SAHAL DA SAHALA haysa novels complt

 💞💞

💞💞

*SAHAL DA SAHALA*



*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


*written by*

Shamsiyyah salis


*Edited by*

Ayusha Iliasu musa


*Dedicated to*

Ayusha iliasu 

    Nd 

Haima (mmn abul)


  *1-5*


*Bismillahi rahmanir rahim*


A guje ta fito daga cikin dakinsu tayo falon su,karon da taji tayi da mutum ne yasa tai saurin tsayawa, tare da dafe goshinta  runtse idon ta tayi saboda azabar da goshin ke mata, cikin masifa da tsiwa ta fara magana:

  "Wannan wani  irin wulakanci ne mutum na tafiya baya kallon  gab......."

Maganar ce ta tsaya sanda tai ido hudu da wanda ke tsaye a gabanta shima din dafe da goshinsa, 

Cikin kuka ta fara magana:

 

"Yaya dan Allah kai hakuri wallahi Allah bnsan kai ba......."

Dukan da ya kaimata a baki ne yasa ta yin shiru tare da dora hannunta a bakinta,


"Ke wace iriyar mahaukaciya ce, ke kwata kwata bakya abu da nutsuwa, kuma saboda baki da mutunci kin bige mutum baza ki tsaya ki ga wa kika buge ba zaki hau masifa, ke ga fitsarariya koh? 

 Ya fda yana jan kunnenta,

Zafin da taji a kunnenta yasata sakin kara ba shiri,

"Kut lalaima yarinyar nan sbda baki da mutunci tin kafin ma na dakeki shine zaki fara yi wa mutane kara haka, aiko yau zaki fadawa mai garin ku"

Ya fda lkcn da yake janta tsakiyar falon,


"Me zan gani  *sahal* kai wai me yasa mugu ne, yanxu da sanyi safiyar nan zaka fara yiwa yarinya mugunta" wata mata datijuwa dake fitowa daga cikin wani daki ta fda fuskarta a hade,


"Ummi fah bigeni tayi kuma zata fara min rashin kunya sbda bata da kirk....."

"Kaga yimin shiru ni wlh ko da wasa naji ka kara cewa yarinyata bata da kirki Allah ranka sai ya baci" 

Ummi ta fda cikin bacin rai,

Hannun yarinyar taja suka bar falon,

Sahal kan ba karamin bacin rai ya shiga ba ganin yadda ummi ke ta sirfa mashi fada akan yarinya yar karama, ganin bazai iya jurewa ya sa shi fita daga falon ya dau motarsa ya fice ya bar gdan.


Kan gado ta zaunar da ita, sannan itama ta zauna tare da kwanto da ita jikinta"Sahala ki bar yima sa rashin kunya kinga bbu kyau in ki kaima babba abu sai kina bashi hakuri kinji diyata" 

"Ummi bazan kara ba, yanxu ma bansan na bigeshi" sahala ta fda lokacin tana dagowa daga jikin ummi,


"Yauwa yar albarka, Allah yay miki albarka, tashi kije kiyi wanka"


"Toh ummi na", sahala ta fda ta mikewa ta fice, murmushi ummi tayi ta bi bayanta dan fara yin aikin gda,


Sahal kan na fita ya wuce gdan abokinsa bashi ya dawo gda ba sai la'asar, dakinsa ya wuce kai tsaye, wanka yayi ya canza kaya sannan ya kwanta


*washe gari*


Washe gari ya kama monday, tin karfe bakwai da rabi sahala ta gama shirinta tsaf na tafiya makaranta a falo ta tadda ummi tana shirya abinci a dining, cikin girmamawa ta gaida ummi, 

Fuska a sake ummi ta amsa mata gaisuwarta,


"Dota har kin gama shirin muje ki ci abinci"

Ummi ta fda tana janta zuwa dining, ummi ce da kanta ta zuba mata abinci sannan ta fara ci

Abba ne ya fito daga dakin sa ya nufo su a dining, tin kan ya karaso sahala ta fadada murmushinta, shima murmushin yake mata

"Yar gdan Abba yau har kin shirya da wuri haka" 

Abba ya fada yana dafa kanta,


"Kasan ai yar tawa ta fara girma ta kara hankali sosai"  

Murmushi kawai Sahala tayi ta cigaba da break fast dinta, sai da ta koshi sannan Abba ya sauketa a bakin makarantarsu

LAMIDO INTERNATIONAL SCHOOL (Havana collage) dake unguwar tarauni u.d.b road

Yana sauketa ta daga mashi hannu tai cikin makaranta,

Bayan an gama Assembly sannan suka shige aji



```ina yima kowa da kowa barka da sallah da fatan anyi sallah lpya Allah ubangiji ya karbi ibadunmu da mukai ```




By

*shamsiyyah salis*





💞💞

💞💞

*SAHAL DA SAHALA*



*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


*written by*

Shamsiyyah salis


*Edited by*

Ayusha Iliasu musa


*Dedicated to*

Ayusha iliasu 

    Nd 

Haima (mmn abul) 


*6-10*


Suna Shiga aji ta wuce layin baya, ta shiga tsakiyar wasu manya daga gani sun girmemata da shekara biyu zuwa uku,


"Litle ya akai kika ki zuwa da wuri haka gashi munsha hira bakya nan" 

Daya daga cikin yan matan ta fda tana kallonta,

Harara 🙄🙄🙄ta wulla mata cikin fitsara ta fara magana,


"Sai ki fdan wanda baizo da wuri ba, yar rainin hankali ina ga duk na rugaku zuwa, kawai dai ba kuje assembly bane yau"


"Allah baki hakuri me yay zafi haka zaki fara masifa" yarinyar ta fda tana taba kafadar sahala,


"Shike nan yanxu ya wuce sai ku bn lbrin da kukai bana nan" 


"Kin ma isa ai lbr ya Riga ya wuceki sai dai ki jira na gaba" dayar  da ba tai magana ba ta  fda tana dungure mata kai,


"Kinga khady ba da ke nake ba bare kimin wulakqnci" ta fda tana turo karamin bakin ta,


"Allah baki hkri little ai bn isa na hana a baki lbri ba kuma yau din ai ni nazo da lbrin ba zee ba" ta fda tana murmushi,

Murmushi sahala tayi

" da gaske kike khady?" 

Murmushi tayi tare da daga mata kai alamar eh,


"Jiya zani gdan su zee na hadu da wani hadadan guy, har shopn ma ya kai mu ni da zee din"😳😳😳

Zaro ido sahala tayi cikin mamaki, 


"Da gaske kike?"

"Na taba yi miki karya ne bari ma kiga naki tsarabar" khady ta fda tana fito da chocolate daga cikin jakarta masu yawa,


"Wow wannan kayan duk nawa ne ni kadai" sahala ta fda lkcn tana taba su,

"Amma gaskiya sun min yawa sai dai ki bar min a jakarki sbda in ummi ta gani nasan zata min fda"


"Ke wallahi bnza ce ki boyesu a cikin kayanki, in yaso ki nunawa ummi leda biyu, kice mata baban kawarki ne yay tafiya shine ta kawo miki tsaraba" zee ta fda tana samata chocolate din cikin jakarta ihu sahala tayi suka tafa  ita da zee, "shi yasa nake sanki zee badai dabara"

Dariya suka sa gaba daya .


Malamin da ya shigo ajin su ne yasa sahala saurin shiga kasan benci, a hankali take rarafawa tana wucewa ta gefen kafafun mutane, suna jin ta ba wanda ya kulata inda sabo sun saba da halinta dan kwata kwata bata zama a gaba sai dai inda malami a cikin ajin yana fita zata bi ta saman benci ta koma baya, a haka ta iso har  bencin ta dake gaba sannan ta fito ta zauna 

Bayan an tashi suka jero tana tsakiyarsu suna tafe suna shewa, musamman *sahala* dan jin ta take cikakiyar buduwar, duk inda suka wuce sai an musu dariya sbda kan kantar ta a cikin su a haka suka karasa gate  kowa ya kama hanyar gda



Kwance yake kan doguwar kujerar dake falon, ya mai da hankalinsa ga wayarsa ga dukkan alamu chrtn yake kuma yana jin dadin chrtn din,

Banko kofar da yaji anyi an shigo ba tare da yin sallama ba yasa  shi saurin dago kansa, 


A gajiye ta shigo tare da fadawa daya daga cikin kujerun falon, tsawar da taji an mata ne yasa lura da wanda ke cikin falon, nan take hanjin cikinta ya fara motsawa


"Ba magana nake miki ba nace kixo nan" *sahal* ya kara mai maita maganar ransa a hade, 


    A hankali ta taso ta fara tafiya kamar kwai ya fashe mata a ciki, kusa da kafafunsa ta tsugunna tare da sunkuyar da kanta kasa


    "Ke wace irin mahaukaciyar yarinya ce, sbda baki da hankali baki san me kike ba shine zaki na shigowa mutane gda bbu sallama" ya fda yana jan kunnenta, 


  Hanunsa ta rike ta fara magana kamar zatai kuka "yaya dan Allah kai hakuri wallahi mantawa nayi,amma bazan kara ba"


   "Munafuka kin iya bada hakurin munafurci tashi ki ban waje kan naci miki mutunci" ya fda yana sakin kunnenta


  Yana sakin ta tai dakinta da gudu, tana shiga ta fda gado, "Allah ya isa na mugu kawai, kuma wallahi sai an kara rashin jin ta fda tana murguda baki" kayanta ta cire ta shiga wanka


 Cikin mintunan da ba su wuce ashirin ba ta shirya tsaf cikin doguwar riga blue iya gwiwa sannan ta fito falo, har lkcn yana kwance a inda ta barsa, sallama tayi, ya amsa ciki ciki ba tare da ya kalleta ba


 "Wannan ai wulakqnci ne sai mutum baiyi sallama ba ace bai yi ba kuma yayi anki a amsa masa" *sahala*ta fda tana karasawa kan dining


  Cikin bacin rqi ya fara magana " da uban wa kike wanan maganar"Mutuwar tsaye tayi ba tare da ta juyoba, dan kwata kwata batayi zatan maganar ta ta fito fili ba, 


  Sallamar da aka yine ya sashi boye fishin sa dan baya san abinda za a masa fda "ummi sannu da zuwa" *sahal* ya fda yana mikewa, sai a lkcn *sahala* ta lura da shigowar ummi, da gudu ta je ta rungumeta 

  "Sannu da zuwa ummi" yauwa ummi ta fda tana dagota daga jikinta, sun dan taba hira sannan ta shige daki,  shima ya fice



By

*shamsiyyah*




💞💞

💞💞

*SAHAL DA SAHALA*



*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


*written by*

Shamsiyyah salis


*Edited*

Ayusha Iliasu musa


*Dedicated to*

Ayusha iliasu 

    Nd 

Haima (mmn abul) 


  *11-15*


 Da daddare bayan sun gama dinner suna hira abba ya kalli *sahala* cikin kulawa " Dota when zaku fara junior waec dinku?"

"Nan da two weeks Abba" "Allah nuna mana lkcn, ki dage da karatu in ba haka ba aure zan miki kuma baza ki zama likitan da kike san zama"

"Insha Allah Abba zanyi karatu"

"Allah yasa dota" 

"Amin" ummi ta fda, 

Tinda Abba da *sahala* suka fara magana *sahal* ke ta faman tabe baki, yana mamakin yanda Abba ke zama yana hira da wanan yarinyar, maganar Abba ce ta katse mashi dogon tinanin da ya tafi

 

 " *Sahal* karshen watan nan zaka tafi karo karatunka india, sai ka fara shiri, kuma in kaje ka kula bnda wasa ka rike mutunci addininka da mutuncin iyayenka tare da tarbiyar da muka baka"


"Insha Allahu zan kula Abba a shigaba dayi mana addu'a,"A haka taron ya watse cikin jin dadi kowa ya wuce dakinsa.



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su *sahala* an fara jarabawa cikin ikon Allah, *sahal* kuma saura sati daya ya tafi india, sosai yake shirin  tafiya 


Kamar kullum *sahala* ta dawo daga jarabawa a gajiye, da sallama ta shigo falon bbu kowa, haka yasa ta nufi dakinta kai tsaye, wanka ta shiga tayi sannan ta fito kitchen dan samun abinda zata ci, 

Ganin girkin da ummi tayi bai mata ba yasa ta yanke shawarar dafa indomie, hadi tayi  indomie taji kifi da nama sosai, tana  gama girkawa ta juyeta a plate, 


 Da sallama ya shigo falon, kamshin da ya doki hancinsa ne yasashi lumshe idonsa, a hankali ya fara tafiya har ya isa kofar kitchen, ganin wadda ke dauke da abinci a hanunta ya sashi bata fuska shi a dole babba .


 "Ke ina ummi take?"

Ya fda fuskarsa a hade bbu dariya,"Bata nan taje unguwa, nima da na dawo bn tadda ta ba," ta fda cikin rawar murya, Harara ya wula mata,Sannan ya fara magana cikin isa 


"Me aka girka a gdan?" Ya tambaya yana bude flask din abincin, ganin abincin dake flask din yasa yaji ba dadi, gaskiya indomien hanunta yake shaawa, sannan yaga alama kamar ba ita akayi ba da kanta ta dafa, toh taya zaice ta girka masa shima? Shi kadai yake maganar sa a zuciya, ganin tana neman fita daga kitchen din yasa shi saurin nutsuwa

 

"Uban waye ya sallame ki da za ki fice ba tare da na umarce ki ba" ya fda yana hade girar sama da kasa "Yi hakuri yaya wallahi yinwa nakeji shiyasa, kuma ni bnsan me zanmaka ba yanzu"


Murmushi yayi, wanda ni kaina da nake dakko muku rahoto narasa murmushin me yakeyi nai


A hankali ya fara tafiya har ya karaso inda take, sosai jikinta ya fara rawa dan ba karamin tsoran sa take ba musamman yanda taga yayi wannan murmushin


"Yinwa kika ce kina ji ba, toh mikon abincin hanun naki, shi zanci, inyaso sai ki ci wancan, sbda kar yinwar ta kasheki"


"Yaya wallahi ban sha'awar wancan abi......."  Tsawar da ya daka mata ne yasata mika mashi abincin ba shiri, dariyar mugunta yayi sannan ya fice daga cikin kitchen din


 Kuka sosai *sahala* tayi ganin kukan bbu inda zai kai mata yasata goge hawayenta tq fara shirin dora wata, kafin ta gama dahuqar indomie tai ma *sahal* Allah ya isa yafi sau dari, tana gama girkawa ta juye a faranti tayi dakinta, ko kallon falon batayi ba bare ta ga wanda yake wajen



Yau ya kama tafiyar *sahal* india, tin jiya da daddare ya gama hada komai nasa na tafiya, sun dade da abba yana masa waazi, 

A bangaren *sahala* kuwa murna take sosai yau zatai kwanan farin ciki bbu mugun da yake takura mata, a haka driver ya sauketa a makaranta


 Shewa suke sosai ita da kawayenta bayan sun fito daga exams dinsu a haka suka fito bakin gate dinsu tana tsakiyar su


Tin daga nesa *sahal* ya hangota cikin kawayenta, wanda suka fita girma da kuma tsayi, dariya ce ta kusa kwace masa sanda ya hangosu 

 

"Abba gaskiya yar nan taka ta fiye manyance, jibi fah irin kawayen ta take kulawa" hararsa Abba yayi "ina ruwanka ita taga zata iya kuma ai bbu haramci a cikin hakan ai"

"Allah bada hakuri abba batai laifi ba"  fuskarsa ya hade ganin ta karaso gab dasu, Ganin wanda ke gaban motan yasa ranta ya baci tq bude baya tashiga suka tafi

Sai da suka raka *sahal* airport ya tafi sannan suka dawo gda



Ku kasance dani dan jin su waye sahal da kuma sahala 


Taku ce har kullum mai kaunar farin cikin ku a ko da yaushe



*shamsiyya salis*




💞💞

💞💞

*SAHAL DA SAHALA*



*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


*written by*

Shamsiyyah salis


*Edited*

Ayusha Iliasu musa


*Dedicated to*

Ayusha iliasu 

    Nd 

Haima (mmn abul)


   *16-20*




Alhaji muhammad haifafen garin kano ne a garin gezawa, ba laifi yana dan taba  kasuwanci wanda Allah yasa masa albarka a cikin kasuwanci, duk da ba wani shahararan kudi gare sa ba amma Allah ya rufa masa asiri, yana da mata daya fatima, da yaransu guda uku biyu maza sai mace guda daya

Ahmad shine babban dansa sai kuma Aliyu, sai autarsu hafsat, yan uwan sun taso cikin so da kaunar junan su

Sosai Alhaji muhammad ke kula da karatun yayansa, Ahmad yayi karatu bngaran kasuwanci inda ya fara kasuwanci cikin ikon Allah yasa mu budi, Aliyu kuma ya karanci accntng inda ya samu aiki a banki

Autar su kuma Hafsat na aure a katsina, lkcn da Ahmad da Aliyu suka isa aure suka gina gdan su dan madaidaici, a nan garin gezawa Ahmad ya auri Aisha sai kuma Aliyu ya auri halima, suna zaune cikin mutunta juna basa taba yin fda, sosai Halima na bawa Aisha girman ta, cikin ikon Allah Suka samu ciki kusan tare Aisha  ce ta fara haihuwa ranar suna yaron yaci suna,yaron aka samashi  Abubakar yana da sati uku a duniya Halima ta haihu, itama namijin ta haifo ranar suna aka samashi *sahal*

Hafsat kan har lkcn Allah bai bata haihuwa ba hakan yasa yan uwan mijinta suka tsaneta daga karshe uwar mijin tasa aka mata kishiya, watanta tara ta haihu, nan fa dangin mijin suka kara tsanarta,Shekarar su *sahal* goma  su halima suka kara samun ciki, su sahal na da shekara shida, mahaifan su suka gina katon gda a unguwar tarauni suka dawo da zama, Halima ce ta fara haihuwa ta haifi mace ranar suna aka sama yarinyar hauwa'u ana ce mata jiddah, sati biyu da haihuwar jiddah Aisha ta haihu, cikin ikon Allah itama ta samu ya mace aka sa mata *sahala* , ganin halin da hafsat ta shiga na tsangwama da gori daga dangin mijin yasa Aisha ta yanke shawara  ta barwa Hafsat yarta,mijinnata 

Yana zaune a daki da daddare taje ta sameshi da zancen, sosai yaji dadin yadda ta nuna so ga tilon kanwar tasu

Nan take ya mata waya akan tazo in ta samu lkci,


 Washe gari karfe hudu ta sauka q garin kano, sosai ta samu tarba a wajen matqn yayen nata, 


Bayan sallar isha'i suka hadu gaba daya a falon Alhaji Ahmad, gyarqn murya yayi ya fara magana cikin nutsuwa

     " jiya da daddare Aisha ta same ni da magana wadda naji dadinta sosai kuma nayi murna da yadda take kokarin karfafa mana gwiwa, ganin Hafsat na cikin matsala ta rashin haihuwa yasa ta nemi shawarata akan zata bata kyautar yarta bayqn ta yaye ta" Cikin rashin fahimta hafsat ta dago kanta, murmushi ya sakar mata, cikin rawar murya ta fara magana "yaya bn gane me kake nufi ba?   Kqna nufin Aisha ta mallakqmin *sahala* yarta kyauta"

  Daga mata kai yayi alqmar eh, kukq ta saki  wanda kowa na dakin sai da yasa shi zubda hawaye.



Ngde ngde sosai Aishq bnda bakin da zan miki godia fatana kawai Allah ya bani ikon kyauta ta miki Allah ya bani ikon yi mata tarbiya, Allah ya tayani rukon ta Allah.... Kuka ne ya kufce mata, "kar ki damu Hafst ki daina kuka kinji" Aisha ta fda tana rungumeta.



 Ni ya kamata ace nayi tinanin nan amma bnyi ba har aunty Aisha ta rigani yi, amma tin da ta riga ta bata kyautar *sahala* ni kuma na bawa aunty Aisha kyautar hauwa'u, nafi kowa sanin yadda kike san diya mace amma saboda kyautatawa kikai kyautar da ita" Halima tayi maganar cikin kuka, murna sosai Aisha tayi sanda taji batun halima, Alhaji Ahmad da Aliyu wanda tin da ya zauna be ce komai ba murna sukayi tare da yima iyalan nasu godia a haka taron ya watse zuciyar kowa fal da farin ciki, kwanan hafsat biyu a kano ta koma katsina, sosai mijinta yaji dadi, dan yasan ko ba komai matarsa zata rage damuwa


Kamar yadda Aisha tai alkawari hakan ya faru, ranar da aka yaye  *sahala* aka bawa hafsat ita, a ranar kuma hauwa'u ta dawo wajen Aisha da zama,

Sosai *sahala* ke samun kulawa wajen hafsat da mijin ta lkcn da ta isa makaranta aka sakata a makaranta, a haka rayuwa ta ci gaba da tafiya 


 Lkn da *sahala*ta gama pri skul su *sahal* ana level 3 a b.u.k yana karantar MBBS (MEDECINE) shakuwa ce ta shiga sosai tsakanin *sahala* da mamanta hafsat, shi kansa mijin hafsat santa yakeyi kamar yar da ya haifa da cikinsa

Wata safiyar laraba Hafsat ta tashi da masanancin zazzabi, ganin zazabin yayi tsauri yasa mijinta ya kaita asibiti, ana zuba gwajin farko likita ya gano ciki makale da ita na wata biyu, murna wajen maauratan baa cewa komai ahaka suka dawo gda cikin farinciki, duk wani Wanda yaji tana da ciki sai yay mata murna a haka suka fara rainon cikin cikin kulawa



```Fatan alkairi gareki sis haima Allah yay miki jagora a alamuranki, Allah rayamana abul bisa turbar musulunci amin summa amin```



By


*shamsiyyah*




💞💞

💞💞

*SAHAL DA SAHALA*



*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


*written by*

Shamsiyyah salis


*Edited*

Ayusha Iliasu musa


*Dedicated to*

Ayusha iliasu 

    Nd 

Haima (mmn abul)


  *21-25*



    Kwanci tashi ba wuya wajen Allah haka cikin Hafsat ya shiga watan haihuwa lkcn su *sahala* na jss1, har lkcn san da hafsat takema *sahala* batayiwa cikin jikinta, tinda cikinta yq shiga watan haihuwa kwata kwata ta farajin sauyi, kwata kwata bata da walwala da kuzari, hakan yana damun mijinta sosai, in ya tambayeta dalilin damuwarta sai tace mashi ba komai.


Wata ranar lahadi hafsat ta tashi da matsanancin  ciwon mara, *sahala* da mijin hafsat na falo yana koya mata karatu hafsat tazo ta samesu, da fara'a ta karaso ta zauna kusa dasu


"Sanunku da hutawa, ana ta karatun ne" ta fda sanda take zama kusa dashi, "eh maman biyu har ma mun gama karatun yanxu" "Usman" Hafsat ta fda cikin nutsuwa, gaba daya ya maida hankalinsa gareta, dan ya lura maganar da zatai tana da muhimmanci.


"Ga amanar yarinyata nan zuwa ranar da mahaifanta zasuzo ka danka musu ita cikin mutunci, kamar yadda suka bani ita, naso ace na raini *sahala* har aurenta amma nasan hakan dakyar ya yihu, amma na san....... Maganar da usman yayi ne ya katse mata maganarta, "Ki daina fadar haka hafsat insha Allahu zakiga aurenta harma da jikokinta, bn san kina fadar haka, kwata kwata na rasa gane kanki kwanan nan" murmushi hafsat tayi sannan ta fara magana cikin yanayin damuwa


"Hmmmm usman nidai fatana ka yafe mun ko bayan raina ina so kana min addu'a, in Allah yasa na haifi abinda ke cikina ina san ka masa tarbiyya cikin tafarki mai kyau, in kuma bn haifeshi ba, Allah yasa mu cika cikin aminci ni dashi" *sahala* dake gefe tana kuka ta matso kusa da ita.


"Mumy ki daina fadar haka insha Allahu baza ki mutu ba, zaki haifar min kani ina goyashi" ta karashe maganar tana goge mata hawayen fuskarta, hanunta hafsat ta rike sannan ta fara magana cikin so da kaunar yar tata


 "Allah  k albarkaci rayuwar yata, Allah tsareki daga sharrin makiya da mahasada, Allah ya tsareki ki yasa alumma tai alfahari dake, ta karashe maganar cikin kuka mai tsuma zuciya, shima usman din kuka ya fara, gaba daya aka rasa mai rarrashin junan su, jiyo alamun kuka yasa nafisa dake zaune a tsakar gda shigowa dakin, mutuwar tsaye tayi ganin yadda suke ta kuka, a hankali ta karasa inda suke ta cire *sahala* daga jikin hafsat, lkci guda taji nadama tazo mata na wulakanci da takeyiwa hafsat ya dirar mata,



 "Nafisa ki yafen dan Allah, ki duba girman Allah kar laifin da na miki ya shafi dan da ko yar da zan haifa, nasan mutuwa zanyi, ga amanar abinda zan haifa nan, kar ki nuna mashi tsana ki rikesa kamar dan da kika haifa" Hafsat ta fda tana rike da hannun nafisa,

  

 "Insha Allahu zan kula dashi, kuma kema ki yafe mun, mu zama yan uwa daga yau, sharrin shaidan ne da zugar kawaye, amma daga yau na sadaduda mun zama yan uwa mu tarbi yayan mu cikin so da kauna, baza ki mutu ba insha Allahu"


 "Ni dama can bn rike ki ba nafisa,na yafe miki duniya da lahira, ki riken amanat........." Karar da cikin ta yayi ne yasata yin shiru, cikin hanzari usman ya sata a mota nafisa ta rufe gdan sukai asibiti gaba daya,


Cikin muntina da ba su wuce ashirin ba suka isa asibiti, cikin gaggawa a dauketa sai dakin haihuwa ,Abu kamar wasa kusan minti arba'in bata haihu ba, likita ya fito ya samesu akan za a mata aiki yasa hannu, wata nurse ce ta fito da sauri 

"Likita kazo zata haihu....." Bai jira ta karasa magana ba ya shiga,Yana zuwa kai ya fara fitowa, da taimakon Allah Hafsat ta haifo Zan kadedan yaronta, yana fadowa kuma numfashin ta ya fara sama sama, taimakon gaggawa likita yayi mata, jiki a sabule likita ya fara kokarin rufewa hafsat ido,Allahu akbar, daman ance, dukkan wani mai rai zai mutu, haka ta kasance ga hafsat, ta koma ga Allah, ta haihu, kamar yadda suke so, lkci guda kuma Allah ya karbi ranta, A sabule likita ya fito dan sanar da su halin da ake ciki




Ku kasance dani dan jin cigaban lbrin 



By

*shamsiyyah*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

  *shamsiyyah salis*


Edited by 

  *Ayusha Iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

          Nd 

 *Haima ( mmn abul)*

     

        *26-30* 



   *Diz page goes 2 yuh aunty Ayusha, Allah ubangiji yayi miki jagora, Allah yasa jarabawa ta fito da kyau  ILYSM*😘



Ganin halinda sahala ta shiga na damuwa yasa uaman sa nafisa ta maida ta gda, sanda suka je gda suka zauna suna ta rera kula gaba dayansu bbu mai rarrashin wani


     Ganin likita ya fito daga dakin yasa usman saurin karasawa inda yake hankali a tashe ya fara jero masa tambayoyi


   " Likita ya jikin nata? Ta sauka lpya?"cikin tausaya likitan ya dafa  kafadunsa, " Ko wane bawa da tasa kalar kaddarar, ina so ka karbi taka kaddarar hannu biyu, kar ka kasance mai butulci" 

  

    "Insha Allahu zan yi kokarin karbar ko wace kaddara ce"  gyaran murya likitan yayi sannan ya fara magana cikin nutsuwa


   "Allah ya azurta matarka da samun da namiji" washe hakora usman ya fara tare da godia ga Allah, maganar da likitan ya fda ce yasashi yin mutuwar tsaye


    "Amma kayi hakuri Allah ya karbi matarka, Allah da ya baka ita shi ya karbi abarsa, ka yi masa godia Allah ya baka hakurin rashin ta" ga ba daya usman kasa magana yayi, 


    Cikin mintinan da ba su wuce ashirin da biyar ba aka sallamesu,sannan  suka wuce gda, har lkcn usman ba ya iya tabuka komai sai hawaye kawai da ya keyi, 


     Karar motar da *sahala* ta jine yasata saurin mikewa, ganin ana fito da Hafsat daga cikin mota yasa ta kwalla kara ta fadi sumamiyya


    Karar da *sahala* tayi ne yasa nafisa saurin fita ganin *sahala* a kwance ga kuma usman a kusa da ita, yasa ta saurin karasawa inda take, wannan da yay dai dai  karasowar mutane rike da gawar hafsat,


  Kuka sosai Nafisa tayi, usman ne ya dauki *sahala* ya shiga da ita,


   Cikin mintunan da basu wuce goma ba, kofar gdan usman ya cika sosai da jamaa, haka ma cikin gdan ya cika da mata, Hafsat kan ba laifi akwai jammaa, kowa yana yaba kyawun halinta


   Sanda su Alhaji Ahmad da kaninsa sai kuma iyalansu suka iso garin katsina lkcn yay dai da farfadowar *sahala* sosai iyayen *sahala* suka tausaya mata ganin halin da take ciki


    A haka aka yi mata sutura dan kaita gdan ta na gaskiya, "Inalilahi wainailaihirrajiun" abinda umma ( mahaifiyar usman) ke maimaitawa ke nan, sosai take nadamar abinda tayi ma hafsat, a haka aka yima hafsat sallah aka dauketa zuwa makwancinta


   A haka a ka share sadakar uku cikin jimami na rashin hafsat, *sahala* kan ta rame tayi baki ko abincin kirki bata iya ci, sai idan ummi ( halima) tayi mata da gaske sanan take shan ruwan tea ko kunu, 


    A bangaran usman ma, baya Iya komai kullum yana zaune shiru, da kyar yake iya amsar gaisuwa, haka ma yan uwansa sun ji mutuwar hafsat sosai, nafisa kan kullum cikin kuka take tana makale da jaririn in ba dole ba bata iya ajiyeshi ko nan da nan,


   Ranar sadakar bakwai, ranar mumy ( Aisha) da ummi sukai shirin komawa gda, kuma ranar zasu koma da *sahala* ranar gdan haka ya kara zama kamar ranar hafsat ta rasu a haka sukai sallama suka tafi ko wannensu yana kuka musamman *sahala* Nafisa da kuma usman


    Yau kwana satin *sahala* daya da dawo wa garin kano har lkcn bata sake ba kullum cikin kuka take, wannan dalilin ne yasa *sahal* tsanar *sahala* dan a duniya ya tsani mutum da baya karbar kaddara, kuma ganin yadda gaba daya iyayenta ke nan nan da ita shima yasa ya tsaneta, ban garan *sahala* kuma tana jin dadin yadda suke kula da ita musamman ummi, wannan dalilin ne yasa kullum suna tare, wanda ta tsana kawai *sahal* ne sbda ta lura tinda tazo gdan yake faman shashareta ga dukkan alamu girman kai ne dashi, ita kuma a duniya ba wanda ta tsana irin mutum mai girman kai



 *bayan sati biyu*

       Tafiya ta gaggawa ta tasowa Alhaji Ahmad zuwa garin lagos, kuma zai dau shekara biyu a can, wannan dalilin yasa shi tafiya shi da iyalansa, ganin hauwa'u na hannun mumy yasa aka barwa ummi *sahala* 



    *cigaban labari*


Satin *sahal* daya da tafiya  su *sahala* aka kammala jarabawar junior waec, wanda ya rage saura sati guda su mumy su dawo kano, sosai suke gyaran gdan musamman bangaran  dady yafi shan gyara


  Ana gobe zasu dawo, ummi zaune a falo ana mata jan lalle, *sahala* ta shigo falon da sallama, suka amsa mata fuskarsu dauke da faraa


   " ummi sannu da gda" ta fda tana zama kusa da ita, " yauwa yar gdan ummi, ya hanya?" Alhamdulilah"

   " ina wuni aunty hajara" ( mai lalen) " lpya lau, kin kusa makara, da baki dawo ba na gamawa ummi tafiyata zanyi" aiko da na biki har gda" gaba daya sukai dariya, a haka aka gama musu lalen cikin farin ciki



By


 *shamsiyyah*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

  *shamsiyyah salis*


Edited by 

  *Ayusha Iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

          Nd 

 *Haima ( mmn abul)*

     

        *31-35*



*wannan fejin  sadaukarwa ne ga dukkan official da kuma members din eloquence writers association, Allah ya kara hada kan mu, Allah ya dauka ka mu, Allah ya bar so da kaunar junar mu*





      Tin da su *sahala* suka tashi da safe suke ta faman aikin tarbar bakin su, abinci sosai suke yi kala, a ban garan lemuka ma haka aka shirya su kala kala, karfe sha daya da rabi na rana, Abba, ummi da kuma *sahala* sai kuma drivern su a mota shi daya,   hanyar airport suka nufa  dan tarbar jirgin su dady da zai sauka sha biyu,


    Karfe sha biyu dai suka isa cikin airport din, ba su fi minti goma da zuwa ba jirgin su ya sauka,


    A hankali  suka fara maida duban su ga mutanan da ke sakkowa daga cikin jirgin, farar Abba ce ta fadada sanda ya hango yayan nasa cikin wata dakakiyar shadda, bayan sa kuma mumy ce, sai hauwa'u da kuma big bro din su, 


   Cikin jin dadi suka karasa inda suke, murna sosai dady yayi ganin kanin nasa da kuma iyalansa, haka ma mumy tana gano ummi suka yi musabaha ko wannen su dauke da faraa, a haka suka fara gaisuwar yaushe gamo, ganin hirar baza ta kai su ba ga badaya suka dun guma suka wuce gda, mumy, dady, ummi, da kuma Abba a motw daya, sai Big bro, hauwa'u da kuma *sahala*a mota daya


    Sanda suka shiga gda part din su suka nufa, sai da sukai wanka suka shirya sannan suka zo suka ci abinci tare, ranar haka suka wuni suna hirar yaushe gamo, big bro kan sai tsiya yake ma *sahala* wai har yanxu taki sakewa dasu, dan tinda ta gaidashi bata kara magana, in yay mata magana sai dai ta dinga murmushi kawai bata magana

   


    Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, rayuwa mai tsafta da jin dadi akeyi a tsakanin iyalan guda biyu, sosai suke kaunar junan su, soyayya da kauna ce ta shiga tsakanin *sahala* da hauwa' u duk inda zasu tare suke tafiya, kwata kwata vasa so wani yay nisa a tsakanin su


    Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su *sahala* ana shirin komawa skul saura sati guda su koma, Anje an yima hauwa'u regstrtn zatayi joining dinsu a ss1 

Da daddare bayan su gama dinner Abba ya kalli *sahala* cikin kulawa sannan ya fara magana

   

     "Yar gdan Abba wane klaz zaki shiga ne, har yanzu kina San karantar likitan ne?" 

    " eh Abba science klaz Zan Shiga, nafiso na karanci likita"

    "Toh yar gdan Abba Allah taimaka, Allah sa ki fara a sa'a" gaba daya yan dakin suka amsa da amin

    

 " tin da ni ba a damu da tawa yar ba, ai shike nan, yanxu sbda Allah shine zaka tambayi *sahala* ita kadai ba tare da ka tambayi jiddah ba" mumy ta fda fuska a hade ita a dole ranta ya baci

   

     "Allah ya huci zuciyarki matar yaya, ai ita ma zan tambayeta katse mun hanzari kikayi"

    " bbu wani nan da kana da niyya ai da ka tambayeta" 

"Jiddah mi kike so ki karanta kema" Abba ya fda yana maida dubansa ga jiddah,

  "Abba nima likitan na kesan zama shine buri na nima tin tini" 

"Toh Allah taimaka,Allah sa ku fara a sa'a" ga badaya suka amsa da amin, a haka taron ya watse ko wanen su yana farin ciki



Yau ta kama monday, kuma yau sati da komawar su makaranta amma bata  je ba sai yau, tsaf ta gama  shirinta cikin riga fara sai skirt blue black, sai kuma farin hijab, sosai tayi kyau cikin uniform dinta, ummi ta tadda a falo tana jere abinci, cikin girmamawa ta gaida ta sannan ta nufi part din su mumy


 Da sallama ta shiga falon, bbu kowa a falon hakan yasa ta nufi dakin jiddah, sun gaisa sannan tai mata sallama kafin taje ta gaida mumy da dady ta tafi skul, sbda ba yau jiddah zata fara zuwa ba



By

   *shamsiyyah*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *36-40*


*Diz page goes 2 yuh sis haima Allah ubangiji ya bada nasara a jarabawa, Allah yay miki jagora Allah ya sa a fito da sakamako mai kyau, yanda kika fara a sa'a Allah sa ki gama a sa'a, Amin summa amin ILYSM😘😘*


Sanda ta karasa skul an gama assembly hakan yasa ta nufi ajin su kai tsaye, ba karamin tashin hankali ta shiga ba sanda ta hango malamin da ke cikin ajin nasu, malamin maths din su ne, karamin tsaki taja 

"Aikin manza shine ba a canza mana malami ba aka kara dawo mana da wannan mutumin" ita kadai ta ke maganar ta har ta isa bakin ajin su

Da sallama ta shiga cikin ajin

"Gud morning si....." Kallon da yayi mata ne yasata yin shiru bata karasa maganar ba, 

"Me ya hanaki dawowa makaranta wancan satin, shine kuma yau da kika tashi dawo wa shine kika dawo a makare koh"

Ya fda fuskarsa a hade bbu alamun wasa, yanayin da ta ga yayi yasa gaban faduwa amma ta dake ta tsare shi da ido kuma taki yin magana, 

"Ba magana nake miki ba kika min shiru" ya fada yana daka mata tsawa, 

"Bana nan ne, kuma yau ma yau ma na makara ne" ta fda tana turo kara min bakinta, 

Mtswwww tsakin mr Abdul yayi ya shiga da abinda yake, leken inda zata zauna take yi, ganin wani seat a gaba kuma bbu kowa yasa ta zauna, a hankali ta fara leka baya ko zata ga aminan ta amma bbu su bbu alamunsu, hakan yasa ta maida hankalinta ga karatun

Sai da yay awa biyu sannan ya fice ba laifi tana gane karatunsa sosai, matsalarta dashi kawai rainin hankali


Yana fita ta juya ta fara gaisawa da yan ajin nasu, ba laifi sunyi sababin dalibai da yawa

"Aisha wai ina su khady ne na ga ban gansu ba ko basu dawo bane" *sahala* ta tambaya tana kallon Aisha dake kusa da ita, 

"Basa zuwa ranan nan sun zo sun mana sallama wai sun bar garin nan zasu koma Abuja sun ce a gaida ki sosai" 

Sosai *sahala* taji bbu dadi hakan yasa ta karbi buk din Aisha ta fara kwafar note din da suka wuce sbda Aisha na da kokari

Sanda aka fita break duk suka fice bnda surayya sabuwar daliba ce wancan satin  ta fara zuwa makarantar 

"Sanunki da aiki" surayya ta fda tana taba *sahala* dake rubutu

"Yauwa kema sannun ki" sunana surayya wancan satin na fara zuwa skul in baza ki damu ba zan so a ce mun zama frnds" Ayya kar ki damu ni suna na *sahala* nan suka fara hira kamar wanda suka dade tare, Aisha ta taya ta wasu note din har aka dawo break, a haka har lkcn tashi yayi suka fice, tan fita ta tadda driver yazo, tayi ma Aisha da surayya sallama ta shige suka nufi gda da sallama ta shiga falon, ummi, mumy sai kuma jidda ta tadda zaune, suka amsa mata fuskar su dauke da fara'a musamman ma ummi, kan kusa da ummi ta zauna tare da dora kanta a cinyar ummi, 

"Gaskiya ummi ba kya kyauta, jibi yadda kika shagwaba yarinyar nan" 

Ni kan mumy wlh ban ga aibu a abinda nqi mata ba" ummi ta fda tana shafa kan diyar ta ta, 

" ummi na bari naje na cire uniform na gaji yau da yawa" owk je ki yi wanka kafin nan na hada miki abinci" yauwa ummi na" *sahala* ta fda tana manna mata kiss a kumatu tare da mikewa



*washe gari*


Tin bakwai *sahala* ta tafi makaranta, big bro ne tsaye a falo yana ta duba agogon hanunsa, ganin har takwas da rabi tayi ya sashi jan tsaki sannan ya nufi hanyar dakin mumy, cikin bacin rai ya fara magana

" wlh mumy ni zan tafi driver ya kaita makarantar tinda ai an gama biyan komai sai ta tambayi office din *pc* din ta masa bayanin kanta, yarinya sai nawar jar........" Kan ya karasa maganar jidda ta fara magana cikin shagwaba

" big bro kayi hakuri wlh sai sauri nakeyi plsss kayi hkri dnt mean 2 hurt yuh" ta karashe maganar kamar zata yi kuka

Bai kulata ba yay ma mumy sallama sannan yay waje, ganin ya fita ta bi bayansa har taje bakin kofa kuma komi ta mnta ta koma, cikin mota ya shiga, ganin bata fito ba,

Cikin nutsuwa take tafiya kamar wadda kwai ya fashewa a ciki, sanye take cikin wata ransatsiyar doguwar riga coffee mai ratsin milk, sosai ta shiga da fatar jikinta, tayi roln da milk din gyale sai takalmi milk, sosai tayi kyau,

Tin da ya hangota ya ke ta furta masha Allah har ta shigo cikin motar maganar da tayi masa ne ya dawo dashi daga tina nin da ya tafi

" am sorry bro" ta fda tana dora hanunta akan nasa, lumshe idonsa yayi sbda wani abu da yaji a zuciyarsa, a hankali ya tattaro nutsuwarsa sannan ya ja motar suka nufi *sabara avenue*



Ku kasance dani danjin shigaban lbrin



*eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *41-45*


*Diz page goes 2 yuh sis basira, auta, nd pherty da kuma kowa da kowa na eloquence writers  Allah ya kara hada kan mu😘*



Har suka isa bakin makarantar bai ce da ita komai, ganin alamun kamar yana fushi da ita yasata kallon sa cikin marainiyar fuska

   " Big bro dan Allah kayi hkri, wlh bazan iya jure ganinka cikin wannan yan......." Hannu ya dora akan lebensa alamar tayi shiru

   "Kar ki damu my dear baki min komai ba, a dage da karatu bnda wasa kinji kanwata" daga masa kai tayi alamar toh

A tare suka jera har office din *pc* bayan ya gama komai yay mata sallama ya tafi

Pc ne a gaba jiddah na bayansa har suka isa ss1 lkcn malamin english ne a ajinsu, nan ya nuna mata seat a gaba ta zauna, tinda ta shigo yan ajin suke kallonta, sosai mutane suka yaba da kyanta

Fatima da suwaiba na ta ala ala malamin ya fita su mata magana dan ta zama kawarsu, a cewar su basa so *sahala* ta fara yi mata magana

Malamin na fita fatima ta mikowa jidda hannu "suna na fatima, muna miki murna da shigowa wannan makarantar ta mu" murmushi ta musu " ngde ni kuma sunana jiddah"

Toh mara kirki baza ki tarbi mutum ba koh?"Jiddah ta fda tana dukan *sahala* dariya sahala tayi sannan ta fara magana "ai naga kina ta faman dadaga kai ne shi yasa" dariya sukayu gaba daya, nan *sahala* ta gabatar da jiddah a matsayin sis dinta gdan su daya 

Tin daga ranar *sahala*, Aisha, jiddah da kuma surayya suka zama frnds, duk inda zasu tare suke yin komai, ga rashin ji da fitina, bbu wanda bai san su ba a makarantar, dan ma dai kawai suna da kokari ne



*****************************


*waiwaye adon tafiya* 


*sahal* na sauka a airport ya samu mai taxi ya sauke sa har masaukin sa, tin da ya tafi ya maida hankalinsa ga karatunsa bbu ruwansa da kula yan mata, haka ma abokanai abinda ya kaisa kawai shi yake yi, sau tari mata na aiko mashi da sako ko zasuyi soyayya, amma sai yayi burus yace musu a'a kwata kwata baya musu dariya kullum fuskar nan tashi a hade



*Bayan shekara biyu*

Su sahala ana ta shirye shiryen shiga ss3 sosai ta kara girma ta zama cikakiyar budurwa, *sahal* kan saura sati guda ya dawo, sosai iyayen nasa ke ta murnar dawo warsa, musamman mumy da ta dade bata gansa ba


Da daddare *sahala*da jidda na daki suna hira *sahala* ta kalli jiddah cikin damuwa ta fara magana

    

      "Wallahi jiddah har fargabar dawo war yaya nake yi, yanzu yana dawowa zai addabi mutane ya hanamu sukuni, idan fa yana waje, ko tari kayi wanda bai gamsu dashi ba zai hau masifah da jaraba" 


  "Lallai kice za mu shiga takura, amma ba sai muna kin shiga harkarsa ba bare ya takura mana"

" gaskiya jiddah naga alama baki san waye yaya ba, toh bari kiji tinda nake a rayuwata ban taba ganin yaya yayi dariya, sai dai ko murmushi, murmushin ma bai fi a kirga ba" 

Tabe baki jiddah tayi " Nikan wallahi ba zai takura ni ba" nan dai suka canza hirar su zuwa ta makaranta har bacci ya dauke su


Washe gari


Kamar kullum bayan su *sahala* sun tashi daga bacci sukayi wanka kasancewar suna hutun zangon karshe yasa basu tashi da wuri ba, gyaran dakin su sukayi sannan suka fito falo, cikin girmamawa suka gaida iyayen nasu sannan suka hadu dasu danyin break fast


Abubakar ( big bro) yayi sallama ya shigo cikin falon cikin girmamawa ya gaida iyayen nasa, sannan ya ja kujerar kusa da jiddah ya zauna

     "Big bro ina kwana" *sahala* da jiddah suka fada a tare, murmushi yayi musu ya amsa cike da nishadi


   "Big bro dan Allah da yamma zaka kaimu gdan su Aisha kawar mu" *sahala* ta fda tna kallonsa, 

    " Litle ( sunan da yake ce mata) gaskiya bazan samu kai ku ba, kusa isah ( driver) ya kai ku sbda ina da uzuri, amma insha Allahu idan na dawo zan biyo na dauke ku" toh yaya ta fda tana maida hankalinta ga abincin dake gabanta


Karfe biyu isah ya sauke su a gdan su Aisha, sanda suka je surayya na gdan, ranar haka suka wuni suna shewa, kamar yadda Big bro yay musu alkawari yana dawo wa ya biya ya dakko su



*eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *46-50*


*wannan fejin sadaukarwa ne gareki aunty Ayusha Allah ya dauka kaki ya kare ki daga sharrin makiya da mahassada Allah yayi miki jagora, Allah yasa sakamako ya fito da kyau, misss u alot aunty na ILYSM😘*






     Tin safe gdan ya gauraye da aiki kasancewar yau *sahal* zai dawo gdan, ran *sahala* in ya kai dubu ya gama bacci, da da yadda zata yi wallahi da tayi dan kar ya dawo gdan amma bbu halin yin hakan, ranta bai kuma bacci ba sai da taga abubuwan da ake ta faman hadawa duk dan sbda shi kadai, ita kadai ta dinga tsaki, a haka suka gama hada komai



Karfe 12: 00 dai dai sukai nufin tafiya airport jidda ce rike da dakaken attaruhu a hanunta zata kaishi kitchen sai ga *sahala* ta fito gwaran da suka yi ne yasa atrarun zube, kara *sahala* ta saki wanda ya jawo hankalin su mumy suka yo wajen, *sahala* suka gani rufe da ido tana ta ihu sai kuma jiddah da ke gefe tana mata dariya


     " mai ya sameki *dota* " ummi ta fda ta rike kafadar *sahala* " ummi attaruhu ne ya shigar min id......" Magar da jiddah tayi ne ya sata kin karasa zancen

" ummi ba wani nan karya takeyi, daman tana neman hanyar da baza taje airport dauko yaya bane, amma yasin bai fda mata id......" Ashar din da *sahala* ta shiga durawa jiddah ne yasa Jidda kin karasa maganar

Duka mumy ta kaiwa *sahala* a baki ta hau zazzaga mata masifah ta inda take shiga bata nan take fita ba, *sahala* man kamar jira take ta fara kuka sannan tai dakin ba irin rarashin da ummi bata yima *sahala* ba dan ta hakura su tafi airport amma taki hakura, dole aka barta a gda, jiddah mumy sai kuma ya Abubakar suka tafi dakko shi

Karfe 1:30 suka isa filin jirgin Aminu kano, basu fi minti goma da zama ba jirgim su ya sauka

Daya bayan daya na fara bin masu sakkowa da ido wani hadaden saurayi na hango dogo, gasa da fari kamar ka taba fatarsa jini ya fito, sumar kansa bakikirin ta kwanta akansa tana ta faman sheki, yana da dogon hanci tubarkalla, sai kuma saje da ya ajiye a gefe tare da tsaida gemu kadan a habarsa, ba karamin kyau gemun ya karawa fuskarsa, bakinsa dan karami bai fi ka tura dan karamin cokali ba a ciki, idon sa fari tas kwayar ciki kuma tai baki sosai, a hankali yake sakkowa daga kan step din jirgin, kana ganinsa kasan yana cikin hutu da jin dadi, 

Sakin baki nayi sanda na hango su mumy sun nufeshi fuskarsa dauke da murmushi, a zuciyata nace ba dai *sahal* bane ya zama haka, ganin shima yana musu murmushi yasa nai saurin binsu dan dakko harota

Mumy na karasowa *sahal* ya rungumeta " miss yuh alot mumy na" ya fada yana kara rungumeta, itama din rungumesa tayi, "Nima nayi missing dinka alot my son"  nan *sahal* ya rungume Abubakar, hango jidda a bayan mumy ya sashi dagowa cike da mamaki

" mumy wacce wannan a bayanki ba dai jiddah ce ta girma haka ba" murmushi mumy tayi "aikuwa dai ita ce kasan girman dan mutum ba wuya" cikin ladabi ta gaidasa sannan suka nufi mota ya Abunakar ya ja motar suka nufi gda


A falo ya tadda ummi zaune tana kara gyara dining, cikin farin ciki ya nufi umminsa tare da rungume ta, ita din rungumesa tayi suka fara gaisawa, dakinsa ya nufa danyin wanka dan rage gajiyar tafiya 


Bayan sunyi sallar azahar suka hadu gaba daya a dining dan yin lunch, tin da ya sauka yake ta raba ido ta ina zaiga jerry dinsa amma bai ganta ba, da yazo gda ma bai ganta ba ko dai ta bar gdan ne, toh ina zata koma? Shi kadai yay ta abinsa a zuciya, tabe bakinsa yayi ita ta sani, ya cigaba da cin abincinsa


Ku dai cigaba da kasancewa da ni yar mutan dabo dan jin yadda zan cigaba da kawo muku lbrin



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *51- 55*


*wanan fejin naku ne hawwa sale nd classic feedoh, Allah ya bar zumunci*



Fuskarta a hade kamar wadda bata taba dariya ba ta fito daga dakin, da sallama ta karaso inda suke, sautin muryarta da ta daki dodon kunensa yay saurin dago da kansa, sanye take cikin wata doguwar riga ta atamfa, sosai atamfar ta zauna a jikin, fara ce amma ba sosai ba, tana da dogon hanci sai kuma dan karamin bakin ta, tana da dogayan gashin ido sai kuma manyan idanu tubar kalla, tsaya fadan yadda ta hadu bata lkci muryar mumy da yaji ce ta dawo dashi daga dogon tina nin da ya tafi

   "Son tina nin me kake ne, ina lura da kai fa tinda ka zauna baka ci wani abincin kirki ba" murmushin karfin hali yayi, "mumy bbu komai kawai dai gajiya ce bata sake ni ba har yanzu" daga kai mumy tayi cike da gamsuwa da baya nan *sahal*


    "Sannu da zuwa ya hanya" *sahala* ta fda ba tare da ta kalli inda yake ba, koh dago kansa bai yi ba ya amsa mata da "Alhamdulilah" sannan ya cigaba da cin abincinsa, bayan sun gama cin abinci ya nufi dakinsa dan kwanta wa ya huta


  Tin da *sahal* ya kwanta yake ta faman juyi bbu abinda yake gani sai fuskar *sahala* tin tana karama, da kyar ya samu bacci barawo ya sace shi, bashi ya farka ba sai wajen karfe shida, a gagauce ya fda toilet yayi wanka sannan ya dauro alwala ya gabatar da sallar la'asar da ake binsa, sannan ya nufi masalaci danyi jam'in mangariba, a masallaci ya tadda Abba da dady, cikin girmamawa ya gaidasu suka amsa cike da kulawa sannan suka mashi barka da dawo wa, 


    Bayan an idar da sallar mangariba basu shigo gda ba sai da suka jira akayi sallar isha'i sannan *sahal* da ya Abubakar suka dawo gda, falon mumy suka wuce kai tsaye dan yin dinner 


Kan doguwar kujera *sahal* ya kwanta

   " mi zan gani son yana ga ka kwanta, abincin fa" mumy wallahi duk a gajiye nake" Ayya son bari na zubo abincin na kawa maka" no mumy ki barshi bari nazo na ci" bata jira cewarsa ba ta zubo masa abincin ta kawo masa, kansa ya dora a kafadar ta "Ngde sosai mumy da kulawa dani" murmushi ta masa kawai ta fara basa abincin yana ci 

"Assalamu alayku......" Kasa karasa sallamar *sahala* tayi sbda ganin yadda *sahal* ke ta faman zabgawa mumy shagwaba, tabe bakin ta tayi ta karasa shigowa falon, 

"Mumy ina jiddah take? " ba tare da ta dago ta kalle ta ba tace mata tana dakinta, 

Sahala na shiga daki ta tadda jidda a kwance cikin bargo ta rufe fuskarta, 

"Besty na amin afuwa nayi laifi raina ne ya baci" ko dago kanta jidda bata yi ba bare ta sa ran zata amsa mata,

*sahala* ta kusa minti goma tana ma jiddah magana amma taki kulata, ganin bata niyyar kulata yasa ta mike ta fice jikinta a sanyaye


Washe gari


*sahala* ta shirya cikin uniform dinta, falon mumy ta nufa bayan sun gaisa da ummi da Abba, da sallama *sahala* ta shiga falon mumy ta tadda tana shirya abinci a dining cikin girmamawa ta gaida ta bayan ta amsa mata sallamar, 

" mumy dan Allah kiyi hakuri wlh Allah bazan kara yin zagi ba, jiyan ma raina ne ya baci" sai da sahala ta sha wuya kan mumy ta hakura, haka ma jiddah basu shirya ba sai a hanyar dawowar su daga makaranta *pc* ya kira su dan su tattauna game da jarabawar su


*bayan sati biyu*


Da daddare dady, mumy, Abba, da ummi na zaune a falo dady ya sanar wa da su mumy *sahal* ya samu koyar wa a jami'ar bayero dake kano, sosai su mumy suka ji dadi suka masa fatan alkairi, washe gari dady ya sanarwa da su sahal sosai yaji dady




Ku cigaba da kasancewa dani, dan jin yadda zan cigaba da kawo muku lbrn



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *56-60*



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su sahala an shiga ss3, sosai suka maida hankalin su ga karatun su kwata kwata basa wasa, 

*sahal* kan an fara koyarwa sosai yake ksratun da ake ganewa, amma ba wanda ya taba ganin murmushinsa bare dariya a cikin dalibansa, sosai daliban ke shakkar sa kuma *sahal*na masifar yi musu kwar jini


Tin safe su *sahala* ke ta faman shiri kasan cewar bikin wata yar ajin su a islamiyya da za ayi, duk wani aiki da suka san su zasuyi sai da sukayi shi, karfe biyu da rabi suka gama komai sannan suka ci abinci, bayan sun gama cin abinci, suka fara shirin zuwa zuwa bikin, karfe biyar dai dai suka shirya cikin wata hadadiyar doguwar riga ta material milk, tsayawa fadar yadda sukai kyau bata lkci ne su ummi sukai wa sallama sannan suka tafi 


Cikin mintu nan da ba su wuce talatin ba suka isa event din da zaa gabatar da bikin sanda sukaje amarya har tazo, kujeru suka samu suka zauna


Tinda suka iso wajen ido aka bisu dashi kowa yana yaba irin kyan da sukayi, kana ganin za kace twince ne sbda komi iri daya suka saka, tubarkallah shine abinda mutane ke cewa kawai


Karfe takwas aka tashi daga bikin amarya sukaje sukai ma Allah ya sanya alkairi suka fito dan tafiya, sun fi minti goma tsaye amma bbu alamar napep bare su sa ran tafiya gda 


   "Assalamu alaykum" sallamar da suka ji a bayan su yasa su juyawa gaba daya, ganin wani hadaden saurayi sanye cikin blue din shadda sosai yayi kyau, shaddar ta zauna a jikinsa kamar daman dashi aka yi ta, ciki ciki suka amsa masa sallamar tare da maida kansu gefe 


     "Sunana Umar muktar, tinda naga kun shigo naga kin kwanta min ina sanki kuma wallahi da gaske nake ba yaudara bace ta kawo ni" ya fda yana kallon *sahala* 


   "Ngde sosai da sona da kayi, amma kayi hakuri bana soyayya" ta fda tana jan jiddah dan su bar wajen, gaban su sha " haba dan Allah ki duba girman Allah ki karbi soyayya ta wlh Allah da gaske nake sanki" ba irin nacin da umar bai ma *sahala* ba amma taki, dole ya hakura amma ta masa alfarmar ya kaisu gda, da kyar ya samu suka yarda suka shiga motar sannan ya ja suka tafi *sahala* ce a gaba sai kuma jiddah a baya, hira sosai yake jansu da ita, jidda kan tana dan taya sa hirar amma *sahala* kan koh magana ba tai ba har suka iso layin su


Suna zaune a bakin gate din gdan su shi da ya Abubakar suna hirar su, motar da yaga ta shigo layin ya sa su  dago kansu, ba karamin mamaki sukai ba lkcn da suka hango *sahala* zaune a gaban mota, sosai ran *sahal* yay masifar bacci, yaushe ma aka haifi yariyar da har zata na fita da samari tana kaiwa dare? Shi kadai yake zancen sa a zuci, kwafa yayi sanda ya hango motar ta tsaya suna kokarin fitowa


Su *sahala* na gano su a zaune suka tsorata, shikenan yau sun shiga uku, daman ya abubakar ne kadai ya gansu za su iya yi masa bayani ya fahimce su, amma *sahal* sun san bazai fahimce su ba


   Suna fitowa daga motar *sahala* ta leka ta murfin " mun gode Allah ubangiji ya saka da alkairi" bata jira cewar sa ba suka taho, kallon da suka ga ya abubakar na musu ya sa suka kara shiga tashin hankali


    "Daga gdan uban wa kuke, kuma uban waye yace ku kai dare, sannan waye wanda ya sauke ku a mota?"  *sahal* ya jero musu tambayoyin cikin tsawa, fitsari ne kawai su *sahala* ba suyi ba sbda tsoro

   " ku shiga ciki zaku min bayanin inda kuka je"


   basu jira ya kara mgana ba suka shiga cikin gda da gudu, ya Abubakar ne ya bi bayan su, sahal na shirin shiga cikin gda yaji ana masa mgana, a fusace ya fara magana sbda ganin wanda ke masa mgana

   " Kaga dalla malqm bnsan jin komai a bakin ka, kuma wlh Allah idan ka kuskura kai gangancin zuwa gdan ko sai dasu a hanya, Allah hukuma ce zata raba ni da kai"

Bai jira cewar sa ba yay cikin gda, umar kan jiki a sanyaye ya juya ya shiga motarsa yana mamakin dalilin hana su kula samari


    suna shiga bangaran mumy suka nufa, gaba daya sun gama tsorata da yayan nasu, sun san yau Allah ne kawai zai kwace su a hanun yayan nasu, jin an turo kofar dakin kuma suka ji muryar mumy nacewa "ka shiga suna cikin dakin" yasa suka kara tsurewa nan da nan suka fara hawaye tin kan ya shigo dakin



Ku kasance da auntyn abul dan na cigaba da kawo muku lbrin




*Eloquence writers association*





💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *61-65*




*Wannan fejin sadaukarwa ne ga dukkan eloquence writers, Allah ya bar zumunci Ameen summa Ameen*




Turo kofar da akayi ne yasa suka kara makalewa jikin bngo, ganin mumy ce yasa suka dan sauke ajiyar zuciya amma sun tsora sosai da yanayin da suka tadda yasa suka kara tsora,


   "Tsoran ku na banza da hofi, dalla ku taso ku sameni a falo yanxun nan kafin ranku ya baci" ganin basu da niyyar tashi yasa mumy ta daka musu tsawar da suka mike ba shiri,


    Kusa da *sahal* suka tsugunna, kan su a kasa, mumy kan waje tayi sbda ta bashi damar yi musu hukuncin da ya dace da su,


   Sai da suka kusa minti goma a tsuggunne bai tanka musu ba sai da ya gama shan kamshin sa sannan ya fara mgana rai a hade


    "Zan tambaye ku kunsan Allah idan kuka kuskura kuka min karya wlh na lahira sai ya fi ku jin dadi" ya karashe maganar fuskarsa a hade bbu alamar dariya, ku fdam miye tsakanin ku da wanda ya kawo ku kofar gdan

    Cikin rawar murysr jiddah ta gaya mashi komai tin daga farko har karshe, yanayin da sukai maganar yasa ya gamsu da baya nan su


    " To bari kuji wannan ya zama na farko kuma na ksrshe da za kusa kafa ku bar gdan nan ba tare da izini ba, kuma wlh kuka kuskura kuka kara gangancin shiga motar wani" kwafa yayi tare da cije leben sa, 

" ku tashi ku bani waje kan na kwakwada muku mari" jikin su na rawa suka mike suka bar wajen sukai falo


Tin daga ranar basu kara fita biki ba ba tare da izinin sa ba, duk inda zasu zai basu lkcn da zasu dawo, indai kuwa suka kuskure lkcn fda zasu sha kamar mi



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, *sahala* sun kusa fara waec, sosai suka kara maida hankalin su ga karatun su, ya Abubakar ke musu lesson a gda, 


Cikin ikon Allah su sahala aka zana jarabawar jamb *sahala* ta samu fiye da yadda ake bukata haka ma jiddah, duk medcn suka cike a bayero universty, Aisha kuma ta cike f.u.d tana neman chemistry  sai kuma surayya ta cike k.u.t tana neman biology

Cikin ikon Allah jarabawa ta fito suka samu fiye da yadda ake so


Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su jiddah an kusa gama neco, jarabawa daya ta rage musu

Da daddare suna zaune gaba dayan su a falon bayan sun gama dinner 

*sahala* ta kalli abba cikin nutsuwa

  

    "Abba in jarabawar mu ta fito zaka mana walima a gda na murna?" " Insha Allah yar gdan abba amma fa sai result yayi kyau, kuma zamu je daku ku zabi waya guda biyu masu kyau" murna sosai sukai sanda suka ji batun abban su, dady yay musu alkawarin laptop ranar dai kwanan farin ciki sukayi


Yau ta kama littinin, yau ce ranar da ta kama su gama jarabawa, shiri suke sosai dan tafiya makaranta, suna zuwa makaranta aka shiga exam, karfe 12:30 suka fito daga exam, murna wajen su baa cewa komai, a haks suka rabu cikin kewar juna bayan anji chanjin numbobi



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah jarabawa ta fito, dukkan su sunyi nasara a jarabawarsu, murna wajen su kamar mi, 


   Kamar yadda Abba yay musu alkawari, da kansa ya dauke su suka je store aka yi musu siyayya ta gani ta fda sannan ya sai musu wayoyi kala bibbiyu, dady ma ya sai musu laptop, tin ranar da aka siya musu wayoyi suka fara chrtn, laotop din su kan film suka laloda musu kullum basu da aiki daga chrtn sai kallo


Kamar kullum cikin sauri suka karasa aikin su da suka san nasu ne, break fast suka hada sannan suka jere a dining, sannan sukai daki dan cigaba da kallon wani film na india da suke kallo mai suna *Rustom* sosai suka mai da hankalin su ga film din domin suna masifar jin dadin film din

 


    "Gaskiya dady ya kamata a karbi laptop din yaran nan jibi yadda kwata kwata suka mai da hankalin su ga kallo, ko abincin kirki basa san ci bare kuma suyi wani cikaken aiki" mumy ta fda cike da damuwa " gaskiya kan abinda mumy ta fda gaskiya ne ya kamata a duba lamuran nasu" ummi ma ta fda itama fuskar cike da damuwa


    "Kar Ku damu insha Allah za su daina, ai yanxu sun ga suna zaman gda ne, amma indai aka fara zuwa skul basu daina ba duk Zan kwace" dady ya fda cike da kulawa, a haka suka dora wata hirar sannan kowa yaje ya kwanta



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah gaba dayan su sun samu admission a makaranta, saura 2 weeks su fara karatu, sosai su *sahala* suke shirin makaranta dan da gaske suke San karatun 


Da rana suna falo suna hirar makarantar su *sahal* ya turo kofar ya shigo tare da sallama, bayan sun amsa sallamar suka gaidashi cikin girmamawa, ba tare da ya kallesu ba ya amsa musu, har sun tashi za su bar falon ya Kira su, dawowa sukai suka zauna, sai da suka kusa minti goma a zaune sannan ya fara magana kamar mai koyo


     " Ina san na jan kunen Ku, Ku taimaki kanku kuyi karatu, bbu ruwa na da na sanku, abinda kuka aikata shi zaku gani, sannan kar wadda tai gangancin nuna ta sanni a skul, gwamma ku taimaki kanku kuyi abinda zai anfane ku" sai da ya gama musu fda sannan ya fice



Ku dai cigaba da kasancewa dani yanxu lbrn ya fara, nice dai taku yar mutan dabo, sha lelan aunty ayusha nd haima



*Eloquence writers association*





💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *61-65*




*Wannan fejin sadaukarwa ne ga dukkan eloquence writers, Allah ya bar zumunci Ameen summa Ameen*




Turo kofar da akayi ne yasa suka kara makalewa jikin bngo, ganin mumy ce yasa suka dan sauke ajiyar zuciya amma sun tsora sosai da yanayin da suka tadda yasa suka kara tsora,


   "Tsoran ku na banza da hofi, dalla ku taso ku sameni a falo yanxun nan kafin ranku ya baci" ganin basu da niyyar tashi yasa mumy ta daka musu tsawar da suka mike ba shiri,


    Kusa da *sahal* suka tsugunna, kan su a kasa, mumy kan waje tayi sbda ta bashi damar yi musu hukuncin da ya dace da su,


   Sai da suka kusa minti goma a tsuggunne bai tanka musu ba sai da ya gama shan kamshin sa sannan ya fara mgana rai a hade


    "Zan tambaye ku kunsan Allah idan kuka kuskura kuka min karya wlh na lahira sai ya fi ku jin dadi" ya karashe maganar fuskarsa a hade bbu alamar dariya, ku fdam miye tsakanin ku da wanda ya kawo ku kofar gdan

    Cikin rawar murysr jiddah ta gaya mashi komai tin daga farko har karshe, yanayin da sukai maganar yasa ya gamsu da baya nan su


    " To bari kuji wannan ya zama na farko kuma na ksrshe da za kusa kafa ku bar gdan nan ba tare da izini ba, kuma wlh kuka kuskura kuka kara gangancin shiga motar wani" kwafa yayi tare da cije leben sa, 

" ku tashi ku bani waje kan na kwakwada muku mari" jikin su na rawa suka mike suka bar wajen sukai falo


Tin daga ranar basu kara fita biki ba ba tare da izinin sa ba, duk inda zasu zai basu lkcn da zasu dawo, indai kuwa suka kuskure lkcn fda zasu sha kamar mi



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, *sahala* sun kusa fara waec, sosai suka kara maida hankalin su ga karatun su, ya Abubakar ke musu lesson a gda, 


Cikin ikon Allah su sahala aka zana jarabawar jamb *sahala* ta samu fiye da yadda ake bukata haka ma jiddah, duk medcn suka cike a bayero universty, Aisha kuma ta cike f.u.d tana neman chemistry  sai kuma surayya ta cike k.u.t tana neman biology

Cikin ikon Allah jarabawa ta fito suka samu fiye da yadda ake so


Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su jiddah an kusa gama neco, jarabawa daya ta rage musu

Da daddare suna zaune gaba dayan su a falon bayan sun gama dinner 

*sahala* ta kalli abba cikin nutsuwa

  

    "Abba in jarabawar mu ta fito zaka mana walima a gda na murna?" " Insha Allah yar gdan abba amma fa sai result yayi kyau, kuma zamu je daku ku zabi waya guda biyu masu kyau" murna sosai sukai sanda suka ji batun abban su, dady yay musu alkawarin laptop ranar dai kwanan farin ciki sukayi


Yau ta kama littinin, yau ce ranar da ta kama su gama jarabawa, shiri suke sosai dan tafiya makaranta, suna zuwa makaranta aka shiga exam, karfe 12:30 suka fito daga exam, murna wajen su baa cewa komai, a haks suka rabu cikin kewar juna bayan anji chanjin numbobi



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah jarabawa ta fito, dukkan su sunyi nasara a jarabawarsu, murna wajen su kamar mi, 


   Kamar yadda Abba yay musu alkawari, da kansa ya dauke su suka je store aka yi musu siyayya ta gani ta fda sannan ya sai musu wayoyi kala bibbiyu, dady ma ya sai musu laptop, tin ranar da aka siya musu wayoyi suka fara chrtn, laotop din su kan film suka laloda musu kullum basu da aiki daga chrtn sai kallo


Kamar kullum cikin sauri suka karasa aikin su da suka san nasu ne, break fast suka hada sannan suka jere a dining, sannan sukai daki dan cigaba da kallon wani film na india da suke kallo mai suna *Rustom* sosai suka mai da hankalin su ga film din domin suna masifar jin dadin film din

 


    "Gaskiya dady ya kamata a karbi laptop din yaran nan jibi yadda kwata kwata suka mai da hankalin su ga kallo, ko abincin kirki basa san ci bare kuma suyi wani cikaken aiki" mumy ta fda cike da damuwa " gaskiya kan abinda mumy ta fda gaskiya ne ya kamata a duba lamuran nasu" ummi ma ta fda itama fuskar cike da damuwa


    "Kar Ku damu insha Allah za su daina, ai yanxu sun ga suna zaman gda ne, amma indai aka fara zuwa skul basu daina ba duk Zan kwace" dady ya fda cike da kulawa, a haka suka dora wata hirar sannan kowa yaje ya kwanta



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah gaba dayan su sun samu admission a makaranta, saura 2 weeks su fara karatu, sosai su *sahala* suke shirin makaranta dan da gaske suke San karatun 


Da rana suna falo suna hirar makarantar su *sahal* ya turo kofar ya shigo tare da sallama, bayan sun amsa sallamar suka gaidashi cikin girmamawa, ba tare da ya kallesu ba ya amsa musu, har sun tashi za su bar falon ya Kira su, dawowa sukai suka zauna, sai da suka kusa minti goma a zaune sannan ya fara magana kamar mai koyo


     " Ina san na jan kunen Ku, Ku taimaki kanku kuyi karatu, bbu ruwa na da na sanku, abinda kuka aikata shi zaku gani, sannan kar wadda tai gangancin nuna ta sanni a skul, gwamma ku taimaki kanku kuyi abinda zai anfane ku" sai da ya gama musu fda sannan ya fice



Ku dai cigaba da kasancewa dani yanxu lbrn ya fara, nice dai taku yar mutan dabo, sha lelan aunty ayusha nd haima



*Eloquence writers association*



💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *66-70*




*wannan fejin sadaukarwa ne gareki, sis nafisa salis, Allah ya bada zaman lpya*


Suna tashi suka nufi daki kowanne ransa a bace, a ganin su ai ya gama raina musu hankali


Akan gado suka ma kan su masauki " gaskiya jiddah yaya dan rainin hankali ne, jibi yadda yake ta famam dadaga kai wai kar mu nuna mun sanshi, ai ko bai fda ba wlh bazan nuna nasanshi ba" sahala ta fda fuskarta a hade,


   Dariya jidda tayi, " Ni wlh dariya ma ya bani sai kace wani shugaban kasa, wai kar mu nuna munsanshi, kuma wai mu dage da karatu babu sanayya, kamar da can shi yake samu karatu ko kuma shi ke bamu markn" 

Mtswwwww, tsaki *sahala* tayi, kyale dan rainin hankali kai, wlh shiyasa yaya abubakar yafi burgeni" nan dai sukai ta hirar su har  dare


Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, yau saura kwana 2 su fara zuwa makaranta, da daddare ya Abubakar ya kai su super market dan suyi siyayyar kayan da suke da bukata 



Yau ta kama monday tin 8:00 na safe su *sahala* suka gama shirin su dan su tafi makaranta, dady ne da kansa  ya sauke su a makarqnta hall din da suke da lecture suka shiga, sannan dady ya juya, da sallama suka shiga front seat suka zauna kusa da wata yarinya ga dukkan alamu bazata wuce sa'ar su ba, sallama suka mata tare da mika mata hannu, 


    " sunana sahala, sannan kuma yar uwata sunan ta hauwa'u amma jiddah ake ce mata" murmushi yarinyar tayi " Ni sunana juwairiyya, nyc 2 mit yuh, hpe zamu zama frnds" insha Allahu" sahal da sahala suka fda a tare, 

Malamin da ya shigo ajin sune yasa su yin shiru, 

   Cikin harshen Hausa malamin ya gabatar musu da kqnsa, sannan ya gaya musu course  din da zai na koyar dasu, bayan ya gama yq Shiga karatunsa kai tsaye, sosai sahala jiddah tare da kawar tasu suka mai da hankali suna sauraransa, bayan ya gama ya tambaya ko akwai mai tambaya, sahala ta daga hannu yace umarce ta da ta tashi tayi tambayar, cikin muryar ta mai dadin sauraro sahala ta fara mashi tambayoyi yana amsa mata, bayan sun gama shima yayi tambaya suka amsa masa


Karfe 11:00 ya fita ya bar ajin, kasan cewar basu da wata lecture din suka tafi gda


Tinda suka dawo daga makaranta, suka ci abinci sannan sukai sallah , aikin gda suka taya su mumy sannan sukai shirin makarantar islamiyya suka tafi,


Bayan sunyi sallar isha'i suka fara bitar karatun da aka musu a makaranta, bayan su dady sun dawo yasa aka kira su, cikin girmamawa suka gaidashi ya amsa fuskarsa a sake


   "Ya karatu, hpe dai kun gane karatun da aka muku a skul yau koh" 

   " eh dady mun gane yanxu ma karatun muka gamayi duk bamu da matsala da na yau" sosai dady yaji dady ganin yadda suka maida hankali


Washe gari ma da wuri suka tafi makaranta sbda suna da lecture karfe takwas, yau kan a bakin hall din da zasuyi karatu yau suka hadu da juwairiyya, a tare suka shiga sannan suka zauna, basu fi minti biyar da zuwa ba malamin yazo, shima ba laifi sun gane karatunsa sosai, bayan ya fita claz monitor din su ya mike ya je gaba


"Assalamu alaykum" yay musu sallama cikin sakin fuska, gaba daya suka amsa mashi sallamar sbda sun lura sanarwar da zaiyi mai muhimmanci ce


   "Gobe zai kama wed, malamin da muke dashi, an ce yana da zafi, amma idan ka fahimce shi yafi duk sauran malaman saukib kai, abinda zakai ka fahimce shi kuma shine kabi dokokinsa, da kuma tsarinsa,komi zaiyi cikin tsari yake yi dan haka ku kula ku kiyaye, kuma idan har ya shiga aji ba a shiga duk naci mutum, hpe zaku kiyaye, muna neman hadin kanku gobe kowa yazo da wuri karfe 9:00am zai shigo zuwa 12:00 yana yin baya shiga ko wanne klaz kafin 9:00 sbda ya dagawa mutane kafa, hpe zaku kokarta ku kiyaye" 

Bayan ya gama sanarwa sannan kowa ya fice 


" gaskiya ko wane malamin nan ya fiya iyayin jaraba, Allah dai ya bamu ikon bin dokokin nasa" sahala ta fda fuskarta cike da dan damuwa,


" insha Allahu zamu sameshi da sauki fiye da yadda aka fda" Allah yasa yanda yake da tsarin nan ba mumuna bane" juwairiyya ta fda tana dariya, suma din dariya sukayi, aiko da munsha dariya dan mafi akasarin masu iyayin nan munana ne, duk suka kwashe da dariya drivern su da yazo ne yasa sukayi ma juwairiyya sallama sbda ita nata bai zo ba suka tafi


Da daddare suna falo suna yin dinner *sahala* take bawa dady lbrn malamin su Wanda suke dashi gobe, "sai kuyi kokarin bin dokokinsa" Mumy ta fda 

*sahal* dake gefe murmushi kawai yake yi sanda yaji suna bada lbrn malamin nasu a xuciyarsa yana mamakin yanda wannan malami yay suna haka da kuma yadda ake karfafa dokokinsa





Nice dai yar mutan dabo Ku cigaba da kasance wa dani dan cigaba da kawo muku lbran






*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*®ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by 

*Ayusha iliasu*


Dedicated 2 

*Ayusha iliasu* 

      Nd 

*Haima ( mmn abul)*



     *71-75*




*Wannan fejin naku ne sis Ayusha and Haima, a kullum bana gajiya da mika godia ta gare Ku kun can canci yabo na a ko da yaushe, addu'a da fatan alkairi shine kadai tsakanina da ku ILYSM*




Washe gari tin da su sahala suka tashi da asuba basu koma bacci ba, gyaran gda suka gama yi sannan suka dora break fast, karfe bakwai suka gama jere komai a dining sannan suka nufi wanka cikin minti goma sha biyar suka gama shirin su tsaf, a gurguje sukayi break fast sanan driver ya kaisu makaranta, yau ko jiran Abba ko dady basuyi ba suka tafi 


Takwas da mimti ashirin suka isa makaranta, suna zuwa suka tadda juwairiyya ta zo 


" juwairiyya naga fa kamar  kin tsorata da malamin nan sosai" sahala ta fda lkcn da ta zauna, dariya juwairiyya tayi

"Shi yasa naga ke sai bayan 9 kika zo tsabar ba kya tsoransa" 

"Ai tinda bnji tsoron mugun yayana na gda ba, ba wanda ya isa naji tsornsa" 

"Lallai ma sahala ai yaya da ban malami ma da bn" nan dai sukai ta hira



Karfe bakwai dai dai ya tashi daga bacci, cikin minti goma ya gyara dakin sa tsaf dama can dakin bashi da wani datti, bangaran su mumy ya nufa, bayan sun gaisa sannan ya dawo ya gaida ummi anan yay break fast lkcn takwas har tayi, bayan ya gama ya shiga wanka cikin minti ashirin ya shirya cikin wata dakakiyar shadda sosai shaddar ta zauna a jikin sa hula yasa da takalmi kallar kayan sannan ya dora a gogo a hanunsa, su mumy yay ma sallama sannan yaja motarsa yay b.u.k 


Karfe tara saura minti goma ya karaso bakin hall din da suke, tinda muta nan ajin suka hango tsayuwar motarsa aka fara hirarsa kowa yana yaba tsadar motar ala ala suke ya shigo suka fuskarsa, *sahala* da jidda suna ganin sayuwar motar yayan nasu suka tabe baki, 

Mtswwww " daman ashe yaya ne, nasan za a rina ai" jiddah da *sahala* suka fda a zuciyar su


Karfe tara dai dai ya fito daga cikin motar, "masha Allah" abinda mutane ke ta fda kenan a zuciyarsu, 


Cikin nutsuwa yake tafiya kamar wanda ke tsoran taka kasa 

Sallamar da yayi ne cikin muryarsa mai dadin sauraro yasa gaba daya mutane suka kara juyowa suna kallonsa tare da amsa mashi ssallama inda aka tana da dan tsayuwar malamai ya tsaya,


Sunan sa ya fara fda musu sannan ya gaya musu duk wani tsarinsa, wanda dama tuni klaz cptn ya sanar musu 


Ka tsaye ya shiga cikin karatu, tsit ajin yayi sai sautin tattausar nuryarsa ke fita, sai da yay karatun awa daya sannan ya fara musu tambayoyi, ba laifi yadda yaga ana bashi amsa yasan an fahimta, 

Waya ke da tambaya? Sahala ya fda cikin harshen turanci, sahala ce ta daga hannu kallo daya yay mata sannan ya dauke kansa 

" ina jinki miye tambayarki" nan ta fara tambayarsa ya na bata amsa, sannan ta zauna,


Karfe 12:00 dai dai ya bar cikin ajin, yana fita aka fara hirarsa yan ajin na ta yaba kyansa, 

"Gaskiya malamin nan ya hadu iya haduwa" juwairiyyah ta fda lkcn da suke fitowa daga cikin hall din, 


Mtswwww, *sahala* tai saki, " nikan dai bn ga wani kyau ba, kina ganin mutum sai girman kan tsiya, ga shegen muskilanci" 

Ke dai ki fdi gaskiya ko dai ana ciki da shi ne? Juwairiyya ta fda cikin zolaya


"Allah ubangiji ya tsare na rasa wanda zan so sai wannan, kar ki kara min haka bn so" sahala ta fda fuskarta a hade


"Allah baki hkri ranki ya dade, bazan kara ba" nan suka wuce kowa ya nufi gda


Yau sati biyu da fara zuwan su makaranta, sosai suka maida hankalinsu ga karatun su, basa wasa kullum basa kwanciya bacci sai sun tabbata sun karance karatun da aka musu na ranar, sosai dady ya ji dadin yadda yaran suka mai da hankali ga karatun su



*Amin afuwa bisa jina da kukai shiru hakan ya faru ne sbda wasu uzirika da suka danno kai, amma insha Allahu zaku na jina akai akai*




*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *76-80*


     Tin da suka tashi da asuba suke shirin makaranta kasancewar yau suke da Dr sahal, gyaran gda suka fara yi tsaf sannan suka dora girki, cikin mintinan da basu wuce talatin ba suka jere komai a dining,


Sahala ce ta fara shiga wanka, lkcn karfe bakwai da rabi hakan yasa jidda jiranta bakin gado tare da daukar buk dinta sbda ta karanta, cikin minti goma sha biyar sahala ta fito daga toilet 

  

   "Inalilahi wainailaihir rajiun" abinda *sahala* ta fda ke nan lkcn da ta hango jidda tsugunne bakin gado tana murkususu


   "Sister mi ya sameki, baki da lafiya ne, ko marar ki ce ke ciwo?" *sahala* ta jerowa jiddah tambayoyi tana dafe da kafadarta, ganin jidda bata da niyyar mgana yasa *sahala* fita dan kiran mumy, 


    A falo ta tadda mumy lkcn ta fito daga dakinta, "Yauwa mumy daman ke nake nema jidda ce bata da lpya sai faman kurm........." 


   Mumy bata jira *sahala* ta karasa maganar ba tayi dakin su jiddah da gudu, ba laifi lkcn da ta isa dakin cikin nata ya rage ciwo hakan yasa mumy tashinta daga kasa ta kwantar da ita akan gado, ummi ce ta shigo sannan aka kira likita dan ya dubata, ganin jikin jiddan da sauki yasa *sahala* shiryawa dan taje skul 

Kafin likitan ya zo *sahala* ta tafi gda


    Karfe tara da minti goma *sahala* ta isa bakin hall din da taye, gabanta ne yay mugun faduwa lkcn da ta hango motar Dr *Sahal* a bakin hall din sai a lkcn ta duba agogon wayarta taga lkcn jiki a sanyaye ta bude murfin motar ta fito ta nufi bakin hall din 



    Tin da ya tashi yaga ya kusa makara yasa shi saurin shiga wanka a gagauce ya shirya cikin farar shadda, sosai ta amshi jikin sa, ko break fast bai tsaya yi ba ya dau key din motarsa yay makaranta, 


  Tin da ya shiga cikin aji yake ta faman leken ta inda zai fara gano kanen nasa amma bbu su bbu dalilin su, hakan yasa ya dau wayarsa dan kiran mumy yaji mi ya hanasu zuwa, gano motar gdan su ta tsaya yasa ya fasa kiran ya mai da hankalinsa ga karatunsa lkcn da ya hango *sahala* ta fito


     Bakin kofar hall din ta tsaya fuskarta dauke da damuwa, kallonta yayi suna hada ido ta sunkuyar da kanta kasa, ganin wata muguwar harara da ya wullo mata, 


   Kusan mintin ta ashirin a tsaye shi bai ce ta shigo ba kuma bai ce ta juya ba, ganin bashi da niyyar kulata yasa ta juya dan ta koma gda 

Tsawar da ya dakata mata ne yasa ta saurin tsayawa, ba ita ba har sauran jamaar dake cikin hall din sai da suka tsorata, bare kuma ni da nake dakko muku rahoto sai da biro na ya fdi


    Ganin ta tsaya bata juyo ba yasa ran *sahal* ya kara baci,

" Ke dan iskanci ba da ke nake ba nace kixo nan" yq fda cikin dga murya, cikin rashin kuzari ta fara jan kafarta kamar wadda kwai ya fashewa a ciki har ta karasa inda yake


    "Sanda nake fdar dokokina ina hqnkalin ki ya tafi da har zaki zo mun a makare, sbda kuma kin raina mutane shine zaki juya ki tafi koh, kin fi karfin ki bada uzuri ko kiyi magana sbda kin maida mutane yan iska koh"


    Tinda ya fara magana *Sahala*hawaye suka fara taruwa a idontq, tin da take ba a taba wulakanta ta a gaban mutane irin haka ba yanxu gashi ya dizgata, da tasan ta makara ma baza ta zo ba 


    Ganin *sahala* bata da niyyar magana yasa ran *sahal* ya kara bacci, lalai yarinyar nan ta gama raina sa, sai ya koya mata hankali yaga alama tukunna kafin ta nutsu,


   Karatunsa ya cigaba dayi har lkcn tana tsaye, sai da yay karatun awa biyu har lkcn tana tsaye bnda sharar hawaye bbu abinda takeyi sbda azababen gajiya da tayi, jefi jefi yake satar kallonta, 


    Sai da ya gama karatunsa tsaf ya kalleta, "ki sameni a office yanxun nan, saura kuma ki ki zuwa kiga yadda zata kaya sakanina da ke," ba tare da ya jira cewar ta ba yq fice




Ku cigaba da kasancewa dani dan jin yadda zan cigaba da kawo muku lbrin



*eloquence writers association*



💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *81-85*



    *wannan shafin tukuici ne gare ku eloquence writers Allah ya kara hada kan mu Allah kara basira da daukaka amin summa amin*




   Yana fita ta bi bayansa, jin kamar ana kiranta a baya, yasa ta juya, ganin juwairiyya na tahowa 

     "Mi yasa kika makara" juwairiyya ta tambaya lkcn da ta iso kusa da *sahala* turo bakin ta gaba tayi ta shagwabe fuska kamar mai shirin yin kuka ta fara magana a hankali


    " wlh bn san na makara ba juwairiyya da ba abinda zai sa na zo makarantar nan bare har wannan malamin ya wulakanta ni, tin da na tashi da asuba bn koma bacci ba fa, mun fara shiri zamu taho jidda ta fara ciwon ciki tana can ma a kwance na barota ganin jikin nata ya dan lafa" 


    "Ayya kiyi mata sannu idan na koma gda zan kiraki na mata ya jiki" juwairiyya ta fda fuskarta cike da damuwa 


  Sanda suka isa kofar office din juwairiyya ta sami wata kujera ta zauna sbda gudun kar su shiga tare a dizgata


    Da sallama ta shiga office tin, ba tare da ya dago kansa ba daga danna wayar da yake ya amsa mata, nesa dashi ta tsaya, sai da ta kusa minti goma a tsaye sannan ya dago ya kalleta fuskarsa a hade 


     "Ni kike jira na matso kusa dake, ko kuma nufinki na daga muryata kowa yana jin mi nake fda" 

    Ba tare da tace kala ba ta matso daf dashi, tare da turo karamin bakinta,


     "Me ya hana jiddah zuwa makaranta yau, sannan me yasa kika makara?" 


   Ba ta basa amsa ba sai kara turo bakin ta da tayi hadi da murguda sa, sosai ransa ya baci ganin yadda ta mashi


    "Sahala ni sa'an ki ne ina miki magana kina turo bakin ki wato ga dan iska koh"


   "Yaya fa mun shirya za mu taho shine jidda ta fara ciwon ciki, mumy da ta duba baka nan shine ta kira doctor, ni kuma da naga jikin ya dan lafa shine na taho makaranta" 


  " Uban mi ya hana da kika zo ki fdan hakan" 

   "Ba komai" yayi miki kyau wuce ki bn waje" ba tare da musu ba ta juya tayi waje, juwairiyya zo mu tafi,

   Haka suka shige mota kowa ya kama gabansa yay gda


   Sanda *sahala* ta isa gda ba laihi, jikin jidda ya danyi sauki, bayan tayi wanka ta ci abinci ta kwashe komai yadda sukai da yayan nasu a makaranta ta bata, sosai jiddah tayima *sahala* dariya hakan ba karamin bata mata rai yayi ba ba tare da ta tanka mata ba tayi daki sbda bacin rai 


   Washe gari tin wuri suka tafi makaranta, duk da cewa *sahala* ta tashi da ciwon kafa hakan bai hana ta zuwa makaranta ba, 


    Bayan malamin da suke dashi ya fita, suna zaune suna kwafar note din dr *sahal* da ya wuce su jiya wasu yan mata su uku suka zo wajen su sai faman iyayi suke su adole sun gadu


    " Ke *sahala* ki ke kowa wajen ki muka zo" daya daga cikin yan matan ta fda lkcn da suka tsaya gaban *sahala* ko dago fuskarta bata yi ba bare su sa ran zata amsa musu, jiddah ce ta dago ta kalle su fuskarta ba yabo ba fallasa


    "Ya akayi zaku zo ku tsayabakan mutane bbu ko sallama kamar wasu arna" sosai suka ji zafin kalaman jidda hakan yasa daya daga cikin su ta fara mgana tana huci kamar wadda tai gasar gudu


    " kin ga malama ba dake muke ba ki kula in ba haka ba kuma ranki yay masifar bacci" kafin tai mgana *sahala* ta fara mgana cikin iyayi


     " Ya akayi za kuzo kan mu ku tsaya ko sallama bbu kamar an zo daga can" *sahala* ta karashe maganar cike da rainin hankali


    Mtswwwww tsaki suka ja daya daga cikin su tai magana "Koma mi zaki ce ki fda abu daya zan fda miki, ki fita har kar Dr *sahal* naga sai wani faman dadaga kai kike, kina iyayi toh bazai taba sanki ba" 

  

   "Allah min tsari yarinya koh na rasa masu sona nikan nafi karfin wannan wanda kike fda dan na riga na masa nisa" shigowa malamin da suke dashi ne yasa suka juya suka tafi ba tare da sun ce komai ba 


    Bayan malamin yq gama karatun sa ya fice, suma din fita sukayi 

    "Juwairiyya wai kin san wadannan yan matan ne?" "Eh mana wadda tafi zakewa sunan ta Rufaida ita ce  ke san Dr *sahal*jiya  da ba kuzo ba na zauna kusa da su naji suna hirar kawayen ta kuma sunan su sumayya da rukayya" tabe baki tayi "Allah ya kyauta" gaba daya suka amsa da "Amin" sannan suka nufi gda 




*eloquence writers association*



💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *86-90*




Yau ya sake zagoya wed yqu ne kumq suke da Dr *sahal* tin 6 na safe jidda ta fara aikin gda karfe bakwai ta gama komi kasancewar *sahala* yau bata tayq ta aikin ba, hasali ma ko bacci bata tashi ba, karfe bakwai da arba'in jiddah ta gama shirinta na makaranta, sai a lkcn tayi bngaran mumy dan ganin koh *sahala* ta shiryq suyi break fast su tafi da wuri 


   Sosai jidda tai mamakin ganin *sahala* na kwance tana bqcci cikin kwanciyar hankali, ran jidda yay mutukar bacci hakan yasa ta nufi gadon tai mata wawan duka a cinya wanda yasa *sahala* mikewa ba shiri, 


   "Wannan wani irin wulakanci ne kin dai san yau yaya gare mu shine zakije kiyi kwanciyar ki tsabagen rashin mutunci" 

   Mtswwww *sahala* ta ja dogon tsaki, "aikin bnza ina ruwanki da makarata, in naje yau ma yq dizgani ai ba ke aka dizga ba meye damuwarki, aikim bnza kawai mutum yana baccin sa an tashe sa, wlh gwamma ma ki tafi dan yau sai tara ma zan bar cikin gdan" *sahala* ta fda tana fdawa toilet, sosai ran jidda ya baci hakan yasa ko break fast batai ba tasa driver ya kaita makaranta, karfe 8:45 *sahal* ya fito falo Abba da ummi ya tadda suna break fast cikin girmamawa ya gaidasu suka amsa cikin sakin fuska, daya daga cikin kujerun *sahal* ya ja ya zauna ya fara brak fast cikin sauri, yanayi yana kallon agogo, yana shirin mikewa ya ga *sahala* na karasowa falon, sosai *sahal* yay mamakin ganin ta


    Ummi da Abba *sahala* ta gaida cikin sakin  fuska suka amsa  mata " me kikeyi har yanxu baki tafi ba" Abba ya tambayeta yana kallonta, kqme kame tq fara " Abba makara nayi sbda jiya bnyi bacci da wuri ba kaina na ciwo, shine jiddah ta tafi ta barni" gyada kqnsa Abba yayi cike da gamsuwa " yanzu ki jira yayan naki ku tafi tare, ba *sahal* ita kan ta *sahala* sai da ta rqzana da batun Abba da tasan haka zata faru da ta bi jiddah sun tafi Abba ne ya katse mata tinaninta 

    "Tinanin me kuma kikeyi ki zauna ki ci abincin mana" toh Abba na koshi" me kika ci da kika koshi?" Ba komai Abba na makara ne" sai da Abba yay mata da gaske taci kadan, jefi jefi take satar kallon *sahal* da ya cika yay fam, karfe tara saura minti biyar suka bar gdan


    Gudu sosai yake da ita a titi, sosai *sahala* ta tsorata da yanayin da taga yana tukin, sai da suka kusa karasawa b.u.k ya taka burki fuskar nan tashi a hade


    "Sbda kin raina ni shine zaki ce bari kizo yau a makare koh, kuma duk salan na rage miki hanya muje makaranta a ce ke kanwa tace har da kin tafiya da wuri, toh a nan zan sauke ki kuma na baki 10 mnt bayan na shiga klaz Allah baki ikon kara mintina akai kiga abinda  zan miki fita ki bn waje" ba tare da ta tanka mashi ba sai ma turo karamin bakinta da tayi ta bude murfin motar ta fice, tana fita yaja motarsa yay gaba


   Sai da tayi kusan minti shida tana tsaye duk wata motar da zata wuce a cike take da mutane 


   Jiddah kan ganin har tara tayi *sahala* bata zo ba duk sai taji ba dadi, dan kwata kwata bata san abinda zaa a zo ana dizga ta hakan yasa ta dau wayarta da ta kirata bugu biyu ta daga tare da karawa a kunnenta 

  

  "  *sister* ina kika tsaya ne har yanzu baki karaso ba" bari kawai ina nan kqn titin b.u.k din yaya ne fa Abba yace mu taho tare dan wulakanci sai ya saukeni" ki hanzarta dan ga motarsa nan ta iso" toh kawai tace tare da kashe wayar 


   Motar da taga ta tsaya gabanta ne yasata daga kanta dan ganin ko waye, zaro ido tayi cikin mamaki wa nake gani kamar M.D shima din wanda ta kira da M.D dariya yayi 

" makaranta zaki ne naga kina tsaye" wlh kan toh shigo nima makarantar zan shiga, ba musu ta bude ta shiga yaja sukai gaba



Ku cigaba da kasancewa dani dan jin waye wanda *sahala* ta shiga motarsa



*Eloqunce writers association*



💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *91-95*



     "Ya akayi na ganki a titin nan a tsaye ina driven na ku" m.d ya fda yana kallon *sahala* murmushi tayi na takaici " makara nayi shine suka taho shi da jidda, ni kuma da yayana na taho ya sauke ni a nan wai yana da uzuri na gaggawa, ya bayan saduwa?" Sahala ta tambayi m.d sbda gudun kar ya kara jeho mata wata tambayar 


    " wlh Alhamdulilah kwanaki ina taso na sami numbern ki waje dan klaz din ku shine yace bashi da numbern ki amma yace kina b.u.k shine nace zan zo nemanki kuwa" Ayyya gashi yanzu mun hadu kasan tin bayan da kuka gama makaranta bn kara ganinka ba sai yanzu" wlh kuwa sai tanzu Allah ya hada mu" yqnzu sai ki sami numbern ki a waya, ma dinga gaisawa naga kamar yanzu kina sauri" wlh kuwa numbern ta ta sa mashi lkcn sun iso dai dai hall din sannan ta mashi godia ta fito fuskarta dauke da murmushi 


    Sosai ran *sahal* ya baci lkcn da ya hango wani ya sauke *sahala* a mota, daman baifi minti goma da shigowa ba yana ta kallon ta inda zata bullo 


   Hankalinta a kwance ta fara takunta har ta iso kofar hall din, gaba daya yan cikin hall din suka bita da kallo, kowa da abinda yake rayawa a ransa, wasu su ce dan tai suna a gunsa take latti wasu suce sanshi take, haka dai kowa ya dinga saka abubuwa, 


    Gud morning sir....... Kallon da sahal yayi mata ne yasata saurin tsuke bakin ta, 

    "Shigo nan" ba musu ta shigo ta karaso inda yake, minti nawa kika kara akan wanda na bayar" agogon wayarta ta kalla, sannan ta turo karamin bakinta minti uku na kara kuma abin hawa ne bnsa mu ba shi........ Bai jira ta karasa ba ya harareta bace ki bn waje mu zuba ni dake, zan kamaki ne, ciki ciki tai magana sannan ta nufi wajen zaman tata


Dan karamin tsaki Rufaida ta ja, "gaskiya rukayya sai na koyawa yarinyar nan zama jibi yadda take ta faman yi mashi abu, yanzu da wani ne yayi ba ita ba ai da anshiga uku" aiko dai ki taka mata burki sumayya ta fda,  shiru sukayi gaba daya suna sauraron karatunsa cikin bacin rai ya gama karatunsa ya fice bayan ya basu grp assignment akan zai karba wani satin



   Bayan ya fita suka fice cpteria jidda ta kalli sahala cike da tuhuma, "waye wanda ya kawoki makaranta yau naga ba motar gda bace" toh irin wannan bata rai haka, gaskiya baza ki sanshi ba dan lkcn da suka gama makaranta muna j.s3 sunan sa muhammad amma M.D ake ce mashi shine head boy lkcn suna mkrnta, muna shiri dashi sosai shima nan makarantar yake shine ya dakko ni dazu da na rasa abin hawa" gyada kai jidda tayi shike da gamsuwa, "Ai na zaci kwashe kwashe kika fara" dariya sukayi gaba daya, 


Da daddare *sahala* da jiddah na falo suna assignment din su wayar mumy tai kara ta dauka tare da karawa a kunnenta "toh" kawai sukaji tace ta sauke wayar 


   *"sahala* tashi ki kaima yayan ku abinci yana dakinsa" sosai gaban *sahala* ya shiga faduwa yau tasan ta shiga uku, gashi ba damar tace baza ta ba jiki a sanyaye ta dauki abinci ta nufi dakinsa da salama ta shiga falon ba tare da ya dago ba ya amsa mata sallamar, kusa dashi ta ajiye kwanan ta mike zata fita


   "Zauna" ba musu ta koma ta zauna, sai da ya gama abinda zaiyi da wayarsa sannan ya dago ya kalleta fuskar nan tashi a tamke " uban waye ya kawo ki mkrnta yau" turo bakinta tayi ba tare da tace komi ba, " Au wasa nake miki ina tambayarki ki turo min baki wlh in kina min haka watarana sai na fasa miki bak, ki bn amsar tambayar da na miki"


    "Tare mukai makaranta dashi, yazo wucewa ne har lkcn bn samu napep ba shine yace na shigo ya sauke ni ni kuma ganin na makara lkcn da kaban ya kusa kurewa shine na shiga" 


  " wannan ya zama na farko kuma na karshe da zan ganki da wani namiji a makaranta ko da wasa kika kuskura na ganki da namiji ki fara tausayawa kanki kinsan Allah ba zan yi kaffarar rantsuwa ta ba sai na zane ki, idan kuma kina ganin wasa ne toh kije ki aikata, tashi ki bn waje" ba musu ta mike ta fice falo ta koma ganin mumy bata falon yasa ta bawa jidda lbrn abinda ya faru sosai jidda tayi dariya, ko assignment din basu karasaba suka fara fda kowa yayi bngaren su suka kwanta


  Washe gari da suka tashi ba Wanda ya kula wani har sukaje makaranta 



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *96-100* 



    *wannan shafin sadaukarwa ne gare ki kakata kuma kawata bn mnta dake ba, kina daya daga cikin masoyan wannan littafi kuma masu bibiyarsa Hafsat Abubakar, fatana Allah ubangiji ya bar mu tare, ILYSM*




    Tin takwas na safe suke a cikin makaranta kasancewar yau Dr *sahal* zai karbi assignment din sa kuma presntn za'a yi, suna zaune wayarta tai kara ganin wanda ke kiranta yasa ta dauka tare da karawa a kunnenta 


    "Ina bakin hall din da kuke ki leko mu gaisa har zan wuce na gano ki" badan *sahala* ta so ba ta mike dan su gaisa dan dai kawai yace ya ganta ne


   " Jiddah bari naje mu gaisa da M.D yana bakin hall din nan" bata jira cewar ta ba tai waje 


  Kusa da motar sa ta tsaya suna ta faman hira cikin kwanciyar hankali amma mafi yawan hirar su dan gane da makaranta ne 


   Tin da ya tqho daga nesa ya hango kamar *sahala* a tsaye da wani tana hira, sosai ransa ya baci, ji yake kamar zuciyar sa ta fashe sbda bacin rai, 


   Kqmar daga sama ta ji tsayuwar motar sa, cikin tashin hankali ta dago fuskarta dan ta tabbatar da wanda ke gabanta, ido hudu sukayi dashi, cikin dakewa ta dauke idon ta M.d taima sallama ta shige hall din


   Fuskarsa a hade ya fito daga motarsa ya shigo hall din, yanayin da suka ganshi yasa yan ajin kara nutsuwa sbda ba su taba ganin sa a hakq ba, 


    Ranar bai bar ajin ba sai da grp hudu sukayi prsntn ciki harda na su *sahala* yana fita su jiddah suka fita, 

  " wai mi yasa *sahala* baki jin mganar yaya ne sai kina tsayawa da samari yanzu idan ya dake ki kice me bayan sai da ya gargade ki" jidda ta fda bayan sun shiga mota zasu tafi gda, 

    " kinga malama ina ruwanki haka nace miki shi m.d saurayi na ne, kuma ko saurayi nane ai ya isa a ce na isa fara kula samari, ko shi zai auren in ban kula samarin ba" ta karashe maganar fuskarta a hade, har suka karasa gida bbu wanda ya kara kula wani a tsakanin su


Suna zuwa gda su yada zango a falon mumy lkcn ummi ma na falon kamar daga sama *sahal* ya turo kofar fuskarsa a hade wata waya ya zaro cikin bacin rai ya janyo *sahala* ya fara dukan ta da ita, kuka take sosai amma yaki sarara mata, mumy na gefe ko kallo basu isheta ba, ummi sai mgana take mashi amma yaki denawa, jiddah kuwa itama kukan take 


  *"sahal* wlh idan ka kara mata duka daya ban yafe ba" cak ya tsaya tare da sakin bulalar a kasa, ummi ce ta karasa ta rungumo *sahala* wadda sbda azaba kukan ma dena fita yayi 


   " bnda iskanci ko me tayi ai dukan nan yayi yawa, bnda iskanci tayaya kanaji ana maka magana kashare  mutane ga yan iska ko mi tayi maka ai dukannan yayi yawa" 

Ummi fa nai mata mgana akan ta daina kul.........." Daga masa hannu tayi alamar yayi shiru " bn tambayeka komi ba" ta fda tana  jan hannun *sahala* suka tafi bn garan su

Jiki a sanyaye ya zauna kusa da mumy kallon da yayi ma jiddah ne yasa ta tashi tayi daki 


Kansa ya daura a cinyar mumy ya fara mgana kamar zai yi kuka " mumy bn san mi yasa na daketa ba *sahala* bata jin mgana kula samari take a makaranta wancan satin na mata mgana shine yauma tayi" kar ka damu my son zan mata mgana kayi hkri kaji" ta fda tana shafa gashin kansa da kyar ta lallabashi ya ci abinci sannan yaje ya kwanta 


   Washe gari bai tashi ba sai kusan karfe tara a gagauce ya shirya ya tafi mkranta sbda akwai taron da zaayi da dalibai karfe goma, cikin wani dakaken yadi mai tsada ya shirya sosai yayi kyau kamar mi sai dai fuskarsa ta dan fda tayi fayau ko break fast bai zauna yayi ba ya wuce makaranta

Ranar bai dawo ba sai kusan laasar a falo ya tadda mumy ummi jiddah sai sahala suna hira da sallama ya shiga bayan ya gaidasu ya zauna ya ci abinci sama sama yana lura da yadda ummi take share sa


  Yau kwana uku kenan da zane *sahala* har lkcn ummi bata sakko daga fushin da take ba a daki ya taddata tana kwance, da sallama ya shigo ta amsa ba yabo ba fallasa, a kasa ya zauna ya dora kansa a cinyarya 

   " Ummina kiyi hkri ki yafe mun bazan iya jure fishinki a kai na ba wlh laifi tamin na ja kunnenta ta ki ji kwata kwata ta raina ni amma wlh in baki so na daina hukunta ta" ya karashe maganar kamar zaiyi kuka


   Sosai jikin ummi yayi sanyi "bn hanaka ka hukunta ta ba *sahal* amma ka dinga musu saffa saffa duka ba ya gyara" ranar bai bar dakin ba sai da ummi ta hkra



Ku cigaba da kasan cewa dani dan cigaba da kawo muku lbrin



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *101-105*



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su *sahala* anci Rabin semester har sun tafi hutun mid semester, ba laifi yanxu *sahal* ya dan rage takura mata kasancewar bata yin latti kuma bata sayuwa da maza, sai dai wata sirfa da suka sira ita da jidda ta saka yan kananan gyale suna zuwa mkranta kuma sai sun dau kwaliyya, hakan ba karamin batawa *sahal* rai yake ba amma ya kyale su



    Tin safe suke ta shirya abinci da lemuka kala kala kasancewar yau big bro zai dawo daga madina yaje karatu na  wata biyu 


Karfe 12:00 jirgin su ya sauka a filin jirgin malam Aminu kano, ummi da *sahal* ne suka dauko shi sosai *sahal* yay murnar ganin dan uwan nasa haka ma ma ummi a haka suka wuce gda kowa farin ciki fal ransa


Da sallama suka shiga falon da gudu jidda da sahala suka zo suka rungumeshi suna mashi barka da zuwa shima din rungumesu yayi cike da kewar kanan sa, bayan ya sake su ya wuce inda mumy take ya gaidata fuskarta dauke da fara ta amsa mashi gaisuwarsa ta mashi sannu da zuwa 


Bayan sun gama hirar yaushe gamo ya wuce daki yay kwanka, bayan yayi kwanka ya dawo sukai lunch sannan suka dora da hirar su 


   "Big bro nikan bnji kace ga tsarabar mu ba ko ba kayo mana bane" *sahala* ta tambaya tana kallon yayan nata, hararta shima yayi cikin wasa " Ai ni na mnta dake ma kowa nayi mashi tsaraba amma bnda ke" turo karamin bakinta tayi " daman ai ummi da Abba ne kawai ke sona a gdan nan" da sauri *sahal* ya dago ido ya kalleta, murmushi kawai yayi ya dauke kansa wanda ni kaina bazan iya fassara wannan murmushin na meye bane 


"Toh da wasa nake miki kema nayo miki tsarabar ki sai na huta tukunna anjima na baku" murna sosai sukayi sanda ya Abkr ya basu tsarabar su 


  *Bayan kwana biyu* 


Da daddare gaba daya suna falo suna hira bayan sun gama dinner dady yay gyran murya ya fara mgana cikin nutsuwa


     "Abubakar, sahal, jiddah da kuma ke sahala, ina so ku shirya jibi zaku tafi katsina kuje ku gano dan gidan margayya tare da mijinta sbda tin rasuwarta baku je ba gwanda mu muna dan lekawa" tin da *sahala* taji an ambaci katsina ta fara murna kamar mi kowa ya kalli fuskarta yasan tana cikin farin ciki 


  "Dady amma sati daya za muyi koh" gaba dayan su suka zaro ido "amma gaskiya *sahala* baki da hankali kawai sai mu tattara mu tafi gdan mutane muyi sati a can makarantar kuma fah" jiddah ta fda tana kallon ta, dariya dady  yayi baza kuyi sati ba kwana 2 kawai zakuyi Ku dawo turo baki tayi dady ni dai gaskiya sati daya zanyi" toh ai sai kije kiyi din ana fda kina fda da kin san da zuwan" mumy ta fda fuskarta a hade, shiru sahala tayi kamar zata yi kuka 


  "Mumy a barta tayi satin ni naje na dakkota" sahal ya fda yna maida dubansa ga mumy ba *sahala* ba ni kaina sai da nai mamakin sahal da yace a barta 

"Bbu inda zata tai sati, makarantar fa taje Ku dawo tare" Mumy plsssss ki barni naj....... Kallon da mumy tayi mata ne ya sata yin shiru duk yanda sahala ta so tayi sati mumy taki dole aka hkra



Yau ta kama littinin yau ne kuma tafiyar su sahala katsina tin safe suka fara shiri karfe 10:00am sukayi ma su mumy sallama suka kama hanyar k.t sahal ne ke drvn din su suna tafe suna hira jefi jefi jiddah kan sa musu baki har suka isa garin k.t suna sauka *sahala* da jiddah ne suka fara shiga gdan aunty nafisa na zaune sai wani yaro dan kimanin shekara bakwai ga dukkan alamu kuma shine dan margayan 

Aunty nafisa ta amsa musu cike da tambayoyi a fuskarta cikin girmamawa suka gaidata ta amsa


  "Aunty baki gane mu ba koh" sahala ta tambaya fuskarta dauke da fara'a 

  "Wlh kan bn gane ku ba" daga kano muke *sahala* ce" zaro ido tayi cike da mamakin ganin su "sahala daman zan sake ganinki, kinga yanda kika girma" dariya kurum tayi, "Aunty da baki muke suna waje" jidda ta fda ganin sahala bata da niyyar fda jidda ce ta musu iso har falon sahala ce ta taimakawa aunty suka yi girki sannan suka ci 


    Abba sanda ya dawo ya gansu ba karamin farin ciki yayi ba ranar haka suka dade suna hira sannan suka tafi makwancin su




*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *106-110*


Washe gari tin da aunty nafisa ta tashi daga bacci bata koma ba ta fara shirya musu break fast, karfe bakwai *sahala* ta fito ta taimaka mata da gyare gyaren gda karfe takwas suka gama jere komai a dining sannan ta shiga wanka


Karfe tara dai dai suka fito gaba daya danyi break fast bnda *sahal* da ko tashi baiyi ba daga bacci, 


   "Dota ina yayan naku naga shi bai fito ba" abba ya fda yana kallon *sahal*tabe bakinta *sahala*,tayi "bai tashi daga bacci" nan suka cigaba da hirar su har kusan karfe goma 


   "Sahala je ki duba kiga in sahal ya tashi ki kai mashi abinci kinsan miskilancin shi ba zai barshi ya fito ba" ya Abkr ya fda yana kallon sahala, ba tai musu ba ta mike ta fice daga dakin da sallama ta shiga dakin ciki ciki ya amsa sallamar sannan yay mata umarni da ta shigo 


   "Yaya ina kwana" lpya lau ya fda a takaice, a kawo ma abinci yanxu, "mi kuka girka?" Ya tambaya kamar wanda akama dole "doya da kwai sai dankaki sai kuma tea nd bread" tabe bakin sa yayi " bnsan jin cin su, indomie nike so da kwai sai ki hado mun da tea amma bnda bread" turo karamin bakinta tayi " mutum sai faman iyayin jaraba a gdan mutane ma kace sai ka zabi mi zaka ci" ta fda tana ficewa, sahal da bata zaci yaji ba yay murmushi kawai tare da shafa sajensa hade da cije lebensa na kasa 


Cikin minti goma sha biyar ta hado mashi ta kawo masa har zata fita ya janyota ta fdo kansa hannunsa yasa gaba daya ya riketa 


   "Ki fdan mutumin da yake da iyayi, laifi ne dan na zabi abinda zanci ko kuma sabagen raina nine da kikayi" sahala kan kwata kwata kasa motsi tayi dan tin da ya janyota taji wani iri dan tin da take a rayuwarta namiji bai taba yi mata haka ba 

Iskar da taji ana hura mata a ido ne ya katse mata tunaninta 


   " ya kikai shiru ko bakin rashin kunyar ya mutu, ai nasan maganinki ba dani keke ba mu zuba ni dake tashi ki ban waje" jiki a sanyaye ta tashi ta bar dakin dan gaba dayq ya gama kashe mata jiki tin da take dashi bai taba yi mata haka ba, da kyar ta tattaro nutsuwarta ta shiga falon ta zauna suka cigaba da hira 


Sahal kan tana fita yay dariya ya jqnyo abincinsa ya fara ci hankalinsa kwance 


A haka su sahala sukayi kwana 2 a garin katsina daman mutanen katsina ba dai karamci ba cike da kewar junan su suka baro grn aunty nafisa kan har kuka tayi 



Yau sati guda da komawa makaranta sosai suke karatu sbda malamai sun fara cin rabin karatun sy wasu ma sun kusa kammalawa 


Da daddare suna zaune a falo suna hira jiddah ta kalli sahala ta fara magana 


     "Sis muje daki mu samu yaya sahal ko zai na koya mna karatu a week end kinsan abubuwan sun fara yawa yanzu" turo baki sahala tayi " nima wlh na dade ina tinanin hakan amma kinsan shi da wulakanci kila in muka je ya dizga mu" kar ki damu tashi muje mu gwada, jiki ba kwari sukayi sallama suka sameshi a daki 


   "Yaya daman karatu muke so kana kara yi mana bita a gda sanda ka ke da lkci" sahala ta fda kanta a kasa, bai tanka musu ba sai da suka fidda ran da zaiyi mgana ya dago ya kalle su 


"Allah ya kaimu zan na yi muku asabar da lahadi karfe 10:00-12:00 amma fa kuka kuskura kuka min wasa duka zaku ci" 


   "Insha Allahu za mu kiyaye" cike da jin dadi sukai mashi sallama suka fice daki 


Sanye suke cikin riga da wando na pakistan sukayi roln da karamin gyale kalar wando tsayawa fadar yadda sukai kyau bata lkc ne ummi sukayi ma sallama suka fice makaranta, tin da suka fito a mota ido aka bisu dashi kowa da abinda yake sakawa a ransa, a haka suka shiga aji 


   Da sauri ya fito daga motarsa kasancewar tara tayi har da kwata bai shigo ajin ba maganar da yaji matasa nayi ya sashi tsayawa cak 


    "Abokina gaskiya babies din nan na burge ni, dama za mu samu kula mu ai da mun samu na zuwa chasu dan ba karamin haskawa zamunayi ba" bari kawai sadiq ni sahala ma tafi burgeni duk yan matan makarantar nan ina ga ba wanda ya kaita iya daukar wanka 


 Ba karamin baccin rai sahal ya shiga ba hakan yasa ya shige aji baima tsaya ya karasa jin me samari suke fda 


Ganin irin kwaliyyar da su jiddah sukai yasa ransa ya kara baci fuskar nan tashi a hade ya gama karatunsa ya fice yana fita su rufaida suka bi bayansa 


   Yana zaune a office dinsa ransa duk a jagule maganganun samarin nan ne ke mashi yawo a kunne akayi sallama aka shigo ganin wanda suka shigo office din yaja karamin tsaki 


    "Sir daman zuwa mukayi mu gaisar da kai har za mu wuce muka shigo" owk ngde sosai ya fda yana lumshe idonsa rufaida kan ba karamin burgeta ya karayi ba 


  Sir....... Zata kara magana ya dakatar da ita dan Allah kwa dawo gobe koma menene yanzu bnsan hayaniya kadaici nake so 


Ba dan su so ba suka fice jiki su duk a mace ganin zaman bashi bane mafita a gareshi ba ya dau key din motarsa yay gda



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *111-115*



Yana zuwa gda ya shige dakinsa bai bi ta kqn su ba, da daddare bayan sun gama dinner ya kalli dady 

   "Dady daman akwai maganar da nake so muyi da kai" gaba daya dady ya maida hankalin sa gareshi " ina jinka sahal mi ya fru


   "Dady shigar da su sahala suke suna zuwa makaranta Sam baya dacewa wlh kowa kallon yan iska yake musu, dazuma wasu samari naji suna hirar su nan sahal ya kwashe komai ya fdawa su dady, sosai ransu ya baci 


    "Daga yau sai yau karna kara ganin wani a cikinku yaje makaranta da gyale koda kuwa babba ne, ku na saka hijab, in kuma kuka karyan doka wlh summa tallahi ranku in yay dubu sai yq baci" dady ya fda ransa a bace nan ma abba yay musu fda ya nuna bacin ransa sannan ya shema mumy gobe da daddare suje sukara yanko yadin hijabai da yawa sannan ya sallame su 

Sosai su sahala sukaji haushin abinda yayan nasu yayi musu haka suka dade suna gulmarsa sannan suka kwanta 



Tin daga ranar da sahal ya kai su kara wajen mahaifin su basu kara zuwa makaranta da gyale ba kullum da hijab suke zuwa tin basu saba ba har suka saba



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, saura sati guda su sahala su fara exam din first semester tin da aka kafe musu time table suka maida hankali wajen karatun su ko da wasa basa zama a mkranta dan hira sai dai suyi tq bitar karatun su kamar kullum yaums suna zaune suna krtun su suka kasa solvn din wani topic da sukayi duk yanda suka so su gqno yadda akayi shi suka kasa 


   "Jiddah ku jira naje na tambayo mana yadda akeyi bnso mu bar skul din nan bamu gama wannan topic din ba" sahala ta fda tana mikewa office din Dr sahal ta nufa da sallama ganin rufaida da kawayenta zaune a office din yasa ta hade ranta 

Bayqn ya amsa mata sallama yay mana izinin shigowa, ganin ta tsaya bata da niyyar mgana ya dago ya kalleta 


  "Yq akayi kin shigo kuma kinyi shiru" turo bakin tayi ta karasa inda yake littafin da suke krtn dashi ne ta ajiye mashi a gaban sa  " muna yin krtu ne kuma mun kasa solvn wannan shine na kawo ka koya min" ta fda tana nuna mashi wajen, sosai ran rufaida ya baci da yadda takeyi mashi mgana cikin shagwaba 

" toh anawa zan koya miki shi" ya fda yana kashe mata ido daya wayyo zo kuga yadda rufaida tq zaro ido zuciyarta ta fara zafi lalai sai ta koyawa yarinyar nan hqnkali

"Allah zai biyaka" dariya kurum yayi ya fara koya mata sai da ya gama ta fice, tqna fita yq hade fuska kamar bashi bane, 




Sun kammala jarabawar su cikin kwamciyar hankali, sai dai abu daya da yake damun ta tinanin yayan nata wanda kullum shi ke hanata sukuni ta kuma rasa wanda zata fdawa ko taji sanyi, ta tabbatar wa kanta ta dakko dala ba gammo tin da zuciyarta ta fara san wanda ko a mafarki ta san bazai taba santa ba kowa yaga sahala yasan tana cikin damuwa, idan kuma aka tambayeta tace bakomai




Yau satin su daya da kammala exam suna zaune a falo da daddare gaba dayan su dady yq fara magana 


    "Sadiq da kai da sahal ya kamata kuyi aure yanzu na baku nan da sati guda ku kawo mata in ba haka ba wlh na aurar da ku ga wanda na ga dama ba su sahal ba hatta jiddqh da *sahala* sai da sukai saurin dagowa dan kallon fuskar dady ganin fuskarsa bbu alamar wasa yasa su sunkuyar da kansu 


   "Dady ni dai ina da wadda nake so toh baban ta yace bazai aurar da ita ba sai ta gama krtu shiyasa bn fda mata ba" 

Mtwwww zancen bnza bama tasan kana yi ba wace yarinyar waye mahaifinta? Dady yay masa tambayar 

   "Dady bafa kowa bace yarka ce jiddah" ba dady ba hatta ummi Abba da kuma mumy sai da sukai mamaki bare kuma jiddah, sosai sukai murna dajin batun sa suka sa mashi albarka 


Kai kuma fa *sahal* kaima kana da wadda kake so " eh dady" a razane *sahala* ta dago ta kalleshi jin hawaye na kokarin zubo mata yasa tai saurin sun kuyar da kanta kasa 


   "Toh kai kuma wace ce wadda kake so" Abba ya tambaya "Abba daman mumy tasan wadda nake nasan yarinyar da nake so bai zama lalle ta soni ba amma dan Allah dady a rokar min ita da soni, wlh mumy ta san ina santa tin da dadewa" 


Cike da mamaki iyayen nasa ke kallonsa koma wacce wannan ba da wasa yake santa va ita kuwa  sahala hawayen da take boyewa sai da suka zubo tai saurin gogewa, duk abinda take mumy na lura da ita sai yqnxu ta gane dalilin damuwar yarta ta kuma gudan jininta gyara zama mumy tayi sannan ta fara mgana





*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *116-120*



     " *sahal* na da wadda yake so tin tana  karamarta koma nace tin sanda aka haifeta yake dakon santa kuma ya nemi alfarmar kar na fdawa kowa har sai ta isa auren, daga ni sai shi muka san zancen, sannan yarinyar da yake so insha Allah muna fatan itama zata soshi" 


   "Mumy kiyi mana bayani mana har yanzu ba mu fahimci inda zancenki ya nufa ba" ummi ta fda cike da san karin bayani 


   Murmushi mumy tayi "Ummi ba kowa bace face yarki *sahala* muna kuma fatan za'a bamu ita" ba su ummi ba hatta sahala sai da tai mamakin jin wai ita sahal ke so tin tana karama 


Cikin farin ciki Abba ya fara mgana "Masha Allah, Allah shine abin godia da yasa ba tare da an hada Ku ba zaku dorar mana da zumuncin mu Allah ya baku ikon hkri da juna gaba mumy dady ummi, sadiq da sahal suka amsa da Amin 


   " Abba bafa aji ta bakin su *sahala* ba ko sun amince" ummi ta fda  "A'a a basu lkci tukunna su dan zanta su sasanta tsakaninsu in sun yarda za muga alama ai" Abba ya fda nan kowa ya tafi daki cike da farin ciki fal ransa 


  Washe gari bacci mai nauyi ne ya dauki sahal dan ya dade baiyi bacci mai dadi kamar na yau ba har suka gama suka gama break fast bai tashi ba, gaba daya suka fice dan yima abokin Abba taaziyyar mutuwar mahaifiyarsa *sahala* kawai aka bari a gda 


Karfe 12:00 sahal ya tashi daga bacci da wata azababiyar yinwa ya tashi, da kyar ya shiga bandaki yay brush ya fito falon mumy ya nufa ganin bbu kowa yasa yay falon ummi 


  Tana kwance kan doguwar kujera tana sanye cikin bakar doguwar riga kanta bbu dankwali tana kallon maimaicin shirin *Happy new year* a mbc bolly wood ya turo kofar tare da sallama kwata kwata bataji shiba sai muryarsa da taji sanda ya iso kusa da ita 


     "Koh baza a kula ni ba ina laifin in nai sallama a amsa min" mikewa tayi zaune tare da turo bakinta " bnji shigowar taka bane ai" kusa da ita ya zauna "ba gaisuwa" "ina wuni" ta fda a takaice "lpya lau" a tqimaka min da abinci yinwa nakeji sosai" ba tare da tayi mgana ba da wuce dining ta kawo mashi 


   "Haba sweat hrt yanxu wannan abinci ai yayi min kadan kin san yinwar da nakeji kuwa, duk da ma sanda na ganki sai da naji na koshi" ya fda yana kashe mata ido 

Sosai abinda yaya sahal keyi yake bata mamaki daman duk miskilancin nashi haka yake maganar da yayi mata ne ya katse mata tunani 


   " yana ji kinyi shiru koh har yanxu ban karbu ba a zuciyarki, sakkowa yay daga kan kujerar ya dawo kusa da ita tare da kamo hanunta 


   "Cwt hrt kiyi hkri da duk laifin da na miki a baya ki yafe mun kishin ki kawai nake ki lura indai ina miki fda toh in na ganki da saurayi ne, tin ranar da mumy ta haifeki naji sanki a zuciyata, tin daga lkcn nai alkawarin kin kula ko wacce mace da sunan soyayya plssss kar ki ce min baki sona" 


  "Ba komi yaya na yafe ma Allah yasa hakan shi yqfi alkairi, ta fda fuskarta ba yabo ba fallasa, jiki a sanyaye ya dau plate ya zuba abincin ya fara ci yana rokon Allah ya bashi nasarar koyawa *sahala* sanshi 



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su sahala anyi sati biyu da komawa makaranta har yau dr sahal bai shiga a jin su ba 


A gaggauce suka shirya suka tafi mkranta kasan cewar yau karfe 10- 12 suke da dr *sahal* a kofar shiga hall dn suka hadu da juwairiyya suka tafi suna hira har suka je mazaunin su dai dai sahala zata zauna rufaida ta janyo mata hijab dinta 


   "Karamar yar iska musulunci a fili kafirci a boye, an iya saka hijab har kasa amma ana bin office din malamai ana karuwanci, sosai kalmar karuwar da ta kirata ta bugi zuciyarta ba tare da ta tankata ba ta zauna 


   "Ai na zaci zaki musa na kawo shaidu bnza yar iska wanda kike shishigewan yafi karfinki yarinya sai dai ki ga anayi" ta fda tana dungure mata kai


  "Cikin bacin rai *sahala* ta dago fuskarta ta kwadawa rufaida mari har guda biyu kyawawa dai dai sanda dr *sahal* ke karasowa ajin


   "Akwai dan iska kamar ke bnza ke a dole kina sanshi to bema san kina yi ba, kuma ni nafi karfin naga namiji nace ina so koda kuwa sanshi zai kashe ni jahila kawai" 


Ganin dr *sahal* tsaye bakin kofar hall din yana kallon su yasa duk suka zauna, cikin bacin rai yaje gaban bord su waye *sahala* nd rufaida ku fito waje 


    Cikin nutsuwa suka fito har suka karaso inda yake " sbda baku da hankali baku san mutuncin kan ku ba zaku zauna kuna cacar baki ke kuma ga saurin ido har da marinta sbda ga saarki koh" ta bude baki zatai mgana ya daga mata hannu bn saki kiyi mgana ba idona ya riga yaga komai ya fda cikin tsawa ba karamin firgita tayi ba da tsawar da yay mata hakan yasata fara hawaye ba shiri


Ke kuma rufaida kike ko wa, ki fita idona na rufe, idan ma akaina kike fda toh gwanda ki taimaki zuciyarki ki bata hkri, ina da wadda nake so, yar uwatace kuma kanwa tace tin tana karama nake santa kuma ba ke kadai ba duk wanda yake da tinani irin nata gwanda ya cireshi" yay tsaki ya dau takaddunsa yay waje, gaba daya jamaa sukayo kan rufaida suna zaginta ta zubarwa da kanta mutunci kuma tasa malamin su yayi fishi


Sahal na fita sahala ta koma wajenta tana rera kuka kamar wadda aka ma mutuwa mutane sai bata hkri suke suna Allah wadare da halin rufaida



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *121-125*



Claz captn da wasu shugabanni ajin su uku suka bishi dan bashi hkri,  da kyar suka samu ya hkra amma bazai shigo yau ba sai gobe 2:00-4:00 sannan suka dawo aji 


    "Munje mun bawa dr sahal hkr amma yace bazai shigo aji ba yau sai da gobe zai shigo 2-4 dan Allah a dinga kokarin kiyaye dokar sa" claz captn ya fda lkcn da suka dawo ajin kasancewar shi kadai suke dashi yasa duk suka fara ficewa 


     Har *sahala* ta koma gda ba ta daina kuka ba bbu irin rarrashin da jiddah bata yi mata ba, amma taki yin shiru, sanda su mumy suka tambayi dalilin kukan ta jidda ta basu lbri, hkri suka bata da kyar aka samu ta dan rage kukan amma har lkcn idonta na zubda hawaye 


   Sai dare sahal ya dawo gda sanda ya shiga falon ummi bbu kowa sai jiddah ta zaune tayi shiru tana tinani

   "Ina su ummi suke?" Sahal ya tambayi jiddah bayan ya amsa gaisuwarta, "suna bangaran mumy" *sahala* fah" tana cikin daki sai kuka take har yanxu ma taki cikin abinci" lkci guda fuskarsa ta canza ta shiga damuwa "zubo mata abincin ki kawo min dakinta ina jiran ki" ya fda yana wucewa hanyar dakin ta, da sallama ya shiga dakin, lkn tana zaune akan gadonta ta hada kai da gwiwa tana rera kuka a hankali, runanun idonta ta dago ta sauke su akan sa lkcn da ya zauna a gefen ta 

Kallonta kawai yake har lkcn bai tankamata ba mintinsa uku da zama jiddah tai sallama ta shigo ta ajiye mashi flask din abincin ta juya 


     "Sakko ki ci abinci" *sahal* ya fda fuskarsa a hade, kallo daya tayi mashi ta maida kanta kasa, "mgana fa nake miki kikayi min shiru" "na koshi bnjin yinwa'' 


    Ganin bata da niyyar  cin abincin ya hade fuska ya dakko abincin ya ajiye mata a gabanta, nan take ya koma mata yaya sahal din su na da "wlh kin ji na rantse tin kan raina ya baci kema naki ya baci ki dau abincin nan ki ci, idan ba haka ba ya cije lebensa wanda kana gani kasan ba wasa a fuskarsa, ganin da gaske yaya sahal zai bata ranta yasa ta fara tura abinci a bakinta, a haka har ta koshi, dauke plate din yay daga gabanta sannan ya mika mata ruwa tasha kadan 


Janyota yayi ta lafe a jikin sa kamar wata mage daman *sahala* ba dai san jiki ba " kiyi hkri habibty da bn tsaya naji baa tsin fadan ku ba nayi miki tsawa cikin mutane ki yafe mun kinji" ya karasa maganar kamar zaiyi kuka sai da ya kusa yi mata kuka sannan ya samu ta hkra




Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su jiddah ana shirin zana jarabawar second semester nan da sati hudu soyayyq ake mai tsafta tsakanin masoyqn hudu, sadiq da jidda sai *sahal da sahala* zumuncin su kuma yqyi karfi sosai da juwairiyya amma har lkcn bata san dr *sahal* yayan su jiddah bane, dan duk zuwan da take basu taba haduwa ba


     Da matsanancin zazzabi *sahala* ta tashi dashi, ganin yadda take rawar sanyi yasa jiddah saurin fita dan kiran mumy a falo suka ci karo " mumy sahala ce bata da lpya" da sauri mumy ta shiga dakin ita kuma tayi bngaren ummi dan ta sanar da ita, kan ummi tazo har *sahala* ta suma da sauri ummi ta kira Abba suka dauketa sukayi asibiti


   Cikin minti goma sha biyar suka isa asibitin, taimakon gaggawa aka mata aka shiga da ita, duk yadda likitocin suka so ta farfado a lkcn abu ya faskara har kusan awa biyu amma taki motsi ba karamin tashin hankali suka shiga ba, sadiq ne ya tuna da sahal yasa yay saurin dakko wayarsa dan ya kirashi ganin missed kal din sahal din har guda uku yasa shi saurin kiransa



   A bangaran *sahal*kuwa tin da ya shiga aji yaga baiga su  *sahala* ba yay kokarn kiransu amma shiru ba wanda ya daga, ya kira mumy ma bata daga ba duk sai da ya kira yan gdan amma bbu wanda ya daga hakan ya tabbatar masa da ba lpya, yana tsaye gaban dalibai, ya fara karatu amma kana ganinsa kasan yana cikin damuwa ba karama ba wayarsa ce da tai kara yasa shi saurin dagawa tare da karawa a kunnensa


   "Haba brother ina kuka shiga gaba daya ina ta kiranku har su mumy da dady amma kunki dagawa" ya fda cike da damuwa, dan gaba daya ya mnta ma a gaban student din sa yake 


   "Wlh kaga muna asibiti, *sahala* ce bata da lpya ta suma tin dazu har yanxu bata farfado ba" cike da tashin hankali *sahal* yace "shine kuma ba a kirani ba" bai jira cewar sadiq ba ya kashe wayar takaddunsa ya tattara dan Allah kuyi hkri an kirani daga gda autarmu ba lpya" ya fda yana ficewa yanayin da sukaga dr *sahal* ya shiga ya tabbatar musu da yadda *sahal* keji da kanwarsa



Cikin minti ashirin ya karasa asibitin ganin har lkcn likitoci na kanta da yawa amma taki farfadowa ya sashi kiran amininsa dr nauwaff tare sukai karatu dashi dan yasan inshi ya shiga bbu abinda zai iyayi




*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *126-130* 




  Cikin minti goma dr nauwaff ya iso asibitin abu kamar wasa sai da *sahala* tai awa biyu sannan likitoci suka samo kanta, sannan suka fito cikin farin ciki da samun nasara 


    "Insha Allahu nan da kowane lkci zata iya farfadowa, amma bata san hayaniya tana bukatar hutu sosai" 


   Godiya *sahal* yayi ma abokinsa, sannan ya tafi rakashi, "ya kamata fa mutumina ka bar wannan koyarwa da kake ka komo asibiti zaifi ma sauki" dr nauwaff ya fda lkcn da suka karasa bakin motar dr nauwaff, ajiyar zuciya *sahal* ya sauke "abinda nima na gama tinani dazu kenan, jibi fa halin da cwt hrt ta shiga, insha Allahu muna karasa semeater din nan zan koma india na kara kwarewa a bngaran na yi ko shekara hudu ne sannan na dawo gda" gaskiya gwanda kan hakan zaifi muhimmanci, nan sukai sallama ya tafi gda, shi kuma sahal ya komo asibitin 


   *Bayan awa hudu* 


     Sadiq, jiddah na zaune kan kujerar da ke dakin sai kuma *sahal* na kwance akan kujerar dake gefen gadon *sahala* hanunsa na rike da nata, jin hannun ta na motsi yasa yay saurin dago kansa, a hankali ta fara bude idonta tin tana ganin dishi dishi har ta sauke su a haka yayan ta suna hada ido ya sakar mata murmushi, itama murmushin tayi mashi 


   "Ya jikin naki" da sauki yaya" jin maganarta yasa sadiq da jidda karasowa inda take, suka mata ya jiki, da kansa ya taimaka mata tayi brush, sannan ya hada mata tea mai kauri ya fara bata, tana cikin sha su mumy suka shigo sosai suka ji dadin ganin ta da kyar ya tilasta mata tasha tea din kadan ta ajiye ranar bai bar asibitin ba sai 12:00 dare sai da ummi ta mashi da gaske ya tafi sbda ita zata kwana da ita 



    Yau kwanan *sahala* uku a asibiti kullum sahal yana makale da ita sosai suka kara shakuwa baya barin asibitin kullum sai 12:00 sannan yake tafiya ko makaranta ma baya zuwa, kasancewar yau jikin sahala da sauki har suna sa ran zaa sallameta yasa jidda zuwa mkrnta, duk wanda ya ganta sai yayi mata ya jikin sistern ta sbda sun san bata da lpya 


    "Yau fa gdan ku zan wuce na dubo *sahala* tinda bn samu zuwa asibiti ba juwairiyya ta fda lkcn da suka fito daga hall din su zasu tafi gda


   "Owk ba matsala bari drivern namu yazo sai mu tafi" basu fi minti biyar ba da tsayuwa ba ya zo suka tafi



  " Hello yaya an sallame Ku kun koma gdan ko kuma kuna asibitin ne" jidda ta fda lkcn da ta kira wayar sahal "eh an salamemu yanxu ma muka shigo gda" toh daman tambayanayi sai na dawo" toh kawai yace mata ya kashe wayar



   A falo suka tadda sahala a kwance kana ganinta kasan taji jiki a ciwon da tayi ta rame ga wani haske da ta karayi 


   Da fara'a juwairiyya ta karasa kujerar da take "kawata ya jikin ki" murmushi *sahala* tayi "jiki yayi sauki juwairiyya kun dawo lpya sai jiya jidda ke shaidan wai kin kirata kin fda mata kunyi tafiya" wlh kuwa mumy na raka jigawa jiya ma sai kusan 8 na dare muka dawo" ayya sanunku da hanya "yau........" Wanda ta gani ya turo kofar ya shigo ne ya sata kin karasa maganar dazatayi yana sanye cikin coffee din jalabiyya sosai ta amshi fatar jikin sa 


    Cikin mamaki ta kakalo maganganunta tace "sir" murmushi yayi mata "na'am juwairiyya kece a gdan namu yau" sosai ta kara shiga mamaki sanda taji yace gdan su daman dr na da alaka da su jidda basu taba gaya mata ba maganar da *sahal* yayi ne ya katse mata tunaninta tare da shiga wani mamakin 


    "Ai har nayi fishi ace duk yadda kuke da swt hrt baki zo dubiyaba sai da na tambayi jidda jiya ta shaida min baki nan" swt hrt ta maimaita zancen a ranta 

  "Sir ni fa bn gane ba wace swt hrt din" juwairiyya ta tambaya cike da mamaki zaiyi mgana kenan wayarsa tai kara ya dauka tare da ficewa 


    Cike da zargi da tuhuma juwairiyya ke kallonsu kan tai mgana *sahala* ta fara mgana " kiyi hkri a rashin fda miki alakar mu da yaya tabbas nasan zakiji ba dadi amma kiyi hkri dr sahal yayan mune gdan mu daya kuma shine wanda zan aura"


   Sosai juwairiyya ta nuna baccin ranta kan yadda basu dauketa da muhimmanci ba da kyar suka samu suka shawo kanta har ta hkra 



    Washe gari aka wakilta mutane daga cikin ajin su dan suje su dubo sahala ciki kuwa harda rufaida juwairiyya da jiddah ne suka musu jagora har cikin gdan sannqn aka musu iso zuwa falon kasancewar akwai maza, kowa yqba kyan gdan su sahala yake, mumy da ummi ne suka fara shigowa suka gaisa " kuyi hkri sun kusa dawowa sunje ganin likita ne" ummi ta fda suna mikewa dan su bar falon 


    Turo kofar da aka yine yasa gaba daya suka dago kai suka maida duban su ga kofar, gaba daya yan dakin kallon mamaki suka bisu dashi, rufaida kan har da tsoro ne ya kamata murza idonta tayi dan tabbatar da abinda take gani *sahal* ne rike da *sahala* suka shigo cikin falon tare da sallama da kyar suka samo nutsuwarsu suka amsa musu sallamar cike da fara'a suka karaso falon kan doguwar kujerar da jiddah take ya zaunar da ita shima yq zauna kusa da ita 


    Cikin girmamawa suka gaidashi kowa fuskarsa dauke da mamaki, fuskarsa dauke da murmushi ya amsa sahala ce ta gaidasu suka amsa sannan suka mata ya jiki har lkcn rufaida na zaune kamar gunki 


   "kuyi hkr fah bamu san zakuzo yau ba asibiti mukaje kuma tq fara ragima" bakomai sir daman sahala ce kanwar taka? Dariya yayi ita ce rigimamiyar kanwar ta....maganar da sahala tayi ne yasa shi kin karasa mganar da zaiyi " kai yaya dan Allah rigimar me nayi kuma ta fda cikin shagwaba tare da dora kanta a kafadarsa, yi hkri my kanwa, nan dai sukai ta hira rufaida kan kunya ta hanata sakewa ita kuma sahala da gayya take ta faman makale mashi tana mashi shagwaba ranar dai kowa sai da yay mamakin daman haka malamin nasu yake da fara'a sun dade suna hira kafin suka tafi gda ko wannen su dauke da mamaki




*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *131-135*



    Washe gari da suka je makaranta suka bawa ragowar yan ajin lbri daman ashe sahala kanwar dr sahal ce, kowa sai yayi mamaki, nan sukai tayima rufaida tsiya daman shiyasa baa so kana jan mutane baka san ko waye shi ba, gwanda ka zauna da kowa lpya, ita ko rufaida sai dai tai shiru dan ita kanta tayi data sannin abinda tayima sahala, ashe kanwar sa ce ranar dai duk inda aka zauna hirar malamin nasu suke


      Yau takama monday, tin da sahala ta tashi da asuba bata koma ba take ta faman gyaran gda, sbda yau so take ta shiga mkranta da wuri, Dan ji take kamar ta shekara bata je ba sosai tai missn mkrantar tasu, karfe takwas suka gama break fast sannan suka nufi mkranta  


  Sanda suka shiga hall din gaba daya aka bisu da kallo sai a lkcn suka lura da kamar da sukai da dr sahal din zuwa aka dinga yi ana yimata ya jiki 


   "Assalamu alaykum" sahala da jidda suka dago kansu dan ganin wanda ke musu sallamar, ganin wadda ke tsaye akansu yasa suka amsa mata sallamar fuskarsu ba yabo ba fallasa " Dan Allah sahala kiyi hkri nasan nayi kuskure sosai amma ni bnsan ke kanwarsa bace shiyasa, da nasan kanwarsa ce bazan fara zargin ku ba" dariya sahala tayi "ba komai ya wuce daman kuma ni ai bn rikeki ba" murmushi rufaida tayi ngde sosai sannan tayi mata sallama ta tafi 


   Ranar kan mutane taita mamaki wasu ma bata sansu ba wanda suke zuwa yi mata ya jiki a haka lkcn tashi yayi suka tafi gda 


   Tin daga ranar sahal baya kunyar yi ma sahala komi kuma a gaban kowa a haka har suka fara shirin fara jarabawa ranar da zasuyi lectr karshe dashi bai hana kowa shigowa ba sai da ya gama sannan ya fara mgana


    "Ina bawa kowa da kowa hkr a iya zaman da mukai ina batawa wani, nima kuma duk wanda na batawa ya yafemun, bama ajin nan ba makarantar gaba daya zan ajiye sbda wasu dalilai" nan dai yayi musu nasihohi masu shiga rai yayi musu sallama ya fice



  Ranar da suka gama jarabawar karshe ta second semester din su washe gari kuma sahal ya bar kasar lkcn da zai tafi ba karamin jin ba dadi sukayi gaba daya ko wannensu ji yake baya san rabuwa da juna a haka har jirgin su ya tashi



   *Bayan shekara hudu* 


  Abubuwa da dama sun faru a shekarun ciki ko harda auren rufaida, su sahala na ta shirin kammala makaranta ga kuma auren juwairiyya da zaayi nan da karshen satin nan 


   Da daddare suna hira bayan sun gama dinner dady yake shaida musu dawowar sahal nan ba da dadewa ba sosai kowa yay farin ciki



    Yau ta kama alhamis yau ne kuma aka fara bikin juwairiyya, lunch zaa yi, tin safe suka zo gdan su juwairiyyya suke ta faman shiri, karfe 12 mai kwaliyya tazo suka fara kwaliyya karfe biyar dai dai suka isa *fatima event center* kasan cewar a can zaayi 


Tin da su jidda suka karaso kowa ya bisu da kallo sosai sukayi kyau kamar basu ba, jidda ce suka jero ita da abokin angon shahid sai kuma sahala da abokin ango kuma abokinta m.d tare suka jero suka shiga wajen, sosai suka burge mutane yadda sukayi kyan a haka aka gama shagalin bikin ranar sannan suka fito motar m.d suka shiga dan ya kaisu gda 



    Wata mota ce taxi ta tsaya, a bakin gate din gdan su, sanye yake cikin jeans baki, sai t- shirt fara, sosai kayan jikinsa suka zauna cikin jikinsa, gashin kansa ya kwanta luf a kansa, sai sheki gashin kansa yake, a hankali yake tafiya har ya isa cikin gdan su 


    "Assalamu alaykum" yayi sallama tare da shiga cikin falon, cikin farin ciki mumy ta mike tare da amsa mashi sallamarsa " wa nake gani yanxu da yamman nan, dariya sahal yayi " nine mumy zuwan bazata nayi muku" nan dai suka dan taba hira yana ta raba ido ta inda zai gano farin cikin sa amma bbu ita bbu alamunta, jikinta ba kwari yayi daki yayi wanka sannan yaci abinci, ganin har karfe bakwai bai gansu ba yace " mumy wai ina su *sahala* ne bn gan su ba tin dazu " eh suna gdan biki" biki kuma " eh mna bata fda maka bikin juwairiyya ba da aka fara yau" eh mumy bata fdan ba kila ta mnta" 


   Mumy ta kwatanta masa sannan ya fito dan yaje ya dakko su bazai iya jira har su dawo bai gansu ba 


    Ba karamin tashin hankali *sahal* ya shiga ba sanda ya hango sahala a gaban motan wani, tana mashi faraa ji yayi kamar ya mutu sbda bakin ciki 


Kwata kwata basu lura dashi ba har suka karaso bakin gate wata kara cikin su ya bayar sanda sukayi tozali da yayan nasu a bakin kofa sai faman huci yake kamar wanda yay gasar gudu


    Yaya sannu da zu......... Kallon da yayi musu ne yasa su tsuke bakin su, ta gefenshi sahala tai kokari wucewa sosai ransa ya baci a ganinsa inda ne ai bata isa ta wuce ba, wato yanxu ta raina shi kenan, cikin bacin rai ya ja hanunta yay bangaransa da ita, mukulli ya sawa kofar sannan yay wulli da ita, doguwar kujera kanta ya buga tai saurin dagowa idonta na zubda kwallah 


    " uban waye ya ajiyeku a mota yanxu, watakan ku yan iska koh shine sbda zabagen kin raina mutane har da zuwa ki gifta ta kusa dani ki wuce koh" ya fda yana nuna da yatsa bnza tayi mashi kamar bataji shi ba, cikin tsawa yay mata mgana "ba tambayarki nake ba uban waye ya saukeku a mota" turo karamin bakinta tayi M.D ne" yanayin da ta bashi amsar yasa kara bacin rai cikin bacin rai ya kaiwa bakinta duka  kuka sahala ta saka dan sosai taji zafin dukan da yayi mata har cikin ransa yake jin kukan nata amma ya dake "idan kin cika mara kunya ba a isa dake ba gobe kisa kafa  ki bar gdan  tashi ki ban waje" ya fda yqna bude kofar sai da ta gaji da zama dan kanta ta tashi  ta fita a kofa suka ci karo da sadiq a'a zance kika zo ne" ya fda ya rukota fusze hannun ta tayi tai gaba, dariya yayi ya shiga dakin a tsaye ya tadda sahal fuskar nan tashi a tamke kamar bai taba dariya dafa kafadarsa yayi "mutumin me kuma ya faru daga dawo wa kun fara fda kuda ba kwa rabo da fda kamar wasu kaji" hararsa sahal yayi " toh wayasani ko mu kajin ne" zan fa fasa baka ita tinda baka min biyayya" tinda kai ai baka neman tawa kanwar ai sai ka hana ni" ya fda yana zama akan kujerar "Allah bada hkr yau naga daga kai har jerryn taka da fda kukeji nan dai yay ta zolayarsa har kuma suka cigaba da hira


   Sahala na zuba falon ummi ta fda cinyarta tana rera kuka "ummi kinga yaya kawai ya hau duka na bbu abinda nayi mashi wai dan abokin ango ya kawo mu gda kuma wai gobe bbu inda zani" me ya kaiku hawa motar wani bnda rigima irin taku ni dai ba ruwana kinsan idan dady yaji ma dukanki zaiyi gwanda ki hkra ki daina kukan gobe ki lalabashi ya barki kije" ganin ummi taki goyan bayanta yasa ta tashi tana bubuga kafa kamar wata karamar yarinya tayi daki tana kuka



   Washe gari tin safe big bro ya sauke jidda a gdan su juwairiyya sahala kan kuka ne kawai batai ba dan bakin ciki, koh da sahal yazo break fast ko kallan sa ba taiba bare ya san gaisuwa yana zama ma a dining tai cikin daki 


   Ganin da gaske mumy da ummi basu da niyyar barinta ta tafi gdan bikin gashi kuma har laasar ta fara kawo kai danma yau dai dinner zaa yi a *salma event* sai 8 zaa tafi 


  Tana kwance a kan gado ta saka wancan ta warware a haka taji wayarya ta fara kara ganin sunan juwairiyya ya bayyana barobaro kan screen din wayar yasa ta daga da sauri tare da karawa a kunnenta 


    "Wai har yanxu baki taho ba sahala" juwairiyya ta tambaya kamar zatai kuma, itama sahala cikin muryar san tayi kukan ta fara mgana "wlh su mumy sunce ba ruwansu tin da yaya ya hanani zuwa" toh kije ki tambayeshi mana" gani nake juwairiyya bazai barni ba, " kije ki gwada nasan zai barki toh kawai tace mata ta kashe wayar tana nan zaune har akai kiran sallar laasar ta tashi tayi sallah sannan tai adduar Allah ya dorata akan yayan nata sannan ta nufi bngaransa 


   A hankali ta tura kofar dakin hango sa da tayi a kwance yana kallo yasa ranta ya bacci wato shi ko ajikinsa ya hanata fita shi kuma yana nan yana kallo, turo bakinta tayi ta shiga tare da sallama kallo daya yayi mata tare da amsa sallamar ya maida dubansa ga kallonsa sai da ta kusa minti biyar a zaune a kasa ta kasa cewa komai shi kuma yaki kallonta da kyar ta tattaro kalamai ta fara mgana " yaya wajen ka nazo" ba tare da ya kalleta ba yace " ina jinki " daman zuwa nai na Baka hkri dan Allah ka barni naje gdan bikin nan" toh ai yanxu kin makara cikin fara tace " wlh yaya bn makara ba ai dinner ce sai 8 zaa ta...... Kallon da yay mata ne yasa maganar ta ta tsaya cak " amma baki da hankali dinner zan barki kije na yamma ma saurayi ya kawo ki gda bare kuma na dare" ganin bashi da niyyar barinta yasa ta hau kuka kamar wadda akaiwa mutuwa 


    Ganin bazai iya jure kukan nata ba yace zan barki amma da shardi " eh na yarda yaya da sharadin naka " ni zan kaiki kuma na dawo dake" shiru tayi sai kuma tace "toh ai yaya da daga wajen dinnern gdan su zamu wuce mu kwana" koma ina zaku hankalina zaifi kwanciya na kaiku toh yaya amma zaka kaini gdan yanxu anjima in zaa tafi wajen kazo ka kaimu ba damuwa jeki shirya


  Murna sosai tayi ta fice kallonsa ya cigaba dayi yana kallo jefi jefi yana dariya 


Karfe takwas yaje ya kaita wajen dinner duk inda sukai ido na kansu fan klaz din su ne na b.u.k suka zo gaidashi mata da maza hira sosai suka sha dashi


   "Sir ko dai sahala ce matar da zaka aura wacce kace yar uwarka" dariya yayi sannan yace "eh mana ko ba mu dace bane yusuf (claz captn) kun dace sosai ma sir, anci ansha ba laifi biki yayi dadi sai 12:00 aka tashi ya kaita har gdan su juwairiyya, big bro kuma ya kai jiddah 


 Washe gari aka daura auren juwairiiyya sosai jamma suka halacci daurin auren da yamma kuma akayi yini aka kai amarya da karfe tara nan suka baro amarya da angonta suka hau motar yaya sahal ya dawo dasu gda sai kuma fatan Allah ya kaimu auren su sahala





*Eloquence writers association*



💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*



*136-140*



*wannan fejin sadaukar wane gare ku Hafsat Abubakar,  Amina Musa funtua(6ter) tare da ummu hayat kuna daya daga cikin masu bibiya da kuma masoyan littafin nan ina alfahari daku* ILYSM 😍😍😘😘



   Kwanci tashi  ba wuya wajen Allah su sahala ya rage saura sati daya su fara jarabawar su ta karshe suna ta hada project din su, a bangare guda kuma ana ta shirin auren su bayan kammala jarabawar su da sati biyu


  Juwairiyya na da yarinya daya mai suna khadija ana ce mata (emaan) rufaida kuma na da yara biyu mace da namiji ba laifi yanxu suna shiri sosai bakamar da ba


   Da sassafe tazo makaranta kasancewar yau zata zo dr sameer ya duba mata project din ta karfe tara ta shiga office dinsa yana zaune yana danna laptop dinsa da sallama ta shiga fuskarsa dauke da murmushi ya amsa mata sallamar malamin su ne tin sanda ya fara daukarsu yaji yana santa sanda ya gaya mata ta bashi hkr ta shaida mashi an bada ita, dole ya hkra amma har yanxu akwai santa a zuciyarsa adduar sa kullum Allah ya bashi hkrin rashin ta tare da zaba mashi mace ta gari wadda zaiyi alfahari da ita


    "Mrnnnnnn sir" ta fda lkcn da ta karaso office din "hw r yuh" ya fda cikin murmushi "am fyn, daman sir na kawo ka duba min last pg din na gama" sahala ta fda tana ajiye masa takaddun cikin nutsuwa ya fara duba mata takaddun biron sa ya daga sautsayi yasa ya shigar mata ido cikin sauri ya dago kwata kwata ya manta da yadda suke ya rike mata fuska "am sorry "  ya fda yana hura mata ido "ba komai ai bn ji wani z........ Ido hudun da sukai da sahal, yana tsaye bakin kofa idon sa har ya canza kala sbda bacin rai 


    Da sauri ta nufi inda yake amma kan ta karaso ya fice sanda ta bishi waje har ya shiga mota ya tada ya tafi jiki a sanyaye ta juya ta dawo office din 


    "Yayan ki ne dr sahal din" daga mashi kai tayi alamar eh " kuma shi zan aura" kiyi hkr dn mean 2 hurt u" kar ka damu zai hkra" 

Sai da ya gama duba mata tas sannan ta juya ta tafi da daddare taje ta sameshi a daki yana danna laptop a hankali ta iso inda yake "zan iya yi bayani" ta fda kamar zatayi kuka dago kqnsa yayi ya maida kan laptop "plssssssss" ta kara fda sanda taga bashi da niyyar kulata 


    A hankali ya taso ya karaso gaban ta "trust me durln u cn nt" ta gefenta ya wuce ya tafi


  Abu kamar wasa sahal sai da ya kwashe sati guda ko kallon inda sahala take bayayi  tin abun baya damunta har ya fara damunta yau ta yanke zuwa ta fda mashi ko ya yarda koma kar ya yarda 


   Yana zaune a daki yana kallo amma kwata kwata hankalinsa ba akan kallon yake ba Dan kwata kwata baya fahimta ta turo kofar tare da shigowa, tana shigowa ya mike tsaye ta tsaya cak bata karasa inda yake ba a hankali ta fara rera kuka tana matsawa inda yake har lkcn yana tsaye kamar gunki da gudu ta karasa inda yake tare da rungumeshi 


    "Yaya kayi hkr wlh baka fahimce ni ba ranar, bazan iya daukar shirun ka da shariyarka gareni sosai yake cutar dani plsss ka tsaya na maka bayani" ta karashe maganar cikin kuka mai tsuma zuciya a hankali ya dora hannayensa a bayanta tare da rungumeta sai ta  gama kukanta mai isarta sannan ya janyota suka zauna  me yasa kike san ki bata min habibty kin san duk duniyar nan bbu wanda nafiso kamarki kuma ina kishinki duk duniya bbu namijin da nake so ya rabeki in ba big bro ba, shi kadai ne na yarda ya zauna dake dan Allah ki daina kula kowa kinji dear" insha Allah yaya bazan karaba kuma shima ba da san ransa ya taba ni ba" nan ta kwashe komai ta fda mashi, nan dai suka canza zuwa soyayyar su 



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah komi yay farko yana da karshe, yaune su sahala suke zana jarabawar su ta karshe a b.u.k sosai sukayi kwaliyya ranar dai kan sun karyar dokar dady dan gyale suka saka suka tafi suna fitowa daga exam aka fara hotuna na bnkwana suna sahal na ganin lkcn fitowar su daga exam yayi ya taho suna cikin yin hotuna da yan claz din su sahal ya zo wajen, nan aka dinga zuwa ana hotuna dashi, da kyar ya samu ya ruko hanun sahala da jidda sukai office a can ma hotunan sukai gda 



Tin safe su sahal da sadiq suka daga kasar China dan acan zasu hado lefen su, kwanan su hudu suka dawo gda, nan suka fara rabon aibi har gdan rufaida suka je suka kaimata nan ma sai da ta kara neman afuwar sahala tace mata bakomai ya wuce, juwairiyya da suka kaimata yini sukai a gdan sai dare sahal yazo ya dauke su 



Kwanci tashi ba wuya wajen Allah yau saura kwana uku a fara biki, zo kuga yadda amare suka yi ga wani haske da sheki da suke, ga kuma kamshi na musamman da sukeyi musamman mumy tasa aka dakko mata me gyarn jiki daga mai duguri ake gyara mata yaran nata 



    Ana gobe kamu mai lalle tazo ta musu ja da baki sosai lalan ya zauna a fatar jikin su, kawayen su su surayya da sukai secondry skul suma ranar suka zo su ma tin tini suka kammala karatun su har sun fara aiki kowacce kuma an sa mata ranar aurenta, tsayawa fadar yadda amare sukayi kyau bata lkci ne 



Yau ta kama alhamis yaune kuma zaa yi kamun bikin su a *meena event* tin karfe bakwai suka tafi gyaran kai, lkcn da aka fara yima jidda gyaran kai wata mace ta shigo rike da hannu babyn ta a hanunta kujerar da ke kallon sahala ta zauna tinda ta zauna sahala take ma matar kallon sani amma ta mnta a inda ta santa can dai tace 


    "Sannu baiwar Allah dan Allah sunan ki zainab" matar da ta kira da zainab tai murmushi eh sunana zainab "ihu sahala ta saki tare da rungumeta daman zee zan kara ganinki a rayuwata basan baki ganeni ba sahala c..... Ai bata karasa ba zee ta kankameta nan suka fara hirar yaushe gamo ta basu lbrin aurenta da kuma auren daya kawar tasu ( da fatan masu karatu kun gane zee, kawar sahala da sukayi jss da ita) nan ta basu aibin bikinta ranar basu bar shagon saloon ba sai wajen 1 shima mumy ce ta dinga kir ansu a waya


   Karfe hudu motoci suka fara dibar mutane aka nufi wajen daza ayi kamu, sosai amare sukayi kyau ciki golden din material sukayi dinki riga da zani buba tsayawar fadar yanda sukai kyau bata lkci ne suma angwayen suka hade cikin golden din shadda sosai sukayi kyau abin ka da farare nan suka shiga mota sukayi meena event, suna shigowa hall din aka fara tafa musu sbda yadda sukayi masifar dacewa da juna a haka aka gama kamu ba laifi malaman su na b.u.k sun zo haka ma daliban kowa da abinda yake fda na sambarka a haka taro ya watse 


   Washe gari akayi dinner anci ansha abu dai sai san barka duk wanda yaje sai yayi shaawar amare sbda yanda sukai kyau, kuma kayi komi cikin tsari 


   Yau ta kama asabar yaune dubbban jamma Wanda baza su kirgu ba suka shaida daurin auren  *sadiq tare da amaryarasa jidda* akan sadaki dubu hamsin sai kuma *sahal da sahala* akan sadaki dubu hqmsin jin maroka suna ta yima angwaye kirari ya tabbatar musu da cewar an daura aure, jin sheshekar kuka a bayanta yasata saurin juyowa, haba *sahala* miye kuma abin kuka, so kike ki daga min hankali tin yqnxu" ummi ni bnsan bari gdan" toh daina kukan muje cikin gdan 



   A bangadan angwaye kuwa sai washe hakora suke duk wanda ka ganshi kasan yana cikin farin cikin da bazai musaltu ba suna sanye cikin fararan shaddoji suna sha aiki rantsatse mai kyau da tsada kalar aikin kalar takalmin su da hula bayan an daura aure suka shirya walima ta angwaye basu dawo gda ba sai azahar 


    Amare kan angaji da yin kyau dan ma sahala na bata kwaliyyarta tayi kukan da takeyi akai akai bayan angwayen sun dawo suka sake kaya akai ta hotuna sai faman nan nan suke da amaren su, ba laifi rufaida tayi kara dan tin da aka fara bikin kullum sai tazo mutanan katsina ma su aunty nafi ba a barsu a baya ba dan duk sun halacci bikin


   Da daddare bayan anyi sallar isha'i dady Abba, ummi da mumy suka hada su a falo sukayi musu nasiha sosai, kuka sosai take sai a lkcn mutuwar auntyn ta dawo mata sabuwa, dan kullum burinta ta ga auren diyarta, sai gashi anzo auren bbu ita kuka sosai take haka ma jiddah su kansu angwayen sai da suka karaya su ummi ma kukan suke sosai da kyar Abba da dady suka banbare su daga jikinsu suka sa su a mota suka nufi hanyar Amadu bello sbda a can suka tamfasa katon gdan su kowanne da bngaransa


   Tubarkallah abinda kowa ke fda sanda suka ga saruwar gdan a haka kowa ya watse aka bar amare, karfe goma akaima angwaye rakiya suma basu fi minti goma ba kowa ya tafi ya barsu




*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


    *141-145* 




    A hankali ya karaso inda take tare da cire mata gyalen kanta har lkcn kuka take sosai kamar wadda aka aikowa da mutuwa janyota yayi jikin sa "haba habibty idan kina wannan kukan daga min hankali kike plssss ki daina kukan nan in ba so kike nima na fara ba" da kyar sahal ya lalashi sahala tayi shiru tare sukaje bndaki sukai alwala sannan suka fito sukayi sallah raka biyu addua sosai yayi musu Allah ya dauwamar da farin ciki a tsakanin su har abada bayan sun idar ya je kitchen ya dakko plate ya zuba musu kazar amarci da kyar ya lalabata taci sannan suka wanke baki suka kwanta nesa dashi ta kwanta, murmushi kawai yayi ya kashe kwan ya ja musu bargo suka kwanta


   A bangaren sauran amaren angwaye na tafiya sukayi alwala sannan sukai sallah raka biyu bayan sun gama cin abinda ya shigo suka yi brush sannan suka kwanta janyota yayi jikinsa wasa ya fara yi da ita yana kissn dinta a takaice dai sai da big bro ya maida amaryar sa cikakiyar mace ranar, kuka sosai ta dinga yi masa shi kuma sai faman samata albarka yake, da kansa ya gyara dakin bayan ya taimaka mata tayi wanka sannan ya canza musu bed sheet ya kwantar da ita sannan shima ya kwanta tare da jawota jikinsa suka koma bacci



   Kiraye kirayen sallar asuba din da aka fara ne yasa sahal saurin mikewa, bayan ya fito daga toilet ya tashi sahala sannan yayi masallaci, har aka idar da sallah sahal yana jiran ta inda sadiq zai fito amma bbu shi bbu dalilinsa ganin har gari ya fara wayewa yasa shi komawa gda 


   A kwance ya taddata kan sallaya ga dukkan alamu bayan ta idar da sallah bacci ya dauketa, daukanta yayi cak kamar karamar yarinya ya hau gado da ita bayan ya kwanta ya janyota jikinsa yana shafa gashin kanta da ya kwanta luf a bayanta a haka har bacci barawo ya sace shi


    Karfe bakwai dai dai big bro da amaryarsa suka tashi shi ya fara Shiga yay alwala sannan jiddah ta shiga itama tayi alwala sannan suka zo suka koma bacci 


   10:00 mumy ta aiko musu da driver ya kawo musu abinci bangaran sadiq ya kwankwasa kamar a mafarki yaji ana buga gda ya mike yaje ya bude 


    "Yallabai barka da asuba ga abincin mumy tasa akawo muku"  yauwa sannu da zuwa kaje bngaran sahal ne?" Ya tambaya yana karbar kular abinci "a'a nan kawai mumy tace na kawo" "owk mun gode a gaida su mumy" toh yallabai yana shiga ya tadda jiddah har ta shiga wanka 

   Karfe 11:30 sadiq ya kira sahal a waya sai da wayar ta kusa katsewa sannan ya daga "dallah malam kana ji ana kiranka amma sai ka ja aji zaka daga" Allah baka hkri daga wanka na fito ne" toh kuzo mu karya mumy ta aiko mana da abinci " toh gamu nan zuwa"


    Sai da suka gama shiryawa tsaf sannan sukayi bangaran sadiq suna tura kofar ta bude jiddah na zaune a kasan crpt ta mike kafafuwanta tana sanye da atamfa dinkin riga da skrt kanta ba dankwali, kusa da ita sahal ya zauna "yaya ina kwana" lpya lau ya fda yana janyo sahala jikinsa 


Sadiq ne ya fito rike da plate da kofuna ya jere kallon zargi sahal ya fara yiwa Jidda  "me zan gani haka dan iyayi kina zaune kin mike kafa kin bar mijin ki yana ta faman aiki anya kwa kina neman aljannar ki" kaga bnsan gulma da munafurci ina ruwanka bata da lpya ne" ya fda yana zama kusa da ita "owk na gane zance ashe shiyasa fa na makara koh sallar asuba bn samu ba" gaba daya sukai dariya dan sun gane me yake nufi a haka suka cigaba da cin abinci suna yi suna zolayar juna 



  Haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin kwanciyar hankali sosai suke soyayya tsakaninsu kana ganin su kasan suna cikin kwanciyar hankali  sai da sahala tayi sati sannan sahal ya rabata da budurcinta washe gari kuwa yini yayi yana nan nan da ita sai faman shagwaba take mashi 



*Bayan sati biyu*


   *sahal* ne zaune a falo kan carpt yana chrtn sahala ta shigo falon kusa dashi ta zauna tare da dora kanta akan cinyar sa "swt hrt dan Allah ka kaini gda yau naga ummina" "gaskiya dady yace kar mu zo bayan sati biyu mu bari sai anyi wata kinga kuma zai mana fda in mukaje kiyi hkri ayi wata dayan" turo karamin bakinta tayi " ba wani fdan da zaa yi mana sai dai in bazaka kaini ba" ni na isa na hana gimbiyata zuwa inda take so kawai dai bnsan na bata ran dady ne "toh ba komai Allah ya kaimu lkcn" Amin habibty shiya nake kara sanki kullum 


   Kwanci tashi ba wuya wajen Allah su sahala anyi wata guda  da aure tin da suka tashi sallar asuba basu koma bacci ba sai shiri suke yau zasu gda karfe bakwai ta gama shirinta tsaf ta fito falo lkcn yana zaune a falo kasancewar yau week end ne bashi da aiki "yaya yana ga baka shirya ba ni har na fito" dariya ce ta kusa kufce mashi amma ya dake "lalaima yanxu da sassafen zamu tafi ko tashi daga bacci ma ai basuyi ba" ni dai kawai ka tashi mu tafi kar su yaya suzo suna jiran mu" ni kan babu inda zani yanxu da sassafe ko wank....... Maganarsa ce ta tsaya shak sanda yaga jiddah ta shigo ita da sadiq cikin shirin fita " mi zan gani big bro har kun shirya kuma" sahal ya fda cike da mamaki, " toh ya zanyi tinda gimbiya tana san tafiya yanzu dole na bi umarninta" ai sai kui ta tafiya nikan sai na karya kuma nayi wanka ma taho da tawa gimbiyar" "chab wlh bazan iya jiranka ba ma hadu a gdan" ta fda tana turo bakin ta "aiko sai dai ki tafi bani ki bisu dan ni bnshirya tafiya yanxu ba" eh na yarda zan bisu" Allah ya kiyaye hanya nikan sai anjima" ya fda yana shigewa daki 


    A hanya jiddah ta dinga zolayarta, mijinta baya santa tinda bazai so abinda take so ba tin sahala bata jin haushi har ta fara jin haushi 

   "Wlh yaya ka jama matarka kunne wlh zan mata rashin mutunci" chab aiko da mun sauke ki a hanya karya tayi ne da yana sanki ya kawo ki mna kinga kuma be kawo ki b...... Kukan da sahala ta sa musu ne yasa suka hkra suka dena tsokanarta tin suna yimata dariya akan kukanta har suka koma bata hkri amma kamar zugata suke dadayi suna isowa gdan ta bude ta shiga gdan da gudu tana kuka a falo ta zauna tana rera kuka 


     Jin kukan gudan jinita yasata saurin fitowa "sahala me ya faru me aka miki me sahal din yayi miki?ummi ta jero mata tambayoyin cike da tashin hankali sanda ta iso gurunta 


   "Ummi yayana ne baya sona kuma su jidda na ta tsokanata" wa yace miki baya sanki ko shi sahal din ne ya fda da bakinsa" girgiza kai sahala tayi alamar a'a "toh wa yace baya sanki" dai dai lkcn da su jidda suka shigo dakin "su yaya sadiq ne suka fda" ta fda tana nuna su da yatsa, dariya ummi kawai tayi sanda suka bata lbri da kyar suka samu ta hkra tai shiru shima sai da dady da Abba suka zo mumy ta basu lbri ta hkra bayan sun rarasheta


   Sahal bai zo gdan ba sai kusan sha biyu sosai ta kara kuluwa suna zaune a falo lkcn su Abba sun fita dubiyar abokin su ya turo kofar tare dayin sallama gaba daya suka amsa mashi cikin girmamawa ya gaidasu sannan yay ma kansa masauki akan kujerar da sahala take yana zama ta matsa nesa dashi nan dai sukai ta hira yana lura da sahala da taci magani sai faman huci take tana kada kafa 


   Wai mumy me ya sami sahala ne bata da lpya ne naga tana ta huci kamar wadda tayi gamo" habawa kamaar jira sukeyi suka fara dariya cikin kuka ta kaima sahal duka sannan tayi daki da gudu "lalai ka jama kanka fitina baka san kai kayi laifin ba ake ta jiran zuwanka tin dazu" zaro ido yayi ni kuma me nayi mata" nan suka bashi lbri sai da ya gama dariyarsa kuma ya mike har zai wuce ya dawo ya rankwashi jiddah " munafuka ai duk ke kika jawo mun" 


   Tana zaune kan gado ta hada kai da gwiwa tana ta rera kuka a hankali ya matsa inda take tare da jawota jikin sa duk yanda taso ta kwashe ta kasa ta bude baki zatai mgana ya hada bakinsa da nata ya fara tsotsa kamar ya samu sweet sai da ya tabbatar ya kashe mata baki sannan ya fara mgana "kiyi hkr nasan bn kyauta amin afuwa" da kyar ya samu ta hkra



*Eloquence writers association*




💞💞

💞💞


*SAHAL DA SAHALA*


*® ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION*


Written by

*shamsiyyah*


Edited by

*Ayusha Iliasu*

 

Dedicated 2 

*Ayusha Iliasu*

     Nd

*Haima ( mmn abul)*


   



*last page* 


  Baki na a ko da yaushe bazai gaji da anbatonku ba ina alfahari da ku fatana kullum Allah ya kara dauka kaku Allah ya kareku daga sharrin duk wani mai sharri *Ayusha iliasu musu* nd *Haima (mmn abul)* 

 Na sadaukar da littafina gareku *Ayusha nd Haima*


Ina alfahari daku a ko da yaushe kanena Allah ya kare ku Allah ya kara hasken makaranta 

*Nafisa*

*zainab*

*Fatima*

*Firdausi*

Da kuma autar mu 

*sadiya*


Ban manta da ku ba 

*Aysha mazoji, khadija candy, khairat up, maman shaheed, Abeedah, Hawwah saleh, suhana, classic feedoh*


Ina alfahari da ku yan eloquence writers association fatana Allah ya kara hada kanmu *Basira sabo, autan eloquence, yar india pure green, A y indabo, yar aljannah, umee smart, Aeeshat abba, sumayya gereii, fatima aderm, Queen hafsy, jannah jay, da kuma Rama lurv* ana tare


Bn manta ku ba kawayen arziki kuna raina a ko da yaushe kuna cikin masoyan littafina


*Hafsat Abubakar, Amina musa funtua, ummu hayat, saada m saad, surayya Auwal,Aysha mai dala and  zainab kd*


Ina Alfahari da duk yan grp din 


*Haisham novels, kasaitattun mata, eloquence writers fans, first klaz, musan kanmu marubuta, musan juna ohw, maman shaheed fans, haima novels, feedoh online novels, khadija candy novels* 



*146-150*


  Basu bar gdan ba sai bayan sallar isha'i, washe gari kuma suka wuni gdan juwairiyya


Bayan wata biyu


  Tin safe sahala ta tashi da matsannancin zazabi lkcn sahal na asibi bbu kowa a gdan daga jiddah sai ita, daukarta jiddah tayi suka nufi asibiti da kanta tayi drvn, suna zuwa ta kamata suka je har office dinsa, cikin tashin hakli ya ce " me ya sameta" ya fda yana karasawa inda suke, "tin safe ta tashi da zazabi shine nace bari na kawota" tambayoyi sahal ya fara yi mata tana bashi amsa, da kansa ya kaita lab ya sa aka mata gwaje gwaje

   cikin murna ya rungumeta "swt hrt mun kusa zama mum nd dad" cikin rashin fahimta ta kalleshi "kamar ya bn gane ba" kina da ciki wat.... yanayin da yaga ta shiga ne yasa shi kin karasa zancen da zaiyi "sahala me ya faru naga kin shiga damuwa dan nace ciki"  ya tambayeta cike da tsoro yana kuma fatan Allah yasa sahala bata cikin matan da basa san haihuwa, "gaskiya yaya azubar min da cikin nan tin ina yanxu xanyi ciki" ta fda kamar zata yi kuka "haba swt hrt ki godewa Allah da ya baki wani ma nema yake amma Allah bai bashi ba me yasa ke zaki yi butulci da kyautar da Allah ya baki" gaskiya ni dai bn so haka kawai daga aure sai haihuwa, mtswwwwww ta karashe zance da tsaki sosai ran sahal ya baci dan a duniya idan da abinda ya tsana bai wuce tsaki ba "sahala ni kike ma tsaki sbda kyautar da Allah ya bamu" toh ka zubar da cikin mana ko ana dol...... marin da ya kaimata a fuska ne yasta yin shiru, sosai taji zafin marin tini idonta ya fara xubda kwallah, da gudu ta bude kofar ta fice, tana fita ya bi bayanta gnin tayi hanyar fita shi kuma yayi office dinsa "kije ku tafi ta fita, ki kula kiyi tuki a hankli' toh yaya" jiddah ta fda tana ficewa, a bakin mota ta tadda sahala tana hawaye, mota ta bude mata ta shiga, tin da suka shiga mota jidda ke tambayarta abinda aka mata amma taki fda har suka je gda, waya ta dauka ta kira shi, bugu uku yadauka "ya akayi" ya fda a takaice, "yaya daman sahala ce ke ta faman kuka tin a asibiti gashi har mundawo gda amma taki dainawa" ta fda cike da damuwa, "kyaleta kije kiyi aikin gaban ki iskanci take ji dashi wai ciki ne da ita kuma bata so sai anzubar kar ki kulata ki kyaleta kije kiyi aikingaban ki" toh kawai tace mashi ta fice,tana mamakin halin kanwar tata 


   Abu kamar wasa yau kwana uku kenan har lkcn sahal da sahala basa kula junan su bbu wanda ya sakko daga fushin da yake, ba irin waazin da big bro bai yima sahala ba amma tai burus dashi kamar ma kara zugata yake yi dole ya hkra ya kyale su 


    Da safe sahal na shirin fita office sahala ta shigo dakin ko sallama bbu, fuskarta a hade, ko kallonta sahal bai yi ba ya cigaba da harkokin sa, yana gama shirinta yazo ta gabanta zai wuce "malam wajenka nazo fa kake kokarin fita" tsayawa yayi ba tare da ya kalleta ba "idan baza ka zubar da cikin nawa ba ni zan je a zubar min ai ba kai kadai bane likita a duniya kuma ai ko ni zan iya z.... bai jira ta karasa ba ya ja hanunta sukayi waje a mota yasata bai tsaya ko ina ba sai da yaje kofar gdn su zagayawa yayi ya fito da ita "ki je ki fdawa su ummi su kaiki a zubar tinda naga baki da hankali, kuma kar ki kuskura ki dawo min gda in bn nemeki ba ya fda yana shiga motarsa bai jira cewarta ba ya bar wajen

cikin gdan ta shiga ta tadda mumy da ummi zaune ta gaidasu suka amsa cike da faraa "ke kadai kika zo" eh ni kadai ce yaya ne ya sauke ni yace zai dawo da daddare" nan dai sukai ta hira sai wajen 12:00 taima su ummi sallama akan yaya yace driver ya kaita asibiti ya bata magani sannan ta dawo" ba tare da sun kawo komi a ransu ba suka kyaleta


   Wani karamin asibiti ta shiga, ta hau layin inda ake ganin likita bayan ta bude file a asibitin, wata mata tagani an fito da ita a mace nan taji likitoci suna mgana akan zaa zubar mata da ciki ne ta rasu, sosai ta tsorata bata kara shiga tashin hankali ba sai da taji wata mata suna hira tana cewa ai ita ma da haka tayi zubar da ciki, sai yanxu da take neman haihuwar kuma Allah baibata ba haka kuma tai ta bata lbrin hatsarin da kawayenta suka shiga wanda suke zubda ciki wasu sun mutu wasu sun shiga hali mai wuya sosai jikin sahala yay sanyi ta koma gdan su, ko da taje ba kowa a falo sai ta wuce daki 


   wasa wasa sai da sahala tayi sati amma bbu sahal bbu lbrin sa kullum da karyar da take gaya musu akan yayi tafiya ne, amma ita kanta tayi nadamar abinda ta aikata sosai, da safe sahal na shirin tafiya office yaji wayarsa tayi kara ganin wanda ke kiransa a waya yasa yay saurin dauka tare da karawa a kunensa, "toh kawai naji yace ya kashe wayar" da sauri ya dau key din motarsa da su sadiq ya hadu zai kai jidda gda suka tafi gaba daya sanda sukaje duk suna falo a zaune hakan yasa suka gaidasu suma suka zauna 

"sahal wane iskancin ne yasa ka turo sahala gda kuma kaki zuwa har yau" Abba ya fda ransa a bace, "Abba bata fda muku ba" da ta fda mana zamu tambayeka ne"ummi ta fda cikin bacin rai, "ciki ne da ita kuma wai bata so sai an zubar shine nace tazo gda ta fda" sosai hankalin iyayensu ya tashi da jin batun sahal cikin bacin rai mumy ta fara dukan sahala, shi kansa sahal sai da ya tausaya mata da kyar aka samu ummi ta kwaci sahala daga hanun mumy fda sosai dady yayi mata daga karshe yayi mata nasiha, sannan ya umarce shi akan da daddare yazo ya dauketa


   sai da akai sallar isha'i sannan sahal yazo lkcn ta shirya tana jiransa sai da ummi ta kara mata nasiha sannan suka tafi tin da suka shiga mota ba wanda ya kula wani suna hada ido kuma sai ya harerreta, suna zuwa gda kowa yay dakinsa


  yau kwananta uku da dawowa amma har lkcn sahal baya kulata da daddare tana zaune tana jiran shigowarsa dan yanxu baya dawowa sai anyi isha'i da sallama ya shigo falon ta mike tare da karbar jakarsa har daki ta bishi "yaya dan Allah kayi hkri ka yafe mun bazan karaba, ko gaisuwata fa baka amsawa ta fda tana kallonsa lkcn yana kokarin shire kayan jikin sa a hankali ya karaso inda take "ai nayi fishi sosai har na fara tinanin auro wadda zatana haihuwa tinda ke baki san haihuwa" duka ta kai mashi nace kayi hkri bazan karaba" ranar dai sai da suka shirya 


bayan wata shida

  jidda ce kawai ta fara aiki a asibiti bnda sahala ance tai hkrin ta haihu tukunnah, dole ta hkra badan ta so ba, kwanci tashi ba wuya wajen Allah cikin sahala ya shiga wata tara haihuwa yau ko gobe


  yau ta kama lahadi duk suna gda kasancewar ba aiki bayan sungama break fast sahala ta fara nakuda kamar wasa a gigice sahal yayi daki kan ya dakko key din motarsa kan babyn har ya fara fitowa, a hankali ya taimaka mata har ta haiho danta namiji, sai da ya gyara wajen ya gyara jaririn sannan ya kira su jidda, sosai sukai murna sannan aka fdawa su mumy da abokanan arziki kan kace me gda ya cika da mutane 


   Ranar suna yaro yaci sunan dady ana ce mashi Aslam, sosai taro yay albarka gda aka kaita washe garin suna,sai da tai arba'in ta dawo gda kullum aslam na wajen jidda, sai da tai wata biyu da haihuwa ta fara aiki a asibiti, sai da Aslam yay shekara uku sanan aka mashi kani yaci sunan Abba ana ce mashi shahid, har lkcn jiddah bata haihu ba daman tinda ta yaye Aslam ta barwa jiddah, sai da shahid yay shekara uku lkcn Aslam na da shekara shida sannan jiddah ta haifi mace, sosai suka yi murna ranar suna yarinyar aka sa mata sunan mumy ana ce mata eslaam"watan ta 12 jiddah ta kara samun ciki hakan yasa eslaam ta dawo wajen sahala, cikinta na shiga wata tara ta kara haohuwar mace taci sunan ummi ana ce mata shahida,


haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin family cikin so da kaunar junan su


Alhamdulilah


abinda nai kuskure Allah ka gafar ta mana gaba daya, na takaita lbrn sbda wasu dalilai


*Eloquence writers association*



Post a Comment

0 Comments