsu itama Hajiya ta tashi ta shiga kitchen saboda ita har cikin ranta bata qaunad Hauwah hakan yabawa Muneef dake zaune a gefe damar tasowa ita bata ankara dashi ba ta miqe ta cire hijjab dinta ta ajiye ta fara gogewa Hajiya kayan da take gogewa ta tashi.

Batayi aune ba saijin hannu tayi a saman qirjinta da suka qara cika suke daukar ido, bin hannun tayi da kallo gabanta ya bada wani rass ganin farar fata sabanin ta mijinta chocolate, hannunta tasa ta janye hannunsa da sauri.





Miqewa tayi shima ya miqe kafin yayi aune ta daukeshi da mari bai dago ba ta sake sauke masa wani a daya kuncin jikinta na rawa ta nunashi da yatsa daidai lkcn da Hajiya take fitowa tace “Allah ya isa tsakanina dakai dan iska fasiqi maci aman....." 

Itama Marin taji an dauketa dashi daya sanyata faduwa cikin bala'i Hajiya tace “lallai kinzo birni kinci shinkafa kinsha madara har dana Zaki mara ki kalla a gabana kicewa fasiqi ubanki yayi miki...." Dagowa tayi ta zari dankwalinta daya fadi tace “au yanzu Hajiya bakiga abinda yayimin ba saini kikaga abinda nayi masa wannan zindiqin fasiqin har dane da zaayi alfahari dash....."






Dauketa taji an sakeyi da mari tana dagowa taga Muneef dinne, hannunta ta dora akanta ta rusa ihu tace “Allah ya isana wlh bazan yafe muku ba" fitowar Lameer da Alh tayi daidai da miqewarta ta zari hijjab dinta tana kuka mecin rai.

Nufota yayi da sauri ya riqota cikin tashin hankali yace “menene me sukayi miki" fadawa tayi jikinsa ta rushe da kuka me tsuma zuciya tana girgiza kai tana cewa dashi “mu tafi babe mu tafi bazan qara zuwa gidannan ba har abada wlh na tsaneshi na tsani Muneef Allah ya isana ya cuceni" 





Dagota yayi cikin tashin hankali yace “me yayi miki Hauwah fadamin meye ya hadaku?" Ita dama ba isasshiyar lfy ba dan ta kusa sati tana fama da zazzabin dare da amai, nandanan numfashinta ya fara daukewa, hankalinsa fa ya tashi yayi qasa da ita yana jijjigata yana Kiran sunanta.

Itama Hajiya tsuru tayi gabanta yana faduwa don batasan asalin rigimar ba taka haye tayi shikuwa Alh kafe Muneef  da ido, miqewa Lameer yayi gashin jikinsa duk sun miqe saboda tashin hankali idonsa ya kada yayi jajir ya kalli Muneef da Hajiya ya girgiza kai ya dauki matarsa ya fice da sauri.





Asibiti yakaita suka fara bata kulawa sannan suka binciketa gwajin farko sakamako ya fito tana dauke da ciki na sati bakwai, farin ciki kamar anyi masa albishir da Aljannah nandanan ya nemi damuwarsa ya rasa abinda ya dade yana addu'ar zuwansa yazo ji yakeyi kamar baa taba samun ciki a gdansa ba.

Sai Tara na dare ta farfado Koda ta farfado da kukan ta tashi tanajan zuciya ya matsa da sauri yace “don Allah ki fadamin menene Babe wlh kinsayani cikin damuwa me Muneef yayi miki?" Kukanta ta qarawa qarfi tace “nidai kawai ka mayar dani gurin iyayena na gaji Babe nagaji da zama da zuri'ar da basa qaunata meye laifina meye aibina da mahaifiyarka bata sona laifin me nayi Mata?"...........……….







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/12, 6:31 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*


*43*


Duk yanda yaso tayi masa bayani taqi sai kuka kawai da takeyi da yayi Mata mgn hakanan ya qyaleta suka koma gda yaci gaba da tattalin ta duk wani motsinsa akan idonta baya sakaci da duk wani abu daya shafeta qauna yakewa cikin na musamman.

A wannan tsakanin ne tafiya ta taso masa zuwa Germany lkcn tana tsakiyar laulayi yaso tafiya da ita amma tayi fur tace ita bazataba ya mayar da ita kano, dolensa badon yasoba ya kawota Kano kwana biyun da yayi a part din Mubaraka ne itakam zaman doya da manja akeyi ita dashi tunda ta lura da samuwar cikin na Hauwah ta dauki kishin duniya ta dorawa cikin.





Ranar da ya bar dakinta ranar ya tafi amma saida ya nemowa Hauwah wata dattijuwa da zatake kula da ita saboda tsaro, farin ciki gurin Muneef kam baa cewa komai kura ta mutu ya huta gda ya dawo nashi.

A ranar itama Mubaraka bata kwana a gdanba gdan wani Alhnta ta kwana ta zubewa Nanny din yaran su a cewarta bikin qawarta akeyi, itadai Hauwah tana samanta tana fama da kanta bata sanin wainar da ake toyawa sosai.




A hankali ta fara fahimtar wani abu wata rana ta sauko daga saman wajen biyar na safe daga ita sai  rigar bacci tunda ta fito ya kafeta da ido tare da qara lafewa a kujerar da yake kwance, itakam batama lura dashi ba ta wucce ta shiga kitchen din da niyyar dauko fresh milk saboda tashin da tayi taji cikinta kamar anyi mata yasa.

Kitchen din ta shiga hakan ya bashi damar miqewa zumbur yabi bayanta batayi aune ba kawai saijin mutum tayi a bayanta ya dora hannunsa a saman weast dinta, zabura tayi tayi baya tare da qwallah qara yayi saurin rufe mata baki ta hannunsa tare da murdawa qofar key.





Jikinta tsuma yakeyi tanaja da baya da sauri shikuma yana binta har takai qarshen kitchen din, yana wani murmushi yana lasar lebe ta wawuro wata shafceciyar wuqa tayi kansa yaja baya da sauri hakan ya bata damar murda mukullin ta bude qofar ta fita da gudu har suna karo da Ladi me rainon yaran gdan riqeta tayi da sauri tace.

“Hajiya meye hakan?" A firgice ta qwace ta nufi saman a guje tana rusa kuka ta fada dakinta ta datse da mukulli jikinta na rawa tana kuka hatta abinda ke cikinta hautsinawa yakeyi haqoranta sai haduwa sukeyi.





 Ta dauki wayarta cikin kukan tashin hankali ta latsa number Lameer Ring daya cikin saa ta shiga ya daga da sauri yace “jiya kinyi bacci da wuri maman twins banji muryarki ba..." Kukanta ne ya katse masa maganar yace.

“Meye kuma ya faru yanzu" cikin kuka tace “karo na uku kenan yanayimin haka Lameer nagaji da wannan akuyancin na qanin ka tunda ka tafi Laraba tacemin a gidannan yake kwana ban yarda ba ban gasqatata ba sai yau Lameer me yake nufi danine meye yakesa kullum burinsa ya ketamin haddi"






Tunda ta fara mgnr ya miqe tsaye yana auna kalamanta da kalaman Sabon maigadin daya canza da yace masa Alh kullum sai qaninka yazo gdannan nayi yunqurin hanashi Hajiya babba tace karatu yake koya mata"

Gabansa ne ya fadi sosai yace “me...me yayi miki?" Nan ta kwashe komai ta fada masa yace “ok ki shirya kayanki yau zansa azo a daukoki zuwa Lagos ku tafi da Laraba very soon zan dawo idan na dawo zansan abinyi"





Kashe wayar yayi ya Kira ta Hajiyansa cikin tashin hankali yace “Hajiya Ina dan iskan yaron nan yake kwana" katseshi tayi da cewa “wlh bansani ba wani lkcn idan abin nasa ya juyo sai ya daina kwanan gida kwata²"

Kashe wayar yayi ya kira wayar Mubaraka lkcn suna manne da juna yana bata labarin rashin sa'arsa na cimma buqatarsa gurin Hauwah da sauri ta daga tace “sai yau ka tuna damu?" Bai tsaya sauraron qorafinta ba yace “meye ya tasheki da wuri?" Tsaki tayi tace “nifa natsani tuhuma kaji na fada maka" bai kuma cewa komai ba ya kashe wayarsa.






Duban Muneef tayi tace “ina tsoron wannan bagidajiyar yarinyar ta ballo mana ruwa fah" dariya yayi yace “habadai ita mahaukaciyar inace da zata fada masa" share mgnr sukayi sukaci gaba da sharholiyarsu inda ita kuma ta fara hada kayanta wani yaronsa yazo ya daukesu daga gdan ba tare da kowa ya sani ba.

Shikuma cikin sirri ya turo aka maqala masa C.C camera da takeyi masa record na komai batare dasun sani ba, saida aka dauki sati guda sannan Mubaraka ta kirasa lkcn taje gdan Hajiya suke qyanqyasa masa wai wani mutum yazo har gida ya dauki Hauwah har Hajiya tana fadin ai dama tasan zaayi haka duk macece zata iya hqrn da Mubaraka takeyi dashi.






Shidai bai nuna shine yasa akazo aka dauketa ba hasalima cewa yayi zaisa a nemeta, su Mubaraka duniya ta samu shima maigadin kudi take basa batasan leqen asirinta yakeyi ba yana ganin takunta tayi wanka ta qyafe wani Alh birni yazo ya dauketa.

Da dare kuma Muneef yazo susha shagalinsu, yau tun safe ta shirya zuwa gidan Hajiya abokin shedancinta babu lfy tana zuwa suka gaisa da Hajiyan ta miqe tace bari taje ta duboshi, Hajiya bata dauki komai ba tabita da kallo ta bude qofar ta shiga ta mayar ta rufe yana kwance ya bude idonsa ganin itace yasasa bude mata hannu ta shige jikinsa tana kissing dinsa tace “inata missing dinka jiya nasha magunguna na tsumu najika shiru Saida mukayi waya da Hajiya take cemin bakada lfy"





Shima shigewa yayi jikinta yana lasar lips dinta yana tura hannunsa cikin rigarta yace “nima nayi kewarki yanzu sai muyi qara'in rayuwa" zaro ido tayi tace “hajiya fah" kanne mata ido yayi yace “manta da ita" daga haka suka soma fajircinsu sunma manta da a Ina suke, ita kuwa Hajiya tananan zaune taji Shiru tayi yawa sai tayi kamar ta miqe saidai ta share candai taga abin yayi yawa kuma ta tuna da wani gani da tayi musu suna kissing din juna, ai saita zabura ta miqe tana fadin Mubaraka yamma fah tayi kizo ki tafi gdan....."

Maganarce ta maqale saboda abinda idanunta ya gane Mata taja baya da sauri tare da kurma ihu tana fadin “innanillahi wa innah ilaihirraji'un me zangani ni jikar me sabulu Muneef Mubaraka lahaula wala quwwata illah billahil aliyul'azeem matar yayanka yau nayi baqin gani ni maryamu meye ya kawoni ne....." 







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/13, 9:46 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*


*44*




Zunbur suka daga junansu kowa yana neman abinda zai sitirta jikinsa kafin su gama kimtsawa Hajiya tayi waje batakai ga zama ba jiri ya debeta ta fadi qasa tim daidai lkcn da Alh yake shigowa gidan ya qarasa da hanzarinsa ya dagota yana jijjigata.

Fitowar muneef da mubaraka yasa Alh binsu da kallo kowa sai rawar jiki yakeyi na alamun rashin gaskiya shidai bai tsaya sauraronsu ba ya dauki Hajiya ya fita da ita zuwa ga likita, aka shiga dubata.





Kwanan Hajiya uku batasan waye ke akanta ba a rana ta hudu ce ta samu kanta Koda ta farfado taga muneef a kanta kuka ta kamayi tana girgiza masa kai tana nuna masa hanyar waje tun daga wannan rana bata yarda yazo inda take balle mubaraka wadda da tazoma hanata shigowa tayi.

Takasa fadawa kowa abinda ya faru sai aikin kuka da nadamar abubuwa da yawa.





Sati daya da faruwar lamarin Lameer ya diro 9ja Lagos ya sauka gurin gimbiyarsa zuciyarsa wasai, itama tayi murnar ganinsa sosai ta rasa Ina zata ajeshi don murna, ya sunkuceta yana dariya ya shige da ita bedroom nasu ya kwantar da ita a gado yace “nayi missing kyakkyawar kulawar matata nayi missing farin cikina"

Rungumeshi tayi tace “nafika kewa babe kullum sai nayita juyi ina rungume pillow" 





Dariya yayi ya dora lips dinsa a nata yana tsotsar da salonsa me narkar da ita yana shafa cikinta a hankali yana sauke numfashi ya janye bakinsa ya daga rigarta ya zubawa cikinta ido da ya shiga wata na hudu yace.

“Yaushe babyna zai fito ne babe?" Dariya tayi masa tace “soon on sweet amma ni duk kabi ka dameni da babynka babynka naga kanada wasu babyn..." 

Hannunsa ya dora a bakinta yace “su daban shima daban jinsa nakeyi a tsakiyar ruhina" daga haka bai qara cewa da ita komai ba ya fara kewayeta da wani salonsa mai tsayawa a rai tun tana zuqewa har ta sakar masa jiki sukaji dadinsu ta hanyar tsotse tsotsensu.





Lkcn da sukaje qarshen ta tsorata matuqa da yanda taga daga farawarsa ko minti daya bai cika ba yayi release amma bata nuna masa ba saima kwanciya da tayi luf a jikinsa tana wasa da gashin qirjinsa shima yana shafa sumarta yace.

“Yaushe zan zama namiji ne nima Hauwah?" Kallonsa tayi da rashin fahimta tace “dama ai kai namiji ne" shafa kanta yayi yace “namijin gaske shine wanda sai buqatar matarsa ta biya sannan tasa take biya, babe inada tabbacin tunda muke dake idan kika dauke dararenmu na farko banta biya miki buqata ba saboda kinada nisan zango ruwanki baa kusa yakeba" 





Kunya ce ta lullubeta ta sake shigewa jikinsa tace “ni a hakanma kayimin inasonka a duk yanda kake kuma zan rayu dakai a haka koda ace kwata² baka motsawa" sake matseta yayi a jikinsa yana sauke numfashi har zuwa wani lkc sukayi wanka suka fito ta fara hada masa abinci yana binta da kallo ta gama hada masa ta zauna dakanta ta rinqa basa a baki yanaci yana zuba mata shagwaba. 

Da suka gama suka koma parlour sukaci gaba da wasanninsu na masoya har zuwa wani lkc ya dauketa cak ya shigar da ita dakinsa ya dauko wata qatuwar akwati ya bude.





Zaro ido tayi tare da kallonsa ya kashe mata ido tace “kayan babe sweet Ina zamu kaisu ai sunyi yawa" kallonta yayi yace “waye ya fada miki kaya suna yiwa yaro yawa?" Qasa tayi da kanta ya taso ya zagaya bayanta ya dora mata wata sarka ya zare barimar kunnenta yasa Mata dankunnen sarkar yasa mata zobba agogo da banguls dinsu.

Zaro ido tayi tace “wannan fah sweet?" Ajiyar zuciya yayi yace “nayi niyyar hado miki lefenki da banyi miki lkcn aurenmu ba sai kuma naga bakida buqatarsu suturu sunyi miki yawa shiyasa na hada na tattara da tukuicin kyautar budurcinki da kikayimin da kudin kayan lefenki na siyo miki wadannan"





Rungumeshi tayi tana dariya wasu hawaye suka zubo Mata tace “kana shagwabani da yawa babe ni ba bashine tsakanina dakai ba saboda bakayimin lefe ba shine zaka siyomin wannan sarqar Koda bansan kudinta ba nasan zatayi tsada fa" 

Kallon dan qaramin bakinta yakeyi yace “kinfi qarfin komai a gurina ki shirya da shirinki zamu koma Abuja da zama" gdy tayi masa sosai sannan suka kwanta.

Washegari ma yini sukayi suna soyewarsu ko qofar gida bai fita ba Saida yayi kwana uku sannan ya shirya musu tafiya Kano shima kiransa akayi aka sanar dashi jikin Hajiya ya matsa.





Basu bar Lagos ba sai shida na yamma kuma bai sanar da kowa zuwansa ba lkcn da suka sauka a airport ma Salees ya Kira yazo ya daukesu zuwa gidan nasa har suka shiga suka ajiye kayansu sukayi komai Mubaraka batasan sun dawo ba.

Tanacan ita da Muneef suna harqallarsu saida ya shigarwa da Hauwah kayan ta bangarenta sannan ya sauko ya nufi part din Mubaraka ya shiga dakinsa domin daukan key din store ya tarar da dakin kaca kaca gadon kamar an shekara baa gyaraba.





Wata takaici ya tokare masa maqoshi ya fita daga dakin ya nufi dakinta cikin saa a bude yake kawai tura kai yayi ya shiga dakin dudum yake babu haske sai wani nishi da wasu maganganu da suke tashi da baya iya bambamce abunda ake cewa.

Hannunsa yakai ya kunna sweech din ya sauke manyan idanunsa a kan gadon gabansa na tsananta dokawa yayi saurin ja da baya yana fuzgo numfashi yana qara goge idanunsa Mubaraka ce da Muneef da wani abokin Muneef din sunata lashe lashensu Muneef na shan gabanta abokinsa na shan nononta ita kuma tanata murza Dick's dinsu.






Fita yayi da sauri yana hada hanya saboda tashin hankali yaja qofar ya rufe tare da zare mukullin ya sauka qasan ya zube a tsakiyar parlourn jikinsa na rawa zuciyarsa na tafasa wata zuciyar tana cewa ya harbesu gaba daya wata kuma tana hanashi.

Haka ya wanzu a gurin sama da awa biyu ya rasa abinyi sai can dabara ta fado masa ya dauki wayarsa ya kira jami'an tsaro ya sanar dasu abinda yake faruwa, take cikin yan mintuna suka iso yayi musu jagora suka haura saman ya bude musu dakin suka shiga har yanzu basu daina cinye junansu ba abokin Muneef ne a samanta yanata antaya mata bura, wani cikin sojojin ne ya saita qafar Muneef ya sakar masa kunamar bindiga, qarar ce tasasu tarwatsewa shikuwa Muneef wani ihu ya saki tare da qanqame qafarsa, itama Hauwah qarar Halbin ne yasata sallame sallar da takeyi tunaninta yan fashine suka shigo musu...............







*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/17, 5:11 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*


*45*




Da sauri ta nufo qasan gabanta na faduwa sai kuma ta koma ta dauki wayarta ta kira layin Lameer din Kira daya ya daga yace “kada ki fito ki jirani yanzu zan shigo" cikin tashin hankalin jin yanda taji muryarsa tace masa “amma basuyi maka komai ba ko?"

Numfashi ya furzar cikin bala'i yace “nace miki ganinan ko aa..." Qit ya kashe wayarsa ta koma ta zauna gabanta na faduwa har zuwa wani lkc sannan ya shigo dakin a fusace ya dubeta da wani irin kallo daya fadar Mata da gaba ya juya ya fice a fusace.





Gabadaya lamarin ya firgitata hakan yasata komawa ta kwanta a kasalance ta fara qoqarin tursasa kanta tayi bacci Amma ta kasa dole ta tashi ta sake komawa saman sallaya ta dauki qur'ani ta fara karantawa cikin alamun gajiya tanayi tana hamma saboda sabon abune a gurinta takai qarfe daya na dare batayi bacci ba.

Koda baccin ya kamata anan ta bingire ta fara baccin bataji shigowarsa ba sai asuba ta farka taganta nannade a jikinsa ta janye a hankali ta miqe ta shiga bathroom ta dauro alwala tayi raka'atainul fajri ta zauna tana lazumi kafin daga baya ta tashi ta tasheshi shima yayi miqa tare da kamota jikinsa.





Janyewa tayi tace “lkcn sallah yayi Kaine kake min fadan makara gashi yau kaima ka makara" miqewa yayi ya shiga bathroom yayi wanka ya dauro alwala ya fito ya nufi masallaci, itama sallar tayi ta sake komawa ta kwanta.

Sai tara ta tashi Laraba me aikinta ta gama mata komai ta fito cikin kwalliyarta mara hayaniya ta zauna a dinning din ta fara break Laraba ce tazo ta zauna tace “Hajiya jiya kina bacci akayi wani abun kunya a gidannan" 

Kallonta tayi da rashin fahimta tace “kamarya?" Karkacewa tayi ta fara bata lbr tun daga farkon abinda ya faru har qarshe.




Ta tabe baki tare da cewa "Allah ya kyauta” cigaba tayi da harkokinta tunda ita abun ba sabo bane itama ta taba kamasu a parlourn qasan kawai dai bata bawa abun muhimmanci bane a lkcn shiyasa bata taba fadawa kowa ba.

Tana gama cin abincinta ta shige dakinta ta dauki wayarta taci gaba da harkokinta da Zulaiha suke chat dinsu tanata bata sirrika, bai shigo gdanba sai dare sosai ya shiga dakinta ya tarar da ita tana baccinta cikin kwanciyar hankali ya rabata ya kwanta ya fara hura mata iska a kunnenta ta dora hannunta a saman kunnen ya ciza a hankali tayi murmushi.





Shima murmushin yayi ya kwanta yace “meye hukuncin matar da tanajin shigowar mijinta ta shareshi ko sannu da zuwa batayi masa ba?" 

Birkitowa tayi ta zuba masa ido itama tace “shima mijin da yaje yayi dare a waje meye hukuncinsa" dariya sukayi a tare yace.

“Inacan zuciyata cike da kewarki naje Rugar Sambajo Goggo da Inna suna gaisheki" miqewa tayi da sauri tace “don Allah da gaske kakeyi Babe Ina Baffana shikuma baya gaisheni?"

Lakace Mata hanci yayi yace “banma gansa ba ance ya kada shanu ya tafi jaji" komawa tayi ta kwanta tace “nasan shi har yanzu bai hucce ba yanada masifar ruqo a ransa sannan...."





Rufe Mata baki yayi yace “karki wani damu ki barni zanji da komai nidai fatana ki haifamin yarona lfy" bata kuma cewa komai ba ta kwanta ya shige jikinta yana yamutsa mata lissafi tabbas yau da bambamci da kullum.

Lameer ya bata kashi taji a jikinta yaji dadin da tunda yake a duniya baitabajin irinsa ba, ya samu nutsuwar da baisan akwai irinta a duniyar bani adamu ba, Hauwah kasa motsawa tayi saboda mamakin yanayin daren nasu na yau.

A cikin shekaru biyun tasu da rabi da sukayi matsayin ma'aurata bata tabajin ta kwanta da namiji ba sai yau bata taba sanin dadin shigar namiji jikin mace ba sai yau da kanta ta tambayi kanta dama haka akeji idan namiji ya dade yana sex da mace?





Da wannan tunanin bacci ya dauketa tana rungume a jikinsa wannan rana makara sukayi saboda sunyi abinda basu tabayi ba a ratuwarsu sex sau biyu a dare daya kuma kowanne yabada citta yanda ya kamata.

Da safe suna tashi wanka sukayi ya kalleta cikin faduwar gaba yace “zamuje ki duba Hajiya a asibiti ne?" Dagowa tayi da sauri tace “meye yake damun Hajiyan?" Numfashi ya sauke yace “kusan wata guda kenan tana asibiti nima ban sani ba sai shekaran jiya dana dawo" kwantar da kanta tayi tace “Allah sarki bansani ba wlh kuma ko Aunty Zulaiha batayimin mgnr ba"





Da wannan suka tashi suka fita yajasu a mota suka tafi gdansu suka nufa gabanta na tsananta faduwa saboda takasa mantawa da ranakun nan guda biyu ranar da Muneef ya zagayo ta bayanta ya taba Mata nono da ranar da yabita kitchen a gidan mijinta zaiyi Mata fyade.

Wadannan abubuwan sun cake Mata a qahon zuciya har tanajin tsoro da fargabar zuwa gidan gani take abinda zai faru kenan a gaba hakadai yayi parking ya juyo ya kalleta tare da Kama hannunta yayi kissing kuncinta ya sake mata murmushin qarfafa gwiwa yace “idan kina dari dari da parents house dinmu sai na rinqajin kamar baki yarda duk abinda ya shafeni ya shafeki ba my Hauwah"






Numfashi ta sauke a kasalance tace “inajin tsoron kada abinda ya faru last zuwana ya sake faruwa ne Babe" idonta ne ya ciko da qwallah yasa harshensa ya lashe yace “babu abinda zai faru sai alkhairi kinji" daga masa kai tayi suka fita yana riqe da hannunta suka shiga cikin gdan tana kwance a jikinsa ya bude qofar parlourn tayi saurin janyewa daga jikinsa ganin Alhajinsa a parlourn da sauran iyalansa gabadaya.

A kunyace ta zube a parlourn Zulaiha da da Aunty Zainab suka kalleta sukayi murmushi ita kuwa Hajiya kunya ce tasata yin qasa da kanta, Alh ne ya Kira sunanta yace “uwata" sunan da yake kiranta kenan ta dago tace “nan...naam Alh Ina kwa...na" yanda muryarta take rawa yaba Lameer dariya komai nata burgesa yakeyi musamman kunyarta.





Amsawa Alh yayi yace “uwata tafi ta kowa uwata sarkin kunya taso ki dawo kusa da danki kinji “sake qunshe kanta tayi Lameer yayi murmushi yace “yar qauye da ita" dagata yayi cak ya direta gaban Alh itadai kamar qasa ta tsage ta shige Alh ya kamo hannunta yace “Alfarma zan nema a gurinki uwata kinji?" 

Kada kanta tayi yayi murmushi yace “zamu riqe Muftahu a gurinmu tunda qaddara ta dora mana nasan idan nace Lameer ya riqe dinma zai riqeshi amma hakan ba adalci bane gara mu rabashi da ganin abinda zaike tuna masa da baqin cikin baya ya shiga sabuwar rayuwa me tsafta da iyalansa da suke dolensa"






Shiru Alh yayi inda kowa ya kasa kunne yanason jin abinda ya faru wani murmushi me ciwo Alh yayi yaci gaba da cewa “Abubuwa da dama sun faru marasa dadi wanda suka samu daurin gindin sakaliyar uwarku Lameer, nayi iyakar qoqarina akanku da tarbiyyarku alhmdllh na samu uku Mukhtar yayanka da kuma kai Lameer sai Zulaiha Zainab kuwa da Muneef dama na dade da sallama Mata su domin hudubarta sukebi ba tawaba.

Wannan dalilin sakacin da sakalcin na uwarku ya kawo mana wannan gagarumar barakar nasani tun farkon aurenka da Mubaraka baka soba amma kayiwa mahaifiyarka biyayya bisa tursasawata saboda tsayin lkcn daka dauka baka tabayi mana mgnr aure ba tabbas da nasan abinda ka dade kana fada mini kenan akan yarinyar nan da dakaina zan kashe aurenku kafin zuwan wannan ranar.






Ka aureta bazawara ka riqeta baka taba kawo mana matsalarta ba saidai ita ta kawo mana taka mun matsa maka mun takura maka a lkcn da kaso auro muradinka kazo ka sanar damu kanason zaka sauwaqe Mata saboda zuciyarka ta kasa nutsuwa da ita.

Amma muka hanaka mukace saidai ka zauna dasu a haka to yaudai qarshen tukatukin tik mun gane abinda ka dade kanaji a ranka cin amanarka da qaninka uwa daya uba daya, cin amanarka da abokin qaninka, cin amanarka da mazan kwararo, abubuwan sun munana sun qazanta har takai anyi ciki da qaninka an liqa maka wanda Allah ya sani tun ranar dana fara ganin yaron nan Muftahu har kawo yanzu da binciken likitoci ya tabbatar da Fadwah itace jininka Muftahu ba naka bane na Muneef ne idan na kalleshi gabana faduwa yakeyi saboda tsananin kamarsu ta munana.






Abisa wannan dalilin yasa na yanke shawarar baku Fadwah ku riqe a hannunku shikuma wannan zai zauna a hannunmu alhmdllh naji dadin datse igiyoyin aurenka akanta.

Bullet ya shige ta gabanta a lkcn da aka harbi abokin barnar Tata qafa zaayi Mata aiki cikin satinnan idan taji sauqi ta gama iddarka zan daura musu aure suje su qarata su riqe shegen dansu a tsakaninsu..."

Wata zabura Hajiya tayi tace “aa Alh kadama ka fara iri me kyau akeson yayi yado a cikin zuri'a wannan mummunan irin bana fatan cigaba da wanzuwarsa cikin zuri'ata don Allah ka qyaleta ta koma Jalingo akwai Amina me tallan awara ta gidan Idi dillali wlh gara ka aura masa ita da wannan baqar kadarar Alh kada kace aa yarinyar tafi wannan tarbiyya"




 


Shidai Alh baice komai ba saima miqewa da yayi yace “Lameer ka rufe taron da addu'a ka dauki iyalinka ku wucce" gdy yayi masa ya rufe musu taron da addu'a sannan suka gaisa itadai Hauwah sai quqqunshe cikinta takeyi a haukanta bataso su gane cikin jikinta amma saiji tayi Hajiya tace.

“Ashe matar taka ma takusa haihuwa?" Shafa kansa yayi yace “eh wlh nan da wata uku insha Allahu banmasan ya abin zai kasance ba idan na gama karbar magani qarshen watannan nakeson wuccewa America na samu aiki a Flight Emirate kuma inason tafiya dasu" 





Kallon Hauwah Hajiya tayi cikin kunya tace “idan ta amince sai kabarta anan idan ta haihu lfy sunyi arba'in saikazo ka tafi dasu..." Wani gumine yake karyowa Hauwah ya zuba mata ido tare dayin murmushin yaqe yace “karki damu Hajiya zan kaita gidansu ina ganin zatafi nutsuwa naga kamar ta tsorata daku"

Zulaiha ce ta matso jikin Hauwah tace “don Allah kiyi zamanki damu anan Hajiya tayi nadama kuma zata baki  kulawa sosai" 

Sakeyin qasa tayi da idonta Zainab ta matso tace “idan bazata zauna anan ba ni kabani kwangilar kula maka da ita...." Wata uwar harara daya zuba Mata tasata tsuke bakinta ya miqe yace “tashi muje duk yanda mukayi da ita zakuji" 






Dama kamar akan qaya take ta miqe ta zari Jakarta ta fice murmushin nadama Hajiya tayi dakanta akan wannan makirar yarinyar tasa surukarta ta arziqi tana gudunta.

Yana driving din yana kallonta ita kuma ta kwantar da kanta a jikin sit har sukaje wani shopping Mall suka shiga ya rinqa lodar masu kayan baby har saida ta riqe hannunsa tace “don Allah ya isa haka babe komai munadashi fa ni wani abinma bansan amfaninsa ba" zame hannunta yayi yaci gabada abinda yakeyi Saida ya gama suka fita suka nufi gda.






Daqyar ya samu ya shawo kanta ta koma gurin Hajiya lkcn da zai tafi America shima saida yace Mata ai Muneef bayanan yana England ana kula da qafarsa data fara rubewa saboda Harbin da akayi masa.

Haka watannin suka yita turawa kulawa ta musamman Hajiya ke bawa surukarta Alh ma komai ya gani uwarsa wannan dalilin yasa ta saki jikinta tana boffidonta a hannun surukanta, 

Ranar wata Laraba suna parlour Hajiya nayi Mata tsifar dogon gashinta tanata yimata surutu sunata dariya Hajiyan taji ta dauke wuta, shiru na dan lkc can kuma taga ta muskuta zata miqe Hajiya tayi saurin riqeta tace “menene Hauwah?" Qanqame qafar Hajiya tayi cikin fitar hayyaci tace “ci...cikina Hajiya wayyohh bayan...." 






Kamata tayi suka shiga daki ta sake durqushewa jikinta yana karkarwa tana kuka kafin Hajiya ta nemo Mata hijjab me afkuwa ta afku yaron ya sawo kai tayi kanta da sauri kafinma tazo ya fado gabadaya Hajiya tasa hannu ta dauko yaron ta yanke masa cibiya.

A towel ta nadeshi ta dawo ta fara gyara Hauwah kafin wani lkc ta gama gyarasu tsaf sunkucecen yaron me masifar kama da ubansa yanata wawurar hannunsa da alamun abinci yake nema.

Kiran Alh tayi ta fada masa abinda yake faruwa ya turo musu likita tazo ta dubata tayi Mata dinki saboda qaruwar da tayi ta bata magunguna sannan Hajiya ta hada Mata shayi ta fara bata tanasha a hankali tana kallon yaron hawaye na zuba a idonta so qauna da tausayin iyayenta na qara narkar da zuciyarta.






Nadamar watsin da tayi da iyayenta tana nuqurqusar zuciyarta ashe irin wahalar da Goggonta Tasha kenan ta kawota duniya amma ta zabi mijinta akanta wani kuka ya qwace mata ta kwantar da kanta a kafadar Hajiya daidai lkcn da Lameer ya kira wayarta.

Hajiya ce ta dauko ta daga ta miqa Mata ta miqe ta fice, ajiyar zuciya yayi yace “Yau Ina cikin farin cikin da bantabajin irinsa ba Hauwah nasan baby na baiyi kama dakeba dani yake kama saboda nasha wahala a daren da zan bakishi alhmdllh alhmdllh alhmdllh Hauwah don Allah ki shafamin kansa kiyimin kissing lips dinsa kafin nazo insha Allahu jibi zan taho" shassheqar kukanta yasashi yin shiru da kalamansa yace “meye kikeyiwa kuka?" Cikin shassheqa tace “yau... Yaushe zaka kaini gurin Goggona?"  Dariya yayi sosai yace “sai yanzu kika tuna da ita da kikaji abinda akeji ko?".............






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/18, 8:50 AM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*


*46*




Zuciya ta aje tace “nidai ka kaini nagansu na roqi gafararsu wlh indai haka haihuwa take abban Fadwah bazan qaraba bazan sake haihuwa ba ni wannan ya isheni don Allah kada kacemin na qara haihuwa kaji?" 

Numfashi ya sauke yace “kin tsorata da yawa babe ki kwantar da hankalinki ke bakisha wahala bama a sadaka kika samu haihuwarki" saurin katseshi tayi da cewa “au ahakan?" Dariya ta bashi sosai yace “eh mana insha Allahu Ina dawowa zan baki wani babyn kiyi maza ke haifamin dozen guda kinji" qit ta kashe wayarta saboda kalamansa kawai bata Mata zuciya suke.





Shigowa Hajiya tayi ita da Alh Alh ya dauki yaron yayi murmushi yace “masha Allahu yaro me kama da babansa Allah ya albarkaceka Muhammad Nurraddeen...." Dagowa tayi da sauri ta kalli Alh yayi murmushi yace “tun kafin Lameer ya tafi yacemin idan kin haihu nayiwa yaron huduba da sunan mahaifinki"

Sunkuyar dakai tayi wasu hawayen farin ciki suka zubo Mata ta zame qasa tana hawaye cikin rawar murya tanayi musu gdy Hajiya ta dagata tace “bamu zakiyiwa gdy ba Hauwah tsakaninki da mijinki ne kunfi kusa kuma sakayyar halacci halacci insha Allahu idan ya dawo har dani zamuje mukaiki ki daidaita da mahaifanki aure dai damu da mukaqi dama wadanda sukaso babu wanda ya iya hanashi saboda Allah ya riga yayisa"






Suna wannan mgnr Aunty Zulaiha da Aunty Zainab suka shigo suka zauna Suma anata hira dasu itadai bata cewa komai saboda ciwon da cikinta yake danyi Mata ciwo basu ankara ba saida sukaji ta fara kakarin amai sukayo kanta duka.

Sabarta Alh yayi yasata a mota Hajiya ta shiga da jaririn sai asibiti suna zuwa sukayi Mata Allurai suka bata wasu magunguna sannan suka juyo gda, sunata zuba mata sannu suna zuwa dama isha tayi aka ciro gadon baby aka sanyashi a ciki aka kwantar dashi itama ta kwanta Hajiya me jika cewa tayi saidai su kwanta a dakinta bazaayi mata nesa da jikanta ba.






Fadwah ita ke kusan yini tanawa yaron wasa wata shaquwa ta shiga tsakaninta da jaririn ba kamar Muftahu ba da basa jituwa ko kadan ita kuwa Mubaraka ta koma dangin mahaifinta Jalingo inda Alh ya shiga ya fita Muneef da Hajiya ma basu sani ba aka qullah shirin aurenta da Muneef din.

Kwanan Hauwah uku da haihuwa Lameer ya diro cike da shauqi bai bari kowa ya ganshi ba ya shige dakin da lallaba ya sanya hannu zai dauke baben data rungume take feeding nashi tayi sauri qanqame abunta tare da bude idonta, murmushi yayi Mata yace “mata sunyi da rigima ta qare ohhhh Hauwah rikicin ki yawa gareshi kuka wiwi ke banasonki naqi baki baby to yaudai ga babenki dana baki a hannunki"






Sunkuyar dakai tayi cike da kunya tana wasa da sumar yaron ta fulanin na gaske wacce ya debo gurin uwarsa amma komansa har fatarsa na ubansa ne hannu yasa ya daukeshi yayi masa addu'a sosai sannan ya rungumeshi a jikinsa yanajin ninkin qaunar yaron da uwarsa na mamayar zuciyarsa.

Kwantar dashi yayi ya zuba masa ido kawai yana kallon buwaya ta ubangiji sumar yaronce kadai ta uwarsa amma hatta farcensa irin nasane a hankali yace “Allah daya"

Kwantawa yayi a jikinta ya sanya hannunsa ya shafo nononta yace “inason taya babyna shan madara sweet abani" turo baki tayi tace “ni ka tashi ka tafi saura kadan na mutu yaseen da nasan haka haihuwa take da babu abinda zaisa nasaka kayimin ciki"






Yanda take mgnr da qumajinta ya bashi nishadi yace “kuma gwarne nakeson kiyi kafin kiyi arba'in na baki wani ko?" Tureshi tayi ya koma gefe yana dariya Hajiya ta shigo yanayin data gansu ya bata kunya sosai har zatayi mgn taji tsoron amsar da lameer zai bata don yafita wauta.

Miqewa yayi ya dauki Fadwah ya fita bai jima ba ya dawo dauke da wani babban akwati ya ajiye Mata a gabanta yace ki bude ki gani abinda baiyi miki ba ki ajiyeshi gobe saina canzo miki yanzu nidai kuyimin guri a dakinnan na kwanta bacci nakeji"





Hajiya dake fitowa daga bathroom tace “badai dakin nan ba kaje gurin maigadi ku kwana tare tunda ka manta hanyar gdanka, sosa qeyarsa yayi yace “aa ba haka bane Hajiya kawai so nakeyi mu kwanta tare Noor dinmu a tsakiya nasan baccin zaiyimin dadi sosai..." 

Daquwa tayi masa tare da jifansa da pillon hannunta tace “zaka tashi ka fice mana a daki ko saina Kira Alhajinka yazo ya fitar dakai" miqewa yayi yace “ya zanyi tunda baa qaunata" sunkuyawa yayi daidai fuskar Hauwah yayi kissing nata yace “kin samu daurin gindi lkcnki ne Allah ya kaimu lkcn da Zaki shigo hannuna saina....."






Rufe masa baki tayi da sauri da nata yayi saurin tallafo kanta ita kuma tana qoqarin kwacewa Hajiya ta juyo saida gabanta ya fadi ganin yanda yake wani lumshe ido tayi saurin dauke kanta daga kansu ta fice da baya da baya.

Da sauri Hauwah ta tureshi ya kamota yana wani sauke numfashi yace “kinsan Allah kisan yanda zakiyi dani nazama fitinanne nima kullum sai nayi wanka a Texas saboda tunaninki" qwalqwal tayi zatayi masa kuka tace “sai kayi duk yanda zakayi dani kama kasheni ka huta ai dama nasan basona kakeyi ba..." 






Rufe mata baki yayi cikin dariyarsa yace “haba yarinya nikam ai kowa ma ya shaida Ina qaunarki tun kina qwailarki lkcn da kike tsoron bindira" duka ta fara kai masa ya kauce yana dariya yace “lkcn da akeyi miki adumbuli a bayan...." Toshe kunnenta tayi tace.

“Naji naji nace kaje kawai basai kayimin barbada ba" dariya yake sosai ya lakace Mata hanci yace “saida safe amarya ta ki kulamin da kanki kinji" daga masa kai tayi ya shafa kan babynsu yace “wannan shine raba gardama nasan yanzu idan kikaje garinku zasu qara yarda da cewa kowacce qwarya da abokin burminta wlh koda ban matsa nayi amfani da qarfin hukuma an bani keba idan lkcn zuwan Noor duniya yayi sai mun hadu kuma sai yazo kota wanne hali qila da sai anyi asarar rayuka ma akanshi shi daya tak sai a rasa rai sama da goma"






Juyawa yayi ya fice tabisa da kallo cikin sanyi jiki tare da zubawa yaron ido ita ba komai yake bata mamaki ba girman yaron amma wai ita ta haifesa a cikinta ya rayu harna watanni tara yanzu gashi yana rayuwa a duniyar da take rayuwa to wai ma ta Ina cikin ya shiga, a Ina yake zama a cikin nata?

Matsa cikinta ta farayi itadai bataji wani guri da yayi alamar wannan qaton yaron ya zauna ba, kuka ya fara ta murguda baki tace “yaro inma zakayi shiru gara kayi nagaji sai tsotse nono kakeyi bandama rainin hankali na ubanka Hajiya tace a baka madara yace aa saboda ba jikinsa kake jaba to Nima bazan bayar ba aiba dankai akayimin nonon ba lol Hauwah ananan da hali.






Komawa tayi tayi kwanciyarta ta juyawa yaron baya yanata kuka yana neman abinci, Hajiyace taji kukan yayi yawa ta shigo da sauri taga yanda yaron yake neman abinci ta matsa ta daukeshi tace “ni narasa wacce irin yarinya ce ke Hauwah waike yaushe gidadanci zai barki ne yaro sai kuka yakeyi yana neman abinci amma kinajinsa"

Turo baki tayi tace “toni Hajiya zafi nakeji wlh idan yanasha kamar lkcn da babansa ya farasha harma yafi haka zafi shifa jaririn nan har cizona yakeyi shikuwa Dadynsu baya cizona"

Wani takaici Hajiya ta hadiya tace “to yanzu akira miki mijin naki ki bashi kenan ko?" Sai yanzu ta fahimci wautarta tace “am imm nifa ba haka nake nufi ba Hajiya kawai dai kice ya daina cizona dan yaseen ya qara cizona saina mareshi"






Abin dariya yabawa Hajiya yau tana ganin ikon Allah daqyar ma aka samu ta yarda tabawa babyn nono wai ita kunya takeji yana namiji bazai gane Mata nononta ba saida taga ran Alh ya baci sannan ta karba ta bashi tana kuka wai an cuceta tasan sai babe yayi mata fada🤔

Itako Hajiya dama ta zama kakarta kowanne shirme ita ake dorawa, cikin kwanaki hudun da suka rage mata tayi kyau sosai binjintar da Lameer yakeyi abin har mamaki yake bawa kowa hatta ankon suna shine yayiwa kowa hadda yan uwanta da yaje ya fada musu haihuwar sukace zasuzo suna.





Bai fada Mata ba saboda sanin haukanta hana kowa sakat zatayi musamman yanzu da take a fusace saboda ance saita rinqa bawa danta nono har cewa tayi ai an tsaneta ne don anga bata da kowa.

Ana gobe suna da kansa ya tura da mota cikin saa kuwa Baffa bayanan ya  maqarfi yakai shanu kasuwa kuma yanayin sati bai dawo ba aikuwa su Inna Jumme su lantana da babbar yayar Hauwah ladiyo da qawarta Lahira suka dungumo suna birni.

Wayyohh murna gurin Hauwah taga na gda tama manta da rakinta da takewa mutanen gidan da ance tazo parlour tayi baqi yan barka sai tace ai dinki akayi Mata tana miqewa farkewa zaiyi,

Tuni ta take ta rugo a guje ta rungume Inna Jumme tanata dariya sai kuma kuka tana dube dube ganin bata hango kowa ba tace “Inna Ina Goggo da Baffa" 






Shafa fuskarta Inna tayi tace “yaushe Ina aka tabayin haka autar wuro goggonki bata zuwa sunan danki ai Baffa kuwa baya gari yana Maqarfi" gefe tayi ta riqe qugu ta zube a qasa ta kama kuka rarrashin duniya taqi yin shiru saida aka Kira Lameer yana yan awaki ya tafi siyan abin hakika aka fada masa sarqa me rikicin gangan ta rikice fah.

Babu shiri ya basu kudin ragunan daya siya aka sanya masa a mota suka tafi Salees yanata yimasa tsiya yayi murmushi yace “bakasan yanda nakeji bane nasan tabata akayi kuma bari muje kaji yanzu idan bani dinba ko waye zaizo bazatayi shiru ba yini zatayi tana kuka"





Dariya sosai Salees yayi yace “wannan raino naka bansan yaushe zai qare ba kayi rainon yaya kayi rainon uwar yaya" shidai bai qara cewa komai ba har suka isa gdan ya qyale Salees da sauke ragunan ya shige ciki ya hangota can qarshen dakin ta hade kai da gwiwa tanata kukanta.

Matsawa yayi ya riqota tanajinsa ta sake rushewa da kuka tace “ni ka daina tabani nama daina sonka na daina kulaka kullum kai babu ruwanka da damuwata to wlh babu ruwana da danka nima Gwaggona da Baffana nakeson gani shine kace kada a tahomin dasu ko?" 

Ta fada tare da kafesa da jajayen idanunta fuskarta harta tasa abinka da farar fata yayi murmushi kawai ya sanya hanunsa ya dagata cak ya nufi dakinta da ita tana zamewa tana cewa ka sakeni banaso ni banaso kowama ya tafi banason ganinsa Gwaggona nakeson gani"






Bai direta ba saida yakaita har dakin ya sauketa a gadon ta miqe zata fice yayi saurin cafkota ya kulle qofar ya mayar da ita ya kwantar ya kwanta a jikinta yayi qasa da muryarsa yace “ke bansan yaushe zakiyi hankali ba kema fa uwace yanzu haka Zaki rinqa yimin idan natafi dake American?" 

Ajiyar zuciya tayi tace “ni bazani ba Gwaggona kawai nakeson gani" kwantar da kansa yayi a kafadarta yace “yanzu kuma shine saikin tashi hankalin kowa a gidannan kina gani su Inna ko ruwa sun kasa shs daga zuwansu kin fara nuna musu halinki wato kinaso suje suce har yanzu bakiyi wayo ba a birnin ko?" 

Shiru tayi batace masa komai ba yayi murmushi yace “banason shirmenki wannan ni dakene zan kaiki kije kiyi sati a gurin Gwaggonki kafin mu tafi amma sai kinyi hankali idan bakiyi hankali ba bazakije ba" 





Saurin qaqalo dariya tayi tace “namayi daga yau bazan qara ba" kissing dinta yayi yace “yawwa kin bawa Noor abincinsa kuwa?" Qasa tayi da kanta yayi murmushi yace “baki basa ba ko?" Daga Kai tayi yayi murmushi ya fita ya karbo yaron ya miqa mata ya saita mata kansa ta kalleshi ta kalli yaron tace “kamarku daya dashi"

Murmushi yayi yace “ba abinda na tambayeki ba kenan ki bawa dana nono nagani" noqe kafada tayi tace “kaje zan bashi ni basai ka...." Wani kallo da yake mata yasata hadiye mgnr ya sanya hannunsa ya zuge zip din rigar ya sanyawa yaron nono ya kama da sauri.






Qara tayi saboda zafin da taji, yayi murmushi yace “kokefa amma danki na cikinki ki rinqa yimasa horon yunwa" hawaye takeyi tace “ni kaje banason surutu" miqewa yayi yace “babu komai na gode" ficewa yayi yaci gaba da harkokinsa bai samu zama ba sai da gama da baqinsa sannan ya wucce gdansu yayi wanka ya kwanta.

Wayarta ya kira tana gani taqi dagawa yayi dariya itafa a dole laifi yayi mata yasata ta bawa danta nono, yananan kwance yanata tunanin wautarta da rikicinta yanata dariya har bacci ya daukeshi.

Tun asuba daya fita bai dawo gdanba gidansu ya tafi ya shiga gurin mahaifinsa suka gaisa yayi masa addu'ar Allah ya raya musu Muhammad Nuraddeen  sai lkcn su Inna sukaji ashe Ardo akayiwa takwara sukayita murna kuwa basu taba zataba.






Shagalin suna sosai akayi ranar su Inna sunga ikon Allah yanda aka rinqa girmamasu a gidan abin ya tsaya musu a rai musamman Hajiya data rasa inda zata ajiyesu  komai nasu na dabanne me jego ta shiga ta fita an kece raini anyi hotuna na uban ubansu.

Washegarin suna su Inna sukace sufa tafiya zasuyi sosai Lameer da Hajiya sukaso su bari su qara kwana biyu amma sukaqi hakanan suka hada musu goma ta arziqi Hauwah na kuka suka tafi suka barta kan cewa sai tazo kawo musu Baffa.

Sake bada mota yayi da kudi me yawa da kayan sawa atamfofi da lasina yace akaisu har gda, aikuwa yasha ruwan albarka suna tafiya a gaban Hajiya ya sunkuceta yana juyawa da ita itakam Hajiya ta gaji da ganin rashin kunyar Lameer saboda haka ta nufi cikin gda ta barsa da ita tasan indai Hauwah ce ba qarewa zasuyi qlau ba balle yanzu da take ganin yan uwanta sun tafi sun barta...............





 


*UMMUH HAIRAN CE...✍️*

[7/18, 3:50 PM] OPEN AYES MULTIMEDIA: *MATAR LAMEER*


*47*




Direta yayi ya Kama hannunta suka shiga ciki ya zaunar da ita a kujera yace “meye na damuwar nan da yan kwanaki kema zakije kiyi sati guda"murmushi tayi ta saki ranta suka fara hirarsu kafin ya tashi ya fice.

Haka kwanaki sukayita tafiya Noor yanata girmansa gwanin sha'awa kyakkyawa dashi son kowa Lameer yana bata kulawa sosai lkcn da tayi arba'in kamar zai saceta haka yakeji saboda qauna a ranar yazo wai yazo ya dauketa ita kuma Hajiya ta kafe akan bazai dauketa ba sai sunje Rugar Sambajo sun dawo, dolece kawai tasa ya hqr saboda bayason tsayawa yana jayayya da Hajiyan amma a matse yake da iyalinsa.





Kwananta biyu da arba'in ya shirya musu tafiya hardashi akayi tafiyar zuwa rugar Sambajo itadai Hauwah har sukaje bata iya gane qauyen nasu ba saboda cigaba da qauyen ya samu an zuba musu kwalta har gaban gidansu an dasa musu turakun lantarki gashi memakon taga bukkoki sai taga gidaje ginin zamani duk an zagayesu da bulo, mamaki yasata sakin baki tana kallon ikon Allah Saida taji ana qoqarin karbe mata da sannan ta dawo nutsuwarta ta juyo kadai sai taga baffanta aikuwa tayi wani ihu ta rungushi.





Dukka gurin suka kamayi Mata dariya ya tureta yace “kaji yar qaniya da bazatayi hankali ba zata karyani kinje kinci cimar birni kin zama bukekiya dake kauce ki bani guri ni takwarana nakeson gani"

Turo baki tayi tace “aidai saida aka sameni sannan aka samu takwaran badanni ba bazaa sameshi ba" sanda Ardo ya wawuro yace “aifa dama nace duk ranar da kikazomin nan saina rade miki qafafu" nan fa suka fara zagaye gurin har Allah ya bata saa ta dafe bayan Lameer Baffa yace “ai shima me laifine ya sacemin autata ya tafi da ita birni ta manta damu lamuni daya zanyi muku da kukayimin takwara"






Sauke Hauwah yayi sunata dariya wasan dake tsakanin Hauwah da mahaifinta yafi komai birgesu Hajiya suna shiga dakin Gwaggonta tayi tsalle ta fada gadon Gwaggo tana dariya tace “shekara biyu da rabi ban hau gadon nan ba tun Ina yar qwailata yau gani hard...." 

Gwabe Mata baki Gwaggo tayi tace “bantaba ganin mara kunyar yarinya irinki ba a gaban mijinki da surukarki zakice danki ko?" Rufe idonta tayi tana dariya Hajiya tace.

“Ai rainon Lameer ce abinda yafi hakama zatayi nikam na sabada da rashin kunyarsu kune dai zakusha fama"





Kunyace ta lullube Lameer ya kalli hauwa da taketa lalube lalubenta tayi masa gwalo yace “ni kikewa gwalo ko?" Dagowa tayi tace “lahhhh Allah sarki ni baiwar Allah ni ko kallonsa ma banyi ba kiji wai Hajiya nice nakeyi masa gwalo"

Inna ce tace “hajiya kina kallon tabara" murmushi tayi tace ai sababbune wadannan yayanma nakeji" 

Haka suka yini yana manne da ita shammatarsa Hajiya yayi yajata yace “zo ki rakani gdan gonata mugani nakwana biyu banje ba" da haka suka fice yaja motar sukabar qofar gdan dama Noor yana gurin Ardo suna zuwa ya shiga dasu yayi parking suka rinqa zagayawa.





Tanata santin gurin yayi murmushi yace “nakine wannan halak malak" juyowa tayi a sukwane tace “ni kuma Abban Noor?" Daga Mata kai yayi yace tukuicin kyautar da da kikayimin kenan, inasonki Hauwah ji nakeyi kamar bazan iya rayuwa babuke ba" 

Wasu hawayene masu zafi suka zubo Mata ta rungumeshi tana kuka tace “bansan dame zan saka maka ba Abban Noor bansan me zanyi maka ya zama tukuicin halaccinka gareni ba wanne irinso kakeyimin da baya baka damar ganin laifina?"






Dagata yayi cak ya nufi wata qofa da ita ya bude ya shiga dakine babba a gyare tsaf katifar ya dauketa ya janye mayafinta ya kwantar da ita yasa hannu zai zuge mata zip ta riqeshi ya dago idanunsa da suka kada sukayi jajir ya kada Mata kai.

Hawayene ya zubo Mata yace “ba zanyi miki komai ba Amma idan kin bani hadin kai" bazata iyayi masa musu ba tabbas sunyi qoqari daga ita har shi watansu na hudu kenan wani abu bai shiga tsakaninsu ba sosai suka tsotsi albarkar jikin junansu.

Koda Lameer yakai qarshe yaso shigarta Amma taqi ta ma sanya masa kuka iyakar rarrashinsa taqi yimasa Shiru dolensa yayi yan dabaru ya samu yayi release ya miqe ya shiga yayi wanka ya fito yace.





“Ai saiki tashi kije kiyi wanka mu tafi" turo baki tayi tace “ni bazanyi wanka anan ba kawai mu tafi" bai kulata ba ya dauki key dinsa yayi waje itama ta miqe ta mayar da kayanta suka fita yaja motar suka tafi bata taba bata masa raiba irin yau.

Qiri² yaga samu yaga rashi data barshi da yasamu nutsuwa amma yanzu banda sha'awa babu abinda ta qara masa murmushi yayi na qeta ya kalleta yace “jibi zaki dawo ko?" Wani kallo tayi masa yayi murmushi yace “bazaki wucce hakan ba idan kuma kikayimin wata mgn wlh ranki baci zaiyi kuma a yau sai mun koma dake" 





Mirgina kai kawai tayi ta rinqa hadiye kukanta suna zuwa ta bude motar ta fice ya tabe baki shima ya fita gurin su Baffa ya tsaya suka qara gaisawa sosai Baffa yakejin kunyar Lameer saboda irin abubuwan da yakeyi musu bazasu qirguba shine ya shige gaba wajen kawo musu titin kwalta da wutar lantarki qauyen nasu shine ya gine musu qauyen yayi musu gidaje na zamani musamman gidan baffan sannan duk watan duniya saiya kawo musu kayan abinci da kudin cefane tun baffa baya karba har ya fara karba.

Yanzu gashi yayi masa takwara kuma fada tsakanin manoma da makiyaya ya qare ya shiga ya fita ya sasanta dangin mahaifinsa gidan sarkin Alqalawa da gdan Moddibo Durange kakan Hauwah har an fara hada surukuta bayan tashi da Ardo.





Har bakin mota Hauwah ta rako Hajiya tace Mata “saimun taho Hajiya agaida Alhaji har ta juya zata tafi ya cafkota bai wani damu da yawan mutanen dake gurin ba ya hadeta da jikinsa ya dago kanta ya dora bakinsa saman nata ya sauke Mata wani hot kiss.

Numfashi yaja da qarfi da saida kowa yajishi ya saketa cikin sarqewar murya yace “ki shirya da wuri zanzo na daukeki" itadai kunya bata bata damar bashi amsa ba ya zaro kudi masu yawa ya tura Mata a hannunta yayi mata bye bye ya wucce ya shige yaja motar suka tafi Hajiya na daga Mata hannu.





Cikin kwanaki biyun Hauwah tayi zagayen danginta wayyohhhh hauwa taga gata saboda mijinta ya siye rugarsu da danginta ya gama musu komai burinsu na shekara da shekaru ruwa hanya wutar lantarki duk sanadin aurensa da Jiddoh sun samu.

Aikuwa daga masu yiwa Baffaji wato Noor kyautar akuya tunkiya rago kai harda masu yimasa kyautar shanuwa abin gwanin birgewa.

Itadai badon taso ba suka gama kwanakinsu a Rugar Sambajo ranar da kwana biyun ta cika kuwa 4 na yamma sai gashi anan yake fada musu aikinsa ya mayar dashi America saboda haka zai tafi da Hauwah.






Shidai Baffa babu bakin mgn saboda yanzu qaunar Lameer yakeyi kamar shine dan nasa saida ta gama shirinta tana kuka take fada musu kyautar gdan gonar da yayi mata nanfa suka rinqa godiya Baffa harda hawayensa.

Kyauta taban mamaki jiddah tayiwa Mahaifinta kudade ba qananu ba Gwaggonta kuwa kyautar wata qaramar sarqarta da dankunne tayi mata qaramin kudinsu 1.5 Gwaggo tace siyarwa zatayi tasai shanu.

Itama Inna ta kwashi ganima itama tayi Mata kyauta taban mamaki yan uwanta ma haka tabisu da dubu biyar biyar da atamfofi maza kuma dubu goma da shaddodi masu tsadar gaske.





Lameer ya dauke matarsa suka tafi tunda suka taho ake take kuka yariga yasan laifinsa ne shiyasa bai wani damu da bata hqr ba har suka shiga Kano kalma daya bata shiga tsakaninsu ba, ba asalin gdansu ya nufaba wata unguwarce taga ya nufi wani katafaren gida yayi horn aka bude masa yasa kan motar yayi parking ya bude mata kamar bazata fitoba saida ya daka mata tsawa sannan ta fito.

Bude Mata qofa yayi ta shiga ya mayar ya rufe ya qwallawa Laraba Kira ta fito yace “kiyiwa Noor wanka ki kula dashi kafin mu sauko" karbarshi tayi a hannunsa ta shiga bangarenta shikuma ya sunkuci hajiyar tasa yayi sama da ita, kayan jikinsa ya rage ya kalleta fuskarsa babu rahma yace “ki cire kayanki nicked nakeson ganinki" 





Zaro ido tayi idanunta suka fada cikin nasa yace “ko bazakiyi ba?" Saurin zare mayafinta tayi tana kuka tana karkarwar haqori ta zuge zip din rigar ta fadi ya zagayo bayanta ya rungumeta ya zare Mata under siket din ya balle Mata bra din ta rintse idonta ya sanya hanunsa ya kama boobs dinta tare da sauke ajiyar zuciya.

Yace “na azabtu da yawa Babe bansan haka akeji ba sai yanzu bantaba shiga damuwa da tashin hankali irin Wanda na shigaba a tsakanin wata biyu zuwa yau kullum sex nakeso ashe gskyr Salees da yake cemin nayi hqr na daina kuka babu ciwon da basa da magani saidai idan baa daceba, baffanki shine ya bani maganin matsalata wani zuwa da nayi muna hira da Hamma Lawal ashe yanajina shine ya shiga ya fita ya karbomin magani gashi yanzu nima na zama cikakken namiji zan moreki son Raina"





Yana fadin haka ya sanya Mata dick dinsa a bayanta yana goga mata ruwan maziy dinsa dake fita yana sauke numfashi, a haka ya saukar Mata da kasala ya zagayo ya sanya bakinsa ya kama nipples dinta ya fara sha ta qanqameshi ta saki ajiyar zuciya ya turata gadon suka fada,  ya rinqa kewayeta da salonsa har yakai ga cimma gaci ya ratsata daqyar tana kuka tana qanqameshi ya dago ya zuba Mata ido yana pompim dinta.

Ya dauki kusan 1 hour da romance da sex sannan ya samu yayi release ya rungumeta ita kuma saboda rashin sabo sosai taji a jikinta.

Hqr ya rinqa bata hardai ya samu tayi shiru sukayi wanka sukayi sallar magrib da Isha ta koma ta kwanta zazzabi yana neman rufeta ya fita na nemo mata abinci ya dawo ya lallabata taci yabata fresh milk din da suka taho dashi Tasha tayi brush ya karbo Mata Noor suka kwanta tasa masa nono yaron da dan banzan wayo sai qare mata kallo yakeyi.






A wannan dare Hauwah taga ruwan jaraba gurin Lameer ya hanata sakat kuma ci yake Mata slow motion me fitar da hayyaci itakam har saida tace dama be samu maganin ba suyita zamansu a yanda suke.

Shikuwa wani mahaukacin dadi yakeji Hajiya ba qaramin gyara tayiwa surukar tataba sannan take a kwana biyun nan baffa da yasan tsiyar daya qullah ya sanya Inna ta rinqa tsumata ruwanta tsumi ruwan tsarkinta tsumi da dare kuma a bata wani baqin hadi da aka kwaba da man shanu ace ta tura a gabanta haka take turashi daqyar.

Ashe wani hadine nasu na fulani na mallaka sadidan aikuwa Lameer ya zama nama sai yanda sukayi dashi tunda kwadayi yakaishi ya shiga wannan guri.





Kwana bakwai suka qara ya debesu ita da Fadwah da Noor suka daga zuwa Texas, bayan tafiyarsu da sati biyu wani mummunan al'amari ya faru lfyr Allah muneef ya dawo sun fita sharholiyarsu shida abokansa yaje yasha wata qwaya ya fada ruwa suka tafi suka barshi baasan dashi ba sai bayan kwana biyu da sukaji shiru din tayi yawa.

Sosai mutuwar ta taba Hauwah shikuwa Lameer kamar ma abin bai dameshi ba saboda shi dama ya dade da cireshi a ransa cewama yayi mugun iri aka rage, ita kuwa Mubaraka tanacan data koma Jalingo ta fara iskancinta abin yaqi saboda bullet yayi Mata illah sosai ta dawo ta zauna tana jinya.






Dole badon Allah ba ta koma ga ubangiji ta kama addu'a har Allah ya fito Mata da wani dattijo ta aura kusan saan babanta ne sauqinta ma daya baya haihuwa sai kishi na hauka da matansa sukeyi gashi jarabbe duk da yasan matsalarta yaqi daga Mata qafa wasa wasa har saida aka kumayi Mata aiki likita yace ya rinqa daga Mata qafa.

Sannan ne ta samu sauqi amma fah tanashan jifa gurin kishiyoyinta ga gori cewa sukeyi garin neman maza haqqin mijinta yasa ta nakasa harsashi a gindi, idan sukayi Mata wannan gorin har kuka takeyi gashi shekara biyar babu haihuwa garama Muftahu tana ganin hotonsa ita kuwa Fadwah tama manta kalarta Lameer ya dauke yarsa sun tsallake boorder.





Cikin shekaru biyar din Hauwah ta goge ta zama babbar mace yaransu uku Noor Ma'eesha Mufeed sai babbarsu Fadwah yaranta kyawawa sosai sun saje da yayan turawa idan suna turanci kamar wadanda suka hadiyi dictionary idan suka juya larabci ma baa cewa komai ga uwa uba fullanci shi dama wannan kamar yaren ubansu kasancewar shima Lameer ya iya sosai ko 9ja sukazo basa hausa sosai sai kakanninta sunyi da gaske shikuwa Mufeed da yaji sun fara hausa zaisa kuka yace zaginsa sukeyi dan sunga be iyaba.

Wannan zuwan basuyi niyyar dadewa ba saboda exams din da Hauwah zasu fara kasancewar tana deegre dinta a can American, ana gobe zasu tafi da yamma sunata tserensu sukaji ana taba belt din parlourn lameer yayi dariya yace “fadwah bude zakuyi bayani Momynku ta wucceni shine kukemin dariya ko?...." 





Mgnar ce ta maqale saboda ganin me shigowar yayi saurin miqewa ita kuma ta zube ta rushe da kuka tace “kullum cikin kuka nake Ina fadawa Allah ya nunamin ranar da zanzo na gurfana gabanka na nemi qafararka" 

Hauwah ce ta fito daga kitchen ta saki tire din tare da cewa wace wannan Babe" matsowa tayi ta kama qafarta tace “dama an fadamin hqr ya baki babban matsayi a gdanki sai kinso mijinki yakeyin komai Hauwah kiyimin alfarma daya ta qarshe a rayuwata ki roqamin mijinki ya yafemin ko haqqinsa zai barni haka kishiyoyi sun sani a gaba da gori na rasa Ina zansa rayuwata"

Numfashi Hauwah ta sauke ta dagota tace “wlh ya dade da yafe miki Mmn Fadwah dama wannan zuwan nakeson na lallabashi mu kawo miki ita kiganta" juyawa tayi ta yafito Fadwah tace “fadwah Ina qannenki" tabe baki tayi tace “tunda mahaukaciyarnan ta shigo sukabi dady sama kinjisu canma ball sukeyi nima bari naje" 






Kamota tayi tace “kada na qaraji tsugguna ki gaisheta ki bata hqr mahaifiyarki ce" zaro ido yarinyar tayi tayi saurin daga Mata hannu tace “kiyi abinda nace kadai" sunkuyawa tayi ta gaisheta ta kamota ta rungumeta daidai lkcn da Lameer da yaransa biyu suka sauko ya tsugunna ya janye Fadwah yace “kada ki damu mubaraka kije kinci albarkaceka Hauwah da Fadwah na yafe miki amma ki kiyayi yata kima qaddara baki taba haihuwarta ba baa canzawa tuwo suna to Amma idan yayi ruwa saidai a kirashi talge sabida haka ni na canzawa Fadwah uwa wacce ko a lahira inada tabbacin bazanji kunya ba"

Ba itaba hatta Hauwah saida kalamansa suka sanyata hawaye ya dauke Mufeed ya kama hannun Noor zasu fita Hauwah tayi saurin tarar gabansa tace “don Allah kayi hqr kayi Mata wani Abu" kaucewa yayi yace “kiyi Mata transfer ta 2 millions ta account dinki sai ki dauki wayata ki mayar da abinki"






Tasan ba sake sauraronta zaiyi ba saboda haka itama bata sake cewa komai ba ta shiga kitchen ta dauko Mata abinci ta dawo ta dauki wayarta ta tambayeta account ta bata ta sanya Mata 3 millions ta haura sama ta hado mata akwati guda ta kayanta ta bata gdy rasa irin wacce zatayi tayi mubaraka sai kuka abinda tafi qarfi yanzu yafi qarfinta hakanan ta tafi tanata kuka tana kallon Fadwah amma taqi zuwa inda take.

Haka komai ya wucce suka tarkata suka koma Texas rayuwa taci gaba da tafiyar musu cikin farin ciki Lameer ya zama cikakken namiji Hauwah tana ciyuwa babu daga qafa idan tayi masa mgn yace qara'in rayuwa yakeyi...............






_Tammat bih hamdullah_



_Nan wannan lbr yazo qarshe kurakuran ciki Allah ya yafe mana baki daya_




_Kamar yanda duk Wanda yaga status dina na yau ya sani cewa, littafin *DUBAI* ya koma na kudi  da sabon farashi VIP 1k  30 people's kawai nakeso single 300_



_Idan kinada interested zaki iya biyan kudinki ta wadannan hanyoyin_



_Account number_

             👇🏻

     _0255526235_

_Fauziyya Tasi'u Umar_


_GTB_


_Ko katin waya MTN ta wannan number a WhatsApp_

          👇🏻

_09013718241_


_Saiki tura avidance of payment dinki ta wannan number_

           👇🏻

_09013718241_




_Zanga adadin mutanen da suka biya kafin naci gaba da posting nashi_



_Wassalamu alaikum_






*UMMUH HAIRAN CE...✍️*



Post a Comment

0 Comments