SAKACI*
💍💍💍💍💍💍
💍💍💍💍💍
💍💍💍💍
💍💍💍
💍💍
💍
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
{Onward together}
*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*
*Dedicated to*
*Sa'adatu Basheer Aliyu*.
_Special gift to Haruna Umar._
*PAGE 1*
Acikin wani irin katafaren parlour ne mai k'unshe da kayan alatu ko'ina acikinsa zad tsari da k'awatuwa, matashin magidanci ne zaune saman cushion d'in dake malale cikin parlourn yayi tagumi cikin tsantsar damuwa kallo d'aya zakayi masa ka hango tsagwaron takaici da bak'in ciki cikin k'wayar idanunsa saboda sun kad'a sunyi jajir akan matsananciyar damuwa, wani irin tururin d'aci da zogi zuciyarsa keyi asanadiyar rashin samun abokiyar rayuwa ta gari, yayi shiru yana sak'e sak'e cikin zuciyarsa domin abin duniya yasha masa kai saboda matarsa Nazifa kwata kwata bata basa hak'k'insa dake rataye awuyanta ita dai babu abinda ta sawa gaba illa ta zamo hamshak'iyar mai arzik'i duk dayake babu abinda ta nema ta rasa awurin mijinta Yaseer.
Ya fad'a cikin duniyar tunani saiga sallamar Nazifa rik'e da hannun 'ya'yanta Sameer da Sameera sun shigo tsakiyar parlourn, firgigit ya dawo cikin natsuwarsa tareda had'iye wani irin abu mai matuk'ar d'aci azuciyarsa kallonsu kawai yakeyi batare da yace uffan ba, Sameer dayake yafi wayo ya iso wurin dad d'insa ya fad'a ajikinsa rungumeshi yayi cikin tsantsar k'aunar d'ansa yana shafa kansa yana murmushin da baikai zuci ba dak'yar ya bud'i baki yace"Sameer ina fatar kun samu su hajiya lafiya?".
"lafiyarsu k'alau dad sunce ma agaisheka".
Yaseer ya saukar da numfashi yana kallon Nazifa yace"ina amsawa".
Alokacin ne Nazifa ta k'araso wurinsa ta zauna tana murmushin dake k'ayatar da fuskarta tace"daddyn Sameer mun bar ka kai d'aya cikin gida kayi hak'uri wani uzuri ne ya tsayar dani"..
Murmushin dake bayyanar da tsantsar bak'in ciki da takaici yayi yace mata"karki damu Nazifa bakiyimin wani laifi ba ai Fauzeeya bata dad'e da fita daga cikin gidan nan ba".
Cire gyalenta tayi tana fuskantarsa tace"ayyah da fatar dai ta baka abinci kaci bata barmin kai da yunwa ba? ".
Yaseer ya nisa yace"gaskiya alhamdulillahi yarinyar tana iyakar bakin k'ok'arinta batada son jiki ko matsala".
"masha Allahu haka nakeson ji yanzu dai bari in shiga ciki inyi wanka in d'an kwanta na gaji sosai wlh".Ta fad'a ayangace.
"ba damuwa zaki iya tafiya".
"To".Ta fad'a tareda mik'ewa tsaye baby Sameera ta tashi tsaye tana shagwab'e fuskarta kamar zatayi kuka.
Nazifa ta kalleta cikin so da k'auna tace"babyna ya akayi ne kike fushi?".
Sameera ta zumb'ura baki tace"nima zan biki a d'aki".
"to yayi wannan ba abin fushi bane 'yata".Tana rufe bakinta taja hannun Sameera suka fice daga cikin parlourn suka nufi cikin d'akinta.
Ganin sun fice daga cikin parlourn yasa Yaseer yaja tsoki zuciyarsa sai k'una da tsantsar tafasa takeyi masa, ya rasa abinda yakeyi masa dad'i aduniya domin yana buk'atar kulawar Nazifa amma ita babu ruwanta dashi hatta da gyaran gado Fauzeeya 'yar aikinta ce keyi masa, ya rasa miyasa matarsa batada sirri babu abinda take b'oyewa Fauzeeya ta amince da ita tareda bata amana d'ari bisa d'ari.
Cikin zuciyarsa sai cewa yakeyi Nazifa batada wani amfani awurinsa daga taci ta kwanta sai neman kud'i babu abinda ta iya, shi ya rasa wace irin mace ce wadda batada sirri da kulawa arayuwa hak'ik'a ya tabbatar baiyi dace da mace ta gari ba, numfashin takaici ya sauke ya kalli Sameer yace"my boy je wurin mom d'inka ni fita zanyi yanzu".
Sameer ya mak'e kafad'arsa yace"dad zan bika muje".
Yaseer ya dafe goshinsa cikin damuwa yace"ohh ni kaina Sameer ka cika yawan damuwa".
"yi hak'uri dad zan bika".
Yaseer ya sakar masa murmushi yace"ok tashi muje d'in tunda ka matsa".
Sameer ya mik'e tsaye yayinda Yaseer yaja hannunsa suka nufi parking lot, suna isa Yaseer ya sanya d'ansa cikin mota sannan shima ya zagayo mazaunin driver ya zauna, yana zama ya danna horn getman ya wangale musu get suka fito daga cikin gidan tareda nufar gidan iyayen Yaseer.
____________________
Nazifa tana shiga cikin d'aki ta zaunar da Sameera saman gado tana kallonta, cire tufafinta tayi ta d'aura towel ajikinta ta fad'a cikin bathroom da nufin wanka ta dad'e sosai tana gurza jikinta ko'ina sannan ta fito d'aure da towel ta nufi wurin dressing mirror, kujerar dake fuskantar mirror ta jawo ta zauna ta fara shafa lotions ajikinta kayan kwalliya ta d'auko ta fara tsantsara kwalliyarta mai k'yau da gani, bayan ta gama ta ciro atamfarta orange colour ta sanya ajikinta sannan ta feshe jikinta da turare mai k'amshin dad'i.
Tana kammala shiryawa ta dawo wurin Sameera ta zauna alokacin ne baby Sameera ta kalli mahaifiyarta tace"mom kinyi matuk'ar k'yawo".
Murmushi Nazifa tayi tace"da gaske nayi k'yawo?".
"eh mom da gaske nake fad'a".
Nazifa zata sake magana kenan wayarta tayi ruri alamar ana kiranta da sauri ta d'auko phone d'inta tayi receiving tace"hello besty Safiya".
Ab'angaren Safiya ta musk'uta tace"ya kike Nazifa yasu Sameer?".
"Lafiya k'alau suke Safiya ya naki yaran?".
"k'alau suke Nazifa dama dalilin dayasa na kiraki shine sak'on kayan da muka basuwa asiyo mana sun iso yanzu saboda haka ki shirya zuwa gobe zamu had'u shago".
"OK ba damuwa Safiya kamar da k'arfe nawa zamu had'u goben?".
Safiya tayi ajiyar zuciya tace"da k'arfe takwas na safe zamu had'u".
"karki damu zanzo insha Allahu".
"OK sai anjima".
"sai anjima d'in".Tana k'arasa maganarta ta katse wayar tareda saukar da numfashi yayinda Sameera sai kallon mahaifiyarta takeyi tana murmushi.
**********************
Yaseer yana isowa bakin tangamemen get d'in gidansu ya danna horn da k'arfi maigadi yazo da gudu ya wangale masa get d'in ya kunna hancin motarsa cikin tsakiyar filin gidan,direct wurin parking lot ya nufa ya parker motarsa yana parkerwa ya fito daga cikin motar ya nufi gefen Sameer ya bud'e masa k'ofar ya fito, yana fitowa Yaseer ya sanya key ya kulle motarsa tareda jan hannun Sameer suka nufi cikin parlour.
Suna isa tsakiyar parlourn suka isko hajiya Sadiya zaune saman cushion idanunta sanye da farin glass domin ya zamo mata garkuwa, jin motsin mutane yasa hajiya Sadiya ta d'ago fuskarta ta kallesu cikin sakin fuska, suna isowa wurinta Yaseer ya gaisheta ta amsa masa cikin farin ciki da walwala yayinda taja hannun Sameer ta zaunar dashi kusa gareta tace"'k'aramin maigida kaine ka kawomin ziyara ya mom d'inka da school?".
Sameer yayi mata murmushi yace"lafiya k'alau take hajiya".
"masha Allahu ubangiji ya k'ara rufa mana asiri".
"Amin amin Ummi".Inji Yaseer bak'in ciki k'unshe cikin zuciyarsa.
Alokacin ne hajiya Sadiya ta tsurawa d'anta idanu na tsawon lokaci tana nazari da karantar abinda yake cikin k'wayar idanunsa, damuwa da tsantsar takaici ne ta hango kwance cikin k'wayar idanunsa cikin natsuwa da tausayi tace"Yaseer mi yake damunka?".
Yaseer ya marairaice fuskarsa yace mata"babu abinda yake damuna Ummi".
Hajiya Sadiya ta girgiza kanta alamar rashin yarda da maganarsa wani irin abu ta had'iye mak'wat cikin mak'oshinta mai d'aci tace"wannan maganar taka ba gaskiya bane Yaseer har kanada damuwar da zaka b'oyemin cikin zuciyarka, nifa mahaifiyarka ce aduniya babu wadda ta dace tasan matsalarka fiye dani haba d'ana ka gayamini mi yake damunka?".
Kwallar zallar takaici ne ta cika masa idanu dak'yar ya had'iye ruwan hawayensa yace"kema Ummi kinsan matsalar bata wuce Nazifa akullum batada wani buri illa taga ta samu kud'i babu wani kulawa da tsantsar soyayyar gaskiya da take nunamin, komai nawa Fauzeeya ce keyimin ta yaya rayuwa zata cigaba da kasancewa haka?".
hajiya Sadiya ta kallesa cikin tausayawa da tsantsar k'aunar d'anta bak'in ciki da damuwa ne shimfid'e afuskarta zad tausayi tace"ka cigaba da hak'uri Yaseer ubangiji yana tareda bayinsa".
Yaseer ya gyad'a kansa kamar k'adangare yace"Ummi ina iya bakin k'ok'arina wurin ganin nayi hakuri da halayyar Nazifa amma na fara gajiya da halinta na rashin nuna halin ko inkula game dani, gaskiya bazan b'oye miki ba hakuri ya fara kai k'arshe".
"subahanillah!Ka daina cewa hak'urinka ya k'are Yaseer duk abinda Nazifa takeyi maka ka daure ka cigaba da hak'uri tabbas wata rana zakaga ribar hak'urinka anan gaba, sannan kada ka kuskura ka gayawa abokinka sirrinka domin ba kowane aboki ake fayyacewa sirrin zuciya ba".
Yaseer ya girgiza kansa alamar gamsuwa da maganarta yace"to babu damuwa Ummi zan cigaba da hakuri da halayyar Nazifa da yardar Allah ni zan wuce gida".
"to shikenan ka gaidamin da Nazifa".
"zataji da yardar Allah".Yana rufe bakinsa yasa hannu cikin aljihunsa ya ciro kud'i masu kauri ya mik'awa mahaifiyarsa yace"Ummi ga wannan ba yawa ayi hak'uri sannan idan Alhaji ya dawo ki mik'a sak'on gaisuwata zuwa garesa".
Hajiya Sadiya tayi murmushi tace"ubangiji yayi maka albarka Yaseer idan Alhajin ya dawo zan gaya masa sak'on gaisuwarka,kai Sameer tashi ku tafi zuwa gida kar ya manta dakai ".
Sameer ya zumb'ura baki tareda b'ata fuska yace"ni bana zuwa anan zan zauna wurinki ".
hajiya Sadiya ta kalli Yaseer cikin matuk'ar mamakin zancen Sameer tace"kaji yace baya zuwa gidanku".
Yaseer yayi ajiyar zuciya cikin kamala yace"dama Ummi na gaya miki Nazifa batada kulawa da tarairaiyar yaranta shiyasa kikaga yace baya zuwa, saboda haka babu matsala idan yayi miki kwana biyu zanzo da kaina in d'aukeshi".
"hakan yayi Yaseer ubangiji ya kaika gida lafiya".
"Amin ya rabbi ".Yana kai k'arshen maganarsa yaja k'afafunsa ya fice daga cikin parlourn direct parking lot ya nufa wurin motarsa, maigadi yana hango fitowarsa ya wangale masa get tadda motarsa yayi ya nufi hanyar fita daga cikin gidan yayinda ya iso wurin maigadi ya ciro kud'i ya basa, godiya maigadi yayi masa Yaseer ya fisgi motarsa da sauri ya nufi unguwarsu babban amininsa Abduljalal........
_Shin ko ya zamantakewar rayuwar aurensu Yaseer zata kasance, shin Nazifa zata gyara halayyarta ta kula da mijinta Yaseer, shin wane irin k'alubalen rayuwa zasu fuskanta? Sai ku cigaba da bina sannu ahankali domin jin yadda zata kasance atsakaninsu._
_Mugirat Musa_
~I love you my fans~.🥰
. 💍💍💍💍💍💍
*SAKACI*
💍💍💍💍💍💍
💍💍💍💍💍
💍💍💍💍
💍💍💍
💍💍
💍
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
{Onward together}
*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*
*Dedicated to*
*Sa'adatu Basheer Aliyu*.
_Special gift to Haruna Umar._
*PAGE 2*
Yaseer yana isa bakin get d'in gidan Abduljalal ya parker motarsa yana zaune yayi dialling nombar abokinsa,wayar tana shiga ta fara ringing d'id'id'id'i Abduljalal yana ganin kira sunan Yaseer ne b'aro b'aro akan phone d'insa receiving call yayi yace"hello Yaseer".
Yaseer yayi doguwar ajiyar zuciya yace"kai ba wani hello ka fito daga cikin gida gani a k'ofar get d'in gidanka".
Abduljalal dayake kwance saman gadonsa yayi zumbur ya tashi zaune yace"da gaske kake fad'a kana k'ofar gidana?".
"auuu zanyi maka k'arya ko kana kusa ga madam Rufaila shiyasa ka kasa fitowa?".Yace azolaye.
Abduljalal ya mik'e tsaye tareda jawo jalabiyarsa ya sanya yace"hmmm friend baka rabo da zolaya fa bana kusa gareta to ina d'akina da nufin inyi barci saiga kiranka ya shigo".
"naji dai ina jiranka yanzun nan awaje".
"haba mizai hana ka shigo daga ciki Yaseer tunda gidan ba bak'onka bane?".
"kaga banason dogon surutu sauri nakeyi akwai abinda zanyi agida".
"OK ba matsala ganinan zuwa abokina".
K'it Yaseer ya katse wayar murmushi k'unshe afuskarsa babu wani jimawa can ya hango Abduljalal ya fito daga cikin gidan sanye da jalabiyarsa, yana isowa wurin Yaseer ya bud'e k'ofar ya shigo ya zauna yace"gani Yaseer two days ka b'oye ina fatar dai lafiya k'alau?".
"lafiya k'alau Abduljalal saidai abinda ba'a rasa ba".
Abduljalal ya mayarda hankalinsa kacokam wurin Yaseer yana masa kallon k'walelecewa can yace"mi nene matsalar Yaseer kardai kacemin har yanzu babu wani chanji daga wurin Nazifa?".
Hucin takaici yayi damuwa da tsantsar bak'in ciki ne shimfid'e afuskarsa yace"har yanzu bata chanza ba friend nidai agaskiya banyi sa'ar samun mace ta gari ba kuma bazan b'oye maka abinda yake cikin zuciyata ba tabbas nayi nadamar auren Nazifa arayuwata! ".
Abduljalal yayi wuru wuru da idanunsa yana kallon Yaseer cikin tausayi da tsantsar rad'ad'in abinda yake faruwa ga amininsa yace"ka cigaba da hak'uri Yaseer komai na duniya yanada farko yanada k'arshe tabbas wata rana zata iya yiyuwa Nazifa ta gyara halayyarta".
Yaseer yayi nishi mai tattare da bak'in ciki da takaicin rayuwa yayinda wani irin abu ya tokare masa a k'irji yace"zaiyi wuya Jalal ta gyara halayyarta saboda ta riga tayi nisan kiwo batajin kira".
Abduljalal ya dafa kafad'arta cikin tausayawa rayuwar abokinsa yace"ka daina cewa haka Yaseer saboda ba'a yanke k'auna da samun rahamar ubangiji sannan shiriya ta ubangiji ce shine mai shiriyar da duk wanda ya gadama alokacin da yaso".
Cikin gamsuwa da bayanin Abduljalal Yaseer ya musk'uta yace"haka ne gaskiya ba komai ubangiji yasa tanada rabon gyarawa".
"Amin abokina hakan ya dace ka fad'a tun farko ka rage sawa kanka damuwa da yardar Allah komai zai zama tarihi".
"zan rage Jalal nizan koma gida sai mun sake had'uwa".
"OK Yaseer ka gaidamin da madam".Yace bayan ya fito daga cikin motar Yaseer.
"zataji friend".Yana kammala maganarsa ya tadda motarsa ya fice daga cikin unguwarsu Abduljalal, yayinda Jalal yake tsaye yana kallon bayan motar Yaseer saida yaga b'acewarsa, sannan ya juya ya koma cikin gidansa wurin matarsa Rufaila.
**********************
Yaseer yana barin unguwarsu Abduljalal bai zarce ko'ina ba sai cikin gidansa ya parker motarsa aparking lot, sannan ya fito daga cikin motar ya nufi cikin parlour yana isa tsakiyar parlourn ya hango Fauzeeya budurwa 'yar shekara goma sha shida zaune saman cushion tana kallon TV show, da sallama ya shigo cikin parlourn ta amsa masa cikin sakin fuska tareda yi masa sannu da zuwa, Yaseer ya amsa mata tareda zama nesa da ita saman cushion mik'ewa tayi ta nufi frizer ta ciko masa tire da kayan mak'ulashe ta kawo ta dire agabansa, ruwa kawai ya iya sha saboda kwata kwata bayajin dad'in zuciyarsa kallo d'aya zakayi masa ka gane yana cikin matsananciyar damuwa da tsantsar buk'atar kulawar Nazifa,Fauzeeya ta koma ta zauna saman kujerar data tashi kallonsa tayi atsanake cikin ladabi tace"daddyn Sameer ko akwai abinda kake buk'ata ne yanzu?".
Numfashi ya sauke mai tattare da d'acin rai da tsantsar bak'in cikin rayuwa yace"a'a babu abinda nake buk'ata".
Fauzeeya bata sake cewa uffan ba ta cigaba da kallonta cikin natsuwa yayinda Yaseer yake kallon duk wani motsinta ta wutsiyar idanunsa, wani irin yanayi yakeji acikin zuciyarsa game da ita wanda ya kasa tantance ko miye, ganin cigaba kallonta bazai iya haifar masa da komai ba illa tunani da damuwa dole yasa ya mik'e tsaye cikin mutuwar jiki ya nufi room d'in Nazifa dake kusa ga nashi.
Yana isowa bakin k'ofar d'akinta yaji ta akulle knocking d'in k'ofar yayi yana jiran tazo ta bud'e masa k'ofar, Nazifa tana kwance ta shagala dayin charting taji ana knocking d'in k'ofarta zumb'ura baki tayi kamar zatayi kuka saboda tasan ba kowa bane illa Yaseer mijinta, dak'yar ta isa wurin door d'in ta sanya hannu ta bud'e masa k'ofar tana bud'ewa taga Yaseer tsaye yana kallonta na tsawon lokaci, can dai ta bashi hanya ya shigo ya rufe k'ofar direct wurin gadonta ya nufa yana murmushin takaici, Nazifa tayi tsaye ta rungume hannayenta saman k'irjinta tana kallon mijinta kamar yaune ta fara ganinsa numfashi ta saukar tace"daddyn Sameer ashe ka dawo ban sani ba?".
Yaseer ya kalleta da idanunsa da suka chanza colour yace"ya za'ayi kisan na dawo bayan bak'ya bani kulawar data dace ke kullum cikin fita kasuwanci sai kace gareki aka fara business ".
Nazifa taji zafin maganarsa har azuciyarta amma dayake tasan abinda ya fad'a gaskiya ne, tattaro dauriya da juriya tayi ta sanya azuciyarta sannan tace"haba daddyn Sameer ka cika yawan complain wallahi ka dinga hak'uri dani tabbas wata rana komai zai wuce kamar amafarki ".
Yaseer ya banka mata uwar harara asanadiyar haka saida d'iyan hanjin cikinta suka motsa tsoro k'arara cikin k'wayar idanunta, domin yau ta hango masifa kwance afuskarsa cikin tsinkewar zuciya da fargaba yace" kullum kullum haka kike fad'a Nazifa komai zai wuce kamar amafarki sai yaushe abin zai wuce ki bani kulawa da tsantsar soyayyar gaskiya? Na gaji ina buk'atarki kusa gareni matata ni kad'ai nasan yadda nakeji adalilin rashinki akusa dani ki taimakawa rayuwata ki bani abunda nakeso ".
Nazifa ta langwab'e kanta tayi narai narai da idanunta tace"dan Allah Yaseer ka daure kayimin uzuri na zuwa tsawon lokaci da yardar Allah zan baka tsantsar kulawa na musammam fiyeda misali".
Yaseer ya d'aga mata hannu cikin tsananin takaicin maganarta yace"na gaji da yawo da hankalin da kikeyimin Nazifa akullum bakida burin daya wuce kiga rayuwata ta b'aci, bakida wani fata illa kiga na kasance cikin matsananciyar damuwa da tsantsar bak'in cikin rayuwa".
"ka fahimceni mana mijina.......... ".
Katse mata magana yayi yace"bazan tab'a fahimtarki ba Nazifa har sai kin dawo kamar yadda nasanki afarkon aurenmu".
Nazifa tayi shiru cikin haushinsa domin ita arayuwarta ta tsani mutum mai yawan damuwa da tsantsar ganin laifi, can ta d'ago fararen idanunta tace"gaskiya nace maka ka bani lokaci zanyi tunani akai".
Yaseer ya mik'e tsaye ya nufi wurinta yana isa kusa gareta gab da gab yadda zasuji numfashin juna, kallonta yayi ya kauda kansa gefe domin idan ya cigaba da kallon wani irin tururin d'aci da zogi zuciyarsa keyi dak'yar ya furta cewa"tunda bazaki bari mu fahimci junanmu ba Nazifa taurin kanki ya hana ki saurareni to ki sani duk abinda ya biyo baya banida laifi !".
Nazifa tayi saurin kallonsa cikin matuk'ar mamakin maganarsa tace"babu abinda zai biyo baya sai alkhairi daddyn Sameer".
Yaseer bai sake cewa komai ba yaja k'afafunsa ya dawo cikin parlourn ya zauna, koda yazo ya iske Fauzeeya ta kwanta rigingine, santala-santalan cinyoyinta awaje dayake ita kadaice cikin parlourn jin motsin mutum yasa dole ta gyara sicket d'inta, shiru ne ya biyo baya ak'arshe saida Yaseer ya d'auko newspaper yana duddubawa ko damuwar dayake ciki zata ragu yayinda Fauzeeya ta tsurawa k'yak'k'yawar surarsa idanu tana yi masa kallon k'urilla,shidai bai lura da ita ba abinda yasha masa kai kawai yakeyi .
Fauzeeya sai kallonsa takeyi tana k'udurta abubuwa da dama cikin zuciyarta wani irin shauk'in soyayyarsa da tsantsar k'aunar Yaseer sai fisgarta yakeyi, burinta bai wuce ace ya furta mata kalmar so ba amma tasan hakan yanada matuk'ar wuya wai gurguwa da auren nesa.
*********************
Nazifa ce naga tayi wanka bayan sallar isha'i ta ciro kayan barcinta masu shara shara yayinda su Sameer suna d'aki daban wanda suke barci suda Fauzeeya,kwantawa tayi saman k'asaitaccen gadonta ta fara karanto addu'o'in neman tsari daga sharrin masu sharri ta jima tana kwararo addu'o'in sannan daga baya ta shafa afuskarta ta jawo blanket d'inta ta lullub'e ko'ina ajikinta, ta lumshe idanunta kenan ta fara barci saiga shigowar Yaseer cikin d'akinta sanye da kayan barcinsa mara nauyi jikinsa sai tashin k'amshin turarensa yakeyi, direct wurin Nazifa ya nufa yana isa wurinta ya zauna saman gadon yana murmushin dake k'ayatar da fuskarsa ya shafi gefen fuskarta tareda kwantawa ya rungumota ajikinsa, jin ta fad'a ajikin mutum yasa ta falko dayake batayi nisa cikin barcinta ba.
Ganinsa kusa gareta yasa Nazifa ta yamutsa fuskarta ta jaye jikinta daga nasa Yaseer ya jawo hannunta ya sanya cikin nasa yace"lafiya kike wani jaye jikinki anawa kamar kin fini? ".Nazifa tayi hamma alamar barci ne ke cikin idanunta tace"ka tafi zuwa d'akinka barci nakeji daddyn Sameer ".Yaseer yayi mata wani irin kallo mai nuni da bata isa ba cikin kakkausar murya yace"babu inda zanje ayau sai kin bani hak'k'ina dake rataye saman wuyanki Nazifa kina cutar da rayuwata kina cin amanata wannan sauyin yanayin da kike nunamin ya isheni! ".
Dummmm taji fad'uwar gaba ya ziyarceta wani irin abu ne ya tokare mata a k'irji cikin tsinkewar zuciya da tsantsar fargaba tace"wai miyasa kakeson b'atamin rai Yaseer waikai wani irin mutum ne da baya gajiya dayin abu d'aya? ".Yaseer yayi murmushin dake bayyana hak'ora yace"haka zaki fad'a kice bana gajiya dayin abu d'aya alhalin rabon daki bani hak'k'ina na auratayya harna manta Nazifa, nifa cikakken namijne lafiyayye dole in buk'aci mace amma miyasa kikeson jefa rayuwata cikin had'ari!? ".
Nazifa ta aza hannunta saman kai tace"kayyyy Yaseer nifa gaskiya ban faye son namiji mai yawan buk'ata ba dan Allah ka rabudani barci nakeson yi".Cikin d'acin rai da zafin kalamanta yace"hmmm rayuwarki tana bani matuk'ar mamaki Nazifa ki kalli tsabar idanuna kicemin na faye yawan buk'ata alhalin ko hak'k'ina bak'ya bani "."Naji dai bana baka kaje wurin wadda zata iya baka abunda kakeso nifa ka dameni zaka sani ciwon kai! ".Yaseer ya tashi tsaye yana girgiza kansa cikin jimami da tsantsar takaici azuciyarsa yace "shikenan zan wuce in barki kiyi barci Nazifa sannan ki sani duk abinda kikeyi ubangiji yana sama yana kallonki ".Yana rufe bakinsa yaja k'afafunsa ya fice daga cikin d'akin fuskarsa k'unshe da tsantsar b'acin rai da bak'in cikin rayuwa..............
💍💍💍💍💍💍
*SAKACI*
💍💍💍💍💍💍
💍💍💍💍💍
💍💍💍💍
💍💍💍
💍💍
💍
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
{Onward together}
*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*
*Dedicated to*
*Sa'adatu Basheer Aliyu*.
_Special gift to Haruna Umar._
*PAGE 3*
Yaseer yana fita daga cikin d'akin Nazifa ya fad'a cikin d'akinsa cikin zafi da k'unar zuciya akan yawan damuwa har wani irin duhu duhu yake gani cikin idanunsa, dak'yar ya kwanta saman gadonsa yayinda hawayen nadama da takaicin Nazifa suka dinga sintiri asaman k'yak'k'yawar fuskarsa,wani irin tururin d'aci da zogi zuciyarsa keyi ya rasa miyasa Nazifa ta kasa fahimtarsa ya rasa miyasa bazata bashi kulawa shida yaransa ba,ya rasa abinda ta nema ta rasa acikin gidansa dazai sa ta dinga neman kud'i har ya zamo sanadiyar tarwatsewar farin cikin gidansa dana yaransa.
Juye-juye ya dingayi saman gadon zuciyarsa cunkushe da tsantsar bak'in ciki da damuwa ya rasa miyake masa dad'i aduniya,hak'ik'a yayi nadamar auren Nazifa arayuwarsa saboda bata nuna masa tsagwaron k'auna da tsantsar *SOYAYYAR GASKIYA* blanket ya jawo ya lullub'e jikinsa yanata faman tunane-tunane dak'yar ya samu barci mai nauyi yayi awon gaba dashi.
____________________
Washe gari da safe misalin k'arfe shida da rabi 6:30am na safe Fauzeeya ta farka daga barci bayan sallar asuba, ta fad'a kitchen ta had'a breakfast ta d'auko komai ta jajjera saman dinning table, sannan ta nufi cikin d'aki ta shiga cikin bathroom tayi wanka direct wurinsu Sameer taje ta tayardasu daga barci, Sameer ta fara shiga dashi cikin toilet tayi masa wanka sannan tazo ta dauk'i Sameera tayi mata wanka tass tareda lullub'e mata jiki da towel, itace ta shiryasu cikin school uniform d'insu sky blue and white itama ta shirya cikin uniform d'inta na secondary school, tana kammala shiryawa taja hannunsu suka nufi dinning table anan suka isko Nazifa da Yaseer suna yin breakfast babu mai magana daga cikinsu..
Fauzeeya ta jawasu Sameer kujera suka zazzauna sannan itama ta zauna serving d'insu tayi suka fara yin breakfast,sun d'an jima suna cin abincin atsanake cikin kwanciyar hankali sannan daga baya suka jaye hannayensu alamar sun k'oshi, alokacin ne Yaseer ya kalli agogon dake mak'ale ahannunsa yace"kun shirya kufa nake jira".
Fauzeeya tace"eh mun shirya".Tareda rik'e lunch boxes biyu nasu Sameer ahannunta.
Nazifa ce ta wurga mata harara kamar idanunta zasu fad'o daga cikin idanunta tace"Fauzeeya ina zakije alhalin baki kammala gyaramin bedroom d'ina ba?".
Fauzeeya ta marairaice fuskarta kamar zatayi kuka saboda tasan ba k'aramin aikin Nazifa bane ta hana mata zuwa school, cikin tattausan lafazi tace"kiyi hak'uri Aunty idan na dawo anjima zan gyara miki".
"yanzu nakeson kije ki gyaramin kafin jikinki ya gaya miki anjima".
Yaseer dayake rik'e da briefcase d'insa kamar bazaiyi magana ba amma ganin tana son b'ata musu lokaci dole yace"ki bari idan ta dawo daga school ta gyara miki idan bazaki iya barin ta dawo ba ki gyara da kanki ai kinada hannuwa".Yana k'arasa maganarsa ya tisa k'eyarsu Fauzeeya agaba suka nufi parking lot.
Kukan motar Yaseer taji alamun sun fice daga cikin gidan kenan Nazifa ta musk'uta cikin takaicin abinda Yaseer yayi mata tace"zaki zo ki sameni saina ci ubanki Fauzeeya!".Tana kammala maganarta taja k'afafunta ta shige cikin d'akinta batare data tsaya gyara bedroom d'inta ba ta fad'a bathroom sharp sharp tayo wanka ta fito d'aure da towel ajikinta, wurin mirror ta nufa ta jawo lotions ta shafa kayan kwalliya ta d'auko ta tsantsara kwalliyarta mai k'yau sannan ta ciro lace light brown colour ta sanya ajikinta fitted gown ce, takalmi da gyalenta duk kalarsu d'aya ta sanya handbag d'inta ta rataya a kafad'arta tareda jawo k'ofar d'akinta ta rufe.
Parking lot ta nufa direct domin taje gidan k'awarta Safiya maigadi yana hangota ya wangale mata k'ofar get d'in, Nazifa ta sanya key ta bud'e motar ta shiga cikin yanga tadda motarta tayi ta fice daga cikin gidan da masifaffen gudu kamar zata tashi sama, hanyar unguwarsu Safiya ta nufa domin atare suke yin harakar kasuwancinsu cikin rufin asiri.
Ta jima tana tafiya cikin motarta har ta iso bakin get d'in gidan mijin Safiya wato Haidar awaje ta parker motar,sannan ta fito daga cikin motar rataye da handbag d'inta a kafad'a sanya key tayi ta kulle motar ta isa wurin get d'in ta bud'e k'ofar ta shiga cikin tsakiyar filin gidan, babu kowa afilin gidan direct ta shiga cikin tsakiyar parlour hango Safiya tayi zaune tana dudduba kayayyakin da aka aiko musu irinsu dogayen riguna, handbags, shoes, hijabbai, turaren d'aki dana fesawa ajiki da dai sauran kayayyakin da ba'a rasa ba.
Jin takun tafiyar mutum yasa Safiya ta d'ago idanunta suka fad'a cikin na Nazifa zumbur ta mik'e tsaye ta iso wurinta ta rungumeta, fuskarta k'unshe da farin ciki mara misaltuwa dak'yar suka jaye jikinsu ana juna Safiya taja hannunta suka iso saman cushion suka zazzauna, suna zama Safiya ta kalleta cikin fara'a tace"'k'awata kinsha hanya bari in kawo miki ruwa ki jik'a mak'oshinki".
Zata mik'e kenan Nazifa ta rik'eta tace"ki barshi kawai Safiya bana jin k'ishirwa".
"ayi haka k'awata?".
"ba komai ni nace ki barshi".Inji Nazifa yayinda take gyara zamanta.
Safiya ta k'ara bud'e kayayyakin tana kallon fuskar Nazifa tace"kinga kayayyakin da aka kawo mana sunyi matuk'ar k'yawo sosai".
Nazifa tayi murmushi tace"gaskiya sunada k'yawo ba laifi".
Safiya ta numfasa tace"yanzu dai bari in d'auko gyalena mu wuce can shago gaba d'aya domin na fahimci ke ashirye kikazo".
Nazifa ta musk'uta cikin yanayin damuwa tace"kedai Safiya wani abu ke damuna cikin raina wallahi".
Safiya ta tattaro natsuwarta ta mayar kacokam wurin Nazifa cikin sanyin jiki tace"ayyah k'awata mi yake damunki?".
Nazifa ta marairaice fuskarta kamar zatayi kuka tace"Yaseer ne yake yawan damuna akan bana bashi kulawa shida yaransa na rasa yadda zan b'ullowa al'amarin".
Safiya ta yamutsa fuskarta tareda bintsire baki tace"bak'ya bashi kulawa yake fad'a to mi yakeson kiyi masa? So yake ki zauna gida kada kiyi sana'a ki nemi na kanki inyaso sai abinda ya gadama ya baki, ki daina damar da kanki akan maganarsa saboda kwata kwata wannan maganar bata ko kawo kallo ba! ".
"hmmmmmm kedai Safiya harda cewa yakeyi duk abinda ya biyo baya in kuka da kaina".
"dallah shareshi babu abinda zai biyo baya sai alkhairi".
Nazifa tayi ajiyar zuciya tace"shikenan k'awata zan dinga shareshi".
"aiko ni da kike gani Nazifa mijina Haidar yashamin complain akan in daina wannan business d'in in tsaya in kula dashi da yaranmu na nuna masa nikam bazan iya daina business d'in dayake kawomin kud'i ba, yacemin kenan nafison kud'i akansa na shareshi har ya gaji da ji nini ya k'yaleni".
Nazifa ta rik'e baki tace"ashe kice kema mijinki ba baya ba wurin complain ubangiji yayi musu sauk'i".
"ai duk jirgi d'aya ya d'aukosu Nazifa bansan dalilin dayasa mazan yanzu basa son cigaban matansu ba".
"haka suke mafi akasarinsu yanzu dai je ki d'auko mayafinki mu wuce zuwa shagon".
Safiya ta mik'e tsaye tace"to bari in shirya".Tana rufe bakinta ta nufi d'akinta domin ta yafa mayafinta da shigarta cikin d'aki, ta shafa powder tareda feshe jikinta da turare sannan ta yafa mayafi kalar kayanta ta fito daga cikin d'akin ta iso wurin Nazifa dake zaune tana jiranta, tana isa wurinta ta kalli Nazifa tace"na shirya wuce muje ko".
Nazifa ta mike tsaye suka fito daga cikin parlourn direct bakin get suka nufa inda Nazifa ta parker motarta, sanya key Nazifa tayi ta bud'e motar sannan suka shiga ciki suka zazzauna tareda tayarda motar suka d'auki hanyar da zata kaisu katafaren shagonsu.
____________________
K'arfe biyu daidai Fauzeeya ta dawo daga school yayinda ta iskosu Sameer wad'anda suka dawo tun k'arfe d'aya dai-dai, tana dawowa uniform d'inta kawai ta cire ta d'aura towel ajikinta sharp sharp ta watsa ruwa ta fito daga cikin bathroom d'in doguwar rigarta ta sanya mai adon stones red, sannan tayiwasu Sameer wanka ta shiryasu cikin kayansu masu k'yawo direct kitchen ta nufa tana kichaniyar had'a musu abinci shinkafa da miyar stew taji naman kaza k'amshin girkinta duk ya gauraye cikin gidan gaba d'aya.
Ta dad'e tana k'ok'arin ganin abincin ya dahu yana dahuwa ta juye shinkafar cikin kula madaidaiciya miyar ta zube cikin k'aramar kula, sauran kayayyakin data b'ata ta wankesu tasss ta adanasu a ma'adaninsu wanke hannuwanta tayi cikin ruwa masu tsabta, sannan ta d'auki kulolin ta nufi wurin dinning table dasu ta jajjera samansa sannan ta shiga cikin d'akin ta iskesu Sameer sunata wasanninsu.
Kallonsu tayi cikin sha'awa tace"ku tashi muje kuci abinci yarana".
Atare suka mimmik'e tsaye sukace"to Aunty Fauzeeya".
Fauzeeya taja hannunsu suka nufi cikin parlourn direct wurin dinning table suka isa suka ja kujeru suka zazzauna tareda jawo plate agabansu,serving d'in kowa tayi itama ta zauna ta fara cin abinci ci sukeyi atsanake har suka kammala cin abincin suka xare hannayensu, Fauzeeya ta tattaro plates d'in taje ta wankesu tasss akitchen ta adanasu cikin kwando.
Dawowa wurinsu tayi taja hannunsu suka dawo parlour suka zazzauna Fauzeeya ta kunna musu TV suka fara kallo, sun jima axaune saiga sallamar Yaseer ya shigo hannunsa d'auke da briefcase su Sameer suka shek@o da gudu suka fad'a ajikinsa suna yi oyoyo oyoyo daddy, dak'yar Yaseer ya jayesu ajikinsa yaja hannunsu suka iso saman cushion ya zaunar dasu Fauzeeya tayi masa sannu da zuwa ya amsa mata agajiye, direct room d'insa ya nufa domin ya watsa ruwa ajikinsa yaji sanyi ya jima kad'an sannan ya fito da towel d'aure a k'ugunsa, yana fitowa ya nufi wurin wardrobe ya d'auko lotions d'insa yana shafawa ajikinsa yana lumshe idanu yana kammala shafawa ya zura jallabiyarsa ajikinsa, ya d'auko laptop d'insa yana operating d'inta yana daddannawa yana yin wani aiki bai jima da farawa ba saiga Fauzeeya ta shigo cikin d'akin da sallama abakinta hannunta rik'e da tiren abinci, tana isowa wurinsa ta aje tiren agabansa tace"ko akwai abinda kake buk'ata?".
Sai alokacin ne Yaseer yasan ta shigo dago fuskarsa yayi amurtuk'e yace"waye ya baki iznin shigowa d'akina idan ina ciki Fauzeeya!?".
Jikin Fauzeeya ya d'auki k'yarrrma da mazari gabanta sai bugawa yakeyi da k'arfi tace"kayi hak'uri daddyn Sameer ganin nayi ka dawo agajiye shiyasa nace bari in kawoma abinci maybe kana jin yunwa".
"Dakata! Nine nace miki ina jin yunwa? Nasha gaya miki duk lokacin da ina cikin d'aki ki daina shigowa ki bari har saina fita sannan ki shigo, idan badan inada sakaryar mata ba wane matsayi kikedashi awurina da har zaki shigomin d'aki ki daina please banason shisshigi".Fauzeeya ta langwab'e kanta tayi narai narai da idanu tace"haba yah Yaseer don kawai na kawo maka abinci shine nayi laifi to kayi hak'uri bazan sake ba kaji, banason rayuwarka ta b'aci asanadiyyata saboda haka bazan sake ba ".Tana k'arasa maganarta ta fice daga cikin d'akin.
Yaseer yayi shiru na tsawon lokaci yana nazarin maganarta can dai ya saukar da numfashi yace"hmmm Fauzeeya bazaki tab'a gane dalilin dayasa banason ki kusanceni ba ni kad'ai nasan abinda nakeji cikin zuciyata".Yana rufe bakinsa ya cigaba da aikinsa har ya kammala sannan ya jawo plate ya d'ibi abincin yana tsakura kad'an kad'an, can ya tsame hannunsa yasa ruwa ya wanke hannunsa leda ya bud'e ya ciro hollandia yasha domin yaji sanyin cikin zuciyarsa,yasha rabi ya ajiye sauran ya kwanta yanata tunanin rayuwarsa ta baya alokacin dayake cikin kwanciyar hankali da farin ciki, alokacin da baisan miye matsalar rayuwa wani irin yanayi yakejin kansa mai wuyar fassaruwa shi kansa yasan shi namiji ne mai yawan buk'ata da son akula dashi amma babu yadda zaiyi saboda baiyi dace da mace ta gari ba.........
0 Comments