Sanadin Boko 1 01
Posted by ANaM Dorayi on 09:25 AM, 10-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Na
Maryam Abdullah K.Mashi
Ina sauraren duk hirar da kowaccen su ke yi, motar ta
kacame da surutu. Wasu na murnar ganin Iyayensu, wasu
kuma suna zancen auren su. Mafi yawa daga ciki kuma
suna fadin makarantun da za su ci gaba, wasu su ce
poly wasu Jami'a, wasu Nursing school.
Sa'adatu da ke kusa da ni ta ce, "Hafsy don Allah kema
ki shigo (A.B.U Zariya) mu hadu mana." Nayi dan
murmushin takaici.
"Samun (A.B.U) fa ba kamar shiga Bakori ba ne, saboda
in ma zan samun bani da wani tabbas akan za a barni."
Ta zaro ido. "Kada kice min kina cikin wadanda za'a
dakile a kai gidan miji?
Na sake ajiyar zuciya.
"Ke dai Sa'a taya ni da addu'a, Allah Yasa ina da rabo,
dan kuwa ina son in ga karshen boko." Jamila ta dube ni,
"Hafsy ko yaushe kina bani mamaki in kina cewa za ki
ga karshen boko. To bari kiji, sai dai boko yaga karshen
ki. Ance miki wannan lokacin yana jira ne?
Na ce, "To Malama, ban saka bakin ki ba, ina ruwanki. Ke
ba kince aure ba?" Jamila ta ce, "Aure kuwa insha Allahu
ba ya hana karatu, zan yi aurena na ci gaba da karatuna.
Sa'a ta ce, "Wahala ai daya za ki zaba, don da kin yi ciki
za ki watsar da batun karatu. Na ce, "Dubu nawa akayi?
Ai ni boko yanzu muka sa dan ba."
Ta ce, "Shikenan, Allah Ya taimaki kowa kan niyyarshi ta
aikhairi". Na ce, "Ga magana da za ki yi kawai, Amin".
Da tafiya tayi tafiya, sai ka ji kowa shiru. Ni kam
fargabar Babana nake yi, nasan inba wani ikon Allah ba,
da wuya naje wata Makarantar.
An sauke *yan zariya, sannan mu *yan Kaduna muka
nausa hanya, motar makaranta da ke Bakori Katsina, ita
ce ta debo mu zuwa gidajenmu, bayan mun yi bankwana
da makarantar wato mun kammala.
Gidanmu ya kaure da sowa, yara na ta murna "Ga Hafsat
ga Hafsat". Innarmu ta fito da gudu ta rungume ni, ina ta
dariya. Almajiran da suka dauko min kaya suka sauke, na
ce, "Innarmu ba su hamsin". Ta kwance habar zani ta
mika musu.
Yaran gida suka taya ni da kaya zuwa cikin daki, matan
gidanmu kowa sai sannu da zuwa suke min ina amsawa.
Inna ta aje min kwano tare da cewa, "Alalar har ta
huce". Ta dire min kofin ruwa na ce, "Har yanzu bata
kare ba ne?" Ta ce, "Ta kare mana, ai tun kwanaki da
Kawunku Bako yazo ya ce min cikin kwanakin nan za ku
kammala, kullum sai na aje alalar sai dai in naga
magariba tayi ne sannan in ba yara.
Nayi dariya tare da cewa, "Innarmu kenan! Ina Yaya
Ummar?" Ta ce, "Tun safe bai dawo ba, kin san nasai
mashin da aka yi mana rabon gadon nan, Kawun ku Bako
na kawo min kudin na ce a sai mishi mashin wannan
yaran, tunda zaman banza yake, aikin gyaran wutar nan
ba ko yaushe ake samu ba. Ina fama da kannan shi ina
fama da shi.
Na ce, "Kinyi dabara Innarmu, in yayi Achabar sai a rufa
asiri". Ta ce "Kwarai kuwa. Ummi ta zo ta zauna kusa da
ni, na ce "Ummi da ba ina ta kiranki kin ki zuwa ba? Inna
ta ce, "Kullum sai ta ce Innarmu ina Auntyna?"
Na rungumota a jikina ina cewa, "Gani na dawo". Ta rufe
fuskarta, ita dole taji kunya.
Cin alalata nake ina jin dadi ga ni ga Innata, ta ce "Kin
zo a daidai bikin su Hajara da Sakina ya kusa". Na rike
baki, "Inna har da Sakina?"
Ta ce, "Eh! Na ce, "Uhm! Ni da so samu ne in ci gaba da
karatuna ma". Innarmu ta ce, "Malam ne matsala, amma
ko Nas din nan da 'ya'yan Kawunki suke yi ai zan so
kiyi." Na ce, "Wane Nurse? Ni fa Jami'a nake so, burina
in zama 'yar Media".
Ta ce, "Me kenan? Na kafa kofin ruwa na daddaka,
sannan na ajiye tare da cewa, " 'yar jarida mana! Sai dai
matsalar kudi ne". Kai lomar alala da nayi baki, ta zo
daidai da sallamar Baba, nan take naji wani daci tamkar
na tauna madaci. Innarmu ta mishi sannu da shigowa,
tare da shimfida mishi tabarma.
Cikin fargaba na soma gaida shi, ga mamakina yau
fuskar shi sake ya amsa, har da ce min "An dawo lafiya?"
Na ce, "Lafiya lau". Innarmu ta ce, "Allah cikin ikonSa
Malam yau dai su Hafsat karatun Sakandire ya
kammala."
Ya ce, "To dama tunda da mai sonta sai ta yi masa
magana ya fito in hada su da Sakina in huta". Inna ta ce,
"Anya kuwa? Ina ga daurewa da zaka sake yi ta tafi
makarantar gaba da..."
Wani kallo da ya mata shi ne ya dakatar da ita. Ya mike
tsaye ransa a bace.
"Na gaji da wasa da hankalina da ku ke yi, ba zan iya
ganin Hafsa gandandan cikin gidan nan ba, duk wanda ya
shigo ba zai bambance ta da matan gida ba, duk wata
tana zubar da jini, ta zama Uwar mata. Wannan karon
zamu yi tsiya da ku yanda bakwa zato. Wai menene cikin
wannan bokon da ku ka nace mawa? Ina ce karatun
gidan duniya ne?"
Inna ta kufulo itama, ta ce, "To dama ka saba ka min
tijara cikin gida gaban kowa akan Hafsa, tun da babu
sisinka kasa ido, kuma karatu ba fashi. Ya ce, "To zan ga
wanda ke auren wani, tsakanin ni da ke". Ya fita.
Na dago ido da hawaye, takaicina ace kullum Iyayena
basa rigima sai a kaina, bari Munnir yazo anjima, zan ce
masa kawai ya turo manyansa ayi magana, ko ina dakin
nasa zanyi karatuna. Ban dai fadi ma Innarmu kudurina
ba.
Na mike ina tattara kwanukan gabana, Inna kuma sai
mita take, na ce "Innarmu ki bar batun haka, kinsan
gidan nan da gulma, yanzu kowa ya baza kunnuwa yana
sauraro". Ta ce, "Suyi ta sauraro din, ina ruwana. Iyaka
dai mace tayi da ni naji mu kwashi 'yan kallo ni da ita".
Na idar da sallar isha'i, ina zaune a gurin ina istigfari,
wani yaron gidanmu yayi sallama, bai jira amsa ba ya ce
"Innarsu Ummi wai ana kiran Hafsa a waje". Ta ce, "To".
Na mike, nasan Munnir ne, don na aika masa da letter
cewa na dawo.
Na bude jakata na ciro turarena forever na fesa, sannan
na sabi gyalena na fita. Tun kafin na karaso na jiyo
kamshin turarensa.
Yana zaune saman motarsa kirar (Toyota camry), baka
wuluk, sanye yake da wando jean baki, rigarsa fara. Cikin
farin ciki na isa gabansa, nayi masa sallama ya dago da
kanshi daga wayar da ke hannunsa yana latsawa.
"Babyna". Sunan da yake kirana kenan. Na ce, Na'am".
Ya diro "Zo muje cikin mota." Na ce, "A'a mu zauna
can". Na nuna mishi dakalin kofar gidanmu.
Ya dan gyara tsaiwa, "Kin ce fa baki son Baba ya dinga
ganina da kananan kaya, kin san dai in muna can zai
ganni dole ko?"
Na dan yi jim ina nazari. Hakika Baba na fada cewa
Munnir ba dan mutunci ba ne, ya gane haka ne tun daga
suturar da yake sakawa.
Amma bana son shiga motarsa saboda ya cika son taba
jikina.. Ya katsemin tunani da cewa.
"Zo muje, na zo da muhimmiyar magana". Na ce masa,
"Nima ina da nawa muhimmin zancen". Baya ya bude ya
shiga, nima na shiga dayan gefen, sai dai ban rufe ba. Ya
ce "Rufo kofar mana". Na ce, "Ka barshi haka ma ya yi.
Ya kunna wutar motar, haske ya bayyana, ni da shi muka
kalli juna cikin ido. Nayi saurin janye nawa idanun, domin
wani abu da na ji yana bin jijiyoyin jikina.
Ya ce, "Ina sonki Hafsy, ban san irin son da nake miki
ba." Ya kama hannuna na kwace, tare da mai da su baya
na ce, "Don Allah Munnir ka daina son taba jikina,
haramunne fa". Ya ce, "Zamu fara ko? Haba Hafsy, ni ne
fa zan aure ki. Ko yaushe ina son in gwada miki so sai ki
yi ta ki, yaya ki ke yi tamkar wacce bata je makaranta
ba? Sai ka ce ba *yar boko ba? Ni fa kullum ina fada miki
ba zan auri mata muje kina min wani kunshe-kunshen jiki
ba.
Na bata rai, ya shafi kumatuna.
"Small beby, dan yi murmushi. Ba kya yin kyau in kin
daure fuska". Shikenan, ban san lokacin da murmushin
ya subuce min ba, matsalar ina mutuwar son Munnir. Ya
ce, "To fada min maganar kafin kiji tawa, don tawa in
kinji saikin bani goron albishir.
Na ce, "To ni dai dama ina son ne in ce maka ya dace
yanzun muyi aure, don wallahi da kyar Baba ya bari na
gama karatun nan. Sam shi ba ruwan shi da da boko, ka
dai sani". Ya ce, "Haba Baby, aure fa ki ka ce? Kin
manta alkawarin da muka yi ni da ke?"
Na ce, "Ban manta ba". Ya ce, "To ki kyale fadan Baba
kawai, ba nine ke biyan komai na karatunki ba? Come on
aje wannan topic din. Na shirya miki gagarumin party ne
saboda murnar gama karatunki, don haka yaushe zamu je
kasuwa musai kayan sawa?
Takaici ya cika ni, don haka ban tanka ba. Ya sake
matsowa in banyi magana ba nasan zai iya cewa zai
rungume ni. Da sauri na ce, "Duk lokacin da ka shirya".
Ya ce, "Gobe yayi? Dan ranar sati ne party din."
Na ce, "Um". Ya ce, "Wai ba ki murna ne angel dina?
Kada ki damu, kwanan nan za ki zana (JAMB), sai kin
zama *yar media insha Allah.
Na dube shi, "Yanzu sai zuwa yaushe zamu yi aure?" Ya
ce, "Mun kusa, ai shekara hudu ya rage min na hada
master dina, before time din kin zama *yar media ko?
Nayi shiru. Ya sake matsowa har muna jin numfashin
juna, bakinshi daidai kunnena ya ce, "Kin san ina son
aure nima tuntuni damuwa daya Dad dinmu shi ne yaki.
Yayyena guda uku suna nan harda mace, kin sani dai ya
ce duk sai sunyi master sun fara aiki balle ni.
Na ce, "To sai yanda Innarmu ta ce". Ya ce, "Bana jin
Inna, zata yarda". Ya sake yin kasa da murya "In dan yi
kissing din kunnenki?" Naja baya tare da cwa, "A'a". Ya
ce, "To bari na tafi". Yana magana yana kallon agogon
hannunshi, "Zan kalli wasan Arsenal yau." Na ce, "Kai
kam har yanzu kana nan da kallon kwallon nan."
Ya ce, "Kema za ki koya in kinzo gidanmu". Nayi dan
murmushi. Ina son Munnir, shi yasa zan jure na jira shi,
amma Allah Ya sani ina son aure, don ina zaton ina cikin
mata masu bukata.... Ya katse tunanina da cewa, "Ko
kada in tafi ne?" na ce, "A'a kaje sai gobe". Ya ce,
"Shikenan." Ya miko min wata farar leda.
""Gashi kisha, ice cream ne da fresh milk." Na ce na
gode, amma don Allah ka daina yimin irin wannan
dawainiyar.
Innarmu ta dubi ledar bayan na ciro kayan ciki, ashe har
da kayan tea. Ta ce, "Kai yaron nan baya gajiya da
dawainiya. Ni da zai fito ayi auren nan tunda yana zon
karatun kyayi can a dakin shi.
"Inna nayi mishi wannan zancen ya ce min in kara
hakuri." Kamar na fadawa Inna zancen party din gobe,
sai na fasa don nayi imani ba zata barni ba, duk da tana
son abinda nike so.
Yau Baba dakinmu yake, don haka dakin Babah kishiyar
Innarmu zamu kwana. Ina kwance kan yaloluwar katifata
mu da Sakina, can kasa sauran kannena da aka musu
shimfida. Ko wannan cakudin na daga cikin abin da yasa
nake son in ganni a dakin kaina.
Washe gari tun safe muka soma aikin alalar siyarwa da
Innarmu ke yi. Misalin uku saura Nazifi ya shigo yana
cewa, "Hafsa ga saurayinki a waje. Ko da bai ce na kira
ki ba, nasan gurin ki ya zo.
Dama tuni nayi wankana, ina sanye da riga da siket na
atamfar (Java), gyale na sura na ce "Inna Munnir na
kirana."
Ta ce, "To." Na nufi waje kai tsaye.
Yana sanye da kananan kaya kamar ko yaushe, ina isa
ya budemin gaban motar na shiga, sannan shima ya
shigo. Na gaida shi ya amsa tare da yiwa motar key, na
ce, "Muyi sauri ban ce zamu fita ba." Ya ce, "To".
Wani (Boutique) muka je, duk tsinannun kaya ne a
gurin, shi dai ya zabi nashi, amma ni nace ban ga
wanda ya yi min ba. Nan ya shiga jidar min, na bata rai
tare da nuna mishi sunyi yawa. Ya ce, "To zabi wanda
ki ke so."
Na daga duka babu na arziki, siraran wanduna ne da
*yan riguna, sai doguwar riga wadda in nasa da kyar
zata wuce gwiwata. Na aje su gefe, na dube shi.
"Duk ba su yi min ba". Ya bata rai sosai, "Tashi muje".
Na kafa mishi ido. Ya ce, "Tashi mana". Cikin daga
sauti na ce, "To, to naji zan amsa, amma ni na gane
kamar zasu yimin kadan." Ya dan sassauto "Muje
gidanmu ki gwada." Da sauri nace, "A'a zasu yi min."
Yayi murmushi, sannan muka je ya biya muka shiga
motarshi. Ya ce, "Muje mu dan sha Ice cream". Na ce,
"A'a kai ni gida, Innarmu bata san na fita ba, kuma
nasan zata sa a leka ni, fada kuma zata yi min". Ya ce,
"To naji sarkin tsoro, ke dai kawai kina tsoro ne kada
na cinye ki."
Gabana yayi muguwar faduwa ganin Baba zaune a
dakalin kofar gidanmu, na ce na shiga uku, ga Babana,
ya ce "To menene? Ina jin mamakin ki wallahi. Shi
yasa Dad din mu yake matukar burge ni, baya takura
mana, shi dai in dai zamuyi karatun boko to duk abin da
muka ga dama muyi. Kuma zai kashe mana the last
kudin shi don muyi karatu.
Na ce, "Uhm, don Allah ka tafi da kayan, na karba,
amma ka fito ku gaisa.
Tare muka fito daga motar, jikina har bari yake. Na nufi
cikin gida, Munnir yayi gurinshi. Ina isa Inna ta ce,
"Daga ina ki ke Malam ya shigo yana ta fada yaga
lokacin da ki ka shiga mota? Na ce, "Um asibiti muka je
dubo kanwarshi". Ta ce, "Shi ne ba za ki fada ba? Kin
san fadan Malam, don Allah ki rufamin asiri kada ki ja
min surutu sanadin bokon nan."
Na ce, "Kiyi hakuri Inna." Ina rufe baki Babanmu yana
shigowa, tun kafin ya karaso na jiyo muryarshi yana
cewa.
"Na fada maka kenan, in da gaske ka ke yi ka turo min
manyanka. Shekara nawa ina ganinka a kofar gidan nan
wai ku *yan boko, zaku ce min sai kun gama boko, to
ban laminci wannan ba."
Hanyar uwar daka nayi, don nasan yanzun ya make ni,
ya ce "Ke *yar boko kinbi saurayi kasuwa ko? Inna ta
ce, "A'a Malam asibiti fa suka je." Ya zaburo tamkar
zai kai ma Inna duka, ya ce, "In ji wa? Wa ya fada
miki?"
Inna ta ce, "Ga ta nan." Ya ce, "Makaryaciya, to shi
abokin yawon nata ya ce min daga kasuwa suke, duk
ya rasa wanda zai ce ya raka shi kasuwa sai ke?" Inna
ta tsare ni da ido, "Kasuwa Hafsa?" Nace, "Kuyi hakuri,
ba zan kara zuwa ba." Tayi kwafa tare da ci gaba da
yin aikinta. Baba ya ce "To wallahi ba zan yarda da
gantali ba, wai ku *yan boko."
Inna ta dube ni, "Ai gara ki saka min da haka. Tunda ni
na jajirce ki samu karatun boko." Na ce, "Don Allah
Innarmu kiyi hakuri, wallahi ba zan sake ba". Ta ce, "To
me yasa ki ka min karya? Kin san dai na tsani a min
karya, duk abin da ya faru nafi son gaskiya ko?" Na ce,
"Na sani.
Haka nayi ta bata hakuri, kun san Uwa, nan da nan ta
sauka. Ta min fadan cewa kada na sake yarda na bi
saurayi wani guri.
Kwana daya, biyu ban ji daga Munnir ba, lallai Babane
ya kore shi letter na rubuta na ba Nasirun gidanmu na
ce ya kai masa. Tambayarshi nayi ko lafiya? Na jishi
shiru. A bayan takardar ya rubuto cewa Babana ya kore
shi, don haka shi ya hakura da ni. Na girgiza da jin
wannan zancen, don ina son shi kullum burina na aure
shi. Shi kadai nake jin sha'awa. Na rasa yanda zan yi
ko satar jiki zan yi na je gidan su? Innarmu ta gane ina
cikin damuwa, ta ce "Hafsat ba ki jin dadi ne? Na ce,
"Ciwon kai ne yake damuna." Ta bayar da Naira goma
a amsomin panadol."
Da dare nace Innarmu zan je gidansu wata yarinya *yar
makarantar mu, in amso wasu takarduna, ta ce, "Kar ki
zauna, maimakon kije tun ido na ganin ido?" Na ce, "Ai
dazun ciwon kai ke damuna." Ban yi wata kwalliya ba,
kada ta gane, sai kawai na dan fesa turare. Na zari
mayafi, gidan su Munnir da dan tafiya tsakanin mu
saboda mu muna Rigasa ne Abuja Road ta kasa, su
kuma suna Makarfi Road.
Tun daga nesa na hango shi su da wani tsaye, ga
motarshi gefe, ina zaton fita zasu yi. Sai na kara sauri.
Daidai ya bude motar zai shiga na ce, "Munnir" Ya juyo
da sauri, ya mai da motar ya rufe. Abokin nasa yana
ciki, ya ce, "Beby lafiya?" Na jingina da motar, sannan
na sauke ajiyar zuciya, domin na gaji. Sai dai kuma
lokacin ne naga rashin hankalina.
Yanzun ince mishi me? Na zo in bashi hakuri ko nazo
biko? Ya sake cewa, "Me ya faru Baby? Na ce, "Ai ba
ka ma sani ba?" Dabara tazo min, na ce "Dama nazo ne
na maka godiya akan dawainiyar da kayi da ni, don ko
zamu rabu bai dace mu rabu ba zumunci ba."
Ya ce, "Baby kenan, don na fada kina ganin zan iya
rabuwa daKe? Ni ina sonki, Babanku ne ya tozarta ni"
Kafin nayi magana ya ce, "Ina zuwa." Ya leka motar
yayi magana, sannan ya ce, "Zo muje ciki kiji." Na ce,
"A'a. Ya bata rai, "Bana son yawan gaddamar nan, ki
daina kada muyi aure mu zo muna samun matsala.
Na ce, "Ina jin kunya ne, saboda Mamanku, Ya ce, "Ba
za ta san kin shigo ba, zo muje. Na bishi, ya tura Gate
din gidan, muka shiga.
Yau ne na soma shiga gidansu, ginin zamani ne ga
haske tamkar rana, me gadinsu ya ce, "A'a, ka fasa fita
dinne? Ya ce, "A'a Baba, yanzun zan fita.
Na gaida maigadin muka tafi ginin farko daga cikin
gine-gine ukun da ke harabar gidan, ya ce, "Yau kin zo
gidan mu, ba don kunya ba da na kira miki kannena su
Nana.
Na ce, "Barsu yanzun zan tafi, kuma bai dace su ganni
cikin wannan yanayi ba, ina nufin shigar da nayi. Ya ce,
"Shikenan.
Katon falo ne, yana dauke da kayan more rayuwa, sai
kofofi guda uku, yace in zauna kan kujera, na zauna.
Ina kallon ko ina, ya nufi kofa daya daga cikin kofofin,
jim kadan ya fito dauke da gwangwanin maltina da kofi
ya zauna hannun kujerar da nike
Zaharaddeen Shomar
whatsapp 08168575100
Sanadin Boko 1 02
Posted by ANaM Dorayi on 09:42 AM, 10-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Na
Maryam Abdullahi K/Mashi
Katon falo ne, yana dauke da kayan more rayuwa, sai
kofofi guda uku, yace in zauna kan kujera, na zauna. Ina
kallon ko ina, ya nufi kofa daya daga cikin kofofin, jim
kadan ya fito dauke da gwangwanin maltina da kofi ya
zauna hannun kujerar da nike.
Ya balle hancin gwangwanin ya cika dan kofin ya mika
min, na girgiza kai tare da cewa, "Na gode. Ya ce, "Wasa
ki ke yarinya, rike nan ko na dura miki.
Da sauri na amsa saboda nasan halin shi sarai, zai iya.
Kurbata biyu na aje, ya kama hannuna na kwace tare da
mikewa.
"Tunda ka huce ni zan tafi. Ya ce, "Dama ni banyi fushi
ba. Na kalli fuskarshi muka hada ido, ya kashemin
idonshi daya, nayi saurin kauda idona saboda yarr din da
tsigar jikina tayi.
Na ce, "Yaushe zaka zo? Ya ce, "Zauna to mu tsara in da
zamu dinga haduwa, don Babanku ya ce in manyana ba
su zo ba kada ya sake ganina.
Na ce, "Fada min daidai ina ne zamu dinga tsayawa? Ya
dan yi shiru, "To ni bansan yaya zamu yi ba, na ce zan
hada miki phone kin ce a gida ba za a barki ba, wai ke
ba ki da irin 'yar dabarar ku ta mata ne? Ki saka ta a
silent.
Na ce, "Barta kawai. Ya dube ni, fatin kuma fa? Na
marairaice murya ina kallon shi da idanuna, da na lura
yana son su. Mu bar maganar party din nan, wallahi ba
Babana ba har Innarmu in ta sani zan bani, ka ji.
Ya tsare ni da manyan idanunsa.
"Yanzun nayi asara kenan? Ya ci gaba "Ban san me yasa
gidanku ake yin haka ba, ni kinga kannena su Nana da
Suhaila Mom din mu da Dad din mu sune suka shirya
musu party din su last week. Amma ku sai ana hana ku.
Wannan duhun kai ne, yanzu fa an waye.
Na ce "Ba wani duhun kai, kowa da irin tarbiyar da yake
son ya yi ma 'ya'yanshi. Ya ce "Shikenan dai, mu bar
maganar, naji nayi asarar kudina, kuma ba wani gida ke
ce dai ba ki ga dama ba.
Wani friend dina yarinyarshi itama 'yar Geto ce, amma ta
jirga Iyayenta da cewa suna biki ne tazo muka yi shagali,
amma ke kin kasa.
Na ce, "Ni dai kayi hakuri kawai. Ya zuba min ido, sai kin
yi min kiss zan hakura. Da sauri na dauki hanyar fita, sai
kawai naji ya rungume ni ta baya, jikina ya dauki rawa.
Cikin rawar murya na ce, "Munnir la..la....lafiyarka? Don
Allah sake ni. Da kyar na kwace, kamanninshi sun canza,
da sassarfa na fito na dau hanya. Ya biyo ni da mota shi
da abokinshi, wai na shiga su kaini gida, na ce, "A'a don
na tsorata, dole suka bar ni.
Da na zo barci na jima ina tuno abin da Munir ya min,
dama an ce mace da namiji in suka kebe na ukun
shaidan ne. Ba don son da nake yiwa Munir ba, da tuni
na bar shi.
Mun canza gurin hira, bayan layinmu yake tsayawa. Na
fada ma Innarmu ta ce saboda me? Na ce, Baba ya hana
shi zuwa nan.
Inna ta ce, "Mallam ho! Shikenan, ki dinga zuwa da
Ummi kin san mutane da sa ido, yanzun sai ace wani
abin ne yasa ku ke zuwa can. Fatana ki kama kanki.
Na ce, "To, nima zuwa da Ummi zai fi min, duk da Munir
ganin Ummi bai hana shi son taba jikina ba.
Cikin haka muka soma shirin zana (JAMB), Baba bai sani
ba, Munir ne ya sai min form, sai dai tsorona daya randa
Baba zai sani.
Na zama cikin sa'a kamar ko yaushe, Munir ya tsaya
tsayin daka har na samu gurbin karatu a (B.U.K) Kano,
sai dai ya zamuyi da Baba? Haka na ce ma Innarmu, ta
ce yau na yanke shawarar sanar da shi komai, tunda
gobe za ku je yin rijista.
Kusan goman dare, lokacin ina kwance muryar Innarmu
nake ji tar daga dakin Baba, domin bangonsu daya. Tana
sanar da Babanmu komai.
Bai katse ta ba har ta kai karshe, ya ce, "To bokon nan
ba da yawuna ba, bayan shekara shidan da na hakura
tayi yanzu kuma wata zata? Wai lahira take so ko
duniya?
Inna ta ce, "Duka. Ya ce, "Karya ne, duniya ku ke nema,
kuma ga ku gata nan. Jami'ar da aka ce 'ya'ya suna
lalacewa? Yarinyar ta fada a gabanki sama da shekaru
amma baki damu ba. To magana ta ni uku ce, bata kai
hudu ba.
Na farko duk abin da ya faru da ita SANADIN BOKO ba
ruwana, zai shafe ki ne da ita.
Na biyu ba zan yafe hakkina da ku ka tauye ba,
matsayina na Ubanta, kuka hana ni in sauke nauyin da
Allah Ya dora min.
Na uku kuma ta nemi Ubanta ke kuma ki nemi mijinki,
duk ranar da wata ashsha ta samu SANADIN BOKO.
Ba innarmu ba, ni kaina zancen ya girgiza ni. Baba
kishiyar Innarmu ta fito daga uwar dakinta, ta zo kusa
dani ta zauna.
Tasa hannu ta dan dake ni, "Tashi Hafsatu.
Na tashi zaune jikina sharkaf da zufa, ta ce "Nasan kin ji
duk zancen da Malam yake yi ko?
Na ce, "Eh. Muryar Innarmu ta katse ni, ta ce, "Insha
Allahu Malam karatun Hafsa zai zama alkhairi garemu da
kai gaba daya.
Ya ce "Ruwanku. Cikinsu ba wanda ya sake magana.
Babah ta ce, " Hafsatu ki bar Babanki yayi iko da ke, ki
ce ma Innarku kin fasa karatu. Kalamanshi ba baki yayi
miki ba, amma ina ji miki tsoron alhakinshi kada ya kama
ki.
Na ce, "Babah wanda zan aura karatu yake yi, ba yanzu
zai yi aure ba, kuma Iyayenshi ba za su yarda ya auri
mara ilimi ba.
Babah ta ce, "Sai shi? Akwai masu sonki da yawa, kuma
sun ma Babanki magana. Nayi shiru ina nazari, nasan
Babah gaskiya ta fada min, amma ya zan yi da son
Munnir?
Na dube ta, "Babah ki duba irin hidimar da Munnir yake
yi da ni, ba zan mishi adalci ba in na ce ba zan jirashi ba.
Ta ce, "To yanda ki ka gani, amma karatun nan tunda ba
na Muhammadiyya ba ne, banga dalilin naci ba.
Kuma ni sai in ga yaron nan tamkar yaudararki yake yi.
Anya auranki zai yi? Na ce, "Allah Babah aurena zai yi, ki
dubi dadewar mu da hidimar da yake min.
Ta ce, "Ba ta a nan, amma fa shawara ce." Na koma na
kwanta, ita kuma ta mike ta nufi cikin dakinta.
Zancen Babah ya taba zuciyata, illah magana daya da
ban kama ba, wai tana ga Munnir ba zai aure ni ba. Nayi
guntun murmushi, me zai sa shi ya yi ta dawainiya da ni
ba zai aure ni ba?
Yanda na raba dare ban yi bacci ba, na tabbata
Mahaifana biyu ma haka ne, duk SANADIN BOKO. Da
safe ina zaune da kofin koko sai juya shi nake yi na kasa
sha, Innarmu ma sukuku take.
Lokacin da ta zauna tana shafa ma gwangwanayan
alalarta manja, na ce "Inna ko dai zamu hakura da batun
bokon nan ne?
Ta dube ni, "Saboda me? Na sunkuyar da kai na ce, "Naji
duk yadda ku ka yi da Baba jiya. Tayi shiru, can ta ce,
"Abu daya zuwa biyu nike so ki min.
Na zuba mata ido, na farko ki tsaremin kanki da
mutuncinki, kada ki banzantar da kanki, na biyu kiyi abin
da ya kai ki makaranta, wato karatunki wanda nike fata
ya zama sanadin alkhairi.
Ta haka ne za ki wanke wa Mahaifinki tsanar da ya yi
wa boko, har kannanki suma su samu dama suyi cikin
kwanciyar hankali. Yayanki da bai samu damar ci gaba
ba yana jin haushi.
Ke tunda kin samu dama kada ki bani kunya. Na hada ki
da Allah, ki rufamin asiri. Tausayin Innarmu ya cika ni,
na ce, "Insha Allahu zan kula sosai, kuma zan fidda ki
kunya, SANADIN
BOKOn nan kowa zai huta, Baba zai yi alfahari da ni.
Munnir yayi tsayin daka har na zama daliba a jami'ar
Bayero da ke Kano, har lokacin da zan tafi Innarmu bata
daina rokona in rufa mata asiri in lura da kaina ba.
Nan na tafi na barta da surutun 'yan gidanmu, da 'yan
unguwarmu. Wasu suce tana so ne ta auri mai kudi, shi
yasa muka nace boko, wasu su ce dan kyan nawa bai fi
cikin cokali ba, amma mun kuke sai nayi boko.
Wasu su ce dan-dan masu hali ke sona, duk dai ta toshe
kunne watan kwaram daya ne. Baba har fushi yayi da ita,
sun jima kafin ya soma amsa gaisuwarta.
Karin haushi yakai kararta ga danginta, maimakon su
bata rashin gaskiya suyi mata fada, sai suka ba shi
hakuri suka ce wai karatun yana da amfani.
Ya ce, shi ba ya ce babu amfani ba ne, a'a tayi shi can
gidan mijinta. Aure shi ne sama da karatun ta, sai suka
ce ya yi hakuri 'yan kwanaki ne zata gama, don haka sai
ya dawo ya zura mana ido
******* ********** ********** *********** *********
Jami'a wata rayuwa ce da ta sha bamban da
secondary, banga laifin Baba ba yanzun don ya
kyamaci boko, sai dai na sha alwashin kula da kaina,
don haka na tsare gida bani da kawa ko aboki. Duk da
Munnir na shirin tafiya Dubai karatu don kammala
Masters dinshi, haka bai hana shi zuwa duk bayan sati
biyu ba. Tafiyar tashi bata yuwu ba har muka samu
hutun first semester, sati biyu dai za mu yi amma naji
dadi, sai dai wannan hutun ne hutun da ba zan taba
mantawa dashi ba a rayuwata. (Kuma shi ne dalilin
rubuta labari na "SANADIN BOKO" .
Sauran kwana biyar na koma Makaranta duk da inata
dokin zuwa gida amma zaman gidan bai mun dadi ba,
ko gaisuwata Baba baya amsawa har ta kai da naji
muryarshi zan boye.
Bello Abokin Munnir shi yayi sallama da ni, na sha
mamaki don bai taba zuwa shi daya ba. Ya ce, Munnir
ya aiko shi muje tare bashi da lafiya. A rude na je na
fadawa Inna, ta ce, "Yana asibiti ne?" Duk da ban sani
ba sai na ce mata, "Eh." A zatona yana asibiti ne, sai
da yaja mota sannan nace, "Wane asibiti ne." Sai ya
ce, "Ai yana gida." Har gefen su Munnir Bello ya raka
ni, ina shiga sai yace mun, "Toh yana ciki ni na wuce ki
fada masa don ya dameni in kawo ki har ciki. Na ce,
"Toh!" Na nufi ciki da tafiya cikin dari-dari. Tsakiyar
falon na tsaya na zabga Sallama, ga mamakina sai ga
Munnir ya fito daga kitchen sanye da gajeren wando da
vest duka farare tas, hannunshi dauke da ruwa (C way)
yana sha. Na ce, "Ah! Ka samu sauki ne?" Ya ce, "Eh,
A'a." Ya nuna min kujera, "Zauna." Na zauna ina kallon
shi tare da son jin karin bayani, "Ban gane eh, a'a ba?"
Ya tsugunna a gabana, "Ciwon ya dade yana ci na, ga
shi zan iya tafiya Makaranta cikin kowane lokaci ba
tare da na samu maganin ba." Na ce, "Wane irin ciwo
ne?" Ba tare da shakka ki tunani ba ya ce, "Ciwon
sha'awarki....."
Gabana ya fadi, na mike tsaye da sauri. Shima ya mike,
"Hafsat kin san ina son ki, wallahi na gaji da
sha'awarki. Ki so ni kamar yanda nike son ki." Na ce,
"Munnir ka san ina son ka." Ya ce, "To ki nuna min."
Na ce, "Ban gane ba? Sau nawa nake cwa ina son ka?
Ka sani." Ya ja tsaki, "Kin dai gane nufi na, ina son yau
daya ki taimaka ki nuna kaunarki gare ni." Na ce, "A'a
ba zan iya ba, domin haramun ne." Ya ce, "Ni fa zan
aure ki!" Na soma tafiya don fita ina cewa, "Sai ka jira
sai ka....." Maganata ta tsaya sakamakon murda kofar
da naji nayi ta a rufe gam. Na dube shi yana murmushi
ya ce, "Ki bani hadin kai don yau ta karfin tsiya ma zan
iya biyan bukata ta." Jikina ya soma bari na ce,
"Wallahi Munnir zan maka ihu, ka bude min kofa." Ya
zauna, "Ko kin yi ihu ba wanda za ya ji ki. Mom bata
nan tana gurin aiki, Dad ma haka, su Nana da Suhaila
suna Makaranta." Na zube gwiwoyina biyu a rude ina
cewa, "Ka min rai kada ka sa ni cikin matsala, don
Allah." Na soma kuka. Ya ce, "Nima ki taimake ni na
gaji, wanene za ya gane me muka yi?" Na ce, "Allah ya
sani, na tabbata zai kama mu." Amma da yake Shaidan
ya hura ma Munnir kaho sam ya ki karban uzirina.
Muka yi ta zaga falon har na fada wani daki, sai dai
kafin na rufo tuni ya banko, mun yi damben bala'i dashi
kafin ya samu nasarar aikata mummunan nufinshi a
kaina, bayan ya bi duk wata gaba ta jikina ya bugeta,
fuskata kuwa ta sha mari sai na ga kamar ba Munnir
dina ba.
Kuka iya kuka na yi shi, na mike ina gyara daurin
zanina, da kyar nake tafiya na fito falon, ya ce, "Duk kin
sa mun wahala, a yanzu wa zau sani in ba kin fada
ba?" Na ce, "Bude min kofa kawai ni dai na tafi." Ya
nufo ni, "Come on kiyi wanka sai na kai ki." Ban san
lokacin dana daka mishi tsawa ba, "Budeni mana"
Sabon kuka ya kwace min na ce, "Allah ya isa tsakani
na da kai, Insha Allahu sai Allah ya saka min." Ya tashi
ya bude tare da cewa, "Sai na zo." Ban kulashi ba na
fita, dole na share hawayena saboda Maigadinsu, na
fita ko ina a jikina ciwo ya ke. A haka na kai gida, kallo
daya Inna ta min tace, "Lafiya?" Jikina ya soma bari, ta
ce, "Ba dai jikin nashi ba? Na ga duk kin rude fuska a
kumbure." Na ce, "Umm jikin ne." Ta ce, "To shine na
kuka? ki masa addu'a." Na ce, "To." Na nufi ciki. Ta ce,
"Hafsa zo nan, menene wannan a zaninki?"mummunar
faduwar gaba ta ziyarce ni, zufa kuma ta shiga keto
min, amma sai na yi saurin cewa, "Fashin Sallah ne."
Duk da ban juyo ba kuma ban san mai ta gani jikin
zanin ba. A gani na in muka hada ido zata gane, ta ce,
"Haka kika ratso titi? Ga ruwa da na daura chan kan
wuta na tuwo ki diba ki maida min sai ki dauraye
jikinki."
Cikin bayi ina wanka ina kuka tausayin Innarmu ya cika
zuciyata, na karya alkawarin da na daukar mata, Allah
ya isa Munnir.
Cikin kwanakin da suka biyo baya ko Munnir ya zo
bana fita, ranar da zan koma Makaranta har goman
safe ina kwance a tsakar daki, Innarmu ta ce, "Ke da
naji kina cewa sammako zaki yi? Har yanzun kin kasa
tashi?" Na ja tsaki, yanzun na soma tsanar boko bani da
daman in tona asirina...
Yaron gidanmu ya shigo ya ce, "Hafsa wai in kin shirya
wani mai mota ya ce ki fito yana can saman layi." Na
ja tsaki, "Ka ce masa ya tafi na san hanya." Innarmu ta
ce ma yaron, "Kai zo, je kace tana zuwa." Yana fita ta
fara min fada wai bani da hankali, ta lura kullum zai
kirani in 'ki fita, haka ake yi? In ma sabani kuka samu
ba sai kiyi hakuri ba tunda shi har ya zo? Na kalli
Innarmu a zuciya na ce, "Da kin san abinda ya min sai
kin fini tsanar shi." Ban ce komai ba na ci gaba da
shiri. Inna ta kwance habar zaninta kudine 'yan hamsin
hamsin dubu uku na adashena na kwasa, sannan cikin
robar can tumatir ne na tafasa shi ga sabulu can inji
Baabarki..... Na ce, "Ki bar kudinki." Ta ce, "A'a na dai
baki ne, amma badan zasu ishe ki wani abu ba ne.
Yaron nan dake dawainiya da ke Allah ya gwada min
aurenku." Yana zaune yana latse-latsen waya ya diro,
"Gimbiyata, amaryata har yau fushi kike da ni? Gashi
doguwar tafiya za muyi? Don Kano zan kaiki." Ban
tanka shi ba ya amshi robar hannuna da leda ya daga
but ya sa. Ni dai tamkar na haushi da duka nake ji, ya
bude mun gaba na shiga don bani da yadda zan yi.
Tunda muka dau hanya yake mun magana amma ban
tanka shi ba. Ya ciro waya daga gefen shi ya ce, "Ga
wayarki." Sai lokacin na yi magana, "Bana so." Ya
daurata kan cinyarshi, "Dole ki so ta Hafsat don in na
tafi karatu ta yaya zan dinga jin muryarki? Ki saki ranki,
abun da ya faru ba wata matsala bace saboda ni zan
aureki..." Na zabga mishi harara tare da cewa, "A
ganinka kenan, amma ni addinina bai yadda don zaka
aure ni kayi ZINA dani ba." Ya katseni, "Ki daina cewa
Zina." Na daga murya na ce, "Ka biya sadaki na ne?
Iyayenka sun nemi aurena gun iyayena ne an basu? Ko
jama'a sun shaida." Ya ce, "Ba daya." Na ja tsaki ban
kara tanka shi ba har muka kai.
A dakinmu ba yadda bai yi ba na'ki tankashi, ya aje
mun kudi da waya ya tafi. Na saka kuka nayi ma ishi
na, tunanina in Allah bai yi aurena da Munnir ba fa? Ya
sakani cikin matsala kenan don ban san mai zance ma
mijina ba yayin da yace ina nakai budurcina? Dole in
dauki hakuri in lallaba Munnir ya aureni.
-Yana kiran wayata sosai, tun ina sharewa har na
hakura don ban san yadda zan yi ba, sai dai bashi da
wata daraja ko kima a ido ba, ko na aureshi gani nake
ba zan girmama shi ba, tunda na ga irin nashi rashin
Imani.
Sai mene? Tun jiya sha hudu ga wata ya dace in ga
al'adata amma har yau sha biyar shiru. Wannan ya
tilastamin shiga rudani.
Dora John dakinmu daya har ta gane ina da matsala ta
ce, "Hafsy yaya ne?" Na ce, "Ciwon kai ne." Ta bani
panadol da sauri na sha don kuwa kan nawa na ciwo.
Kwanaki uku suka biyo baya gashi banji daga Munnir ba
cikin 'yan kwanakin, naje na sai kati na kira shi, yana
dagawa na soma kuka, ya ce, "Mai ya faru?" Na ce,
"Banga period dina ba yau kwana uku." Ga mamaki na
sai na ji bai damu ba ya ce, "Zan shigo wannan ba
wani abun damuwa ba ne."
Washegari sai gashi da wani abokin shi, yana shigowa
na soma kuka nan take ya bata rai, "Kukan nan ya
soma isata, zan barki ki karata in dai ba zaki daina mun
kuka ba." Abokin shi Bello ba karamin tsanarshi nayi ba
har da cewa, "Daga sau daya sai ciki?" Munnir ya ce,
"Nima dai nayi mamaki bata fa tsaya ba ma, gaskiya in
anyi bikin mu juya Mahaifarta za'ayi don bana son yara
su wuce biyu tsanani uku." Tsabar bakin ciki ya hana ni
tankasu, ni dai burina ya san yadda zai yi dani. Bello ya
kira wani abokin shi anan Kano wai shi Nasir, ya zo
suka tafi suka yi magana sannan suka ce inzo mu je
asibiti.
Mun shiga office din Likita mace 'yar kimanin shekara
arba'in tana tsaye da farin gilashi, ta tsareni da ido
bayan duk mun zauna ta kalli Nasir, "Me ke tafe da
ku?" Duk muka yi shiru, Munnir ne mara kunya shine ya
ce, "Mun kawota ne bata ga period dinta ba, so muna
so a gwada ta." Ta tsareshi da ido, "Kanwarka ce?" Ya
ce, "Budurwa ta ce." Bakin ciki ya cika ni, na sunkuyar
da kai ina hawaye, "To ku dan bamu wuri." Suka fita.
Ta zabga min harara, "Kin bashi kan ki ko?" Murya ta a
sarke na ce, "Wallahi...
Zaharaddeen Shomar
what's app 08168575100
Sanadin Boko 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 09:47 AM, 10-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
NA
Maryam Abdullahi K/Mashi
To ku dan bamu wuri." Suka fita. Ta zabga min harara,
"Kin bashi kan ki ko?" Murya ta a sarke na ce, "Wallahi
Anty fyade yayi mun." Ta ce, "Tun yaushe?" Na ce,
"Za'a kai wata daya." Ta bani wata 'yar roba ta nuna
min wata kofa, "Shiga toilet ki bani fitsarinki." Ina
fitowa naga wata nurse tsaye ta ce, "Don Allah sister
ina son result yanzun nan." Ba jimawa ta shigo, Likitar
tayi ta juya takardar sannan ta dube ni ta ce, "Kina da
cikin wata daya da kwanaki." Nan da nan na soma
zufa, zuciyata na kwadayin ina ma mafarki ne? Cikin
tsananin kuka da kunan rai na ce, "Ya cuce ni. Mai
zance da Innarmu? Abun da Baba yake tsoro ya faru.
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un." Kuka na ya shigo da
su, ta mika mishi result ya duba sannan ya kalle ta, "To
yanzu doctor ya za'a yi tunda gaskiya ni da ita karatu
muke yi, bamu shirya taron Baby yanzun ba." Na dube
shi yana magana hankalinshi kwance kamar wanda ya
aikata abin arziki. Ta ce, "Baka shirya tarban Baby ba
mai ya kaiku aikata haka?" Ya ce, "Tsautsayi ne." Ta
ce, "A'a ku ji tsoron Allah, aure shine ya fi dacewa da
ku, karatun boko ba zai hanaku aure ba. Amma sai
kaga ana wasa da Sunnag kun zabi boko sama da raya
sunnar Manzo (S.A.W), to ku sani Manzon Tsira
(S.A.W) ya ce aure Sunnar shi ne, duk wanda ya ki
sunnarshi baya tare da shi. Kun fi yadda kuyi ZINA fiye
da aure." Ta nuna shi da biron hannunta, "Musamman
irinku 'ya'yan 'yan boko, Iyayenku sun rike wuta sai
kunyi karatu mai zurfi basu damu da halin da zaku
shiga ba kasancewarku balagaggu, burin su ku iya
turanci tare da kawo musu kyawawan sakamako
lokutan jarabawar ku. Ba su damu ku san addininku ba
bare kusan illar ZINA."munir yace to doctor, yanzu
menene mafita? Don matsala ne cikin nan don Allah a
cire shi tayi suru tana tunani. Bello yace in bazaki
iyaba muje wani asibiti doctor hindu tayi shuru tana
nazari, tace to zan tai makeku sai a lokacin naji sanyi
ya ratsa zuciya ta. Ta bani wasu kwayoyi wai kafin nan
da sati daya zai fita, suka ce nawa? Tace dubu goma
nan take suka biya. Sun saukeni makaranta sanan suka
wuce, da alkawarin zaya rinka kira yaji abinda ke tafiya.
Yau kwana tara shuru sai laulayin da nasoma gadan-
gadan, ga sheka amai nan ga zazzabi na kwasa na
koma wajen doctor hindu ana kai mata kati na tace a
turo ni duk da yarinyar da naga ta shiga bata fito ba,
itama yarinyar duk a firgice take, taci kuka ta gode
Allah nace sannu doctor. Tace yauwa ya jiki? Cikin
saurin baki nace da sauki amma fa har yanzu bai fita
ba. Ta mikye tare da diban wayoyin ta ce ku biyo ni.
Muka biyo ta cikin harabar asibitin muka nufi wani gida
kirar zamani dan madaidai ci. Ta umurce mu mu zauna
kan kujerum da ke kayatacen falon,ta shiga wani daki
daga cikin dakunan biyu dake cikin falon. Jim kadan ta
fito ta canja shigarta zuwa doguwar riga ta atanfa. Ta
shiga kicin yafito da doguwar gorar ruwa (swan) da
kofuna guda biyu. Ina takure cikin hijabi na, zazzabi ne
ya rufe ni ta tsiyaya ruwan ta miko min, sha ruwa nace
a a sanyi nake ji ta koma takawo min paracetamol na
sha. Ta zauna ta zuba mana ido, ta dubi dayar tace
asabe ko? Yarinyar tace eh, menene labarinki?
Yarinyar ta ce, Sunana Zainabu,amma an fi kirana da
Asabe.Mu 'yan asalin nan kano ne, a karamar hukumar
kunci can wani kauye ana ce masa kurje. Wata mata
mai suna Gambo tana zuwa kayaunkan garinmu tana
diban yara 'yan aiki, wata rana taxo gidanmu ta ce da
Babata su bada ni ana samun kudi sosai, wai can zan
samu kudin kayan daki. Sai na ce ni ba zani ba, nafi
son nan don ina talla kuma ina zuwa karatun allo. Sai
Babata ta ce to abar shi, don Babanmu in ya ji ba zai
yarda ba, ta ce can ma ana karatun Muhammadiyya,
kuma za su saki ga cima mai kyau za ki canza. Haka
dai ta zuga Babata hr ta yarda, sai da suka yi rigima da
Babana sannan ya yarda. Gidn Hjy Mairo aka kai ni, ba
wani aiki sosai kuma bata da tukara. Ba ta da Matsala
in kaga damuwarta to ran danta ya 6aci, don shi ne
dan ta kwallin tal. Yawancin aikin nawa duk nashi ne
don tana zuwa aiki shi ma yana zuwa makaranta,
amma ya fi ta zama gida.Ba mu cika shiri da Yasir ba,
don shi yana da fada. Watana 3,ranar wata Litinin ina
kicin, ya shigo wai in dafa masa Idomie, nan na bar
komi na shiga dafa masa, don Hjy ta ce kome nake yi
in yazo da nasa in bari in masa don a zauna lfy. Ba ta
so ta ga yana zagina, na ce to. Da na gama na nufi
dakinsa, na aje zan fita ya ce in dawo, cikin sauri na
dawo don ina matukar tsoronsa, kawai sai ya ce in cire
kayana. Na soma zare ido, ya ciro wuka da sauri na
cire ya kwantar dani ya aikata alfasha da ni, sannan ya
hana ni kuka. Ya kuma ce idan wani ya ji sai ya kashe
ni. Naja baki nayi shiru, duk uwar wuyar da na sha tun
daga nan muka daina fada, Yasir ya maida ni tamkar
matarsa. In Hjy bata nan sai ya kira ni dakinsa, akwai
lkcn ma da Hjyn taje Umra ta barmu tare da wata 'yar
uwarta don ta lura da mu, da kuma gidan,amma Yasir
cikin dare zai zo ya buga in kofa, dakinshi nake kwana.
Nan da nan nayi wani girma, kirjina ya cika. Daku abn
da ya gani zai sai min,wata rana na tashi ba lafiya,sai
amai nake shekawa,Hjy ta kira Likitansu tun kafin ya
gwada Ni ya ce yana zaton ina da ciki,ya ce amma bari
dai ya gwada. Gwajin Farko ya nuna ina da ciki, nan ta
shiga salati da sallallami, ta tsare ni wai in fada mata
wanda ya min, na ce Yasir ne.
Nan ta hau ni da duka wai na masa sharri, dan shekara
ashirin da biyar dinne yaya iya yi min ciki? Da ya dawo
ta tambaye shi da har ya musa sai yaga ta watso min
kayana, wai na tafi zan yi ma danta sharri, sai ya ce
mata shi ne,amma tsautsayi ne. Ga mamakina, bata yi
masa wani fada ba, sai dai ce masa tayi kada ya kara,
kuma Babanshi zai dawo. Ta kai ni wani asibitu aka
cire min shi ta dinga min fada wai ko ya kira ni kada
naje. A cewarta, wai bashi da laifi ni ce mai laifi. Sati
biyu ina jinya, Sannan na gyagije, ganin ta sa mana ido,
sai ya ce in dinga barin dakina a bude zai ringa zuwa.
Na ce Hjy ta ce mu daina. Ya sake zare min ido, dole
na bi yanda yake so, wai baya so Hjynshi ta sani, don
ta ce mishi in ya sake sai ta aura masa ni, shi yasa duk
ya tashi hankalinsa yanzun. Doctor ta ce, To shi baya
son ya aure ki ne? Asabe ta ce, tab ita ma nasan tana
tsorata shi ne, domin ba ta da burin yayi aure yanzun.
Burinta shi ne ya yi karatun boko mai zurfi,kuma ya
zama wani abu a kasar nan SANADIN BOKO." Na jinjina
kai, tuni zazza6ina ya sauka. Labarin Asabe ya ta6a ni,
kallo na dinga bn ta da shi, Yarinya ce ba zata wuce
Shekara sha uku zuwa sha hudu ba. Wanna ma ai child
abuse ne, ya kamata a hukunta su shi da Hajiyar shi.
Doctor ta katse min tunani da cewa Hafsat me ya faru
da ke kuma, menene labarinki?? Na zuba mata ido,
hawaye suna zubowa, ta ce fada min ina so ne in
taimake ku, na ce zaki cire min cikin? Ta ce Eh, zan
cire miki in har naji labarinka, kin cancanta a cire
miki.Ina nufin in ban da son ranki hakan ta faru ba. Na
share hawaye,sannan na ce da ita. "Sunana Hafsatu,
Mahaifina dan asalin jihar Borno ne, ya fito daga gida
tun zamanin yana saurayi, a kano ya yada zango, nan
yake 'yar sana"arshi.Sun hadu da Mahaifiyata a can
lkcn tazo gidn yarta a Na'ibawa. Babana Shi ne ta
tambaya ya yi mata kwantancan gidan Malam Ma'aru
me Almajirai mijin yarta kenan.Daga lkcn ya nuna yana
sonta, ta amince hr yaje Maliunfashi jihar Katsina,
unguwar Fayamasa. Ya samu kar6uwa cikin dangi, don
yana da nutsuwa da ilimin addini aka ce ya turo
magabatansa.Mahaifanshi sun rasu sai babban wansu
Babagana, shi ne ya zo suka hadu da wani uban
dakinsa. A nan kano suka zo, sune suka amsar masa
auran Innarmu.Ba su jima a kano ba ya soma zuwa
kaduna, ya fara sana'ar saida lemo da Ayaba,daga
bisani ya nemi gida a hayin rigasa ya dawo da
Innarmu,lkcn tayi haihuwar farko wato Yayana Ummar.
Gidanmu gidan haya ne, Mai girma gaske a layinmu kaf
ba gidan da ya kai namu yawa don gidan yawa ake ce
mana. Mata goma sha ne, kowace da 'ya'yanta wasu
hudu wasu shida,wasu goma sha. Babana ya sake auro
wata matar daga kano, itama nan gidan ya samu daki
kusa da na Innarmu., Babah tana da kirki da nutsuwa,
shi yasa duk yanda Innarmu taso suyi rigima bata
biyewa, dole itama ta saki suka zauna lfy. Yanzun
Babah 'ya'yanta 6, Innarmu 8. Ni ce 'ya ta 2, masu bina
3 duk maza ne, sannan mata. Innarmu gidan su 'yan
boko ne, ko na ce kowa yasan Katsinawa da boko. Don
haka tana da burin mu 'ya'yanta muyi boko, shi ko
Baba ba ya da burin mace ta wuce primary. A nashi
ra'ayin nayi saukar Alkur'ani mai girma ya min aure.
Tun muna kanana Innarmu ta kwadaita mana boko, don
haka ni da yayana mun taso muna son karatun
boko,Primary 5 Umar yake lkcn da ni ma aka sani.
Babanmu bai cika biya mana kudi Makarnta ba, don bai
cika samu ba.Amma in yana da shi yana ba mu,ganin
haka ne yasa Innarmu ta kama sana'a. Gyada take
soya mana ni da Yayana in lkcn dafaffiya ne kuma ta
dafa mana da wannan muke samun rufin asiri. Cikin
haka Yayana ya gama Primary aka kukata ya shiga
Junior. Kwanci tashi nima na gama primary, sai dai
lkcn ne Baba ya ce Bokona ya isa haka, izifina ishirin a
Islamiya ya ce da na sauke za a min aure. Innarmu ta
ce ina, yanzun kai ya waye ko ita tayi makarantar gaba
da primary balle 'yarta. Sun yi hatsaniya hr abokinsa
makocinmu Baba Garba, ya saka baki kan cewa Baba
yayi hakur ko aji 3 in yi wato karamar Sakandire. Baba
ya ce, shi kenan,amma fa ba ruwan shi, ko yana taka
kudi ba zaya ba ni ko na fensir ba. Abubuwa suka kara
yi wa Innarmu yawa, ga Yayana Umar kudin jarabawa
yasa makarantar tsaya. Sai dai karen mota ya koma
yana yi wa wani mu2m a layinmu,kasuwa-kasuwa.Inna
ta zaunar da ni ta ce Hafsatu,kin san yanda zamu yi?
Na ce A'a na me? Ta ce, na karatunki, kina so ko? Na
ce "Tab so kai ba ki ga su Saliman ajinmu na su suna
ta zuwa, ta ce to dagewa za ki yi zan dinga alala da
safe ki dan zaga. Sai kuma ki zo ki dauki gyada, na ce
Innarmu ni wlh Na gaji da talla,wata rana mu2m ya yi
ta yawo a ki sayar ta ce sakarya kin zaga tas za a
saye. Asusu zan yi riba ko nawa aka ci sai mu zuba
kafin gama zangon farko mun tara kudin da za ki shiga,
na ceto,gwangwanayen gyada muka fafe wasu tayi
alala.Nan da nan ya kare, Ta dafa min gyada na dauka
ta ce maza Hafsatu, Allah ya bada sa'a kin ji, kan lkcn
Ismaiyya ki saida. Na ce to, Ta ce bn da wasa fa, don
na san ki, na ce to.Wasa kam inadashi,kowa ya sani
har na gama primary duk report card dina ba wanda ba
a rubuta min na cika wasa ba, a haka kuma nake
karatuna.
a haka kuma nake karatuna haka kuma na dage da talla
na wata ranar litinin ina tafiya nice har baban titi na
tsallaka, sai ga wata yarinya tana tallan kwakumeti,
tace ke ina kike zuwa? Na ba ko ina yawon talla nake.
Tace zomuje (governmeet college) ana cinikin gyada in
yan makaranta suka tashi nace, to muje tafiya ce sosai
har gidan gwamna ta nuna min. Muna isa agajiye muka
zauna gin din bishiyoyi ga yan talla nan kala-kala har
da masu gyada babu abin da yafi mun dadi irin yanda
naga yara nata wasa saboda yan makaranta basu tashi
ba. Masu carafke masu yar gala gala nayi, wasu na
tayin ziro-ziro duwatsu na tsinta nima nashiga yin yar
carafke, batare da na huta ba koda dalibai suka taso
nan kowa yasaki wasa suka shiga saida kayansu, ni ko
ban damu ba na cigaba da wasa na sai da takowa ta
kare sanan aka shiga siyan nawa. Washe gari nacewa
innarmu a kara mai makon mudu hudu a dafa biyar.
Yau ma wasa na dora haka nan sai da ta kowa ta kare
don su suna zaune, a gaban kayan su niko ina can ina
wasa na. Zuwa yanzu na saba da dabar hanya zuwa
(government college) wata rana ina zaune kan duntsen
da na dasa a matsayin abin zama na, gaban tirena
hannuna zarene ina ta wasa dashi na hada injin nikan
barira inata yar waka ta. Sai naji magana kusa dani
ance ke gyadarki ba ta saida wa bace? Ba tare da na
dubeshi ba nace ta saidawa ce mana,ya ce, "Sa min
daya a leda sarkin wasa." Na ce, "Zaba." Ya ce, "Zabar
min." Sai lokacin na kalle shi na dan kara zare ido
saboda kyawun shi. Haka nan ba Uniform a jikin shi,
kenan ba dan Makaranta ba ne. Na mika mishi ya ciro
wani farin kyalle ya shinfida akan jijiyar bishiya ya
zauna ya soma cin gyadar. Ni kam kallonshi nike a
raina ina cewa, "Dama 'yan gayu suna cin gyada?" Ya
dube ni, "Ki yi wasanki mana kada ki sa na kware." Na
dauke idona daga bisani na tashi, na soma 'yar gala-
gala ta. Yana lura da yadda kowa ke tsaye kan kayansa
banda ni, da ya mi'ke zaya tafi ya ce, "To sarkin wasa
ga kudinki." Sabuwar naira biyar ya bani a mike, a
rayuwa ta babu abinda ke burgeni irin sabon kudi, na
ce, "Amma na gode, kalleta kar-kar bazan kashe ta ba."
Ya ce, "Mai zaki yi da ita?" Na ce, "Ajiyewa zanyi ba
zan sashi cikin asusu ba bare har na lankwasa ta."
Murmushi yayi sannan ya ce na bashi daya. Ba bashi
ya ci rabi ya bar saura, na ce, "Ji fa baka cinye ba." Ya
ce, "Na koshi." Da zai tafi ya kuma bani sabuwar naira
goma wai in bashi canji na ce, "Wai don Allah kai kuwa
a ina kake samun sababbin kudi?" Bai amsa ba yana ta
kallona. Na ciro tsohuwar biyar na mika mishi. Ya
girgiza kai, "Ba na amfani da Tsohon kudi." Na ce,
"Saboda mene?" Bai amsa ba ya ce, "Gobe zan amshi
gyada." Na ce, "Toh"Ku san kwana 2 ban ga mu2min
ba, sai ranar 3. Yau ma shigar shi ta 'yan gayu kamar
kullum. Ya amshi gyada zai tafi ya kuma bani sabuwar
10. Na ce a, ka manta ne kana bi na canji? Ya ce haka
ne, to rike wannan don ni in na ciro kudi bana maida
su. Na ce ko? Tab, amma dai sun maka yawa ne ko?
Ya dube ni ba alamar wasa, ya ce "Mu ne ai muke kera
su. Na zaro ido ina kallon shi, cikin matukar mmk
"Kana nufin ku ke buga kudi? Ya sake dubana, kwarai
kuwa, na Maida hankalina duk a gare shi. Ka ce kana
da su lodi? Ya saka hannu cikin aljihu shi ya ciro
sabababn dal 'yan naira ashirin da goma-goma na zaro
idanu. Tabbas yanzun na yarda na ce kai ko kaji
dadinka, ina ma ni ce. Ya ce da me za ki siya? Na ce
na farko zan biya kudin makarantana, kuma na dinga
sai mana kayan dadi da su nama da mota, su
mashin.Kai komai sai na sai mana. Ban lura ba, ashe
shi kam dariya na ba shi, ya ce to ai ni kin ga duk na
siya abubuwan da ki ka ce, na yarda kam, shi yasa
gaka nan dan gayu da kai, ka ta6a zuwa kasar waje?
Ya sake darawa, sannan ya ce eh, da yawa ma. Ya tafi
ina ta kallon shi. Sa'a da Zaituna wadanda muke tafiya
tare dasu, da na basu labarin dan gayun nan na ce
ashe sune suka buga kudi kin yarda suka yi. Suka ce to
in shi ne me zai kawo shi nan yana karyawa? Na ce shi
ne ya fadamuku karyawa yake yi? Suka ce min tun
yaushe suka san shi a nan Makarantar. Na ce ko dai
yana koyarwa ni na yarda su ke buga kudi, Ga sabbin
kudi nan dami a gunsa, Lura da su Sa'a suka yu cewa
ba zan yarda da su ba sai suka bar ni. Sau dai suka ce
min ni wawiya ce, sai ka ce bn yi zaman aji ba, sunan
na gama aji 6 bn san komai ba, na ce naji din. Su
Innarmu a da Baba na kuke ina ba su labarin dan gayu
mai buga kudi, amma wai sai suka ce zolayata yake yi,
nayi duk wani kokari na wai don su yarda da ni cewa
gaske ne,amma sun ki. Sai dai na dauki alwashin zan
masa tambayoyin da zai gamsar da su.
washegari jumma‘a ba mu cika jimawa ba, saboda ana
sallah juma‘a a masallacin da ke kallon makarantar
amma kin bin su Sa‘a nayi na fake da cewa sai gyada
ta ta kare. In tashi yan makaranta tuni sun watse ina
ina zaune gaban gyada yar ragowa ce ma, sai kalke
kakle nake. Can na hangoshi zai shiga makarantar, ya
sanye da wani ubansun yadi fari kar hatta takalminshi
da hular kanshi. Duk da yau ce na soma ganin shi da
manyan kaya ban kasa ganeshi ba. Da gudu na bishi
ina cewa tsaya tsaya ban san sunan shi ba bare na
kira. Shiko bai san dashi nake ba a haka mukayi nisa
cikin makaran tar sai dai wani ya lura shi nake bi sai
ya tai maka ya tsai da mun shi. Na lura yaji mama kin
ganina yace, sarkin wasa ina zaki haka? Na tsaya ina
haki saboda gudun da nasha yace sannu na ce yauwa,
dama kai nake ta jira zan tam bayeka ne. Yace na me?
Nace wai dan Allah da takarda kuke yin kudi? Yayi
dariya har hakoranshi farare suka fito yace eh, da
takarda ne to in na baka zaka iya yi min saboda
mutane sun kiyarda ne dani in nace naga masu buga
kudi sai ace karya ne zolayata kake yi. Yace zanyi
maki in kina so nace innaso kai, to da wace irin takarda
kuke yi? Yace ta rubutu nace gobe zan duba jaka ta da
in dauko. Yace ba ayi fa da tsohon littafi ko kina son
tsohon kudi ne? Nace a a taf na fison sabo yace to
shike nan ki kawo sabo nawa za abuga maki yawan
kudin? Nace zaka iya min dubu malala gashin tunkiya?
Ga mamaki na sai naga yana dariya har da rike ciki
nima na soma dariyar ya numfasa ya ce,in ban da abin
ki sarkin wasa wane ne ya san yawan malala gashin
tinkiya, Na ce to ko dai nawa ne ina so yanda dai ishe
ni na gama karatuna. Ya ce,wai dama nan kin yi
karatu? Na dube shi, ba na fada maka ba cewa na
gama primary? ya ce ban ji ba lokacin da ki ka
fada,yanzun JS1 za ki shiga? "Eh tallar da nake ai kudin
rijista muke nema, kaga in ka bugo min kudin na daina
talla, ina gama secondry har ta gaba in je in fara aiki.
Ya ce "Wane aiki ki ke son yi,? Ina nufin me ki ke son
ki zama? na daga kaina sama ina nazarin ya ma ake ce
musu? Ya ce ba ki san me ki ke so ki zama ba? Na ce,
"Ya ma mutanen da ke yin labarai a Talabijin ko
Rediyo? Ya ce, " Media ki ke so? na ce yawwa, haka
zan zama 'yar media,yayi murmushi, to ni zan wuce, ina
kayanki? Sai lokacn na tuna da tirena da kudina cikin
ledar gwangwani, na ce to sai gobe. Na tafi ina
waiwayanshi, ina cewa kai,wannan mu2min dan gayu
ne,ga kamshin turare yana yi. Ranar Litinin tsawo naga
ta min,yau kam d murna na iso,na nutsu ban yi wasa
ba,saboda wata zuciyar da ke ce min in ya ki zuwa fa,
ga shi na zo da sabon littafina, ba karamin damuwa
nayi ba da na ga lkcn tafiyarmu yayi ban gan shi ba.
Ina kulle gwangwanaye sai gashi, na ce hr na cire rai,
ya ce ai zan zo, na ciro littafi na ba shi, tare da cewa
wannan takardar ta isa? Ya ce eh, na ce na gode, na
mika mishi gyada tare da cewa na rage mishi ne. Ya ce
ya gode ya tafi. kai, kuruci dangin hauka, nifa
tsakanina da Allah na yarda suke buga kudi. Daga
ranar ban kuma ganin shi ba, Kusan sati 2 hr na soma
tunanin ya gudune da kudina kun ji shirme. Wata ranar
Jumma'a ranar za a yi wa dalibai hutu hr cikin
Makaranta muka shiga muna ta ciniki,mun saida mun
fito sai na hango shi tsaye gurin zaman mu. Da sauri
na isa gurin shi, me bugakudi......
Zaharaddeen shomar
whatsapp 08168575100
Sanadin Boko 1-04
Posted by ANaM Dorayi on 09:56 AM, 10-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
@* NA
Maryam Abdullahi K/Mashi
"Da sauri na isa gurin shi, me buga kudi ina ka tafi na
daina ganinka? Ya ce aikin kudin ki ne ya 6oye ni, na ce
Allahu! Har ina cewa ka gudu. Ya yi dry, na gudu da
kudin ki ki ke zato Na ce eh, nima ina dry. Ya ce kai kina
da bn dry, to ga kudinki,amma muje gidan ku na bawa
iyayenki kada wani ya bi ki ya kwace. Cikin murna na ce
to daga nan ma in sun gan ka sun fi yarda. Na kama
hanya a kafa ya ce ga mota can zo muje, in kin san
hanya direbn mu sai ya kai mu, ba tare da wata shakka
ba na ce to. Sam na manta da su Sa'a, sai da zamu
shiga motar naji muryarsu,suna cewa ke Hafsatu ki ka
sani ko dan yankan kai ne? Na dube shi, shima ya ji
amma sai yayi tamkar bai ji ba, na ce ba wani dan
yankan kai na shiga motar da dan tirena, shima ya shiga
ya ce kawarki fa,shawara suka baki nace tame? Yace
kin san ni ko dan yankan kai ne? Duk da gabana ya fadi
amma sai na dake nace, bakayi kama dasu ba yace suna
da kama ne? Nace oho amma kai bashi bane yace, dama
sunanki hafsatu? Nace eh abakin su sa‘a kaji ko da suka
kirani dazu ko? Yace eh nace yan bakin ciki ne, dan fa
nace masu kana buga kudi sai suka ce mun karya ne, kai
malamin makaran tane. Yace gaske ne ni malamin
makaranta ne, amma daga yau na gama nace, duk da
kudin da kuke bugawa basu ishe ka ba sai kayi koyarwa?
Yayi dariya yace bautar kasa aka turoni daga jahar mu.
Nace bautar kasa kuma? Yace kema watarana zakiyi in
dai kikayi karatun da kike fadi, gwamnati zakiyi wa aiki
na wata tara ko shekara.
Ban gane nufinshi ba amma nace Allah yasa naga
lokacin.
Da gudu na shiga cikin gidan mu ina cewa inna fito kiga
mai buga kudi ya bugo min inna ta saka hijab ta fito tana
cewa ni ban gane wanan shirmen naki ba, ina mai buga
kudin? Wannan yarinya da wautar tsiya kike inna tayi
turus lokacin da tayi arba da rantsatsiyar motar tace
hafsatu aina kika jajibo wadan nan...? Cak! Maganar ta
tsaya lokacin da saurayin ya bude motar ya fito
kyawunshi yasa inna tunain ko aljani na janyo, ta soma
karanta (ayatul kursiyu) zata juya gida na rike mata
hannu. Inna dan Allah ki tsaya mana zo muje gurin su
tace a a hafsatu muje ciki bana tsamanin wadannan
bil‘adama ne nifa nasan banda aljan ke ina kika isa kiga
mai buga kudi, sai dai in jabun kudi. Saurayin yatako har
gaban inna ya dan rusuna ya gaishe ta, ta amsa tana
dan dari dari, nace to wanan ce inna ta sai ka bata
kudina inna tayi ta maza tace samari daga ina? Ni fa ban
fahimci surkulen da yarinyar nan take yi min ba? Yayi
mur mushi ya dube ni jeki kawo min ruwa nasha, da gudu
nayi ciki ban saurari inna ba da takecewa in dibi na baba
yafi sanyi
ina tafiya ya dubi inna yace mama zolayarta nake yi, ni
dan bautar kasa ne an turo ni daga Adamawa state, ina
koyarwa a makaranantar da take zuwa talla. Yawan
wasanta ke burgeni har na shiga sabagarta, sai kuma na
fiskanci cewa tana son karatu amma rashin hali ya hana
hakan. Dan ta fada mun tana talla ne dan kawai ta tara
kudin makaranta. To ni nazo ne in ba damuwa zan
taimaka mata don ni daga yau in sha Allahu na bar
kaduna kenan, don na gama abin da ya kawo ni, dai dai
nan na taho da ruwa na ce masa gashi. Inna tace mika
mashi yace a a dama basha zanyi ba bakiga na sha ruwa
a mota ba? Nace eh yace to maida. Yaci gaba da cewa
dama nawa ne kudin nata? Tace ni ban tambayi nata ba
amma lokacin na wanta inaga dubu uku muka kashe? Ina
ga ba zai wuce hakan ba. Ya ciro yan daurin nera goma
gama guda uku sababbi fil ya mika mata ga wanan
mama dan Allah ku biya mata kudin makaranta, ku cika
burinta har tazama abin alfahari nan gaba. Allah ne kadai
ya san al‘ummar da zasu anfaneta. Innarmu jiki yana bari
ta amshi kudi tana ta zubo mashi godiya ma, sai daka
tsale nake tamkar yarinya karama, ina cewa shi kenan na
huta talla. Innarmu ta harareni tana cewa to kiyi mashi
godiya mana, nace na gode yayi murmushi ya tafi yana
daga mun hannu nima haka. Sai dai kash nayi mantuwa
ban tambayi sunan shi ba, a lokacin ban damu in san
sunan shi ba muka nufi cikin gida da murna innarmu bata
da rufi, don haka a tsakar gida ta fada musu cewa wani
bawan Allah ya taimaka min da kudin makaranta. Wasu
suka taya mu murna ciki harda babarmu, wasu kuwa sun
nuna bakin cikinsu a fili don Ade ina bayi naji tana cewa,
maman abba yau kinji matar nan mu zata rainamawa
hankali ta dai tura yarinyar ta maula. Maman abba tace
ai shegen son kudi irin na maman hafsatu ya isa, ace
mata sai rashin godiya Allah duk fa kokarin mujinta ta
raina. Daga can asabe ta sako baki shi wannan mujin
nata ai tuni ta gama dashi katsinawa kuma da shegen
asiri? Dubi fa fada irin na mutumin nan sai da tasha
karfin shi ga kishiya kuma sai yan da akayi da ita Ade ta
ce, ayi dai mu gani, kina nan yarinyar zata janyo mata
abin kunya, Maman Abba ta ce ta dage sai yarinya tayi
boko, za su ga boko ai. Na fito cikin takaici ina kallon su,
sai nan da nan suka canza mgn. Asabe ce suna ta zagin
ki,wai kina asiri ke Bakatsina,wai zan ja miki abin kunya.
Inna tana da fada, balle in an ta6o ta, ta fita da sauri
Yayana Umar ya hau ni da fada,wai don ubana ni
mahaukaciya ce da zan fada mata, na ce ka ji gulmar da
suke yi ne? Hayaniyarsu ce ta fito da mu, Umar ya je
yana cewa, Inna ta bari ta dawo daki, nan dai haka gidan
kan rikice wani lkcn. Musamman in ana fada kan yara, ko
gulma. Innarmu tana da fada kowa a gidan yana shakkar
ta6o ta. Bayan komai ya lafa, muna daki ta ce "Hafsatu
kin dai ji da kunanki, ina so ki baiwa mara da kunya, ki
kare min mutuncinki, kiyi karatunki ki zama abn sha'awa
da kwatance na ce to Inna. Cikin kwazo na soma
karatuna, kudin dan gayu mai buha kudi ya bugo min sun
taimaka min kwarai. Inna tayi musu kyakykyawan
adani,sun ishe ni har zuwa lkcn da na gama JS 3, lkcn
shekaruna 14 girma ya soma zuwa min 'yan alamu sun
bayyana. Na kan ji mutane suna cewa, wai ban cika kyau
a fuska ba, sai dai jiki. Yawan fadin ina da diri shi ne ya
sani jin cewa ni mace ce musamman in nayi kwalliya.
Wata safiyar Jumma' naje fitsari sai naga jini, cikin
fargaba nazo har da hawaye nake fada wa Inna. Ta ce,
Hafsatu girma ne ya kama ki yau nawa ga watan bature?
Na ce 7. Ta ce to duk 7 ga wata za ki ga wannan jinin.
Ta iya yiwuwa yazo kafin 7, ko bayan 7, amma duk wata
dai za ki gan shi. In kuma ba ki gan shi ba hakan na
nufin kina da ciki. "Na zaro ido ta ce ai ba a samun ciki
haka sai in kin kasance me wasan banza da MazaNa
sauke ajiyan zuciya,don nasan bana yi. Na ce ni dama
ba ruwana da maza, ta ce na sani, amma ki kara.sannan
ki kara sa tsoron Allahn ki cikin zcyrki. Daga yau din nan
an bude miki fayil dinki, duk aikin alkairi ki ko akasin
haka za a rubuta miki, don haka sai ki kula, ki kuma san
me ki ke ciki. Tun daga wannan lkcn nasa ma raina
tsoron maza, nake kuma duba duk wani aiki da zan yi
zunubi zai ja min ko lada.
Marubuciyar tace'Yan uwa mata zan dan mana wani tuni
nan gurin, mu nutsur da 'ya'yanmu muyi musu bayani
mai kyau tare da nutsa tsoron Allah cikn zukatansu, lkcn
da suka samy kan su a irin wannan yanayin na
balaga.....Allah yayimana jagora
Ba zan manta da Jumma'ar ba, misalin 4 da mintina na
yamma gari yayi sanyi La'asar, nayi kwalliyata da riga
da wandon pakistan da Inna ta sai min a gurin wata
mai gwanjo. Kore ne kalar lemun tsami da gyalanshi,
Sakina kanwata yarinyar Baba kishiyar Innarmu ta ce "
Yaya Hafsatu zan biki." Na ce, zo muje gidan kanwar
Innarmu zan je Hayin Malam Bello na kai mata kudin
dashin sabulu da suke yi. Ko can gidan matan gidan
suna ta yaba yanda kayan suka yi min kyau.Dai-dai kan
layin Biliya wasu matasan samari suna tsaye jikin
mashin, kallo daya na musu na dauke kaina ban kuma
kawo komai a raina game da su ba. Sai naji takun
tafiya, ana cewa 'yanmata ji mana,maza sun sha yi min
haka bana tsayawa, don Innarmu ta fada min karatu
basa haduwa da soyayya, kada na sake na kula kowa.
Ya zagayo ta gabana Beby saurare ni mana. Na' kalli
fuskarshi,sai zcyta ta buga, ina son mu2m mai kyau,
daga ganin shi dan gidan 'yan gayu ne. Na harde
hannuwana a kirjina, ya sake dubana daga sama kuwa
gsa kasa, "Wow! Ya sunanki?" na ce "Hafsatu." Ya ce
"Nice name, Hafsy ina ne gidanku?" Kawai sai na samu
kaina da yi masa kwantance, can kasa muke Abuja
Road, layi na shida marar kwalta, kana zuwa layin ka
ce ina ne gidan yawa za a nuna maka. Ya dan yi shiru
don ya fahamice a geto take amma sai yace zan zo
anjima ko gobe zan samu ganinki? Nace eh yace to sai
kin ganni na tafi ina wai wayanshi sakina tace yaya
hafsat mijinki ne? Cikin yar dariya nace eh mijinane
wasa ne ya ruda ni na kasa sukuni, tare da boyiwa
innarmu don kada ta hanani fita, sai dai har tara banji
ance ana kiran hafsa ba,har fita nayi gurin bakin titi ina
tunanin wai ko yazo bai gane layin ba na dawo daf da
zan shiga gida na ganshi tsaye kofar gidan mu. Wani
sanyi naji acikin zuciyata, sai na soma tunanin zan jene
na ce mashi gani ko ko ce mashi zanyi ni kake nema?
Sai na yanke shawarar na bi ta gabanshi, har na daga
labulen buhun da yake kofar gidadanmu zan shiga, sai
naji yace hafsy sai na tsaya tare da sauke a jiyar
zuciya, sannan na wai wayo na tako cikin irin tafiyar da
ban taba sanin na iyata ba. Duk da yake dare ne a kwai
kwan lantarki a kofar gidan, yace nafi minti 5 ina jiranki
nace ina yini? Yace lfy da farko dai sunana munnir jafar
dalibi ne a (A B U) zariya ina shekara ta 2. Sanan
muna zaune ne a nan makarfi road son munnir ya kara
shiga ta, don a rayuwa ta inaso in auri miji dan boko
nace ni kuma na gama js3, yace me ya hanaki cigaba?
yanayin garin ne. Haka muka ta fira sam bansan dare
yayi ba har 10 ta gota ba sai da naji karan raidiyon
baban mu ya nufo gida. Ya tsaya tare da cewa wacece
nan? Ke hafsatu me kikeyi haryanzu? Na dubi munir
nace ga baba na. Ya cire hular kansa hana sallah yace
ina yini baba? Ya dubeshi lfy lau zo ki shige muje, nace
to sai anjuma yace zan zo gobe nace to. Tun kafin
mushiga daki baba yake min fada tare da tambayata
wanene wannan yaron ya dame kugu? Nace dazum ne
muka hadu dashi. Hayaniyar shi ne ta tashi inna daga
dan baccin da ta soma, tana tam bayarshi lfy malam
kake fada da tsohon daran? Yace amma dai ke
sakaryar uwace, 10 ta wuce yarinyarki tana can tana
zance da wani kato ke kuma kin hamgame baki kina
bacci Inna tace hafstu na can tayi baci tuni dakin
babarsu, ba ita kagani ba ita da bata fita zance ma
yace to ga tanan ma bare ki karyata ni. Inna tace hafsa
zance kika fita? Ya mukayi da ke? Baba yace ni dai
tashi ya turo mun iyayensa dama ni burina in aurar da
ita. Inma shi bayi zaiyi ba akwai mutane da dama sun
min magana. Inna tace je ki kwanta itama ta maida kai
ta kwanta alamun zancen baba bai shigeta ba. Da safe
ta tsareni da son jin wajen wa na fita? Nace inna wlh
jiya ne fa da kika aikeni ya ganni shine yazo. Tace
amma nace maki ki fita hanyar samari ko? Kin san
babanki matsawar zaki rinka tsayawa zance kina son
karatun nan zaki barshi ko nace inna naga shi wannan
yana son karatun, don su gidansu yan boko ne. Maman
shi da baban shi duka aikin gwamnati sukeyi yace min
jami‘a yake yi (A B U) zariya tace to ni dai banaso
kurinka tsayawa nace yama ce zai bani kudi nacigaba
da karatu na. Inna tace to indai ko haka ne sai dai
kitafi makarantar kwana, saboda kin san babanku sarai.
Koda munnir yazo washegari, haka na zauna na fada
mashi komai dangane da ma haifina game da kin boko.
Yace taf kice cutarki zaiyi? Tun kina karama zai
kasheki da aure ai gaskiyar innarki ne kada ki yarda.
Nace kudine matsalar mu sai dai in shiga ta kwana
yace haka ne, yace zan baki kudi bari dad dinmu zai
bani kudi in yadawo tafiya. Nayi ta masa godiya yace a
a shidai abinda zanyi mishi kada in saurari kowa kuma
na saki jikina dashi, nace kada yaji komai cikin sati 1
na gama yarda munir na sona, nima kara sonsa nake
duk zuwa yakan zo min da wani abu, turare ko dan
zobe ko dan wani abun kwalama. Bana manta ranar
lahadin da yazo min sallama zai koma makaranta ya
kuma bani kudi naira dubu 20 har kuka nayi mashi dan
bana so rabuwa dashi. Ranar shida abokin sa sukazo
wai shi faisal, kawai sai naji munnir ya rumgume ni,
wani abu naji tun daga tafin kafata har tsakiyar
kaina,shiko sai cewa yake inyi shuru in daina kuka
hannun shi kuma na zaga sassan jiki na, fadan inna ya
fado min cikin rai inda take cewa. In kula da kaina
wasan banza da namiji zai iya sawa in sami ciki, nayi
sauri na janye jiki na daga gareshi, yasa hannu yana
share min hawaye muka yi ban kwana na shiga gida.
Suna tafiya faisal yace munir dagaske kana son
yarinyar an? Munir yace da dai nazo na dan kwashi rabo
nane, sai kuma na gane yariyar ba yar hannu bace.
Sannan kuma nasamu kaina da sonta na gaske faisal
yace ka dai san dadinka ba zai barka ka auri yar geto
ba ko? Yace kai nif zan zaba da kaina ba zan yarda ace
min naje ga yar wani ba. Nikam ina shiga gida muka
soma murna da inna, nan muka shiga tsara yanda
zamuyi wa baba bayanin munir. Washegari inajin inna
tana cewa baba wai kananta da yayansu sunce ta kaini
zasu nemmar min makarantar kwana. Baba yace a a
shifa bai yarda ba, tace yayi hakuri kwana nawane zan
gama? Baba yace nifa ba kin karatun nake ba, nafiso
tayishi a can dakinta inaso kisani har in yarinya ta
soma tsayawa da saurayi mafi kyawu shine ayi mata
aure. Inna tace za ayimata malam, wannan yaro da ka
ganta dashi shene yake son auranta na lura itama tana
sonshi yace to ba sai ya turo magabatan shi ba muyi
zancen manya! Inna tace yo shima ai karatun yake sai
ya gama itama ta gama kafin nan. Shuru yayi bai sake
tankawa ba shurun ba yana nufin ya yarda bane,
shurunsa yana nufin mukarata can shi ba ruwansa.
Kwana 2 tsakani muka shirya ni da inna muka nufi
manunfashi kananta kawu sha‘iabu da kawu bashir
harda wanta kawu kabiru sun sunji dadi sun kuma tsaya
har saida nasamu shiga ss1. Haka baba ya hakura ya
zuba muna ido, na cigaba da karatu cikin nasara da
kwazo, yan gidanmu kam da makota sai gulma da
tsegumi, ba mu damu ba. Fatan inna shine inzama abin
kwatance nan gaba.
A duk lokacin da nazo hutu munnir nazuwa, haka duk
lokacin ziyarar dalibai in yana da sarari yakan zo.
Hidimar karatuna shi yake yinta haka nan duk wani
kaya na yan mata shi ne yake siyan min, wanan shine
yasa na kara sake wa dashi. Matsalata dashi son taba
jiki na, kawai lokacin da wani hawaye yayi min wai in
bishi muje dakin wani abokin shi, niko nace a a muji
tsoron Allah ba don son da nake yiwa munnir ba a tuni
na hakura dashi. Cikin haka na gama karatuna na
secondary. Na dubi likitar idanuna suna zubar da
hawaye nace, anty ko lokacin da na gama karatu na
baba ko gai suwa nayi baya amsawa, kannena yaran
kishiyar mama na guda 2 ya musu aure. Sannan
karatuna kafin na tahoshi sai da ta kai yace in har wani
abu ya biyo baya abakin auran innata, sannan in nemi
uba..... Kuka ya kwace min mai karfi, ina fadin na shiga
ukuna zan kashe auran iyaye da kaina. Munir ya cuceni
fyade yayi min anty ki taimaka ki cere cikin nan. Yan
gidanmu da yan unguwarmu duk dariya zasuyi mana.
Kalo kawai likitar keyi cikin tausayi har nayi kukana mai
isata na gama ba wanda ya bani hakuri. Daga ita har
asabe tace to, ke hafsat ki koma makaranta gobe kizo,
keko asabe ki kwana nan nace anty don Allah nima zan
kwana nan din, ko naje makarantar ba zan iya komai
ba, tace shikenan. Ta mike sannan ta nuna mana wani
daki, ku shiga nan kuyi sallah da komai a ciki. Ba tare
da ta jira amsa ba ta nufi dakin ta, kaiwa da kawowa
kurum take yi. Ta ina zata bullowa wayanan yara? Sam
bazata cire cikin ba, bazata kuma bari suje su cire su
zubar ba. Ta lura Asabe tafi saukin kai don haka da ita
zata fara. Yanda naga rana haka na ga dare, alwaula
kawai nayi na yi nafila. Daga bisani na koma istigifari,
washegari bayan ta lalabemu mun karya, sai ta bamu
wasu magun guna tace kada in damu in koma
makaranta insha, suna da karfi na sati 3 ne, ta tabata
cikin zai fita nayita godiya na komo. Sai da daktar
hindu ta sami shugabar kungiyar kare hakkin bil adama.
Tayi mata bayanin komai game da halin da asabe ke
ciki, Shugabar Hjy Adama ta ce, to za su samu Hjyr
Yasir su fara neman sulhu, in ta ki kuma to za a maka
Yasir a kotu. Doctor Hindu taji dadin haka, don haka ta
tambayi Asabe yaushe aka fi samun Hjy Mairo a gida?
Asabe ta ce Lahadi da rana, sauran ranakun sai dare
ake samunta. Sun same ta cikin Kasaitaccen falonta
tana shan kayan Marmari, suka sanar da ita dalilin
zuwansu. Ta ce, sam ita dai ba danta ba, ai ta ja mata
kunne, nan suka nuna mata cewa zata amsa kira a kotu
gobe Litinin. Yasir na dawowa ta hau shi da fada, ya ce
tayi hakuri sharrin shaidan ne, ta daka mishi tsawa ta
ce, yi min shiru,wawa kawai. Ta tausasa murya a bin
da nake so da kai, za su shigar da mu kara, saura in
mun je ka saki baki ka nuna kai ne, ina so ka bata rai
ka hade fuska ka nuna sam ba ka sam ba ka san
zancen ba. Ni kuma zan tsaya maka, Babanka zai tsaya
maka, domin duk Alkalin garin nan ba wanda zai ketare
bukata mahaifinka. Yasir cikin murna ya ce, "To Hjyta.
A daran ranar ta kira mahaifin Yasir ta shaida mishi
abn da ya faru, wai me aikinta tayo ciki tazo ta ce
Yasir ne, yanzun haka kungiyar kare hakkin dan adam
ta shigo cikin lamarin sun ce za su shigar da kara,Ni
kuma na ce su shigar, ya ce amma ba ki da hankali,
kina fa da masaniyar ina da burin tsayawa takara a
siyasa mai zuwa, ko kin manta? Kin san cewa abokan
gaba za su iya fakewa da wannan su ci zarafina har
suyi nasarar kada ni? Ta ce to yanzun yaya za'ayi? Ya
ce bani Yasir din a waya, ko ba ya kusa? ta ce ba ya
kusa, ka kira layinsa. Yasir ya daga kiran wayar
Mahaifinsa, ko gaisawa ba su yi ba ya jeho masa
tambaya, gaya min gaskiya kai ne kayi cikin? Yayi shiru,
fada min na ce kai ne ka min shiru? Uban ya fada cikin
daga murya. Yasir ya ce "Dad ba zan kara ba,
Mahaifina ya ce, Ok kai ne kenan? Ya ce Tsautsayi ne.
Alhjn yayi shiru yana nazarin abn yi. Can yaja tsaki, in
ka kuma ranka zai 6aci fiye da zatonka. Abn da zan
maka sha mmki, kila ma kayi zaton ko ba ni ne na haife
ka ba. Ya ci gaba da fada. In ma ba iskanci ba duk
nawa ka ke 25 years amma ka iya jarabar mata? Yasir
ya dinga ba wa Mahaifin shi hakuri, Alhjn ya ce shi
kenan, ya kira Hjy Mairo ya ce, kada su shiga kotu, su
nemi sulhu duk yanda aka yi su fada mishi. Washegari
da kanta taje ofishin shugabar kungiyar don neman
sulhu. An kira Dakta Hindu sun zo tare da Asabe,
sharadin 2 suka gindaya wa Hjy Mairo, aka c ta za6i
daya.Na farko ko dai dan nata ya auri yarinyar bayan ta
haihu, na 2 kuma in ba zai aure ta ba, to zai dauki
nauyin cikin tun daga yanzu hr zuwa lkcn da za a haife
shi a yaye shi. Daga bisani su dauke shi. Hjy Mairo ta
nemi saukin Asabe ta rike danta za su ci gaba da mishi
komai,amma shugaba ta ce a'a ba za su yarda ba,
domin Asabe in ta samu miji aure zata yi. Ba zai yiwu
ta tafi da dan wani gidn wani ba. Nan ta take ta kira
mijinta ta mishi bayanin komai, ya ce su dauki za6i na
biyun in yaso zasu yi shawara in ya dawo. Ta ce to.
Nan dai aka yi dogayen rubuce-rubuce, kowa yasa
hannu Daga nan ta tafi........
Zaharaddeen SHOMAR
WHAT'S APP 08168575100
SANADIN BOKO 1-5
Posted by ANaM Dorayi on 11:57 AM, 12-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Nan dai aka yi dogayen rubuce-rubuce, kowa yasa hannu
Daga nan ta tafi. Likita ta dubi shugaba ta ce, " Amma
ko da Asaben zata ba su dan su sai an sake zama, don
kada suje su halaka shi, kin san mutane ba imani.
Shugaba ta ce, wannan ka'ida ne, yanzun ki dauki
yarinyar nan ki koma da ita gidanku,gobe zamu je mu
samu iyayenta. "Doctor ta ce, Insha Allahu." Washigare
suka nufi kauyen kurje, iyayen Asabe sunyi murna da
zuwanta, amma da suka ji dalilin zuwan nan suka soma
kuka tare da yiwa Asabe Allah ya isa. Asabe na ta kuka,
Doctor suka yi ta bai wa iyayen baki tana rokon su yafe
ma Asabe. Da kyar suka shawo kan su, sannan suka yi
musu bayanin komai game da yanda suka yi da Yasir.
Mamanta ta ce, to ni dai ba za ta zauna min a nan va,
kauyen nan suyi ta zagina suna yada ni 'yata tayo ciki.
Ta sake rushewa da kuka, Likita Hinda ta ce zan tafi da
ita in zauna da ita hr ta haihu, in ta yaye sun dauki
dansu sai ta samu miji tayi aurenta, ko a nan ne.
Maman Asabe tana ta gdy, shi ko Babn tunda yayi waje
hr suka tafi bai dawo ba, suka dauko hanya bayan sun ba
uwar Asabe sha tara ta arziki.
***** ***** *****
Sati 3 daidai babu alamun cewa cikin jikina zai zube,duk
da cewa kusan kullum sai na je gun Likitar, ita kuma sai
tayi ta kwantar min da hnkl, wai in jira sati 3n su
cika,don ba za ta iya bani wani magani ba tunda aikin
wannan bai kare ba. Sam lkcn bn san yaya Asabe take
ciki ba, don nima ina cikin nawa tashin hankalin, gara ma
Asabe. Bana iya cin abnci,yunwar ma ba jin ta nake
ba,karatu kuma ina mantawa cewar shi na zo yi, don ko
na shiga aji ba na fahimtar komai, ga laulayi mai tsanani.
Munir kuma bai kuma zuwa ba,wayar ma sau 2 ya kira ni,
cikin sati 3 da likita ta bani yau kam ko sisin mashin bani
da shi, a kafa na sabi hanyar zuwa gidan Doctor. Asabe
tare da me yiwa Likita aiki wata gyatuma ana kiranta
Yalwa, su na samu. Asabe ta ce min Likita tana cikin
asibiti zama nayi don jiranta. Sai uku da rabi muna sallar
La'asar ta shigo, da fara'ar ta tare ni tana cewa? na dai
san bukata ta biya tunda ban gan ki ofishina ba. Kamar
ko yaushe,sai hawaye suka soma zuraro min, na ce wlh
Likita ya ki fita, ni dai a kwakule min shi. Ganin tashin
hankalin da na shiga, sai ta lallashe ni da cewa, nayi
hakuri bari ta dan huta. Na koma na zauna ina
kuka,wanda ya zama abn yina koda yaushe, tun da
Asabe ta bani lbrn yanda aka kwashe da tata rigima
hankalina ya kara tashi. Addu'ata Allah yasa nima kada
Likitar ta ce haka za a yi, domin zancen cikin ne sam
bana kaunar Innarmu taji bare Babana. Sai shida saura
ta fito, na dora sabon kuka Nan ta hau ni da fada,wai in
tashi ni tafi kukana ya min magani. Na share hawayena,
tare da bata hakuri,ta ce "Hafsatu! Ina son ki bani aron
hankalinki, ki saurare ni, na ce to. Ta ci gaba da magana.
Cikin nan naki ba zaya fita ba, domin na baki duk wani
magani mai karfi,amma a banza. In ko ki ka ce a
kwakule shi akwai yiwuwar ki rasa ranki. Da sauri na ce
gwara na mutu zan fi son akai gawata ga iyayena fiye a
kai ni gaban su da ciki. Ta ce, To naji amma kin shirya
abn da za ki fada wa Mahalccinki? Kin mutu gurin kisan
kai ko in ce ma kin kashe kanki? Kin fi son kunyar lahira
fiye da ta duniya? kada ki manta, kin ce fyade ya miki
ko? Na daga kai cikin kuka, ta ce to ki dauki wannan abn
a matsayin kaddara. Kada ki manta, Ubangiji ya kan
jarabci bayinsa don ya gwada Imaninsu, ke me zai hana
ki rungumi kaddara? Allah ba ya dora ma wata rai abn da
ba zata iya ba, Zufa ta rufe ni, na ce Likita ba za ki gane
ba ne.Innata da Babana auran zai mutu SANADIN
BOKONA. Alhakin Babana ne kash! Hakika da na san
haka zata faru gare ni da na yarda Babana ya aurar dani,
in yaso sai in ci gaba da karatun acan gidan mijina.
Likita ta ce, Yanzun dai shawar da zan baki ita ce, kije ki
samu shi saurayin ki tunda yana sonki, ku sulhunta, in
kin haihu a daura muku aure. In kuma kina son sako
hukuma kamar na Asabe to in sako, za su tsaya miki a
kwatar miki 'yanci. In ta kama hr kotu kuma ko su waye
iyayenshi. Na ce A'a zan fi son in same shi muyi magana
don bana son asirina ya tonu a unguwarmu. Likita ta ce,
yauwa, in kun sasanta ni kuma zan fahimtar da iyayenki,
na rike kai, Boko! Boko!! Na jajirce sai nayi boko,yanzun
kuma gashi tun ban je ko ina ba bokon na tsane ta.
Likita ta ce, "Hafsaty duk wanda ya dauki boko sama da
aure a karshe sai yayi nadama, saboda halin da ki ka
shiga ina son ki kwana a gidannan anjima zan baku lbrna,
don ki san kinyi kuskure kema." Tara na dare da 'yan
mintina Likitar ta shigo sanye da kayan bacci masu kauri
riga da wando, tire ne a hannunta dan karami mai dauke
da kayan marmari, lemo da ayaba da abarba. Ina zaune
zugum kan sallaya Asabe na kwance a tsakar daki ta
dubi Asaben "Tashi! "Tashi!! Tun yanzy kin soma bin
sanyin kasa? kada na kuma ganinki.Asabe ta tashi,
Likitar ta ce In bacci ne ki hau gado mana. Ta zauna
bakin gado ta turo mana plate din kayan marmarin bayan
ta dauki abarba guda daya dama ina jin bakina babu dadi
sai shiga bayi nake ina zubar da miyau Na dauki lemu
guda daya ina dan lasa, Asabe ma ta dauka. Likitar ta
dube ni Tun ranar da naji lbrnki naji ina son in fada miki
nawa. lbrn. Amma kafin na fada miki ina son ki sanar da
ni daga ranar da ki ka fara ganina zuwa yau me ya birge
ki a tare da ni? Na gyara zama, Na farko iliminki,sai kyan
halinki,ga shi kina da kyau,ke ba kya tare da matsala
kina da kudi. Tayi guntun murmushi,sannanta dubi Asabe
ta ce, Asabe ban yi kama da mai matsala ba ko? Asabe
tayi murmushi. Anty ai ke ba ki hada hanya da damuwa
ba, bare matsala. ke kam kin ji dadinki. Likita tayi shiru
na dan lkc sannan ta ce. "Sunana Hindu, mahaifiyata
Bafullatana ce, mahaifina yana da kudi sosai,don lkcn da
aka haife ni ma yana matsayin Sakataren Gwamnati.
Mun taso cikin daula da gata, haka nan muna da kyau
'yan gidanmu tamkar mu ne muka hallice kanmu.
Yayyena 2 maza,sai kuma kannena guda 5. Mu 8 ne
gurin mahaifinmu, amma a gurin Mamanmu mu 5 ne,
Kishiyar ta ke da 3. Tun da na taso nake da tsananin son
BOKO burina kullum in zama Likita,wannan yasa
mahaifina ke matukar sona,don shima dan bokon rikau
ne. Shi irin matanan nan ne wadanda za su iya hana
cikinsu su ba ma boko,takarda komai tsadarta in dai ta
boko ce zai siya. Wannan tasa nake zaton dama an
halicce ni don nayi Boko. Lokacin da na gama secondary
ina da shekara 18, kyawuna ya kara fitowa Nan fa
samari suka min ca 'ya'yan manyan mutane,masu kudi
da sarakuna.Ni kam lkcn wani faifai na bude na
walakanta samari, don in fito in zage saurayi ko dan
wanenr baya damuwata.Bana manta wani saurayi
Nasir,Babanshi shi ne Gwamnan jiharmu wancan lkcn
tamkar zai yi hauka don sona, kullum sai ya zo gidanmu
ya min kuka,amma na ce ni fa sai na zama Doctor.
Babana ya daure min gindi, ina ta tsulawa samari tsiya.
Yayuna maza sukan suna son aure,mma Babanmu ya ce
suma ba yanzu ba. Amma shi a wannan lkcn ya sake
dallo wata amaryar wadda bata wuce sa'a ta ba.Sam ban
damu ba, Su Hjy kam ransu ya 6aci,haka yayuna. Babban
sai ya shiga dibn mata yana kawo su wai don Babanmu
ya gani ko zaya mishi aure,amma sai Baba ya kira shi
yana zagin shi. Abn da in na tuna yake bani mmk lkcn
Baba hr d cewa in zya nemi matan shi yaje can ya
nema,amma ya daina kawo masa gida. Na ce Alhj fada
zaka masa ya daina,ya ce kyale shi Hindu, yaje yayi ta
yi,wata rana kan shi zaya bari. Ni dai har na tafi Jami'ar
Ahamadu Bello,ba suyi auran ba.Karatu gurina ba
sauki,sam bana wasa da BOKO. Shekarata 3 a Jami'a
sannan aka yi wa yayuna aure, shima da kyar suna ta
hada Babanmu da mutanen da yake jin kunya. Kwanci
tashi na kammala karatuna,tsawonshekara 7. Lokacin ina
da shekara 25. Saboda kwazona, na samu damar zuwa
wani kwas kasar Germany na tsawon shekara 2. Hjyta hr
d kuka,don bata son tafiyar burinta in yi aure,amma na
kekasa kasa na ce ko na gama karatu sai na fara aiki.
Haka kuwa, ina gamawa ban jimaba na soma aiki a
babban asibitinmu a matsayin babbar Likita. A lokacin
Shekarata 30 babu kadan,sai a wannan lkcn ne hankalina
ya dawo jikina. Nayi boko na zama Likita,yau gani inna
aiki. Nan fa maza suka sake min ca! amma duk wanda
na ta6a babu na aure,sai dai in zan yarda a lalace,daga
wanda zai ce in zo in raka shi Abuja,sai me cewa in zo in
raka shi Dubai. Da na nuna ba haka nake ba, sai na dinga
nemansu daya-bayan-dayaina rasawa,daga karshe duk
suka gudu. Lokacin ne kuma idona ya raina fata,wasu
suka dan soma zuwa amma fa ba yaro,don ko wani ma
zaya girmi Babana, na ce tab, ni kan ai saurayi sabon
jini. Kafin shekara na nemi suma tsofaffin na rasa.Bana
manta wani dattijo da ya soni na ki, sai gashi ya kawo
min wata 'yar yarinya ba za ta fi sha takwas ba, ba ta da
lfy tana laulayin ciki. Ya ce min, Matarsa ce. Sai na
soma tunanin cewa in nemo samarina na da mana,duk
wanda na bncika sai in samu lbrn cewa yayi aure.
Hankalina ya tashi matuka, yanzun gurin mu2m daya
nake sa rai,wato Nasir wanda ya soni tamkar ransa, duk
in da zan samu lbrn Nasir naje amma bn samu lbrnshi
ba. Wata safiyar Asabar, misalin karfe goma na safe,na
nufi supre markte don siyan kayan shafa, domin nawa
sun kare. Ina sa kafa daya kan na dago dayar,wata 'yar
kyakkyawan yarinya 'yar kimanin shekara sha biyo ko sha
daya ta rugo da gudu daga ciki sai ko ta rungume kafata
tana cewa . Anty 6oye ni Fadil za ya kwace min
(Teddy)na. Na daga ta sama,daidai lokacn da yaron ya
iso, daga gani kaninta ne yana da kiba. Ya ce, Anty nima
ki ce ta bani boll dina. Na dube ta, ina boll dinsa? Tana
dry ta ce, Anty boll dinsa fa tana mota. Na ce to dauko
masa, zan sauke ta ta sake kankame ni. Anty Fadil yana
da karfi zaya ture ni ya kwace (Teddy) na. Dry na ke t
musu, ga shi sai naga sun shiga raina, na ce to muje in
sai maka wata boll a ciki. Muna isa daidai gurin kwallaye
na ce za6i wadda ka ke so, yarinyar ta ce Anty nima zan
kara (Teddy) daya. Muryar Babnsu naji ya ce, sannu da
kokari sun dame ki ko? Ina daga ido na sauke kan Nasir,
da sauri na ce Nasir! Da alama sai lkcn ya gane ni, ya ce
a'a Hjy Hindu BOKO uwaka ubanka ya karatu? Sai naji
tankar ya min habaici ne, na ce Alhmdulillah, mun gama
hr na soma aiki,ya ce lallai kam buri ya cika, na ce
yaranka ne wadandan? Ya ce, eh Fadil da Fadila,sai
kanwarsu Yasmeen. Na karkata kai tare da cewa, Allah
ya raya su. Ya ce Amin. Na ce, yanzun kana ina ne?
yace muna Abuja ne mun zo hutu ne, ke fa? kafin nayi
magana wata mata kyakkyawa ina ga zan girmeta ta iso
tana sanye da after dress me shegen kyau. Ta ce Beby
ka gan su? Ya ce ga su nan sweet heart, ta dube ni ta
yatsina baki tare da cewa, wannab fa? Ga mmkina sai na
ji ya ce,Ina tsohuwar budurwata Hindu,? To ita ce
wannan. Nan take ta watso min wani mummunan kallo,
sannan ta figi yaranta gami da cewa, mijin mace daya zo
muje. Yayi murmushi tare da daga min yatsu 2 gami da
cewa bye. Ban iya tsayawa siyan komai ba na fita. A
gida ma ina shiga kai tsaye dakina na nufa,na fada kan
gadona ina kuka. Tambayar kaina nake, wai dama gaske
ne da Bature ya ce dama sau daya take zuwa ma mu2m
a rayuwa? In ko haka ne na cuci kaina na bar damata ta
wuce. A ranar ne na soma tsanar BOKO akida, tun daga
nan na koma ga Allah, ko yaushe nayi sallah addu'ata ita
ce Allah ya ban miji. Kawayena, sa'annina duk sunyi aure
da yaransu,kuma bn tsere musu a karatu ba,tunda aina
aiki suma suna aiki. Amma sun tsere min don suna da
aure ga kuma 'ya'yansu. Doctor Hindu ta dube ni,
Hafsatu kin ganni nan da kama aikina yau shekara goma
sha biyu kenan,amma babu miji. Har Malamai na shiga
don kawai in samu miji. Daga wanda zai ce Aljani ya
aure ni, sai wanda zai ce asiri aka mini,suka yi ta cin
kudina suna min karya, daga karshe naga babu wani ci
gaba na watsar da su. Yanzu na rumgumi kaddarar da
nawa kaina, mahaifina ya rasu shekaru hudu da suka
wuce abin da yasa nabar gida katsina na dawo nayi
asibitin kaina shine, kannena yaran amaryar babanmu
duk sun raina ni gashi ba mu cika shiri da hajiyata ba.
Shiyasa da aka raba muna gado na yo nan na gina asibiti
da gidana, sai dai ina zuwa gida kan lokaci in duba su
hajiya ta. Share hawayenta nima sharar kwalla na ke
tayi, dan murmushi me kika fahimta ko nace wane darasi
kika samu cikin labari na? Nace na farko ba kyau
wulakanci, sannan mu daina sanya boko ya zama gaba
da aure kamar yanda nima nayi. Tace hafsatu naki mai
saukine dan ke kin kama saurayi shi ne dai wanda kika
kaman ya cuce ki. Amma ni abinda nayi saboda boko! Ta
jin jina kai sanna tace ko rabi ban fada maki ba kuma
halin da nake ciki yanzun nima na kirashi SANADIN BOKI,
nace auty haryanzu baki wuce aure ba. Tace to in ban
wuce ba hafsat ina mijin? Kwata kwata na daina burge
maza, sam ba sa jin sha‘awa ta sai yan yara wanda da
nayi aure kan ka ida na rantse miki hafsa da yanzu inada
kamarki koma wanda yafiki don haka sha warata dake ki
daure ki haifa dan cikinki baki saniba ko shi kenan
kwanki a duniya. Sannan kiyi aure tun da kuruciya, aure
ba zai hanaki boko ba kamar yanda mahaifinki yace.
Magana daya zan fada maki, kada ki sake yarda saurayi
ya taimaka miki game da komai na kudi, zai iya anfani
da hakan ya cutar da ke, duk da nasan akwai masuyi don
Allah. Asabe da ke gefe cikin tagumi sai yanzu ta tsoma
baki, anty wallahi ban taba zaton kina da matsala ba, duk
kalon da nake maki mijinki da yaranki suna kasar waje.
Maganarta sai ta dan bamu dariya. Har likitar ta barmu
ta koma dakin ta ban daina mamakin lbr ta ba, duk
kyanta duk kudinsu duk bokonta ta kasa samun miji lalle
kuwa boko yaja mata. Wata zuciyar ta ce min ba boko
bane wulakancinta ne ya jamata, koma mene yanzu na
fiskanci aure yana sama da komai. Washe gari gida na
shirya wucewa kaduna, sai dai kudin mota bani dashi
amma ba zan iya fada mata ba. Dan haka nayi shuru dari
biyar ta bani wai nasha ruwa a hanya. Makaranta na
koma na canja kaya na dauki kwalin wayata na nufi
kasuwar masu waya ni dai ban tsaya ciniki ba, dan ba a
cikin nutsuwa nake ba, yace dubu 6 inji mai siyan
wayanr, bani kudin kawai nace don na kosa insami munir
inji yadda zamuyi. Kai tsaye gidansu na dosa ko
unguwarmu ban sauka ba, koda mai gadinsu yace min
sun fita da maman shi sai nasami can gefen gidan na
zauna. Ko shekara zasuyi sun dawo su same ni, na fada
cikin raina. Kusan awa 3 sanan motarsu ta dawo tayi
hon, mai gadinsu ya bude ban bata lokaci ba na mike na
rufa musu baya. Daga inda nake tsaye ina hango
kannanshi mata suna sanye da gajerun wanduna, kai ba
dan kwali suna ta shiga da kaya. Dayarce ta hangoni sai
naji tace mom ga wata can ko mai aiki ce? Matar ta
waiwayo, kamanninta sak da munir haka ma kannanshi.
Ta nufoni lafiya? Warin munir yayana ya aikoni, tace wai
me? Nace abokinsa ne zan amsar masa sako ne, sunyi
magana da munir din. Tace ok ta nufi ciki tana kwala
mashi kira. Yafito daga cikin gida yana cewa yes mom....
ganina yasa shi yin wani turus! Tace gawata can wai
yayanta ya aiko ta." Da sauri ya ce, "Oh na gane sako
zan bata." Ya iso gurina fuska daure, "Lafiya Hafsatu
kika biyo ni gidanmu?" Na ce, "To ciki fa bai fita ba." Da
sauri ya dora yatsanshi a lebe tare da cewa, shishsh. Ya
nufi gefensu gami da cew Zo. Muna shiga ya ce, "Kina
nufin cikin bai fita ba?" Na ce, "Wallahi." Ya ce, "To ki
koma gida zan zo anjima da dare in kaiki wani asibitin a
fitar da shi, wannan bata san aikinta ba." Na ce, "A
gaskiya ba zanje a kasheni ba, don Likitar tayi duk wani
kokari don ganin ya fita amma abin ya ci tura. Ta kuma
fada min in na matsa cewa sai an cire to zan iya rasa
raina. In je in cema Ubangiji na me?" Ya ja tsaki, "To me
kike nufi?" Na ce, "Shine na zo mu san abin yi." Ya ce,
"To me kike ganin za'a yi?" Sanyi na ji cikin raina, Allah
ya sa ya yarda na ce, "Ina ga mu hakura in zauna can
gidan Likitar, ko Inna ba zan fadawa ba in na haihu sai
muyi aure." Ga mamakina sai na ga yana dariya, a zato
na zancen ya masa dadi, kuma shawara ta ta shige shi.
Amma sai naji ya katse tunani na da cewa, "Amma ban
taba sanin baki da hankali ba sai yau. Kina zaton ko aure
na yi yanzun nan da shekara goma zan haihu?" Ya girgiza
kai, "Ba zan haihu ba, saboda haka dole ne a cire
wannan cikin, in kuma kin dage to kije can ki nemi Uban
danki." Da sauri na dube shi, "Munnir ka san me kake
fada?" Ya ce, "Eh, ina da ja kan wannan cikin, cewa nawa
ne. Daga sau 1 shima ba cikin kwanciyar hankali ba
amma shine ciki zai shiga?" Bakin ciki ya hana ni
magana, idanu kawai na tsura mishi, shima ni yake kallo
cikin harara gami da daure fuska. Na ce, "Allah ya sani
ni ba mazinaciya ba ce,,,,,,,,," Kuka ya kwace min, "Kai ne
ka soma keta min mutuncina, ka raba ni da 'yan matanci
na, yanzun kuma ka bini da sharri. Allah ya isa tsakani
na da kai." Ya matso kusa da ni, "Zan mare ki in kika
zage ni, banza butulu. Duk taimakon da nayi miki da
kokarin da nayi miki amma kin kasa gode min,
shashasha, Kin zata zan kashe miki kudi a banza ne
tsawon shekaru? Ki sani in kin ga kare yana shinshina
takalmi to dauka zai yi, ni ba ajinki bane don ki sani."
Kuka mai karfi ya kwace min, "Allah ya isa Munnir, dama
yaudarata kake yi kace zaka aureni?" Ya yi 'yar dariyar
mugunta, "Kin dai yaudari kanki, to ai ni ne ma zanyi
Allah ya isa tsawon shekara 3 zuwa 4 ina miki bauta ke
da me kika taba saka min?" Ban san lokacin da nayi
kukan kura na shako wuyanshi ba ina kuka ina cewa,
"Allah ya isa." Shi kanshi yayi mamakin yadda ya so
kwacewa daga jikinshi ya kasa.Muryar Mom dinsu muka
ji tana cewa, "Lafiya? Ke, ke sake shi mana me ya faru?"
Na kasa magana sai wani irin kuka nake yi ina fadin, "Ya
cuce ni." Ta dubi Munnir, "Me kayi mata?" Ya ce, "Ban fa
ko sanya ba daga aiko ta gurina ta shakeni wai na mata
ciki." Wani kallo Mahaifiyarsa ta watso min sannan ta
nuna ni da yatsa gami da cewa, "Ke! Shiga taitayinki, tafi
can ki nemi wanda ya miki ciki." Cikin tsananin kuka na
ce, "Wallahi shine ya min fyade. Kuma da shi muka je
asibiti Likita ya ce ina da ciki." "Ke!" Ta kara daka min
tsawa, "Fita a nan." Na ce, "Nifa ba inda zani sai dai ya
san yanda zayayi da ni......." Saukar mari na ji, sannan ta
ce, "Fita ko in kirama Iyayenki 'yan sanda." Ta fita da
sauri tana kiran Baba megadi, ya iso ta nuna mishi ni,
"Baba fita da wannan bana son in kuma jin ko labarin an
ganta a layin nan, in haka ta faru har da kai zan
hukunta." Ya dubeni ya cem "Mu je." Na tsaya ya ce,
"Shige mu je mana ina magana kina kallona." Na dago
jajayen idanuna na kalli Munnir, wani murmushi ya saki
na mugunta sannan na ce, "Akwai Allah." Na fita
megadin yana biye da ni sai da muka fito ya ce, "Yarinya
kin yi kuskure, koda ban san abinda ya faru ba, amma na
san yana da nasaba da abinda yayi ta faruwa da wasu
'yan mata a gidan nan." Na dube shi, "Baba me ya faru
da wasu 'yan matan?" Ya ce, "Samarin gidan nan da
abokansu suna kawo 'yan mata ta hanyar yaudararsu da
kudi, su yi lalata da su." Na dube shi bayan mun fito
wajen gidan, "Baba ni nawa salon yaudarar ya bambanta
da na sauraNan dai aka yi dogayen rubuce-rubuce, kowa
yasa hannu Daga nan ta tafi. Likita ta dubi shugaba ta
ce, " Amma ko da Asaben zata ba su dan su sai an sake
zama, don kada suje su halaka shi, kin san mutane ba
imani. Shugaba ta ce, wannan ka'ida ne, yanzun ki dauki
yarinyar nan ki koma da ita gidanku,gobe zamu je mu
samu iyayenta. "Doctor ta ce, Insha Allahu." Washigare
suka nufi kauyen kurje, iyayen Asabe sunyi murna da
zuwanta, amma da suka ji dalilin zuwan nan suka soma
kuka tare da yiwa Asabe Allah ya isa. Asabe na ta kuka,
Doctor suka yi ta bai wa iyayen baki tana rokon su yafe
ma Asabe. Da kyar suka shawo kan su, sannan suka yi
musu bayanin komai game da yanda suka yi da Yasir.
Mamanta ta ce, to ni dai ba za ta zauna min a nan va,
kauyen nan suyi ta zagina suna yada ni 'yata tayo ciki.
Ta sake rushewa da kuka, Likita Hinda ta ce zan tafi da
ita in zauna da ita hr ta haihu, in ta yaye sun dauki
dansu sai ta samu miji tayi aurenta, ko a nan ne.
Maman Asabe tana ta gdy, shi ko Babn tunda yayi waje
hr suka tafi bai dawo ba, suka dauko hanya bayan sun ba
uwar Asabe sha tara ta arziki.
***** ***** *****
Sati 3 daidai babu alamun cewa cikin jikina zai zube,duk
da cewa kusan kullum sai na je gun Likitar, ita kuma sai
tayi ta kwantar min da hnkl, wai in jira sati 3n su
cika,don ba za ta iya bani wani magani ba tunda aikin
wannan bai kare ba. Sam lkcn bn san yaya Asabe take
ciki ba, don nima ina cikin nawa tashin hankalin, gara ma
Asabe. Bana iya cin abnci,yunwar ma ba jin ta nake
ba,karatu kuma ina mantawa cewar shi na zo yi, don ko
na shiga aji ba na fahimtar komai, ga laulayi mai tsanani.
Munir kuma bai kuma zuwa ba,wayar ma sau 2 ya kira ni,
cikin sati 3 da likita ta bani yau kam ko sisin mashin bani
da shi, a kafa na sabi hanyar zuwa gidan Doctor. Asabe
tare da me yiwa Likita aiki wata gyatuma ana kiranta
Yalwa, su na samu. Asabe ta ce min Likita tana cikin
asibiti zama nayi don jiranta. Sai uku da rabi muna sallar
La'asar ta shigo, da fara'ar ta tare ni tana cewa? na dai
san bukata ta biya tunda ban gan ki ofishina ba. Kamar
ko yaushe,sai hawaye suka soma zuraro min, na ce wlh
Likita ya ki fita, ni dai a kwakule min shi. Ganin tashin
hankalin da na shiga, sai ta lallashe ni da cewa, nayi
hakuri bari ta dan huta. Na koma na zauna ina
kuka,wanda ya zama abn yina koda yaushe, tun da
Asabe ta bani lbrn yanda aka kwashe da tata rigima
hankalina ya kara tashi. Addu'ata Allah yasa nima kada
Likitar ta ce haka za a yi, domin zancen cikin ne sam
bana kaunar Innarmu taji bare Babana. Sai shida saura
ta fito, na dora sabon kuka Nan ta hau ni da fada,wai in
tashi ni tafi kukana ya min magani. Na share hawayena,
tare da bata hakuri,ta ce "Hafsatu! Ina son ki bani aron
hankalinki, ki saurare ni, na ce to. Ta ci gaba da magana.
Cikin nan naki ba zaya fita ba, domin na baki duk wani
magani mai karfi,amma a banza. In ko ki ka ce a
kwakule shi akwai yiwuwar ki rasa ranki. Da sauri na ce
gwara na mutu zan fi son akai gawata ga iyayena fiye a
kai ni gaban su da ciki. Ta ce, To naji amma kin shirya
abn da za ki fada wa Mahalccinki? Kin mutu gurin kisan
kai ko in ce ma kin kashe kanki? Kin fi son kunyar lahira
fiye da ta duniya? kada ki manta, kin ce fyade ya miki
ko? Na daga kai cikin kuka, ta ce to ki dauki wannan abn
a matsayin kaddara. Kada ki manta, Ubangiji ya kan
jarabci bayinsa don ya gwada Imaninsu, ke me zai hana
ki rungumi kaddara? Allah ba ya dora ma wata rai abn da
ba zata iya ba, Zufa ta rufe ni, na ce Likita ba za ki gane
ba ne.Innata da Babana auran zai mutu SANADIN
BOKONA. Alhakin Babana ne kash! Hakika da na san
haka zata faru gare ni da na yarda Babana ya aurar dani,
in yaso sai in ci gaba da karatun acan gidan mijina.
Likita ta ce, Yanzun dai shawar da zan baki ita ce, kije ki
samu shi saurayin ki tunda yana sonki, ku sulhunta, in
kin haihu a daura muku aure. In kuma kina son sako
hukuma kamar na Asabe to in sako, za su tsaya miki a
kwatar miki 'yanci. In ta kama hr kotu kuma ko su waye
iyayenshi. Na ce A'a zan fi son in same shi muyi magana
don bana son asirina ya tonu a unguwarmu. Likita ta ce,
yauwa, in kun sasanta ni kuma zan fahimtar da iyayenki,
na rike kai, Boko! Boko!! Na jajirce sai nayi boko,yanzun
kuma gashi tun ban je ko ina ba bokon na tsane ta.
Likita ta ce, "Hafsaty duk wanda ya dauki boko sama da
aure a karshe sai yayi nadama, saboda halin da ki ka
shiga ina son ki kwana a gidannan anjima zan baku lbrna,
don ki san kinyi kuskure kema." Tara na dare da 'yan
mintina Likitar ta shigo sanye da kayan bacci masu kauri
riga da wando, tire ne a hannunta dan karami mai dauke
da kayan marmari, lemo da ayaba da abarba. Ina zaune
zugum kan sallaya Asabe na kwance a tsakar daki ta
dubi Asaben "Tashi! "Tashi!! Tun yanzy kin soma bin
sanyin kasa? kada na kuma ganinki.Asabe ta tashi,
Likitar ta ce In bacci ne ki hau gado mana. Ta zauna
bakin gado ta turo mana plate din kayan marmarin bayan
ta dauki abarba guda daya dama ina jin bakina babu dadi
sai shiga bayi nake ina zubar da miyau Na dauki lemu
guda daya ina dan lasa, Asabe ma ta dauka. Likitar ta
dube ni Tun ranar da naji lbrnki naji ina son in fada miki
nawa. lbrn. Amma kafin na fada miki ina son ki sanar da
ni daga ranar da ki ka fara ganina zuwa yau me ya birge
ki a tare da ni? Na gyara zama, Na farko iliminki,sai kyan
halinki,ga shi kina da kyau,ke ba kya tare da matsala
kina da kudi. Tayi guntun murmushi,sannanta dubi Asabe
ta ce, Asabe ban yi kama da mai matsala ba ko? Asabe
tayi murmushi. Anty ai ke ba ki hada hanya da damuwa
ba, bare matsala. ke kam kin ji dadinki. Likita tayi shiru
na dan lkc sannan ta ce. "Sunana Hindu, mahaifiyata
Bafullatana ce, mahaifina yana da kudi sosai,don lkcn da
aka haife ni ma yana matsayin Sakataren Gwamnati.
Mun taso cikin daula da gata, haka nan muna da kyau
'yan gidanmu tamkar mu ne muka hallice kanmu.
Yayyena 2 maza,sai kuma kannena guda 5. Mu 8 ne
gurin mahaifinmu, amma a gurin Mamanmu mu 5 ne,
Kishiyar ta ke da 3. Tun da na taso nake da tsananin son
BOKO burina kullum in zama Likita,wannan yasa
mahaifina ke matukar sona,don shima dan bokon rikau
ne. Shi irin matanan nan ne wadanda za su iya hana
cikinsu su ba ma boko,takarda komai tsadarta in dai ta
boko ce zai siya. Wannan tasa nake zaton dama an
halicce ni don nayi Boko. Lokacin da na gama secondary
ina da shekara 18, kyawuna ya kara fitowa Nan fa
samari suka min ca 'ya'yan manyan mutane,masu kudi
da sarakuna.Ni kam lkcn wani faifai na bude na
walakanta samari, don in fito in zage saurayi ko dan
wanenr baya damuwata.Bana manta wani saurayi
Nasir,Babanshi shi ne Gwamnan jiharmu wancan lkcn
tamkar zai yi hauka don sona, kullum sai ya zo gidanmu
ya min kuka,amma na ce ni fa sai na zama Doctor.
Babana ya daure min gindi, ina ta tsulawa samari tsiya.
Yayuna maza sukan suna son aure,mma Babanmu ya ce
suma ba yanzu ba. Amma shi a wannan lkcn ya sake
dallo wata amaryar wadda bata wuce sa'a ta ba.Sam ban
damu ba, Su Hjy kam ransu ya 6aci,haka yayuna. Babban
sai ya shiga dibn mata yana kawo su wai don Babanmu
ya gani ko zaya mishi aure,amma sai Baba ya kira shi
yana zagin shi. Abn da in na tuna yake bani mmk lkcn
Baba hr d cewa in zya nemi matan shi yaje can ya
nema,amma ya daina kawo masa gida. Na ce Alhj fada
zaka masa ya daina,ya ce kyale shi Hindu, yaje yayi ta
yi,wata rana kan shi zaya bari. Ni dai har na tafi Jami'ar
Ahamadu Bello,ba suyi auran ba.Karatu gurina ba
sauki,sam bana wasa da BOKO. Shekarata 3 a Jami'a
sannan aka yi wa yayuna aure, shima da kyar suna ta
hada Babanmu da mutanen da yake jin kunya. Kwanci
tashi na kammala karatuna,tsawonshekara 7. Lokacin ina
da shekara 25. Saboda kwazona, na samu damar zuwa
wani kwas kasar Germany na tsawon shekara 2. Hjyta hr
d kuka,don bata son tafiyar burinta in yi aure,amma na
kekasa kasa na ce ko na gama karatu sai na fara aiki.
Haka kuwa, ina gamawa ban jimaba na soma aiki a
babban asibitinmu a matsayin babbar Likita. A lokacin
Shekarata 30 babu kadan,sai a wannan lkcn ne hankalina
ya dawo jikina. Nayi boko na zama Likita,yau gani inna
aiki. Nan fa maza suka sake min ca! amma duk wanda
na ta6a babu na aure,sai dai in zan yarda a lalace,daga
wanda zai ce in zo in raka shi Abuja,sai me cewa in zo in
raka shi Dubai. Da na nuna ba haka nake ba, sai na dinga
nemansu daya-bayan-dayaina rasawa,daga karshe duk
suka gudu. Lokacin ne kuma idona ya raina fata,wasu
suka dan soma zuwa amma fa ba yaro,don ko wani ma
zaya girmi Babana, na ce tab, ni kan ai saurayi sabon
jini. Kafin shekara na nemi suma tsofaffin na rasa.Bana
manta wani dattijo da ya soni na ki, sai gashi ya kawo
min wata 'yar yarinya ba za ta fi sha takwas ba, ba ta da
lfy tana laulayin ciki. Ya ce min, Matarsa ce. Sai na
soma tunanin cewa in nemo samarina na da mana,duk
wanda na bncika sai in samu lbrn cewa yayi aure.
Hankalina ya tashi matuka, yanzun gurin mu2m daya
nake sa rai,wato Nasir wanda ya soni tamkar ransa, duk
in da zan samu lbrn Nasir naje amma bn samu lbrnshi
ba. Wata safiyar Asabar, misalin karfe goma na safe,na
nufi supre markte don siyan kayan shafa, domin nawa
sun kare. Ina sa kafa daya kan na dago dayar,wata 'yar
kyakkyawan yarinya 'yar kimanin shekara sha biyo ko sha
daya ta rugo da gudu daga ciki sai ko ta rungume kafata
tana cewa . Anty 6oye ni Fadil za ya kwace min
(Teddy)na. Na daga ta sama,daidai lokacn da yaron ya
iso, daga gani kaninta ne yana da kiba. Ya ce, Anty nima
ki ce ta bani boll dina. Na dube ta, ina boll dinsa? Tana
dry ta ce, Anty boll dinsa fa tana mota. Na ce to dauko
masa, zan sauke ta ta sake kankame ni. Anty Fadil yana
da karfi zaya ture ni ya kwace (Teddy) na. Dry na ke t
musu, ga shi sai naga sun shiga raina, na ce to muje in
sai maka wata boll a ciki. Muna isa daidai gurin kwallaye
na ce za6i wadda ka ke so, yarinyar ta ce Anty nima zan
kara (Teddy) daya. Muryar Babnsu naji ya ce, sannu da
kokari sun dame ki ko? Ina daga ido na sauke kan Nasir,
da sauri na ce Nasir! Da alama sai lkcn ya gane ni, ya ce
a'a Hjy Hindu BOKO uwaka ubanka ya karatu? Sai naji
tankar ya min habaici ne, na ce Alhmdulillah, mun gama
hr na soma aiki,ya ce lallai kam buri ya cika, na ce
yaranka ne wadandan? Ya ce, eh Fadil da Fadila,sai
kanwarsu Yasmeen. Na karkata kai tare da cewa, Allah
ya raya su. Ya ce Amin. Na ce, yanzun kana ina ne?
yace muna Abuja ne mun zo hutu ne, ke fa? kafin nayi
magana wata mata kyakkyawa ina ga zan girmeta ta iso
tana sanye da after dress me shegen kyau. Ta ce Beby
ka gan su? Ya ce ga su nan sweet heart, ta dube ni ta
yatsina baki tare da cewa, wannab fa? Ga mmkina sai na
ji ya ce,Ina tsohuwar budurwata Hindu,? To ita ce
wannan. Nan take ta watso min wani mummunan kallo,
sannan ta figi yaranta gami da cewa, mijin mace daya zo
muje. Yayi murmushi tare da daga min yatsu 2 gami da
cewa bye. Ban iya tsayawa siyan komai ba na fita. A
gida ma ina shiga kai tsaye dakina na nufa,na fada kan
gadona ina kuka. Tambayar kaina nake, wai dama gaske
ne da Bature ya ce dama sau daya take zuwa ma mu2m
a rayuwa? In ko haka ne na cuci kaina na bar damata ta
wuce. A ranar ne na soma tsanar BOKO akida, tun daga
nan na koma ga Allah, ko yaushe nayi sallah addu'ata ita
ce Allah ya ban miji. Kawayena, sa'annina duk sunyi aure
da yaransu,kuma bn tsere musu a karatu ba,tunda aina
aiki suma suna aiki. Amma sun tsere min don suna da
aure ga kuma 'ya'yansu. Doctor Hindu ta dube ni,
Hafsatu kin ganni nan da kama aikina yau shekara goma
sha biyu kenan,amma babu miji. Har Malamai na shiga
don kawai in samu miji. Daga wanda zai ce Aljani ya
aure ni, sai wanda zai ce asiri aka mini,suka yi ta cin
kudina suna min karya, daga karshe naga babu wani ci
gaba na watsar da su. Yanzu na rumgumi kaddarar da
nawa kaina, mahaifina ya rasu shekaru hudu da suka
wuce abin da yasa nabar gida katsina na dawo nayi
asibitin kaina shine, kannena yaran amaryar babanmu
duk sun raina ni gashi ba mu cika shiri da hajiyata ba.
Shiyasa da aka raba muna gado na yo nan na gina asibiti
da gidana, sai dai ina zuwa gida kan lokaci in duba su
hajiya ta. Share hawayenta nima sharar kwalla na ke
tayi, dan murmushi me kika fahimta ko nace wane darasi
kika samu cikin labari na? Nace na farko ba kyau
wulakanci, sannan mu daina sanya boko ya zama gaba
da aure kamar yanda nima nayi. Tace hafsatu naki mai
saukine dan ke kin kama saurayi shi ne dai wanda kika
kaman ya cuce ki. Amma ni abinda nayi saboda boko! Ta
jin jina kai sanna tace ko rabi ban fada maki ba kuma
halin da nake ciki yanzun nima na kirashi SANADIN BOKI,
nace auty haryanzu baki wuce aure ba. Tace to in ban
wuce ba hafsat ina mijin? Kwata kwata na daina burge
maza, sam ba sa jin sha‘awa ta sai yan yara wanda da
nayi aure kan ka ida na rantse miki hafsa da yanzu inada
kamarki koma wanda yafiki don haka sha warata dake ki
daure ki haifa dan cikinki baki saniba ko shi kenan
kwanki a duniya. Sannan kiyi aure tun da kuruciya, aure
ba zai hanaki boko ba kamar yanda mahaifinki yace.
Magana daya zan fada maki, kada ki sake yarda saurayi
ya taimaka miki game da komai na kudi, zai iya anfani
da hakan ya cutar da ke, duk da nasan akwai masuyi don
Allah. Asabe da ke gefe cikin tagumi sai yanzu ta tsoma
baki, anty wallahi ban taba zaton kina da matsala ba, duk
kalon da nake maki mijinki da yaranki suna kasar waje.
Maganarta sai ta dan bamu dariya. Har likitar ta barmu
ta koma dakin ta ban daina mamakin lbr ta ba, duk
kyanta duk kudinsu duk bokonta ta kasa samun miji lalle
kuwa boko yaja mata. Wata zuciyar ta ce min ba boko
bane wulakancinta ne ya jamata, koma mene yanzu na
fiskanci aure yana sama da komai. Washe gari gida na
shirya wucewa kaduna, sai dai kudin mota bani dashi
amma ba zan iya fada mata ba. Dan haka nayi shuru dari
biyar ta bani wai nasha ruwa a hanya. Makaranta na
koma na canja kaya na dauki kwalin wayata na nufi
kasuwar masu waya ni dai ban tsaya ciniki ba, dan ba a
cikin nutsuwa nake ba, yace dubu 6 inji mai siyan
wayanr, bani kudin kawai nace don na kosa insami munir
inji yadda zamuyi. Kai tsaye gidansu na dosa ko
unguwarmu ban sauka ba, koda mai gadinsu yace min
sun fita da maman shi sai nasami can gefen gidan na
zauna. Ko shekara zasuyi sun dawo su same ni, na fada
cikin raina. Kusan awa 3 sanan motarsu ta dawo tayi
hon, mai gadinsu ya bude ban bata lokaci ba na mike na
rufa musu baya. Daga inda nake tsaye ina hango
kannanshi mata suna sanye da gajerun wanduna, kai ba
dan kwali suna ta shiga da kaya. Dayarce ta hangoni sai
naji tace mom ga wata can ko mai aiki ce? Matar ta
waiwayo, kamanninta sak da munir haka ma kannanshi.
Ta nufoni lafiya? Warin munir yayana ya aikoni, tace wai
me? Nace abokinsa ne zan amsar masa sako ne, sunyi
magana da munir din. Tace ok ta nufi ciki tana kwala
mashi kira. Yafito daga cikin gida yana cewa yes mom....
ganina yasa shi yin wani turus! Tace gawata can wai
yayanta ya aiko ta." Da sauri ya ce, "Oh na gane sako
zan bata." Ya iso gurina fuska daure, "Lafiya Hafsatu
kika biyo ni gidanmu?" Na ce, "To ciki fa bai fita ba." Da
sauri ya dora yatsanshi a lebe tare da cewa, shishsh. Ya
nufi gefensu gami da cew Zo. Muna shiga ya ce, "Kina
nufin cikin bai fita ba?" Na ce, "Wallahi." Ya ce, "To ki
koma gida zan zo anjima da dare in kaiki wani asibitin a
fitar da shi, wannan bata san aikinta ba." Na ce, "A
gaskiya ba zanje a kasheni ba, don Likitar tayi duk wani
kokari don ganin ya fita amma abin ya ci tura. Ta kuma
fada min in na matsa cewa sai an cire to zan iya rasa
raina. In je in cema Ubangiji na me?" Ya ja tsaki, "To me
kike nufi?" Na ce, "Shine na zo mu san abin yi." Ya ce,
"To me kike ganin za'a yi?" Sanyi na ji cikin raina, Allah
ya sa ya yarda na ce, "Ina ga mu hakura in zauna can
gidan Likitar, ko Inna ba zan fadawa ba in na haihu sai
muyi aure." Ga mamakina sai na ga yana dariya, a zato
na zancen ya masa dadi, kuma shawara ta ta shige shi.
Amma sai naji ya katse tunani na da cewa, "Amma ban
taba sanin baki da hankali ba sai yau. Kina zaton ko aure
na yi yanzun nan da shekara goma zan haihu?" Ya girgiza
kai, "Ba zan haihu ba, saboda haka dole ne a cire
wannan cikin, in kuma kin dage to kije can ki nemi Uban
danki." Da sauri na dube shi, "Munnir ka san me kake
fada?" Ya ce, "Eh, ina da ja kan wannan cikin, cewa nawa
ne. Daga sau 1 shima ba cikin kwanciyar hankali ba
amma shine ciki zai shiga?" Bakin ciki ya hana ni
magana, idanu kawai na tsura mishi, shima ni yake kallo
cikin harara gami da daure fuska. Na ce, "Allah ya sani
ni ba mazinaciya ba ce,,,,,,,,," Kuka ya kwace min, "Kai ne
ka soma keta min mutuncina, ka raba ni da 'yan matanci
na, yanzun kuma ka bini da sharri. Allah ya isa tsakani
na da kai." Ya matso kusa da ni, "Zan mare ki in kika
zage ni, banza butulu. Duk taimakon da nayi miki da
kokarin da nayi miki amma kin kasa gode min,
shashasha, Kin zata zan kashe miki kudi a banza ne
tsawon shekaru? Ki sani in kin ga kare yana shinshina
takalmi to dauka zai yi, ni ba ajinki bane don ki sani."
Kuka mai karfi ya kwace min, "Allah ya isa Munnir, dama
yaudarata kake yi kace zaka aureni?" Ya yi 'yar dariyar
mugunta, "Kin dai yaudari kanki, to ai ni ne ma zanyi
Allah ya isa tsawon shekara 3 zuwa 4 ina miki bauta ke
da me kika taba saka min?" Ban san lokacin da nayi
kukan kura na shako wuyanshi ba ina kuka ina cewa,
"Allah ya isa." Shi kanshi yayi mamakin yadda ya so
kwacewa daga jikinshi ya kasa.Muryar Mom dinsu muka
ji tana cewa, "Lafiya? Ke, ke sake shi mana me ya faru?"
Na kasa magana sai wani irin kuka nake yi ina fadin, "Ya
cuce ni." Ta dubi Munnir, "Me kayi mata?" Ya ce, "Ban fa
ko sanya ba daga aiko ta gurina ta shakeni wai na mata
ciki." Wani kallo Mahaifiyarsa ta watso min sannan ta
nuna ni da yatsa gami da cewa, "Ke! Shiga taitayinki, tafi
can ki nemi wanda ya miki ciki." Cikin tsananin kuka na
ce, "Wallahi shine ya min fyade. Kuma da shi muka je
asibiti Likita ya ce ina da ciki." "Ke!" Ta kara daka min
tsawa, "Fita a nan." Na ce, "Nifa ba inda zani sai dai ya
san yanda zayayi da ni......." Saukar mari na ji, sannan ta
ce, "Fita ko in kirama Iyayenki 'yan sanda." Ta fita da
sauri tana kiran Baba megadi, ya iso ta nuna mishi ni,
"Baba fita da wannan bana son in kuma jin ko labarin an
ganta a layin nan, in haka ta faru har da kai zan
hukunta." Ya dubeni ya cem "Mu je." Na tsaya ya ce,
"Shige mu je mana ina magana kina kallona." Na dago
jajayen idanuna na kalli Munnir, wani murmushi ya saki
na mugunta sannan na ce, "Akwai Allah." Na fita
megadin yana biye da ni sai da muka fito ya ce, "Yarinya
kin yi kuskure, koda ban san abinda ya faru ba, amma na
san yana da nasaba da abinda yayi ta faruwa da wasu
'yan mata a gidan nan." Na dube shi, "Baba me ya faru
da wasu 'yan matan?" Ya ce, "Samarin gidan nan da
abokansu suna kawo 'yan mata ta hanyar yaudararsu da
kudi, su yi lalata da su." Na dube shi bayan mun fito
wajen gidan, "Baba ni nawa salon yaudarar ya bambanta
da na saura
Zaharaddeen Shomar
whatsapp. 08168575100
Sanadin Boko 1-6
Posted by ANaM Dorayi on 12:26 PM, 12-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
." Kuka ya sake sarkeni, na ci gaba da cewa, "Shekara 3
da doriya yana min dawainiya da sunan zai aureni, kuma
Wallahi Baba fyade ya min." Megadi ya ce, "Kuskurenki
shine zuwan da kika yi gidan nan, ki kiyaye zuwa gidan
samari ko dakin samari. Yanzun kije ki yi hakuri, in ba
haka ba zaki jawa Iyayenki matsala. Kin san masu kudin
nan ba duka bane suke da tsoron Allah, 'ya'yansu su ne
'ya'ya na wasu tamkar dabba suka dauke su. Shi Munnir
sau nawa yana samuna yana rokona shi da abokansa wai
in kai musu kudin gaisuwa gidajen 'yan matansu a
matsayin nine Ubansu." Na ce, "Baba ka je?" Ya ce, "A'a
ni nasiha na musu dan nima inada yara da jikoki. Tunda
haka samarin yanzu suke yi, su kai kudin gaisuwa don su
bata yarinya. In ta'ki su ce aurenta zasu yi. Na san koda
ban kai musu ba sun je sun samu wani, kuma ya kai
musu, kila ma sun cimma burinsu, don haka ki je kiyi
hakuri ki kuma kiyaye gaba." Na ce, "Na gode." Ko da
wasa ba zan ce maigadin nan ina da ciki ba.
Tahowa na yi ina mamakin kalaman Munnir, wai ya
taimakeni ne don bukatarshi, dama haka halin maza ya
ke? Dama Munnir mayaudarin 'yan mata ne? Tafiya nake
amma sam ban dauki hanyar gida ba ko cikin mafarki ai
ba zanje gida ba. Zuciyata ta bushe na share hawaye na
na nufi Babban titi. Kwatsam! Sai ga Yayana Umar ya
sauke wani a mashin, cak na tsaya don mun riga mun
hada ido. Cikin mamaki ya ce, "Hafsa daga ina haka?"
Gabana ya fadi matuka, amma sai na kanne banda wata
damuwa na ce, "Na zo ne yau ko gidama ban karasa ba,
gidan su wata na zo." Ya ce, "Wacce watan?" Na 'kirkiro
'yar dariya, "Yar ajinmu ce ta yo mana gaba da kaya to
na zo kuma bata karaso ba." A take karyar tazo min, ya
ce, "Hau na kaiki gida." Muna cikin tafiya ina tunanin ban
so na hadu da Yaya Umar ba, sai ya jeho min tambaya,
"Hafsa sai na ganki duk a hargitse, fuska a kumbure
kamar kin sha kuka." Gabana ya yi mummunar faduwa
amma don kada ya ganoni na ce, "Kukan lafiya? Ka sam
zaman mota, kuma baccina na sha har na gaji." Ya ce,
"Irinku ne ake sace wa, nan da Kano kin hangame baki
kina bacci,." Na ce, "Cikin kwanakin nan ne bamu samu
bacci ba saboda karatu."
Ko Inna abinda ta soma tambaya ta shine lafiya? Cikin
dariyar da bata kai zuci ba na ce, "Lafiya Innarmu." Na
shige daki na kwanta kan gado.Jim kadan Ummi kanwata
ta shigo da kwanon alala ta ce, "Anty gashi." Na amsa
na aje. Ummi ta tsaya tana kallona, ina zaton dan wasan
da na saba yi mata ne taga ban mata ba. Inna ta shigo,
"Wai Hafsa lafiya na ganki kwatsam! Kuma kina zuwa kin
zube a gado?" Ban san yadda aka yi maganar ta zo min
ba, sai dai kawai naji ina bata amsa, "Innarmu gajiyar
mota ce, kuma dama bani da lafiya ne. Can ma muna ta
sintirin asibiti shine aka ce in zo gida in nemi na hausa."
Cikin fargaba da Tausayi ta ce, "Ashsha, me ke
damunki?" Sai kurum na ji bakina ya ce, "Shawara da
Basiri." Ta jinjina kai, "Sannu, Allah ya sauwake, jiki da
jini haka ne. Ta ce ci alalar." Ta daga murya, "Ummi!
Ummi!!" Yarinyar ta shigo da gudu. Inna ta ce, "Kira min
Baban gida in aike sh dattawa ya hadowa Hafsa
maganin basir da shawara." Ta kwance habar zaninta ta
ciro kudi naira dari 3 da ashirin ta ce, "Ungo ka hau
mota ka je layin dattawa gurin masu magungunan
gargajiya ka siyo mata maganin shawara da na basir."
Ya ce, "To." Ya amsa ya fita.
Bani da damar in ki sha domin Inna tsareni take, a
cewarta tun ina karama bana son magani. Duk lokacin da
zan sha ina sha da niyyar cewar Allah ya sa cikin nan ya
fita amma shiru, sai ma tsananin amai da ya karu gareni
da kuma kasala. Tausayin Inna yana sani kuka, in naga
irin fadi-tashin da take yi gurin neman min magani.Wata
rana ina kwance dakin Baabah amai ya sarkeni na tashi
da sauri kafin na bude kofa na soma sheka shi. Baabah
ita ce ta taimaka min na gyara jikina ta kuma kwashe
aman. Har na kwanta ta ce, "Hafsa!" Na ce, "Na'am." Na
tashi zaune, ta ce, "Zo nan." Na mike na bita can kuryar
daki ta ce, "Hafsa ki fada min tsakaninki da Allah me ke
damunku?" Gabana ya yi mummunar faduwa, zufa ta
keto min na ce, "Me,,,,,me kika gani?" Ta ce, "Hafsa na
ga wasu alamu da suke nuna kina da ciki, menene
gaskiyar hasashena?" "A'a bani da komai." Tayi-tayi da ni
in fada mata gaskiya amma na dage kan cewa bani da
komai, don haka ta kyaleni tare da cewa, "Shike nan.
Dama ke nake tunanin zaki bani hadin kai domin Innarku
ba zata fahimce ni ba na sani shi yasa na miki magana."
Na ce, "Ni fa kalau na nake." Don haka sai ta rabu da ni.
Kafin sati 2 duk 'yan gidanmu sun gane halin da ake ciki,
amma banda Innarmu sam bata lura ba bata zata ba, ba
kuma ta tsammanin haka zata faru ba, 'yan tsegumi har
cewa suke mata, "Yaya 'yar boko da jiki?" Haka ta ce,
"Da sauki." Tana washe baki ita a dole an gaishe ni.
Sannu a hankali zance ya soma fita makota sai gashi ana
shigowa dubani, niko ko yaushe ina cikin Hijabi. Baabah
Maimuna ita ce ta shigo dubani yau kawar Innarmu ce
kut da kut ta kalli Innarmu, "Kin san zancen da yake
yawo unguwar nan?" Ta ce, "A'a." "To 'yan gidanku sun
fita suna yada cewa Hafsa ciki ta yo." Inna ta mike cikin
tsananin tashin hankali, "Wane dan sharrin ne? Wallahi
zan iya maka mutum a kotu." Maimuna ta ce, "Saurara
kiji, kafin ki fita kiyi wata magana soma tuhumar ta
tukunna." Innarmu ta ce, "Haba Maimuna, sanin kanki ne
Hafsa bata da rawar kai irin na 'yan iska, sharrine kawai
za'a mata. Kin san bani da hakuril dole sai ba ni ba'asni
wanda ya mata wannan sharrin." Maimuna ta ce, "Don
Allah ki bar zancen nan." Amma Inna bata saurareta ba
ta fita tana fada, wai yaya za'a yi ta bar wannan zancen
ana kallon 'yarta a matsayin 'yar iska!
Kai tsaye sashen su Asabe ta nufa tana fadin, "To
munafukai magulmata masu zuwa lahira da kokon
dambu! Za kuce 'yata cikine da ita, to aniyarku ta biku.
Kuma Insha Allahu 'ya'yanku ne zasu yi ba tawa ba.
Kanta aka fara ciwo da za'a mata sharri?"Kuma in sha
Allahu yayanku ne zasuyi ba tawa ba kanta aka fara ciwo
za a mata shairi? Asabe tace aina kika ji? Mu nan dai ba
wanda ya san haka inna tace rufe min baki munafukai, to
nazone in muku gar gadi zan maka mutun a kotu, sai ta
fito mun da wanda ya fada mata. Ade tace maganar
gaskiya ki bin ciki yarki dan muma a makota mukaji. Inna
tace ahaf na san duk inda aka zaga aka zago kune zaku
fadi wanan maganar, kuma zaku amsa kiran alkali,gida
ya hautsine baba ya shugo yana tambayan ba asi, babah
tace a a yar rigimar yara ce ba sai kaji ba. Nufinta kada
yaji don tasan in yaji sai yabi duddugi amma jin zantukan
sun cika gidan har makota sun soma zagayowa, ya fito
dan jin ba‘asin tun bai karasaba ya soma jin muryarsu
Ade na cewa an dai fada maki kije ki tuhimi yarki, ba kizo
ki tasamu kina zagi ba. Ki dau mataki tun kafin lokaci ya
kure miki, in shairi a ka mata sai kiji dadin kaiwa kotun.
Asabe ta kara da cewa, inko kin tafi yanzun kya iya zuwa
kiji kunya. Ya iso gurin yace zo, babah ta malam na
kiranki don Allah kiyi hakuri ki bar zancen nan, wanda ya
fada ba don kansa ba. Ta nufo daki inda baba ke kiranta,
ina kuryar gado tare da fatan Allah ya dauki raina
yanzunnan. Baba ya dubeta, to in kin gama fadan kira
min yar bokon yar taki inna tace saboda Allah malam
daga ciwo sai ayi mata sharri? Ca wa fa sukayi tana da
ciki yace ai ba abin mamaki bane kira min ita. Hafsa
zonan, na fito kishirya mutafi asibiti inna tace malam
asibiti suna bada maganin basir ne? Acan makarantarsu
fa sunyi na asibitin sun gaji shinefa sukace ta taho gida
ayi na hausa. Yace to ai ba matsala bace wanan,
matsalata in tabatar da zargin da ake yi mata inna tace
ai! Malam kaima ka yarda za ta iya? Yace kwarai kuwa,
yace ita ba mutum bace? Ya ba kanshi amsa yacemutum
ce kuma baliga mai lafiya, don haka yanzu da bayanin
likita zan yarda da duk abinda zakuce. Nan take tsoro ya
kamani hankalina yafi da tashi. Inna tace je kushirya
kutafi asibitin inma har har danine sai muje. Yafita tare
da cewa ina jiranku waje. Nace inna kice masa don Allah
mu bar zuwa asibitin nan kinji? Tace a a ki shirya kindai
san halin babanki, in ba‘aje likita ya wankekiba bamu da
zaman lafiya, nace inna mudai mu hakura ba sai mu
barsu da Allah ba, masu cewa inada cikin? Tace shin
hafsat kodai kina da cikin ne?nazaro ido nace a a ni bani
da komai tace to shirya muje, garuwa ki daureye jiki
nace to a ban daki tamkar in haure yar gajeruwar
katangar mu in gudu, domin na san yau idan mukaje
asibiti asiri na yagama tonuwa. Yau auren iyayena zai
rabu na shiga 3! Nan wata zuciyar ta fada mun ba laifina
bane, in bisu inje asibitin inyaso duk yanda Allah yaga
daman zai faru dani shikenan, sai in rungimi kaddara.
Afili nace Allah ya isa munnir asibitin dutse muka je,
baba shine ya yankar min kati suka tura mu gurin da
zamu ga likitan mata. Duk da halin da nake ceki sai da
nayi Allah wadai da shugabannin da muke dasu. Asibiti
ka mar wannan ace likitoci mata basufi uku ba, ga mata
nan sun kusa 100, wata mata dake kusa dani tace min
tun asubahi suka zo nan tayi sallah. Amma har yanzu
ba‘a zo kanta ba. Ina ganin rashin kula da ba ayi da
likitocin shine dalili da yasa basu zuwa aiki. Haka muka
yini a gurin, amma baba ya dage sai munga likita. Muna
shiga ya bashi kati likita ya tambayi meke damuna?Kafin
nayi magana baba yace yata ce, munzo ne ayi mata
gwaji kotana da juna biyu. Likita yace bari yaji ta bakina,
ya tambayeni meke damuna? Nace basir da shawara,
yace yaya kikeji a jikinki? Nace amai da zazzabi. Kama
hannuna yayi ya duba, nan take ya bamu wata takarda
wai muje amin gwaji nayi fitsari na kawo. Nan take
sakamako ya fito baro baro ina da ciki nurse bata fada
muna ba, ta dai bamu sakamakon mu kaiwa likita.
Lokacin zuciyata ta gama bushewa, na mekawa Allah
komai. Mun shiga yana rubuta muna wani magani, sai da
ya gama sanan ya duba. Ya kali baba, tana da miji? Baba
yace a a likita yasake kalona, amma ke kinsan kina da
ciki? Wata muguwar faduwar gaba naji, tamkar yau
nasoma jin cewa inada cikin. Baba yace tanada ciki ko?
Yacigaba da rubuta wata ta karda yana cigaba da cewa
tana dauke da ciki. Abinda sakamako ya nuna kenan.
Amma kuje ayimata (scan) don kusan ko wata nawa ne
inna kawai na kallah wada ta kafa min idanu sun kada
sunyi jajajir,Baba ya ce a"a bama bukatar sai tayi
hoto,dama tabbacin cewa akwai cikin muke son sani,
tunda akwai shi kenan. Ya kalli Innarmu,bana bukatar sai
na sake tuna miki komai daga ke har ita. Ya fita abinshi.
Inna cikin kuka ta ce, Hafsa haka zaki min? Hafsa na
dace da wannan sakamakon? kin min adalci kenan? cikin
kuka nima na ce kiyi hakuri Inna, wlh fyade Munnir ya
min. Ta ce, karya ne, ki min shiru. Ta dubi Likitan da ya
zuba musu ido,don Allah Likita ka taimake ni ka cire
mata cikin nan. Da saurin Likitan ya mike tsaye cikin
murya mai karfi, fita anan domin nan ba asibitin zubar da
ciki ba ne. Muka fito muka nufo gida, Inna na fadin
Hafsa kin cuce ni kin kuma cuci kanki. kafin mu isa gida
tuni Baba yaje yayi fadan shi a tsakar gida kamar yanda
ya saba, muna isowa kowa sai kallonmu yake yi. Muna
shiga yazo ya ce ya va mu zuwa da safe mu fice,
yanzun ma don dare ne. Mutane na ta bashi hakuri,amma
ya ce to wane hakuri zai yi? Dan ya ce mata in haka ta
faru a bakin aurenta, kuma ta yarda. Ranar inna kasa
fadan nata tayi, duk da matan gidan da suka cika a kofar
dakinmu. Ni kaina kasa min fada tayi sai kuka da take
shara6awa. Mun kule can daki, can cikin sulusun dare
na tashi dan bacci taya dauki Inna na fice. Bayan na
kwashe duk wani abuna mai mahimmanci,
Baban titi na mika ina tafiya ba tare da tsoro ba. Daf! da
Asubahi naji wata mota suna cewa kano ne? na tsaida su
na shiga duk da cewa ba ni da ko sisi,saboda ragowar
kudina na mikawa Inna tun zuwa na, wato kudin wayata.
Sai da muka dau hanya suka ce dari biyar zan ba da, bn
yi mng ba, don haka sai suka zata na yarda ne. bakwai
da 'yan mintuna muka isa Gyadi-Gyadi, suka ce kudina,
na ce bani da kudi,don Allah su taimaka min. Nan
kwandastan ya hau ni da zagi, ni dai kallon shi nake yi.
Direbn ya ce, in je amma nan gaba in banda kudi in dinga
magana tun kafin na hau mota, don ba kowa zai iya
kyale ni ba. Na ce na gode.Sai lokacn kuma na soma
tunanin ina zan je? Wata zuciyar ta ce bakina karanta
littattafan su Anty Fauziya D. Sulaiman da su Anty
Sadiya ba? Ai suna fadin cewa in yara sun gudu su kan
je wani gidan a rike su a taimake su. To suma ai sa rike
ki in kin je ki zauna da sy za su fahimce matsalarki don
suna rubutu kan haka. Amma sai wata zuciyar tace, ki je
gurin Likita nan, ban san lkcn da na tsaida dan mashin
ba, na masa kwantace muka tafi. Ta fito kenan zata ofis
sai gani, ta ce a'a Hafsa ce .da safen nan? Na ce eh,
Anty ga shi ma bani da kudin da zan ba mai mashin din.
Ta zuge jakarta tana cewa, nawa ne? na ce,daga Gyadi-
Gyadu ne ba muyi ciniki ba, ta bashi dari biyu,naga dai
ya bata canji, amma bn san ko nawa ba ne, ta ce daga
ganin ki ba wata nasara amma shiga ciki. Sai da ta huta
bayan ta dawo sannan na fada mata komai, tace to ke
yanzun menene burinki? Na ce ni da zan samu wani dan
aiki in dauki nauyin kaina ba tare da na sake neman
taimakon kowane da naminji ba, zan so haka,amma da
wuya tunda takardun sakandire kawai gare ni, ta ce
amma bn san hikimar guje ma iyayenki da ki ka yi ba,
musamman mahaifiyarki wadda ta gwada miki kauna. Da
kin bita kun gudu tare ko kwa tsira tare. Na ce Aunty ina
tsananin jin kunyar mahaifiyata. Ba zan iya zama da ita
ba. A halin yanzun itama nasan ta dauki hanyar gidansu,
da wane ido zan kalle su? Ta ce to yanzu ina son ki
zauna nan mu ga yanda za"ayi. Ni da Asabe mun zama
'yan gidan Doctor Hindu, ita ke mana awo da komai,
magunguna duk ita ke ba mu. Cikin haka hr muka shiga
watan Haihuwarmu ko na ce haihuwar Asabe. Ta kawo
min kaya jarirai yayin da Asabe aka kawo mata daga
gidan su Yasir. Doctor ta ce, Kin gani kin hana mu dauki
mataki da kema yanzun dole su ringa yi miki komai. Na
ce, Bar su kawai Anty, Ni yanzun ba n da burin da ya
wuce in haihu lafiya, ina so in tsaya da kafafuna ko Allah
zai taimake ni in dawo da iyayena farin cikin su. Ina tuna
kannena, musamman Ummi, Nasan Baba kishiyar
Innarmu bata da mugunta, zata rike su amma nasan ba
za su yafe min ba, Matsawar suka ji cewa ni ce na
kashe auren uwarsu da ubansu. Doctor ta ce kada ki
damu, Insha Allahu za ki dawo musu da komai. Asabe ta
haihu'ya mace, kyakykyawa. Duk da 'yan gidan su Yasir
da shi kan shi ba su zo ba, amma sun aiko da komai
hatta ragon suna. Sannan suka ce ta sa ma 'yarta sunan
da take so. Doctor ce ta bada shawar a saka sunan
mahaifiya Yasir wato Maryam.A cewar Likitar, zai fi
girmama yarinyar duk lkcn data koma gare su. ...
A ganina matsalar Asabe mai sauki ce, don mahaifiyarta
har duba ta tazo sa6anin ni da ban san halin da nike ciki
ba? suma ba su san in da nike ba, Mai aikin Doctor ita
ce ke mata wanka., Kwanci tashi ni ma(E .D. D) na ya
cika har ya gota, amma shiru ba batun nakuda bare
haihuwa, Ranar Litinin tana min gwaji ko na ce awo, ta
ce yaran nan naki fa yayi girma da yawa ga shi kin kasa
kwantar da hankalinki jininki kullum kara hawa ya ke yi. ,
Yanzun ya wuce ka'ida ina miki tsoron afkawa cikin
matsala, kin kasa daukan kaddara. Kuka ya kwace min
Anty zan so in mutu a gurin haihuwa nan, shi ne kawai
burin zcyta. Likitar ta ce dama mun saba fada, duk lkcn
d zan miki awo,mugaye fatan d ki ke yiwa knki kuwa da
kina da kambun baka da yanzun kin lalace., Na ce Allah
isa tsakanina da Munnir Ta ce " Ameen. Amma yanzun
na fi so ki kwantar d hnklnk kin ji? Na ce to. Wasa- wasa
gani na kara sati 3 ta ce in na kara kwana 3 za a yi min
akin. Talata Doctor ta tafi wani taro a brnin Tarayya,
ranar ce kuma na soma nakudar Haihuwa. Haka na kwna
na yini, mai aiki tana kula dani, bayan magriba ta shigo
fada ta hau mu da shi me yasa b muje asibiti ba? Ni kam
na galabaita matuka,gado aka turo aka dauke ni, zuwa
cikin asibiti, amma haka na sake kwana dole ayi min aiki.
dn hk Likitar tasa a min shiri a sani a dakin tiyata.Tare
da taimakon wani Likitan suka yi nasarar ciro min katon
yaro namiji. Hakika na matukar shan wahala, kusan
kwana 3 ban sami kaina ba., Sai a rana na 4, din ranar
har na tashi an jingina min filo. Likitar ta kawo min
yaron. kai na kauda domin a ganina shi ne silan raba ni
da iyayena. Ban ta6a ganin fushin Likitar ba a iya
zamana a gidanta sai yau. Ta ce, Dauke shi ki ciro nono
ki bashi . Na fashe da kuka Anty ban yi aure ba kada ki
sa in ba shi nonona su fadi, ba zan ba shi ba. Ya ya
za'ayi ya raba ni da iyayena, na ci gaba da kuka, ta ce
ke rike shi kafin in zabga miki mari. Shi ina ruwan shi?
Shi ya samar da kan shi ko samar da shi ku ka yi? Don
me za ki ga laifin shi ? Da ba ku aikata abin da ku ka
aikta ba da Allah bai samar da shi cikin mahaifarki ba,
ganin irin kukan da nike yi yasa ta koma lallashina,
bayan na dauke shi. Babansa ya juya masa bya, kada
kema ki zama kin juya masa, Kina nufin ba za ki rungumi
kaddara ba? da lallashi ta shawo kaina na ciro nono yana
sha ina kuka. Satina daya na gargije, muka koma gida.,
Ba a yanka ragon suna ba, sai dai na ce ma Anty duk
sunan da ya dace ta sa mishi ta ce a sa mishi
SHADDAD. sunan wai yana mata dadi. Har ta kara da
cewa da Allah ya nufe ta da aure ya bata da sunan da
zata sa masa kenan, don haka yaro ya ci suna Shaddad.
A hankali na rinka jin kaunar yaron tana shigata, sai dai
kullum kamanninshi da Munnir kara bayyana take, ban
ta6a ganin da mai tsanabin kama da ubansa ba irin haka.
Zuwa yanzun zcyt ta dake,watanmun 3, Wata rana Doctor
Hindu ta zo mana da lbr mai dadi, wai ta samu miji,
tsohon ministan ilimi na kasa. Muka yi ta murna, ita kam
har da Azumi 2 don nuna godiya ga Ubangiji. Sati 4 aka
sa bikinta, mu ne har Katsina gidansu. 'Yan uwanta da
take bamu lbr duk mun gansu,ita ce ta dinka mana
ankon dinner. Ranar daurin aure da dare aka yu dinner.
Sam na kasa sakewa,saboda kallon da maza ke min, duk
da yaron da ke kafadata. Ni kuwa yanzu duk namiji da
zai kalle ni ko da bisa rashin sani ne ai bn da makiyi
kamar su. Mun sha biki,sannan muka dawo,mun samu
gidan yasha gyara,an zuba komai sabo,shi yana zaune a
Abuja da Iyalansa, amma ita zata zauna a gidanta
saboda aiki. Ada na cika wasa da tsokana ga son raha,
amma yanzu na koma miskila,masifaffiya, mara
fara'a.Bugu da kari yanzu ba ni da tsoro, musamman
akan namiji. Kwanci tashi hr Asabe ta yaye 'yarta, kuma
tuni an kaita gidan su Yasir. Bayan hukuma ta shiga
batun don kare lafiyar yarinyar. Sannan ta samu miji a
can kauyensu, mun je har can bikinta garin da aka kaita
ya dan fi kauyensu zama birni. Ni kam kullum cikin yiwa
Likita naci nake, ta samar min aiki ko na gida ne, ta ce
an gudu ba a tsira ba, dubi abin da ya faru da Asabe
sanadin aikin gida. Cikin satin da muka yi wannan
maganar tazo min da lbrn cewa ta samo min aiki a wani
Super market, amma da nisa tsakaninsu da unguwarmu.
Zaharaddeen Shomar
what's app 08168575100
Sanadin Boko 1-7
Posted by ANaM Dorayi on 12:29 PM, 12-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Cikin satin da muka yi wannan maganar tazo min da lbrn
cewa ta samo min aiki a wani Super market, amma da
nisa tsakaninsu da unguwarmu.Na ce ba komai zan iya,
ba d jimawa ba na yaye Shadad, na ci gaba da zuwa
aikina, a wata dubu goma ake biyana. Shawara ta bani,
wai in bude (account) tunda bn rasa komau ba, hatta
sutura tana bani nata. Dan Adaidaita ta samo min duk
wata sai dai in biya shi, sauran na kai banki, Nayi-nayi ta
dinga cire wani abu a cikin albashina, amma sai ta ki ta
ce ita don Allah take zaune da ni,matsala daya a gurin
aikinmu ita ce manajanmu ba shi da mutunci.Farkon
zuwana ya yi ta shige min shi yana sona, ganin yanda na
birkice mishi sai ya sama min lfy, amma akwai zuga
rashin mutunci. In minti daya ka kara bisa karfe 8, to
zaya iya korarka, ban ta6a kai takwas ba tare da naje ba,
sbd ina matukar son aikina. Shadad yana da hkr yana
zaman shi gurin mai aiki. Cikin haka muka wayi gari cikin
farin ciki, Doctor ta samu juna biyu, Mijinta mu2m mai
mutunci da sanin ya kamata. Yayi murna, sai dai cikin
yazo mata da matsaloli masu dama, ko dn ta manyanta
ne? oho. Kwanci tashi ta shiga watan haihuwarta, mijin
ya ce ta shirya su tafi Abuja ta haihu a can, wani asibiti
na musamman. Sun tafi ko yaushe muna waya da ita,
maganarta daya kullum ita ce mu sa ta addu'a, sannan
ta ce min " Hafsa koda bn dawo ba kiyi kokari ke nemi
mahaifanki tare da neman yafiyarsu. Mummunan lbrn da
ba zamu ta6a mantawa da shi ba, musamman ni, shi ne
na rasuwar Doctor Hindu, nayi kuka tamkar raina zai fita.
Ta rasu bayan awa daya da haihuwarta, ta samu 'yan
tagwaye mace d namiji, Innalillahi wa inna ilaihin raji'un,
ko dangin Doctor basu kai ni jin mutuwarta ba, domin ni
ita ce dangina uwata kuma ubana. Can Abuja a kayi
jana'izarta, amma gidanmu ake zamn makoki, in da
dangin ta da na shi suka zo. Tun kafin bakwai na soma
tunanin gurin zuwa, don kan yanzun asirina ya tonu,
gatana ya fadi., A zaton danginta ni 'yar aiki ce, amma
dangin mijinta sun zaci ni 'yar uwarta ce, yaranta
tubarkalla, lafiyyu ana ta ji da su. Ranar 7 kuwa
subahanallah,tunda aka ce mu hada kayanmu za su rufe
gidan hankalina ya tashi, mai aiki kuwa dama daga
kauye take, bata samu matsala ba don ta riga ni tafiya.
Ga shi gobe zan koma aiki hutun da gurin aikina suka
bani a matsayin uwata ta rasu, kamar yanda na fada
musu. Rahma ce ta fado min a rai, yarinyar da muke aiki
shago daya da ita.Rahma tana da mutunci, bari in nemi
taimakonta. Na kira lmbrta t daga, na ce Rahma don
Allah ina nema wani agaji, ta ce na me? muryata ta
sarke, Rahma ina son dakin haya a unguwarku, zan
samu? Ta ce yau-yau din nan? Na ce eh, ta ce gskiya ba
za a samu ba, sai dai in an bincika a hnkl. Na ce na
shiga uku! Ta ce wai me yake faruwa? Na ce ba ni da
gurin kwana, ta ce, gidanku fa,? Na ce ba gidanmu ba
ne, kuma yau masu gidan zasu rufe gidansu, Ina da
matsala. Ta ce ok, yanzun kina ina? Na ce ina gidan ina
hada kayana, ta ce to za ki gane gidanmu? Na ce eh, ba
Tukuntawa ba? Ta ce eh, Mama tana nan sai kiyi mata
bayani kafin na dawo, na ce to na gode. Sun bani kayan
sawa nata da yawa, na nemo dan tasi ya dauke ni zuwa
Tukuntawa unguwar su Rahma, Mama da matar Yayan
Rahma ne kadai a gidan. Muka gaisa, Mama ta ce daga
ina? Sobada ganina da ta yi da kaya riki-riki na ce
sunana Hafsat gurin aikinmu daya Rahma. Ta ce oho,
yarinya da ku ka zo duba ni kwanaki ko? Na ce eh, ta ce
ba Rahma ta ce min Mamanki ta rasu ba? Na ce eh ba
Mamana ba ce, ta rike ni ne kuma yanzun 'yan uwanta
sun zo zasu rufe gidan saboda ya zama na 'ya'yanta. To
shi ne nake son ko zan samu dakin haya nan kusa da ku?
Ta ce to za a cigita, sauke yaron ki shiga da kayan ki
can dakin Rahma.
Ina jin dadin zama da su Rahma don ina yin biyayya gare
su, matar wan Rahma ce ka dai ke son min tambayar
kurilla,tana yawan cewa to wai ina iyayenki? Ban ta6a
amsamata ba, don ko Rahma bata san komai a kaina ba,
bata san Matsayin Shadad a gurina ba, duk da ta
cancanta in fada mata. Matsawar da nayi da son samun
dakin shi yasa su Mama suka sa ne man dakin, amma d
ta ce in yi zamana a nan gidan tun da ba ni da matsala,
haka dana. Na ce, a'a ni dai na fi sobn na samu daki
gidan mutunci gidan Hjy Iya aka samu dakin sai dai sun
ce min sai nayi hakur, don tana da fada. Na ce, ba
komai, in dai sai an tsokane ta ne zata yi to ba za ta
ta6a yin fada da ni ba. Matsalar in da zan dinga kai
yarona kafin ya isa shiga makaranta, ko da rainon kudi
ne. Ta ce, ki dinga kawo shi nan mana tunda shi ba mai
haya niya ba ne, Mun je naga dakin, karami ne ta ce
dubu shida shekara, dari biyar kenan dk wata, na ce ba
komai, zan biya. Naje banki na ciro dubu ashirin cikin
kudina nazo na bata shida, naje kasuwa na siyo kayan
abnci da yar tukunuya da dan risho na dawo.
Zaman mu da Hjy Iya ba matsala, don ina bn ta sau da
kafa,daga ni sai ita a gidan tun Asubahi in na tashi zan
wanke mana bandaki, in share tsakar gidan, komai na
dafa zan bata. In ko zan yi wanki na kan ce kawo naki
Hjy, kullum sai dai ka ji tana shi min albarka, Shadad
kuwa dama tuni ta ce in dinga bar mata shi tunda in
bana nan ba shi da matsala, musamman in ya gane cewa
gidan muke kwana. In ko unguwa na fita dashi kiwa ce
dashi, sannan ya yi ta 'yan rigime-rigime. Mun zauna
yanzu albashina da kyar nike kai dubu biyar banki a
wata, saboda hidimomin gida wanda a da ban san suba,
kai ko kan wannan ba zan manta da Doctor ba, domin ita
ce ke yi min komai. Burina na gaba shi ne, in koma
makaranta, amma yaya zan yi da aikina wanda shi na
dogara da shi? Wata rana da dare na shiga gurin Rahma
muna hira, na ce mata ina son na koma makaranta, ta ce
aikin fa? Na ce shi ne matsala, amma ina son in samu ko
'yar Diploma ba sai nayi jami'a ba, ta ce hakan ma yana
da kyau. Aikina daga karfe takwas din safe ne zuwa
hudu na yamma, sannan wasu su zo masu kaiwa dare,
na ce Rahma ko in koma aikin dare ne. Ta ce albashinsu
fa bai kai namu ba kuma yawan cinsu duk maza ne, na
ce to ya zanyi? Haka nan zan hakura in dai manaja zai
yarda ta ce matsayaci ba, sai shegen iko sai ka ce gurin
shi. Na ce ai dama ba shi ne da gurin ba? Ta ce ba shi
ba ne, na wata Hjy ce mai kudi, ina zaton ma ba a kano
din nan ta ke ba. Na ce to Allah dai yasa in dace zan
tare shi in masa mgn, Rahma ta ce to in ya ki fa? Na ce
ki taya ni addu'a ya yarda, Rahma ta ce to Allah yasa a
dace, in za ki masa magana sai muje tare .Haka ce kuwa
ta faru, domin washegari muna tashi daga aiki sai muka
nufi ofishin manaja, yana zaune gabn shi laptop ce.
Muka gaishe shi, cikin daurewa ya amsa, na ce "Yalla6ai
nazo neman uziri ne. Ya harare ni,wannan karon ko me
kika zo nema kuma kowa ya mutu ba zan ba ki wasu
kwanaki ba, sai dai in ki nemo wadda zata zauna
madadinki. Rahma ta ce, Sir, ba mutuwa akayi ba, tana
son koma mkrnt ne. ya ce, to sai ta bar aikin. " Ya ci
gaba da abn da yake yi. Muka kalli juna ni da Rahma, na
ce ko zan iya komwa akin dare? ko kuma in zo duk lkcn
d nike free hr dare? Ya ce wace makaranta? Na ce poly
zan shiga, ya kalle ni dama ba ki riga kin shiga ba? Na
ce eh, ya ce to in kin shiga sai muyi magana. Ni da
Rahma muka yi godiya, bai amsa mu ba, mu dai muka
fita muna mamakin yanda ya saurare mu. Ina jin an fara
saida form na garzaya na sayo. Rahma tana ta min
dariya wai na cika zumudi, Allah shi ne mai shirya ma ba
wa al'amuran shi. Yau gani na samu gurbin karatu a poly,
daga karfe daya zuwa biyu nake tashi, uku in zo shago,
bn damu da rage min dubu biyun da aka yi cikin
Albashina ba, saboda na samu shiga makaranta. Kuma
na samu irin course din da nake so, wato (Mass comm)
Rahma da murnarta take shaida min saurayinta Sagir zai
turo magabatan shi, na ta6a baki tare da cew. "Yau an
yo odar kaya a shop din nan, kin lura? Tace eh na lura
mana. Amma me yasa kullum na dauko batun Sagir sai
ki daure fuska? Haka nan ranar da na ce kuje ku gaisa
kikaki.Shi ko kullum sai ya ce in gaishe ki. Na ce, um, ki
dai yi hattara da samarin yanzun. Ta ce, Sagir yana da
kirki kuma aurena zaiyi, na kafa mata ido, kada ki ba wa
namiji amana fa, in kin yarda kenan. "Ta ce, to zan kula.
Wata rana ta ce min za su je gidan Yayar Sagir, zata
gaishe ta, wai tayi 6ari, na shirya muje na kalle ta
dabadan Rahma ba ce dana zabga mata ashar. Amma
Rahma ta wuce in zage ta, kema da zan fada miki ki ji
da sai na ce miki kada kije, ta ce ko zan san dalili? na ce
yaudarar mazanzamani.Tayi 'yar dariya, "Hafsat me yasa
kin matukar tsanar maza ne? Me suka miki har haka?"
Murmushin takaici ya subuce min na ce, "Sun min da
yawa." Ta ce, "Kada ki manta shekararmu 1 da Sagir
kuma kudin gaisuwarshi na gidanmu." Sam ban san
lokacin da maganar ta subuce min ba sai ji nayi ina
cewa, "Shekaru 3 da watanni muka yi ni da Munnir,
amma hakan bai hana shi yaudarata ba."Hawaye suka
soma zuba daga idona. "Rahama zan fada miki amanar
sirrina, in kin boye min kin kyauta, in kin tona min don
kanki ke da Allahn ki." Nan na kwashe komai na labarta
mata, ni kuka Rahma kuka, ta rungumeni babu mai ba
wani hakuri sai da muka gaji da kanmu. Na ce, "Rahma
zan koma boko ne kawai don faranta Ran Mahaifiyata,
Insha Allahu zan kawo haske cikin zukatan Iyayena
SANADIN BOKON nan." Rahma ta ce, "Ina bayanki, Allah
ya shige mana gaba. Lallai zan ja baya da Sagir kuma ba
zanje gidan Yar tasa ba." Na ce, "Na kula Sagir dinki
kamar bashi da matsala, duk daba anan take ba. Ki ci
gaba da mishi yadda kika saba amma ko da wasa kada ki
bishi wani guri. Amma ni a kan kaina na gama soyayya,
na kuma sha alwashin duk namijin da yayi gangancin
cewa yana sona zan ci zarafinsa matuka. Rahma ko
kinga laifina?" Ta ce, "A'a."Rahma 'yar amana ce, ko
Mahaifiyarta bata fadawa labari na ba, haka na ci gaba
da Karatuna tare da aikina, na tsare mutuncina ko a
makaranta nasha jin ana zagina wai na cika girman kai,
daga ganina ni ba 'yar kowa bace sai shegen Iyayi, ga
daure fuska. Sam ban damu ba, sai dai mutum in ya isa
ya zo gabana ya fada.
Kwanci tashi har na hada Diploma, kuma ina da burin ci
gaba da HND,shekara 2 kenan. Cikin shekara 2 har
Shadad ya isa shiga Makaranta, kuma na lura zaya dauki
Karatu sosai, shekarunshi 4 kenan da 'yan watanni. A
hanyar zuwa gurin aikina naga wata Makaranta Al-Iman,
boko ce da Islamiyya don haka na je Makarantar na
karbar masa form, sun ce yaro ya zo tun 8 na safe sai 6
na yamma. Duk da Islamiya da hadda, sati da lahadi sai
karfe 2 zai je. Alhamis da Juma'a karfe 2 zasu tashi.
Tsarin makarantar ya min daidai domin zan samu lokacin
daukan shi, sati na zagayowa ya soma zuwa, da dare
kuma inai masa bita.
Tambaya daya ya min wadda ta sa ni kwana kuka, tare
da tunanin me zai faru nan gaba? Ko ba komai nasan
nan gaba akwai kura, abin da ya faru ranar da ya fara
zuwa Makaranta ya dawo muna yin home work ya ce,
"Anty." Na dube shi, "Menene?" "Me yasa da kika kaina
Makaranta baki sa min sunan Babana ba? Duk 'yan
ajinmu ana kiransu da sunan Babansu, ni kuma ana
kirana da Shadad H." Gabana ya fadi, amma da yake shi
karami ne yanzun ba zai fahimta ba sai na ce, "H din nan
farkon sunana ne Hafsat na sa maka ko baka so?" Ya ce,
"Anty kowa sunan Babanshi yake sawa, wani yaro yace
min wai menene H? Wai Hamza sunan Babana?" Na ce
masa, "Ban sani ba, nace ba sunan Babanka ba ne,
sunana ne kaji ko?" Ya ce, "To." Can kuma sai naji ya ce,
"To shi Babana ya sunan shi?" Gabana ya sake faduwa
na daure na ce, "Na manta, amma in na tuna zan fada
maka." Na mike don kar ya sake yi min wata tambayar.
Shadad karamin yaro ne amma in ya maka magana sai
kayi zaton Babbane. Ina tsoron nan gaba kadan ya
tsareni don in fito masa da Ubansa, abu 1 na sa a raina,
shine zan zama uwarsa kuma ubansa, zan yi masa komai
da uba zai ma dansa.
Tun da na bar gida har yau ban daina kuka ba, ban daina
tunanin iyaye da 'yan uwana ba, kullum sai na zubar da
hawayena tare da yin Allah ya isa kwando dubu ga
Munnir, ba zan zagi Boko ba sai dai ba zan gaji da cewa
itace sanadin shigata matsala ba.
Haka kwanaki suka yi ta shurawa Allah ya taimake ni na
koma don samun HND sai dai manejin rayuwa nike,
albashina yayi karanci ya dauki nauyin karatuna da na
Shadad, don ma na tara kudi da farko lokacin Dr. tana
nan. Sai dai na dauki alkawarin ko zamu kwana ba mu ci
ba bazan taba neman taimakon abokin halitta ba, sai dai
in nema a gurin Mahalicci.
Cikin wannan halin yarinyar Hajiya Iya wadda ke zaune a
Saudi ta zo ta dauke ta tare da barin amanar gidan a
hannun Babban Yayan Rahma. Amma ni Hajiya Iya ta ce
in yi zamana kyauta har sai lokacin da Allah ya daga,
don ta ce ina lura da ita, kuma duk abinda na ci sai na
bata koda bata san da shi ba. Na ji dadin samun wannan
rangwame duk da cewa kudin ba wasu yawa bane dama,
amma sauki yana da dadi. Na dawo ni 1 a cikin gidan, in
zan fita na kulle, in sati ne ko lahadi ko dai wane lokacin
ne Shadad ba zai je Makaranta ba sai na kai shi gidan su
Rahma gurin mama, in ko ba nisa zanyi ba nakan yi
kasadar kulle shi ya taka kujera ta ciki ya sa sakata, in
na dawo sai na kwankwasa ya bude.
****** ******** *******
A garin Kaduna tun da aka wayi gari Hafsat ta gudu,
bakin ciki ya karu ga zuciyar Innarta, don haka ta tattara
yanata-yanata ta fice ta bar su Ummi suna ta kuka,
Baba tana lallashinsu. Har ta isa Malimfashi idanunta
basu kafe da hawaye ba, bata boyewa 'yan uwanta
komai ba,sunji bakin ciki suma saidai sun bata shawarar
tayi mata addu'a kada ta mata baki.Haka ta ci gaba da
zama har zuwa lokaci mai tsawo. Wani abokin wansu
Babba ya zo ziyara daga Huntuwa ya ganta ya ce yana
sonta, bata da zabi tunda duk yayyinta sunnuna sun
amince, kuma aurenta da uban 'ya'yanta ba kome.
Alhaji Danlami Matarshi ta rasu wurin haihuwa, amma
yana da yara kuma yana zaune tare da su ne,
shekarunsa 3 kenan rabonsa da aure, ta tare a gidansa
dake Nasarasa Funtuwa, dole ta koyi hakuri domin zama
da yara sai hakuri, in ta kalle su sai ta tuna da nata da
ke can wani gida. Sai ta kyautata musu ko don a
kyautata ma nata, yadda take kula da Yaran sai suma
suke son ta.
Cikin haka ta samu ciki ba don san ranta ba, amma ba
zata butulcewa kyautar Allah ba. Ta haifi danta namiji ya
ci sunan Rabi'u. Umar ya kan kawo mata ziyara da 'yan
kannanshi, mijinta yanada kara don in zasu tafi yanai
musu shatara ta arziki. Shi kuwa Babansu Hafsa har yau
yana bakin cikin tafiyar ta duk da shine ya koreta, yana
kuma addu'a Allah kada ya bashi mai irin halin Hafsa
cikin 'ya'yansa, ganin halinta ne da na Uwarta, ko wani
buri suka ci na son abin duniya shiyasa suka dage da
boko, boko har taje ta yi abinda taga dama.Ni kuma
lokacin rayuwa ta min tsanani, zuwa wannan lokacin
kudin da ke cikin account dina sun kare, albashina ya
min karanci, karatuna ga na Shadad, ga abinda za mu ci,
omon wanki, sabulun wanka har da suturar sawa, duk a
dubu 8. Don ma bana biyan haya. Yau na wayi gari ko na
karyawa bani da shi, ga shi wannan watan shine zan
bada kudin term na Shadad dubu 4, gashi zan yi
registration, gashi bamu da komai na abinca ga kudin
dan adaidaita sahu. Hakika komai ya tsananta gare ni,
kukana ya karu, nadamar barin gidan Iyayena ta sake
shigata sai dai ba zan iya komawa gidan yanzu ba, duk
da kuncin rayuwar da nake fuskanta. Lallai babu komai
cikin barin gida in ba takaici ba, danabi Mahaifiyata na
san danginta za su saurareni za kuma su fahimceni, zan
samu gata ni da dana kafin Allah ya min sakayya akan
Munnir. Bana ba duk wata 'ya mace shawarar barin
gaban iyayenta don gudun zubewar mutuncinta. Hawaye
na bin kumatuna ban damu da na share su ba, domin da
hawaye na karewa da yanzun nawa sun kare. Muryar
Shadad ce ta katseni, "Antyna menene yake damunki
kullum kike kuka?" Na share hawaye tare da kakaro
murmushi, "Babu komai." Ya dafa cinyata, "Kina tunanin
Iya ne?" Na ce, "Eh." Ya tambayeni ni don ya san kalmar
da zan fada mishi kenan, a duk lokacin da ya tambayeni
haka nake ce masa. Ya bata rai, "Anty to muje gurin Iya
din, ni bana so kina kuka." Na ce, "Da nisa jirgi ake hawa
kuma bani da kudi." Ya ce, "To ina girma zan saya mana
jirgi muje ko?" Na ce, "Allah ya sa." Kicin na shiga ina
dubawa, ko zan ga dan wani abin na baiwa Shadad, duk
da nasan cewa bani da komai. Shiru na yi tare da tunanin
abinda zan bashi. Rahma ta yi sallama, na amsa, ta
shigo kicin din tana cewa, "Ina Hajiyar gidan nan?" Na yi
guntun murmushi tare da cewa, "Rahma kenan, duk
tsokana kin santa." Ta ce, "Na zo shan tea din kin nan
mai kayan kamshi." Na ce, "Sai dai na baki kayan
kamshin ki je ki dafa." Ta zuba min ido cikin sanyin jiki,
sannan ta ce, "Hafsa kin 'ki daina kukanki ko?" Na ce,
"Ina kika ga ina kuka?" Ta ce, "Haba Malama, ga idonki
nan?" Ta shiga bude-bude, bata ce min kala ba ta fita.
Ina cewa, "Rahma zo ki ji." Bata juya ba ta wuce. A
zuciyata na ce Rahma kenan, ita dai ta tsani ta ganni
cikin damuwa, ina son zama da ita don ita kadai ce kan
sani murmushi. Jim kadan sai gata da kunshin kosai da
jug dauke da koko, bata min magana ba ta zuba ma
Shadad. Na ce, "Rahma koko kuka dama?" Ta zabga min
harara sannan ta ce, "Ai wallahi Hafsat kina bani haushi,
ina lura da ke duk matse-matsen da kike yi cikin satin
nan, har ta kai baki da abinda za ki ci amma ba zaki iya
tambaya ba? Ni kam ko yaushe gidan ki nake cin abinci,
saboda ina daukarki 'yar uwa ta jini." Na ce, "Rahma
dama ni dake ai babu wani bambanci duk daya ne." Tsaki
Rahma taja, sannan ta dora min dari 5 kan cinya, zan yi
magana ta ce, "In kin ce tak Allah ya isa." Da kallo na
bita har ta fita sannan na saka dariya, Rahma kenan.
Karatuna ya shiga wani hali, har ina ganin in ba wani
ikon Allah ba tsayawa zaiyi. Cikin wannan matsatsi aka
sa ranar auren Rahma da Sagir, kullum tunani na me
zanyi ma Rahma lokacin bikinta? Da dare Rahma tana
min kitso muna hira na ce, "Rahma kin san me nake
tunani?" Ta ce, "Kudin Registration?" Na ce, "A'a, so nake
ki fadi abin da zan miki lokacin biki." Cikin tsokana ta ce,
"Italian bed da leader sit." Muka sa dariya, na ce "Allah
ya hore, har kayan kicin sai na miki." Ta ce, "Ni dai
Hafsat nafi son ki bada hadin kai lokacin bikina kin ga
dai bani da wata aminiya sai ke, sauran duk kawaye ne."
Na ce, "Tabdijan! Rahma kada ki sani yin abinda ba zan
iya ba." Ta saki kaina, "Kin san Allah?" Ta nuna ni da
kibiya, "In bikina ya yi kyau ke ce in ya baci ke ce, kuma
yanzune zan san matsayina a gurinki." Na ce
Zaharaddeen Shomar
what's app 08168575100
Sanadin Boko 1-8
Posted by ANaM Dorayi on 12:13 PM, 18-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
, "Maida wukar, Allah ya kaimu. Yauwa dama ina son in
miki batun da ke raina. Ina son in samu manaja ya bani
koda rabin albashina ne in sai ma Shadad takardu." Ta
ce, "Kin san rashin mutuncin sa, abinda zai fi dai in
tambayar miki rance gurin matar Yayana." Na ce, "A'a ki
bari zan same shi in yaga dama zai yarda." Rahma ta ce,
"Hafsa kenan, ke bakya son bashi sam! Kuma ai naga
bashi hanji ne yana cikin kowa." Na yi 'yar dariya. Haka
kuwa na yi, na samu manaja da bukata sai ya ce, "Kin
cika daure fuska, da ace kina da fara'a har karin albashi
zan miki. Banda kyautukan da zaki yi ta samu a kai-a
kai." Na sake hade fuska, "Bana bukatar karin ko wata
kyauta. Hakkina kawai nake so." Ya ja tsaki, "To sai ki
jira lokacin baki hakkin ya yi, ke bazaki taba ganewa ba.
Wai me ma zakiyi da kudin?" Ban amsa shi ba har sai da
ya sake maimaita tambayar, Na ce, "Zan biya kudin
littafan makaranta ne na yaro."Ya yi tsaki, "To sai ki jira
lokacin don in kin ga na yiwa mace mutunci itama ta yi
min ne." Na mike ba tare da na sake magana, don
Manzon Allah ya ce ka fadi alkhairi ko kuma ka yi shiru,
amma na so in zabga masa ashar in ya so ya kore ni
gaba 1 daga aikin. Cikin kwanakin sai manaja ya soma
shige min, duk da dinke fuskar da nayi masa, ya zo ya
kawo min albashina wai gashi nayi bukatar da zan yi, na
ce ya barsu ai ni na ma hakura. Kwatsam! Rannan sai
naji ana buga min gida, lokacin 9 ta gota na dare, don
har na soma bacci. Na zo na bude, nayi mamakin ganin
manaja a gidanmu na ce, "Lafiya?" Ya ce, "Kalau, na zo
ne mu gaisa." Na ce, "Na gode da gaisuwa. Sai da safe."
Na juya ya ce, "Kina nufin har mun gaisa? Bai dace ki yi
min haka ba." Na ce, "Za a min fada an hanani fita." Na
fadi haka da nufin karema kaina mutunci. Ga mamakina
sai naji ya ce, "Haba yarinya, ni zaki yi wa karya? An ce
miki bansan cewa zaman kanki ki ke yi ba? Ni zaki saki
jiki ki ci arziki ki saki, in ba zaki saki ba talauci sai ya yi
ajalinki." Jikina ya yi sanyi lakwas, na maimaita kalmar
zaman kaina! Na ce, "Ni ce mai zaman kaina?" Ya ce,
"Sharri na miki? Kowa ya san ke kadai ce ba kuma a san
iyayenki ba." Ya ja tsaki tare da cewa, "Banza mara
rabo." Ya tafi.
Ranar na yi kukan da ya isheni, wato kowa ya san
zaman kaina nake? Wata zuciya ta ce, "To yanzun ai an
daina kiwon dabba mutum ake kiwo." Sai dai da mutane
zasu min adalci ya kamata su san cewa bana hulda da
maza, da ace ina da wani aikin lallai zan bar super
market din nan, sai dai bani da zabi.
Da safe duk da kirkiro fara'ar da nike yi sai da Rahma ta
gane cijewa nake yi saboda damuwar da ke raina. Ta
kafa min tambayar me ke damuna? Nanfa na fada mata,
na kara da cewa, "Dama duk mutanen unguwar nan
kallon da suke min kenan? Ina zaman kaina?" Rahma
cikin muryar lallashi ta ce, "Sam, shi dai yabi diddigi ya ji
cewa ke 1 ce anan. Amma ba maza kike tarawa ba,
kowa yana yabonki a unguwar nan don kin tsare kanki,
kuma shi ya fada hakane don takaicin bai samu abinda
yake so ba. Ki barshi da Allah." Nace, "To in ban barshi
da Allah ba yaya zan masa? Ai bani da yanda zan yi
dashi. Da ace ma ina da wani aikin barin musu wurinsu
zan yi." Rahma ta ce, "To ai ba gurinshi ba ne shima cin
arziki yake yi, don haka ba inda za ki je." Daga wannan
lokaci muka sa 'yar tsama da shi, ya bi duk ya tsane ni,
nima kuwa ya kara dasa min tsanar maza, yana son ya
ga nayi wani dan kuskure ya tozarta ni, niko duk wata
hanya da zata ja min cin mutuncin shi na 'ki sakaci da
ita, lokacin zuwa aikina baya cika nake isowa,
musamman in zuwan safe zan yi.
******** ******** *****
Munnir an kammala karatu an kuma dawo gida. Tuni ya
manta da wata Hafsa da labarinta. Ya iso gida cike da
soyayyar Mina, yarinyar wani kusa ce a gwamnati, sun
kulle ne tun a yanar gizo ta (Facebook), sun jima suna
soyayya kafin suga juna, bayan ya zo hutu itama ta dawo
daga inda take karatu, suka hadu. Sun yaba da juna, sai
dai sanin cewa ba za ayi musu aure da wuri ba suka
kazanta soyayyar su ta hanyar biyan bukatar zukatansu.
Sam! basu dauki hakan laifi ba, nasu ganin duk cikin
soyayya ne a nasarance suke koman su don boko suka
sani, shi suka iya, kuma shi suke yi. Sun dai kulla
alkawari ga junansu cewa za suyi aure in lokacin yinsa
ya zo, Allah ka shirye su shirin Addinin musulunci.
(Ameen).
¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Bikin Rahma ya gabato don haka na ciro dubu goman da
na makale na ce mata na ba da rabin kudin Registration
naje nasai mata sestin kula da jug. Dubu bakwai na
kashe, nazo na kai mata gida, batan hakan ya min dadi.
Su Mama suna ta gdy, ta ce yanda garin nan babu kudi
shi ne zaki ta wannan dawainiya har haka? Na ce Mama
ta kama ne. Da dare ina krtn Alkqur'ani,sai gata ta ce,
Yayi kyau Hafsa, ina kika samu kudin sayan kayan ban
masu tsada?Na ce Daga Sarki Allah. Ta ce, ba dai kudin
Registration din ba ne? Na ce in sune fa? Don Allah zo ki
zauna muyi batun anko. Ta ce ba zama nazo ba ki zo in
ji Sagir da wani abokinshi, ki fada musu kudin abubuwan
da zamu yi. Da karfi na ce " What? hum........ hum.....
Rahma kada ki sani cikin hulda da maza. kije kawai ki
amsa, na yarda zamu je kasuwa siyayyar tare. Zata yi
mgn na rantse mata da girman Allah cewa ba zani ba, ta
juya ba tare da ta ce kala ba. Nasan tayi fushi, amma
sam fushinta bai dame ni ba, in dai akan abin da zai sa
nayi hulda da maza ne har nai musu dry. Don ni nasha
alwashin namiji ya gama ganin hakorina. Mun je kasuwa,
duk abn da zamu bukata gurin walima mun sayi, don
Walima kadai zamu yi kayatacciya, sai dai ta ce, Sagir za
suyi (Dinner) kuma za su yi (Pink & blue day). Kullum
rokona take in je har dai na amsa mata zani. hakan ya
tilasta min siyan shadda kamfala (pink) mai ratsin
bulu,yayin da Shadad na dinka masa(blue) din shadda,
atamfar walima kuwa Rahma da kanta ta sai min.,
Bikinmu yayi kyau, komai a gidana aka yi duk da cewa
ina zuwa gurin aiki da mkrnt, kin yi wa Manaja mgn nayi
don ba zan sake yi mishi wani zance ba, ko neman wani
abu. Ranar daurin aure kam ban je makarantaba, kuma
banje aikin ba, saboda aubuwan sun kwa6e min.
Malamai sun halarci walima, sun kuma yi nasiha akan
mahimmancin yin aure tare da falalar da ke tare dashi.
Sun ja hanklin iyayen yara masu cewa su dole sai
'ya'yansu sunyi boko mai zurfi, ko sai sun kama aikin
kafin suyi aure. da cewa wannan ba koyarwa addinin
Musulunci ba ce. Suka ce, ita mace babu abinda yafi
daraja da mutunci a gare ta irin aure. Sun ce boko ba ya
hana aure, kamar yanda aure baya hana boko. In
'ya'yanku suka lalace saboda kun hana su aure sai boko,
hakika laifin zai fi ta'allaqa a kanku iyaye., Nasihar da
suke yi ta sani shiga dogon tunanin, ni kaina misalice
SANADIN BOKO gani yau na zama 'yar kaina, domin da
ace ban ce bokoba nabi zancan mahaifina nayi auran da
yaso, da yanzun ina tare da dangina da ban kashe auran
iyayena ba, da ban haifi shege ba, da maxa ba su dinga
latsa ni suna son mu lalace ba. Ban san hawaye na
sauka daga idanuna ba, sai dai hannun Rahma naji a
kumatuna tana share min tare da yi min rada a kunne.
Haba Hafsa cikin fa taro ki ke, ya ya za ki ba mutane
damar yin tunanin ke wacece? Please ki share don Allah.
Walima ta tashi lfy, na ce da Rahma bari na leka shop,
kin san ban dauki uxiri ba, ta ce min ba damuwa. Naje na
samu su Ishak, ya ce nasan kuna biki shi yasa ban tashi
ba, na fada mawa manaja cewa zan zauna madadin ki
har ku gama biki, ya kuma san auran Rahma ne shi yasa
bai ce komai ba.Ya kara da cewa, ki koma har sai kun
gama ki mata fatan alheri, mun so muzo daurin aure
amma kin san Manaja. Na ce na gode, ya ce a'a ba
komai, wata rana irin haka zata iya faruwa da mu, na
dawo nake fada ma Rahma ta ce, Ishak da Musa suna da
kirki sosai, dn dai kin kasa Fahimtarsu ne. Na ce, Ba zai
sa don sun kar6ar min aiki in sakar musu fuska ba,
gaisuwa kawai ke hada mu ko da, kuma ita zan ci gaba
da yi kadai. Anje anyo ma Rahma danki(jere) an zo ana
ta lbrn kyan gidan an ce ango ma ya zuba labulaye da
kayan wuta, Sai an kai Amarya sannnan za'ayi sauran
shagalgulan da ango suka shirya, wai ba a son mutane
suyi yawa, sai ka nuna pass sannan zaka shiga. Da muka
kai amarya unguwar Sharada, gidan kam ko ni ya min
sosai, taso in kwana na ce mata ta min hakur sai gobe in
mun hadu gurin (pink & blue day' . Ta ce don
girman Allah kada ki ki zuwa, na ce kin sanni Rahma in
har na ce zan yi abu bana fasawa, ta ce shi kenan, ki
gaida min Shadad. Na tafi ina hawayen rabuwa da
Rahma, don ita wani bangare ne na farin cikina. Gidan
su Maman Rahma naje na dauko Shadad, jikinshi naji da
dumi, ina zuwa gida na bashi (paracetamol) Na kwantar
da shi. Sannan na shiga gyaran gida. Ina zuwa na samu
ma yayi bacci, nayi Shafa'i da wutiru nima na kwanta.
Cikin dare na farka don yin nafila kamar yanda na saba,
sai dai kawai naji jikin yaro sharkaf da zazzabi. Na cire
masa riga na dunga goge masa jiki da ruwa mai sanyi.
Sanna na kara bashi magani, kafin safe Allah ya
taimakeni jikin yayi sauki. Sai dai yan rigin gimun da
yake yi na shiga gidan su Rahama muka gaisa da su
mama, ina zama
Kiran Rahama na shugowa, ina ji dama nasan ita ce, dan
bani da number kowa a cikin zumu dina na daga ina
cewa hajiya kenan, amarsu ta ango. Ta katseni da cewa,
ba wata hajiyarki, shine ko ki kirani da safe ko? Nace shi
kenan sai na hau doka maki kira da safe kisa angonki ya
ji haushi na. Tace wane ango? Kin san Allah ba nan ya
kwana ba, tare da su hadiza kawaye na muka kwana, ba
ke kinki ba? Nace ai gara da na dawo, dan na sami
shadad da zazzabi haka muka kwana. Amma yanzu
Alhamdu lilahi. Tace to Allah ya kara sauki. Tace don
Allah ina sa ido gurin programme din nan, wlh in baki
zoba bikin zai baci, don kina da muhinmanci matuka a
gurin. Nace to zan kokarta duk da shadad nata yan
rigingimu, kin sanshi in baya jin dadi sai yayi ta rigima,
tace yaro kenan Allah dai ya kara sauki,nace amin, yace
kizo da wuri dai. Sai da na fara yima shadad wanka,
sannan na shiga na fito naga gari ya soma hadari, nayi
alawala dan yin sallar la‘asar, haka kawai yau naji ina
sha‘awar shafe shafe a fuskata. Na fito da kayan shafa
da rahama ta di bar min na lefenta, har da jaka da
takalmi da mayafi ta bani duk pink, tun asali ni mai son
yin kyale kyale ce, halin da na tsinci kaina ne yasa na
daina, nafi minti 30 ina kyalekyale a fiska ta. Na dinga
kalon kaina a madubi nasan nayi kyau sosai, har shadad
yana kallo na, nace nayi kyau? Ya daga kai ina kulle gida
rahama na kira na, na daga tace aminiyata ki tai makeni
kada kisa naji kunya, wlh guri yayi guri amma ke kadai
muke jira da wani abokin sagir da ya sauka daga
adamawa state, anje daukoshi daga filin jirgin don Allah
kiyi sauri. Nace to zubaina ganin zuwa amma fa garin
akwai hadari, Allah yasa in sami abin hawa da wuri.
Tsaye nake a bakin titi duk wani dan a daidaitan da yazo
yana dauke da mutane, masu son banza watan yan rage
ma mata hanya suna tsayawa Amma ni ko kallon su
bana yi. Wata jibgegiyar jeep ta zo ta gifta, sai kuma ta
dan dawo.sai tin inda nake ta tsaya, gilashin motar ya
sauka a hankali,naga mai tukin saurayine yana sanye da
shadda yar gaske blue mai duhu, hularshi itama blue ce,
amma kalar sararin samaniya. Ta gefen ido na kaleshi,
sannan na dauke kaina. Yace, yan mata ina zaton guri
daya zamuje in na lura da shigar da ke jikin ki ko? Na
kaleshi nace ba dole hakan ta kasance. Yace, yace ki
shugo muje kinga hadari. Nace kuje na gode. Glashin
baya ya sauka, naji saukar galas din ne da wani sauti da
yayi, amma ban waiga ba, saima na dan kara taku biyu
ta baya na. Muryar da naji ne tamkar in waiga, amma sai
na dake yace shugo mana ga hadari nason zubo da ruwa
gaki da yaro. Na dubeshi dan son in tuna inda na san
wanan muryar, kyawunshi yasa nayi saurin kauda kaina,
tare da cewa kuje ni ba zan shiga ba.daga cikin motar
naji wani yana cewa don Allah mutafi amma za a
taimaka mata tana yiwa mutane yanga,da sauri na
kallesu cikin bacin rai, idanuna har kan kancewa sukayi
don ta kaici, cikin kalon hadarin kaji nace taimako? Ce
muku nayi ina neman taimako? Na dan duka tare da leka
motar, kai me fadin taimakon nan kasani bana neman
taimakon wani abin halita sai ma halincci, ni ban tsai da
ku ba. Na kara rike hannun shadad da kyau, na soma
tafiya dai dai da ruwan ya kece, kamar da bakin kwarya,
ba tsanmani sai naga kofar ta wangale na bakin kofar ya
sauko kafa tare da sauko hannu ya dauki shadad zuwa
cikin motar, a gigice na dubesu yace ki shigo in kuma ba
zaki shigoba ki samemu a can. Amma shi kam ruwa ba
zai dake shi ba. Bani da zabi, tunda sun daukar min yaro
dole na shiga. Gashi bana son dukan ruwan, don haka sai
na shiga. Shadad na ciyar mutimin da muryarshi ke sani
faduwar gaba, kamar na taba jinta ada innaso in tuna
inda nasan muryar ko mai irinta. Muryar ta sake katseni
da tunanin da nake yi, yace ma shadad boy ya sunanka?
A zatona shadad ba zai yi masa magana ba, saboda shi
yaro ne mara son ma gana, musanman in bai san mutun
ba, sai naji yace shadad. Mutumin ya mai maita sunan
shadad, sunanka yayi dadi, to wanan fa? Ya nunani ya
sunanta? Shadad ya kalle ni, na zabga mashi harara,
amma ga al‘ajabi na sai yaron nan ya kauda kai yace
anty. Mutumin yace to kana zuwa makaranta? Yace eh
al‘iman sunan makarantar mu, kuma muna yin (A B C D)
har da(1234). Na rike baki inata al‘ajabin yaron nan,
tunda nake dashi ban taba jin yana rarata surutu haka ba,
harda kin kalona shida ko abu aka bashi da ya kali
fuskata zai gane, in ina nufin ya karba ko karya karba
amma sam ya ki kallona tunda ya gane ina hararan shi.
Mutumin yace gud, kana yin kokari? Yace eh mana, har
ma naci number one, aka min kyautar books. Anty na
kullun tana koya min karatu, da su home work harda ma
islamiyya, ban san sanda nace shut up stupit boy!
Mutumin ya kalle ni, shikuma shadad ya kwanta lakwas a
jikin mutumin. Ya tsorata dan bana mashi tsawa, ko
yawan zaginsa. Na daga can gefen yace. Ke! Wai wane
irin hayaki kanki ya keyi? Ko kuwa ance maki wani kyau
ne dake? Ko ance miki sonki ake yi? Ko kuwa burgewa
ce wannan masife masifen da kike yi. Nace kai saurareni
bana son shishshigi da katsalandan cikin lamari na, nayi
magana da kai? Ko nace ka kalle ni ne bare ka tan tance
kyauna?gani na kayi a filin gasar kyau? Balle kace nace
ina da kyau ne? Masifa kuma dole ku jita tunda ku ka
nace sai kun dauko ni, haka nan bana bukatar burge
kowa cikinku na fison in burge kaina. Don haka yi ta
kanka dan dukanku bakwa gaba na, zaiyi magana mai
dauke da shadad ya daga masa hannu alamun yayi
shuru. Shi kuma yaci gaba da shafa kan shadad wanda
yayi kwance a jikinsa. Wayata ta shiga ruri, ban ko kula
ba dan nasan rahama ce, sai yi take tana katsewa, ana 5
din na daga a kufule, don itama haushinta nakeji ba don
bukin ta bane wa za ya hadani da wayanan gardawan.
zaharaddeen Shomar
what's app 08168575100
Sanadin Boko 1-09
Posted by ANaM Dorayi on 12:23 PM, 18-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Don itama haushinta nakeji ba don bukin ta bane wa za
ya hadani da wayanan gardawan. Cikin fada nace wai
meye ne kika dame ni da kira, ina hanya in kuma zaki
matsa min sai na juya gida abina. Tace mai da wukar
Allah ya baki hakuri, da ma ruwan da ake shekawa ne
nace bari naji ko kin koma gida ne saboda ruwan sai
direban su sagir yazo ya daukeki. Nace na hutar dashi,
gani nan zuwa na kashe wayata tare da tsaki.Harabar
hotal dam yake da jama‘a, ko ince motoci jama‘a sun
cika holl din suna tsayawa na kama kofar zan buduwa.
Ashe daga gaba ne direbab zai bude mu. Yana budewa
na fita, sanan na nufi ciki mai surutun tsiya nan shadad
ba tare da na kalesu ba na nufi wata yar baranda ina ta
yi mashi fadan irin surutun da ya dinga tsugawa acikin
motar, sai ya bale mun da kuka yana fadin.uncle! Uncle!!
Nace yi min shuru ko in mareka, sarkin shishigi, bai daina
kukan ba, na na ciro wayata na kira rahama gani nan fa
ba zan iya shiga ba, mutane sunyi yawa. Ta ce mun
ganki kin tsaya ga Aisha nan tazo zata taho dakegurin
mu tare zamu shiga. Nice a gefen amarya sauran
kawaye suna bayan mu,haka nan ango da abokan shi
suna biye da mu, ina reke da hanum shadad, wanda har
lokacin bai daina gunjin kuka ba, muka shiga. Kidan da
ke tashi kamar zai fasa kwanya yasa naji tamkar in bar
gurin kai tsaye. Wani mai dauke da abin magana yace,
ango da amarya sun shigo, kowa da amininshi zai zauna,
sagir ya zauna gefen shi wanan mutumin, ni kuma ina
gefen Rahama tare da shadad
ta dube ni, mutuniyata wa ya taba ki ne, naga fuskarki ta
kasa boye fushinki, nace uhm! Ke dai bari, abokanan
muijinki ne wlh, sai kuma shadad yaron nan ya kular dani
yau. Tace to dan saki fuskar mana saboda guri ya
kayatu, kisan fushinki zaisa gurin ya dishe. Na harareta
tare da dan murmushi, tace ko kefa. Sagir yace ranki
yadade, ya gajiya? Na nace tana gurinku ya jama‘a?
Yace gasu muna tare nace Allah yasa alheri, da ganan
na maida hankalina gun mai abin magana, yace za mu
kira baban bako kuma baban abokin ango don yayi mana
jawabin maraba tare da dan fada mana wanene sagir.
Sai dai kafin nan babar kawar amarya hajiya hafsat sai
ta bude mana taro da adu‘a, na kali rahama tace please,
tashi kawai. Na mike cikin natsuwa na isa gurin na
amshi abin maganar. Shadad yazo ya rikeni yana kuka,
sai wai abokin ango ya taso ya daukeshi. Bayan n gama
adu‘a na dora da karanbanin nawa, ina bawa jama‘ar da
ke gurin nan shawar kada suyi liki, almubazaranci ne ga
duk mai sha‘awar ya burge ango da amarya su dan ka
musu a hanun su, amma ba dole bane kuyi yanda
nace,sha wara ce. Na koma na zauna, bayan sun bini da
tafi. Shiko da zaije yin jawabin maraba tare da shadad
yaje yana rike da hanunshi. Cikin jawabin ne naji yana
jaddada maganata cewa abinda na fada yayi kyau, don
haka ba‘a son liki, duk wanda zai lika yazo ya ba ango ko
amarya a hannusu. Wanan ma yasa aka kashe rawa da
za‘ayi, rahama ta dinga yi min dariya wai a gaisheni da
karfin hali har ta sanima na dinga dariyar. Sagir cewa
yayi nazo na hanasu rawa, to wane rawa zasuyi ba liki?
Nace tai makonku nayi ai rawa haramun ce ko? Haka
aka ta gabatar da abubuwan da za ayi har lokacin da
akayi sanarwar ango da amarya tare da da masu tayasu
zama dan dibar abinda suke son ci da kansu,
kasancewar dibi da kanka ne za ayi a gurin. Muka hadu
muka jeru amarya tana biye da ango yayinda ni kuma
nake biye da abokin nashi, shi kuma yana dauke da
shadad a kafada tamkar wani danshi. Ango yasa abida
yake so sai fruit ya ce ko zaki tai maka min? Inji abokin
ango tamkar ince a'a amma sai nace me zan sa maka?
Ganin yana sabe da shadad yace ki samin ko menene,
zan ci. A raina nace kaji dashi, ba tare da tsayawa tunani
ba ko mai hanu na yakai shi nake zuba masa, sai da na
shake plate din sannan na bi bayanshi da plate 2. A
gabanshi na dire tare da samashi cokali, na koma ma
zaunina. Sai kurum naji sarkin surutun nan wato mai rike
da abin magana yana cewa, kai gaskiya ango da amarya
kun burge ni, kun zauna da aminan ku kuma mata da miji
har da dansu, to yace ke amarya yaya bakiyi koyi da
kawarki ba kema ki zuba ma ango da kanki? Kai abokin
angon nafa yi maka murna, matar kada kayi mata
kishiya, dubi yanda ta cika maka plate da kaji da kifi kila
abinda ka fi so kenan, wanan ya nuna ko a gida ba a
barinka da yunwa. Sai kurum naji gurin ya dau tafi. Da
sauri na dubi plate din, lallai kam kaji ne da kifi, sai dan
cosilo a gefe, na dubi fuskarshi yana dan murmushi.
Rahama da sagir kuma dariya naga suna ta shekawa nan
take na hade rai tare da kin kai komai bakina. Shiko
shadad sai uban cin naman nan yake yi, shi da mutimin
tuni gurin ya rikice da ciye ciye kowa na diba da
kansaRahama tace to kici mana,nace mata ke ni nama
koshi, ba yan haka ma ni ba zan iya cin komai a taron
nan ba, kowa yana kallona. Haka nan bayan an tashi duk
na matsu naje gida domin magariba ta yi, ina so inyi
sallah sai dai tun da muka fito banga shadad ba, ban ga
mutumin nan ba. Nace rahama ina suke? Tace suna
cikin jama‘a in dan jira. Can nesa na hango wani shago
naje na siyo ruwan naira 10 nayi alwala, nasami gefe
dama da hijabina a jaka, nayi sallah ta. Rahama tazo
tana ce min sun dawo? Nace ke zan tam baya, ina
mijinki? Kune kuka sanshi ku zaku nemo shi. Takira sagir
tace sun ko dawo? Hafsat tana son zuwa gida. Yace a'a
na kira wayarshi kuma a kashe, tace a a to ina ya shiga?
Kai kana inane? Yace gani nan kusa da shago ina kallon
ku ai. Muka nufi girin ango, hankalina ya tashi da rahama
take fada min wai wayanshi a kashe.rahama ta dubi
angon ta tace, ba kace min bako ne ba? Yace eh amma
kano ba bakuwa bace a gurinshi. Ki kwantar da
hankalinki, yauwa gasu nan zuwa ma, duk muka kai
duban mu gurin shi. Yana rike da hanunshi, shi kuma
yana reke da leda. Suna tafe suna yan zan tukansu har
suka isko mu, nace kai ka cika shegen yawo, ina kaje?
Na finciko shi yace anty munje masalaci ne da uncle, ba
kin ce mun wai in dinga sallah a farkon lokacinta ba?
Nace naji ni dan Allah wuce muje na dubi rahama sai
watarana, tace dinner din fa, anjuma karfe 10 naja tsaki
ke kinsan ba zan iya wanan galafirin ba, gara ke sai dai
nazoo. Sagir yace ki bari a kaiki don Allah, gari yayi
sanyi ga duhu, nace nagode, sai anjima nayi gaba.Wani
daga cikin abokan da suke tsaye wanda har dashi muka
shigo motar nan da zamu zo, ya dubi rahama yace kai
wanan kawar taki ta cika masifa, ita ba kyau ba rahama
tace a a kada ka zagar mun kawa masa‘udu, hafsat bata
da masifa,tana da kirki sosai na jima banga mace mai
saukin kan hafsat ba, ita dai abu 3 ta tsana a rayuwarta,
inko mutun ya kiyaye ba mai jin su. Ni da ita bamu taba
yin fada ba koda munyi sai dai ni ni na ta sababi na
amma bata biye min. abubakar lamido yace yanzu kai
kaga masifarta? Ya dubi masa‘udu masa‘udu yace au
yanzu duk abinda take maka baka gani ba? Yace ni kam
me tamin? Bata min komai ba, duk abubuwan da takeyi
sun matukar burgeni. Ya dubi rahama, ni kam in tambaye
ki? Rahama tace ina jin ka, yace amma dai ba matar
aure bace ko? Rahma tace a a daga nan bai sake
magana ba. Duk abubuwan da Abubakar Lamido ke gani
daga hafsat bai taba ganin wani aibunta ba, tunani 1 ya
dameshi, ina ya santa? Shi dai yasan cewa koda a hanya
ne ya taba ganin ta. Anashi ganin Hafsat ta san
mutuncin kanta shiyasa take wanan dabi‘un. Acikin
masauki ya kasa zaune da tsaye, baisan meyasa ya
damu kanshi da dabi‘un hafsat ba, bai taba ganin mace
da ta burge shi irin ta. Yasan daga ganin halayenta za
asha wuya kafin a samu soyayyar ta, duk da bashi da
tabacin sonta yake ko burgeshi take. Ya dai san ko ma
dai menene ya damu da ita. Kafin kwana 3 ya damu da
son sanin wacece ita? Alwashi ya sha ma kansa ba zai
bar kano ba har sai yasamu cikaken labarinta, wanda
yasan gurin rahama ne kadai zai san haka, haka a rana
ta 4 ya kira sagir yace gashi nan zuwa, zaya ci dinner
tare dasu. Duk da tulin kayan da aka tara a gaban shi na
lashe-lashe da tande-tande, sam basu dameshi ba, ya
dubi sagir cikin hausarshi na fulanin yola ya ce, nikam ka
bani dama inyiwa amaryarka wasu tanbayoyi game da
kawarta nan sagir yace wace ba dai hafsatba? Bai san
da lilin fadiwar gaban da yaji ba, haka nan bai san
lokacin da kalma ta fito daga bakinshi ba, tana da miji
ko? Ya tsare sagir da idanun shi masu kama da na
mata.Sagir ya ce bata da miji, amma fandarrarun
halayenta ne zasu gundire ka, yace bana zaton haka,
yanzu dai nafi so ka min izinin zantawa da matarka,
yace to ya kirata tazo ta zauna tare da cewa ba dai har
ka gama cin abincin ba?Yace ai kafin abincin ya samu
shiga nikam sai naji batun kawarkinnan hafsa. Rahama
ta dubeshi da sauri tace me kake son sani game da ita?
Yace unguwarsu da kuma dan lbr ta haka rahama tace
unguwarmu daya, sannan ita daliba ce a Poly yanzu haka
tana HND dinta ne. Iyayanta fa mutanen kirki ne?
Rahama ta danyi din sanan tace eh yace ta taba aure
ne? Kuma shadad dan tane? Nan take zufa ta karyo
mata, amma bata da amsar da ta wuce eh ya jijiga kai,
dama nayi zaton danta ne duk da batayi kama dashi ba
sun rabu da mijinta ne ko ya rasu ne? Nanma tace eh,
yace Allah sarki inaga shiyasa bata son hulda da maza,
dama ance mace in mujinta ya rasu kafin ta manta da
wuya. Iyayan ta din sunan layinku? Rahama tace eh, a a
karatu tazo suna kaduna. Gurin aikinmu daya ne super
market ne, yace to zan iya samun number dinta?
Rahama tace wai gaskiya yallabai sai dai kayi hakuri, in
na baka number ta zai iya zama sanadin rabuwar mu
kwata-kwata. Ya dan yi shuru yana nazari, Rahama tace
duk yanda kake tunanin hafsat ta wuce nan. Yace amma
ina zaton bakinki naji yana fadin tana da saukin kai da
dadin zama, kuma bata da fada? Rahma tace gurinmu
mata ba, amma game da maza sam bata da sauki, ta
tsani namiji ta kijinin ace anason ta sanan bata son
taimako daga namiji, ko wannen abu 3nnan ba taso.
Yace to me tafi so? Rahama tace abinda tafi so shine
kada kashiga harkarta, in kuma kashiga kayi tsananin
dace ta kula ka to kada ka tam bayeta ko wace irin
tanbaya, sannan kada kace kana sonta, ban san me
zakayi ba ta saki jiki da kai ba, don naga maza da yawa
wanda suka sota amma dole suka hakura rashin sakin
fuskarta yasa maza suna tsoranta. Da zaka hakura da ya
fi maka lada don ko taji hau shin abinda MC yace mata a
gurin bikinmu inda yace ku miji da mata ne. Abubakar
yace niko sai naso ace gaske naji dadi maganarsa.
Rahama ba zan iya hakura da hafsat ba don ina jin wani
abu game da ita wanda ban taba jinshi a wata yarinya ba
ina zaton shine so. Su Rahma suka sa dariya sagir ya
nisa yace lalle sonka din nan ya iya jan rigima ya fada
inda zaku sha wahala Abubakar yace sona yayi daidai
don yasan bama ra‘ayin mata marasa aji wadanda ke bin
maza da kansu suce suna so zanje in gwada sa‘a ta
kafin na bar kano zanga yada zamuyi. Sukace Allah ya
taimaka yace kasan ban sami daurin aure ba so bansan
gidansu rahama ba bare insan nasu hafsa din. Yace bari
inje in nuna maka daga nesa suka fita suna dariya ba
tare da yace komai ba shi tuni ya manta da menene a
gabanshi ko da sagir ya nuna mashi sai yace ba yanzu
zanje ba sai gobe da safe.
Ni kam tuna ranar da muka dawo daga bikin rahama
kulin shadad bashi da magana sai ta uncle dinshi tun ina
jin haushin shi ina mai fada har na dawo lallashinsa,
saboda har lokacin yana fama da zazzabi nakan
lallabashi da cewa kayi hakuri zai zo ya daukeka
ranar cikin dare har da cewa to anty kirashi a waya nace
to ka bari sai da safe yanzu yayi bacci, cikin kwana ukun
nan da kyar na samu ya manta da maganar uncle sai
jifa-jifa. Da safe yana sanye da kayan makaranta ni kuma
nayi shirin gurin aiki. Yau bani da lecture da safe don
haka gurin aiki zanje dama ka‘idar da manaja ya bani
kenan dan a daidaitanmu yana jira, shadad ya fita da
gudu ni kuma na kule dakin na fita. Ina rufe gida naji
muryar shadad yana cewa anty ga unclena anty na wai
wayo baya na datse kwado, ilai kuwa yana tsaye jikin
wata yar kyakyawar motar blue kiran kanfanin (toyota)
sanye da t-shirt da wando jeans baki, riga baka da ratsin
ja. Ta kalmin kafarshi baki ne sauciki. Na dauke fuskata
daga kalonshi bacin nayi fuskar shanu shadad wanda
tuni ya daneshi, murna yake yana cewa unclue kazone?
Da ma anty tace indaina kuka zakazo, takaici ya kamani.
Shi kuma sai ya dubeni anty antashi lfy? Ba tare da na
kaleshi ba nace kalau na daga labuln dan a daidaita na
shige. Sai naji yana cema dan a dai daitan, ungo nan
malam kaje sai bayan kwana 2 ka dawo tun da nazo ni
zan rinka kaisu kafin in tafi. Ya mika mushi yan dubu
dubu sababi fil guda 3 ya amsa yana cewa na gode
yalabai to sai zuwa yau she zan dawo yace nan da
kwana hudu haka nace sannu da karfin hali menene
gamina da kai? Da har zakaso ka min iko? Bai ce kala ba
ya juya. Na cema dan a daidaita sahu muje na leka
nacewa shadad zo mutafi ko nayi tafiyata. Mutumin ya
kaleni shima fuska a kame ki fito muje ban san sanda
nace to ubana! Sai kazo ka jani ya kara matsowa saitin
dan a daidaita yace ka sauketa katafi abinka. Sai kawai
mai a daidaita yace kiyi hakuri yar uwata, ki sauka ban
tankashi ba bankuma sauka ba,gani nayi zamuyi latti
nace yanxu kai malam haka zamuyi da kai? Duk tsawon
lokacin da muka dauka yau kace bazaka kaini ba? Yace
to Alhaji ne yace ki sauka ai, kuma ni bansan
dangantakarku ba kada in shiga hurumin da banawa ba.
Nace to bawata dan gantaka a tsakanin mu, asalima ni
ban sanshi ba da muna da alaka da baka gan shi ba ko
sau daya? Yace ki sauka mana nasan duk yanda akayi
kunsan juna. Ganin zai bata min lokaci sai na sauka na
dauki jakata nace shadad ya wuce muje, a mota yasaka
shi amma ya tada mota sukayi gaba. Na tare mai mashi
muna ciniki yazo yace mai mashi tafi abinka, in ka
dauketa zaka gamu da hukunci... kafin ya rufe baki yaja
mashin ya kara gaba. Na kaleshi nace me kake nufi
dani? Yace gurin aiki zan kaiki kawai,nace banaso dan
Allah kai mayene? Yace a'a ni ba maye bane, to bin me
kake min? Nifa ba yar iska bace. Yace nasani ai, to dan
Allah kafita hanyata, in kanawa darajar mahaifinka. Yace
don girman Allah ki shiga motar nan mu tafi, kada
shadad yayi latti, sannan inaso ki bani lokaci nazo mu
dan tautauna, nace bani da lokacin da zan iya baka, ka
fita harkata please, nacigaba da tafiya. Ranar dai a kasa
na tafi gurin aiki, shikuma sukayi wani guri shida shadad,
nasan sai dai suyi tambaya amma shadad ba zai iya
gane makarantar ba, ganin nakusa bansha wahalar hawa
abin hawa ba na karasa, takwas ta gota ina shiga ishak
yace yau bamakaranta kenan? Nace eh, gashi ma nayi
latti, musa yace manaja kuwa yazo yananan ya zagaya
ciki nasan sai yayi maki surutu, nace uhum sai dai yayi
tunda dai latti na riga nayi shi.Ina zama yana isowa, ban
ko kalleshi ba na jawo takarda dake kan teburina zan
fara duba abubuwan da suka fita da safen nan, sai ya
ce, "Kin san zaki zo da safe me yasa zakiyi latti?" Na ce,
"Abin hawa ne ban samu ba." Ya ce, "Amma ai ba'a
wahalar mai ko?" Na ce, "Kamar yaya?" Ya ce,
"Ballantana ki ce ana wuyar abin hawa." Na ce, "Akwai
abin hawa mana." Ya ce, "Baki da kudi ne?" A kagare na
ce, "Ina da shi." Ya ce, "Ok kin soma gajiya da aikin
kenan?" Na san shi sarai zai iya cewa ya koreni, kuma
dai Allah ya sani da aikin na dogara, don haka nace,
"Tunda ba halina bane lattin amin uzuri." Ishak yace ayi
mata hakuri Sir. Ya ce, "Kune kuka iya bada hakuri ita
bata iya ba ko? To ba zan mata uzuri ba, sai dai in
taimaka mata." Cikin sauri na ce, "Bana son taimakon
kowa sai na Allah, nace dai amin azuri." Ya ce, "To ki je
gida ki huta na sati 2 don ki koyi yadda zaki dinga zuwa
aiki." Muryarshi muka ji ya ce, "Uzuri za'a yi mata
manaja." Ya dubeni har na mike, "Koma ki zauna.
Manaja akwai uzuri a rayuwa, ko tana latti?" Ya ce, "A'a
ranka ya dade bata dai da mutuncine, in banda rainin
hankali tana fada min akwai abin hawa kuma tana da
kudi amma ta zo latti?" Ya ce, "Duk da haka ka mata
azuri da tace baka san dalilin ta ba, so tayi zamanta." Na
dube shi ina mamakin karfin halinsa, sai naga ya nufi
Ofishin manaja na ce kila ya san shi ne. Ni dai na zauna
na ci gaba da aikina. Ina jin Musa da Ishak suna mitar
rashin mutuncin shi.Abubakar ya dubi Manaja ya ce, "Ka
daina yiwa mutane haka, musamman na kasa da kai, a
rayuwa dole ne mutum ya dinga hakuri, yanzun kasan
uzurin da ya tare ta?" Manaja ya ce, "Yallabai yarinyar
nan bata da mutunci sam!" Ya ce, "Ko zan iya sanin
halayen ta marasa kyau?" Ya ce, "Na 1 bata da fara'a ga
kallon banza, kuma ta fi karfin kace zaka taimaka mata
sai ta hau bala'i, ina ce sakin fuska ma abu ne?" "Ni
kuma hakan ya birgeni." Abubakar ya katseshi, "Ban ga
laifinta ba, don ta kare mutuncin ta. Shi kenan sai ya
zama zubar da mutunci don bata saki fuska ba?" Manaja
ya yi 'yar dariya, "Yallabai yarinyar nan fa in ma sonta
kake ka hakura don ba zata baka hadin kai ba, in mata
kake so 'yan gayu isassu na debe kewa sai in kawo
maka su. A ina ka sauka?" Abubakar ya ce, "Na fada
maka ina son ta ne? Ko na fada maka ina son mata ne?
Inma matan nake so ai baka fini saninsu inda zan same
su ba, ina maka nasiha ne ka daina wulakanta na kasa
da kai, in dai suna yin abinda ya dace." Ya ce, "To zan
kula Yallabai -ya ci gaba da cewa- Ya hajiya? Ai mun yi
waya da ita jiya tace matake fada min kana Kano zaka
shigo ka duba abubuwan dake tafiya." Abubakar ya ce,
"Kwarai kuwa, bari in duba takardun. Fito min da su." Ya
jima sannan ya kammala ya fito, Manaja yana biye da
shi ya tsaya kusa da ni, "Ki yi hakuri kin ji ko?" Sannan
ya fita.Ni kam ban ko kallesu ba. Tunanina 1 ina ya kai
min yarona?
Lokacin tashina nayi na nufi Makarantar su Shadad na
dauke shi muka nufi gida. Tun akan hanya ya isheni da
labarin Uncle, Anty Uncle ya sai min ice-cream ya kai
min da muka yi break da su sweat, kuma ya tambayi
Auntynmu wai ina karatu? Ta ce mishi inayi sosai,
kuma ana lura dani wurin yin home work, yana ta jin
dadi. Na yi tsaki tare da cewa, "Yi min shiru." Da dare
ina Sallar Isha'i naji bugun gida, sai da na idar sannan
na nufi zauren nace wanene? Ba'ayi magana ba har
zan juya aka sake bugawa nace wanene wai? Yace
Abubakar ne. Na gane muryarshi amma sai nace, "Wa
kake nema?" Ya ce, "Shadad." Na yi shiru ina nazari,
hausawa sunce mai Da wawa, inna bar wannan
mutumin zaya fake da dana ya cutar da ni, gara in
masa rashin mutunci ko ya fita daga harkata. Na bude
kofar sannan na dogare bakin kofar, "Kai Malam! Ka
fita idona, ina ganin kimarka bana son ta kaimu ga
rabuwa fata-fata ni da kai, ina nufin in zabga maks
rashin mutunci, ka ja tsumman rayuwarka ka yi gaba,
ka fita harkar yarona, anzo za'a fake da yaro a cuceni."
Na ja tsaki tare da maida kofar garam na barshi tsaye
da leda shake da kaya.
Daga ranar ban kuma ganinshi ba, hakan ya min dadi
don haka na godewa Allah. Sai dai damuna da Shadad
keyi na kiran Uncle har da kuka. Kwana 8 bayan haka
ina ta kici-kicin girkin rana, yau lahadi sai da yamma
zan fita aiki. Tuwon shinkafa miyar alayyahu nake son
mana na gama kwashe tuwon cikin leda na zuba a kula
na samu Shadad yana home-work na ce, "Yauwa ka
zauna zanje kasuwa in dawo." Daman nakan barshi. Ya
ce, "To Anty." Ya tashi ya dauko kujerar da yake
takawa yasa sakata ta ciki.
Na nufi kasuwar don ba nisa sosai. Ban fi minti 30 ba
na dawo, sai dai me? Kofar gidan a bude, haka na nufin
Shadad ya cire sakata, a hanzarce na shiga. Takardun
shi suna gurin, takalminshi suna gurin. Kaf babu inda
ban dyba ba cikin gidan amma ban ganshi ba, da
hanzari na nufi makota duk da na san baya zuwa,,,,,
Me ke shirin faruwa da nine?
End of 1
Zaharaddeen Shomar
whatsapp 08168575100
0 Comments