NANNY mai reno hausa novels cmplt

 *NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LUVSM💕🔐*_



*Bismillahir Rahmanir Rahim,in The Name of Allah,The Most Beneficent,the most mercifull praise be to Allah Lord of The Words,...Assalamu Alaikum Our Follow Fans,We are Starting our New Book,We Ask Allah Subhanahu wata'ala to guide Us Throught And Make it Succussful Till The End Ameen ya Allah*👏


``` Wannan lbrin Is a Fiction Story Kirkirarre ne Daga Fasaharmu,Juyamana lbri ko Sarrafashi ta Wata Siga,Bada Izininmu ba Toh Hukuma ce Zata Rabamu Insha Allahu```


       *BABI NA D'AYA*


*KADUNA*


_Area:Anguwan Rimi Gra_


   Misalin karfe 9:30pm Daidai na Daran Ranar Asabar,ya baro Office dinsa,Direbansa Garzali ne ke Jansa Cikin Bakar Motarsa Bugatti.


Hon ya Zuba akofar Tamkamemen Get din gidan nashi Mai kama da Aljannar Duniya,Megadinsa Habu ya Rugo da Gudu yazo ya Wangalemusu get Domin yasan Yallabai ne ya Dawo Adaidai Wannan Lokacin.


Lokacin da Motar Ta Sulala parking Space kafin Tagama Daidaita Zama Sai ga Wasu kyakyawan Yara Guda Biyu mace Da Namiji Wadanda Ashekaru bazasu Haura Shekara goma ba Tsawonsu Daya Kuma kamaninsu Daya,sai dai mace Tafi Jiki da Kuma Tsukakkiyar Fuska yayinda Namiji yake Siriri Ammh Fuskarsa nada Fadi,Farare Tas kamar Ka Taba Jini ya Fito akallon Farko zaka musu ka Fahimci yaran yan gayu ne na Karshe Kodaga ganin yanayin Kayan Kantin Dake Jikinsu Riga da Wando da Kuma yanayin Fatarasu na Jin Dadi ne.


Da gudu suka isa jikin Motar Suka Bude Bangaren Baya Suna Fadin"Wlcm Daddy..."Atare na Kallesu na sake sai alokacin Naga Dimple dinsu ya Lotsa Agefen Kumatunsu Lokaci Daya Yaran masu kama da Juna Sosai Inaga ma yan"biyu ne,Bangama Mamaki ba Sai da Naga Wani Cute and Handsome Ya Fito Daga cikin Motar yana Sanye da American Suit masu Ruwan Toka ya Matse Wuyansa Da Tie,Fuskarsa Tana bayyana Tsantsan Farincikin Dayake Ciki Naganin Kyakyawan Yaransa dayake Alfahari dasu 


Rumgumesu yayi yana Shafa kansu yana Fadin"Thank u my Childreen..."Yake Fada Shima Duka Kumatunsa na Lotsawa,aShe anan yaran Suka Dibe Tsantsan kyau da Kuma Kyan Jiki,Dogone kakkarfan Namiji ne mai Tsawo da jiki da Fadin Kirji,Dan Kimanin Shekara 43 aduniya ammh kuma Bazaka iya Kiramasa Wadanan Shekarun ba Saboda Yadda ya Mori Jiki da kyan Fuska Ba Fari bane Tas,Ammh Kuma Bazamu Sanyashi alayin Bakake ba,Fatarsa Tafi Kama da yan Maroco,Saboda Murjewa da jin Dadi,doguwar Fuska gareshi mai Dauke da dogon Hancinsa da Kuma Zagayayyen Bakinsa wanda Wani Bakin Saje yama Wajen Kwanya gwanin Bam Sha"awa yana da Daradaran ido masu Dauke da Wasu Sirrika,ya mallaki Zara zara Gashin Ido Tamkar yana kari,sai Giras sa Dake Cike da gashi Kamar Wani Mace.


    

*ALHAJI TAHIR MANSUR DA'N BATTA* Kenan babban Manaja ne Dake kula da kamfanin *IBRAHIM  KWATANO AND SONS LIMITED* Kuma Babban D"a Awajen Hakimin Dambatta Wato Alhaji Mansur Danbatta,Kuma miji ga *FARIDA IBRAHIM KWATANO* Kuma Uba ga *BASSAM,BASMA,NAILA...* Cikakken Jarumin Namiji mai Hakuri Hade Da Zati Da Haiba Miskilin Namiji Wanda bai maida Rayuwar Duniya da Abunda Ke Cikinta ado ba,wanda ake Alfahari dashi bayan iyayenshi Harta da Garinsa Danbatta Suna Alfahari da samu D"a Irin Tahir daya Fito Daga Ahalinsu


    Zumbura baki Basma Tayi Tana Fadin"Daddy ina Mami...? hararanta Bassam yayi kafin yace"Eh ina Mami..? Kin manta dazu Munkirata da wayar *ANTY MUFEEDA* Tace mana ba yau Zata Dawo ba.."Tura baki Basma Tayi kamar Zatayi Kuka Tahir Dake Tsaye yana kallonsu Wani Takaichi yacikamai Ciki Jin Farida yau ma bazata Dawo ba,Hannun Basma yakama yana Fadin"Bassam Karbomin briefcase Dina Hannun garzali muje ciki.."da Hanzari Bassam yakarba Jakar Hannun Garzali yabi bayan Daddy Wanda ke Rike da Hannun Basma yana lallashinta don Ita Haka Allah yayi ta akwai Kulafacin Uwa ammh ba domin Haka ba yadda Farida ke Banzatar da Mijinta da ya"yanta yaci Ace Basma Tadaina damuwa da Rashinta don ba yau Ake ba.


    Suna Shiga Cikin Kayatattacen Falon Kukan Naila yafara Musu Maraba Inda Take goye bayan Mufeeda wacce Ke Ta Faman Zagaye Falon Da Ita tana Faman Jijjigata ammh Taki yin Shuru,Cike da Tsausayi da Takaichi Tahir ke Bin Mufeeda da kallo Wacce Tajige da Zufa Duk da Sanyin Ac dake Falon Sakamon Naila Irin yaran nan Masu Kiba kamar Kajin Agric,ayayinda Ita Kuma Mufeeda Take Doguwa Siriirya kamar Ta karye saboda Rashin Nama,yarinyar sai Rinjayarta Take kamar zasu Fadi,daga gani Tafi karfinta, gata yarinya karama Domin Ashekaru bazata Haura Shekara 16 ba,Doguwar Fuska gareta mai Hade da Hancinta Shiba gajere ba,Kuma ba Dogo ba,Mufeeda baza ka Sakata Cikin Jerin kyakyawan Mata ba sai dai Tsaka tsaki.


   Tana ganin Sun Shigo Tayi Azaman Dukawa Tana Fadin"Sannu da Zuwa Daddy..."Cikin Siririyar Muryanta Mai Cike da Yarinta,Amsawa yayi yana karisawa gareta bayan ya saki Hannun basma yana Fadin"Mufee,Meya samu Naila ne Take Ta Kuka Haka..? Yafada yana Mika mata Hannu Alamar Ta Kwantomai Naila din.


Batayi gaddama ba Ta Kwantota tana Mikamai ita Wacce Fuskarta Ta Hade da Majina da Hawaye,Ya karbeta yana Kallon Mufeeda dake Fadin"Wlh bansani ba Daddy,Tundazu ta Fara Kuka,na zata yunwa ne,sai na Hadamata Madara na bata taki sha,sai kuka take ganin Haka sai iya ta amasheta nan ma Taki yin Shuru Sai Kuka take tana Kiran Sunan Mamanita..."Tafada itama kamar Tayi kukan.


Mirmishi Tahir yayi yana Rimgume Naila wacce ke ajiyar Zuciya ta Kwanta Luf akan Kafadarshi,Kallonsu Bassam yayi kafin yace"Kunci Abinci..? Suka gyada kai alamun Eh,bai kara mgana ba ya Wuce ya Fara Haura Steps yana Dauke Da Naila kafin ya tsaya ya waigo yana Fadin"Oya kuje ku kwanta sai da safe.."Yafada yana Tamke Fuska Sum Sum Bassam da Basma kowanne ya Nufi Dakinsa yana Bata Fuska yayinda Da Mufeeda Tayi Tsaye tana kallonshi Ido ya sakarmata Fuska ba Walwala yace"Tsayuwar me kikeyi ke kuma..? Jikin Mufeeda na Rawa Tace"Ba...bakomai Dama dama..."Tafada tana Sosa kai Ware idonshi yayi kafin yace"menene..? Akwai Matsala ne..?


Kanta na kasa tace"Dama zance  ne Daddy baka ci Abinci ba gashi chan iya taga jera maka akan Dinning..."Mirmishi ya saki kafin yace"Karki Damu bana jin yunwa,ki koma daki ki kwanta.."Kallonsa Tayi kamar Zatayi mgana sai ta Fasa ganin yadda ya Sakamata ido,jiki asanyaye ta juya tana Fadin"Sai da Safe Daddy..."Alebensa ya Karba da Fadin"Allah tashemu lafiya.,yafada yana kallonta Tana Tafiya kamar Zata Fadi Cikin Sanyinta ta Shige dakinta,.


Ajiyar Zuciya ya sauke kafin ya juya yana Dauke da Naila,Ya Karisa Haura Step ya Bude Kofar Farko Mai Dauke da Kayattacen Royal bed Wanda yaji Shimfidun Alfarma gwanin ban Sha'awa Dakin bashi da Yawan Tarkace sai Wani Cafet Wanda ya mamaye Dakin gabadaya mai Taushi yana Fitar da Kyalli Gwanin Ban Sha"awa sai Makeken Wardrope mai  Cinye Rabin Dakin,sai Dreesing Mirror kusa da Kofar Tiolet.


Kai Tsaye ya Karisa gaban Gadon sai da ya Haura Tsakiyar gadon Kana ya Kwantar da Nihal Wacce Barci ya Kwasheta Tana Sauke Ajiyar Zuciya Jin ya Sauketa,Hannu ya saka yana Shafa Goshinta Ahankali alamar lallashi nan da nan Ta Koma barci Saukowa Yayi Daga Kan gadon yana Sauke Ajiyar Zuciya kafin ya Cire Coat din Dake Jikinsa,Ya Rataye Kan Wani Dogon Abu Alamar na Rataye kayane,Towel ya Dauka ya Bude Kofar Tiolet ya Fada da Addu"a Dauke Cikin Abakinsa 


Akallah ya Ashafe Tsawon Minti Talatin Kafin ya Fito Daga Tiolet,kugunsa Daure da Wani Babban Towel sai Kansa yana Rike da Karami yana Goge Ruwan Dake Diga asaman kanshi kai Tsaye Wardrope din Dake dakin ya Nufa ya sanya Hannu ya Bude Kayane Jere Bisa Hanger Iya Kallanka Mallam,gefen American Suit  bakake da masu Ruwan Toka,Dabam gasunan Ajere na Kowani Kamfani sai Wanda ya Zaba zai saka kama daga DKNY,Tommy,hilfiger,Armani,louls,button,Doke,and Gabbana,Bersace,hakama bangaren Manyan kaya Tazarce Kama daga Shaddodi,gezner,yadika Masu Kyau da Tsada Suma bangarensu Dabam Haka bangaren Shirt da Jeans Suma Waje Gudane,bangaren Kayan Shan Iska Irinsu Short Niker Da Riga mai Gajeren Hannu Suma Suna Waje na Dabam sai Daga Kasa bangaren Kayan barci ne gasunan kala kala masu Taushi Da Tsari.


     Cikin kayan Barci nashi Pjm ya Dauko Riga da Wando Masu Ruwan Toka Ruwa Na Diga Daga jikinsa ya Zura Kayan,Ammh Rabin Hankalinsa na kan Naila dake Barci,Baro Gaban Wardrope din yayi ya isa gaban Madubi ya Dauki Wani Turare Spry ya Fesa kafin ya Mtsa Chan Gefe Inda Wata Katuwar Darduma Ke Shimfide ya Tsaya Shuru kafin ya Daidaita Natsuwarsa ya Tada Sallah,


Tsawon Wasu Mintina ya idar da Sallar Shafa"i da Wuturi ya Dade yana Addu"a Kafin Ya mike Wata Yunwa na Kwakulan Cikinsa In Har Bazai Manta ba,Rabonsa da Abinci Mai lafiya da Kwari Tun Jiya Da Daddare kafin ya Dawo Gida Ishaq ya matsa masa Suka biya ta gidansa Sukaci Abinci Toh bayan Shi banda Ruwan Coffea bai kara saka Wani Abu mai Nauyi abakinsa ba,Cikinsa ya Shafa yana Tuna Kalaman Mufeeda yarinyar Tana bashi Mamaki gata Karama da Ita ammh Tafi Farida sanin Halayyarshi Ta Kuma Fita Karantar yanayinsa..,wata Zuciya tace Toh Ita Ke Zaune dakai Farida Yawon Biki da Suna da Zuwa Gidan Kawaye Bai barta ta Zauna dakai ba Balle ta Karanci Waye kai Tahir 


Kansa ya Shafa yana Sauke Numfashi kafin ya Nufi Karamin Fridge dinsa Dake gefen Gado yazauna kafin ya Bude ya Ciro Madarar Hollandia Hade da Kofi Silba wani Karami mai kyau ya Bude ya Tsiyaya,Ya Shanye Duka Kafin ya sake Cikawa ya Kafa kai ya Shanye yana Ajiyar Zuciya mai da Komai yayi Cikin Karamin Fridge din Kafin ya Dora Kafafunsa Duka biyu kan Gadon Yana Kuma Jingina bayansa da Gado,ganin kamar Sanyin Dakin yama Naila Yawa ne yasa ya Dauki Remote din Ac ya Rageta yana Kuma Kokarin gyarama Naila Kwanciya Aranshi yana Tunanin Farida Wata Irin Uwa ce.


Haushin Hakane yasa Ya Mika Hannu ya Dauki Wayarsa Wacce Da Zai Shiga Wanka ya Ijiyeta akan Side Drower,Cikin Lokaci Kadan ya Lulubo Nombarta Wacce Yayi Sarving dinta da *WIFEY*, yayi Shuru yana Bin Wayar da kallo kafin ya cije baki ya Latsa mata Kira yana kallon Agogon Bangon Dakin 10 ta Wuce,wayar ta Shiga Haka Ta Dinga Ringing har Ta Katse Bata Daga ba,bai Hakura ba ya sake Kiranta Nan Ma har ta Karishi Ringing ta Katse bata Daga ba,Tsaki yaja ya kife wayar Gefensa Kafin ya Dauko Karamin Qur'anin Dake kan Side din Drower din gadon ya Bude Suratul Maryam Inda ya Tsaya Jiya Da Daddare Kafin ya Kwanta Domin ya Riga ya Zamemai Jiki baya iya Barci sai ya Karanta al"qur"ani Shiyaasa baya Taba Kwana da Bacin Rai.


Yafara Karatun Kenan Ahankali Cikin Zazzakar Muryansa mai Cike da Amo da Sauti mai Dadin Sauraro Wayarsa ta Fara Kara Tana Neman Dauki sai da yakai Karshen Ayar Kana ya Dago da Kanshi ya Dauko Wayar ganin Sunan Wanda Ke Kirane yasa Yayi Mirmishin Dayafi Kuka Ciwo ya Daga Kiran Yana Fadin"Yanzu Farida Rayuwar da kika Daukanma Kanki mai Bullewa ce..?


Dagachan Bangaren Farida Dake Gefe Cikin Wani Kayataccen Hal Ana ta Dinner Wajen ya Kaure da Hayaniya Tare da Kidan Dj,Sanye Take da Doguwar Rigar Wani Ubansu Fefe les Wanda yaci Dinki mai kyau da Tsari kalan blue Head din kanta Kuma pick Fuska Taci Uban Makeup kamar Wata Amarya Doguwar mace ce Ammh ba Sosai ba,Fara ce, sosai sai Kuma Akwai Kyau da Dirin Mata gaba da baya Masha Allah,Baki ta Bude Zatayi mgana tana Yatsina Fuska Wanda Fararen Hakoranta Suka bayyana Tare da Hakorin Makkanta Yana Daukan Ido Wanda yake Karamata kyau.


Cikin Kosawa Tace"Toh Uban Korafi Ai ina ganin kiran ka Nasan Abun da Kakirani ka Fadamin kenan,Haba Tahir wai Yaushe ne Zaka Daina Kunyatani ne Gaban Kawayena..? Tafada Tana Hararan Gefen Wayar Kamar Tana kallonshi,Shuru yayi yna Kokariin Danne Bacin Ranshi kafin yace"Au kinfison Kada Ki Kunyata gaban Kaawayenki Ammh Kin Manta da Lahirarki da Abunda Kikeyi zai iya Kaiki Wuta Farida...? Baki ta Tura Kafin Tace"Na Shiga Uku Wai Don Allah Tahir me nakeyi Ne..koda yaushe mganar ka kenan Zan Shiga Wuta.."ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace"Yanzu Fisabillah Kwananki nawa bakinan Kin Saka Kafa Kin Fita kin Zubar da ya"yanki Da Mijinki da Gidanki Abun Takaichi Wai Da Sunan Bikin Kanwar Kawarki Farida Anya Kina Son Gamawa Da Duniya lafiya..?


Daure Fuska Tayi Kafin Tace"Ikon Allah,duk mai ya Jawo Wannan mganar..? Inace Su Bassam Sun Girma Suna da Wayon da Zasu Kula da kansu,..."Ya katseta da Fadin"Naila fa..? Kin ijiye mai Bata Nono ne..? Yamutsa Fuska Tayi kafin Tace"Ina Mufeeda..? Miye Amfaninta dama Don Ta Kula da Ita na Amince nama goggo Mgana Anemin ita,Mganar Abinci Kuma I know iya bata Wasa Komai Kuke Bukata Zata Girka Ta Baku ,Toh kuma Wht Else Tahir..?


Cikin Kulufuwa da Bakin Ciki yace"Nifa..Nace Ni Mijinki fa Farida Hakkina na Aure Wa kika Rataye ya bani,Iyan ko Kuwa Ita Mufeedan...? Yafada Cikin Son Kwantar da Fushinsa Duk da yakasance mai Hakuri.


Yar Dariya ta Saki kafin tace"ai dama na sani Duk Wannan Kumfar bakin naka Saboda Ban Dawo na sakarma Jiki kayi yarda kaga dama bako..? Wai Tahir na Tambayeka..? Bata bashi Ikon Mgana ba Ta Cigaba da Fadin"Kai baka gajiya da Sex ne,Narasa Wani Irin Miji Allah ya Hadani Dashi Haba Abu kamar Bambaran Masara Kaga Mallam Nifa ba Sex machine bane balle Ka Ringa Hawata Duk sanda Kaga Dama Ina laifin Sau Daya Asati,ga Kawaye nan Su Binta su Zeenat Su Smarty Ba Wacce Mijinta ya Kirata balle ya Takura mata sai ni Dayake Allah ya Hadani da Ustaz dan Jaraba Sai na Koma na Nanike a gindinka Tahir Duk Shekara kana Min Ciki ina Haihuwa Kamar Waata Akuya ko..? Toh Wlh Baka isa ba,Hakan bazata Taba Faruwa ba Don Allah kar ka sake Kirana Zan Dawo Tunda ba dauwama Zanyi Achan ba,Muna Wajen Dinner so gobe zamu kai Amarya Kano Dagachan Zan biya na kwana Awajensu Abba may be Sai Jibi zan Dawo..."


Daga Haka ta yanke Kiran Tana Hararan Wayar Kafin Ta saki Tsaki Tana Fadin"Fitinanne..."Wayar ta kashe Gabadaya Ta Wurgata Jaka kafin Takoma Wajen Kawayenta Wadanda Keta Kallonta Tundaga Nesa Suna Dariya 


Tahir yaji Wani Abu na Tasomai Daga Kasan Ransa mai kama da Fushi Da Bacin Rai ammh yana Dannewa Wayar yabi da Kallo kafin ya Sauketa yana Sakin Ajiyar Zuciya,yana Kokarin bama kanshi Hakuri,Ammh Dole ne gobe yayi sammako yaje Kauye wajen Goggo ya sanar da Ita an Kawo Limit din Daya Gaji da Zama da Farida Saboda Haka In bata Amince ya Saketa ba Toh Dole Ta Yarjemai ya Kara Aure,Domin Shi ba Dutse bane lafiyayyan Namiji ne mai Bukatar Kulawar Mace Wanda Keson Ya"yan sa Fiye Da Kansa,yana Bukatar Wacce Zata Kula da Duka bukatunsa dana ya"yansa Wacce Take Daraja Aure ba Sakarya Irin Farida ba,wacce In Har ya Lissafa Daidai Wlh Tafi Wata biyar Rabon Data Hada shimfida Dashi,ko bayan Haihuwan Naila bai Wuce Sau Uku Suka Hadu ba.


Ijiye Qur"anin yayi yana gyara Kwanciyarsa Hannu ya saka ya Kashe Hasken Dakin Kafin ya Kunna Dumlight,blanket yaja Ya Rufe kafafunsa Zuwa Kugunsa Inda ya Hada da Naila ya Rufe Mata Rabin Jiki kafin ya maida Kanshi Bisa Filo yana Nanata Dalilin Goggo na Banza Data Dogara dashi Ta Hanashi Kara Aure,Wai da Cewa yana Aiki karkashim Mahaifinta Shi ya Rikeshi Kome ya Zama Shine Sila,Shi kuma Wannam bai Dameshi ba Tunda Son da Iyayen ke mata yasa Suka kasa Tsawarta mata ,Shikan Wannan Karon ba Gudu baja da baya Koda Kuwa hakan zai saka Alhaji Ibrahim Mahaifim Farida ya Yanke Harkan Nemanshi yaji ya yarda Arziki na Allah ammh In yafada Halaka fa..? Ba wanda Zai Zargi Farida Illah Shi da Zai Shiga Cikin Duniyar Nadama na Har Abada.


Da wannan Tunanin yayi Addu"ar Barci ya Shafa Kafin ya Shafama Naila,Hannuwansa ya Tallafa akirjinsa kafin ya Runtse Ido Yana Fatan Barci ya Kwasheshi bayason Tuna Wata Aba Farida...



*Comment,Share,vote..And Like..*


*Shakira*

*Aisha Alto*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


```Wattpad:Janafnancy13 or Aisha Alto```



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


*BISMILLAHIR RAHAMIR RAHIM*


       *BABI NA BIYU*


  Tun bayan daya dawo daga masallaci shida Bassam lokacin 7 saura na safe, kai tsaye ɗakinsa ya koma ya iske Naila ta tashi tana ta kuka, ɗaukanta yayi yana lallashinta ya shiga toilet da ita ya tuɓe mata kaya ya zage yayi mata wanka tsab domin taji daɗin jikinta amma duk da haka Naila 'yar wata goma sha ɗaya bata bar kuka ba daga gani yunwa takeji shiyasa yana gama mata wankan ya naɗota cikin towel ya sauko ƙasa zuwa ɗakin Mufeeda yana ƙwala mata kira.


Iya dake kichen ta fito jin yana kiran Mufeeda agaggauce in kaji ance Iya zaka zata tsohuwa ce ko ɗaya matashiyar dattijuwa ce mai kimanin shekaru hamsin da wani abu kawai su Basma ne ke kiranta Iya tun sanda Mami ta aiko ma Farida da ita daga Kano, shine kowa ya kama.


Ganin Tahir da kanshi yasa ta washe baki tana faɗin "Alhaji kai ne..? Kar dai 'yar rigimar ta tashi da kukanta yau, barka da safiya..?" Yana murmushi ya ranƙwafa yana faɗin "Ina kwana Iya..?" Ta amsa cike da jin daɗin yadda Tahir ke girmamata da darajata, take faɗin "Hala rigima Naila keyi bata ga uwarta ba..?" Yana sosa kai yace "Eh wallahi Iya inaga yunwa takeji ne, na mata wanka amma har yanzu bata bar kuka ba shine nazo zan bama Mufee ita ta bata madara ko tayi shiru.." Iya ta miƙa hannu ta karɓeta tana faɗin "Eh kuma da yunwar inaga bari na dama mata inaga Mufeeda barci ne ya kwasheta don nima yau najita shiru bata fito ba..." Miƙa mata ita yayi kafin yace "To Iya..." Daga haka ta juya ta nufi ɗakin Mufeeda inda kayan madaran Nailan suke da komai nata, shi kuma ya juya ya haura sama.


Wanka ya shiga yafi minti talatin kafin ya fito domin Tahir akwai daɗewa wajen wanka, yana fitowa ko mai bai tsayawa shafawa ba don Tahir kwata kwata baya ƙaunar shafama jikinsa wani abu, wardrope ɗinsa ya buɗe ya ɗauko ɗaya daga cikin fararen gezner ɗinshi ɗinkin tazarce, wanda ya amsheshi sosai aikin jikin shaddar baƙi ne,  hular kansa zanna bukar mai zanen baƙi ce, haka rufaffen takalmin ƙafarsa ma baƙi ne, sai kyakkyawan haɗaɗɗen baƙin agogon fatar dake hannunsa na kamfanin Rado, shi kanshi Tahir daya kai duban kanshi a cikin madubi sai da ya murmusa a ransa yasan cewa tabbas shi mai kyau ne kuma ko a cikin maza sai an tona uwa uba kuma Baba Hakimi zaiji daɗin ganinsa yau cikin shigar manyan kaya.


   Yana gyara zaman hulan kansa wayarsa riƙe a hannunsa yake saukowa daga saman step ƙamshin turarensa na Man na tashi tun kafin ya ƙariso, Basma da Bassam da Mufeeda wacce ke goye da Naila bayan ta bata madaranta ta sanya mata wata bulawus mai kyau tayi shiru ta goyata ram a bayanta, haka itama tana sanye da riga da siket na atamfa cikin wanda Daddy ya ɗinka musu ita da Basma, sai Iya dake gefe suna zaune bisa wani ƙaton ƙayataccen teburin cin abinci mai kama dana alƙarya guda, dama haka aƙidar gidan Tahir yake ba'a nuna bambamci da bare dana gida duk ɗaya ake, kowa dake gidan, in ka ɗauke Megadi da Direba ne kaɗai basu haɗuwa suci abinci tare Farida kuma bata damu ba, don bata cikama zama agidan ba balle ra'ayin Tahir ya dameta, tun Iya da Mufeeda basu saba ba har sunzo sun saba domin dukkansu sun haura shekara biyu a gidan..


Tun daga nesa yaran suka zuba mai ido suna kallonsa harda Mufeeda wacce duk sanda taga Tahir sai taji ta raina duka mazan duniya domin ya gama cika kowani mizami da zati, ga kyau ga asali ga nasaba da kyan hali har misaltawa takeyi a cikin ranta Allah ya bata miji irin Daddy wanda ya iya ɗaukan wanka da gayu, tunaninta ya katse ne sanda taji su Bassam na gaisheshi, amsawa yayi yana shafa kan Basma yana faɗin "Babyna kin tashi lafiya..?"


Tana haɗiye chips ɗin data tura abakinta tace "Lafiya lau Daddy. Allah Daddy Today u look so Fine kamar ɗan saurayi ko Bassam..?." Ta faɗa tana dariya gyaɗa kai yayi yana faɗin "Eh mana Daddy.." Dariya yayi fararen haƙoranshi suka bayyana yana kallon 'ya'yan nashi cike da jin daɗi ya ɗago kenan karaf idonshi ya faɗa ana Mufeeda data shagala da kallonsa rage fara'arsa yayi yana faɗin "Mufee uwar Naila, har tayi barci ne..?" 


Saurin dawowa cikin hayyacinta tayi kafin ta sadda kai ƙasa tana faɗin "Eh Daddy, Ina kwana..?" Yana duba agogon hannunshi ya amsa Iya tace "Ai da zarar Mufeeda ta goyata zaka nemi kuka ka rasa sai kuma barci ai inaga ko aure Mufeeda zatayi Alhaji sai kun yi haƙuri Naila tama Mufeeda zaman ɗaki.." Ta faɗa Tana dariya, shima murmusawa yayi Basma ko dariya ta saka tana faɗin "Mufeedan Iliya mai rake..." Ta faɗa tana ma Mufeedan gwalo, itako tana ɓalla mata harara, duk yana lura dasu, bai tanka ba sai ma ya maida hankalinsa wajen kallon agogon hannunshi yana faɗin "Kunga lokaci na tafiya ku kula da kanku zan tafi Ɗanbatta.."


Ya faɗa kanshi tsaye yana ƙoƙarin ɗaga fulas ɗin ruwan zafi dake wajen ya tsiyaya ruwan cittan cikin wani kofi Basma ce ta miƙe tana faɗin "Kai Daddy shine bakace mu shirya ba." Bassam yace "Eh mana Daddy don Allah zamu bika mun kwana biyu bamu bika ƙauye mun je mun gaida Goggo da Inno ba.." Ya faɗa yana ɓata fuska, Mufeeda ko tunda taji an ambaci Ɗanbatta idonta ya ciko da hawaye tana tunanin kullum sai tayi mafarki gata gaban Inna Fulera suna hira da dariya, amma sai ta tashi taga ba haka ba, rabonta da garin yau wata biyar kenan tun auren Lantana data roƙi Daddy ya saka direba ya kaita tayi kwana ɗaya ta dawo.


  Yana kurɓan ruwan cittan daga tsaye ya dakata yana faɗin "Islamiyanku fa..? Kuna so yau kuyi missing ne..?" Ya faɗa yana kallon fuskokin Bassam da Basma, Basma ce ta fara buga ƙafa tana faɗin "Plz Daddy na yau kadai...plz Don't say no..." Ƙura mata ido yayi yana kurɓan ruwan Lipton dake hannunsa kafin ya sauke yana faɗin "Ok..ok kuje ku shirya sai mu tafi.." Ya fada yana ajiye kofin ruwan lipton ɗin dake hannunsa.


Jin abunda yace ne yasa Bassam da Basma suka daka tsallen murna suka rungumeshi suna faɗin "Tanque Daddy..." A tare suka bashi peck agefen kumatunshi kafin su sakeshi kowa ya rumtuma zuwa ɗakinsa yana murna, Iya na musu dariya, Mufeeda kuwa shiru tayi ta duƙar da kai tana ƙoƙarin share ƙwallar data biyo gefen ƙunnenta, Tahir na lura da ita sai ya murmusa yace "Kema Mufee tashi kije ki shirya ki kuma shirya Naila duka mu tafi harda Iya, tunda bazamu barta ita kaɗai a gida ba.."


Mufeeda jitayi kamar an sakata agidan aljannah Firdausi haƙoranta duka awaje tace "Da gaske Daddy...?" Kai ya gyaɗa mata yana kallonta yadda jikinta yake rawa saboda murna, ga goyon Naila amma haka ta kwashi gudu ta shige ɗaki da mamaki Tahir ke kallonta ganin goyon na rinjayarta Iya kuwa miƙewa tayi tana dariya tace "Nagode Alhaji kamar kasan ko ina son komawa garin nan naku gaskiya iyayenka ko nace gidanku suna da kirki sosai..." Ɗan murmusawa yayi baiyi magana ba illah ficewa da yayi yana faɗin "In kun shirya ku sameni awaje.."


     Mintina talatin yayi musu yawa kowannensu ya shirya baki yaƙi rufuwa karma Mufeeda taji labari wacce ke ji kamar ta buɗe ido ta ganta gaban Inna Fulera saboda yadda ta zaƙu ta ganta, ta chanza kayan jikinta wannan karon less ne ajikinta riga da zani, sai hijabinta hakama Basma itama wata shadda ce ajikinta iri ɗaya dana Bassam itama hijabin ta saka don Tahir bai yarda da sanya mayafi ba kwata kwata bama ya yarda ya siyo musu ko Farida ta siyama Basma bata sakawa in Daddy na nan saboda tasan baya so, hakama Iya ta shirya itama tsab, kayan abinci Tahir yasaka aka ɗebo daga Store aka cika booth ɗin motar kafin Garzali ya shiga mazaunin direba Tahir ya shiga gaba Mufeeda da Basma da Iya da Bassam suka shiga gidan baya da yake motar nada yalwa, nan da nan yayi ma mator key ya saki horn lokaci ɗaya Megadi ya wangale musu get suka sulala waje yana musu fatan isa lafiya da kuma dawowa lafiya.


******


*ƊANBATTA*


Ƙarfe 11pm na safe motarsu ta tsaya adaidai ƙofar gidan Hakimi wanda tunda suka shigo garin Ɗanbatta yara ke bin motarsu da gudu ana faɗi ga Tahir ɗin gidan Baba Hakimi nan yazo saboda yara da manya sunsan yadda in yazo suke warkewa domin haka zai fito ƙofar gida yayi ta rabon kuɗi baya tsayawa sai ƙudin dayazo dashi duka sun ƙare, shima tunda suka shigo garin yake ta amsan gaisuwan mutane daban daban har zuwa ƙofar gidan mahaifin nashi wanda ke zaune a ƙofar gida kan wata kujera daga ƙasa kuma wata ƙatuwar tabarma ne mutane na zazzaune talakawa masu kawo ƙorafe ƙorafansu, shiko mai girma Hakimi Mansur na zaune bisa kujeran nan yana sanye da babbar riga kansa da rawani farin dattijo ne mai farin gashi da dattako, tunda motar ta tsaya farin ciki ya cikashi na zuwan ɗan nashi mafi soyuwa a cikin ranshi, nan da nan mutanen wajen suka miƙe kafin ma Garzali ya zagaya ya ɓude mai murfin motar har ansamu waɗanda suka buɗe mai suna mai barka da zuwa kamar wani babban mutum zakuyi mamakin yadda dattawa ke girmama Tahir sakamakon mutum ne nagari hankali da hikima kuma duk abokan mahaifinsa ne ya zauna cikinsu lokacin yana zaune agarin kafin ya koma cikin garin Kano domin yin makaranta sakamakon shine ɗa ƙwara ɗaya tak namiji da Allah ya bama Baba Hakimi.


  Hannu ya basu suna musabaha lokaci ɗaya yana ranƙwafawa alamar girmamawa har zuwa bisa tabarman dake wajen ya duƙe yana gaida mahaifinsa hakama Bassam yayi, miƙa masa hannu Baba Hakimi yayi yana faɗin "Yaka nan samarin birni.." Ya faɗa yana dariya tashi Bassam yayi yaje kusa da Baba Hakimi ya zauna ya miƙa mai hannu sukayi musabaha yana tambayanshi ya karatu daidai ƙarisowan su Mufeeda suma durƙusawan sukayi suna gaisheshi da mutanen dake wajen amsawa yayi cike da murna yana kallon fuskokinsu kafin yace "A'a amaryata me kika zomin dashi..?"


Basma na dariya tace "Kaji ka me nazo maka dashi ko kuwa mai ka tara min? Nazo karɓan nawa kajin ne da zabbin wannan shekarar.." Ta faɗa tana dariya gaba ɗaya wajen sai da aka murmusa ganin duka haƙoran Hakimi awaje yana dariya kafin yace "Au hakane, toh ki shiga ciki ki kama iya iyawarki, amma in Abu ta ganki ba ruwana.." Miƙewa tayi tana faɗin "Sai me..? Nida abun mijina.." Ta faɗa kamar da gaske, Dariya yayi yana kallon Mufeeda wacce ta sauko Naila data fara rigima hannu ya miƙa mata yana faɗin "A'a wanake gani kamar 'yar wajen Fulera...?" Tahir dake gefe ya taso ya karɓi Naila ya miƙa ma hakimi yana faɗin "Eh itace ranka ya daɗe.." Karɓan Naila yayi yana faɗin "Masha Allah...Allah yayi maka albarka Attahiru, kai kaga yara duk sun girma gama wata amaryar tawa inaga fa nan zan dawo.." Ya faɗa cike da barkwanci yana kallon fuskar Naila wacce ke zare ido tana bin kowa da kallo, dariya aka sakama Hakimi jin abunda yace, miƙewa su Mufeeda sukayi suka shiga cikin gidan suka bar Bassam da Tahir da Naila dake hannun Hakimi.


Gidansu Tahir babban gida ne mai ɗauke da shashe huɗu ginin bana ƙauye bane amma ginin gidan sarauta ne, duk da yanzu Tahir ya ƙara gyara gidan sosai shashen farko na Baba Hakimi ne na biyu kuma na uwargida sauratar mata wato mahaifiyar Tahir Zainabu Abu wacce suke kira Goggo, sai shashe na uku na mai bi mata ne Salamatu wacce suke kira Innaro sai shashen ƙarshe wacce na marigayiya Binta ne aka mai dashi ɓarayin 'yan aiki da kuma wajen ajiye hatsi, gidan Hakimi cike yake da al'umma daban daban kuma babu 'ya'yansa ko ɗaya sai 'ya'yan talakawa da mutanen gari da kuma masu musu hidima acikinsu harda Inna Fulera mahaifiyar Mufeeda tana ɗaya daga cikin hadiman gidan Hakimi masu dafa musu abinci.


Tun isowarsu yara suka shiga da gudu suka sanar da zuwansu toh dayake Basma ta rigasu shiga suna shiga suka isketa kwance kan ƙafar tsohuwa mai ran ƙarfe Goggo Abu kana kallonta kaga inda Tahir ya kwaso kyawawan idanuwa da dogon hanci, gashin kanta cike da furfura ta zauna bisa wani lallausar cafet daya mamaye tsakar ɗakinta mace mai kirki da sanin ya kamata suna shigowa da sallama ta ɗago tana amsawa cike da fara'a lokaci ɗaya tana yi musu maraba.


Gefenta suka zauna Iya ta fara gaisheta ta amsa cikin sakin fuska kafin Mufeeda wacce ke wulga ido tana son ganin ta inda mahaifiyarta zata ɓullo, cikin fara'a Goggo Abu tace "Mufeedan Fulera an zama 'yan mata ko..?" Ta faɗa tana dafa kanta murmushi tayi tana sadda kai kafin Iya tace "Aikam duk sun girma Goggo harda wannan lukutar banzar data haye miki ƙafa.." Ta faɗa tana zungurin Basma wacce ta tura baki tana faɗin "Kai Iya don ma ta samu na hau wannan ƙafar nata data kusa expier.." Make mata kai Goggo Abu tayi tana faɗin "Tashi ja'ira so take ta ƙarisa ni ta samu damar auren min miji ita kaɗai.." Dariya suka saka banda Mufeeda datayi shiru ganin haka yasa Goggo Abu ta tattaka ta miƙe bayan ta ture kan Basma tana faɗin "Ku tashi ku shiga shashen Innaro ku gaisheta inaga bataji zuwanku ba.." Ta faɗa tana nufar hanyar ɗakinta na ƙurya, miƙewa sukayi suka fita sai shashen Innaro ita ma falonta kamar na Goggo Abun ne durƙushewa sukayi suna gaisheta ta amsa cikin sakin fuska tana yafito Basma da hannu ta ƙariso da sauri ta kwanta ajikinta cike da shagwaɓa tana faɗa mata wai Goggo Abu ta hanata zama a cinyarta Innaro na dariya tace "Aiko zata gamu da mai girma Hakimi amarya guda ai dole mu lallaɓaki.." Ta faɗa tana dariya Iya na tayata Mufeeda ce tace "Innaro ina Innata tunda nazo ban ganta ba, ko ta koma gida ne..?" Innaro tace "A'a Innarki na madafi Mufeeda.." Jin haka yasa Mufeeda ta tashi da sauri ta fice kamar zatayi tuntuɓe su Basma suka bita da kallo Innaro tace "Yi a hankali Mufeeda karki faɗi, ina ruwan Mufeeda akwai ƙulafucin uwa ni banzaci ma zata yarda ta zauna gidan Attahiru har tayi wannan daɗewar ba.."


Iya tace "Toh ya zatayi amma fa ranar da aka tuna da Inna Fulera toh wuni za'ayi sharan ƙwallah.." Innaro ta saki murmushi kafin tace "Allah sarki ina ruwan Mufeeda haka itama uwar take sai dai dayake ita tana da kunya da kawaichi ko tana kewar ɗiyar tata bata taɓa nunawa.." Iya tace "Allah sarki..Haka abun yake bagashi yanzu tasamu kyakkyawar rayuwa ba ai wallahi babu abunda zamu ce ma Alhaji sai fatan gamawa da duniya lafiya.." Innaro ta gyaɗa kai tana faɗin "Ameen Ameen...Haka Attahiru yake kowa nashi ne, yafi son kyautatama mutane fiye da ya kyautatama kanshi.." Iya tace "Ba shakka munga zahiri muda muke zaune tare dashi.."


Mufeeda ko tana fitowa daga shashen Innaro ta nufi babban madafin gidan Hakimi nan tayi ta gamo da 'yan aikin gidan suna gaisawa kowa na mamakin ta ƙara girma gabda shiga madafin sai ga Inna Fulera ta fito da sauri domin itama ta samu labarin zuwan su Mufeedan kamar a mafarki suka ci karo ido Mufeeda ta zaro tana faɗin "Innata..." Da ƙarfi kafin ta rumgumeta cike da murna itama cikin tsantsar farin ciki ta ƙanƙameta tana murnan ganin ɗiyarta tilo ƙwara ɗaya da Allah ya bata.


Ɗagowa Mufeeda tayi tana hawayen farin ciki tace "Innata banzata zuwa ganinki ba ayau...Kina lafiya..?" Kanta Inna Fulera ta shafa kafin ta gangaro tana share mata hawayen fuskarta tace "Nima haka farin cikina, yanzu Gaje ke sanar dani zuwanku kunzo lafiya..?" Farin cikina kin ƙara girma kina jin daɗin zaman gidan Alhaji ko?" Gyaɗa kai Mufeeda tayi idanunta cike da ƙwallah tana dariya tace "Innata mu koma gida akwai labari.." Dariya Inna Fulera tayi kafin ta riƙo hannunta tana faɗin "Yanzu kuwa farin cikina, bari na barma Maman Lantana sallahu sai mu tafi.." Da sauri Mufeeda tace "Yauwa Innata Lantana fa..? Ko sun tafi birnin ita da Ladonta..?"


Inna Fulera tace "Tun yaushe bayan auren da wata biyu suka tafi can Kano gidan da yake gadi da zata tafi tazo tamin sallama tayi tacewa na gaisheki.." Kawai sai Mufeeda ta hau sharar ƙwallah tana faɗin "Allah sarki Lantana Allah sa mugana.." Murmushi Inna Fulera ta mata suna riƙe da hannun juna suka nufi madafi Mufeeda maƙale da ita tana mata surutu.


*******


Tahir ya daɗe awaje wajen Baba Hakimi da jama'ar wajen bai shigo ba sai da ya gama rabama mutanen wajen kuɗin da yazo dashi yara da manya, Bassam ya aika yace ya sanarma Goggo Abu ta dama mai fura shida Garzali, nan ya shiga ciki ya barsa toh bai shigo ba sai da yaq gama da wajen kana yama Hakimi sallama da zai shiga wajensu Goggo.


   Goggo Abu na zaune ta gama dama ma Tahir furarsa kenan ta tsiyayarma Garzali nashi cikin wani kofin silba mai kyau ta miƙama Bassam kenan yayi sallama ya shigo kafaɗarsa ɗauke da Naila wacce tayi barci hannun Hakimi, Goggo Abu ta ɗago tana amsa sallamar nashi fuskarta cike da annuri kai tsaye gabanta ya nufa yana ƙoƙarin zama ta miƙa hannu tana faɗin "Kawo ta nan dama da ita kukazo..? Ina uwarta take ne kuka zo da ita ita kaɗai..?" Ta faɗa tana karɓanta lokaci ɗaya ta miƙe ta shiga da ita ciki ta kwantar da ita shi kuma Bassam tuni ya fice zuwa waje ɗauke da fura zai kaima Garzali Allah Allah yake ya fita ko ya samu damar shiga cikin gari kafin Daddy ya farga bayanan don Bassam akwai son ƙauye musamman ma na Babansu.


   Sai da ta fito kana tazo ta zauna inda ta tashi tana turamai kwanon sha mai cike da fura da nono tana faɗin "Lafiya na ganku kamar daga sama inace shekaranjiya mukayi magana da kai sai sati na sama zaka shigo ba.." Ta faɗa tana kafeshi da ido, rausayar da kai yayi kafin yaja kwanon furan ya buɗe yana motsawa da ludayi kafin yace "Goggo Farida bata nan ta tafi bikin ƙanwar ƙawarta Abuja tun wajen kwana uku da suka wuce.."


Ya faɗa yana sadda kansa ƙasa, shiru Goggo Abu tayi kafin tace "Naji, shine dalilin zuwanka kenan ko..?" Ta faɗa fuskarta ba annuri bai ce komai ba illah maida kanshi ƙasa da yayi yana kurɓan fura itama ganin ya mata banza sai ta ƙyalesa sanin halinsa na miskilanci, bai ƙara magana ba sai da ya gama shan furan nashi kafin ya ture kwanon yaja murfi ya rufe yana faɗin "Alhamdulillah..."


Ya faɗa kafin ya gyara zama yana faɗin "Goggo ya jikin ɗan wajen Ashe..? Jiya munyi waya take sanar dani Muda ba lafiya..?


  Tana matsa ƙafanta data miƙar dasu take faɗin "Yaji sauƙi sosai ɗazu da safe nan yake.." Daga haka bata ƙara magana ba matsowa yayi yana tayata matsa ƙafar yana faɗin "Wai har yanzu ƙafar bata bar matsa miki ba Goggo..?" Bata kalleshi ba tace "Tayi sauƙi kasan jikin tsufa fa abun sai a hankali..." Ta faɗa kai tsaye murmushi yayi ganin yadda Goggo abun ke wani cin magani duk don karya mata maganar daya saba ne, amma duk da haka bai haƙura ba gyara zama yayi yana matsa mata ƙafa yana faɗin "Goggo akan maganar Farida ne, tsakani ga Allah na gaji da haƙuri da ita da kuma hallayarta nazo ne na ƙara roƙonki ki bani dama na sanar ma da Baba Hakimi zan ƙara aure..." Ya faɗa yana ƙoƙarin son su haɗa ido.


Ƙur kuwa tamai da ido kafin tace "Har sau nawa zan ce maka kabar wannan maganar Attahiru, maganar Farida nace kayi haƙuri yarinta ke damunta banaso ka yi abunda iyayenta zasu ga kamar mun ɗaure maka gindi ka tozarta musu yarinya. Cike da wani jin haushi ya marairai ce yana faɗin "Toh amma Goggo..." Kabar maganar nan nace ko Attahiru...?" Goggo Abu ta katseshi rai ɓace, kansa ya sadda a ƙasa yayi shiru yana jin kamar ya kurma ihu, ganin yadda yayi ne sai tausayinsa ya kamata ta dafa kanshi tana faɗin "Kayi haƙuri zan yi magana da ita Faridan insha Allahu kaji..." Kai kawai ya ɗaga mata idanuwansa sun canza launi saboda ɓacin rai.

  

Ya daɗe zaune shuru kafin ya saki ajiyar zuciya ya miƙe yana gyara hulan kansa yana faɗin "Bari na leƙa na gaida Innaro daga can zan gangara wajen Ashe naga jikin Mudan." Kai ta gyaɗa kafin tace "Adawo lafiya.." Jiki asanyaye ya fice ta bishi da kallo wani tausayinshi na ratsata amma kuma bazata bari ya sanar da Hakimi wannan maganar ba sai ta ƙara magana da Faridan tunda abu na zumunci ana tare tun ba'a haifesu ba bazata bari Tahir ya ruguza wannan zumuncin ba.


Koda ya shiga wajen Innaro Iya kaɗai ya gani koda ya tambayi Basma sai Innaro tace ta tafi gidan Innarsu Ashe bai daɗe ba ya fito zuwa waje ya sanya Garzali ya buɗe booth yace ya shiga da kayan ciki, shi kuma yayi sallama da Hakimi akan zai gangara gidan Ashe dayake babu nisa da ƙafa ya taka, duk inda yabi ana gaisheshi cike da girmamawa da ban sha'awa har ya isa gidan Ashe can ya iske Basma da Bassam wanda ya gansu a ƙofar gida shida Mudan wanda sa'an Bassam ɗin ne, ita kuma Basma suna cikin gida ita da Laila ƙanwar Mudan ce 'yar wajen AShe dayake tana da tsawon ƙafa har takamo girman Basma.


  Nan Mudan ya ɗuka yana gaida Kawun nashi shi kuma ya riƙoshi yana hararan Bassam da wasa shiko yana dariya riƙe da hannayensu suka shigo gidan Ashe na ganin Yayan nata ta shiga ina zata saka dashi Laila ma tazo ta gaisheshi ya riƙe hannunta yana tambayanta karatu bai wani daɗe ba ya miƙe ya mata sallama zai tafi 30k ya fito dashi daga aljihu ya bata ta karɓa tana ta godiya 5k ya bama Mudan da Laila yace su siya wani abun buƙatar nasu suna ta murna har waje suka rakosu Ashe natama Yayan nata godiya su Mudan kuwa har gidan Hakimi suka rakasu inda Tahir yace suyi haraman tafiya nan fa aka nemi Mufeeda aka rasa Goggo Abu tace yanzu haka sun koma gida ita da Inna Fulera Tahir bai damu ba yace sai su biya su ɗauketa nan ya cika Goggo Abu da Innaro da kuɗi hakama Baba Hakimi wanda ya dinga sakamai albarka tare da nasihan riƙo da gaskiya Allah ya taimakesu har sukazo tafiya Naila nata barci, wajen karfe 3 na yamma motar su tabar ƙofar gidan Hakimi bayan su Laila da Mudan sun sanar da Kawun nasu wannan hutun yasa azo aɗaukesu agidanshi zasuyi hutu yace karsu damu in sun samu hutun zai turo Garzali yazo ya tafi dasu, murna ta cikasu harda su Bassam, wadanda suka kwaso zabbi da kaji gidan Hakimi wai zasu kiwata Tahir na kallonsu ko tankasu baiyi ba bazai shiga tsakanin jikokin da Kakanninsu ba.


Daganan sai ɗan karamin gidan da Inna Fulera ke zaune suka tsaya Iya ne da Basma suka shiga basu daɗe ba sai ga Mufeeda ta fito ita da Inna Fulera ganin haka yasa Tahir ya fito yana amsa gaisuwan Inna Fulera wacce ke neman dukamai tana ta zubamai godiya harda ƙwallarta kuɗi ya ciro 20k ya bata ta kasa karɓa sai kuka take tana faɗin "Nagode Alhaji wallahi basai kabani ko sisi ba alherinka ga Mufeeda kaɗai ya isheni ka tufatar da ita ka ciyar da ita haka zalika ka ilimantar da ita kuma baka taɓa bambamceta da 'ya'yanka ba duk da ta kasance ita ɗin hadimarka ce mai renon 'ya'yanka wallahi bani da bakin gode maka sai dai nayi fatan Allah yasa kagama da duniya lafiya ya kuma sakamaka da gidan aljannah Firdausi.." Da Ameen yake ta karɓawa cike da jin nauyin godiyarta gareshi da ƙyar ta karɓi kuɗin suka rungume juna ita da Mufeeda suna kuka gwanin ban tausayi kafin su saki juna Mufeeda ta shiga mota suna dagama juna hannu har suka bar ƙofar gidan, sun fita cikin garin kenan Naila ta tashi wacce ke hannun Tahir ya waigo yana kallon Mufeeda yana faɗin "Toh Maman Naila bar kukan haka nan gashi tana kukan neman uwar ɗakinta.." Ya faɗa cikin barkwanci yana miƙa mata Naila cikin jin kunya ta share ƙwallarta ta miƙa hannu ta karɓeta nan da nan ta ɓalle jakar data zubo kayan madaranta da Flaks ɗin ruwan zafi da ƙaramin kofi da cokali ta dama mata madaranta ta shiga bata nan da nan takoshi sai kuma ta koma barci bisa kafaɗarta ta kwantar da Naila ita kuma ta jingina kanta jikin ƙofar motar tana sharae ƙwallah..


Ta madubin gaban motar yake kallonta ajiyar zuciya ya sauke kafin ya murmusa yana faɗin "Tasan kan renon yara.." Ya faɗa yana maida kanshi cikin jikin cussinon ɗin kujeran motan shi kuma Garzali ya saki kan mota yana bata wuta.



*Don"t Forget To comment,Vote and Share*



*Aisha Alto*

*Anitha..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


*Wattpad:* *Janafnancy13 or Aisha Alto Alto.*



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


*BISMILLAHIR RAHAMIR RAHIM*


       *BABI NA UKU*


      *ASALIN LABARI*


  

*HAKIMI MANSUR ƊANBATTA* Shine asalin sunan mahaifin Tahir wanda gabanshi da bayanshi haifaffan garin Ɗanbattan ne kuma ya fito daga tsatson Hakimin Ɗanbatta ne daboda haka sarautar Hakimi daya samu ba haye yayi ba gadon gidansu ne.


    Tun suna samarinsu lokacin tasowarsu basuyi karatun boko ba lokacin bai yawaita ba sosai sai dai karatun allo wanda yabi gari lokacin inda ake ɗaukan yara dawaya daga kowane yanki suna zuwa karatun allo cikin Kano da sauraran garuruwa basu dawowa har sai sun sauke alqur'ani wasun suma har sai sun fara sana'a, sunyi ƙarfi kafin su waiwayi gida, toh hakan ne ta faru da Mansur wanda ɗane ga mai garin Ɗanbatta, lokacin dayake da shekara tara a duniya aka tafi dashi cikin garin Kano aka damƙashi hannun wani malamin addini mai suna Malam Haruna wanda amini ne yake ga Hakimi Hayatu.


A lokacin ba dan talaka ko ɗan mai kuɗi ba ko yaron gidan sarauta a'a lokacin ilimi bai yawaita kamar yanzu ba shiyasa zaka samu yara daga mabambantan garuruwa ankawosu wajen Malam Haruna karatun allo duk kuma daya ke iyayen yara a lokacin basu sake kamar na yanzu da in suka kawo yaro sai sun manta dashi a'a su kowane bayan wattanni suna zuwa ganin 'ya'yan nasu kuma suna musu aike akai-akai.


Wannan shine dalilin haɗuwar amintakan Hakimi Mansur da kuma Alhaji Ibrahim Kwatano wanda shima iyayensa suna da hali suka kawoshi nan makarantar Malam Haruna domin ya sauke Qur'ani lokaci ɗaya haɗuwar jini da abota mai ƙarfi ta haɗasu kuma Allah yayisu hazikai masu kaifin ilimi wanda har iyayensu duka suka shaida amintarsu ahaka suka shafe shekara bakwai kafin suyi sauka murna ba'a magana Malam Haruna ya shirya musu walima duka iyayensu suka zo suka tayasu murna, kafin kowa iyayenshi su tafi dashi gida.


Ibrahim yayi sa'a dama already kafin yazo makarantar allon ya gama Primary Sch ɗinshi suna komawa gida iyayensa suka mai cuku-cuku ya koma makarantar SS1, ayayinda shi kuma Hakimi Mansur koda ya koma sai ya fara daga Primary 1 duk da lokacin yana da shekara goma sha biyar ne toh kafin ya gama Secondry tuni Ibrahim yana BUK inda yake karantar Business Admistration, shi kuma Mansur yana gama Secondry karatunsa ya tsaya saboda rasuwar Hakimi Hayatu wanda dama Mansur ne kaɗai ɗansa namiji sauran duk mata ne so sai aka ɗaura ƙaninshi ya cigaba da riƙon sarautar maigari.


Mansur da Ibrahim suna ƙoƙarin ziyarar juna duk wanda ya samu dama Ibrahim na shekarar ƙarshe mahaifiyar Mansur ta matsa mai sai yayi aure kafin ta mutu taga kwanshi aduniya shine dalilin daya sanya ta nema mai auren ɗiyar ƙanin mahaifinshi Zainabu Abu, wanda cikin lokaci akayi komai aka gama akayi biki lafiya sai bayan bikin ne Ibrahim ya tafi service shi kuma Mansur yana zaune agidansu ɓarayin gadon mahaifinsa shida matarshi Zainabu Abu mai kunya da kawaichi shekararsu ɗaya da rabi da aure ta haifi kyakkyawan ɗanta mai kama da ubansa sak aka sanya masa suna Tahir to bayanshi ta yi haihuwa biyu duka basu zo da rai ba, lokacin ne kuma itama mahaifiyar mansur Allah yayi mata cikawa, wanda har iyayen Ibrahim sunzo gaisuwa shi baya ƙasar yana  ƙasar Ughanda yatafi haɗa Masters ɗinshi, tun kuma bayan rasuwarta sai Abu ta shiga ɓari data samu ciki baya zama sai tayi barinshi kamar bazata rayu ba abunda ya fara damunsu har suka fara neman mata magani amma kuma sai cikin yayi kamar zai zauna sai kuma tayi ɓarinshi.


   Sai da Tahir ya shekara 9 aduniya kana Ibrahim yayi aure bayan ya daɗe da dawowa ya haɗa Masters ɗinshi Babanshi ya bashi kuɗi sosai ya ɗorashi kan kasuwancinsa dayake dama shi ɗin motoci yake saidawa 'yan kwatano shiyasa yake amsa wannan laƙabi bikin da Zainabu Abu ita da Mansur da Tahir sukaje suka kwana uku suka dawo domin Mansur da Ibrahim basu yarda zumunci ba.


Matar Ibrahim Aliya itama 'yar gidan masu dashi ne irin yaran nan da jin daɗi yayi musu yawa, shekaransu ɗaya da aure ta haifi yarta mace wacce aka sakama suna Farida, yarinyar data ga gatan duniya sosai daga ɓangaren iyayenta zuwa na kakanninta kuma tunda ga ita Allah bai ƙara basu haihuwa ba.


Tahir nada shekara sha uku aduniya lokacin har ya kammalah zana jarabawarsa na Primary, Abu ta haifi 'yarta mace mai suna Aisha suna kiranta Ashe wacce Tahir yafi ma iyayensu murna da ɗokin haihuwar Ashe tafi tafi rayuwa na nisa har zuwa lokacin da Tahir ya kammalah Secodary School ɗinsa acikin makarantar Secondry dake garin Ɗanbatta.


Tahir tun yana ƙaraminsa yaro ne mai son yayi karatu shima ya zama wani abu ya taimaki iyayensa da garinsa na haihuwa wannan dalilin ne yasa wani ziyara da Alhaji Ibrahim Kwatano ya kawo mai suka tattauna batun Tahir ɗin shikuma yayi mai alƙawarin zai tafi da Tahir domin ya inganta rayuwarsa labarin dayayima Tahir dadi sosai bai tafi dashi a lokacin ba sai da ya karɓi takardunsa ya tafi dashi ya nema mai gurbin karatu a jami'ar BUK kafin yazo ya tafi dashi shi kanshi Mansur yaji wani iri balle Abu da Ashe da suketa kuka amma sai Alhaji Ibrahim ya lallashesu da cewa in suka samu hutun makaranta Tahir ɗin zai dinga zuwa yana gaisheshi.


Kai tsaye ya nema masa Admission bayan ya zaɓar masa course d'in da yayi wato Business Asmitration domin yana sha'awa tare da burin Tahir ya zama yayi karatu ko don ya taimakeshi bisa harkan kasuwancinsa tun bayan da mahaifansa suka rasu duka kula da kamfanin mahaifin nashi ya dawo hannunshi gashi shi kuma ɗiya mace Allah ya bashi zuwan Tahir gidan sai Farida ta samu Yaya duk lokacin tana da shekara tara da wani abu sai ya kasance shike kula da ita koda home work d'in makaranta ne shi ke mata in bai da lakca kuwa suna tare yana koya mata karatu inda bata gane ba kafin kace me shaƙuwa mai zurfi ta shiga tsakaninsu duk kuma sanda ya samu hutu zai tafi Ɗanbatta tare da Farida yake tafiya saboda bata yarda ya barta agida duk inda ya saka ƙafa anan take saka nata al'amarin daya ke ma iyayenta daɗi domin basu da abar farin ciki irin Farida shiyasa suka sangarta komai sai an mata basu la'akari da ita macece, abun na cima Tahir tuwo a kwarya yadda Farida bamai gaya mata taji tun tana ƙaramarta yarinyace mai ƙawayen bala'i da tarkace kowa nata ne ga kuma shegen zuwa gidan ƙawaye tun tana ƙaramarta jikinta rawa yake in taji labari biki kowani event da za'aje achashe sukuma iyayenta sun bata freedom wani lokacin ma Tahir ke taka mata burki taji dayake tana tsoronshi.


Yana shekarar ƙarshe a BUK Allah yama Hakimin rasuwa aka kuma naɗa mahaifinshi wato Mansur bai samu zuwa ba sai lokacin bikin mahaifinshi inda ya ƙara aure da Salamatu Innaro, lokacin ne ya daɗe agida kafin ayi posting ɗinsu su tafi service ɗinsu suna gamawa Abba Alhaji Ibrahim ya matsa mai ya tafi birnin US ya ɗora Masters ɗinshi yana chan har mahaifinshi ya ƙara aure da Binta itama irin Salamatun ne har ta shekara Allah bai bata haihuwa ba sai Hakimi Mansur ya haƙura ya fara tunanin ƙila iya ƙwanshi da zai gani a duniya kenan.


Sai da ya shekara uku kana ya dawo lokacin Farida har ta gama Secondary Sch ɗinta ta shiga BUK aji ɗaya a yayinda Ashe kuma take SS1 wanda yaje yaji wai za'a mata aure shi ya hana yace don Allah abarta ta ƙarasa toh dalilin haka aka barta sai da ta kammalah Secondry Sch ɗinta kana aka mata aure da yaron limamin garin Badamasi suna zaune anan garin Ɗanbatta.


Dawowarshi ne yasa Abba ya buɗe mai kamfani a garin Kaduna wato *IBRAHIM KWATANO AND SONS LIMITED* Wanda ya bama Tahir ragamar kula da wajen amatsayin manaja murna sosai yayi ya dingama Abba godiya haka Hakimi Mansur da yaji sai da yazo har Kano yamai godiya kowani masoyin Tahir in yaji wannan labarin sai ya tayashi murna da farin ciki, lokaci kaɗan kamfani ya fara aiki bayan an zuba ma'aikata da masu kula da abubuwa lokacin ne kuma Tahir suka haɗu da Ishaq wanda ke matsayin Accounting Manager a kamfanin, sai tasu tazo ɗaya sakamakon amana irin ta Ishaq da kuma hankali da sanin mutumcin kanshi shiyasa lokaci ɗaya abota mai ƙarfi ta shiga tsakanin Tahir ɗin da Ishaq wanda shima ɗan asalin Kaduna ne.


   A nan Kadunan Abba ya siyama Tahir gida wanda yake zaune da motar hawa mai tsada saboda taƙaita zirga zirga daga Kano zuwa Kaduna da zuwa Ɗanbatta shekara uku kamfanin yayi da buɗewa amma yayi ma saura zarra dama Tahir haka yake komai ya sama hannu sai anga albarka kafin kuma wannan shekarun abba na matuƙar alfahari da samun Tahir hakama iyayenshi don zuwa wannan lokaci hatta gidansu ya gyarashi tsab ya kuma sakama duka iyayen nashi mata ababen more rayuwa a duka shashensu daya gina musu, lokacin kuma shekara biyu da rasuwar Binta, Ashe ma sha tara na arziki yake mata bama itama kaf al'ummar Ɗanbatta suna alfahari da samun ɗa irin Tahir saboda shi baya da burin ya tara abun duniya illah yama jama'a hidima da kuma garin haihuwarsa.


  

Farida na shekarar ƙarshe a makaranta ta furtama iyayenta ƙudirinta game da Tahir na tana sonshi da aure jin haka ya daɗaɗa ran Abba da Umma sosai sukayi farin ciki domin sun fi kowa sanin samun ɗa nagari mai halin dattako irin na Tahir sai an tona ko kafin ma Tahir ɗin yaji labarin Abba ya isa Ɗanbatta ya labartama Hakimi suma achan ɓangaren shida Goggo Abu sunyi murna sosai don aganinsu su Alhaji sun ma Tahir hallacin daya kamata shima ya saka musu har Kaduna Abba yaje ya sameshi da maganar hakika ya girgiza dayaji muradin Farida amma ba ita da cewa sakamakon Abba yayi mai abunda bazai iya ƙin jininsa ba duk da ko ya gane tuntuni Farida ba irin macen data dace dashi bane, amma bai da yarda zanyi ganin iyayenshi sun kirashi sun jamai kunne kan karyama Abba gardama kan ƙudurin haɗa auren shi da Farida.


Cikin wata uku aka gudanar da bikinsu wanda yabar dimbin tarihi domin shagali akayi kamar ba gobe, bidi'a kala kala don ma shi Tahir ɗin ya doje Ɗanbatta ya tafi bai yarda ya zauna a kano ba sai ranar aure yazo shida Ishaq da tawagar Hakimi da daddare kuma akayi dinner wanda Tahir yasha mamaki uban mutanen dasu kazo wanda shi baisan ko ɗaya ba ashe duk jama'ar Farida ne, saboda tsabar zuwa bikinta har laƙabi ake mata da Farida biki-biki, abun bai bashi mamaki da saninta da uban ƙawaye da kuma son zuwa sha'ani ita ko bikin waye ko ba'a gayyaci Farida tana zuwa indai tasan cewa za'ayi Event aji daɗi ashana ta sake yadda ranta keso balle shiganta BUK ta ƙara samun ƙawaye na gari dana banza kuma ta ƙara yawo idonta ya buɗe amma bana iskanci ba na wayewa.


Washegari aka kawota Kaduna Anguwar Rimi Gra a babban gidan da Tahir ya gina da guminsa Farida taga gata gaba da baya domin da tsala tsalan motocinta biyu aka kawota gidan, ko wata ɗaya basuyi da aure ba Tahir ya fara gaya musu, saboda ko girki Farida bata iya ba ko kichen bata shiga sai dai shi in ya dawo daga Office ya zage ya shiga ya sama musu wani abun su ci, ko kuma in zai dawo yayi musu takeaway baima wahalar da bakinsa ganin bata iya ba balle tayi ganin haka yasa tama Umma magana ta kawo mata 'yar aiki itama basu daidaita ba watanta biyu ta ƙara gaba saboda halin Farida na faɗa komai aka mata ba'a mata daidai ba, watansu huɗu da aure akayi posting ɗinsu zuwa service a kuma lokacin ne ciki ya ɓulla ajikin Farida wacce ta dinga kuka wai zai hanata tafiya service Bauchi, abu har sai da iyaye suka shigo ciki Abba ne da kanshi ya mata cuku cuku ta dawo Kaduna amma ba haka ranta yaso ba ciki zai mata cikas wajen zuwa biki ko sha'anin kece raini amma bata da yarda zatayi don Tahir ya kasa ya tsare kan cikin jikinta taga ainihin kalanshi 


Sai da cikinta yayi wata goma cur kana ta haihu shima C.S aka mata aka ciro 'yan biyu mace da namiji murna wajen Tahir ba'a magana, saboda shagwaɓan Farida da sangarta sai dai Tahir ya barta aka tafi da ita Kano wajen Umma, ta kula da ita yara kuma suka ci sunan Basma da Bassam, Farida bata dawo ba sai da ta kusa wata uku kana ta dawo har su Basma sun fara wayau data dawo har da 'yan aikinta guda biyu ɗaya ta kula dasu Basma ɗaya kuma tayi girki da gyaran gida, zamanta a Kaduna yasa Farida tayi ƙawaye fita biki sai wanda bata jiba Tahir kuma haƙuri gareshi, ko tayi wani abun bai cika mata magana ba saboda miskilancinsa, uwa uba kuma fifikon soyayyarta azuciyar iyayenta da kuma damar da iyayensa ke ganin taimakon mahaifinta gareshi karya wulaƙanta ta amma zamansu da Farida duka  haƙuri yafi yawa a ciki.


Haka dai rayuwa ta cigaba da gangarawa da daɗi ba daɗi Tahir dai na haƙuri da halin Farida rayuwarsu Basma da Bassam kuwa ta walagigi ce hannun 'yan aiki da kuma shi saboda in ya dawo daga Office yana zama ya kula dasu Farida kuma bakin yawo ke cinta daga yau tana wajen bikin ƙawarta sai gobe bikin ƙanwar ƙawarta gashi ita kuma bata da sha'awar yin aiki amma kuma bata iya zama agida ita kenan yawon biki, gashi shi mutum ne da bayason hayaniya da ɓacin rai ya kai ƙararta sau biyu wajen su Abba amma ba wani chanji shiyasa ya kawo ido ya sakamata yana ƙoƙarin shanye ɓacin ranshi akanta duk babu abunda zai ɗaurar na jin daɗin aure shi kam.


Matsala ta biyu kuma shine Farida tana daga cikin jerin matanan masu ƙarancin sha'awa kuma basu ba hakan muhimmanci ba balle ta nemi magunguna ko na musulunci ne saboda shi Tahir yana daga sahun maza mabuƙata, wani lokacin sai suyi sati biyu Farida bata kalleshi ba in ko ya nemeta sai ranshi ya ɓaci ya rasa meke damunta wani lokacin yana buƙatar saboda gudun ma kanshi ɓacin rai yake ƙoƙarin daurewa shiyasa koda yaushe cikin yin azumi yake koda bana ranar Litinin da Alhamis ba.


Bayan haihuwar su Basma tayi family plaining ba tare da Tahir ya sani ba shiyasa har su Basma suka kai shekara takwas bata ƙara haihuwa ba, tunda har sun shiga makaranta Commond sch Kaduna, har tuhumarta ya taɓa yi ta turje tace batayi komai ba taƙi gaya mai gaskiya haka da suka je Ɗanbatta Goggo Abu ke tambayanta Allah sa ba ƙwayoyin zamani Tahir ɗin ya ɗorata akai ba tace ba komai. Da yake ba'a ma Allah dubara cikin wannan tsukun ta samu cikin Naila wanda ya wahalar da ita shima C.S aka mata tana haihuwarta Farida tayi alƙawarin ta gama haihuwa itama wannan haihuwar gida ta koma, 'yan aikinta kuwa tuni ta sallamesu da zata dawo daga wankan Naila ne ta dawo da Iya.


Tahir ya rasa shi wani irin ƙaddaran rayuwa ce ta faɗa mai yana ganin Ishaq da matarsa Zahra gwanin ban sha'awa amma shi ƙarya ne ya dawo daga Office ya iske Farida agida ko tana gida bashi da wani matsayin da zai shigo tazo ta mai sannu da zuwa tayi kwalliya don ya gani yaji daɗi tana ciki tana waya da ƙawayenta ana tsara yadda bikin ƙanwar wanche zai kasance kullum cikin yi mata nasiha da nusassheta yake amma bataji saboda misalin dayake yawan mata da Zahra matar Ishaq ta yanke alaƙa da ita bata wani sakarmata fuska sai itama Zahran taja baya da ita.


  Goggo Abu ce kaɗai da ƙanwarsa Ashe suka san halin dayake ciki in ya gaya mata sai ta bashi haƙuri ta kuma ce zatama Faridan magana toh ko Faridan taje garin in Goggo Abu ta mata faɗa sai tace insha Allahu zata gyara kuma bata gyarawan kuma Goggo Abu ta hanashi sanarma Hakimi wai kada ya zama sanadiyyar raba amintantakar dake tsakanin Abba da Hakimi.


  Mufeeda Kuma Tahir da kanshi ya ɗauko ta faga Ɗanbatta bisa umarnin Goggo Abu bayan Ita Faridan da kanta ta Nemi Goggon data samo mata matashiyar yarinyar wacce zata tayata kula da Naila amatsayin NANNY...."






*Aisha Alto.*

*Shakira.*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕



*Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto*



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


*BISMILLAHIR RAHAMIR RAHIM*


       *BABI NA HUDU*


  *MALLAM BELLO GURGUN DANBATTA* Sunan mahaifin Mufeeda wanda shima ya kasance haifaffan garin na Ɗanbatta ne gaba da baya, haka ma matarsa Inna Fulera itama haihuwan nan ce kuma tashin nan.


Sai dai kuma tun asali dukkansu biyun sun fito daga tsatson talakawa ne futuk marasa ƙarfi kuma dama auren zumunci ne tsakanin Bello da Fulera, bayan haka kuma dangin nasu basu da yawa saura sun mutu sauran kuma sun lula garuruwa neman kuɗi.


Bello gurgun Ɗanbatta ya samo asali ne da tun yana yaro ciwon daji yakamashi ahannu wanda yayi sanadiyar cire mai hannu guda ɗaya shikenan in za'a kirasa sai adinga mai in kiya da Bello gurgun Ɗanbatta, daga Malam Bello har Inna Fulera duka sun rasa iyayensu so suna zaune awani ƙuntataccen gidan ƙasa cikin matsi da wahalar rayuwa, dukkansu babu wanda yayi ilimin boko sai na allo shima ɗin sama sama don lokacin bawai sanin darajan abun sukayi ba, balle su damu dashi baida wata sana'a sai sana'ar noma kayan lambu kamarsu tumatur dasu kabeji da albasa, yana shiga cikin gari yana siyarwa da hannun nasa guda har su samu su rufama kansu asiri.


Sun shekara kusan goma da aure kafin Allah yabasu Mufeeda wanda bayan ita ta haifi 'yan biyu duka maza basu zo da rai ba daga lokacin kuma haihuwa ta tsayama Inna Fulera sai suka cigaba da rainon Mufeeda wacce suka ɗauki son duniya suka ɗora mata saboda ita kaɗai garesu itace 'yarsu kuma ahalinsu sannan abokiyar hirarsu shiyasa itama Mufeeda ta taso cikin so da ƙaunar duka iyayen nata guda biyu, duk da tazo ta iskesu cikin wahalan rayuwa amma suna iya bakin ƙoƙarinsu akanta don ita kanta Inna Fulera bata zauna ba tana saida dafaffen kabeji acikin gida ana zuwa siya ba laifi tunda tana da   tsabta...


Haka suka cigaba da gangara rayuwarsu da daɗi ko ba daɗi har lokacin da Mufeeda keda shekara goma sha uku a duniya ta girma duk wasu alamun budurci basu bayyanar mata ba sakamakon siririyace ita bata da jiki sosai, kwatsam suka tashi da wani rashi, rashi mai girma daya taɓa zuciyarsu wanda har yau suka kasa mantawa dashi na rasuwar Bello Gurgu sanadiyar faɗawa rafi ruwa ya cinyesa Inna Fulera da Mufeeda sunyi kuka kamar ransu zai fita, duk da a lokacin Mufeedan nada ƙarancin shekaru amma wannan rashin da sukayi ya tsaya mata sosai a cikin ranta. 


Ko takaba Inna Fulera bata fita ba suka fara shiga tasku da wahalar rayuwa na babu sai su kwana basu ci ba, abun na damunta duba da ƙarancin shekarun ita Mufeedan shiya sanya tana gama takaba labarin neman ma'aikata daga gidan Hakimi ya sameta inda Tahir ya bada cigiyar neman waɗanda zasu dingama iyayensa hidima yana biyansu duk wata Inna Fulera batayi ƙasa agwiwa ba ta isa gidan Hakimi gaban Goggo Abu sai dai koda taje an riga angama ɗaukan adadin ma'aikatan, nan Inna Fulera ta faɗi gaban Goggo Abu tana kuka tana roƙonta data rufa mata asiri ta taimaki rayuwarta data marainiyar Allah Mufeeda toh a lokacin sai taausayin ƙarancin shekarun Mufeeda ya ɗarsu a zuciyar Goggo Abu har yayi sanadiyar data ɗauki Inna Fulera amatsayin hadimarta amma in tagama da shashenta takan shiga madafi ta taimaka duk wata 15k Tahir ke biyansu dukkansu wanda cikin lokaci kaɗan ya taimaki rayuwar mutane dadama ciki harda Inna Fulera wanda cikin haka ne ta sanya Mufeeda a makarantar Primary Ɗanbatta tana zuwa idan ta taso sai ta biyo gidan Hakimi wajen Innarta taci abinci ta ƙoshi ba shashen datake zuwa sai shashen Goggo Abu ta zauna tayi shuru dake bata da yawan magana wani lokacin in Goggo Abu ta ganta sai Tahir ya faɗo mata acikin ranta tana tunanin shigen miskilancinsa amma in ta kalli yanayin Mufeeda sai taga ta shanyeshi haka kurum take jin tausayin yarinyar shiyasa take janta ajiki sosai.


Mufeeda bata da wata ƙawa agarin sai Lantana wacce maƙotansu ne itama Mamarta tana aiki agidan Hakimi ita kaɗai ce ƙawarta kuma gashi makarantarsu ɗaya kuma ajinsu ɗaya, shiyasa sai tasu tazo ɗaya kuma in sun tashi daga makaranta tare suke wutowa gidan Hakimi wajen iyayensu, Mufeeda bata da saurayi kamar na sauran 'yanmatan ƙauye ko nace bata bi ta kansu kwata kwata saboda ita bata son auren wurin da'ake musu mutum ɗaya ne take kulawa shima sai ya dameta Iliya mai rake, tun tana ƙaramarta yake bibiyarta abokin saurayin da Lantana zata aura ne Murtala shiyasa wani lokacin in sun biyo hanyar makarantar allo in Murtala yaja Lantana gefe itama sai Iliya ya jata duk dai bata sakarmai fuska bai damu ba saboda yaci ace ya saba da yanayin rayuwar Mufeeda.


  

   Inna Fulera bata rufe shekara da samun aiki agidan Hakimi ba Farida tazo garin inda ta samu Goggo da shawaran tana buƙatar a nema mata wata yar yarinya wacce zata tafi da ita amatsayin Nanny saboda kula da Naila sai su dinga biyanta duk wata suna aikoma da iyayenta tunda ta lura duk waɗanda Umma ke samo mata daga Kano ita basu mata, Goggo Abu na jin haka sai Mufeeda ta faɗo mata arai amma sai ta fara tunanin kamar ba zata iya ba, ilai ko Faridan na ganin Mufeedan tace ko itama aka bata ta isa, Goggo Abu bata yanke hukunci ba sai da ta nemi shawaran Hakimi da Innaro suka kuma bada goyon baya Duk Da Tahir ɗansu ne amma suna da kyakkyawan sheida akanshi shi da matarshi basu wulaƙanta mutane...


Cike da ƙwarin gwiwa Goggo Abu tasa aka mata kiran Inna Fulera ta labarta mata muradinta azahirin gaskiya taji firgicin maganar duba da Mufeedan kaɗai gareta kuma ta ƙwallafa rai da ita amma kuma Goggo Abu bazata nemi alfarma taƙi mata ba, bata da yarda zatayi ta amince amma zuciyarta ba daɗi duk da ko ta tabbatar Mufeeda zata samu ingantacciyar rayuwa agidan Tahir, amincewar Inna Fulera ya sanyayama Goggo Abu rai nan ta mata alƙawarin insha Allahu bazatayi nadama ba, Farida ta koma bayan ta bar sallahun Mufeeda ta shirya sati mai zuwa direba zai zo ya ɗauketa.


Inna Fulera data koma gida tayi kuka sosai kuma bata iya sanarma da Mufeeda ba, fahimtar haka yasa Goggo Abu ta saka Inna Fuleran ta turo mata Mufeedan ta sanar da ita, wayyo gwanin ban tausayi duk da ta kasance mai rauni wajen kazar kazar ɗin rayuwa amma kukanta ya kasa ɓoyuwa tana kiran ita bazata bar Innarta ba Goggo Abu ke ta lallashinta amma taƙi yin shiru ƙarshenta ma ta tashi da gudu ta fita sai gida chan taje ta sakama Inna Fulera kukan ba inda zata tafi ta barta, kwana tayi lallashinta da bata baki amma Mufeeda taƙi yarda.


Sati kuma na cika sai ga Tahir yazo garin Garzali ya kawoshi kuma shi Farida bata sanar dashi komai ba, Goggo Abu kuma tana ganin haka sai ta zata ya sani ne shine yazo tafiya da Mufeedan nan da nan tasa aka kiramata Inna Fulera tace tayi maza taje ta shiryo Mufeeda da kayanta ga Attahiru nan yazo tafiya da ita Kaduna, Allah sarki raba uwa da 'ya sai Allah da kuka da komai Inna Fulera ta kawo Mufeeda gidan Hakimi sai lokacin ma Tahir yasan da maganar bai wani damu ba sanin dama Farida bata ɗaukeshi bakin komai ba, abun kuma yayi mai daɗi ko banza yana daraja garin haihuwarsa haka Mufeeda ke kuka Inna Fulera nayi taƙi shiga mota ta ƙanƙameta Innarta tana wani kuka mai ban tausayi tare da ƙawarta Lantana, har sai da Hakimi yace a haƙura da tafiya da Mufeedan asamu wata saboda yadda daga Mufeedan har Inna Fuleran suka bashi tausayi haka shima Tahir wanda da kanshi yaje ya riƙo hannun Mufeeda yana kallonta ƙwarjininsa ya hanata yi mishi gardama gaban Inna Fulera ya duƙa yana ƙara jaddadamata insha Allahu zai kular mata da Mufeeda kamar 'yar da ya haifa kuma alƙawari ne yayi mata zai dinga kawo Mufeeda lokaci bayan lokaci tana zuwa ganinta, wannan kalaman nashi su suka sanyaya ran Inna Fulera da kanshi ya saka Mufeeda cikin mota da ƙullin kayanta wanda ƙwarjininsa da kimarsa yasa ta kasa mishi gardama amma har motarsu ta ɗaga daga ƙofar gidan Hakimi Mufeeda na kuka tana ɗagama Inna Fulera hannu itama tana kuka tana ɗagamata Iliya ma yana laɓe daga chan yana leƙen tafiyar Mufeedan sai da ya share ƙwallah saboda an rabashi da masoyiyarsa zuwa birni shima Murtalan Lantana ke gaya mai..


  Koda Farida taga Tahir da Mufeeda bata damu ba dama tunda yace yau zashi Ɗanbatta ta sani Goggo Abu zata bada Mufeeda azo mata da ita shiyasa bata damu ba, lokacin da Mufeeda ta tsinci kanta agidan Tahir ta sani ta shiga wata sabuwar rayuwa na bambamcin komai kama daga wayewa da garin ma gaba ɗaya, da farko bata iya sakin jiki ba duk da ko ɗakinta ita kaɗai Farida ta bata bayan ta miƙa mata amanar Naila wacce lokaci ɗaya yarinyar ta shiga ranta abunda ya ƙara sanyayamata rai shine yadda ko su Basma basu nuna mata bambamci duka ɗaya suke ga Iya itama tana mata kyakyawan mu'amala ta ɗauketa kamar 'yar data haifa da cikinta, balle Farida da bakomai take bama muhimmanci ba, kuma ance mai ɗa wawa balle data lura yadda Naila ke samun kulawa sosai wajen Mufeeda cikin lokaci kaɗan tayi kiɓa ta chanza shiyasa komai nata na ɗakin Mufeedan awajenta yake kwana in ba Tahir bane ya matsa ta ɗaukota nono kuma in tana nan ne take bata in ko bata nan sai dai ta wuni shan madaran ruwa.


Farida bata da matsala ta ɓangaren ƙyashi ko wulaƙanta mutane ta fito daga gidan arziki shiyasa Allah bai ɗora mata wannan ƙyashin ba, komai zatama Basma da Bassam sai ta haɗa da Mufeeda da Iya haka ma Tahir baya nuna bambamci akan komai abinci tare suke ci, tun Mufeeda na ɗari ɗari har ta saki jiki ta saba, kuma duk wata Tahir na turama Inna Fulera 20k da farko cewa tayi bazata karɓa ba yayi yawa sai da Goggo Abu ta matsa mata.

Watanta uku da zuwa Farida tabama Tahir shawaran asanya Mufeeda a makaranta nan da nan ko ya yarda da shawaranta shima abun na ranshi cikin sati ɗaya cike cikenta ya tabbata ta samu gurbin karatu a Model School Kaduna inda ta fara daga Js1 duk da tana Primary 4 ta tsaya lamarin dayama Mufeeda daɗi sai da tayi kuka da farko ta fara samun matsala ta ɓangaren wayewa da kuma turanci, sai kuma Tahir ya sama musu Lesson Teacher ita dasu Basma yana koya musu suma kuma suna ƙoƙarin koya mata abunda bata gane ba tunda suma Js1 ɗin suke sai dai su Commond School sukeyi sai an kaisu kana direba ya wuce da ita in ta tafi makaranta sai Iya ta karɓi kula da Naila wacce tasha kuka kafin ta saba da rashin Mufeeda kafin ta dawo makaranta ta gaji da kuka ta haƙura.


  Sai da suka samu hutun farko kana ta roƙi Tahir wanda take cema Daddy don amatsayin uba ta ɗaukesa zata je Ɗanbatta direba ya kaita ta kwana biyar ta dawo saboda Naila, zuwan daya yima Inna Fulera dad'i haka suka ƙanƙame juna Lantana da wasu mutanen gari basu iya gane Mufeeda ba saboda yarda ta zama 'yar gayu tayi kyau kamar ba ita ba, hakama Iliya daya ganta sai da hankalinshi ya tashi na ganin tabbas Mufeeda tafi ƙarfinsa koda ta koma bikin Lantana ya kusa, bata saran zuwa ba amma data roƙi Mami Farida ta roƙar mata Daddy sai gashi ya barta taje ta kwana ɗaya ta dawo zuwan daya sanya ta zama zara cikin wata saboda kyanta da kuma ilimi da wayewar data samu tare da cigaban rayuwa.


Matsalar Farida da Tahir ta fara girma tunda yanzu sai ta shafe wata da watanni bata bashi hakkinshi ba, kuma shi ba dutse bane yana buƙatar wajen ɗebe kewa da damuwa, amma sam Farida hakan baya gabanta in ya nemeta tayi ra'ayi to laba'asa ne da komai ya kammala shikenan ko ajikinta, abun na damunshi kullum cikin azumi yake gashi bata zama agida abun haushi yawon gidajen ƙawaye in Farida taji biki jikinta na rawa tun ada yana ɗauka yarinta ne in taƙara girma zata bari amma ina ko raguwa baiyi ba, su Abba ko ya gaya musu suka mata faɗa zata nuna taji amma kuma ta bayan kunnanta yake wucewa haka Goggo Abu wacce ke tausanshi kada ya sanarma Hakimi halin dayake ciki, maganar ƙarin aure kuma ba ra'ayinshi bane tunda shi mutum ne mara son hayaniya gashi kuma da haƙuri amma ƙanwarsa Ashe ce ta bashi shawaran ya ƙara aure ya bar Faridan ita taje chan ta ƙarata da halinta tun bai yarda da shawaranta ba har ya fara tunanin shine mafita toh Goggo Abu ce ta takamai burki sau uku kenan yana zuwar mata da maganar tana dakatar dashi, saboda dalilinta na kada azo ayi abunda zai lalata zumuncinsu, abun na damun Tahir amma haƙurinsa da kuma kawaicinsa yasa ba'a gane halin dayake ciki banda abokinshi kuma amininshi Ishaq.



Wannan kenan.



******


*Kano*


_Tarauni Gra_



 Ƙudundune take a cikin lallausan bargo tana sharar barcinta hankalinta kwance Umma ce ta shigo cikin bedroom ɗin tana bin Faridan da kallo lokaci ɗaya tana duba agogon bangon daya ƙawata bedroom d'in ƙarfe 12 daidai kai ta girgiza kafin ta ƙarasa kusa da Farida gefenta ta zauna tana ƙara gyara zaman doguwar rigar leshin dake jikinta matashiyar dattijuwa ce fara mai yalwar fara'a kallo ɗaya zaka mata ka fahimci hutu da jin daɗi sun zauna mata fuskarta kuwa ɗauke da kwalliyarta don Hajiya Aliya bata yarda da zama haka ko kuma girma ya cuceta ba a'a tafi kowa kula da mijinta da tattalinshi, inda ace Farida tana lura da yanayin rayuwar iyayen nata da har abada Tahir bai taɓa complain akanta ba.



 Bargon ta yaye kafin ta fara buga ƙafarta tana faɗin "Farida...Ke Farida..." Miƙa tayi tana wani ƙara narkewa bargon take ƙoƙarin ƙara ja, da sauri Umma ta fizge tana faɗin "Wai miye haka..? Tun jiya da kika iso kike kwance kina wannan barcin, bazaki tashi kiyi ƙoƙarin komawa gidanki ba baki tunanin wani hali mijinki ke ciki da 'ya'yanki balle ma ki riƙa tuna ƙaramarsu Naila mai shan nono..."


 Ta fada cikin damuwa, miƙa Farida tayi tana turo baki kafin ta miƙe da ƙyar tana gyara gashin kanta wanda duk ya baje saboda barci, fuska ta yamutsa kafin tace "Toh Umma me zai samesu..? Lafiyansu ƙalau su fa, Basma ba yara bane, Tahir ma haka Naila kuma Mufeeda na kula da ita, in ma ta tafi makaranta iya na gida zata kula da ita.." Ta faɗa tana zuro ƙafarta ƙasa, kallonta Umma tayi kafin ta dafa kafaɗarta tana faɗin "Toh naji tashi dai ki yi wanka ki shirya ki fito ki karya ki yi haraman tafiya kinji Faridata..?" Ta faɗa da sigar lallashi da lalama, miƙewa Farida tayi bayan ta zura wani takalmi mai taushi tace "Umma ina Abba..?


 Miƙewa itama tayi tana faɗin "Abbanki ya fita tun safe yana da baƙi, amma ya bar sallahu direba ya tuƙa ki zuwa Kaduna yace bayason kina doguwar tafiya ke kaɗai.." Murmushi ta saki kafin tace "Abbana kenan toh me zai sameni nifa ko achan Kaduna Tahir baya tuƙani duk inda zani da motata nake zuwa har Ɗanbatta in kinga direba ya tuƙamu tare ƙila tafiyar tazo ɗaya ne.." Murmushi Umma tayi kafin tace "Hakane, toh kindai ji sakonsa ko..? Toh kiyi maza ki shirya ki fito.." ta faɗa tana kama hanyar ficewa, ƙara tura baki Farida tayi kafin tace "Kai Umma sai wani koro na kikeyi.." Ta faɗa tana tura ƙofar toilet Umma bata ba zancenta muhimmamci ba tace "Eh saboda baki da gatan daya wuce gidan mijinki da 'ya'yanki.." Faridar na jinta daga bayi sai ma ta kyaɓe baki don ita basu dameta ba gani take da ƙafarsu da lafiyansu sai ta zauna ta ƙoƙarin ƙare rayuwarta akansu.



 Sai da Farida ta shafe wajen awa ɗaya kana ta fito daga cikin bedroom ɗinta na gidan iyayenta, sanye da wata irin shadda Gezner mai ruwan brown ɗinkin doguwar riga, sai ɗaurin Maryam Babangida data cukashi, fuskarta ba kwalliya amma kuma kallon farko zaka mata ka fahimci bata da wata damuwa, vail ne yafe akanta sai ƙaramar jakarta Umma ta tarar akan dining tana breakfast cikin yanga ta ƙarasa itama taja kujera ta zauna tea kad'ai tasha sai ferfesun kayan cikin ta miƙe tana share bakinta da tissue, kallonta Umma tayi kafin tace "Don Allah Farida ki dinga zama agidanki ba don niba sai don ki girmama darajan aure ki kuma girmama haƙurin mijinki akanki plz.."


 Rausayar dakai tayi kafin tace "Umma kenan Tahir ya gama shanye ku kuma, kamar yadda ya gama da iyayenshi, shikenan kuma ni ban san ciwon kaina ba Umma nafa girma nima daidai gwargwado na mallaki hankalin kaina ai nasan me nakeyi, bikin fa ƙanwar Beauty akayi fa Umma kuma kinsan yadda muke da Beauty tun muna makaranta, kawai shegen ƙorafin shi ne yayi yawa..." Ta faɗa tana ɓata fuska kafin ta wuce ta koma cikin bedroom ɗinta ta ɗauko ƙaramar trolley ɗinta ta fito tana faɗin "Umma zan tafi sai munyi waya.."


   Umma ta bita har waje inda direba ke jiranta trolley d'in direban ya karɓa ya saka cikin wata baƙar Venz ɗin Farida, kafin ya buɗe mata gidan baya sai da ta shiga kana ta leƙa tana fadin "Umma zan bashi kuɗi ya shiga motar haya in mun isa, ki gaida Abba..." Kai Umma ta gyada tana faɗin "Allah ya kiyaye hanya kar dai naji kin sake fita har zuwa nan da sati biyu Allah kuwa.." Dariya Farida ta saki har haƙorin Makkanta sai da ya bayyana kallonta Umma tayi kafin tace "Kinji ni ko baki ji ba..?"


 Kai ta gyaɗa kawai batayi magana ba amma acikin ranta tana tunanin irin shagalin da suke dashi ranar sati anan Kaduna, ƙanin Bilkisu zai yi aure dole suje su raƙashe, har motarsu ta fice daga haraban gidan Umma na ɗaga musu hannu ita kuma Farida sai ta ƙara gyara zama ta jingina kanta jikin kujera ta fito da wayarta ta fara latsawa tana sakin murmushi lokacin data shiga WattsApp, inda taga group ɗinsu na Classes Bbys na waɗanɗa sukayi makaranta tare ya cika da massagea tasan ƙila maganar yadda bikin ƙanin Bilkisu zai gudana ne jiki na rawa ta shiga ta fara bin Chat ɗin cike da farin ciki.







*Aisha Alto*

*Shakira*

*NANNY...!*

     (Mai Reno..)


*Alƙaluman:✍🏻*


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR (Janafty*💕


*Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto*


*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI*💔

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM*💘


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


        *BABI NA BIYAR*


Ƙarfe 3:30pm. Suka shigo garin Kaduna direct suka nufi Unguwar Rimi GRA suna zuwa maigadi ya buɗe tangamemen gate ɗin gidan direba ya sulala motar ciki ya yi parking ya fito da sauri ya buɗewa Farida ta ziro ƙafafuwanta waje sannan ta fito riƙe da wayarta da ƙaramar jaka a hannunta ta buɗe jakar ta ɗebo kuɗi ta miƙa masa "Gashi kaje tasha ka shiga motar haya ka koma gida. Allah ya tsare." Cike da ladabi ya karɓa yana mata godiya, hannu kawai ta ɗaga masa ta juya ta ɗauki ɗan ƙaramin akwatinta ta shige cikin gidan, direban ya juya shima ya fice daga gidan.


Falon tsit yake babu kowa a ciki da alamu yara basu riga sun dawo daga makaranta ba, a gajiye take dan haka bata bi takan komai ba ta nufi ɗakinta, tana gab da shiga ɗakinta ta tsinkayo muryar Iya cike da murna tana faɗin "Sannu da zuwa Hajiya, ashe kece? Ina kichin zan haɗawa Naila madararta na jiyo motsin shigowa..sannu da dawowa." Iya ta faɗa fuskarta cike da fara'a tana tahowa inda Farida take tsaye da Naila riƙe a hannunta tana murmushi.

Murmushin itama Faridan tayi ta aje ɗan akwatin hannunta ta miƙa hannu ta karɓi Naila ta ɗagata sama ta sumbaci goshinta ta shafa kanta sannan ta miƙawa Iya ita ta ɗauki akwatinta tace "Sannunku da gida Iya." Ta faɗa kawai tare da shigewa ɗakinta, turus iya ta tsaya tana bin bayanta da kallo kafin ta girgiza kai kawai ta juya ta koma kichin dan cigaba da abinda take yi, dan in dai halin Farida ne na nuna halin ko in kula da 'ya'yanta da duk wani abun daya shafi gidan aurenta yaci ace zuwa yanzu duk sun saba dashi, bai kamata a kullum ya zama wani sabon abu ko baƙon abu a gurinsu ba.

Kwana da kwanaki bata gida bata tare da 'ya'yanta da mijinta ga yarinya ƙarama mai shan nono wacce ko yayeta bata yi ba amma ta dawo ko ta tsaya ta tambayi yanda suke balle ta ji ina suke da bata samesu a gida ba, gashi ko ƙaramar 'yarta mai shan nonon ma bata wani damu da ita ba ko ta nuna kulawarta a kanta ba, shiyasa itama 'yar ko murna da ganin uwar tata bata yi ba sai kallonta kawai da take kamar wata baƙuwa.


Tana shiga bedroom ɗinta ta zube wayarta da jakarta ta tuɓe kayan jikinta ta jawo tawul ta ɗaura ta faɗa toilet, bata wani daɗe sosai ba ta watsa ruwa ta fito ta faɗa gado tai kwanciyarta abinta saboda wani irin bacci take ji duk ta gaji jikinta sai ciwo yake mata.


Ƙarfe 4pm. Bassam da Basma suka dawo daga makaranta, suna shigowa suka tarda Iya na bawa Naila madara a falo a gajiye duk suka zube saman kujera suna maida numfashi, Iya ta ɗago tana kallonsu da murmushi akan fuskarta tace "Sannunku da dawowa ya makarantan?" Basma na turo baki tace "Ba daɗi Iya, yau munsha wuya ga rana ga zafi." Dariya Iya tayi tana kallonta tace "To Mummy dai ta dawo..." Da murna duk suka miƙe suka kwasa da gudu suka nufi ɗakinta tana kwance suka shigo cike da farin cikin ganin mahaifiyarsu suka faɗa kanta da gudu suna murna suke faɗin "Oyoyo Mummy..!" 

haɗe rai tayi ta yatsine fuskarta ta tashi zaune haɗe da janyesu a jikinta ta ɗaure fuska tace "Please kuje waje ina so zan huta ne, idan na tashi zan nemeku.." ta faɗa tare da janye hannunta ana Basma tana nuna musu ƙofar fita, a sanyaye yaran ke kallonta kafin su juya a hankali suka fice daga ɗakin suna waigenta, ƙaramin tsaki taja ba tare da tunanin komai ba ta gyara kwanciyarta abinta ta lumshe idonta tana jira bacci ya ɗauketa.


Yanda Iya taga sun fito daga ɗakin jikinsu a sanyaye yasa ta miƙe da Naila dake bacci a hannunta ta nufesu ta kamo hannun Basma tana ɗan murmushi tace "Kuje ku cire kayan makarantan kuyi wanka sai ku fito ku ci abinci, kafin nan Mufeeda ta dawo itama sai ku shirya ku wuce islamiyya.." gyaɗa mata kai suka yi kafin kowa ya nufi ɗakinsa, itama ta juya ta nufi ɗakin Mufeeda ta kwantar da Naila ta fito.


Sai da sukayi wanka sukayi sallar La'asar sannan suka fito falo cikin shirinsu na tafiya islamiyya, lokacin itama Mufeeda ta dawo har tayi wanka ta saka uniform irin nasu tayi shirin islamiyya. 

A dinning suka haɗu suka ci abinci kafin da suka gama suka ɗauki jakunkunansu suka fice Garzali ya kwashesu zuwa islamiyya.


Ƙarfe 6:20pm. Suka dawo suna shiga falon kowa ya nufi hanyar ɗakinsa.

Suna shiga falon motar Tahir na shigowa cikin gidan dawowarsa kenan, bayan yayi parking ya buɗe motar ya ɗauki wayoyinsa da rigar suit ɗinsa daya cire ta saman yabar ta cikin a jikinsa ya kulle motar ya nufi cikin gidan da takunsa mai cike da kuzari da izza ya shiga falon da sallama, da gudu Basma da Bassam da suka buɗe ɗakunansu zasu shiga suka rugo gurinsa suka faɗa jikinsa tare da ƙanƙamesa suna masa barka da zuwa, yana murmushi ya riƙe hannun Basma yayinda shi kuma Bassam ya karɓi rigarsa da makullin mota ya riƙe fuskarsa cike da fara'a da murna yace "Daddy Mummy ta dawo tana ɗakinta.." ɗif Tahir yayi ya gimtse fuskarsa yay kamar baiji abunda Bassam yake cewa ba, kallon juna suka yi da Basma kafin Bassam ya ƙara kallonsa yace "Daddy Mummy fa ta dawo.." karɓar rigarsa da makullin motarsa kawai yayi a hannunsa yace "Maza kuje ɗaki ku cire uniform ku canza kaya, sai kuyi alwala ka fito muje masallaci an kusa kiran sallah." Yana faɗa ya saki hannun Basma suka nufi ɗakunansu shima ya juya ya nufi bedroom ɗinsa yana jin wani takaici da ɓacin rai a zuciyarsa.


Yana shiga ya tuɓe kayan jikinsa ya shige toilet a gurguje ya watso ruwa ya haɗo da alwala ya fito ya zira jallabiya ya fesa turare ya ɗauki casbaha ya fice daga ɗakin yana fita ya samu Bassam da Mufeeda zaune a falo, tana ganinsa ta miƙe ta ɗan rusuna ta gaishesa ya amsa yana kallonta kafin ya kama hannun Bassam suka fice zuwa masallaci itama Mufeeda ta nufi ɗakinta don gabatar da sallar Magriba da ake kira.


  Basu dawo ba sai da suka sallaci sallar Isha'i kana wajen after 8 suka shigo gidan, suna shigowa suka iske Mufeeda da Basma suna taya Iya jera warmers akan dinining, kallo ɗaya yayi musu sanda Mufeeda da Basma suke mishi sannu da suwa kai ya gyaɗa ba tare da yayi magana ba ya fara haura step Mufeeda ta bishi da kallo asace tana so ta karanci yanayinsa, karaf ya waigo suka haɗa ido gabanta ne ya faɗi tayi saurin sadda kai jikinta ya fara rawa ganin yadda ya sakar mata ido Basma ce ta lura da tsayuwarshi idonshi na kallon Mufeeda amma bai bari kowa ya fahimta ba cikin kulawa Basma tace "Daddy plz kai da Momy ku fito muyi taking dinner tare tunda all of u yau kuna gida.."


Bassam dake zaune kan ɗaya daga cikin kujerun falon tun bayan shigowarsu shida Tahir yace "Eh mana Daddy plz...We miss u.." Ya faɗa cikin muryan taausayi wani haushin Farida ya ƙara kamasa, amma bai nuna ba sai ma ya murmusa yana fadin "Mufee Naila tayi barci ne...?" Kanta na ƙasa tace "Eh Daddy tun ɗazu dana bata madararta na goyata tayi barci.." Gyaɗa kai yayi kafin ya juya yana faɗin "Gud.." Bai ko ƙara kallon su Basma ba waɗanda suka sakamai ido ganin yana neman haurawa sama ne yasa Basma ta ɗaga murya tana faɗin "Daddy...." Juyowa yayi cike da wani fushi yana kallonta baya taja ganin yadda fuskarsa ta chanza cikin rawar murya tace "Am Sorry Daddy...I didn't mean to hurt u..." Ta faɗa kamar zatayi kuka Mufeeda ma dake gefe yanayin Tahir ɗin yasakata sanyin jiki balle Bassam dayayi tsam a saman kujera yana bin Daddynsu da kallo a tsume.


Ganin yadda duk sukayi ne yasa tausayinsu ya kamashi sai ya ƙaƙalo murmushin dole yana faɗin "It's Ok, don't worry kuyi taking dinner ɗinku me am ok, na biya wajen Ishaq naci abinci ok..?" A sanyaye Basma ta ɗaga kai kafin tace "What abount Momy...?" Atsume ya kalleta kafin ya bi ƙofar bedroom ɗin Faridan da kallo daga inda yake yana jiyo sautin dariyarta da alamu waya take bai  bama takaichinsa muhimmanci ba yace akausashe "Basma kuje kuci abincinku ku shiga ciki ku kwanta u know tomorrow akwai school ko..?" Gyaɗa kai tayi kafin yace "Oya bana son wata magana kuma, ita Momyntaku ai ta fiku sanin cikinta in tana buƙata zata fito taci, saboda haka kuci abincinku kowannenku ya tafi ɗakinsa ya kwanta and don't forget kowannenku yayi Assigment ɗinsa Basma Bassam Mufeeda am i clear..?" Ya faɗa cikin bada umarni.


Gaba ɗayansu suka amsa da yes Daddy, gyaɗa kai yayi kafin ya juya ya ƙarashe hayewa steps d'in ko kallon ɗakin Farida baiyi ba ya tura ƙofar ɗakinshi ya shiga yana sakin siririyar ajiyar zuciya yana ƙoƙarin danne fushinsa yana ƙara tunanin wani irin raini Farida tamai da zata fi kwana biyar bata gida kuma ta dawo gidan bayanan, bayan ya dawo kuma ta kasa fitowa ko sannu da zuwa tamai alhalin yasan ta ji dawowarshi? Tsaki yaja yana ƙoƙarin zama gefen gadonshi lokaci ɗaya zuciyarsa na zafi duk da haƙurinsa wannan karon Farida ta ƙureshi, bai ƙara ƙoƙarin saka ɓacin ranta a cikin ranshi ba ya cire jallabiyar jikinsa ya haye gadonsa daga shi sai dogon wando baƙi duka zatinsa da kwantaccen baƙin gashin ƙirjinsa ya bayyana ƙaramin Qur'aninsa ya ɗauka ya buɗe ya fara karantawa cikin natsuwa lokaci ɗaya ya nemi ɓacin ran Farida ya rasa duk ya gushe acikin ranshi, a hankali ya cigaba da karatunsa cikin jin daɗi da shaukin abun.


Suko su Bassam duk da zuciyarsu ba daɗi da yanayin halayen Momynsu da Daddynsu hakan bai hanasu zama suci abinci ba hatta Mufeedan itama jikinta yayi sanyi, su Basma kuwa ba Momynsu tafi damunsu ba a'a  Daddynsu wanda sun lura indai Farida na gidan bashi da walwala koda yaushe cikin ɓata mishi rai take, kuma abunda yaran suka lura dashi yadda uwar tasu bata damu da rayuwarsu ba hakama bata damu dana Daddynsu ba, abun baya musu daɗi domin sun fi shaƙuwa dashi sosai akanta, shine yake zama dasu ya kuma jasu ajikinshi yaji damuwarsu kuma shine ginshiƙin tarbiyarsu shiyasa in suka ganshi cikin damuwa suke shiga damuwa shiyasa wani lokacin sunfi sakewa in Farida bata gidan haka dai kowa ya tsakuri abincin ya tashi yau Iyar ma datake jansu da hiran ban dariya tunda ta fara taga sunƙi sakin fuska sai ta ƙyalesu Bassam ne ya fara tashi sai Basma dukkansu ba wanda suka ma magana kowanne ya nufi ɗakinsa domin cika umarnin mahaifinsu. Mufeeda bata ci abincin sosai ba itama ta tashi Iya bata damu ba domin indai yanayin gidan Tahir ne ya riga ya zame ma kowa jiki, yau daɗi gobe akasin haka, itama tattara komai tayi zuwa kichen kafin ta shige ɗakinta, hakama Mufeeda ta shige ɗakinta ta kulle wanka tayi kafin ta saka kayan barcinta ta kwanta kusa da Naila bayan ta cika umarnin Tahir tayi Assigiment ɗinta ta rungume Naila a ranta tana tausayin Tahir tana kuma ganin Farida a muguwa tana muzguna ma mutum mai haƙuri da kawaichi kamar Tahir, wani lokacin kamar tamai ƙwalla takeji domin tun zuwanta gidan ta fahimci Tahir da Farida are different sam basu dace da juna ba, akwai abunda Allah ya tsara ne a tsakaninsu amma zamansu waje ɗaya kwata kwata baiyi ba.


*****


Washegari ƙarfe 7 da wani abu Tahir ya fito daga ɗakinshi cikin shirin fita yau ɗin shigar manyan kaya yayi saboda juma'a ce, wata farar Gezner ce mai maiƙo da yarari ajikinsa ɗinkin matasa ne da samari masu jin kansu wato ɗinkin Muhammed, kansa sanye da hula Zanna Bukar mai kalar blue irin aikin jikin shaddar sai agogon fatar dake hannunsa na kamfanin Rado ne, ƙafarsa sanye da buɗaɗɗen takalmi na fatar damisa.


A kallon farko in kamai zaka fahimci tsantsar zatinsa da haibarsa uwa uba kyau da nasaba ga ƙwarjini, fuskarsa na fitar da annuri amma kuma zuciyarsa tana ɓoye ɓacin ransa daidai lokacin daya fito yana ƙoƙarin gyara zaman hulan kansa sai ga Farida itama ta fito daga cikin bedroom ɗinta suka kusa bangazan juna shi yana sauri ya sauka ƙasa zashi Office suna da baƙi daga Lagos ita kuma ta fito sanye da wata doguwar riga ƙirar Armani baƙa sai wani jan vail data naɗa akanta hankalinta na kan wayarta amma kuma ƙamshin turaranshi shiya sanar da ita Tahir is here.


Cak ta tsaya tana binshi da kallo, shima kallonta yayi amma kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai lokaci ɗaya yana ƙara haɗe ransa itama sai ta kauda kai tana wani basarwa saboda kada ya kawo mata wata mgana cikin dakewa ta furta "Good morning Abban Basma.." Kamar bazai yi magana ba sai da ya raɓata ya fara saukowa daga steps kafin ya amsa da cewa "Morning..." Daga haka bai ƙara mata magana ba ya sauko falo da hanzari inda Mufeeda da Basma da Bassam ke zaune kowanne da uniform ajikinsa suna karyawa, suna ganinshi dukkansu suka miƙe suna faɗin "Good morning Daddy..." Yana sakin murmushi ya ƙaraso yana dafa kan Basma da Bassam harda Mufeedan kafin yace "Morning how are u...?" A tare suka amsa da "We are fine Daddy.."


Fuskarsa na kallon Mufeeda yace "Mufee ya kwanan Naila..?" Tana wasa da gefen hijabinta tace "Ta koma barci Daddy tana tare da Iya.." Gyaɗa kai yayi daidai lokacin da Farida ta ƙaraso falon shi kuma ya juya yana faɗin "Bassam hau sama ka ɗaukomin briefcase ɗina, idan kun shirya kuzo mu ajiyeku kafin mu wuce in kuma yaje ya kaini ne ya dawo toh.." Da sauri Bassam ya miƙe yana faɗin "No Daddy zamu bika.." Ya faɗa yana isa gaban Farida kafin ya ranƙwafa yana gaisheta ta amsa tana shafa kanshi kafin ya nufi upstairs da sauri hakama Basma ta taso ta rungume Farida tana gaisheta Mufeeda dai sai da ta koma ɗaki ta ɗauko ƙatuwar jakarta ta fito kana ta durƙusa tana gaida Farida ta amsa ba yabo ba fallasa Tahir na gefe hannunsa na harɗe kan ƙirjinsa yana kallonta cike da mamaki tana ɗagowa suka haɗa ido sai ta wani ƙara haɗe rai kafin ta koma kan ɗaya daga cikin kujerun falon ta zauna tana wani tamke fuska.


Takaichinta yasa ya fice daga falon har yana jan siririn tsaki da kallo ta bishi kafin tace a fili.. "Fitinanne, nema na kake da fitinarka niko bazan biye maka ba.." Tsaki taja daidai lokacin dasu Bassam ya ƙaraso ɗakinsa ya koma shima ya ɗauko jakarsa suka fito Basma ta rigasu ficewa kafin Mufeeda da Bassam su fice suna ma Faridan sallama ko ɗaga kai batayi ba hannu kawai ta daga musu.


Sai da aka fara kaisu Basma School ɗinsu kafin akai Mufeeda har suka ajiyeta tana satan kallon Tahir tausayinshi na ratsata domin agabanta Farida ta faɗi maganar ɗazu ranta bai mata daɗi ba duk da ƙarancin shekarunta tasan hakan bai dace ba, ranar dukuku ta isa ajinsu duk zuciyarta da ranta ba daɗi Tahir ke cikin ranta tana matuƙar tausayama rayuwar mutum mai nagarta da kamala kamarshi.







*Aisha Alto*

*Anitha..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


*Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto*


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


*BISMILLAHIR RAHAMIR RAHIM*


       *BABI NA SHIDDA*


......Har ya isa Office fuskarshi ba annuri, har suka gama sallamar baƙinsu waɗanda abokan harkarsu ne daga Lagos, office d'in Ishaq suka wuce suna cigaba da tattauna abunda ya shafi kasuwancinsu, suna shiga Tahir ya nufi ɗan ƙaramin fridge d'in dake Office d'in ya buɗe ya ɗauko musu ruwa guda ɗaya bayan ya ɗauko wasu ƙananan kofuna guda biyu kai tsaye bisa kujeran dake fuskartar wacce Ishaq ya zauna shima ya zauna ya ajiye kofunan bisa teburin dake gabansa batare da yace komai ba ya tsiyayama Ishaq ya miƙa mai ya karɓa da murmushi kafin yace "Thanks."


Bai yi magana ba illah murmusawa kawai da yayi kafin shima ya tsiyayama kanshi ya kafa kai yana sha, dukkansu atare ko wannen su ya ajiye kofin ruwan kuma suka sakarma juna murmushi alokaci ɗaya, ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana wani lumshe ido kansa ya jingina jikin kujera yana ƙara takure fuska kafin ya sanya hannu yana taɓa naman goshinsa daya tattare, Ishaq na lura dashi ganin yadda yake yamutsa fuskane yasa ya gane akwai matsala sosai.


Gyara zama yayi kafin yace "Uhm..Tahir meke damunka ne..? Tun shigowarka Company na lura baka cikin walwalarka..?" Bai ɗago ba illah sauke hannunshi dayayi yana ƙara lumshe dara daran idanuwansa har Ishaq ya fidda rai da zai yi magana sai chan yaji ya furta.."Kai ma da neman magana kake, a duk duniya ni Tahir ina da wata damuwa ne bayan damuwar Farida..? Bani da ita komai na duniyar nan na mallakeshi Ishaq sa'ar mace tagari ne kaɗai banyi ba, shi kaɗai ne matsalata a yanzu da damuwata Ishaq..wallahi halin Farida ya isheni, na kai maƙura..."


Ishaq ya saki ajiyar zuciya kafin yace "Nasani Tahir buh ya maganar da mukayi dakai last week da kaje Ɗanbatta baka ƙara ma Goggo Abu maganar auren naka bane..?" Sai lokacin Tahir ya miƙe daga kishingiɗan dayayi yana faɗin "Hmmm bari kawai Ishaq, narasa me Farida tama Goggo Abu da take gudun ɓacin ranta, amma ni take ƙoƙarin danne min hakki wallahi ko wannan zuwan taƙi kuma tace zata saɓamin in na sake na tunkari Hakimi da maganar, wai zata ƙara ma Farida magana in sunyi waya.." Tsaki Ishaq yaja kafin yace "Wallahi baji zatayi ba, ai da tana jin magana dataji tasu Alhaji, gaskiya in na samu lokaci zanje ƙauye nama Goggon bayanin za'a cutar dakai kuma Farida bata da asara." Murmushin dayafi kuka ciwo Tahir yayi kafin yace "Kadama ka wahalar da kanka Ishaq, domin Goggo bazata taɓa sauraranka ba daga ƙarshema zatace haɗa baki mukayi na turo mata kai. Kawai nidai yanzu na cire lamarin Farida araina ina ta addu'a amma tabbas Ishaq na kai maƙura nifa mutum ne mai lafiya ba dutse ba ina buƙatar macen da zan dinga samun natsuwa awajenta.." Saurarawa yayi yana maida numfashi cike da ɓacin rai kafin ya cigaba da faɗin "Ko bama haka ba Ishaq ina buƙatar macen da zata kula dani nima, taji dani nima ina so naga ana bani girma amatsayina na namiji, yanzu ka duba kagani Ishaq rainin da Farida tamin har yakai ta tafi tsawon kwana biyar bata agida, amma jiya data dawo basai ta nemeni ba..? Toh sai ma kallon rainin data bini dashi da ƙyar ta iya cemin ina kwana, fisabillahi wannan wace irin rayuwa ce? Duk haƙurinka sai an ƙureka.." Ya faɗa yana dafe kanshi. Ishaq dake kallonsa cike da tausayinshi tsam ya miƙe ya zagayo gabanshi yasaka hannu ya dafa kafaɗarsa yana faɗin "Is Ok...Ya isa haka Tahir maganar duk bashi da amafani tunda ba ji zatayi ba, ni narasa wane irin taurin kai ne Farida ke dashi ko Aliya fa tayi tayi da ita amma ƙarshenta ma yanzu sama sama take mata magana bazata chanza ba, haƙuri zaka ƙara da kuma tausan Goggo Abu har ta amince maka ka sanar da Hakimi kana buƙatar ƙara aure..."


Tahir baiyi magana ba illah sauke ƙananun ajiyar zuciya dayakeyi kafin ya miƙe yana sauke jannun Ishaq dake kafaɗars bai bari sun haɗa ido ba sai ma ƙoƙarin duba agogon hannunshi da yayi lokaci ɗaya yana faɗin "Ishaq zamu makara fa, muyi alwala mu isa masallaci.." Ya faɗa yana kama hanyar ficewa, ajiyar zuciya Ishaq ya sauke kafin yace "Ok..." Daidai lokacin da Tahir ya fice daga Office d'in shima bai zauna ba wayarsa ya ɗauka ya tura cikin aljihu yabi bayan Tahir ɗin da sassarfa.


Farida ko tun bayan fitansu take zaune a falo tana latse latsen waya, sai da ta gaji taga dama kana ta tashi ta nufi dining tayi breakfast ta gama kenan sai ga iya ta fito ɗauke da Naila wacce ta tashi daga barci Iya tayi mata wanka ta saka mata wata riga doguwa bulawus mai kyau rigima takeji don yau ko madarar nata data dama mata bata sha ba, shine ta fito da ita zuwa wajen Farida karɓan ta tayi ta cilla ta sama alamar wasa duk yadda Naila keson wasa yau bata nuna ba don kuka ta saka mata tana binta da kallo, Farida ta kyaɓe fuska tana faɗin "Meya sameta ne Iya..? Baki bata madararta bane..?"


Iya tace "Na bata ta ƙi karɓa Hajiya gwada bata nono ƙila shi takema kewa.." Dariya Farida tayi tana shafa kumatun Naila tace "Wannan babbar yarinyar? Ai tayi girma da shan nono, kinga ina ɗaukanta ina haki shiyasa nake jinjina ma Mufeeda don tana ƙoƙarin ɗaukan Naila, tunda naga tafi sabawa da madararta na yayeta domin bazan iya ma tuna rabon da na bata nono ba gaskiya.."


Iya tayi galala da baki kafin tace "Haba Hajiya Naila fa yarinyace ƙarama har yanzu ko shekara bata rufe ba fa.? Gaskiya bai kyautu ki yayeta tun yanzu ba, don Allah ki barta ko wata sha takwas tayi in bazaki barta ta cike biyu ba..." Tun kafin Iya ta ƙarasa Farida ke jifanta da wani banzan kallo batayi magana ba sai da ta miƙe ta miƙama Iya Naila kafin ta ɗauki wayarta tana fadin "Iya ki kama bakinki, ina ruwanki da hukuncin dana yanke? Ai nima nasan ciwon kaina ko..? So plz ki tsaya iya matsayinki bana so kina shiga hurumin da banaki ba.."


Iya ta rausayar da kai tana ƙara riƙe Naila dake rigima tace "Allah ya baki haƙuri Hajiya.." Bata bi ta kanta ba ta haura sama ta amsa kira, da kallon kaiconki Iya ta bita kafin ta kaɗa kai ta koma ɗakin Mufeeda da Naila da ƙyar ta lallasheta ta sha madararta kuma ma harda rigimar bata ga Mufeeda ba goyata tayi kafin ta fito falo ta fara tsabataceshi, bata gama ba Naila tayi barci sai ta maidata ɗaki ta kwantar ita kuma tazo ta cigaba da aikinta lokaci bayan lokaci tana leƙa Naila acikin ranta kuma tana fatan Allah ya kawoma Alhaji mafita amma tabbas baiyi dacen abokiyar arziki ta gari ba duk da ba Alhaji ya kawota gidan ba amma kuma kyawawan halayyarshi da kyautatarwarshi garesu yasa take ganin girmanshi da darajanshi kuma take zaune dasu da zuciya ɗaya.


******


*BAYAN KWANA UKU*


Duk tsawon wannan kwanakin zaman doya da manja ke gudana tsakanin ma'auratan, shi Tahir ya riga daya fita sha'anin Farida sam domin yana ganin yana gaba da ita amma baida daraja da arzikin da Farida zata nemeshi, shiyasa yayi burus da ita dagashi sai 'ya'yanshi suke harkar rayuwarsu ko alama bai sakama ranshi yana da wata mata agidan, toh itama Farida bata damu dashi ba, hakan da yayi ma yayi mata daɗi domin batason fitinar Tahir sam gani take da zarar ta nemeshi fitinarshi zata tashi shiyasa ta shareshi a zuwan in ya gaji zai nemeta lokacin ya huce sai su daidaita.

  

Kwana biyu ne da dawowarta bata fita ba saboda gajiyar dake jikinta, ranar data kwana uku bata wuni a gida ba, baima san ta fita ba, sai da ya dawo gidan wajen 6 na yamma Iya ke sanar dashi Farida bata gida ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi amma na yau kam Farida takaishi bango sosai. Garzali yaje ɗauko su Basma daga Islamiya sama ya haura ɗauke da Naila wacce ya amsheta hannu Iya har ya shiga wanka ya fito zuciyarsa tafasa take, koda ya fito Naila tayi barci dama ita rigimarta kaɗan ce dan dataji taushi da iska sai barci yana ƙoƙarin zura jallabiyarsa ne yaji ƙarar buɗe gate alamun Garzali ya dawo daga ɗauko su Mufeeda, carbinsa ya ɗauka ya fito kansa na ɗigar da ruwa kaɗan, dasu ya cikaro duk suka gaisheshi ya amsa fuskarsa ba walwala kafin ya kalli Bassam yana faɗin "Oya shiga ka fito mu tafi Masjid.." Kada kai yayi kafin ya shiga ɗakinsa agurguje Bassam ya ɗauro alwala ya fito Tahir ya kama hannunshi suka fice zuwa masallacin dake kusa dasu yayinda Mufeeda da Basma kowacce tayi ɗakinta domin ɗaura alwala tunda wasu masallatan ma sun riga sun tada Sallarsu.


A ƙa'idar Tahir baya baro masallaci sai an idar da sallar Isha'i yau ma ɗin hakane ta kasance riƙe da hannun Bassam kamar koda yaushe suka shigo gidan megadi na musu barka da zuwa basu kai ga isa ƙofar da zata sadasu da babban falon gidan ba horn d'in motar Farida yayi musu maraba da hanzari megadi ya wangale mata gate ta sako hancin motarta cikin gidan, cak Tahir ya tsaya ya waigo yana kallonta tana ƙoƙarin faka motar a parking spaces, ta cikin motar itama take kallonsa ganin yadda yake mata wani kallo ne yasa tasha jinin jikinta sosai tana ƙoƙarin fitowa daga motar ne nepa suka ɗauke wuta wajen yayi duhu shi ya taimaketa don Tahir hannun Bassam yasaki yace mai ya shiga cikin gida shi kuma ya nufi wajen Garzali yana sanar dashi ya duba Genaretor ɗin Allah yasa akwai diseal, lokacin ne Farida ta samu sa'a tayi wuf ta fada cikin falon, yana ganin haka shima ya juya ya take mata baya tana ƙoƙarin haura steps d'in benen ne taji kakkausar muryanshi yana faɗin 


  


  "Da zinin wa kika fita Farida....?" Muryansa cike da amon sauti mai cike da tsantsar ɓacin rai, rass gabanta ya faɗi sai ta kasa juyowa don muryansa kaɗai ta isa ta bayyana mata yau Tahir ya gama haƙuri da ita, bata samu zarafin juyowa ba ya sake daka mata wata uwar tsawar data gigita ta, bama ita kaɗai ba hatta su Basma da Bassam da Mufeeda da Iya dake ɗakunansu sai da suka firgita suka fito falon da sauri daidai lokacin da aka kunna Genaretor haske ya gauaraye ko'ina.


"Nace da izinin wa kika fita Farida...? Saboda raini kina jina ina magana kina min banza..?" Ya faɗa yana tattare naman goshinsa saboda fushi, Farida ta juyo a hankali tana kallonshi tana kuma ƙoƙarin ɓoye razanarta haɗe fuska tayi kafin tace "Dama na saba tambayar izininka ne idan zan fita...? Na ɗauka nida kai mun wuce wannan ƙarnin..." Ta faɗa tana kaɗa key ɗin motar dake hannunta ba tare data jira komai ba ta kaɗa kai ta juya ta cigaba da taka steps d'in cikin halin ko in kula wani ɓacin rai mai zafi ya ziyarci zuciyar Tahir ko gani bayayi yayi kukan kura ya bi bayanta a harzuƙe kafin ma ta ankara ya cimmata sai ji tayi ya jawota baya da sauri ƙiiiiii.....kamar wata kayan wanki, bai direta ko'ina ba sai tsakiyar falon bayan ya ingizata baya tayi taga taga zata faɗi, ba domin Allah ya taimaketa ta daddage ta riƙe kujeran dake falon ba da sai ta faɗi ƙasa..


Cike da mamaki take binsa da kallo kafin ta buɗe baki tace "Tahir...Lafiyanka ƙalau kuwa..? Ta faɗa tana binsa da kallo ganin yanda yake huci bai bata amsa ba illah cewar daya ƙarayi "Nace da izinin ubanwa kika fita Farida...?" Baki buɗe take kallonshi kamar yadda Basma da Bassam suka zura musu ido, cike da wani yanayi hakama Mufeeda, Iya ce dake tsaye ranta duk ba daɗi tunda suke da Alhaji basu taɓa ganinshi cikin fushi hakaba tana ƙoƙarin isa gareshi Farida tace "Kace da izinin ubanwa na fita ko..? Toh da izinin ubana ko..." Ai bata ƙarasa ba taji Tas! Tas! Maruka biyu kyawawa Tahir ya wanke fuskar Farida dama da hauni lokaci ɗaya, kamar walƙiya taji marukan saboda azaba sai gata zaune daɓas da ɗuwawunta akasan cafet ɗin falon hannayenta dafe da kuncinta tana bin Tahir da kallo hawayenta na sauka kamar an buɗe famfo.


Ba Farida kaɗai ba hatta Basma da Bassam saboda razana sai da ya ƙanƙame Basma suna rawar jiki a tare lokaci ɗaya suka fashe da kuka, hakama Mufeeda da ta maƙale jikin ƙofa tana rawar jiki, Iya ko ƙirji ta dafe tana faɗin "Innalillahi Wa'inna Ilaihirraju'un...Alhaji mezan gani jaka..? Ashsha abu baiyi daɗi ba.." Ta fada cike da damuwa.


Ko sauraranta baiyi ba ya kalli Farida yana nuna ta da yatsa kafin ya fara faɗin "Wannan ne na farko kuma na ƙarshe... wallahi in kika ƙara fita bada izina na ba Farida daga ranar zaki tabbatar da babu wani amfanin da kike dashi a cikin rayuwar Tahir..." Ya faɗa cikin kakkausar murya, kuka Farida ta fashe dashi bilhaƙƙi da gaskiya kafin ta miƙe cikin kuka tana faɗin "And So What...Nima ai baka da wani amfani a wajena, waye kai awajen Farida? Ka sakeni in ka isa tunda bani da amfani juz Tahir ka sakeni ka gani in rayuwata zata yanke ko ta wulaƙanta daga yau ka sakeni don Allah..." Ta faɗa tana hargowa cikin kuka.


Basma ce ta saki ihu tana faɗin "No..Momy Daddy Stop plz..." Ta faɗa tana duƙawa haka shima Bassam yayi suna kuka suna faɗin "Plz Daddy Momy don Allah ku bari kuna sakamu muna jin ba daɗi..." Suna faɗa suna kuka, Mufeeda ma kukan take, da kallo Tahir ya bisu lokaci ɗaya kuma sai jikinsa yayi sanyi sosai idanuwansa sunyi jawur kai kawai ya kaɗa kafin ya wucesu da sauri ya haura sama cikin sassarfa, ganin haka yasa Farida tabi bayanshi da sauri tana kuka sai dai kafin ta ƙarasa ya shige bedroom ɗinsa ya banko ƙofa a ƙofar ɗakin ta tsaya tana kuka tana faɗin "In ya isa ya fito ya saketa dama ita tagaji da aurensa..." yana jinta ya mata banza kan gadonsa ya hau ya saka kanshi cikin gwiwoyinsa yana ƙoƙarin daidaita numfashinsa.


Basma da Bassam ko kuka suke sosai na ganin abunda ke faruwa tsakanin iyayensu wanda basu taɓa gani ba da ƙyar Iya ta lallashesu kowanne ya nufi ɗakinsa cikin damuwa, haka ma Mufeeda ta koma ɗakinta ta faɗa bisa gado tana kuka, wanda tarasa dalilinshi, ranar dai gaba ɗaya gidan ba wanda ya yi dinner haka kuma barci sai dai sama sama, daga Tahir ɗin har Farida barci ɓarawo ne ya ɗaukesu balle su Basma da suka tashi fuskokinsu duk a kumbure saboda kuka. 






*Janafty..*

*Aisha Alto.*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


_Don't Forget to Vote us on Wattpad:Janafnancy13 or Aisha Alto alto_



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


*BISMILLAHIR RAHAMIR RAHIM*


       *BABI NA BAKWAI*


....Duk da yaran Sun Tashi Zuciyarsu ba Dadi bai Hanasu Shirin Tafiya mkaaranta ba,Suna bisa Dinning Suna Breafsat,Kowa ka gani Fuska ba Walwala Don Daga Tahir din Har Faridan ba Wanda Sukaji Motsinsa Har Gwarashi yazo da Asuba ya Tashi Bassam sun Tafi masallaci.


Batare da Sun saka iyayen nasu a ido ba garzali ya Kwashesu Zuwa Mkranta Naila Kuma dama Wajen Tahir Ta Kwana,Sun Fita ba Dadewa Farida ta fito Daga Cikin Bedroom Dinta Dauke da karamar Trolly dinta Fuskarta ta Kumbura Idanuwanta Sun Chanza kala Saboda Kuka Tana Sanye da Riga da Sikat na Wata Atamfa Holland,Daurin Dankwalin dai gashi ga kamarshi,sai karamin Gyale Vail Data Yafo Bisa kafadarta,karamar Jakarta na Hannunta Hade da Wayarta sai Key din motarta Dake Hannunta.


    Ahaka ta Sauko Har Zuwa Main Falo din Tana Tafiya tana Share Hanci da Iya taci karo Wacce Tafito Daga Kichen,cikin mamaki Take kallonta kafin Tace"Hajiya lafiya Kuwa..? Wata Uwar Harara Ta maka mata kafin Ta Saki Tsaki takama Hanyar Fita Daga Falon,iya bata Dandara ba Tace"Haba Hajiya gaskiya Wannnan ba girmanki bane,Ina Zaki Tafi ki bar mijinki da ya"yanki Kefa ba yarinya bace Yaji bai kamace ki ba,kin kai Munzalin Da Zaki ma Wata Fada bama Kanki ba..."Tafada Cikin Nuna Alamun Abun bai mata Dadi ba.


Juyowa Farida Tayi Afusace kafin Tace"Wlh iya sai na Tafi nagaji da Irin Tozartanin Da Tahir yake yi nagaji..!kina gani Jiya gabanku gaban ya"yana Ya Tsinkeni da maruka har biyu Saboda ga baiwarsa ko,Allah sai na Tafi Sai ya Zauna Shi kadai.."Tafada Tana Sharbe Kwallah kamar Wata yarinya.


Iya tayi kasake kafin Tace"Hakuri Ake Hajiya,Kowa fa kikagani yana Zama lafiya agidan Mijinshi karki Tambayeshi Hakuri,Kema Kiyi Hakuri Don Allah In kika Tafi Gida Kicema su Umma Mene Don Allah.."?Tana Sharan Ido Tace"Ai ba Kano Zani ba Danbatta zani Wajen Goggo Abu taga Shaidan Yatsun Tahir Akan Fuskata..."Tafada Tana juyawa da Sauri Ta Fice Daga Falon Tana kara Rike zaman karamin Akwatin Dake Hannunta Iya Dake Tsaye ta Yunkura Zata Bita sai Taji Muryan Tahir Daga Sama yana Fadin"kyaleta iya..."yafada Cikin Halin ko Inkula 


Iya ta Waigo Jiki asanyaye kafin Ta Rusuna Tana gaisheshi,Shiko yana Daga saman Benen ya amsa mata Fuskarsa na Nuna Alamun baida Damuwa yana Sanye da Amarican Suit,Ash colour,Yar jakar Briefcase dinsa ne Ahannunshi da alamun Fita Zaiyi Tana Kokarin Barin Falon ya Karisa Saukowa yana Fadin"Naila tana Room Dina iya Ta Koma barci plz ki Haura ki Daukota Ta Zauna Kusa dake.."Ya Fada yanq Nufar hanyar da Zai Sadashi da Haraban Gidan Lokaci Daya yana kallon Agogon Fatan Dake Hannunshi.


Iya tabi bayanshi da kallon Tsausayi kafin Tace"Insha Allahu Adawo lafiya Alhaji.."Bai Jita ba Don ya Riga yaFita Daidai Lokacin Kuma Garzali ya Sawo kan Motar Cikin gidan ya Dawo Daga kai Su Basma mkranta batare da bata Lokaci ba ya Shiga ya Juya Dashi Zuwa Office don Ya Makara gashi Kuma Meeting garesu Suna Tafe yana kallon Agogon Dake Tsitsiyan Hanmunshi kafin Wayarsa kirar iphone 11 promo,tadauki Tsuwa Sunan Ishaq ya Fito baro baro Afuskar Wayar Dauka yayi Da Hanzari suka gaisa kafin Su Cigaba da mgana Cikin Kulawa da Tsantsan Ilimi.


********


*D'ANBATTA*


Goggo Abu Sai Dai Taga Farida Kwatsam Tazo Tana Mata Kuka Wiwi kamar Wacce Aka yanka Ko Akace Uwarta ta Mutu Lokacin Data Iso Ashe na gidan,nan Goggo Abu Ta Rude Ta Shiga Tambayanta Abun ya Faru,Farida na Kuka tana Zayyanama Goggo Wai Tahir ya mareta Har guda hudu Dukkanta ma yaso yi sai da iya mai aikinsu Ta Shiga Tsakani Farida na Kuka Tanama Goggo Abu Rantsen Rantsen Cewa Tahir yace ma bata da Wani Amfani Acikin Rayuwarshi.


Ran goggo Abu ya baci Ta Dinga Sauke Numfashi Takaichi Attahiru na Damunta Ashe ce Tace"goggo Kada ki yanke Hukunci Cikin Fushi yakamata Shima yayan Ki kirashi ki Fara jin Ta Bakinshi Tukunah.."Tafada Da Sigar Lallashi,Cikin Kuluwa Farida Ta Dago Tana Hararan Ashe kafin tace"Eh mana Akirashi mana ai ba karya namai ba Jiya agaban ya'yana Da yan Aiki ya Tozartani nidai kam goggo Ki kirashi na Gama zama da Tahir kamar yadda yace banda Wani Amfani Acikin Rayuwarshi Nima Tahir baida Amfani Awajena ya"yana yaje ya Rike na barmai Dama badasu nazo ba..."Tafada Tana Shesshekan Kuka Lokaci Daya Tana Hararan Ashe din Domin Dama Jininsu baizo Daya Saboda yadda Tahir yake matukar ji da Ashe Ita Kuma Duk Abunda ya Shafi Dan"uwanta bata Wasa Dashi.


Ashe bata mata mgana ba illah kallon Goggo Abu Datakeyi kafin Tace"Kinji goggo Don Allah Kifara Kiranshi Tukunnah.."Jin Haka yasa goggo Ta Mike Ta Shiga Ciki Ta bar Ashe da Farida Anan Cikin Falonta Kowa na kallon Kowa Cike da Takaichi Mikewa Ashe tayi ta Fice Zuwa Shashen Innaro Tana Fadin"Allah ya kawo maka mafita Dan"uwana..."Tafada Cike da Habaici da Kuluwa,Da Ido Farida Ta Bita kafin Ta Rakata da Tsaki Tana Share Kwallah.


Fitowarsu kenan Daga Meeting yana Hanyar Komawa Office ya Fito da Wayarshi Wacce Tun Shigansu meeting din ya sakata A Silent Hankalinsa ne ya Tashi Ganin Misseds Rututu Na goggo Abu gabansa sai dai ya Fadi yana Bude Kofar Office din ya Na Kokarin Kiranta gabda zata Katse Ta Dauka yana Kokarin gaisheta ta katseshi A Fusace Tana Fadin"Dagata min Attahiru Nagode da Abunda Kamin in Har na Isa dakai kazo gida yanzu ka sameni mutumin banza kawai..."Tafada Cikin Fushi kafin ta yanke Kiran,Dafe kai yayi yana salallami,Domin yasan Cewa Farida Tagama Hadama goggo Abu Famfo shi bama Wannan ya Dameshi ba Irin yadda Ta Dau Zafi Dashi Allah ne kadai Zai Kwaceshi.


   Office din Ishaq ya Tafi Agurguje Sukayi mgana Sama sama Kafin Suyi sallama ya Fito bai Tsaya bata Lokaci ba yace ma garzali Su kama Hanyar Danbatta sai da Sukayi Nisa ne Garzali ke Tunamai dasu basma Ba Wanda Zai Daukosu Daga Sch,Dafe kai yayi yana Salati kafin ya Dauki Wayanshi Shugaban mkrantan Su Basma ya Fara Kira inda yabada Umarnin Indan Antashi Daga Mkranta Basma da Bassam Su bi Sch Bus Su Dawo gida Saboda Dukkansu basunan bamai Zuwa ya Daukesu,Daganan sai Shugaban Mkrantar su Mufeeda Itama Abunda yace Kenan Kafin ya Katse Kiran,yana Sakin Numfashi kadan yasan yau sai sunyi Rashin Islamiya Saboda baita yarda Sun Fita Waje Su kadai ba Duk inda Zasu sai dai garzali ya kaisu Kuma yana Da Tabbatacin Tunda Sukaga babu mai Kaisu bazasuyi gangancin Fita ba.


Wajen 2pm suka iso Kofar gidan Hakimi,Shikanshi Hakimi da Jama"arsa Sunyi mamakin ganinshi don Akasari bai Cika Zuwa Cikin Sati ba Sai karshen Sati,Hakimi bai yi mamaki Sosai ba Saboda yaga Zuwan Farida Hartazo ta gaisheshi Yaga Fuskarta ta Chanza kamar tayi Kuka Daya Tambayeta sai tace bakomai tatashi Ta Shiga To Tunda yaga Zuwan Tahir sai yasha Jinin Jikinsa Ammh Dayake yana da Miskilanci sai bai Nunama Tahir din Komai ba Wanda Sai da yagama gaisawa da Jama"ar Wajen kafin ya Karisa garesa yana Kwasan gaisuwa,bayan Tambayi Aiki da yara,bai Zauna ba ya Mike yacemai Zai Shiga Cikin gida,Hakimi yayi Mirmishin su na manya kafin ya kalli Tahir din yana Fadin"Attahiru yau kazama Mara Hakuri ko...? Akullum ina maka Nasihan ka Rika kai Zuciyarka Nesa Domin Akasari mata akarkarce suke Kana Kokarin Daidatasu Suna kara famdarewa ne,Toh Dole sai munyi Hakuri Dasu kaji...?"Yafada kasa kasa Wanda Inba Tahir din ba Wanda yakejin meyake Fada,Sadda kanshi yayi kasa yana Fadin"Naji Hakimi Insha Allahu Zan Kiyaye.."Kai ya gyada kafin yace"Tashi ka Shiga Ciki Allah yayi maka albarka.."Da Ameen ya amsa kafin ya Wuce Zuwa Cikin Gidan...


Sheshen Innaro ya Wuce Direct nan Suka Ci karo da Inna Fulera ta Zube Tana gaisheshi ya amsa Cikin  sakin Fuska Kafin ya Wuce Zuwa Babban Falon Innaro Dake Shashenta,Nan ya iske Innaro da Ashe Suna Hira,Ashe Dataji Dadin ganin Dan"uwanta sai da tatashi ta Fada Jikinsa Tanamai Oyoyo Riketa yayi yana Dariya Lokaci Daya yana Shafa Kanta,Tare Suka Zauna gaban Innaro,Tahir yafara gaisheta ta amsa Cikin Sakin Fuska da Fara"a Tana Tambayanshi su Basma ya amsa da Suna Mkranta,Yadade Awajenta Suna gaiswa da Hira kafin ya barota Zuwa Shashen Goggo Abu Ashe bata biyoshi ba Saboda tasan Goggo Abu Korarta Zatayi.


Lokacin Daya Sawo kanshi Falon goggo Abu Da sallama Abakinshi da Farida yaci karo Tayi Rashe Rashe Atsakiyar Falon Tana Shan Fura,Suka Hada Ido,Daure Fuska yayi kamar bai Taba Dariya ba yana karisowa Cikin Falon Goggo Abu Tana Fitowa Daga Uwar Dakinta Suka Ci karo,Takalmin kafarsa yacire kafin ya Zauna yana gaishe da goggo Abu Wacce Ke Dankaramai Harara kafin Tace"Tashi Tsaye bana Bukatar gaisuwaarka Attahiru,domin ka gama Nunamin Iyakata..."Tafada Cikin Kakkausan Murya.


Kasa yayi Dakai yana Jin Wani Daci Acikin Ransa,Dagowa yayi yana Kallon Farida Wacce Ke kallonshi gabanta ne yafadi ganin Irin Kallon Dayake Jifanta Dashi bai iya mgana baa,sai ma Sauraran Goggo Abu Dayayi Tayi Ta Inda Take Shiga batanan Take Fita ba Sai da Tagama Wanke shi Tas Kamar Zata Dakeshi Ta Koma Gefe Tana Haki,sai da yaga Ta gama kana ya Dago yana kallon Goggo Abu kamar yayi kuka yana Fadin"Goggo Ta Fada miki Fita Take bada Izinina ba,Ta sanar dake batamin Kallon Mijinta Dauka na Take tamkar Wani yaronta ko Ma"aikacinta Ta gayamiki Wannan Ko bata gayamiki ba.."?Yafada kamar Zai Fashe da Kuka.


Daga Farida Har Goggo Abu Jikinsu yayi Sanyi Saboda yadda Tahir din yayi mganar,Sai goggo Abu Ta Koma Da Kallonta kan Farida tana Fadin"Kinji Abunda Mijinki yace In Hakane To Tabbas baki kyauta ba,Taya zaki Dinga Fita bada Izininsa ba Ai ba Zaman kanki kikeyi ba Ko Farida,Gaskiya ki gyara Kina Cikin Fushin Allah da Tsinuwar mala"iku matukar baki Roke Mijinki Gafara ba.."


Farida ta kanta ke kasa ta Fashe da Kuka,Jawota Jikinta goggo Abu Tayi Tana lallashinta Lokaci Daya Tana Fadin"Yi Shuru kibar Kuka,Ki bama Mijinki Hakuri Kune mi gafaran Juna Don Allah bana Jin Dadin Wannam Rashin Jituwar naku,kufa ba yara bane Kune fa Kuke da yara kamar basma da bassam Haba Don Allah Farida Don Allah Ku Sansanta kanku.."Tafada Cikin Sanyi Dagowa Farida Tayi Tana Share Kwallah kafin tace"Toh Goggo.. "Muryanta ta Dishe Sosai...


  Mirmishi goggo Abu Tayi kafin Ta Mike tana Fadin"Yauwa Naji Dadi bari naje na Karboma Atrahiru Fura Wajen Innaro yanzu zan Komo ."Tafada Tana Ficewa Don ta basu Waje bayan Fitanta Falo ya Dade Shuru kafin Farida ta yanke Shurun bayan Ta Dago Tana kallon Tahir Daya Tsurama Cafet din Goggo Abu Ido Fuskarsa ba Annuri ko Kadan Duk da gabanta na Fadi hakanan ta Daure Ta Furta.."Srry...'Tafada Muryanta na Rawa Ko kallonta baiyi ba,ganin Haka yasa sai Jikinta yayi sanyi Tatashi Ta Koma Side din daya ke kallo Ta Sake Furta"Am Srry..."Kauda kai yayi Yana Neman Tashi sai Ta Riko Hanmunshi Da Sauri ta Fashemai da Kuka bayan ta Dora kanta bisa  Cinyarsa,tsayawa yayi yana Kallonta Kukanta na Dakarmai Zuciya,Runtse ido yayi kafin ya Dora Hannunshi bisa kanta yana Tapping cikin Ajiyar Zuciya yake Fadin"Shiii...is ok.."..


Jin Abunda yace ne yasa Ta Dago Da Sauri Fuskarta Jage jage da Hawaye,tana kallonshi Mirmishi ya sakarmata kafin ya Zaro Wani Farin Hankey Daga Aljihunsa,yana Share mata Hawaye yana Fadin"Nace komai ya Wuce ko..? Kece fa kike ja muna Fada Farida,in da bakiyi Saurin Zuwa Wajen goggo Abu banayii Regreating din marin da nayi miki zan baki Hakuri,plz Farida..."Bai karisa ba goggo Abu Ta Shigo Dole yayi Shuru ganinsu haka sai ya sanyayamata Rai,Furar ta mikamai ta sake Ficewa,yana kallon Farida kasa kasa yafara Shan Furarsa,yana gamawa ana Kiran sallar La"asar nan yafice Zuwa Msallaci Ita Kuma goggo Abu Ta Dingama Faridar Nasihan bayan Suma Sun Idar da Sallar.


Bai komo dakin Goggo Abu ba sai da ya sallami kanwarsa Ashe,Har gida ya karata akafa suna Tafe Suna Hiransu gwanin ban Sha"awa,sai da ya Dawo ya Shigo bangaren Goggo Abu yace Farida tataso Su Tafi,nan ma goggo Abu Hadasu Tayi tana musu nasiha Sosai kafin Su mata sallama Shashen Innaro Suka Koma Suka mata sallama nan Tabada Sakon Fura mai Dadi Tace akaima basma da Bassam,Awajema Sallama Suka ma Hakimi ya bisu Shima da Sanya albarka.


Tahir shi ya Tukasu Shida Farida Acikin Motarta Shi Kuma garzali ya Tuko ta Tahir,acikin Motan Ma Hannunshi Farida Ta Damke tana Fadin"Shine ni baka bani Hakuri ba.."Tafada Cike da Shagwaba,Hankalinsa na Wajen Tuki ya Waigo yana Fadin"Ah...Waht Are u Eating na baka is Fooling Down,Zan baki mana ammh ai kinsa nawa Is so Special ko.."Yafada yana kallonta Lokaci Daya yana Kashe mata ido,Dariya tayi tana Kwantar da kanta Cikin kujeran Mota batace komau ba Ammh Hannayesu Sarke da Juna Jefi Jefi suna Hira Har Suka Kariso gida.


  Abun mamaki Haka yaran Suka ga Iyayen nasu Sun Shigo Hannuwansu Sarke da Juna,Saboda Jin Dadi basma da bassam Suka Ruga suka Rumgumesu suna Ihun Oyoyo momy da Daddy,Hatta Iya da Mufeeda Sunji Dadin ganin Farida da Tahir Da Alamun Komai ya Wuce,Ranar dai gidan Gabadaya yayi Dadi Dukkansu tare Sukayi Dinner Suna Yi Suna Hira Fuskar ya"yansu cike da Farinciki,Da Suka gama Cin Abunci Suka koma Falo Suna Hira da ya"yansu Hatta Naila Taji Dadi Sosai ganin yadda Take Tsallake Tsakanin Cinyar Tahir dana Farida,sai Wajen Goma Kana Suka Umarcin yaran da Su Tafi Dakinsu su kwanta Naila Kuma Farida Ta Mikama Mufeeda.


Awannan Daren dai Farida ta Hakura ta bama Tahir Ahakkinshi nan Suka Fahimci Duka Sunyi Kewar Juna,Farida tagayama aya Zagi,domin Tahir dai sai da ya Fanshe,koda Asuba ma Daya Dawo masallaci sai da Ya Dora Farida Tafara gajiya Sosai Sai Tura baki Takeyi Domin Abunda Ke Hadata Tahir kenan Jarabarsa.




*Aisha Alto..*

*Anitha..*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*



_Don't Forget to Follow us on Wattpad:Janafnancy13 or Aisha Alto alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


        *BABI NA TAKWAS*


*BAYAN SATI BIYU*


Zuwa wannan lokacin komai ya gama daidaita a tsakanin Tahir da Fareeda basu da matsalar komai yanzu, Fareeda ta natsu ta bar duk abun da take yi ta daina fita ko'ina kullum tana gida tana baiwa mijinta da 'ya'yanta kulawar data dace, wanda sauyin wannan hali nata ya yiwa kowa daɗi a cikinsu gidan ya zama cikakken gidan ma'aurata masu tsananin so da ƙaunar juna haɗe da tarairaya. Kullum cikin farin ciki da ɗoki 'ya'yanta suke, yanzu babu abunda ke damunsu saboda suna samun kulawar mahaifiyarsu kuma tana jansu a jikinta bata kyararsu komai suke so tana yi musu, Mufeeda da Iya suma abun yayi matuƙar yi musu daɗi gidan ya zama happy family babu damuwa ko matsalar komai a gabansu sai farin ciki.


Suna zaune dukansu a falo gidan suna kallo a makeken talabijin ɗin dake manne a bangon falon Naila na kan cinyar Mufeeda tana bata madararta yayinda Basma da Bassam ke gefe zaune a kan kafet suna yin Homework ɗinsu kasancewar gobe Monday akwai makaranta Iya ta fito daga ɗakinta da sauri tana share hawayen dake zubo mata ta nufo Tahir ɗa Fareeda dake zaune a saman kujera suna magana ƙasa ƙasa wanda su kaɗai suka san abinda suke faɗawa junansu dan babu mai jinsu ta ɗan rusuna a gaban Tahir tana goge ƙwallah tace "Sannunku da hutawa Alhaji." A hankali Tahir ya ɗago da kansa yana kallonta kafin ya gyara zama sosai yace "Yauwa Iya sannu da fitowa... amma lafiya kuwa na ganki haka?" 


Tana ƙara duƙar da kai tace "Yanzu ne aka yo min waya daga can gida Allah ya yiwa Yayana Malam Danladi rasuwa..." Ta ƙarashe maganar ƙwallah na ziraro mata ta kwanto haɓar zaninta ta share wasu na ƙara zubo mata, salati Tahir da Fareeda suka yi yayinda Fareeda ta miƙe ta kamo Iya ta miƙar da ita tsaye tana kallonta tace "Sannu Iya, Allah ya jiƙansa ya gafarta masa Allah yasa ya huta." Da Ameen ita da Tahir suka amsa kafin ya tashi tsaye shima yayi mata gaisuwa cike da alhini kana ya fice waje ya kira Garzali yace ya shirya ya fito da mota zai kai Iya Kano ba ɓata lokaci ya dawo ciki yace da Iya taje ta shirya su wuce Garzali ya kaita, sannan ya haura sama zuwa ɗakinsa ya ɗebo kuɗi masu yawa yazo ya bata ta duƙa tasa hannu biyu ta amsa tana masa godiya ta koma ɗakinta ta ɗauko 'yar jakar gana most go ɗinta ta fito Mufeeda dasu Basma da Bassam harma da Fareeda suka rakata har bakin mota ta shiga Garzali yaja suka fice daga gidan, su kuma suka koma cikin gida cike da kewarta da tayata alhinin rasa ɗan'uwanta da tayi.


Washegari da sassafe wayar Umman Fareeda ta tashesu daga barcinsu mai daɗi da sukeyi rungume da juna, da magagi ta lalubo wayar ta ɗauka ta kara a kunnenta nan take faɗa mata Abbanta ba lafiya ciwon sugansa ya tashi an kwantar dashi a asibiti. A gigice ta tashi ta sauka daga gadon tana tashin Tahir shima ya tashi ta faɗa masa abunda Ummanta tace cikin tashin hankali tashi zaune ya ziro ƙafafuwansa ƙasa ya sauka daga gadon ya riƙe hannunta suka shiga toilet agurguje sukayo wanka suka fito suka shirya Fareeda ta ɗebi kayanta kala biyu ta zuba a ƙaramar jakarta suka fice zuwa falo.


Ɗakin Mufeeda ta nufa ta samu har tayi wanka ta yiwa Naila itama tana shiryata ta shiga ta ɗauki Naila tace Mufeeda ta ɗauko hijabinta ta fito, da mamaki Mufeeda ta ɗauki hijabinta ta saka ta biyo bayanta suna fitowa falo taga Basma da Bassam a shirye cikin kayan gida saɓanin na makaranta da tayi tsammanin zata gansu dashi, duƙawa tayi zata gaida Tahir dake tsaye yana kallonta, ɗaga mata hannu yayi yana faɗin "Lafiya Alhamdulillahi Mufeeda... Ku muje lokaci na ƙurewa." Ya ƙarasa faɗa yana karɓar Naila dake hannun Fareeda ya saɓata a kafaɗarsa ya fice suna biye dashi a baya. Garzali na ganinsu ya taso da sauri ya nufosu ya buɗe masa mota ya shiga gaba ya zauna sannan ya buɗewa Fareeda ta shiga baya Mufeeda ta shiga kusa da ita ta zauna sannan Basma da Bassam suma suka shiga ya rufe ya zagaya da sauri ya shiga ya tada motar maigadi ya buɗe musu gate suka fice sai daya hau titi sannan Tahir ya faɗa masa inda suka nufa, nan ya taka mota suka ɗauki hanyar Kano.


Ƙarfe 12pm. Dai-dai suka shiga garin Kano direct asibitin da aka kwantar dashi suka nufa international Hospital kasancewar Fareeda tasan asibitin saboda anan ake dubasa duk lokacin da jikinsa ya motsa irin haka.


Lokacin da suka shiga room ɗin da aka kwantar dashi yana barci sai Umman Fareeda ce kaɗai suka samu wacce ke zaune a kujerar dake gaban gadon ta zuba masa idanu tana kallonsa, da gudu Basma da Bassam suka nufeta haɗe da faɗawa jikinta suka rungumeta tsam suna tambayarta meya samu Baban Mummynsu cike da so da ƙaunar jikokin nata ta rungumesu tana basu amsa da baida lafiya ne, a hankali Tahir ya ƙarasa gabanta ya durƙusa cike da ladabi ya gaisheta tare da tambayarta mai jiki? Da sakin fuska ta amsa masa da "Alhamdulillahi jiki da sauƙi, barci yake tayi tun ɗazu da akayi masa allura bai tashi ba har yanzu." Yana jinjina kai ya miƙe ya dafa ƙarfen gadon yana faɗin "Allah ya ƙara sauƙi yasa kaffarane.." da "Ameen." Duk suka amsa kafin Fareeda ta zauna bakin gadon da Abban nata yake a kwance tana kallon fuskarsa cike da damuwa kafin ta ɗauke kanta tana kallon Ummanta cikin sanyin murya ta gaisheta haɗe da tambayarta mai jikin itama, cike da kulawa ta amsa mata da faɗin "Ai da alamun yaji sauƙin jikin sosai, dan kwana biyu ko barcin kwata-kwata baya iya samu, yanzu kuwa kinga tunda likita yay masa allura bai tashi ba sai barcinsa yake yi." Gyaɗa kanta Fareeda tayi fuskarta cike da tausayin mahaifinta tace "Allah ya ƙaro sauƙi ya bashi lafiya." Bayan sun amsa Mufeeda itama ta matso tana ɗauke da Naila ta duƙa a gaban Umman Fareeda ta gaisheta haɗe da tambayarta mai jiki, tana murmushi ta amsa mata tare da miƙa hannu ta ɗauki Naila dake riƙe a hannunta tana kallonta ta fara mata wasa tana ɓangala mata dariya, juyawa Tahir yayi zai fita daga room ɗin da sauri Fareeda ta kallesa "Abban Basma ina kuma zaka je?" Ɗan juyowa yayi ya kalleta yace "Zanje inga likitan ne, yanzu zan dawo." Gyaɗa masa kai tayi ba tare da tace komai ba ya juya ya fice.


Koda Tahir yaje yaga Likita Hankalinsa ya Kwanta Tunda Likitan ya Nunamai ba Mtsala ba kamar yadda Suke Tunani bane,wajen 2pm na Rana Abba ya Farka ba laifin Jikin Nashi da Sauki nan yaji Dadi ganin Farida da Tahir din Hade da Jikokinsa,ganin Hakane yasa Karfe 5 na yamma yayi Shirin Komawa Kaduna Shida Su bassam saboda Mkranta ammh Farida Zata Zauna anan Tataya Umma Zama,Da Zasu Tafi Naila Ta makalema Mufeeda sai Farida tace su Tafi da Ita,Umma ce ta Hana Tace Maza Farida Ta karbi Naila Ta Zauna A Wajenta ai ba yayeta Tayi ba,Bude bakin Farida Sai Tace Ai Ta yayeta,Wata Uwar Harara Umma ta sakarmata kafin ta Karbi Nailan Dake Hannun Mufeedan Tana basu Umurnin Suyi Tafiyarsu Tahir yaji Dadin Haka Har saida Fuskarsa Ta Nuna Farida ko Ta Bata Rai ita Dole An Takura mata,nan dai Suka musu sallama Suka Juyo Zuwa kaduna.


Washehari Duka yaran Suka Tafi Mkranta Shima Tahir yatafi Office Gidan ba Kowa,shiyasa bayan garzali ya Daukosu Daga Mkranta ya biya Dasu Restaurant ya Siya musu Takeaway din Abinci kamar yadda Tahir ya Umarceshi Shi sukaci bayan Sun Dawo kafin Suyi Shirin zuwa Islamiya,Sai yammah Suka Dawo Karfe 7 Tahir ya Dawo Gidan,Shi ya Shigo musu Takeaway din Abinci Wanda ya biya Siyomusu kafin ya dawo Gidan Tunda Iya bata nan,kuma bayason Su basma na Shiga Kichen sai Sun kara girma Mufeeda kuma dama ba Aikinta bane.


Haka Suka Dinga Rayuwar Har Tsawon Kwana Biyu,Farida bata Dawo ba Tana kano,Ammh An sallami Abba ya dawo gida,Washegari Tahir ya Koma kanon Shida Hakimi da Goggo Abu da Innaro,Suka Iske Jikin Abba ya Warware kamar bashi ba,Basu jima ba suka Tafi inda Dama su Tahir din Suka biya Danbatta Suka Taho Dasu,kuma su suka maidasu gida,Da Tahir zai Tafi ya Kira Farida gefe yace yakamata tadawo gida Hakanan,bude bakin Farida sai Cewa Tayi yanzuma Jinyar Uban nata sai ya Nuna bayaso,Kokarin Nuna mata mtsalarshi yake ammh Farida Taki Fahimta basu Rabu ba Sai da duka Rayuwakansu ya baci Har Tahir ya Dawo kaduna Ransa na bace da Faridar.


***********


Satin Farida Daya da Tafiya Kano,Har yanzu bata Dawo ba,iya ma Tana gidan Rasuwa bata Dawo ba,kullum Sai dai in sun Dawo mkranta garzali ya Siyo musu Abinci Shi kuma in Zai Dawo Gida da yamma ya Siyo musu Wanda Zasu Dinner Da Daddare,da Safe Kuwa Shi yake Shiga Kichen ya Dafa musu Ruwan Tea ya Soya musu Kwai,Har Mufeeda Taso ya Dinga barinta tanayi Tunda ta iya Don Ita da basma indai Suna gida Toh Suna Nanike da Iya A Kichen Suna Koyon Girki,Ammh ya hanasu Shi gani yake Yara ne babu Abunda Sukayi.


Yau ma Hakan Ta kasance Duk yau Din yatashi bayajin Dadi Ciwon mara kamar Zai mutu Tun Daran Jiya sai da yasha Kanwa kana Abun ya lafamai,Ammh Haka yayi musu Abun karyawa bayan Sun Dawo sallar Asuba,Bassam ne ke Kichen Din yana kallon Mahaifinsu Cike da Tsantsan Kauna da Tsausayawa yana Tunanin Duk Duniya ba Wanda yafi son Su da Kula Dasu bayanshi,Har Suka Tafi Mkranta bai iya Fita Aiki ba Zuwa Chan ya Shirya ya Tafi Kuma bai kai yammah ba Wajen Biyar na yammah ya Dawo gidan Su basma ma Sun Dawo Islamiyane Suka Tarar Dashi Takeaway dinsu na Dinner ma Garzali ya Fita ya Siyo musu,Sun Damu Da Halin da Daddynsu ke Ciki Domin Dakyar ya iya Zuwa Sallar Mangariba Ko Isha"i bai Tsaya anyi ba kamar yadda ya saba Ya Riko Hannun Bassam Suka Dawo Gida.


Duka yaran sai sukayi Wani Iri Dasu Harda Mufeeda Wacce Itama Taji Ciwon Tahir Har Aranta,Zaune Sukae aFalo Sun Zabga Tagumi Gashi gobe Friday Suna da mkranta,Shine ya Fito ya gansu Sunyi Zugum Zumgum ya Sauko yace Kowannensu ya Shiga Dakinsa yayi Shirin Kwanciya,Toh ganin kamar ya samu Sauki ne yasa Suka mai sallama Kowanne ya Shige Dakinsa ya Kwanta Shi Kuma ya Koma sama yana Mukurkusu.


********


Karfe 1:50am na Dare ya Farka da Wani Azababben Ciwon Mara,Dafe Cikinsa yayi yana Salati tare da Kiran Sunan Allah Abu kamar Wasa karamar Mgana Ta zama babba,Domin Tun yana iya Mikewa Har yazo Yaji ya gagara,Jikinsa ba Inda baya Rawa,Saboda Tsabar Sha'awa da Muradi,wani irin Murda Cikinsa keyi kamar mai Naguda Dakyar ya iya Bude Kofar Bedroom dinshi ya Fito yana Dafe Dafen Bango yana Sanye da Dogon Wando ne baki Jikinsa ba Riga,Haka ya Dinga Dafa Karfen Steps din matattakalan Benen,yana Cize baki Acikin Ranshi Yana Tunanin Lalle Dole ya Nemar ma kanshi Mafita kafin Ya Kashe kansa da kansa Domin Farida bata da Asara.


Da Dafe Dafen nan ya Karisa Shiga Kichen yafara Neman Kanwa Daidai Lokacin Kuma Mufeeda Ta Shigo Kichen Din Tana Sanye Da Karamar Rigar Barcinta Wacce Cikin Wanda Farida ke Siya musu ne ita da Basma Rigar iyakarta Cinyarta gata Karamin Hannu gareta Tana da Budadden Gaba,Ga Ta Sharara ,komai na Jikinta ana gani Harda Yan Nonuwanta da Suka Fara Tasawa Ta Cikin Rigarta.


Kishi ne ya Fito da Ita Tazo Frigde din Kichen Din Daukan Ruwa,kichen din Didim ne Sakamakon bai Kunna Wutar Kichen din ba,Kuma bata ji motsi ba Don Azaba yasa ya Sulale Anan Tsakar Kichen din Rike da Ciki yana Mukurkusu,Hannu ta Sanya ta Kunna Wutar Kichen din Haske ya Gauraye Ko"ina Da Farko Bata ganshi ba Sai da Taji Ta Shuru kafar kamar na Mutum yasa taja baya tana Zaro Ido Jikinta yafara Rawa Cike da Tsoro Bata gane Tahir bane Kokarin Juyawa Take ta Fita da Gado,Ya Dago kanshi Cikin Wani yanayi yana kiran Sunanta.."Mufeeda....."Yafada Cikin Muryan Ciwo da galabaita.


.

Cak ta tsaya kafin ta Waigo Tana kallonshi,Zabura Tayi ta Isa gareshi da Sauri Tunda ta Fahimci Daddy ne,Durkushewa Tayi batare da Tunanin Komai ba Ta Rikoshi Tana Fadin"Innalillahi Daddy,Ciwon ne ya Tashi...?"Take Fada Cike Da Tashin Hankali Tana Rikoshi ACikin jikinta,Shiko Tahir Wani Shock ne ya Bi Ilarahin Jikinsa Lokacin da Mufeeda TaRikoshi Tana Kokarin Sanyashi Ajikinta Mahood dinsa ta Kara Mikewa kamar Zata Fito Fili,Jikinsa ne yakama Rawa yana Cije baki ya sauka daga Jikin Mufeeda yana Fadin"Dubamin kanwa Mufeeda plz..."Yafada yana Tamke Baki kamar mai Nakuda.


  Da Hanzari ta Mike Jikinta na Rawa Ta Bude Drower da Kanwar Take tana Dubamai Ammh sai taga yakara Kwanciya akasar Tayels din Kichen din yana Rike da Ciki,sai ta bar Dubawan Ta kara Nufoshi,Ja da baya yake da Jikinsa Ammh bata Fahimta ba Tana Zuwa Ta Dago kansa ta Aza bisa Cinyarta Ta Fashe da Kuka tana Fadin"Daddy meya sameka...? Cikinka ne ke Ciwo na Kira maka garzali yazo yakai ka Asibiti..? tafada Tana kallonshi Runtse Ido Yayi yana Girgiza mata kai Kokarin Tashi yake Ta kara Rikoshi Tana Fadin'Nan ne ke Maka Ciwo Daddy..? Tafada tana Dora lallausan Hannunta Bisa Cikinsa Wani Yam,Yaji har saida ya Dauke Numfashi kafin ya Dawo Dashi baisamu Zarafin mgana ba Ta Fara Dannamai Cikin ,tana Fadin"Sannu Daddy zai bari yanzu Haka Innata keman in ina Ciwon Ciki.."Tafada Hawaye na Zubomata na Tsausayinshi Kokarin Ture Hannunta yake Ammh Ita bata Fahimta,Saboda Yadda Jikinsa Ke Rawa Zuciyarsa na Kokarin Sakashi Aikata Abunda zai yi Nadama Har karshen Rayuwarsa.


   Kokarin mikewa yayi ganin Mufeda Zata Rabashi da Numfashi Saboda Hannunta Dake kan Cikinsa Bakaramin Wani yanayi ya sanyashi ba,Rikosa Tayi ganin yana Neman Faduwa Kallonta yayi kafin ya Runtse Ido ganin Duka Kirjinta yana Waje ne Rigar Barcin Ta yi gefe Kuma bata da Bra,Runtse ido yayi da Sauri Cikin Wani yanayi Yafara Tafiya Sai kawai yayi Luu zai Fadi da Hanzari Ta Rikoshi Tana mai Sannu ganin Haka yasa Tace"Daddy Daki zaka koma..? Muje na Taimaka maka kaga bazaka iya ba.."Tafada Cikin Wani yanayin Tsausayi Bai mata gardama ba ta Rikoshi Har Zuwa Sama Cikin Bedroom Dinshi Tana mai Sannu Sun Kariso Zuwa Gefen gadonshi yana Kokarin Kwanciya Kawai Sukayi Luu Suka Zube bisa gadon Ta Fado kanshi Tunda Jikinsa ba Karfi Tana Fadowa Jikinsa Komai ya Rikice mai,itako kamkameshi Tayi Cike da Tsoro Azatonta Kasa Zata Fadi,Sanda Nonowanta Duka Daki Kirjinsa sai da ya Dauke Wuta na Wasu Mintina,tuni ya Fita Daga Hayyacinsa ya Mika Duka Hannayensa ya Zagaye Kugun Mufeeda Dashi Wacce Ke Kokarin Tashi Ganin ya kamkameta ne ya Matseta yana Sauke Numfashi Da Sauri Da Sauri ya Tsorata ta ga Wani Abu Dataji mai kama da Iccen Daga kasanta yana Tunkuri ta sai Tsoro ya kamata ta Fara Kokarin Kwace Jikinta Ammh Ina Tahir yagama Fita Daga Hayyacinsa Domin Alokacin ya Manta da Mufeeda ce Abun Kawai Shedan da Kwakwalsar ke Nunamai Farida ce 


Shiyasa Cikin Zafin Nama ya maidashi kasanta,Zaro Ido Mufeeda Tayi Ta Bude Baki Cike Da Tsoro Zatayi mgana ganin yadda Tahir ke Tusa kanshi Cikin Wuyanta yana Sumbatarta Cikin Fitar Hayyaci Kalmar.."Dadd....'Bata gama Fita Daga Bakinta,taji ya Hade bakinsu Waje Daya yana Sumbatarta Cikin Fitan Hayyaci Hawaye Suka Barkema Mufeeda Domin Duk da kananan Shekarunta ta Fahimci Kudurin Tahir Akanta Ammh Duk iya Motsin Motsinta bata Tsiraba Haka Tahir ke Sarrafa Sassan Jikinta Cike da Kwarewa da Kuma Fitar Hayyaci Kukan Datake da Shuren Shuren Kafa Su suka kara mai kaimin,cikin Azama ya Zare Wandon Jikinsa Hade da Boxers Rigar Barcin Jikin Mufeeda ko Tuni ya Cireta yayi Wurgi da Ita,tana ji ya Bude Kafarta da karfin Tsiya ya Fara Turamata Abun nan Cikin karamin Gabanta Wani Azaba Taji da Radadi tana Kokarin Ihu Ammh Kuma ya Tare mata baki Danashi Shiko bai Cikin Hayyacinshi ganin ya Tura taki Shiga yasa yakoma da baya yakara Speed ya Danna kai,ya Shiga da karfin Tsiya Wanda Sai Mufeeda Tayi Suman Mintina Numfashinta ya Dauke kafin ya Dawo Kuka Take da Hawaye na Azaban Datakeji Wanda bata taba Jiba,Shiko Shiganshi ya kara Taimakamai Wajen Sake Fita Daga Hayyacinsa Wani Dumi yaji Lokacin daya Shiga sai ya kankameta yakara Tura kai yana Fadin"Ya illahi..."Riketa yayi gam yafara Driving dinta Cikin Wani yanayi na Fitar Hayyaci Lokaci Daya Dadin Daya Ziyarceshi Ya Nemi Zautashi baisan Sadda ya Saki Bakinta ba yafara Sambatu yana Fadin"Farida...Wayyo Allah na Karki Kasheni Kin kara Dadi...Na bani ni Tahir...Zan Mutu wayooo...Allahna..! Yake Fada Cikin Wani yanayi Lokaci Daya yana Cigaba da Hakarta da Zafi Zafi kamar ya samu babbar Mace.



*DON"T FORGET TO VOTE,COMMENT,SHARE AND LIKE...*



*Aisha Alto..*

*Anitha...*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


_Don"t Forget to Follow us on Wattpad:Janafanancy13 or Aisha Alto alto_



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


```Littafin NANNY... Bana kudi bane,Free Novel ne Daga Farkonshi har zuwa karshe,Duk Wanda yace Muku na Kudi ne Dan Damfara ne,Nanny Free Novel ne,ga Masoyanmu Wad'anda Suka Siya Littafanmu,MALIKA MALIK,ZAMAN GIDANMU,da INDO AISHA...SON SO FISABILLAH```



       *BABI NA TARA*


Tsawon Mintina Talatin ya kwashe yana Abu Ɗaya, Ni'imar Mufeeda Da Kuma Wani garɗin Daɗin Budurci shi ya ƙara Rikita Tahir ya Dinga Haƙarta baisani ba Samabatu kuwa, baisan iyakar Abunda bakinsa ya Faɗi ba.


Itako Mufeeda Tun Lokacin Daya samu Kofar Shiga yadinga Turamata da ƙarfi Numfashinta yanemi Ɗaukewa, Kuka shaɓe shaɓe da Majina lokaci Ɗaya Taji Duhu ya mamaye Idanuwanta Tun Tana iya Jin meke Faruwa Har Jinta da ganinta ya Ɗauke ba tare Da Tahir ya ankare ba gaba ɗaya Jikinta ya saki bata Numfashi.


Lokacin da yazo gangara ne ya ƙanƙameta Tsab Kamar Zai Tsaga Ƙirjinsa ya maidata, Nan da nan ya Shiga mata Ɓarin Madara, kafin ya saketa ta koma yaraf bisa gado Shikuma ya Bita Shima ya Faɗa Bisa kanta Bayan ya sakar mata Nauyinshi Yana Sauke Tawagayen Ajiyar Zuciya kamar Wanda yayi gudun Tsere .


Ji yayi maranshi Sakyau ta saki Farin ciki ya Cikashi Domin Ji yayi kamar yana yawo Agajimare Saboda Daɗi Amma Sai me ƙwaƙwalwarsa ne ta Shiga Tunano masa Abunda ya Wakana da Wani Uban Razana da Ɓarin Jiki da gaggawa ya Miƙe Daga Jikin Mufeeda Jikinsa da Zuciyarsa na Rawa Lokaci Ɗaya, Dama already Ɗakin Hasken Dum light ne, Cikin Fitan Hayyaci ya Saka Hannu, ya kunna Wutar Ɗakin Lokaci Ɗaya Haske ya Gauraye Bedroom Ɗin.


Baya Tahir yaja Cikin Bugawar Zuciya, lokacin Daya ci Tozali Da Mufeeda kwance Akan gadonshi ba yarda take da alama bata Numfashi, Hannu ya Ɗora Akai kamar Zuciyarsa zata Fito Waje ya ƙarisa bakin gadon yana kallonta Idanuwansa na Rufewa Saboda Ruɗewa Hannunta guda Ɗaya ya Riƙo kafin ya sakeshi sai yaga ya Tafi Luu ya Faɗi, Cikin Ruɗewa yabi Zanin gadon da kallo da Wajen kafafun Mufeeda Yaga yadda Jini ya ɓata Wajen kamar an yanka Wata karamar Akuya, Gata Tsirara Domin ga Rigar Barcinta nan,ayashe a ƙasa ko bai Tambayi kanshi ba ya Riga ya sani Cewa Mufeeda ce yama Wannan Aika Aikan.


Baya Tahir ya Dinga ja Jikinsa na Rawa kamar Wanda yaga Abun Tsoro Kansa ya Dafe Duk Sanyin Dake Ɗakin na Ac Zufa ke Keto mai, Hannu ya Ɗora bisa kai yana Fadin "Innalillahi Wa'inna Illaihirraju'un..Me na Aikata ni Tahir...? Wani Irin Abu ne ya Shiga kaina na Haikema yarinyar Dana ke kallonta Tamkar 'Yata Basma, itama take kallona Amatsayin Mahaifinta, Kaico na...! Kaico na...Ni Tahir na cuci kaina Wayyo Allah na! ..."


Ya faɗa yana Zubewa A ƙasa Kan Gwiwoyinsa Yana Riƙe kansa Yana girgizawa Lokaci Ɗaya Cikin Wani Tashin Hankali, Wata Zuciya Ce Take Tunasar Dashi Tahir zama bai ganka ba Kada yazo ka kashe yar Mutane, Tuna Haka yasa Yayi Zumbur ya miƙe, sai lokacin ya Lura Tsirara yake, Da Hanzari ya Ɗauki Wandonsa Wanda ya gani nan yashe A ƙasa, da Hanzari ya Isa ga Mufeeda yana Jijjigata Idanuwansa Sun sauya kala Sunyi Jajir Amma ko Motsi Mufeeda bata yi Zuciyar Tahir Ta Sake Tsinkewa Hankali Tashe ya juya ya Faɗa Bathroom d'in Dake Cikin Ɗakin ya Tara Ruwan Zafi A bath ko'ina na Jikinsa na Rawa Aguje ya Fito kamar Zai kifa bai tsaya Shawara da kowa ba ya saka Hannu ya Cicciɓi Mufeedan, Ya Shiga Toilet da Ita Da Hanzari, bai direta ko'ina ba sai cikin Jacuzzi inda ya Tara Ruwan, bayan ya Toshe Rariyan.


Lokacin Data jita Cikin Ruwan Zafi sai Ajiyar Zuciya ya Ƙwace mata amma bata buɗe ido ba Sai Mutsu mutsu Take alaman Dai Tanajin ba Daɗi, ruwan ya ɗiba ya Shafa mata afuska yana Kiran Sunanta A ruɗe, Da Kuka ta Buɗe Ido Lokaci Ɗaya Tana Neman Zabura Saboda yadda Wani Azaba da Raɗaɗi Suka Ziyarceta Jin Ruwan Zafi na Ratsata, Hannu yasa Cike da Nadamar kanshi ya maida ita Cikin Ruwan yana kallon Fuskarta, cikin Azaba da Raɗaɗi Mufeeda ta fara Buɗe Kumburarrun Idanuwanta ta Saukesu kan Tahir, ƙuri tayi mai kafin Abunda ya Faru ya fara Dawo mata Daki Daki.


Wani Baƙin ciki ne Mai Haɗe da Wani Kuka ya Tasoma Mufeeda Da Hanzari Ta Runtse ido Bata son ganin Fuskar Tahir, Fuskar Data Ɗauke Ta mai Daraja mai kima, mai kamala da Dattako, fuskar Datake kallonta amatsayin Mahaifinta yau Shine ya Keta mata Rigar Mutumci yaci Zarafinta ya kafa mata Tarihin da Har Abada bazata Manta ba, idonta na Runtse Tana Tsiyayan Hawayen Baƙin Ciki da Azaba mai Tsanani, Shiko Tahir na gefe yana kallonta ganin Ta Runtse Ido yasa Zuciyarsa Ta Tsinke Shima Sunkuyar Dakai yayi yana Kiran Sunan Allah.


Mufeeda na Kuka Muryanta ta Dishe, tana Faɗin "Innata...Wayyo Ni Innata..." Take Faɗa Tana Kuka mai ban Tausayi da taɓa zuciya, Da ƙyar Tahir ya Jawo Jarumtarsa ya isa ga Mufeeda yana Faɗin "Is..ok..Kibar Kukan haka nan plz.." Yake Faɗa yana kallonta, Amma ina ko Sauraranshi batayi banda Gunjin Kuka babu Abunda Takeyi, Lokaci Ɗaya Kuma Wani ƙarfi ne yazo mata ta Yunƙura ta Miƙe Tana bin Ruwan da Kallo yadda Jinin Dake ɗiga Daga gabanta ya Sauya kalan Ruwa bata ma iya Tsayuwa Saboda baƙar Azaba Datakeji Da ƙyar ta iya Zura ƙafarta Ɗaya Waje Tana Cije baki Take Faɗin "Wayyo Inna Zan Mutu.." Take Faɗa Tana Kuka Lokacin Data Gama Tsayuwa da kafafunta amma sai Taji gangar Jikinta Sun kasa Ɗaukanta Tayi luuu Zata Faɗi Tahir yayi Hanzarin Tarota ta Faɗo Ƙirjinsa, bai Tsaya Sauraran Kukanta da Bubbuga kirjinsa Datake na ya ajiyeta ba ya Fice Da Ita Zuwa Cikin Ɗakin.


Kan gadon ya maidata bayan ya yaye Zanin Gadon, ƙasa ta Sulale Tana Kuka idonta Akulle gam bata Ƙaunar ta Buɗe Idonta ma, Shima Tahir Durƙushewan yayi yana kallonta Zuciyarsa kamar Zata Fashe ya fara magana Cikin Raunin murya.." Mufeeda..." Ya kira Sunanta Cikin Bugun Numfashi Cak Ta Tsayar da Kukanta amma Bata Ɗago Ta kalleshi ba.


  Ganin Haka ne yasa ya saki Ajiyar Zuciya kafin ya cigaba Da Faɗin "Ki yafemin Mufeeda, Ba laifi na bane..Bansan yadda Akayi ba..Bansan yaushe Haka ta Faru ba... Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un..wallahi yau nayi Nadamar Zuwa na Duniya, bansan dawa Ni ido zan kalli Mutanen Duniya in Sanar dasu nayi ma yarinyar Dana Riƙeta Tamkar yata Fyaɗe ba..kaicona Ni Tahir nayi Nadamar Rayuwata Farida ta Cuceni ta cuci kanta da Zuri'armu Gaba ɗaya Duk Halin Dana Tsinci kaina Aciki wallahi Itace Sila Itace Sila..." Ya faɗa kawai yanajin Kuka ya Ƙwace mai Jin yana Kuka yasa Mufeeda ta Buɗe Kumburarun Idanuwanta Ta Bishi da kallo Lokaci Ɗaya Kuma Taji Tausayinshi ya kamata ganin yana Kuka Duk da Halin Dayake Ciki Sai da tace "Ka..ka...Da.daina Kuka Daddy...bazan Faɗama Kowa ba.." Ta faɗa Itama tana Sakin Nata marayan Kukan.


Jin Abunda Tace ne yasa ya Ɗago da Sauri ya Riƙo Hannunta yana Faɗin "Da gaske kike Mufeeda bazaki Fadama kowa ba...?" Ganin yadda Yake Rawan Jiki ga Hawaye na bin Fuskarshi yasa Ta ɗaga mai kai kafin tace "Ka..kaini Wajen Innata..Wajenta zani.." Iska ya Furzar kafin yace "Zan kaiki ki kwantar da Hankalinki kibar Wannan Kukan kada gobe su Basma su Fahimci Wani Abu ya Faru, yanzu bari na Shiga nayi Wanka na Fito Hau gado ki Kwanta naji Jikin ki Temperature yayi yawa Kinji ki jirani na Fito.." Ganin yadda ya Ruɗe ne yasa Ta Ɗaga mai kai da Hanzari ya saki Hannunta ya rarumin Zanin gadon daya baci da Jini ya Faɗa Toilet yana jin Tsanar kanshi, da kallo Ta bishi Sai da ta Tabbatar ya Shiga kana ta fara Rarrafe ta jawo Rigarta ta sanya, tana Neman Hanyar Fita Lokaci Ɗaya tana Zubar Ƙwallah Saboda Azaban Dake cinta ta Tsakiyarta kamar Wacce Aka Tusa mata Wani Katon Abu ya Tokareta...  


Da Rarrafe ta Fito Daga bedroom Ɗin ta Kuma gangaro Steps d'in Benen Tanayi tana Kuka Har Ɗakinta, Allah ya Taimaketa Basma ko Bassam ba Wanda ya Fito, Da Rarrafen ta Ƙarisa Cikin banɗakin Dake Ɗakinta ta Haɗa Ruwa Mai Zafi Ta Shiga Ciki Tana Cigaba da Kuka mai Cin Rai Tana Sane Cewa Wannan Abun Tahir yayi Toh sai fa sai tayi Wankan Tsarki Domin A makarantar islamiya an Sanar Dasu Duk Ranar da Namiji ya kwanta Dake sai kinyi Wankan Janaba kuma ko ba Haka ba Lantana Ta Sanar da ita Ranar Daren Farkonta Haka Mijinta yayi mata, Amma ita yau gashi ba Miji ba Saurayi ba Daddy Shi ya Keta mata Budurcinta yau ya maida Ita mace..


Tana Kuka da Komai tayi Wankar Tsarki ta Fito Tana Dafe bango, Lokacin Zazzaɓi ya Rufeta tana Rawan Sanyi, Da Hanzari ta Faɗa kan gado taja bargo Ta Rufe Jikinta tana Rawan Sanyi, Shiko Tahir Wanke Zanin Gadon yayi ya Shanyashi Acikin Bedroom d'in kafin yayi Wankan Tsarki ya Fito sai dai yana Fitowa yaga Wayam ba Mufeeda Hankalinsa Tashe ya Zura Wata baƙar Jallabiya ya Nufo Ɗakinta Ajiyar Zuciya ya Sauke sanda ya ganta Lulluɓe Cikin bargo baya yaja Cike da Damuwa kafin ya koma sama Yana mai Nadama.


Darduma ya Shimfida ya kabarta sallah dama already ya Ɗauro Alwala, Sallah yayi Raka'a goma Sha uku Haɗe da Shafa'i da Wutiri, Kafin ya Ɗaga Hannuwanshi Sama yana Roƙon Gafaran Allah, Yana yi yana Kuka kamar ƙaramin yaro baƙin ciki da Nadama Sunga ma Lulluɓe Tahir, Bayan ya idar karatun Qur'ani ya dasa gabatowar Asuba, kana ya Tashi Daga kan Sallayar ya Sauko Ƙasa Idanuwansa Sun Masa Nauyi, Ɗakin Mufeeda ya Leƙa yarda ya Isketa sai gabansa ya Faɗi Tana Kwance Cikin Bargo Tana Rawan Sanyi Cikin Hanzari ya ƙarisa gareta bayan ya yaye Bargon ya Taɓa Goshinta yaji Zafi Sosai Ruɗewa yayi Cikin Fitan Hayyaci ya koma Ɗaki ya Ɓallo mata Paracetamol da Kuma Pain Killer yazo ya tada Ita tana Rawan Sanyi gefe Ɗaya Kuma Tana Tsiyayan Hawaye, ya bata Tasha Ta Koma ta Kwanta.


Ranar dai Barci baiga idon Tahir ba Shi ya Tashi Bassam Suka Tafi masallaci Koda Suka Dawo Sai da ya leka Dakin Mufeeda ganin Ta samu barci ne yasa Hankalinsa yadan Kwanta sakamakon baya Cikin Natsuwarsa yasa breakfast ɗinsu ma Garzali ya aika yayi musu Takeaway Koda Basma Ta Fito Cikin Shirin kayan makaranta ita da Bassam, Tahir bai bari Sun Tambayi Mufeeda ba yace musu yau bazataje Sch ba batajin Daɗi, Ransu baiyi Daɗi ba Suka Juya Zasu Shiga Ɗakinta Tahir ya hanasu Cikin Wani yanayi nan yace su bari Su Dawo ya bata Magani ta samu barci Inda Ace Zasu lura da Sunga yadda yake Rawan Jiki kamar baya Cikin Hayyacinsa.


Basu kawo komai Aransu ba Suka Fita Zuwa Haraban gidan bayan Sun karya da takeAway d'in Da Garzali yayi musu, ƙarfe 7:30am Garzali ya kwashesu Zuwa Makaranta Shikanshi Da baiga Mufeeda ba sai da ya Tambayesu Suka ce mai batajin Daɗi Fatan Samun Lafiya yayi mata kafin ya kaisu Makaranta ya Ijiyesu ya Kamo Hanyar Gida yana Tunanin Zai kai Tahir Office.


Shi ko baida Cikakkiyar Natsuwa Hankalinsa A tashe yake na Abunda ya Faru kada Kuma Wani ya ɗau sanau, Ganin Jikin Mufeeda Har da Safen Arikice yasa bai Fita Office ba koda Ishaq yajisa Shuru ya kirasa  Awaya nan yake Shaida mishi bazai Samu Fitowa ba baya jin Daɗi, Sannu yamai kafin Suyi Sallama, Tahir Wuni yayi Tashin Hankali Domin Zazzaɓi yaƙi barin Mufeeda ko Abincin da Garzali yasiyo ta kasa Ci Komai ya bata sai ta kauda kai Tana Kuka Tana Kiran Sunan Innarta ya rasa yadda Zaiyi Tsoronshi Ɗaya kada Farida Ta Dawo ta Fahimci Abunda ya Faru Domin Ko makaho Ya Shafa yasan Cewa Mufeeda ta Illata ganin ko iya Tafiya ma batayi Tana Kuka Tahir nayin na Zucci Suna Cikin Wannan Halin ne yaji sallamar su Basma sun Dawo Daga Makaranta Koda yayi Wuf ya Fito Daga Ɗakin Mufeedan Sai Suka ci karo da Su, Ganinshi Hankalinshi Tashe sai su ka Tura kai Ɗakin Azatonsu Jikin Mufeedan ne ya Tashi Shiko kasa Komawa Cikin Dakin yayi ya Tsaya anan Yana Kiran Sunan Allah yana Fatan Kada Su basma Su Fahimci Wani Abu.


Toh dai basu Fahimci komai ba, Illah Sun Tausayama Mufeedan Ganin yadda Take kuka Tana Kiran Sunan Innarta, Basma kamar ta mata Ƙwallah Ta Fito Daga Ɗakin Tana Faɗin "Daddy Akai Aunty Mufeeda Asibiti Jikinta kamar Wuta.." Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace "Za'a kaita Basma ku Shiga ɗaki ku cire Uniform ɗinku ga Takeaway chan Garzali yayo muku kunji.." Gyaɗa kai suka yi kafin Kowanne ya Nufi Ɗakinsa zuciyarsu ba Daɗi Domin Sun Shaƙu da Mufeedan Sosai.


  Suna gama cin Abinci Sukayi sallah Da Farko Basma taso Ta Zauna da Mufeeda amma Tahir yace maza Ta Shirya ta tafi makaranta Dole Hakanan ta Shirya Ita da Bassam Garzali ya Kwashesu Zuwa Islamiya, Har Suka Taso Daga makaranta Tahir baisamu mafita ba, Sun Shigo Kenan sai ga Iya Ta Dawo Wanda ya Faɗarma da Tahir gaba, Basma da Bassam Suka Rungumeta suna Murna Itama Cikin Farin cikin Ganinsu Take Amsa gaisuwansu kafin Su Dakata ta Rankwafa Tana gaida Tahir ya amsa Cikin Wani yanayi na karaya, yana Ƙara yi mata gaisuwa.


Mufeeda Ta fara Tambaya kafin Farida nan Basma tace Tana Ɗaki Tun Jiya bata da lafiya, Ai kafin Tahir yasamu Mafita Iya da Basma Sun Nufi Ɗakin Mufeeda Zuciyarsa ce ta karye ya Nemi Kujera ya Zauna yana Dafe kai Bassam ne ya katseshi da Faɗin ya Tashi Su Tafi masallaci Shidai Har Aka idar da sallar mangariba baya Cikin Natsuwarsa Saboda Zullumi bai jira Sun Sallaci Issha'i ba kamar yadda Suka saba Ya Riƙo Hannun Bassam Suka Dawo Gida Zuciyarsa na Bugawa Saboda Fargaban kada iya tagano Abunda ya Faru Ta Matsama Mufeeda Har Sai ta gaya mata Abunda ya Faru, Bassam ko tausayin Daddynsa yakeji ganinsa Haka Kamar Wanda ƙwai ya Fashema aciki sai ya yi Tunanin ƙila Jikin Nashi ne Har yanzu.


Suna Shigowa Falon Suka Ci Karo da Iya ta Fito Daga Ɗakin Mufeeda Ɗauke da Ƙaramin Kofi Ahannunta tana ganinsu Tace "Yauwa gama Alhajin nan..." Faɗin Haka da Iya Tayi sai da gaban Tahir ya Tsinke Zufa ta fara Ketomai Tsura mata Ido yayi yana kallonta Domin miyan bakinsa ya ƙafe, bata Lura da Yanayinsa ba tace "Alhaji gaskiya ya kamata Akai Mufeeda Asibiti Zazzaɓin Jikinta yayi Zafi Sosai Inajin Maleria ce Ta Shigeta.." Ɓoyayyiyar Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace "Eh dama Dawowar Danayi kenan, Ta fito muje Adubata yanzu..." Ya faɗa Cikin Sanyin Murya Kai Iya ta kaɗa kafin tace "Yadai kamata Alhaji.." Ta faɗa Tana Komawa Ɗakin Mufeedan.


Iya ta Umarci Basma Data Ɗaukoma Mufeeda Hijabinta ita Kuma tana Ƙoƙarin Miƙar Da Ita Noƙewa Mufeeda Tayi Tana Rawan Jiki Tace "Bazan iya Tashi ba Iya ki barni Akwance Don Allah..." Fuskarta Iya Ta kallah Tana Faɗin "Sannu Daurewa zaki yi Alhaji ne zai kai Ki Asibiti Adubaki Mufeda.." Jin Abunda Tace ne yasa Ta ƙara Ruɗewa, Bata da Kwanar Amin Iya ta Tsayar da Ita da ƙafarta tana Cema Basma ta Bata Hijabin Hannunta, Mufeeda Ji Tayi Ƙafarta na Rawa Saboda Wani Hucin Azaba Dake bin Tsakiyar Kafarta Tana Ƙoƙarin Sulalewa Basma da Iya Suka Riƙota Iya ta Sanya mata Hijabi saman Doguwar Rigar Jikinta, Suna mata sannu Duk da Suna Riƙe da Ita amma yanayin Takunta yadda Take Gwale ƙafa sai da ya bama iya mamaki ta kalleta tana Faɗin "Mufeeda meya sameki ne ga kafarki ba Daidai ba Kina Tafiya Wani Iri..?"


  Iya ta Faɗa Tana kallonta Cike da Mamaki daidai Lokacin Da Suka Fito Falon, kuma maganar a kunnan Tahir, wanda Yaji jiri ya Ɗaukesa ya Ɗago yana kallon Mufeeda Zuciyarsa na Harbawa da Sauri Sauri Mufeeda Wacce Iya ta sakama ido, kafin Ta Waiga Tana kallon Tahir yadda ya Sauya cikin Kwana Ɗaya yasa bakinta na Rawa Tace "Ba..ba komai.. ɗazu ne nazo Fitowa Daga banɗaki Shi..shine Santsi ya ɗebeni na Faɗi na Buge ƙafana.." Ta faɗa Tana Runtse Ido Hawaye na Zubo mata, ajiyar Zuciya Daga Tahir har Iya suka Sauke Iya ce tace "Ashha Sannu.. ƙila Targaɗe Kikayi.." Ta faɗa Tana ƙara Riƙota su suka Fita Da Ita Har Haraban Gidan Saboda Tashin Hankali ko Ɗaki Tahir bai koma ba Da Jallabiyan Jikinsa ya Shiga Mota Daidai Lokacin da Iya da Basma Suka Shiga Motar, Gabansa ne ya Faɗi, amma sai ya Danne ya juya yana Ce musu Su bari yanzu zasu dawo su Zauna Su kula da gidan, ba yadda Suka iya Suka Fito Daga Motar Suna ji Suna gani Garzali yaja Motar Suka Fice Daga Haraban gidan..

.


Iyali Hospital iyalanshi Keda Fayel Amma gudun tonon Asirinshi yasa Suka Nufi Garkuwa Hospital, Suna Zuwa Aka karɓeta suka kuma yi sa'a Dr Hadiza ce kan Duty Ranar Haka ta Fito tana Faɗa Lokacin data ci karo Da Mufeeda Office Ɗinta ta Kira Tahir tana Tambayanshi Suwaye suka ketama yarinya ƙarama Mutumci Suka mata Wannan Illar, Fada Take Sosai, Zuciyar Tahir tashi ga Rawa Da ƙyar ya iya Faɗa mata ba'a san ko Suwaye ba, Nan dai Tace Zasu Riƙesu Domin Mufedan Tana buƙatar Kulawa Saboda An Jimata Rauni Sosai So Zasu Riƙeta Har Zuwa nan da Sati Ɗaya Sugani, Tahir yaji Daɗin Haka Sosai ko banza Asirinshi Zai Rufu, bai bar Asibitin ba Sai Wajen 10pm na Dare Har Mufeeda ta samu barci bayan ansaka mata Drip da Wasu Allurai, gida Suka Dawo Shi da Garzali Wanda baisan Abunda Ke Faruwa ba, inda Allah ya Taimakeshi Asibitin basu bukatar masu jinya, koda Ya Dawo su Basma basu Kwanta ba Suna Jiran Dawowarsu nan yake sanar dasu an bata gado, sun janjanta Sosai yace Suje su Kwanta gobe da Safe sai Suje Su Dubata, Iya ma sai Fatan Allah yabama Mufeedan Lafiya Take har Tashiga Ɗakinta.


Tahir ko bedroom ɗinsa ya Shiga Kafin ya Faɗa Toilet ya sakarma kanshi Shower yana kuka zucci jikinsa na Rawa inya Tuna kalaman Dr Hadiza inda Take mai Faɗa bayan yace Shi mariƙin Mufeeda ne, Da Har yayi Sakaci aka keta mata Mutumci Haka..? Yaya zataji in Taji labarin Shine Da Kanshi ya Aikata mata Haka..? Tun yana Kukan Zucci Har ya Fito Sarari, Dakyar yayi Wanka ya Ɗauro Alwala ya Fito ya Saka kayan barcinsa Riga da Wando, Ya Shimfiɗa Darduma ya Tada Sallah, Issha'i yayi kafin yayi Shafa'i da Wuturi ƙaramin Alqur'aninsa ya ɗauko ya Tankwashe ƙafa ya fara karatu Cikin Rawan Murya yanayi yana Kuka, kukan Nadama Da Kaico da Rayuwarsa.







*Anitha*

*Aisha Alto..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


       *BABI NA GOMA*


Ranar barci ko ɓarawo bai Sace Tahir ba, kuka kuwa yayishi kamar Ranshi Zai Fita Daga ƙarshe ya Haƙura ya Fauwalama Allah komai ya kuma Ɗaukeshi A Matsayin Ƙaddararshi, Amma yasan Duk Abunda ya Faru Dashi Farida ce Sila kana Goggo Abu Da'ace Sunyi Duba da Lalurarsa da Irin Halittarsa, Da Duk Haka Bata Faru ba Amma yana Ta Neman gafaran Allah, sai dai Kunya da Nauyi Sun Cikamai Ƙirji Sun Hanashi Sukuni.


Shi yazo ya tashi Bassam Suka Tafi masallaci Sallar Asuba basu Dawo ba sai Wajen Bakwai Saura Koda suka Shigo Iya ta gyara Ko'ina Tana Kichen Tana Musu Abun Karyawa Bedroom ɗinsa ya shige ya Zauna Kawai ya Zabga Tagumin Makomar Rayuwarsa yadda ya Cuci Rayuwar Yarinya kamar Mufeeda.


Su Iya ko tana gama Abun karyawa Ta ɗorama Mufeeda Abunda Zata Tafin mata Dashi Asibiti Tunda Tahir yace in Sun karya Garzali zai Tafi Dasu, Shiko yana Cikin ɗaki yama kasa Fitowa Bawai bayajin Yunwa bane A'a yanaji Domin Rabonshi da Abinci Tun Jiya da Dare, Amma Cikinsa ne A Chushe bayajin Akwai Abunda Zai samu Wajen Zama ga bakinsa ba Tes Kwata kwata Ɗaci ɗaci ma yakeji Shikanshi Damuwa ta Saukar mai Da Zazzaɓi mai Zafi kan gado ya Kwanta ya Lulluɓa da bargo Haka Basma da Bassam Suka zo Suka iskeshi ya Dunƙule yana Hawaye, yanajin Muryansu Suna Kiranshi yayi Saurin Share Kwallah ya Fito da kanshi yana Ƙoƙarin Daidaita kansa.


   Basma ce Ta ƙarasa Tana Zama Gefen gadon Lokaci Ɗaya Take faɗin "Daddy jikin ne...? Ta faɗa Cike da Tausayawa, Kai ya girgiza musu kafin yace "No ba sosai bane Basma, nasha magani da nayi barci zan Warware, kun Shirya ne..." Bassam ne ya Ɗaga mai kai yana Zama Shima gefen Basma Fuskarshi ta bayyana Damuwar Dayake Ciki, Cikin Raunin Murya ya Furta..." Daddy What Wrong With you ne? bama jin Daɗin Ganinka A haka in Momy bata sonka Why not ka samo mana Wata Second Mom ko Basma...?" Ya faɗa yana kallonta, Saurin Kuka ne da Ita sai ga Hawaye Shar ta gyaɗa kai tana Faɗin "Eh mana Daddy, Momy tana Barinka kana Wahala bamai kula dakai ka ƙaro Aure plz kasamu Wacce Zata Dinga Zama dakai kullum muma Mu samu Mommy Wacce Zataso mu sosai Fiye da Momy.." Ta faɗa Kuka na Ƙwace mata ta Kifa kanta Jikin Tahir tanayi, Hannu ya saka yana Shafa kanta Dake Cikin Hijabin yanajin Ƙaunar 'ya'yansa Har Cikin Ranshi Duk da ƙananan Shekarunsu Sun Fahimci Damuwar nashi Acikin Ranshi Faɗi yake dama dama ace bai Aikata Abunda ya Aikata ba, Amma yanzu da Wani ido Zai kalli 'ya'yansa yace Shine ya Ketama Mufeeda Mutumci.


  Cikin Sigan Lallashi yake Faɗin "Shiii..Is Ok karku damu Kunji na samu Sauƙi Sosai Ku Tashi Ku Tafi Garzali zai kaiku Room 9 Take kunji.." Gyaɗa kai Basma Tayi kafin Ta mike Tana Share Kwallah Hannunta Bassam ya Riƙo Kafin su Duka Dukkansu Su Sakarma Tahir kiss a Goshi, Lumshe ido yayi Idanuwansa Sun Cika da Kwallah Cikin Raunin Murya yace "Take care..." Suka Fice Suna Ɗaga mai Hannu Suka Fita Wani Kuka yazo mai ya Shige Cikin Bargo yanayi kamar ya Shiɗe Saboda Takaichi So yake ya Buɗe Ido yaga Duk Abunda ya Faru mafarki ne Amma Ina bakin Alƙalami ya Riga Daya bushe, Abunda yasa Ma ya bari su iya suka Tafi Asibitin bashi da mafita ne don ya cigaba da Hanasu Zuwa Zasu Zargi Wani Abu, shiyasa yakira Dr Hadiza da Safen nan, dayake sun karɓi Numbarn Juna, ya Roƙeta Akan Don Allah mahaifiyar Mufeeda Zatazo Dubata koda Wasa Kada Ta mata Narrated din Abunda ya Faru da Mufeeda baya son Hankalinta ya tashi Sai daga baya zai sanar da ita, jin Haka yasa Dr Hadiza ta Amince da Roƙonsa suka Rabu Akan sai Anjima zai Shigo Asibitin.


Su Basma Sun Iske Jikin Mufeeda da Sauƙi Tana ta Barci ga Nurses nata kula da Ita sai Wajen 1 ta Farka taji Daɗin ganinsu Iya dasu Basma Ta dinga Murmushi, ta daina Kukan yanzu, Tunda Ta fara jin Sauƙi Gasata Suke bana Wasa ba ga mgaunguna gashi tana samun Hutu Dr Hadiza Da Tazo da Safe Haka ta Dinga Tambyar Mufeeda ko Zata Tuna Fuskar Wanda yayi mata Wannan Aiki Ko Zata Taimakesu Su Nemar mata Hakki, Acikin Ranta Kuka Take Har Asarari, Saboda Bazata iya Buɗe baki ta Furta Wanda ya Inganta Rayuwarta ne ya Aikata mata haka Bazata iya karya Alƙawarin da tayima Daddy ba Koza'a Kasheta Akaro na Farko Zata saka mai da Abunda yayi mata Arayuwa, tana kuka take Cemata bata sani ba Dole ta kyaleta.


Sun Daɗe sai Wajen Uku Suka Tafi bayan Iya Ta Zuba mata Faten Waken Data Zo mata Dashi Abakinsu ma Takejin Wai Daddy baida lafiya, Tana Shan Faten Waken Tana Sharan Kwallah Na Tausayin kanta Dana Daddy Domin Dukkansu Sun Faɗa Cikin Wata Jarabawa, koda suka koma gida Tahir na Kwance Ba yadda yake Ishaq ne da yayi ta Kiran Wayarsa bai samu ba  yazo gidan nan ya iskeshi Kwance Zazzaɓi ya Rufeshi Batare da Tunanin Komai ba ya Taimaka mai ya Fito Suka Tafi Asibiti.


Iyali Hospital Ishaq ya kaisa Suna Zuwa Suka Riƙeshi Saboda Jikinsa ba ƙwari ga Jininsa ya Hau Gado Suka bashi bayan Sun Sakamai Drip, Ishaq kamar yama Tahir Kuka yana Tunanin Duk Damuwar Farida ce Sai da Aka gama Komai aka kawoshi Ɗakin Hutu kana ya samu Sararin Kiran Farida yana Sanar da Ita Tahir bashi da lafiya gashi Anyi Addmiting Ɗinsu, Taji ba Daɗi Sosai Ta Dingama Ishaq din kame kamen batama san Bashi da lafiya ba, Nan tace Insha Allah gobe Zata Dawo Daga Haka Suka Rabu, kafin ya kira Zahra yana Sanar da Ita ta Turo Direba da Abinci yana Asibiti Zai Kwana da Tahir, Su Basma kuwa Jin Shuru basu Dawo ba yasa Suka saka Garzali ya Kawosu Asibitin nan Suka Iske Daddynsu Kwance Kuka Sukayi Tayi Ishaq na lallashinsu bai Tashi ba Har Suka Koma gida, Iya Tayi Tagumi Tana Jimamin Wannan lamarin Gefe Ɗaya tana Tir da Halayyar Farida.


Sai Wajen yamma Farida Ta Dawo, Tun Agida ta samu labarin Itama Mufeeda na Asibiti ga Tahir Abu Lokaci Ɗaya sai ta Fara Zuwa Asibitin Inda Tahir yake Ta Dubashi, taji Tsoro Ganin yadda Tahir ya Faɗa yayi Wani Sukuku Dashi nan ta Iske Ishaq da matarshi da 'ya'yansu, Alokacin ne yake Shaida mata Likita yace Damuwace Tayi mai yawa Sosai Shine ta galabaitar dashi gashi bayason Cin Abinci, Tagumi Farida Tayi Tana kallon Tahir Cike da Tausayi, Yau ne Rana Ta Farko Dataji bata kyauta ba, Shiko Tahir bayama son ganin Fuskar Farida Saboda Duk Itace Silan Shiga Wannan Halin Shiyasa ya Kulle ido Yayi mata barcin karya, Da Farko Ta karɓi Ishaq Jinyar Shi ya Koma gida Amma Sai Tahir ya Hana yace Ta Koma gida Saboda Mufeeda Shi Ishaq ɗin ya cigaba da Zama Dashi bata da yarda Zatayi Hakan ta Haƙura suka Fito da Aliya Kowa ya Shiga Motarshi Zuwa Gida.


Bata samu Zuwa gaida Mufeeda ba sai Washegari dasu Innaro Suka zo Da Ashe da Hakimi Sun Zo Duba Tahir bayan sun Dubashi ne Farida Ta ƙarasa Dasu Suka Duba Mufeeda wacce Ta samu Sauƙi Sosai, Koda Suka Haɗu In Farida zata Lura Mufeeda bata iya kallonta Saboda gani Take kamar Zata Fahimci Abunda ya Faru, Amma ita Farida ba Wannan bane agabanta Damuwarta yadda Tahir bayason kallonta balle yimata mgana sai ya zama Dole.


Washegari ne Umma Tazo Daga Kano, itama Ta Jinjina Ramar da Tahir yayi da Zata Tafi, tayi tama Farida Faɗa lokacin Data Zo Rakata, Akan ta kula da Mijinta Taga dai Halin Dayake Ciki Haƙuri Farida tabama Umma Inda Tamata Alƙawarin gyara Kuskurenta, itama bata Wuce ba sai da ta biya ta Duba Mufeeda, kana Direba ya Wuce Da Ita Kano.


Tahir Kwana Huɗu yayi A Asibiti kafin asallameshi ya Dawo Gida, Mufeeda ko Sai da ta Kwana Takwas Cur ta Warke kamar babu Abunda ya Faru kana Dr Hadiza Tayi Discharging Ɗinsu Tahir da kanshi yaje ya Taho Da Ita Shida Farida Wacce yanzu ke Wani Rawan Jiki Dashi Shi kuwa kallonta kawai yake Acikin Ranshi yana Faɗin Lokaci ya Ƙure miki Farida, Baya son ma Haɗa Ido da Mufeeda Amma itako Tana ta Satar kallonshi ganin yadda ya rame yayi ƙasumba kamar ba Daddy Ɗan Gayu ba, ita kaɗai Tayi ta Sharɓan Kwallah Acikin Ranta Tana Faɗin Ta yafema Daddy Duniya da lahira kuma Har Abada ba Wanda Zaiji Labarin Abunda ya Faru.


Gida yayi Daɗi da Dawowar Mufeeda mussaman ma Basma da Bassam da Iya, Tahir ko yanzu kwata kwata ya daina Sakewa kamar da ko ya'yanshi Sun Fahimci Haka dama kuma baida yawan magana Amma yanzu Abun nashi yayi yawa Tun balle Farida Data zage tana Kula Dashi Amma Sai dai ya Bita da Ido Abun ya Fara bata mamaki da Tsoro ko Ta Tambayeshi sai yace mata ba komai ta bashi Haƙuri Kuma yace ba komai amma ya kasa Sakin Jiki Da Ita Babban Abunda ya bata mamaki Shine bai Nemeta ko Sau Ɗaya ba, Shi ko Gaba ɗaya Sha'awarshi bata Zuwamai Saboda baya Cikin Natsuwarsa, Abunda ma ya ɗan Lafamai Shine ganin Mufeeda ta samu lafiya ta Dawo Walwalwarta Har Ta koma School Shi kaɗai sai ya Riƙa Fita Ta Ƙofar baya Daga sama yana Hangensu in Zasu makaranta ganin Ta Saki Jikinta yasa Hankalinsa ya fara Kwanciya.


Sati biyu ya kwashe Agida yana Hutu kana ya koma Office Wanda ko Alokacin Sai Ahankali Ishaq yasha Kamashi yashiga Zurfin Tunani Akwai Ranar daya ganshi yana Kuka Abun yabashi Tsoro, yayi kuma Tambayar Duniyar nan Amma Tahir yaki Sanar dashi sai ma Murmushin Kuka Dayayi mai yana Faɗin karyayi Fatan Jin Abunda ya Aikata Domin Har shima in yaji Sai ya Tsaneshi, Abun yabashi Tsoro Sosai Sai ya Dinga Fatan Allah ya yayema Tahir Duk Abunda Ke Damunshi Tunda yaƙi Sanar dashi koma menene.


Ita kuma Farida takasa gane kan Tahir yadaina Fitowa Dining Cin Abinci sai dai takai mai Ɗaki, shima bawani ci yake Sosai ba, koda yaushe ya dawo yana Ɗakinsa yana karatun Qur'ani ko Kuma ka ganshi Zaune yayi Tagumi duk ya Chanza kamar ba Tahir ba, bashi da Wata Walwala Komai na Duniya ya Fita kanshi gani yake Watarana Za'a gane Komai yana ji Ajikinsa Asirinsa bai Rufeba Wata rana Komai Zai Fito Sarari, kowa kuma Zaiji yazaiji Da Kunyar mutane Dawani Ido Zai kalli iyayansa yace Shine da kanshi ya Aikata Wannan Aiki, Abun yana Ranshi ya Hanashi Sukuni.


*****


Yau ɗin Takama Weekend ne Sunday, Tun safe Farida ke Lura da Tahir yayi Zurfi Cikin Tunani Ko Ruwan Wanka Data Hadamai bai Shiga yayi ba, Tana Lura Dashi yayi Zaune Kawai yayi Shuru agefen Gado ya zabga Tagumi da Hannu Bibbiyu.


  Shigowarta Bedroom d'in yasa Ta Bishi da kallo kafin ta ƙarasa Kusa Dashi Zama tayi Gefenshi Kafin ta sanya Hannu Ta dafa Kafaɗarshi Tana Faɗin "Abban Basma..." Ta faɗa Lokaci Ɗaya Tana Girgiza Kafaɗarshi, Ɗagowa yayi yana kallonta Kafin ya saki Ajiyar Zuciya, yana Lumshe ido Lokaci Ɗaya yana Furzar da Iskar bakinshi, narai narai Tayi da Ido kafin tace "Meke damunka ne..? Tunda Kadawo Daga Asibiti Ka Chanza kadaina Walwala kamar baya baka sakin Jiki da Kowa, Baka da Aiki sai yawan Zama Shuru da Tunani, kuma kasan Cewa Likita yace kadaina yawan Zama Cikin Tunani Saboda Jinin Ka yayi Sama.." Ta faɗa Cike da Tausayawa.


Ƙura mata ido Yayi kafin ya saki Ajiyar Zuciya, Kawai ya Miƙe bai ce mata komai ba, sai da ya Nufi Hanyar Toilet kana ya Waigo yana Faɗin "Bafa komai Tun Ranar Nake Faɗa miki karki Damu.." Ya faɗa yana Tura Ƙofar Toilet d'in ya Shiga Da kallo Ta bishi Jikinta Duk yayi Sanyi A iya Tunaninta ta kasa gano Abunda ke Damun Tahir Ta tambayeshi ko Itace Amma yace karta damu Bakomai Amma Koda yaushe Abun nashi ƙara gaba yake ba Wani Chanji, tana nan Zaune ya Fito Wanka Ɗaure da Towel a ƙugunsa yazo ta gabanta Zai Wuce Da Hanzari Ta Miƙe ta faɗa Jikinsa Ta Rungumesa ta baya ta Fashe mai da Kuka Tana Faɗin "Nidai don Allah ka sanar dani Abunda ke Damunka..? In nice na maka laifi Tunda na Dawo nake baka Haƙuri Bai ci ka Haƙura ba? Don Allah kadaina Wannan Tunanin.." Ta faɗa tana zagayo da Hannuwanta Ta Cikinshi Runtse Ido yayi Jikinsa Duk yayi Sanyi kafin ya Buɗe ya Juyo da Farida Suna Fuskartar juna, Hannu ya sanya yana Share mata Hawaye kafin yajata Jikinsa yana Faɗin "Shiiii..Nace miki ba komai ko? Ki daina Damuwa..." Ya faɗa yana Shafa bayanta Har Zuwa Tudun Hips Ɗinta, ganin Haka ne yasa ta ƙara Narke mai ajiki kafin Ta Ɗago kanta Ta Haɗa Bakinsu Waje Ɗaya Gefe Ɗaya Kuma Hannunta na saman Faffaɗan Ƙirjinsa Tana Shafawa.


 Tahir bai da Wata Natsuwa Biye mata kaɗai yayi Saboda Kada Allah ya kamashi da laifin Danne ma Farida Hakki Har Suka Dangana da gadonsu sai gashi yau Abun mamaki Farida bata gaji da Tahir ɗin ba Amma Shi Round ɗaya Sukayi ya Zame Jiki ya Shiga Toilet ya sakarma kanshi Shower, yana Jin kamar ya kurma Ihu, yau shine bayan ya Sadu da Mufeeda kuma ya koma ya Sadu da Farida Abun yamai baƙin ciki Sosai Wanda yasa ya kasa Sakin Jikinsa yayi komai kamar yadda ya saba, Har yayi Wanka ya Fito Farida na Kwance Tana Binshi da kallon Mamaki Aranta tana Faɗin Tabbas Tahir bashi da lafiya don A Tarihin Aurensu bai Taɓa mata Ci Ɗaya Alokaci ɗaya ba sai yau.


********


_BAYAN SATI UKU_


 Bayan Sati Uku da Faruwar Haka Abubuwa Suka Fara Sauki, Domin Mufeeda ta Saki Jikinta Sosai ta Koma kamar da, rainon Naila ya Dawo Hanmunta kamar da, kuma Tana Cigaba da Harkarta sai dai Abun na Cikin Ranta Tayi ta Kuka Ita Kaɗai Acikin ɗaki, Sai Abu na Biyu Daya Dameta ganin yadda Daddy yake Ta Rama Atsaye Duk da bata cika ganinshi bane, Shiko Tun bayan Faruwar Haka Mufeeda Ta Zauna Aranshi Komai yake sai ta Faɗo mai tausayi Take bashi yarinya Ƙarama Ta Zama Abun Tausayi, Da ganga yake gujema Haɗuwarsa da Mufeeda Da Zarar Sun Haɗu Abunda ya Faru ke Dawo mai Duk da yanzu Ya fara Maida Natsuwarsa Amma bawai Don Abun yabar Zuciyarsa ba Kwata Kwata...


 Tsakaninshi ko da Farida Kadaran kadahan Domin Tagaji Da Tambayarshi meke Damunshi Ta Haƙura ta Zura mai ido Har ƙararshi Takai Wajen Goggo Abu ta Kirashi yaje ta Turkeshi Daga Ƙarshe Kuka ma ya Fashe mata Dashi Abunda ya bata Tsoro kenan Domin Ita ta Haifi Attahiru, tafi kowa saninshi Bai da Rauni, Amma sai gashi yana mata Kuka yana Faɗin Ta tayashi Addu'a ya Aikata Wani Abu Wanda yakejin kunyar Idon Mutane da Allah Wanda ya Halliceshi, kuma tayi tayi Ya Faɗa mata Amma yaƙi sanar da Ita, ko da ya tafi Ɗaki Ta shiga Tana Tunanin meke Faruwa da Tahir ɗin ne Haka Domin Ko Afuska ya Rame Sosai Duk ya Chanza, hakama Hakimi Yayi mamakin Ramar Ɗan nashi Amma sai ya Danganta Hakan da Rashin Lafiyar Dayayi, Kai Ranar Duk Wanda yaga Tahir yasan Cewa ba Lafiya yake ba Hatta Innaro sai da tayi magana, Toh ba Wanda Zaice ga Abunda ke Damunshi Domin bai yarda ya Sanar ma Kowa Abunda ya Aikatama Mufeeda ba.









*Aisha Alto...*

*Shakira...*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


    *BABI NA GOMA SHA D'AYA*


Rayuwa Tana ta ganganrawa Da Daɗi ba Daɗi, Har yanzu Tahir bai manta da Abunda ya Faru ba, Amma ya ɗan Saki ba kamar Farkon Abun ba, Amma Tausayin Mufeeda yayi Zaune ɗam Acikin Ranshi Tun bayan Faruwar Abun baya iya Runtse Ido bai tuna ta ba, gashi bai cika yarda Suna Haɗuwa ba Saboda gani yake Tamkar Za'a iya Fahimtar Abunda ya Faru.


Ita ko Mufeeda duk da yarinta na Ɗawainiya da ita Zan iya Cewa Tama Fara Manta Abunda ya Faru Tsakaninta da Tahir Tunda gani Take ta warke Komai ya Riga ya Wuce, babu Wanda zai gane Kuma ba Wanda zai sani bata taba Tunanin nan gaba Wani Abu Zai iya Faruwa ba. 


Ɓangarenshi da Farida Kuwa ba laifi yayi ƙoƙarin ɓoye Damuwarshi Saboda Iyayenshi Da Sauran 'yan'uwanshi da Kuma 'ya'yanshi da Hakkin Farida Dake kanshi Amma zancen gaskiya Tun bayan Abunda ya Shiga Tsakaninsa da Mufeeda bai ƙara yin Sex cikin Daɗin Rai ba, sam sam Sha'awar Hakan ya Fita a kanshi ita kanta Farida Tana mamakin Wasu Sauye Sauye Daga Hallayar Tahir kamar An Ɗauke Tahir ɗin baya An kawo musu New One ne. 


Ko awajen Aiki Koda yaushe Cikin Danne Damuwarshi yake kada Wasu Su Fahimta, bayan Ishaq baisan Ko kowa kallonshi yake ba Domin Duk Wanda yasan Tahir Abaya in ya ganshi yanzu sai ya Tambayi kanshi Cewa Yaushe Tahir ɗin ya koma Haka...? Ishaq ko Daga baya Daya Gaji Da Tambayar Tahir meke Damunsa yaƙi Sanar Dashi, Sai kawai ya kawo Ido ya Saka mai Gefe Ɗaya yana Tayashi Addu'ar Allah ya warware mai duk Abunda ke Damunshi.


Duk da ƙoƙarinsa na Danne Damuwarsa in ya keɓe kanshi na Wasu Mintina sai Abun ya Faɗo mai nan da nan zai Rasa Natsuwarsa Har idanuwansa Su kama Zubar da Kwallah Wanda ya rasa Dalili Haka Kurum ya keji Acikin Ranshi Komai bai ƙare ba Akwai Wani Babban Lamari da Zai Faru nan gaba.


***********


Yau tun 8 yake Cikin Office ya kasa Aiwatar da Komai ya faɗa Kogin Tunani Hannunsa Dafe da Duka Kuncinsa Zuciyarsa na Harbawa Lokaci Ɗaya, Koda da Rana Ɗaya Abun bai Taɓa Shafe mai Acikin Kwakwalwa ba gani yake Tamkar Akwai Wani Babban Al'amarin da Zai bayyana Komai yana Ji Ajikinsa Asirin sa bai Rufu ba, kuma Koda ya Rufu ina Zai kai Hakkin Marainiyar Allah?


Wannan Tunanin Shike Sanyashi Shiga Wani Hali har ya fara Zubar da Kwallah bai sani ba, Tsawon Lokaci ya Ɗauka yana Shessheƙan kuka Abunda bai sani ba Tunda ya fara Wannan Koken nashi Ishaq ya Shigo Office d'in Bai sani ba Wanda ya Shiga Tashin Hankali ganin Tahir na Kuka Lokaci Ɗaya yana Faɗin Allah na tuba ka yafemin, Abun ya bashi Tsoro matuƙa Shiyasa yayi Tsaye ƙiƙam ya kasa magana yana Ɗauke da Wasu Fayel ne Wanda ya kawoma Tahir ɗin ya Duba sai ya Tarar Dashi Cikin Wannan Halin.


Da ƙyar ya iya ƙarasawa Ga Kujeran da Tahir ke kai ya saka Hannu ya Dafa Kafaɗarshi yana Faɗin "Subhanallahi Tahir mezan Gani Haka...? Kuka fa kake yi Don Allah ka Daure ka sanar dani Abunda Ke Damunka Don Allah...?" Ya faɗa Cikin Alamun Damuwa lokaci Ɗaya yana binsa da kallo, Firfigit Tahir yayi ya ɗago yana kallon Ishaq dake Tsaye kanshi, Saurin Saka Hannu yayi yana Share Kwallarsa kafin ya ƙaƙaro murmushin Dole yana Faɗin "Haba Friend Sau nawa Zan Sanar dakai babu Abunda Ke Damuna meyasa kaƙi yarda dani ne...?"


Wani kallo Ishaq yabishi Dashi kafin yace "Eh Naga alama, na yarda kana da damuwa amma bankai matsayin Dazaka sanar Dani ba..." Ya faɗa kai Tsaye yana Kafeshi da ido, Cikin Fitan Hayyaci Tahir yace "Toh mene ne Damuwar nafada maka bakomai Allah..."


Tsaki Ishaq yaja yana Faɗin "Toh in ba kana Cikin Damuwa ba Uban Me zai Zaunar Dakai kana Kuka kana Faɗin Allah ka Tuba ya yafe maka? Haba Tahir ban zaci Akwai Abunda Zaka iya ɓoye min ba. Amma ba komai Insha Allahu bazan Ƙara Ƙoƙarin naji Abunda Ke Damunka ba Zan Ta Maka Addu'an Koma Menene Allah ya yayemaka Shi.."


Ya fada kafin ya ajiye mishi Fayels Ɗin Agabanshi ya juya zai Fita Daga Office d'in kamar Daga Sama Yaji Muryan Tahir Yana Faɗin "Ba Abun Kirki bane Ishaq zaka Sha mamaki in nace maka Fyaɗe Na Aikatama yarinyar Datake Daukana Tamkar Mahaifinta...." Tahir ya Faɗa Idanuwansa suna Zubar da Kwallah, Cak Ishaq ya Tsaya kafin ya Waigo yana Faɗin "Fyaɗe...? Wani Irin magana ne Haka, Shikenan Kuma Don ba kasan Faɗa min Damuwarka sai kayi ma kanka Irin Wannan Mugun Bakin..? Ya faɗa yana kallonsa Cike da damuwa.


Cikin ƙarfin Hali Tahir ya miƙe ya isa ga Windown office d'in Yana Share Hawayensa Cikin Raunin Murya ya furta..."Dama Nasan bazaka yarda ba Ishaq Ina Jin Kunyar kaina Da Kaina In na Tuna Abunda na Aikata, Ba karya bane Duk Damuwar Daka ga Ina Shiga Saboda Hakane Mufeeda fa nayi ma Fyaɗe Ishaq..." Ya faɗa yana Dafe Kanshi, Zaro Ido Ishaq yayi kafin yace "Mufeeda Nanny dai Ta Gidanka mai Renon Naila Wacce Kuka Ɗaukota Daga Ƙauye..." Ya faɗa Cikin Fitan Hayyaci.


Gyaɗa kai Tahir yayi yana Hawayen Takaichi Da Nadama yana Faɗin "Ita fa Ishaq, ita nayima Fyaɗe Cikin Rashin Hayyaci Amma Duk da Haka na Ɗauki Hakan A Matsayin ƙaddarata..." Nan ya Shiga labarta mai Duk Abunda ya Faru Daga Farko Har ƙarshe, ya ƙara da Faɗin "Ya zanyi Ishaq..? Abun yaƙi barin Raina ina ganin kamar na Cuci 'yar mutane, ina ganin kamar Asirina bai Rufu ba, Kamar Akwai Wani Babban Al'amari da Zai Faru nan gaba, Da Wani ido zan kalli mahaifiyar yarinyar nan...? Da wani ido zan kalli iyayena da 'yan'uwana da kuma 'ya'yana...? Ishaq ka Faɗa min Da Wani Ido Zan Kalli Mutanen Dasuke gani na Da Mutumci da Kima...?" Ya faɗa Ya kasa Control Ɗin kanshi kawai sai ya Rufe Fuskarshi da Tafin Hannunshi ya Saki Wani Marayan Kuka.


Jikin Ishaq ya gama yin Sanyi da labarin da Tahir ya bashi Jikinsa A matuƙar Sanyaye ya ƙarasa ga Tahir ya Dafa Kafaɗarshi yana Faɗin "Ba laifinka bane Tahir...Duk Abunda ya Faru Rubutacce ne Daga Rabbil Izzati, amma babu Shakka Farida da Goggo Abu sune Silan Fadawarka Wannan Halin Ko Nace Wannan Kaddarar..." Da Sauri Tahir ya Ɗago Idanuwansa Jajir yana Faɗin "Sune Sila Wallahi Ishaq Sune Sila da'ace Farida Tana Kula da Duka Hakkina Da Haka bata Faru ba, da kuma Ace Goggo Abu ta karɓi Uzurina ta barni na ƙara Aure Da Haka bai Faru Dani Ba Ishaq, kaicona na Cuci Rayuwata Na Kuma Cuci Rayuwar baiwar Allah..." Ya faɗa Lokaci Ɗaya yana Faɗawa Jikin Ishaq Shi kuma ya Rungumesa yana Bubbuga Bayansa Alamun Lallashi Tausayin Tahir ya Cika mai Ciki Sosai.


Sun Daɗe A haka kafin Ishaq ya Ɗago Tahir ya kuma sanya Hannu yana Share mai Hawaye Lokaci Ɗaya yana Faɗin "Ba girmanka bane ka Dinga Kuka Haka Friend na Tabbata koda labarin nan ya Fita kowa zai bada Sheda Akanka kai Mutumin Kirki ne Kawai ƙaddara ne ta Faɗa maka Wanda baka isa ka Tsallaketa ba..." Ƙura mishi Ido Tahir yayi kafin yace "Hakane Ishaq Amma kai kaɗai ne zaka Fahimci Hakan Sauran Mutane bazasu gane Haka ba..."


Hannunshi Ishaq ya Riƙo Suka Zauna Bisa Doguwar Kujeran Dake Cikin Office d'in, Ƙaramin Fridge d'in dake Office d'in ya Buɗe ya Ɗauko mai Roban Ruwa da Kofi ya Tsiyaya mai Ruwa ya bashi, karɓa yayi yasha Kafin ya miƙa mai, shima Tsiyayawa yayi yasha kafin ya maida Kofin Da Goran Ruwan Saman Fridge d'in, Ya koma ya Zauna kusa da Tahir ɗin yana Faɗin "Suma zasu gane Friend, Karka damu Nidai Roƙona ka Cire Komai Acikin Ranka Tunda Itama yarinyar Ta manta komai, Kuma Tana da Hankali Tunda Har yanzu Bata Sanar Da kowa ba.." Ajiyar Zuciya Tahir ya saki kafin yace "Hakane Tausayin Yarinyar ne yaƙi barina Ishaq, ina Tausayinta yadda na Cuci Rayuwarta Marainiya ce fa bata da Kowa sai ni sai Allah.." Ya faɗa cikin Damuwa...


  Kafaɗarsa ya Bubbuga yana Faɗin "Cool Down karka Damu Insha Allahu Komai zai Wuce Kuma Allah naganin Zuciyarka, Ai tana Karkashinka ne Kuma Kana Ƙoƙarin Kyautata mata, na Tabbata nan gaba Zata inganta Rayuwarta.." Jinjina kai Tahir yayi kafin yace "Insha Allahu" Nan Ishaq ya zauna yana Ta bama Tahir baki Sai da ya Tabbatar da Tahir ya saki Jiki kafin Su gangara maganar Aikin, Tahir ya natsu ya Na Duba Fayels din da Ishaq ya kawo mai, nan Ya barshi Shi kuma ya Tafi Office ɗinshi Cikin Damuwar Halin da Tahir ke Ciki.


******


*After 2 Month...*


Gidan na Tahir A cike yake da 'yan Hutu Domin Satin Daya Gabata 'Ya'yan na Ashe Suka Diro Sun Zo Hutu, Laila da Muda Sakamakon Dogon Hutun da yan Makaranta Suka Samu na Third Tearm Duka yaran na gida Hatta Dasu Bassam Waɗanda Sukaji Daɗin Zuwansu Laila d'in.


  Misalin Ƙarfe 4:50pm na Ranar Asabar Iya ta Shiga Ɗakin Mufeeda Da Niyyar Ɗeboma Naila madararta A cikin Wani ƙaramin Kofin Da'ake Dama mata Har ta Ɗiba Madaran Tana Shirin Fitowa Daga Ɗakin Idonta ya Hango mata Mufeeda Kwance Gefen Gadonta tana Sharar barcinta Jikinta Dogon Hijabin Islamiyansu ne, Daga ƙasa Kuma Ƙaramar Jakar Makarantan nata ne yashe A ƙasa Daga Ganin yadda Ta Kwanta Zaka Fahimci Barcin ya Kwasheta ne ba tare Data Shirya ba.


Baki Iya ta Riƙe Cike da mamakin Mufeeda A yan Kwanakin nan, Bata da Aiki sai barci Wuni Take barci bata gajiya Alhalin Kuma Ada ba Haka Take ba,Da Hanzari Ta Isa gareta ta Hau Tabata Tana Kiran Sunanta.. "Ke Mufeeda..Mufeeda..." Buɗe Ido Tayi Cike da barci da kasala Tana kallon Iya, wacce ke Tsaye Tana kallonta Cikin Mamakinta tace "Tashi Meye Haka Islamiyan Kenan, Su Basma sun Tsufa A Makaranta Ashe Ke Kina nan Kina Shegen barcinki na Fama..." Ta faɗa Tana Binta da kallo.


Miƙa Mufeeda Tayi Tana Banƙaro Ƙirjinta kafin Ta Miƙe Zaune Tana Kwaɓe Hijabin Jikinta, Baƙar Doguwar Rigar Dake Jikinta na kamfanin Armani ta bayyana, Wacce Ta Fito da Ainihin Cikar da Mufeedan Tayi Tunda ga Kugunta Har Zuwa Nonuwanta, Cike da Kasala ta Ɗaga Ido Tana kallon Iya Kafin Tace "Wallahi Iya bansan Barci ya Kwasheni ba na Idar da sallar kenan Basma ta Shigo Ita da Laila Tace na Fito Mu Tafi, nidai na san na Ɗauko Jaka na saka Hijabin Daganan Kuma Ban ƙara Sanin Inda kai na yake ba.." Ta faɗa Tana Hamma.


Tsam da Ido Iya Tayi Tana Ƙarema Mufeeda Kallo Tun daga kan Fuskarta yadda Ta Cika Tayi Wani Fari da kyau ga Jikinta Duk ya Chanza Ta kara Cika Kamar ba Mufeeda mara Jiki ba, Gabanta na Faɗuwa Tace "Mufeeda meke Damunki ne, Na lura Dake a yan Kwanakin nan, Baki cin Abinci sai Kayan Kwalama Kullum Sai kin Soya Wainar Fulawa, kin kuma yi Ɗanwake ga yawan Barci Da kasala kamar kasa, Anya Mufeeda Zuciyata fa Tana Rayamin Wani Abu...?" 


 Ta faɗa Tana Kurenta da Ido Mufeeda bata bama Tambayar Iya Muhimmanci ba Ta Miƙe Tana Miƙa Tace "Bansani ba Iya Haka Kurum na Tsinci kaina, In ina Sha'awar Abu in banci ba kamar Zan Mutu kuma yawan Barci Kila Don Hutun Da Muka samu ne, Nima Wani Lokacin ina mamakin kaina, na rasa Meke Damuna..." Ta faɗa tana Yamutsa Fuska.


 Cike da Faɗuwar gaba Iya ke Bin Ƙugun Mufeeda da kallo yadda ya Cika Sosai Ta Juya Zata Shiga Toilet, Baki Ta kama kafin Ta Fice gabanta na Faɗuwa Zuciyarta na Tsinkewa Ita ba yarinya ba ce, Ta san Alamomin Ciki Sosai da Munafiki da Fallasasshe, Bata son Abunda Take Zargi Kan Mufeeda Ya Tabbata, Bayan Ta gama bama Naila Madaran Ta Goyata tayi Barci sai ta Nufo Babban Falon Gidan Inda Farida ke Zaune Tana Waya da Umma.


Gefenta Iya ta Zauna saman Cafet, Har sai da Ta kammalah Wayar, Ɗagowa Tayi Tana kallon Iya kafin Tace "Hajiya Iya Naila ce Tasha goyo Haka..?" Yake Iya Tayi Kafin Tace "Eh Hajiya..." Daga Haka Ta Sunkuyar Dakai, Ganin Haka yasa Farida tace "Lafiya Iya da Wani Abu ne..?" Kai Ta Ɗago Tana Faɗin "Eh Hajiya nazo Miki da Wata Magana ne Allah yasa Zaki Fahimceni..."


 Zama Farida ta gyara kafin ta ajiye Wayarta Tana Faɗin "Karki Damu Iya Ina Jinki" Cikin Muryan Dattako Iya Tace "A gaskiya Hajiya ya kamata Ki saka Likita ya Binciki Mufeeda, domin ina Wani Zargi Akanta Duba da Wasu Alamomi Dana ga Sun bayyana Muraratan Tare Da Ita.." Cike da mamaki Farida Tace "Likita ya Binciki Mufeeda Kuma Iya bata da lafiya ne Ko meye Dalili..?


 Iya ta Ɗan Yi Shuru kafin Tace "Maganar Gaskiya Hajiya Ina Zargin Ciki Mufeeda Ke dashi, Amma Ita kanta bata Fahimci Haka ba, ko kuma Tsabar Bariki ne bansani ba..." Zabura Farida Tayi Ta Miƙe Hannunta Dafe A ƙirjinta Tana Faɗin "Ciki Kuma Iya...? Wata magana Kike faɗi Haka? Wazai ma Mufeeda Ciki yarinyar Da bata Fita Daga Makaranta sai gida..?" Iya ta gyaɗa kai kafin Tace "Ƙwarai Kuwa Hajiya Nima Abunda ya Dauremin kai kenan" Nan Ta Shiga gayama Farida Duk Abunda Tagani game da Mufeedan da Alamun Ciki Ta ƙara da Sanar da Ita Halin Data Tarar da Ita yanzu Haka..."


 Cikin Farida ya bada Wani Sautin Tashin Hankali, jikinta na Rawa Tace "Na Shiga goma ni Farida Ya Zanyi Iya.? In ya Tabbata yarinyar nan Ciki Tayi Wani Amsa zan bama su Goggo Abu da Mahaifiyar yarinyar nan...? Mezan Cema Abban Basma Iya...?" Ta faɗa Cikin Tashin Hankali, Miƙewa Iya Tayi Tana Faɗin "Hajiya kafin Mu Fara yanke mata Hukunci Ya kamata Likita ya Duba Ta Tukunnah..." jinjina kai Farida Tayi Kafin Tace "Shiga ki Sanar da Ita ta sako Hijabi ko Keke Napep mu Tara ya kaimu Asibiti Tunda Inaga Daga Makarantarsu Basma Garzali ya Wuce Company ne, Hanzarta Iya.." Ta fada tana Ɗaukan Wayarta Ta Nufi Upstairs Da Hanzari Nombar Tahir Take Nema Amma kuma bata Sameshi ba, Ɗakinta ta Shiga Ta Ɗauko Mayafi Tunda Motarta ta samu Matsala tana Wajen gyara, Koda ta Sauko Ƙasa Har Mufeeda Ta Fito Idanuwanta Sun Shige Ciki Saboda barci, don Kwance Iya ta Tarar da ita.


 Farida sai Lokacin Take ƙarema Mufeedan kallo gabanta na Faɗuwa Na Irin Kyau da Cikar da Mufeedan Tayi basu Tsaya ba Farida Da Iya Wacce ke goye da Naila Suka Tasa ta Gaba Suka Fice Daga Falon, a haraban Gidan Farida ce ta barma Megadi sallahu Koda Tahir ya Dawo ko yara ya sanar dasu Sun Shiga Asibiti yanzu Zasu Dawo Da Toh ya amsa musu yana Musu Fatan Dawowa Lafiya.


Keke Napep Suka Tara Sai iyali Hospital, Ƙuruciya da Yarinta ke Damun Mufeeda Shiyasa Taji Daɗi Tunda Iya tace Za'a Dubata ne Don Itama Ta Gaji da yawan Barcin Datake Fama Dashi Da Kasala, Suna Zuwa Farida da Mufeeda Suka Shiga Ciki Ganin Dr, saboda Daman Nan Suke da Fayel, ganin Farko yayi mata sai ya Fara Jeho mata Tambayan Yaushe Rabon Data ga Al'adanta tace "Wata Uku kenan." Gaban Farida sai ya ƙara Tsinkewa nan Likitan keta Tambayanta Tana bashi Amsa, nan da nan ya kira Waya sai ga Wata Nurse Tazo Yace Suje da Mufeeda Ta Ɗibi Jininta ta kai lab Agwadashi yanzu yana Jiranta Fita Sukayi Ta tafi da Mufeeda lab D'in Ta Ɗibi Jininta, Office d'in Mufeeda ta Dawo Ta Zauna Farida ko na Zaune Tana Fama da Faɗuwar gaba Tsawon Minti 30 sai ga Sakamako ya Fito An kawoma Likita yana karɓan Takardan Ya Buɗe ya karanta kafin ya kalli Farida yana Faɗin "Wai kun ma yaranku Aure ne ba labari..? Da yake Likitan Asibitin ne ya sansu Fiye da Shekaru Huɗu So Duk yasan Mufeedan Dasu Basma.


 Farida Taji miyau mai Kauri ya Tsaya mata da ƙyar tace "A'a Dr meka gani.? Ta faɗa tana Kafeshi Da Ido. Cikin mamaki yace "Ah...Garin ya haka..? Gashi Result Ɗinta ya Nuna Tana Ɗauke da Ciki Har na Tsawon Wata Uku..." Ƙirji Farida ta Dafe Hannunta Akai Suka maimaita kalmar "Ciki.....?" Ita da Mufeeda Wacce Ta Zabura Ta Miƙe bayan Taji Kalmar Kamar Saukar Aradu Akunnenta.







*Janafty...*

*Aisha Alto..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


    *BABI NA GOMA SHA BIYU*


   Da mamaki Likitan ke binsu da kallo, Tun ma Ba Mufeeda ba Wacce Taji Zuciyarta da Jikinta Sun Tsinke Gaba ɗaya, Hannunta Bisa kai Hawaye na Zubo mata Take Faɗin "Na Shiga uku Likita Ni keda Ciki...? Wani Haushi ya kama Farida mai Haɗe da tsantsar baƙin ciki, Cikin Zafin Nama Ta Saka Hannu Ta Kwaɓe mata baki Sai da Jini ya Fito Cikin Taruwan Hawaye tace "Eh Ciki don Ubanki Ai ba ƙarya yayi miki ba, Dama munga Alamu, Son Tabbatarwa ne, kuma yanzu Mun Tabbatar, kin Cucemu Mufeeda Kuma kema kin Cuci kanki..." Ta faɗa Hawayenta Suna Zubowa Lokaci Ɗaya Ta Miƙe Kafin Ta Sanya Hannu Tana Ɗauke Hawayenta Take Faɗin "Mun Gode Dr..." Daga Haka ta Finciki Hannun Mufeeda Dake Kuka Suka Fice Daga Office D'in Kamar Walkiya, Da Ido Likitan ya bisu Abun ya matuƙar Ɗaure mai kai yaran da basu Fita Taya Wannan Abun Zai Kasance.


 Suna Fitowa Iya Ta Miƙe ko bata Tambaya ba ganin Yadda Idanuwan Farida Suka kaɗa Sukayi Jajir, ga Mufeeda na Kuka Wurjanjan Ta samu Amsarta Shiyasa bata Tsaya Tambaya ba Sai ma bin bayan Farida Datayi Wacce Ta Saki Hannun Mufeeda Tayi gaba Zuciyarta na Ta fasa da Fargaban Wani bayani Zatama goggo Abu..? Mezatace da Mahaifiyar Mufeeda..? Uwa uba Kuma Tahir Wanda Amanar Mufeeda Ya Damƙashi Ahannunta ya kuma ce Ta Kula da Ita Tamkar yadda Zata Kula dasu Basma..? Abunda yafi Ɗaure mata kai da bata mamaki Wayayi ma Mufeeda Ciki..? Yarinyar da babu Inda Take Zuwa Daga Makaranta sai makaranta kuma Makarantan ma Akaisu Adawo Dasu..? Kai Wannan Al'amari Akwai Ɗaure kai.



 Ko Acikin Adaidaita Mufeeda Keta Gunjin Kuka Farida da Iya Kuwa Suka mata banza Kowa na Saka Abubuwan Mamaki Acikin Zuciyarsa Ita Farida Baƙin Ciki ne da Kuma Kunyar Wani bayani Zatama Su Goggo Abu Akan Wannan Baƙin Labarin, ita kuma Mufeeda Kuka take Wanda Ta rasa Dalilinshi Sai Da Akace Tana da Ciki Ta Tuna Malamin Islamiyansu ya sanar Dasu Duk macen Data Fara Jinin Al'ada Akayi Abunda Tahir Daddy yayi Da Ita To Zata iya Samun Ciki, ƙananun Shekarunta bai bata Damar Fahimtar Cewa Akwai Rana mai kama Data yau ba, Kuka Take na Baƙin ciki Bakinta bazai iya Taɓa Furta Wanda ya Aikata haka gareta ba Domin Tayi Alkawarin Ko Za'a Kasheta sai ta Rufama Daddy Asiri Domin Shima ya Rufa mata Asiri Lokacin Da bata da Kowa.


 Ita ko iya Cikin Ranta Salati kawai Take, Tana Kuma Hasashe da Tunanin Waye yayi ma Mufeeda Ciki, ita bata ma kai da Nisa ba Tunani Take ko Garzali ne..? Ko maigadi ne..? Domin Iya saninta Gidan Tahir gida ne na Tsaro da Tsantsar Tarbiya, Amma Kuma Taya Hakan Ta kasance..? A iya saninta bata san Mufeeda da Wani Halin banza ba, bata da Saurayi ko Wata Ƙawar Banza Wanda Zai Nuna Alamun Hakan Zai iya Faruwa..? Kai Wannan Abu da Ban Mamaki yake.


 Suna gab da Isowa gida Wayar Farida ta fara ƙara Tana Dubawa Taga Tahir ne sai taƙi Ɗaga Kiran Don bata da Abunda Zata iya Sanar Dashi Adaidai Wannan Lokacin Zuciyarta bata da Ƙwarin Gwiwa, suna Dawowa gidan Suka Iske Su Basma Sun Dawo Daga Islamiya Nan Suke Shaidama Farida Daddy ya Dawo Megadi ke sanar Dasu Sun Tafi Asibiti Shine yayi Ta Kiranta bata Ɗaga ba Sun Tafi masallaci Shida Muda da Bassam, Farida batayi magana ba Illah Hayewa Sama Datayi, Ranta Duk ba Daɗi Itama Iya Ɗakinta ta Shiga Tana Sauke Naila Data Farka Mufeeda ko Tana Kuka ta Nufi Ɗakinta Laila da Basma Suka bita Suna Tambayanta Ko lafiya Da ƙyar Ta Iya Cemusu batajin Daɗi ne, Basma tace "Oh dama ke Momy Taje kaiwa Asibiti? Sannu Allah ya baki lafiya" Nan Laila Itama ta mata Sannu Daga nan Suka Fice Daga Ɗakin Suna masu Tausaya mata ganin Kukan Datake Su Azatonsu Ko Ciwon nata yayi Zafi Shiyasa Take Kuka.


 Farida ko Da ƙyar ta iya Shiga Toilet ɗinta ta Ɗauro Alwala tazo ta kabarta sallar Magriba ta Idar Kenan Tana Zaune Ta Ƙurama Saitin Makeken Gadonta Ido zuciyarta ba Daɗi Kamar mai Nazarin Wani Abu Amma Azahirin Gaskiya Tunanin Mafita Takeyi, Bata ji Shigowar Tahir ba sai da Taji Tattausan Hannunshi Akan Fuskarta yana Shafa Kumatunta Firgigit ta Dawo Cikin hayyacinta, Ta Ɗago Tana kallonshi Shima kallonta yake Cikin Mamaki yace "Lafiya..? Meyake Faruwa Ki kai nisan Tunani  Haka.? Waye ba lafiya mun Dawo Kuna Asibiti..?"


 Miyau Farida Ta Haɗiye mai Ɗaci Kafin Ta Tattaro Murmushin Yaƙe Tace "Amh..Umh...ba komai..." Ta faɗa Muryanta na Rawa Kamar zata Fashe da Kuka Tana Tunanin In Tahir yaji labari Ita Zai Ɗorama laifi yace Duk da Laifinta bata Son Zaman Gida Balle ta Fahimci Wani Hali yaran Ke Ciki.


 Wani kallo ya mata kafin yace "Ban gane ba komai ba Farida? kinga idonki kuwa..? Kuka kikayi ko menene..? Kuma baki bani Amsa ba Waye ba lafiya Kuka Tafi ganin Likita..?" Ajiyar Zuciya Ta Sauke Kafin Ta Yunƙura Ta Miƙe Tana Zame Hannunta dake Cikin na Tahir Hijabin Jikinta ta Cire Tana Ƙoƙarin Isa gaban Makeken Wardrope Ɗinta Take Faɗin "Mufeeda ce take Fama da Zazzaɓi Tun Jiya Shine mukaje da Ita Taga Likita."



Lokacin da Farida Ta Ambaci Mufeeda sai da gaban Tahir ya faɗi, Haka yake Fama Da Faɗuwar Gaba Kwanan nan Duk Sanda Zaiga Mufeeda Ko Kuma yaji Muryanta ko Wani ya Ambaci Sunanta, Toh Hakan sai ya faru yanzu ma Tunaninsa bai taɓa bashi Ciki Mufeeda ke dashi ba Shiyace yace "Tun Jiya kuma..? Shine sai yau zata ganin Likita..?" Ya faɗa Cike da Nuna Kulawa, Farida na Maida Hijabinta Cikin Durowarta Tace "Kasanta da Nuƙu Nuƙu bata Sanar ma Kowa ba Nima Ɗazu ne Iya ke Sanar Dani Ko Islamiya ta kasa Zuwa.."


 Numfashi ya Sauke kafin yace "Naji yanzu me Likitan yace..? Ya jikin Nata..?" Kamar tayi Ihu Da Tambayoyin Tahir Amma Sai ta kanne Cikin Sanyin Murya tace "Taji Sauƙi Zazzaɓi ne ya Dubata ya bata magunguna.." Kai Tsaye yace mata "Wani Dr Kuka gani..?" Gabanta na Faɗi bata juyo ba Saboda Kada ya Fahimci Halin Datake Ciki Tace "Dr Salis ne..." Miƙewa yayi yana Faɗin "Ok yayi kyau Zan kirasa Zamu yi magana." Ya faɗa yana Ƙoƙarin Ficewa Daga Ɗakin.


 Zuciyar Farida na Lugude Ta Waigo Da Sauri bakinta na Rawa Tace "A'ah...Ka..karka kirashi Bafa Komai Abban Basma Zazzaɓi ne Kuma ya bata magaunguna." Ta faɗa Zufa na Ketomata Saboda bata Shirya Tahir yaji maganar nan kai Tsaye ba, Tsam yayi yana Binta da Kallo Cikin Mamakinta yace "Shikenan.." Ya faɗa yana ƙara Karantar Yanayinta, ganin Haka yasa Ta saki Dariyan yaƙe Kamar Wata Sakarya bai ƙara magana ba Ya sakai ya fice yana Girgiza kai,Tana ganin ya Rufo mata Ƙofa ta Saki Ajiyar Zuciya haɗe da Sauke Numfashi Lokaci Ɗaya.


  Bayan Fitarshi Falon Ƙasa ya sauko yaso ya Shiga Ɗakin Mufeeda, Yaga Jikinta Amma Sai ya samu Wayar Ishaq akan yana Haraban Gidanshi ya Fito Su Tattauna nan ya fice Suna magana kan Wasu Sabbin Motoci ne da zasu zo Daga Kwatono gobe Sun Ɗauki Lokaci mai Tsawo kafin Su Rabu Wanda yayi Ya Shiga Su gaisa da Farida Amma yaƙi yace Dare yayi Dole ya Ƙyaleshi Suka Rabu Akan Sai gobe in Sun Haɗu A office, koda ya Shigo Falon ba Kowa Su Basma da Bassam Har Sunyi Dinner ɗinsu Sun Shige Ɗakunansu, Kan Teburin ya Nufa yaja Kujera ya Zauna yana Murmushi Shi kaɗai ganin Tuwon Shinkafa miyar Kuɓewa Ce Ɗanya Yana Son Abincin Sosai bai Damu da Cin Abincin dasu Basma Sukayi ba Tunda Shi ya Saka Dokar Daga yanzu Adaina Jiransa Sai yazo Kana Ayi Dinner, nan ya Zauna yaci Tuwon Sosai bayan ya gama ganin Dare Yayi sai ya Haƙura da Shiga Wajen Mufeeda ya barshi Sai da Safe, alokacin Kuma Daya Shiga Zai Isketa ne Tana Kuka.


 Farida Kuwa Lokacin da Tahir ya Fita ta Daɗe Zaune Tana Tunanin Mafita, kafin Ta Janyo Waya Ta Kira Goggo Abu bayan Goggo Abu Ta Ɗauka Sun gaisa Kawai sai Farida ta Fashe Mata Da Kuka Nan Hankalin Goggo Abu ya Tashi nan da nan Ta Shiga Tambayanta A ruɗe Akan Abunda ke Faruwa, cikin Kuka Farida ke Zayyanama Goggo Abu komai game da Abunda Likita yace na Mufeeda Nada ciki, Wani Razana Goggo Abu Tayi Tana Kan Gadonta ne sai da ta Wuntsulo Ƙasa Saboda Razana da Maganar Farida Innalillahi Kawai Take Maimatawa kafin Ta samu Zarafin Magana Farida ta kwaso Rantsuwan basu san Wanda ya Aikatama Mufeedan Haka ba, Goggo Abu na Share Zufa tace "Farida Ita Mufeeda bata Faɗi Wanda ya yi mata Cikin ba? Na shiga Uku ni Zainabu Abu Mezan cema Uwar yarinyar nan..? Ta faɗa Tana Sharɓe Kwallah.


 Farida tace "Ban Tambayeta ba Goggo Na shiga Ruɗani bana So Tahir ya Fahimci komai goggo laifina Zai gani.." Goggo Abu Tace "Wannan ba Hujja bane Farida Ya zama Dole Tahir ya sani, Babu yadda zamuyi Farida Dole maganar nan Zata Shiga Kunnan Waɗanda ya kamata, yanzu zan Shiga Wajen Hakimi mu Tattauna gobe in Allah ya Kawomu zan ma Tahir Waya ya Turo Direbansa ya Ɗauko mu Nida Hakimi da Ita Fulera ɗin sai Asan Abun yi..." Farida ta saka Kuka Tana Faɗin "Wayyo Goggo nasan Laifina za'a gani Amma ko Shegiyar yarinyar nan Ta Cucemu.." Goggo Abu Tace "Ba kaɗan ba Farida bar Kuka Gobe in Allah ya kaimu zatayi bayani Don Ubanta.." Daga Haka Suka Rabu bayan Goggo Ta Jaddada mata Gobe Suna Tafe.


 Daga nan Zuciyarta taƙi NaTsuwa, Sai kawai ta Latso Nombar Umma Kano Ta Ɗauka Kenan Kafin Tayi magana Farida ta Sanya mata kuka Hankalinta Tashe Take Tambayanta lafiya...? Farida ta Buɗe baki Zatayi mgana sai Wayarta ta Ɗauke Ɗif ba Chaji Taji Haushi Sosai taso ta sanarma Umma Halin Da'ake Ciki, Da hanzari ta tashi ta Jona Chaji sai ta Sha'afa bata Kunna Wayar ba Ita Kuma Umma Daga chan ɓangaren Tayi Ta Neman Farida bata samu ba, Ta maida Akalan Kiranta kan Tahir Shima kamar Haɗin baki bata Sameshi ba Ashe ya sanya Wayarsa A Fligt mode bai sani ba, Hankalinta a tashe ta samu Abba Tana gaya mai Shima Ya shiga Ruɗu Amma sai ya lallashi Umma da cewa Gobe in Allah ya yarda sai Su Tafi Kadunan Tare Shima Dama Zai je Saboda Zuwan Sabbin Motocin nan, Da Haka Umma ta Ɗan Saki Amma Ranta ba Daɗi Jin Kukan Farida Tana Fatan Allah yasa Lafiya.


 Shiko Tahir Daga nan Ɗakin Farida ya Nufa, Farida na Zaune gefen Gado Sanye da kayan Barci masu Taushi Tana Jin Motsin Tahir ta Sulale Bisa Gado Taja Bargo Ta Rufe Jikinta Lokaci Ɗaya Tana Kulle Idanuwanta, yana Shigowa ya Ƙaraso bakin gadon yana Kallonta ganin kamar Tana barci ne sai bai Tasheta ba Illah Ranƙwafawa Dayayi ya Sumbaci Goshinta Kafin ya ƙara gyara mata Blanket d'in Wutar Ɗakin ya Rage ya Kunna mata Dum light, Kafin ya Fice Daga Ɗakin ya Rufo mata Ƙofa ya Nufi Bedroom ɗinsa, yana Fita ta Buɗe Ido tana Sauke Numfashi kafin Taji Kwalla Ta Cika mata Ido, Farida Nadama ta Shigeta Alokacin da Komai ya Riga ya gama Kwaɓe mata.



********


Washegari Tun Safe Tahir ya Fita Office, Saboda Bakin Da zasu zo yau ɗin Kuma Sunyi Waya da Abba Tun jiya Dama yasan Da Zuwanshi Bai Dade Da Isa Company ba Wayar Goggo Abu Ta Iskeshi Inda Tace ya Turo musu Direba Zasu Zo Ita da Hakimi da Fulera Mahaifiyar Mufeeda Abun ya bama Tahir mamaki Sosai ya Shiga Tambayan Goggo Abu Wani Abu ya Faru ne...? Amma Sai tace Kar ya Damu In Suka Zo Zaiji Komai, Abun ya bashi mamaki barin Ma Datace Harda Hakimi, wanda Hakimi baya Zuwa Kaduna sai da Ƙwaƙƙwaran Dalili Mai karfi Amma Ko Ɗaya Zuciyarsa da Tunaninsa basu kawo masa Wani Abu mara Daɗi ya Faru ba, Ya mafi karkata Alaƙan Zuwan nasu ƙila ko Farida ce Takai Ƙararshi Toh Amma Ai yanzu basu da Wata Matsala, Haka dai ya gama Duk Tunaninsa Bai Hango Dalili ba Duk da gabansa na Faɗi bai Ɗauki Abun Nada Nasaba da Haka ba.


Ita ko Goggo Abu Tun Adaren Jiya Ta Isa Turakar Hakimi ta Zayyana mai komai Salati da Sallallami Hakimi ya Shigayi Cikin Ruɗani da Tashin Hankali Sun Daɗe Suna Jajanta lamarin, har Innaro Tazo ta Samessu Itama Taji Ɗimuwa Dataji Wannan Lamarin Daya Faru Haka Suka Zauna Jugum Jugum Abun Duniya ya Ishesu, Hakimi Shi ya yanke Hukunci Kada Asanar da Fulera Abunda Ke Faruwa sai Sun Isa Kaduna Allah barshi Sai Lokacin Taji Komai, Da haka Suka Rabu Innaro Ta Koma Shashenta Ta Kwanta Cike da Mamakin Faruwar Wannan Al'amarin Hakimi da Goggo Abu Kuwa basu Runtsa ba Suna zullumi da Tunanin Yadda Mutane zasu Ɗora musu Laifin Duk Abunda ya Faru.



   Garzali ya bama Umarnin ya tafi Ɗanbatta ya ɗauko su Goggo, Ya koma Office Kenan Sai ga Abba ya iso, nan yake Shaida ma Tahir Cewa Tare da Umma Suke sun ajiyeta Gidanshi Abun sai ya Ƙara Ɗaurema Tahir kai barin ma Da Abba ya Shiga Tambayanshi Duk Gidan Lafiya ba Abunda ya Faru..? Yace mai ba komai, jin Haka sai suka Watsar da Zencen Suka Cigaba da Tattauna Batun Motocin nasu da zasu iso yanzu ba da Daɗewa ba.


Umma kuwa Tana Isowa Farida na Cikin Ɗakinta bayan Su Basma Sun gama mata Oyoyo Suka gaisa da Iya, Ta Haura sama Wajen Farida Wacce Ke Kwance Tana Tunanin Mafita, Sai kawai Taji Sallamar Umma Lokaci Ɗaya Tana Kiranta Zumbur Ta Miƙe Ta Isa gareta ta Rungumeta Lokaci Ɗaya Ta Fashe da Kuka Umma Ta Fara Lallashinta Ta hanyar Bubbuga Bayanta Sai da Farida Tayi Kuka mai Isarta kana Ta Sanar da Umma Abunda Ke Faruwa.

 

 Ƙirji Umma Ta kama Tana Salati Lokaci Ɗaya Idanuwanta Duk A Bude Tana Tsaye ne Sai Da Ta Zauna Hannunta Duka biyu Bisa kai Tana Tambayan Farida garin ya Haka ta Faru..? Farida na Kuka Take Faɗin bata sani ba Wallahi...? Nan Take Shaida mata Abunda goggo Abu Tace Suna Tafe Yau Tagumi Umma Ta Buga Ta fara ma Farida Faɗan Rashin Kula da Sakaci Metake Tunani in Itama Basma Ta faɗa irin Wannan Halin..? Tunda Da Mufeedan Da Basma duk Tare Suke Ita dai Farida Kuka Kawai Take Tana Jin Kunyar yadda Duka kowa zai Bata laifi Amma Maganar Gaskiya Mufeeda Ta Cuceta Wallahi.


    Wajen 12pm na Rana Su Hakimi Suka Iso gidan Tahir Farida Ta karɓesu Hannu bibbiyu Amma Da Faɗuwar Gaba Nan Suka Iske Umma, basu yadda Sun Tada maganar ba saboda Inna Fulera Wacce Tana Zuwa 'yarta ta Fara Nema,Wacce ke Ɗaki Dunƙule Tana Kuka Lokacin Data Ci karo da Fuskar Inna Fulera sai Rauni da Kunya Suka Zomata ta ƙanƙame Innar ta ta Tana Kuka Ganin Haka sai Jikin Inna Yayi Sanyi ta Zaunar Da Ita gefen Gado Tana Tambayanta Lafiya meya ke Faruwa..?" Don Goggo Abu bata mata Wani bayani ba, ta dai ce Ta Shirya Suzo Kaduna Jin Haka Yasa Jikin Mufeeda ya fara Rawa Kamar Mazari Idonta ya fara Zubar da Kwalla, Tana Tunanin Ya Zatayi in Aka Turketa sai Ta faɗi Wanda yayi mata Cikin..? Uwa uba ga Innarta Wani Hali Zata Shiga Intaji labari..? Ƙanƙameta Innar Tayi Ita Kuma Mufeeda tana Faɗin "Inna Kiyafemin Ba Laifina bane, Jin Haka sai gaban Innar ya faɗi Ta fara Tunanin Allah yasa Ba Wani Laifi Mufeeda ta Aikata Musu mara Daɗi ba, Gashi Kuma Mufeedan Taƙi magana sam balle Taji Abunda ya Faru.



Motocin Sunzo ba Daɗewa sai ga Kiran Goggo Abu Tace maza maza Tahir yazo gida yanzu nan, Sun Iso sai Lokacin ya ƙara jin Mutuwar Jiki Sosai da Faɗuwar Gaba, jin Haka yasa Abba Shima Direba ya Wuce Dashi Shi Kuma Ishaq ya Ɗaukosa Zuwa gida Suna Tafe Suna Fatan Allah yasa Lafiya.


 Lokacin da Suka iso gidan Ishaq yaso ya koma Company Sai Tahir ya Matsa mai ya Shiga Ya gaisa dasu Hakimi Suna Dumfaran Falon Suka Fara Jin Shessheƙan Kuka da Koke koke Da Hanzari Tahir ya Fara Shiga Falon Ishaq na Binsa Abaya Idanuwansa Sukayi Tozali da Mufeeda, Wacce ke Durƙushe Tsakiyar Falon Tana Gunjin Kuka ga Inna Fulera gefenta Itama Tana Kukan ga Farida Zaune A ƙasa Kusa da Goggo Abu sai Hakimi dake Zaune kan Ɗaya Daga Cikin Kujerun Falon Shida Abba, Sai iya Dake Zaune chan gefe Kowa ka kallah Fuskarsa ba Annuri.


 Lokaci Ɗaya gaban Tahir ya yanke ya Faɗi Yaji Jiri na Neman Kadashi, sai da Ishaq dake bayansa ya Riƙonsa, Idanuwansa Sun Fito Waje yake bin Kowa da Kallo Kafin ya maida kallonsa kan Farida Cikin Sarkewar murya ya Furta.." Fa...Farida...Meya Ke Faruwa...?" Ya faɗa suna ƙarasowa Cikin Falon, Jin muryansa yasa Duka Ido ya koma kanshi Cikin Damuwa goggo Abu Tace "Yauwa Attahiru Dama kai muke Jira kazo ka Tambayi Mufeeda Wanda yayi mata Cikin Jikinta Tunda Dukkanmu Taƙi Sanar damu komai..."



 Ba Tahir kaɗai ba Hatta Ishaq Sai da Yaji Wani Abu ya Tsirga mai Daga Kwakwalwarsa, Shiko Tahir Kwalalo Ido yayi kamar Idonshi zai Fito Waje, Mufeeda Data Ɗago Kanta Tana Kuka Idanuwanta Suka Kumbura Suka Haɗa Ido da Tahir Wanda Jikinsa Ke Rawa Zuciyarsa na Gudu Naman Jikinsa na Cida Zufa na Keto mai Cikin Wani yanayi ya Saluɓe Hannunsa ana Ishaq ya Sulale A ƙasa yana Maimata kalmar "Innalillahi Wa'inna Ilaihirraju'un"un..." Sai ga Hawaye Suna Fitowa Daga Cikin Kwarmin Idanuwansa.


 Ba Wanda yayi mamakin Halin Da Tahir ya Shiga Sanin Halinsa Mai Ƙoƙarin Kyautatama Kowa, Inna Fulera tana Kuka Take Faɗin "Mufeeda Meyasa Kika min Haka..? Zuciyata ta kasa yarda da Wannan maganar ki ƙaryata ko kuma ki sanar damu Wanda Kika bama kanki yayi miki ciki.." Ta faɗa Tana Kuka Girgiza kai Mufeeda Ta Hauyi Tana Kuka Take Faɗin "Kiyi Haƙuri Inna Ba Laifina bane, Amma bazan iya Faɗar Wanda yamin Wannan Cikin ba Ko zaku Kasheni.." Ta faɗa tana kallon Tahir Wanda Ya Ɗago yana kallonta, Jin Haka yasa Inna Fulera ta Taso da Hanzari ta Isa ga Mufeeda ta Fara Dukanta ta Ko'ina Tana Faɗin "Allah ya isa Tsakanina Dake Mufeeda zan ko kasheki kowa ya Huta da Na Dinga Kallonki kina sakani Baƙin ciki da Takaichi..."


 Kuka Mufeeda Keyi Inna Fulera nayi Tana dukanta Farida ma Kukan Take Kafin Wani yayi magana Tahir ya Miƙe ya isa Ga Inna Fulera ya Duƙa agabanta bayan ya Shiga Tsakaninta da Mufeeda ya kalleta yana Zubar da Hawaye, Bakinsa na Rawa zai Fara Magana Ishaq yace "Don Allah Tahir kar kace Komai na Roƙeka..." Tahir ya Runtse ido kafin yace "Kabarni na Faɗa Ishaq Gwara Kunyar Duniya Data Kiyama..." Ya faɗa Hawaye na Kwararo mai.


 Gaba ɗaya Falon kallo ya Koma kan Tahir Cike da Mamaki, barin ma Farida wacce Kukan Tahir ya fara Tsorata ta, Babu Zato kawai Sukaji Tahir na Faɗin "Bazata Taɓa Faɗa muku Wanda yayi mata...don Ba kowa bane Face Ni...ni...na mata Cikin Jikinta...." Ya faɗa yana Rushewa da Kuka Numfashisa na Sama Sama, Gaba ɗaya Falon Kowa ya Kwalolo Ido, Matan Gaba ɗaya Suka Miƙe Farida Wacce Ta Ɗora Hannu Akai ta Zaro Ido Tana Faɗin "What....? Kace kai kayi mata Cikin...?"



 

  *Aisha Alto...*

*Shakira...*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕



_Dont Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


       *BABI NA GOMA SHA UKU*


Gyaɗa kansa yayi hawaye masu zafi da raɗaɗi na zuba daga cikin idanunsa ya duƙar da kai ƙasa yace "Tabbas nine nayi mata ciki...cikin jikin Mufeeda nawa ne bana wani ba..." Yana faɗa ya sake rushewa da wani irin kuka mai taɓa zuciya da ban tausayi. Itama Mufeeda ƙara sautin kukanta tayi da ƙarfi zuciyarta cike da tausayin Daddy ta tsura masa ido tana ji a ranta dama wannan ranar bata zo musu ba.


Gaba ɗaya falon salati suka ɗauka kowa faɗi yake "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...." Yayinda ita ko Farida ta ƙara gigicewa ta ruɗe da jin kalaman da Tahir yake faɗa, lokaci ɗaya komai ya tsaya mata cak, sai aikin nunashi take da yatsa tana girgiza kai ta kasa magana, kafin ta koma da baya ta faɗa saman kujera daɓas ta zauna a ruɗe tana faɗin "A'a Abban Basma don Allah kar kace haka...wannan nasan ba gaskiya kake faɗa ba...nasan ba halinka bane a ko'ina kuma zan iya yin shaidarka akan haka...kuma nasan kowa ma zai yi shaidarka indai akan haka ne, nasan ko akan wata bazaka taɓa iya aikata haka ba, balle akan Mufeeda 'yar damuka raina muka ɗauketa tamkar 'yar da muka haifa da cikinmu...plz Abban Basma karka sakamu cikin wani yanayi plz kace ƙarya ne abinda ka faɗa ba gaskiya bane...don Allah kace ƙarya ne Abban Basma.." Ta faɗa tana ji a zuciyarta dama a tasheta ace mafarki take ba gaskiya bane abinda kunnuwanta suke jiye mata ba.


Yana kallonta da idanuwansa da suka rine sukayi jajir suna tsiyayar ruwan hawaye yace "Tabbas Farida abinda na faɗa gaskiya ne, kunnuwanki sun jiye miki dai-dai...cikin dake jikin Mufeeda nawa ne...nine na yiwa Mufeeda ciki..cikina ne...amma a bisa ƙaddara data faɗa min ba'a son raina ba..." Salati duka falon suka ƙara ɗauka, kafin Inna Fulera ta fashe da kuka mai sauti ta miƙe ta cakumi Mufeeda ta fizgota ta rufeta da duka baji ba gani tana yi tana kuka take faɗin "Kin cuceni kin cuci kanki Mufeeda, kin wulaƙanta rayuwarki kin tozarta kanki...Allah ya isa tsakanina dake..ki rasa sakayyar da zakiyi min sai ta abun kunya...kina marainiya kin zubarwa kanki kima da mutunci...Allah ya gani iya tarbiyya na baki ita dai-dai gwargwado ban san kuma meya shiga kanki ba har kika iya watsar da mutuncinki a titi ba..." Ta faɗa tana ƙara shurinta da ƙafa tana kuka, Mufeeda ma kukan take tana jujjuya kanta amma ta kasa tashi ta ƙwaci kanta, da sauri Tahir ya matso ganin Inna Fulera ta ɗaga ƙafa zata taka cikin Mufeeda tana faɗin gwara na kasheki da inci gaba da ganinki ina jin baƙin cikinki a raina, da hanzari ya riƙeta yana girgiza kai a hankali yace "Laifina ne Inna, ita da niyyar taimakona tazo, dukkanmu bada niyya mukayi ba...ƙaddara ce ta afka mana..." A fusace Farida ta miƙe tana faɗin "Babu ruwan ƙaddara Malam, dama can kana da niyyar aikatawa shine zaka fake da ƙaddara..." Ta faɗa tana fashewa da kukan takaici da baƙin ciki tana faɗin "Amma Tahir ka cuce ni ka cuci zuri'arka ka wulaƙantamu, yanzu da wani irin idanu kakeso a kalli 'ya'yanka? Ka ɓata mana sunan zuri'a, ka haikewa 'yar da take ɗaukarka a matsayin uba...tirr da kai da irin halinka, wallahi bazan iya ci gaba da zama da kai ba, ni ba fasiƙa bace don haka bazan zauna da fasiƙi ba...sai dai ka zauna da ita da shegen cikinku..." Ta faɗa tana ƙara fashewa da kukan baƙin ciki da takaici tana kallon Mufeeda dake kukan itama tana ji kamar ta tashi ta shaƙeta har sai taga bata numfashi.


Wani murmushin dayafi kuka ciwo Tahir yayi yana kallon Goggo yace "Komai da ya faru bada son raina bane kawai na ɗauki hakan ne a matsayin ƙaddarata kuma na karɓeta hannu biyu, Allah ya bani ikon cin jarabawata... Nan take ya shiga bada labarin duk abubuwan da suka faru, kafin yana kuka ya ɗago yana faɗin "Duk da wannan abun daya faru dani ba kowa bane sanadin shigata wannan halin sai Farida dake Goggo, domin ke kika hanani na sanarwa Baba Hakimi wannan matsalar dake faruwa dani kuma kika hanani maganar ƙara aure, alhalin baki taɓa tambayata dalilin da yasa na nace inaso na ƙara auren ba, sai dai a kullum idan naje miki da maganar irin abubuwan da Farida take yi min sai kice inyi haƙuri zaki mata magana, zata gyara, baki taɓa nuna damuwarki akan halin da nake ciki ko ki tambayeni abinda yake faruwa ba, sai dai dana fara sai ki katseni kice bakyason ayi abunda zumunci zai lalace...Goggo ni ɗanki ne amma baki taɓa damuwa da matsalata ba, domin baki taɓa bani damar nuna miki damuwata ba, sai dai ma kiyi ƙoƙarin hanani faɗawa mahaifina halin da nake ciki, to yau ga abinda kika jawo min nan..." Ya faɗa tare da juyawa yana kallon Farida data daskare a zaune ta kasa ko ƙwaƙƙwaran motsi hawaye sai zubowa suke a idanunta, Girgiza kansa kawai yayi yana faɗin "Kuka ai yanzu kika fara yinshi Farida, domin tun asali abunda na dinga gujewa faruwarsa kenan a tsakanina dake...Nayi haƙuri har na kai maƙura amma Farida baki canza halinki ba, nayi ƙoƙarin gyaraki amma baki gyaru ba...kin ɗauke ni tamkar ba mijinki ba, baki maidani a bakin komai ba, baki san ki sauke hakkina dake kanki ba, baki san ki kula da 'ya'yan da Allah ya baki ba...sai dai kullum kina yawon bin gidan bikin ƙawaye, baki san ki tambayeni fita ba, sai dai duk lokacin da kikaso kiyi fitarki kuma ki dawo duk lokacin da kika so ba abunda ya dameki, na nuna miki nima fa mai lafiya ne ba dutse bane kuma dole ne in nemi hakkina a gurinki, amma yawon zuwa gurin biki ya hana ki zauna ki kula dani da 'ya'yanki...kullum baki nan baki nan, kuma kinsan ban ajiye wacce zata kula dani bayan ke ba, tunda ke kaɗai gareni baki damu da wane irin hali zan shiga ba, kedai kawai abunda ya shafeki kuma ya dameki shi kikeyi, 'ya'yan da kika haifa kin barwa masu raino baki damu da tarbiyyarsu ba, baki damu da halin da zasu shiga ba, kedai kawai ki tafi biki..sai kibar gidanki da mijinki da 'ya'yanki babu abunda ya dameki, babu ruwanki da duk irin halin da zamu shiga, Saboda Haka Dukkan abunda ya Faru Tsakanina da Mufeeda Keda Goggo kuna da Alhaki akai..."


Ya faɗa yana Matse Ƙwallah, gaba ɗaya Falon ya Ɗauki Shuru banda Kukan Mufeeda dana Farida sai Inna Fulera sai na Goggo Abu Dake Tashi ƙasa ƙasa, wani mugun kallo Baba Hakimi ke Jifan Goggo Abu Dashi Lokaci Ɗaya Zuciyarsa na Lulluɓewa da Ɓacin Rai kukan Tahir Tamkar Saukar Dalma ne Cikin Ranshi Cikin Tsawa yace "Kukan me kike Zainabu...? Ai bai kamata kiyi Kuka ba Tashi zakiyi ki Taka Rawa kiyi Murna Kin Yi Sanadiyar Lalata Rayuwar Ɗanki Wanda Kika Haifa da Cikinki. Tir Dake Abu Wallahi Yawonki Da Girmanki Amatsayinki na Uwa bai amfaneki da Komai ba sai Sakarci Yanzu ace Ɗanki yazo ya Sameki da Irin Wannan maganar ki kasa gayamin Abun baƙin ciki kuma kin Hanashi ya Sanar dani..? Ke Har Kin isa ki gyara Abunda Allah bai gyara ba Wato kin Hanashi ƙara Aure Amma baki Taɓa Tunanin ina zai kai Lalurarsa ba kanki kaɗai kika sani Sai Wani Dalilinki mara Tushe Ballantana Makama, Wallahi Tallahi ina so ki Sani Duk Zunubin dake Kan Tahir Akan laifin Zina Dake da Farida za'a Rabawa Domin kune kuke da alhakin Duka Abunda ya Faru..Babu Abunda Zance miki sai godiya kin kuma kyauta.." Ya ƙarashe Faɗa yana Share ƙaramar kwallarsa Data Zubo mai Cikin Tashin Hankali.


Su Basma da Bassam da Muda da Laila Dake laɓe A koridon Ɗakin Basma Kuwa kuka Suke Ka Shirɓan na Tausayin Kukan da Daddynsu yake Duk Abunda aka faɗa kaf Acikin kunnuwansu Lokaci Ɗaya Sukaji Sun Tsane Farida da Komai nata ganin Itace Silan Shigan Daddynsu Wani Hali Hartana Sanyashi kuka dama ba Tun yanzu ba Rashin Kula Dasu da batayi yana Tsaye Acikin Ransu kuma Suna jin Haushin hakan gashi Dalilin Sakacinta Ta saka Daddynsu Cikin wani Hali, Basma Da Laila Suka haɗa kai Suna kuka yayinda Muda da Bassam Suma Suka Ɗora kai Agwiwa suma Suna ta kukan Tausayin Daddynsu.


Goggo Abu ko Kuka Take ba Bakin magana Maganganun Hakimi Sun Shigeta Sosai Tahir Kaɗai Take kallo Tana Jin Ta zama Sakaryar Uwa Mara Damuwa da damuwar ɗanta Data Haifa da Cikinta Innaro ko Tana gefe Itama tana Sharan Ƙwallah Tausayin Tahir na Jarabawar da Allah ya masa, Domin Wanna Jarabawa ce Domin Ajaraba Imaninsa Abba ko Wani Kallo yake Wurgama Farida Dake Jikin Umma Tana Kuka Ita kanta Umma Kukan Take Sharewa Lokaci Ɗaya Tana Faɗin "Muma muna da laifi ba Goggo  Abu da Farida bane keda alhaki Akan Wannan Abun ba Harda mu kanmu iyayen Farida bamu Taɓa Lura da Irin Ƙararta da Tahir yake kawo mana ba, ko yazo ya Faɗama bama Nuna mata batayi Dai dai ba sai ma Mu kama lallashinta Cikin Soyayya musamman ni dana kasance Uwa agareta Wacce Nafi kusanci da Ita, Gatan da Muka Nunawa Farida Shiya Sangarta ta bata iya zama Gidan Mijinta ta bashi Dukkan kulawa, Muma muna da Laifi Muna Dashi muma.." Ta ƙarashe Faɗa Tana Sharɓan Kuka.


Abba yace "Haƙiƙa maganarki gaskiya ne Aliya muna da laifi Wajen Rashin Nuna ma Farida Muhimmancin Mijinta Hakika bamu kyauta ba..kuma bamu kyautama Tahir ba Domin Yayi Haƙuri da Ita Tun bayan Auresu, Dukkanmu bamu Taru mu Duba Halin da Tahir zai Shiga ba..Duka laifin namu Ne sai dai muyi fatan Allah ya ya yafe mana Gaba ɗaya..." Baba Hakimi ya amsa da Ameen Ishaq na gefen Tahir yana Ɗagoshi Amma yaƙi ɗago kansa Saboda Hawayensa Sun kasa Daina zubo mata Baba Hakimi ya Kalli Inna Fulera yana Faɗin "Fulera ki Daina Ma Mufeeda mugun baki kinji da Kunnenki Duka ba laifinsu bane, Ki saka mata albarka ki kuma kalleta kice kin yafe mata Babu kyau bawa ya Nuna Butulci ga Allah lokacin Daya Jarabceka da Wata Jarabawa Godiya zaki ma Allah, kar in sake jin kin aibata 'yarki.." Ya faɗa cikin Sanyin Murya gyaɗa kai Inna Fulera Tayi tana Kuka Lokaci Ɗaya Jikinta yayi sanyi Ta kalli Mufeeda Dake Durƙushe Tana Kuka Lokaci Ɗaya tace "Na..yafe miki Mufeeda...Allah ya bamu ikon Cin Jarabawarsa Haƙiƙa na Shaida ke yarinya ce mai Tarbiya Hakama Alhaji na yarda da Ƙaddara ne ta Faɗa muku Domin Dattakonsa Data iyayensa Shike Riƙe damu Har yanzu... Amma Ina Roƙon ku don Allah kada ku Zubar da Cikin ku barma Mufeeda Shi ƙila Wata rana Shi zaiji kanta ko kuma ƙila Shi kaɗai ne ƙwanta a nan Duniya.." Farida dake Jikin Umma ta ɗago Tana Faɗin "Wallahi sai yabi Rariya Uban Wa zata Haifa ma Shege..? Ba anan gidan ba Wallahi sai an Zubar Dashi..."


Ta faɗa Cikin ƙaraji Da Kuka Abba ne ya mata Daƙuwa yana Faɗin "Kinci Ubanki, Farida In na Sake jin bakinki Anan Wajen Wallahi sai naci Mutumcinki mutuniyar Banza da Wofi.." Ya faɗa yana Hararanta Umma dai ƙwallah Take Sharewa Duk Jikinta yayi Sanyi Su Goggo Abu kuwa An Shiga ƙwaryar Nadama.


Baba Hakimi ne yace "Dama waya ce miki za'a Zubar..? Haba kamar ba masu Hankali ba kenan bamu yarda da Ƙaddara ba, taya zamu aikata Wani Zunubin kan Wani Zunubin kuma..? Mufeeda zata Cigaba da Rainan Cikinta kuma ta Haifeshi da Ikon Allah Acikin gidan nan Saboda Lura, Ɗanbatta ƙauye ne In Muka Tafi da Ita labarin zai yi Tambari Gwara abarta anan Ɗin Harta Haihu muga Abunda Allah zaiyi..."


Zabura Farida Tayi Tana Faɗin "Awani gidan..? Wallahi ba a nan gidan ba..? Bata isa ta haifamin Ɗan Shege a gida ba.." Tahir Dake Duƙe ya Ɗago da Jajayen idanuwansa yace "Toh sai dai ke ki bar gidan, Amma Babu fashi kamar Yadda Hakimi yace Mufeeda zata Haihu anan gidan Insha Allahu..." Ya faɗa yana mata wani kallon Tsana Baba Hakimi ya saki Murmushin Takaici Amma ƙasan Ransa yaji Daɗin Amsan da Tahir yabama Farida.


Kuka ta ƙara sakawa kafin tace "Haka kace..? Toh Wallahi sai dai na bar gidan ni ban zauna ba...Bazan zauna gida Ɗaya da karuwarka wacce kama Ciki ba.." Umma ce ta Make mata baki Tana Faɗin "Rufema mutane baki Mara Kunya Gaban iyayenshi kike gaya mai magana Haka Irin Tarbiyar da muka baki kenan..?"


Ta faɗa Tana kallonta Cikin ɓacin Rai Durƙushewa Farida Tayi Tana Cigaba da Gunjin kuka, Abba yace "Saurareni Da kyau Farida kinga matuƙar naji labarin kinbar gidan Mijinki Wallahi sai na Saɓa miki Sakarya mara Hankali Wacce iliminta da shekarunta basu amfana mata komai ba..Wallahi in baki Shiga Taitayinki ba Naji labarin kinyi ma Tahir ko ita yarinyar Wani Abu sai nazo Har gida nan gaban 'ya'yanki na barki Kwance ja'ira kawai.." Ya faɗa Cikin Fushi da Sauri Farida Ta Miƙe ta Haura sama Tana Gunjin kuka gaba ɗaya Aka bita da kallo kafin Baba Hakimi ya kaɗa kai yana Faɗin "Ayyah Ibrahim ga Wacce Girmanta da Shekarunta basu mata amfanin komai ba nan Zainabu..ai ko banza ta Haifi Farida Tsakani ga Allah bata Fita Hankali ba..?" Ya faɗa Cike da Takaici Goggo Abu Dake kuka ta Buɗe baki zatayi magana Baba Hakimi ya ɗaga mata hannu yana Faɗin "Karma ki ɓata bakinki...Yanzu Maganarki banda ɓata min rai Babu Abunda Zatayi Gwara ma ki rufe bakinki zai fi alheri agaremu Gabaki Ɗaya.." Goggo Abu Tayi ƙasa Dakai Hawaye na Zubar mata tace "Attahiru ka yafemin...Mufeeda kema ki yafemin.." Daga Haka ta miƙe ta Fita Zuwa Haraban Gidan Tana Kuka.


Baba Hakimi ne yace "Fulera kama Ɗiyarki ku Shiga Ciki ki ƙara lallashinta kinji itama ba laifinta bane.." Jiki ba ƙwari Inna ta Miƙe ta Kama Mufeeda Da ƙyar Dake kuka Suka Nufi Ɗakinta Iya Dake gefe sai Lokacin itama ta Miƙe tana Sharan Ƙwallah na Tausayin Waɗannan Ahalin Innaro Ta miƙe Ta Bita tana Faɗin "Kai ni Ɗakinki Iya na kama Ruwa nayi sallah.." Da Toh Iya ta karɓa kafin su Nufi Ɗakinta Kowa Zuciyarsa ba Daɗi.


Umma ma Miƙewa Tayi tana Faɗin "Bari naga Farida.." Kai Abba ya gyaɗa mata kafin Ta Haura sama tabar Baba Hakimi da Abba da Tahir da Ishaq Suna ƙara Jajanta lamarin.


Umma Kwance Taga Farida na Kuka, gefenta ta Zauna Tana Faɗin "Farida...Bai kamata kiyi kuka ba kamata yayi ki zauna kima kanki karatun ta Natsu ki gyara Kuskuranki, ki kama Allah ki kuma Roƙi gafaran Mijinki ki Rungumi 'ya'yanki kinga Abunda ya Faru..? Izina ne gareki da Kuma mata masu irin Halinki Daga ƙarshe ina Ja miki kunne da ki Natsu In ba Haka ba Wallahi Dagani Har Abbanki zamu Ɗauki mummanan mataki Akanki.."



Daga Haka ta miƙe ta Fice Daga Ɗakin Tana Fitowa su Baba Hakimi na Miƙewa, nan Suka ce kowa ya Fito zasu Wuce Inna Fulera Data kai Mufeeda Ɗaki ta saka Gefen Hijabinta tana Share mata ƙwallah Mufeeda na kallon Inna Fulera Take Fadin "Inna ki yafemin...Ba laifina bane.." Murmushi Inna Fulera ta mata kafin tace "Na yafe miki 'Yata..Allah yayi miki albarka ya kuma Saukeki lafiya.." Jin Haka yasa Mufeeda Ta Rungume Inna Fulera Suka Fashe da Kuka Lokaci Ɗaya, Iya Data leƙo kiran Inna Fulera itama sai dai taji ƙwallar Sun kawo mata, muryan Iya ce ta saka suka saki juna Nan take sanar da ita ta Fito zasu Koma.


Kumatun Mufeeda ta Shafa kafim tace "Ki kula da kanki kinji ko Mufeeda..? Allah na Tare Dake..." Daga Haka ta saki Hannunta ta Fice Daga Ɗakin Tana Sharan ƙwallah kan gado Mufeeda ta zame tana kuka mai Cin Rai tana jin kamar Bazata ƙara ganin Innar ta ta ba kenan.


A waje Suka samu Goggo Abu bayan Dukkansu Sun Fito Innaro ce kaɗai ta samu yin Sallah Sauran Baba Hakimi yace in Sun Isa gida kowa sai yayi..Abinci kuwa Da Iya Ta jera ba Wanda ya kalleshi Motar Su Abba da Umma ce Ta fara Fita Daga gidan sai ta Baba Hakimi Wanda Garzali zai Maidasu bayan Baba Hakimi yaja Tahir gefe ya ƙara mai Nasiha sosai ya kuma Nusar dashi ya barma Allah komai Da Haka Suka rabu Bayan Motar Ta Fice Daga Haraban Gidan


Ishaq ma bai koma gidan ba, Daga nan Sukayi sallama da Tahir ya Shiga Motarshi ya Fice Daga gidan Bayan shima ya ƙara bama Tahir ɗin baki sosai...Ya Daɗe Tsaye yana Sauke Tagwayen Ajiyar Zuciya Lokaci Ɗaya yana Goge Siririyar ƙwallar data Siraro mai ya Juya ya tunkari Cikin Falon gidan.






*Anitha..*

*Aisha Alto..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty*💕


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_



_*Muna Mika sakon godiya bisa ga masoyanmu na nesa Dana kusa,Bisa ga yadda suka yi ta aikomana da sakon gaisuwa kama daga Masoyanmu na Whattapp da kuma Wattpad munga tarin sakonninku na Ta"aziya muna godiya Sosai Allah ya bar zumunci Muna Fatan Allah ya Sa Dukkanmu Fatima Binafa tazama mai Cetonmu Ranar gobe Kiyama Ameen..*_🤲



     *BABI NA GOMA SHA HUDU*


""""Cikin Sanyin Jiki Da Takun Jarumta ya Shigo Falon,Babu Kowa ya Tsayawa yayi Shuru yana Bin Dakin Mufeeda da kallo Wani Zuciya yana Tambayanshi Ko Wani Hali Take Ciki..? Ganin bashi da Amsa ne ya sanya ya Kada kai ya Fara Kokarin Haura Steps yaji Muryan Basma Tana Fadin"Daddy... "..


Da Sauri ya Juyo yana Kallonsu Ita da Bassam da Laila da Madu Sun Kuramai Ido Fuskokinsu Cikin Damuwa da alamun ma Basma Tayi Kuka ne,Gabansa ne ya Fadi Kunya Ta kamashi Yama manta Sam da yaran Da wani Ido Zai kallesu bayan Sunji Abunda ya Aikata..? Cikin Karfin Hali ya Furta.."Basma Wht hpped....? Yafada Cikin karfin Hali.


Kuka ne ya Kwace mata Da Gudu Ta Isa gareshi Ta Fada Jikinsa Ta kara Sakin Kuka Kamar Wacce Aka Daka,Hakama Bassam Ya Rugo Shima ya Fada bayan Basma Shima yana Kuka Tahir ya Rutse Ido kafin ya Dora Duka Hannuwansa bayan Yaran Nashi yana Bubbugawa alaman Lallashi Idanuwansa ya Bude da Suka kara kadawa Sukayi Jajir ya Sauke kan Muda da Laila Dake Tsaye Suma Suna Share Kwallar..


Hannu ya Mika Musu Alaman Su Taho Suma Da Gudu Suka Taho Suka Fada Jikinshi Yahadasu ya Rumgume Cikin Kuka Basma Ke Fadin"We Relly Srry Daddy.,Momy Ta Cuceka Daddy Mun yadda Muna Son Cikin Mufeeda Ta Haifama kani.."Take Fada kamar Wata Babba Wani Yam Tahir Yaji Cikin karfi Hali ya Sakesu yana kallon Cikin Idanuwan Basma ya Dafa kanta yana Fadin"Nothing To be Worry My Dota,Stop craying and Kar nakara Jin Sunan Momy ku Abakinki balle kice ta Cuceni koma Menene She is my Wife Ku ma,Kuma Mahaifiyarku ce So Stop All dis Kinji ko..?.

  

Gyada kai Tayi Tana Share Kwallarta Kafin ya Saki Kanta yana kallonsu  Dukkansu Cikin Karfin Hali yace"And All Dis..Don't let Anyone Know abount It kunji Ko  Amkaranta Karku Sake Kuyi Zencen da Wani Kuma Laila Koda Kun Koma Gida ko Mamanku karku Fadamwa Kunji.."Kai Suka gyada Kafin Su Hada baki Suka ce"Insha Allahu Daddy We are going To Hide Dis Secret.."


Mirmishin Dayafi Kuka Ciwo ya Hadiye kafin yace"Ok..Muda da Bassam Kuje kuyo  Alwala naji  Ana Kiran Sallar Mangarib,ku kuma Ku Koma Daki Kiyi Taku sai Mun Dawo ."Da kai Suka amsa kafin Kowannensu Ya Juya Basma da Laila Suka Nufi Dakin Basma Hakama Bassam da Muda Suka Nufi Dakin Bassam Din Ko bakomai Zuciyarsu Ta Warware ba kamar Dazu ba....

  


  Sai da Suka bacemai kana ya Kada kai ya Fara Taka Steps Cikin Sanyi Jiki,ya Dade Tsaye Kofar Bedroom Din Farida yana Nazarin Wani Abu kafin ya Cije Lebe ya karisa Cikin Bedroom Dinshi Tiolet ya Fada agurguje yayi Wanka yazo ya saka Wata bakaer Jallabiya da Hula ya Dau Carbinsa ya Fito,Afalo Suka Hadu dasu Muda Suma Sun Fito nan da Nan ya Rike Hannayensu Suka Fita Zuwa Masallaci.


***


Mufeeda Kuwa Bayan Fitan Inna Fulera Kan Gadonta Ta Fada Tana Gunjin Kuka Wani Tsausayin Kanta Dana Tahir na Kara Kamata Zuciyarta Tana mata Rawa In Ta Runtse Ido Ta Tuno Sanda yake Mgana yana Zubar Hawaye bazata Jura ganin Hawayen Tahir ba Tana Jin Abun Acikin Ranta Bata da yarda Da Zatayi ne.


Tana Cikin Wannan Halin ne Iyya Tazo ta Sameta,Zama Tayi Gefen Gado kafin Ta Dagota Tana Fadin"Mufeeda...Mufeeda..."Tafada Tana Dago Fuskarta Wacce Tayi Faca Faca Da Hawaye Sosai Cikin Mutuwar Jiki da Tsausaya Iyya Ta Fara Fadin"Mufeeda,Kibar Wannan Kukan Kinji ko..? Bashi da Wani Amfani Tunda Mai Afkuwa ta Afkuwa...'Tafada Tana Share mata Hawaye Da Hannunta Duka Biyu.


Kuka ya kara Ciyo Mufeeda Sai ta Sulale kan Cinyar Iyya Tana Yi Tana Fadin"Ya zanyi iya..? Na batama Kowa Rai Ba laifina ba..Bansan Haka zata Faru ba Kuma Shima Daddy ba Laifinshi bane Iyya,Momy zata Kasheni ina Jin Tsoro.."Idon Iyya ya Kawo Kwallah Cikin Lallashi Take"Ayyah Bar Fadin Haka Mufeeda Babu Abunda Hajiya Zata Miki Alhaji bazai barta Kibar Kuka babu Abunda zai Faru Kinji ko.."


Tafada Tana Dago Kan Mufeeda Lokaci Daya Tana Share mata Kwallah Mirmishin Yake Mufeeda Tayi kafin tace"Nagode Iyya Akullum Ina kallonki Tamkar Inna tace..Nagode Sosai.."Kumatunta Iyya Ta Shafa kafin Tace"karki Damu Mufeeda duk Abunda Ke Damunki karki Boyemin ki Sanar dani Kinga yanzu bake kadai bane Kina da Yaronki Ciki Toh yakamata Ki Kula da kanki kinji ko.."Kai Ta gyada mata Tana Mirmishi kafin Tace"Insha Allahu.."


Mikewa Iyya Tayi Tana Fadin"Maza Ki Tashi Kiyi Sallah Nima bari naje nayi alwala,Kafin Na Idar da Sallah Abincin ya Karisa.."Mufeeda Ta Mike Tana Fadin"Toh Iyyah..."Har Iyya Ta Juya Zata Fita Mufeeda Tace"ahm  Iyyah.."Iyyah Ta Waigo Tana Fadin"Na"am Kina mgana ne Mufeeda..? Kai ta gyada mata kafin Tace"Eh nace Ina Naila Take ne banganta ba..?


Iyyah Tayi Mirmishi Tace"Tayi barci Ammh Itama Tayi Ragimar Rashinki Tana Dakina In Kin Idar da Sallah Kije ki Dauki Yarki  "Tafada Tana Dariya Kafin Ta Fice,Mufeeda Dake Tsaye ta Murmusa kafin ta Saki Ajiyan Zuciya Ta Shige Tiolet Din Dake Dakinta Domin Dauro Alwala.


****

Farida Kwance Take Ruf da Ciki Tana Rafzan Kuka Ji Take kamar Zuciyarta zai Fashe da Bakinciki Da Kishi Sun Taru Sun Mata Yawa Tana Ji kamar Tatashi Taje ta Shake Mufeeda Ta Mutu Daga Ita Har Abunda Ke Cikinta.


  In Ta Tuna Wai Tahir ya Hada Shimfida da Mufeeda Sai Taji Tafita Hayyacinta babban Abunda Ke Kara Ruguza mata Zuciya Sai Cewan Datayi Mufeeda ta bar Gidan Ammh Ko Kunya Tahir ya bude baki yace Bazata Tafi ba Kenan awannan Gidan Zata Reni Ciikin Kuma Ta Haifeshi Tana Gani Ina Hakan Bazai Taba Yuyuwa ba Wlh bazata Iya zama da Mufeeda Acikin gidan nan ba Duk Abunda Zai Faru Sai dai ya Faru 


  Hawayen Idonta ta Share Kafin Ta Sauko Daga Kan gadon Wayarta Dake Gefe Ta Dau Tsuwa,Jawota Tayi Ta Duba Taga Daya Daga Cikin Kawayensu Tasan Kan mganar Bikin kanin Bilkisu ne,Tsaki Taja ta Kife Wayar Acikin Ranta Tana Fadin Bata da Lokacin Wannan Bala"in daya Tunkarota ya Isheta Tiolet Ta Fada Domin Dauro Alwala Tanayi Tana Kuka Kamar Wata Karamar yarinya.


Gabadaya Ranar gidan Babu Sukuni Su Basma ne kadai Sukayi Dinner,Tahir Coffea Kadai Yasha ya Koma Dakinsa,Mufeeeda ko Takasa Fitowa Falo Iyyah ce Ta Dauki  Abincin Ta kaimata Dakyar Ta Lallasheta Ta Iya ci Ta Kwanta Tana Ajiyar Zuciya,Ita ko Farida Kofarta ma Arufe ne Kuma ba Wanda yama yabi Ta Kanta Duka Zukatan Haka Suka Kwana Zuciyoyi ba Dadi,Hatta da Umma da Abba Suma Haka Suka Kwana Cikin Zullumi balle Goggo Abu Wacce Tunda Suka Dawo Hakimi bai kara mata Mgana ba Domin yanaganin Duk Itace Silan Faruwan Komai....


Bangaren Inna Fulera Kuwa Kwana Tayi Kuka Cikin Damuwa Gefe Daya na Zuciyarta na Tsausayin Yarta yarinya karama Ta Shiga Cikin Jarabawar Rayuwa,Haka Tatashi ta Dauro Alwala Tana ta kaima Allah Kukanta Kamar yadda Tahir ya Kwana Salloli yana Neman Gafaran Allah kafin Safe yaji Zuciyarsa Tamai Sanyi Duk Nauyin Dadade Tanayi Tun bayan Faruwar Lamarin Yaji ya Washr ko banza ya Rage kaso 74 daga Cikin Damuwarsa.


***


Washegari Tun Karfe 8 na Safe Tahir ya Fita ko Breafsat bai Tsaya Yi ba,Domin baki na Jiransu Ishaq Tun 7 ya Isa Shima ya Tadashi Daga barcin Daya Kwasheshi bayan Sun dawo Daga Sallar Asuba Shida su Bassam da Muda.


Farida najin Fitar Tahir Tayi Zumbur Ta Mike Daga Kwancen Datake Domin Tana Ta saman Steps Din Ta Hangeshi suna gaisawa da Iyya kafin ya Fice Da Sassarfa,Tana ganin Haka ta Fara Saukowa Daga Steps Din Benen Tana Hada Hanya Bibbiyu Sanye Take da Riga da Sikat Din Atamfa Tun na Daran Jiya,sai Wani Hijabinta Red Colour Wanda Tayi Sallar Asuba Dashi,Iyyah na Kichen Tana kokarin Soya Kwan da Za"ayi Breafsat Dashi Taga Wucewar Farida Da Sauri Kamar Ta Kifa Zuwa Dakin Mufeeda,Iyya Tayi Tsam da Sauri kamar Ta Bita sai Wata Zuciyar Tace Bazata saba Mganar Iyayenta ba.


Mufeeda na Kwance Kan Gado Tana barci Gefenta Naila ce Itama barcinta Yadda Naila ta Riketa Kamar Wasu Uwa da yarta Tsaye Farida Tayi Tana Binsu da Kallo Wani Takaichi mai Hade da bakin ciki da Kuma Kishi Suka Taru Suka kara Tunzurata Cikin Fitan Hayyaci Ta Karisa ga Mufeeda Daga Tsayen Ta Saka Hannu Ta Daka mata Duka Abayanta Cikin Masifa tace"Tashi...Tashi Don Ubanki Yau zaki bar gidan nan Tunda Bana Ubanki bane.."Take Fada Tana Kara Sakarma ta Duka Abaya 


  Kamar Amafarki Taji Saukan Dukan Tayi Firgigi Ta Farka Tana gyara zaman Doguwar Rigar Barcin Dake Jikinta Cikin Fargaba da Faduwan gaba Ta kara Ware Ido ganin Farida Tsaye Akanta tana Huci kamar Wata Macen Zakayan,Da Sauri Mufeeda ta Sauko Daga kan Gadon Ko"ina na Jikinta na Rawa Tace"Ina..ina..kwa...kwana Momy.."Rankwashi Farida ta Sauke mata akanta kafin Tace"Karki kara Kirana Mommy Domin Ni ba Uwarki bane,Da"ace Kin Dauki ne Amatsayin Uwa da baki Hada Shimfida Da Mijina ba,Mufeeda Kin Cuceni Mijina fa Kika Sani kuma Har yayi miki Ciki Kuma Shikenan Don Ina Sakarya sai na barki Ki cigaba da zamamin Agida..? Tafada Tana Nuna kanta Lokaci Daya Hawaye Duka Wankrmata Fuska.


Mufeeda da Hannunta Guda Daya ke bisa kanta Daya kuma yana Kan Bakinta tana Danne Kukanta Cikin Wani yanayi da Firgici Take Fadin"Don Allah Mommy Ki..."Bata karisa ba Farida Ta Wani ,mugun Dauketa da Wani Lafiyayyan mari sai da Ta Kife Bisa gado Ta Fashe da Kuka wanda Hakan ya Tashi Naila Daga barci ganin Mufeeda na Kuka sai Itama ta Canyara Kuka.


Iyya na Kichen Tana Kokarin Hada Kayan Karyawan Taji Kuka Daga Dakin Mufeeda Ga Naila Taji Kukanta Da Hanzari ta bar Abunda Takeyi ta Fito,Da Gudu Zuwa Dakin Mufeeda Daidai Lokacin Da Farida Takema Mufeeda Watsi da kayanta Dake Cikin Wardrope Tana Fadin"Tashi..Maza Ki Hada Kayanki Cikin Jakarki yanzu zaki Barmin Gida Bazaki Haifan Dan Shege Agida ba Kije Cutar da Kikamin Allah ya Sakamin.."Take Fada Ta kara Watso mata kayanta Wasu Har kan Jikinta,Itako Mufeedan Sai Kuka Take Kamar Ranta zai Fita tama Kasa Mgana,Naila Kuwa Rarrafowa Tayi Zuwa Wajen Mufeeda Ta lafe Ajikinta Daukanta Tayi Ta Rumgume Tana lallashinta Tana Kuka.


Iyya Dake Tsaye Taji kwallar Tsausayin Mufeeda Sun Cika mata Ido,domin Farida ba Abar Tsausayin Bane Duk Abunda ya Faru Tsakanin Alhaji da Mufeeda Itake da Alhakin Kaso mafi Girma Aciki,Cikin Hanzari Ta Karisa Dakin Tana Fadin"Ashh...Hajiya me yayi Zafi kuma..? Take Fada Tana Rikota Daga Rikito kayan Mufeedan Datakeyi Daga Cikin Wardrope.


Cikin Hargagi Farida ta Fizge Jikinta Daga Na Iyya Tana Fadin"Babu Ruwanki Dani,Wlh kinjima Na Rantse Sai Mufeeda Ta bar gidan yanzu.."Tafada Tana Zaro mata Jajayen Idanuwanta Jin Haka yasa Iyya Tayi baya tana kallon Ikon Allah Farida tana Juyowa Ta Saka Hannu Ta Fizge Naila Hannun Mufeeda Tana Fadin"U get me Right ko..? Toh maza Tashi Tashi ko kuma na Watsaki keda Kayanki Zuwa Waje.."Tafada Tana Rike Naila Wacce Ke kuka Tana Zille zille Ita Asaketa ta koma Wajen Mufeeda.


Mufeeda na Kuka Tana Tattara kayanta Tana Tusawa Cikin Babban Akwatunta Wanda Faridan Ta Siya mata,Ita kuka Farida Kuwa Hawaye ke Zubarmata Saboda Fitina Mufeeda na Zage Akwatin Farida ta Mikama Iyya Naila Tana Fadin"Rikemin Ita Iyyah.."Tafada Tana Tunkaran Mufeeda Wacce Ke Tsaye Tana Kokarim Sanya Hijabin Dake Hannunta Fizagar Hannunta Farida Tayi Lokaci Daya da Akwatin Kayan nataTafara Janta Zuwa Falo Tana Fadin"Fito Muje Mufuka Macuciya Allah ya Isa Tsakani na Dake Mufeeda Wlh bazan Taba yafemiki ba.."Take Fada Tana Kuka Lokaci Daya Tana Faman Jan Mufeedan Har Tsakiyar Falon,inda Taci karo dasu Basma da laila da Bassam da Muda dake Tsaye suna kallon Ikon Allah Domin Hayaniyar Faridan Ya Tadasu Daga barci.


Cikin Mamaki Basma Ta kalli Bassam shima ya kalleta Kafin Su maida Kallonsa kan Farida Wacce Ke Jaye da Hannun Mufeeda Tana Kuka ga akwatunta,Cikin Siririyar Murya "Mommy Ina zaki kai Mufeeda..?

Cikin Tsawa da Fada Farida tace"Gidan Ubanta zata Koma basma Ai nan ba gidan su bane.."


Tafada Tana kara Jan Mufeedan Iyya Dake Biye da Ita Dauke da Naila Dake Kuka Cikin Ranta Addu"a Take Allah ka Jeho Tahir yanzu Kowani babba Wanda zai iya Dakatar da Farida Daga Kudurinta,Basma da Abun ya bata Haushi Kawai sai Tasha Gaban Faridan Tana Fadin"A"a Mommy Kin manta Abunda Su Baba Hakimi Sukace Mufeeda zata Cigaba da zama tare damu ko Bassam..? tafada Tana kallonshi Da Sauri ya Gyada mata kai ..


Farida Dake binsu da kallo Cikin Mamaki da Fushi Tace"Au..Allah Haka Sukace kenan..? Tafada Cikin Salon Rainin Hankali Basma Tace"Eh mommy Harda Daddy ma Haka yace.."Kafin Basma Ta kara Motsi Farida tace"Naji Masu Daddy ban Hanya na Wuce ko naci Ubanki yanzu nan.."Basma Takura ma Farida Ido,idanuwanta Sun Cika da Kwallah batasan Sanda Bakinta ya Furta"Haba Mommy meyasa Zaki yi haka..? Duk Abunda ya Faru da Daddy KE CE SILA,domin da baki banzatar Dashi ba,Kuma baki Banzatar damu da yanzu Muna Cikin Farincikin mu,Saboda Haka bazan Matsa ba Wlh bazaki Kori Mufeeda ba.."Ran Farida ya baci Ta Saki Hannun Mufeeda Ta Dauke Basma da Wasu Tawagen Maruka Tana Fadin"Ni ne zaki Fadama Wannan Mganar Basma.."


Bata Dauke Numfashi ba Taji Itama an Wanketa da Maruka Har Biyu Sai da Tayi Taga Taga Zata Fadi kafin Ta iya Tsayuwa da Kafafunta Cikin mamaki Take bin Wanda ya mareta da Kallo Tahir ne Tagani Tsaye Akanta yana Huci Gefe Daya yana Binta da Wani Matsayin kallo Domin Tun Mganar Basma na Farko yake Tsaye bakin Kofar Shigowa Falon,Ya Dawo Daukan Wasu Fayels ne Daya manta Dasu yau Bai Fita Dasu Shine yana Shigowa Falon yaci karo da Abunda Farida Keyi nan da nan Fushinsa ya Dawo Sabo kusan Mai Hakuri bai iya Fushi ba.


Cikin Nunata da Yatsa ya Furta.."Eh Din ta Fadamiki..? Zaki yi Wani Abu ne .? Ko Abunda Ta Fadamiki ba Gaskiya bane..? Tir dake Farida Kinyi Asara Tunda Har ya'r dakika Haifa Daga Cikinki Tafi ki Sanin Abunda yadace Dake Wlh Kinji Kunya Kuma Kinyi Asara Duniya da Lahira.."Yafada yana Huci kamar zai Daketa.


Baya Taja tana Tsiyayan Hawaye Tana kallonshi Cikin Tsoro Domin Batasaba ganin Tahir Cikin Wannan yanayi ba Cikin Kuka tace"Ni ce nayi Asara Tahir...? Ni Farida ni ka mara gaban ya"ya da Yan Aiki.."Ya Taso mata yana Fadin"Amm mareki Di n ko zaki Rama ne..? Bari ki ji na gaya miki na Fada Kuma zan Kara Fada Wlh Baki isa Ki kori Mufeeda Daga gidan nan ba Sai Dai ke in kin ga bazaki iya ba ga Hanya nan ba Wanda ya Rikeki Dama Banga Uwar Da kike Tsinana mana ba Dake da  babu Ke Zamu Rayu So in Kin Fita wlh zanfi Kowa Jin Dadin Hakan.."Yafada Duka Jijiyon Kansa na Tashi Saboda Bacin Rai.


Farida Dake Kuka Jin Kalaman Tahir sai ta kara Volume din kukanta Cikin Firgici Take kallom Tahir Tana Girgiza kai ko kallonta Baiyi ba yace"Basma Dauki Akwatun Mufeeda ki kaimata Daki.."yafada Lokaci Daya yana Wucewa Ta gaban Farida ba zato kawai Mufeeda Taji ya kama Hannunta zuwa Dakinta yana Fadin"Naga Uban da zai sake yunkurin Koronki Tunda Shima ba Gidan Ubanshi bane Domin Da Gumin Aikin Danikeyi Aka sakamin Dashi Kinga ko baki da Iko Akanshi.."Yafada yana Rike da Mufeeda Zuwa Cikin Dakinta Basma na Biye dasu Abaya da Akwatun Mufeedan Tana Mirmishin Jin Dadi.


Farida Dake Binsu da kallo Wani Bakinciki Da Kishi Suka Kusa Kada Ita Cikin Kuka ta Zura da Gudu Zuwa saman Tana Haura Steps Tana kuka,Har Ta Shige Cikin Dakinta ta banko Kofa,Bassam da Muda da Laila Suka Bita da kallo Iyya kuma Dake Rumgume da Naila Wacce Tayi Barcin Wahala Ranta ya mata Dadi ko Banza yau Alhaji ya Burgeta Sosai,Ta tabbata Farida zata kara Dawowa Cikin Hayyacinta.



*One love*😍💝



*SHAKIRA..*

*AISHA ALTO*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*


_Follow us on wattpad:Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


    *BABI NA GOMA SHA BIYAR*


.....""Har kan Gadonta ya Zaunar da ita,Dagowa Tayi Tana kallonsa Da Jajayen Idanuwanta Tana Zubar da kwallah Cikin Siririyar Muryanta ta Furta"Kayi hakuri Daddy..."Tsam ya Tsaya yana kallonta gefe Daya na Zuciyarsa Tsausayinta na Ratsashi,Basma Dake gefe Tsaye ya kallah kafin yace"Ku kula da Ita sai na Dawo..'


Yafada Haka kafin ya kai ya Fice Daga Dakin da Sassarfa,basma Dake Tsaye ta Kariso Kusa da Ita Tana lallashinta Tahir yana Fita yaci karo da Iya Tsayawa yayi yana Fadin"Iya don Allah ki kula da Mufeeda..."Iya Ta gyada kai Tana Fadin"Insha Allahu Alhaji.."


   Sama ya haye Cikin Dakinsa ya Shiga Daga ganin yadda yake Komai Cikin Hanzari zaka Fahinci yana Cikin bacin Rai,Cikin Sauri ya Dauki Duka Fayels din ya Fito Garzali Dake Waje yana Jiransa ya Shiga Mota Suka koma Campany Wanda Tunda ya Dawo Ishaq ya lura kamar Ranshi abace yake ba Haka ya Fita ba bai mai mgana ba Sai da Suka Dawo Masallaci Sun Shigo Office Din Tahir din 


Kan Wata Kujera Dake Cikin Office din Ishaq ya zauna yana Fadin"Kai inaga fa zan Koma gida cikina yana ta Kiran Ciroma.."Tahir Dake zaune kan Kujeran gaban Tuburansa Ya Dago yana Fadin"Allah Sarki kuda Kukayi Dace kenan Mu ko Mun koma muda banza Duk Daya While sai ka Dawo ni kila sai la"asar in zan Koma gida na Biya na Siya Fura ."


Ishaq ya gyara zama yana Fadin"Tahir meya Faru ne..? Dazu Bayan kaje gida Dauko Wadanan Fayels din ka Dawo Ranka bace.."Ajiyar Zuciyar Tahir ya Sauke kafin ya Mike yana Fadin"Nida Farida ce Wato Ishaq Farida Muguwar Yar Rainin Hankali ce Ayadda nakeji yanzu kamar na kamata nayi ta Duka Gabadaya na Doramata kaso mai girma na Abunda ya Faru Domin Data Kiyaye Hakokina na aure da Duka Haka bata Faru ba.."Yafada yana Saka Duka Hannuwansa Ciki  Aljihun Wandonsa.


Ishaq yace"Me kuma ta Sakeyi..? Tahir ya waigo yana Fadin"Zuwa nayi na tarar da Ita zata kori Mufeeda Daga gidan.."Ido Ishaq ya zaro yana Fadin"Kabari don Allah...? Tahir ya kariso Kusa da Ishaq ya zauna yana Fadin"Wlh Allah ina gayamaka tana Kuka Wai Tana Fadin Ta Cuceta Ishaq can u juz imaging Wai Farida na Kuka saboda ni Tahir na Ma Mufeeda ciki.."Ishaq ya saki Dariya ahankali yace"Dama tana Sonka Tsabar Iskanci ne ke Cinta nayi Takaichin Abunda ya Faru Tahir Duk da bawa bai isa ya Gujema kaddaransa ammh Ta wani Fanni naji Dadi ko banza Lokaci yayi da Farida zata girbi Abunda ta Shuka.."


Tahir ya kuramai ido yana kallonsa kafin yace"Kamar yafa..? Bangane ba..? Tashi Ishaq yayi kafin ya Sakala Duka Hannuwansa Akirjinsa kafin ya Fuskanci Tahir yana Fadin"Eh mana Ai ada Tana ganin baka da Wani amfani Awajenta,Tana ganin ka Daga Ita sai kai yanzu kuwa Dole zata Shiga damuwa Domin Tana Sonka auren Soyayyah Kukayi bana Kiyayyah ba So Dole Farida tayi kuka Kishinka Take Tahir.."Shuru Tahir yayi kafin ya Jinjina kai yace"Hakane..,? Toh ai Ta makara Sai dai komai yagama lalacewa.."Ishaq yace"Shine ake Jiyemata Tun Farko Kada tayi Nadamar Dole Wacce bata da Wani Amfani.."


Mikewa Tahir yayi kafin yace"Wannan ya Rage nata Ishaq Abunda na sani Shine Matukar Farida tace zata matsama Mufeeda Wlh Itama zata Shiga mtsala na Fadamata in batason ganin Mufeedan agidan zata iya komawa gidansu ban Hanata ba ."Ishaq yace"Ina bayanka Wlh gwara ka Nuna mata Kuskuranta Tun yanzu.."


Tahir yace"Uhm,Kabari kawai Ishaq Zata ga ainihin kalata Wlh.."Ishaq yace"Asaussauta mata Alhaji Abarta taji Da Daya..Yafada yana yar Dariya Shima Tahir Dariyan yayi kafin yace"Yau da Safe Goggo Ta Kirani Tana Kuka Tana Fadamin Tunda Suka Dawo Baba Hakimi baya kulata nadai lallasheta nace Tabari Ranar sati zan Shigo D'anbatan,Duk da ina jin kunya Ishaq sai nake ganin kamar kowa yasan Abunda na aikata.."


Kusa dashi Ishaq yazo Lokaci Daya yana Dafa kafadarsa Cikin Sigan lallashi yace"Daga goggo Har Farida nasan Haka zata Faru dasu kayi Hakuri zasu Daidaita ammh kaima kasan Dole Baba Hakimi yayi Fushi mganar Kunya kuma Don Allah ka saki Jikinka ba Wanda zai san Wannan Mganar bayan mu da muka sani kuma ko Ansani Bafa laifinka bane Kaddara ne kuma Bawa bai isa ya kaucemata ba.."Ajiyar Zuciya Tahir ya Sauke kafin yave"Hakane Nagode Sosai Ishaq Da bansamu Amini kamar ka ba Dabansan Wani Hali zan Shiga ba.."Mirmishi Ishaq yayi kafin yace"Nima Haka da Ban Hadu da Amini kamar ka da na Tafka Asara.."Atare Suka saka Dariya kafin Ishaq yace"Allah ya Sauki Mufeeda Lafiya,Ammh sai nake ganin kamar yarinyar tayi kankanta da Haihuwa fa.."Wani kallo Tahir yayi mai kafin yace"Nima fa ina Mamaki kaduba kagani yarinyarnan kamar kara ammh Ta iya Daukeni Tsaf.."Ishaq ya Buga Kafadarsa yana Fadin"Bugu Daya ko Mallam Kasaka Kwallo Araga.."Ture Hannunshi Tahir yayi yana Fadin"kaifa Dan Iska ne Zahra ta bata ka.."


Ishaq na Dariya yana Fadin"Yan Iska dai Mallam kadinga saka Mun jaye.."Shuru Tahir yayi kafin yace"Wani Hanzari ba Gudu ba,ya Zan yi da Mufeeda bayan Ta Haihu..? Ishaq yayi Shuru Shima yana Wani Tunani kafin yace"Mubar Wannan Mganar Fatarmu dai Allah ya Sauketa lafiya Insha Allahu bazai gagaraba."gyada kai Tahir yayi kafin Ishaq yace"Bari na Kira Zahra ta saka Direba ya kawoma Abincin nan kawai sai muci ko..?


Tahir na Shafa Cikinsa yace"Daka Agaza kuwa Domin nafara ganin Hazo hazo.."Dariya Ishaq ya saka kafin ya fice yana Laluban Zahra ta Waya Shiko Tahir komawa yayi yazauna  yana Auna Mganar Yadda zai yi da Mufeeda bayan Ta Haihu..? Wata Zuciyar tace In ta yaye Abunda Ta Haifa sai ka mata Aure ka bata jari..,Toh wazai Aureta bayan Ta Haihu..? Babu Wanda ya chanchanta ya Aureta sai kai Tahir.."Wata Zuciya ta karantamai da Sauri yace"A"a Bazai Yuyu ba Naso kaina Dayawa bayan na lalata mata Rayuwa kuma na Tursasamata zama dani Tana karamar yarinya bazan yi Haka ba.."Yafada Afili Cikin Karayar Zuciya Lokaci Daya Tsausayin Mufeeda na Ratsashi Runtse Ido yayi Yana Tunanin Wani kariya zai Bata saboda Farida Domin yadda ya Zuciya da Farida indai Tace zata Takura Ma Mufeeda Zasu samu babban Mtsala.


****

  

Farida Kuwa Tunda Ta Shiga Daki Tafada Bisa gado Tana Gunjin kuka kamar Zatayi Hauka Gabadaya ta Birkice Haka take Buga kanta bisa katifa Tana Kuka Hannuwanta Dafe da kanta bayan Ta Barbaja Gashin kanta Ya Watse kamar Wata Kamun Hauka Cikin Ranta da Zuciyarta kamar Ta Buga Saboda Kunci Da bakinciki.


Duk bayan Kowacce Dakika sai kalaman Tahir Sun Fado mata arai Wani Jiri take gani Idanuwanta Sun kode Saboda Kuka Tana ji acikinta Ranta Tahir ya gama da Ita Tuni Shedan yamata Zugan dama Duk karya ne plan ne Tahir ya Shirya dama Sun Dade Suna Cin Amanarta Shida Mufeeda munafukar Allah,Ji Takeyi ayanzu Duk Duniya bata da wata makiyiya kamar Mufeeda Tanajin bazata iya Rayuwa acikin gidan Nan Tana kallon Mufeeda da Cikin Tahir ba Watarana Bakinciki zasu Sa Zuciyarta ta buga Ta Fadi ta Mutu .


Cikin Hanzari ta Mike Daga kan Gadon Wajen Jerin Akwatunanta Karamin Ciki Ta Dauko Ta Budeshi Bisa gado kafin Ta Bude Wardrope dinta Tana Debo kayanta tana Sakawa Gefe Daya kuma Tanayi Tana Share Kwallah,Sai da Cikata kafin ta maidata ta Rufe Tana kuka Ta Dauki Wani Hijabin Data Cire Wanda Ke Jikinta Duk gayun Farida Yau batama Tuna da Wani Abu ba Waishi Wanka balle Kwalliya,ta dauko Akwatin kenan Wata Zuciya tace"Farida ina zaki..? Kawai Taji bakinta ya Furta Kano lokaci Daya kuma kalaman Abbanta ya Fado mata Kuka Takara sakawa Kafin Ta koma Bakin gado ta Zauna Tana Faman Sharan Kwallah Cikin Ranta Tana Tunanin bayan Kano bata inda zataje kuma,Danbatta..? Kai ina..? Bazai Yuyu ba Ko Naje chan Duk Daya ne Goyon bayan Dansu zasu yi Toh ina yakamata Naje..? Kai Tsaye Wata Zuciyar Tace"gidan Bilkisu..."


Tuna Haka yasa Ta saki Mirmishin Karfin Hali kafin Ta mike Har Ta kusa Ficewa Ta Tuna Da Wayarta tazo Ta Dauka Ta Fice Cikin kunar Rai Take Saukowa Daga Stairs tana Bin Dakin Mufeeda Dawani kallo har ta kariso Tsakiyar Falon kenan Sai ga Laila da Basma Sun Fito Daga Kichen Laila na goye da Naila Ita kuma Basma na Dauke da Wani Jug ahanunta Da alama Lunching Suke Shiryawa bayan su Kuma Iya ne Dauke da Wasu Manyan Food Flaks kallo Daya Farida Tayi musu Ta Dauke kai bata kara kallonsu ba Ta Nufi Hanyar Ficewa...


Cike da Mamaki Basma ke Fadin"Mommy ina zaki..? Afusace Farida ta Waigo Tana Watsama Basma Harara kafin Tace"Inda Ubanki Tahir ya aikeni zani Don Kakarki Goggo Abu.."tafada Idanuwanta Sun kada Sunji Jajir Daga Basma Har laila balle iya baki Suka Rike Suna salati acikin Ransu Iya ce Tayi Saurin Cewa"Subhanallah...Haba Hajiya Wannan zagin bai kama..."Dallah Malama ki Rufan baki Tsohuwar Munafuka.."Farida ta katse Iya Tana Fadin Haka ..


Ido kawai iya ta sakamata batare Datace komai ba,Baya Farida ta Dawo Tana Nuna Iya da Yatsa Kafin tace"Nasan Duk Abunda Tahir da Mufeeda Suka Taru Suka aikata kina sane ammh Dayake ke Tsohuwar Munafukace Shine kika munafunceni ko .? Toh kema kinsan Da sani Karshen Aikin ki yazo Acikin gidan,Zan Tafi na barma Tahir gidan Tunda Dama Burinku kenan Daga ke Har Mufeedan In Kinji ko kuma In kun Burgeni ku Maye masa Gurbina da Mufeeda kodon Taimakon Shegun ya"yan dazasuyi Ta Haifa.."Tafada Tana Watsama Iyan Wani kallo Lokaci Daya da Mufeeda Wacce Taji Mganar Faridan Ta Fito tana Tsaye Kofar Dakinta tana Kuka..


Wani Mirmishin Kuka Farida Tayi kafin ta Dauki Akwatunta ta Fice da Sauri Su Iya Suka Marata baya,Basma ce tafara Juyawa Zuwa Saman Dining ta iJiye Abunda Ke Hannunta da Gudu Ta Nufi Hanyar Dakinta tana Kuka Laila ta marata Baya Cike da Tsausayi Iya Kuwa Jikinta Asanyaye ta Karisa Jera Kololin Abincin Bisa Dining kafin Ta Waigo Tana kallon Mufeeda Cikin Kulawa tace"Kidaina yawan Kuka Mufeeda bashi da Alheri..Kiyi Hakuri Daman Dole zaki Fuskanci Haka Allah ya baki Ikon Karban Kaddaranki Hannun Bibbiyu.."Daga Haka Ta Shige Kichen Tana Shara Kwallah Aranta Tana Ji ko Farida bata Koreta ba ita da kanta zata Tafi Tunda Gidan ya Rikice komai Babu Dadi,Dama Babu Abunda Ta Nema Rasa na Rayuwa Domin Danta ya samu Aiki Ta Dalilin Tahir Kawai Karamcinene da Mutumcin shi yasa Take Zaune Dasu Haryanzu Ammh Lokaci Yayi da zata koma gida...


******


_Anguwan SARKI_


Bilkisu Kawar Farida ce Wacce Sukayi Mkranta Tundaga Secondry Har Zuwa Buk,Course Daya Suka karanta kuma Suka zo Sukayi Aure A kaduna sai dai Ita Bilkisu Ta Riga Farida Aure da Wajen Shekara Daya da Rabi,Tana Cikin Wadanda Suke Zuga Farida acikin Kawayensu Duk da ko Ita ba Haka take Tafiyar da Gidanta ba Ko yar Aiki bata Dashi sai Wata Tsohuwa mai Zuwa tana mata Wanke Wanke da Wanki Shima Sai Mijinta ya Fita tazo Tagama aikinta ta tafi ya"yanta Hudu yanzu Haka kuma bata Tsaida Haihuwa ba Ammh Tana Daga Cikin Wanda Suka Zuga Farida kan Ta Tsaida Haihuwa Hakannan Dama Duk Inda ka zama Sakarai sai Ana nuna maka Hanyar da zaka sake bi ka kara Sakarcewa.


Farida da Motar Ta Fita Zuwa Gidan Bilkisu Tana Driving Tana Kuka Lokacin Data Shigo Babban Falon Gidan Bilkisu Tana Zaune kan Kujera Tana Waya da kaninta Wanda zai yi Aure Sai ga Farida ta Shigo Tana kuka Abun yabata Tsoro da Hanzari ta yanke Kiran Ta Mike Tana Fadin"Fari Mezan gani Haka..? Mutuwa Akayi..? Farida bata samu zarafin mgana ba Illa Zubewa datayi jikin Bilkisu Ta saki kukan Datake yinshi Acikin Zuciya 


Riketa Bilkisu Tayi Cikin Tashin Hankali Take Fadin"Na Shiga Uku Fari wai meya Faru..? Basma ce Ta Rasu ko Shi kanshi Tahir din ne Wani Abu ya sameshi Kaina ya Kulle Don Allah ki gayamin Abunda Ke Faruwa...? Farida Ta Dago Daga Jikin Bilkisu Tana Fadin"Billy Tahir ya Cuceni...Tahir ya gama Dani Billy Shida Mufeeda Sunci Amanata..."Take Fada Hawayenta Suna Kwararowa 


Bilkisu Tace"Tahir da Mufeeda Kuwa Me Sukayi Kuma...? Tafada Cike da Mamaki,Kan Kujera Farida Ta Fada Tana Dafe kai kafin Tace,"Billy..." Bilkisu tace"Na'am...Farida.." Farida Ta Runtse Ido kafin Tace"Ciki Tahir yayi ma Mufeeda Mai Renon Naila.."Wani Zabura Bilkisu Tayi baya sai gata zaune gaban Farida Duka Hannuwanta akai kafin Tace"Kibari don Allah Farida..! Wani Tahir din Wai Abbansu Basma kikeso kice yayima yarinya Dakuka Daukota Daga Kauyensu Ciki...? Tafada Duka Idanuwanta Awaje.


Idanuwan Farida na Runtse Hawaye Suka kara Kwaranyomata kafin ta Gyada kai Cikin Kuka tace"Kwarai Da Gaske..."Nan ta Shiga labartamata Abunda ya Faru Tundaga Farko Har Karshe Ai sai Bilkisu Ta Mike Tana Fadin"Kutumar Uba..Lalle Tahir Mugun dan Wasa ne Wato Fyade yayimata baya Cikin Hayyacinsa Kajimin Matsiyacin Mara Mutumci da Kima Wato Shine Iyayensa Suka Taru Suka Marama Dansu baya Saboda Tacewa Ke kuma gaki banza Sakarya sai ki zauna  Araini Cikin Shege agabanki ko..? Farida na Share Hanci Tace"Abunda ke sakani Kuka kenan Billy Bansan Iya Adadin Tarayyar da Tahir yayi da Mufeeda Ba Bilkisu ammh Duk da An batamin ba Wanda yaga laifinshi sai ma laifina ake gani Daga Karshe Cemin yayi Mufeeda bazata bar Gidan ba Sai dai ni in nagaji na kara gaba."


Billy tace"Jar Uba..!Lalle Tahir Mugun Dan Iska ne,Haka yace...? Tafada Tana Girgixa Jiki batai Tunanin Magidanci kamar Tahir Tana Surfamai Zagi,Farida ta gyada kai kafin tace"Shine Dalilin Dayasa na Taho Tunda Umma da Abba ya mallakesu ko na Koma Bazasu Taba Saurarana ba Kirufamin Asiri ki barni na zauna Awajenki Har Tahir yagane Kuskuransa.."


Bikisu Tayi Shuru Cikin Nazari Farida Ta kalleta Tana Share Kwalla tace"Ko da kwai Mtsala ne..? Ajiyar Zuciya Bilkisu ta Sauke kafin Tace"Ba mtsala in ma Dashi Abban Su Walida ne,ammh komai ke zanyi mgana Dashi in ya Shigo Tashi na rakaki Dakin da zaki Sauka bazan bari ki koma gidan Tahir ba Domin  Cuta kam an Cuceki Wlh Cikin Shege Acikin gidanki don Wulakanci ma Mafi kaskanci Mai Renon Yarku Gaskiya Tahir ya bata Wayonsa Kuma girmansa ya Zube Acikin Idanuwata.."Tafada Tana Daukan Akwatin Farida Tatashi Suka nufi Wani Korido Suna Tafe Billy na Tsinema Tahir Wanda Har Azuciyar Farida Tana Jin Zafi ammh bata da yarda zatayi Tunda Ita ta Tona ma kanta Asiri.


Daki ne Mai Dauke Da gado da Wardrope sai Madubi da Tiolet ba laifi ko"ina Tsab Tsab nan Bilkisu Ta Fita ta barta Zuwa Kichen Ta Zubomata abinci Domin Duka yaran nata Suna Islamiya Fargaban Bilkisu Daya Megidanta Wanda yake da Zafi Sosai In Har yaga Farida tadawo Gidan sai yaji Dalili Kuma Akwai sanayyah Sosai Tsakaninshi Da Farida Har da Shi kanshi Tahir din Ita kuma bataso ma Tahir yasan Farida na gidanta sai yagama Wahalan Nemanta tukunna Hardai ta Zuboma Farida Abinci bata samu Mafita ba Tana ta Dai Tufka tana Warwara Tsoro ya cika Ranta Saboda Tasan Abban Walida bai da Wasa.


****


Tahir kuwa bai da lbrin Farida bata gidan Domin Bai Dawo Daga Office ba sai bayan Isha"i Suna Zauna Suna Duba sakon Wasu Sabbin Samfur din Motoci Cikin Laptop din Tahir din Shida Ishaq basu ma gama ba Suka Rabu Akan Tahir zai karisa Komai kafin gobe koda ya Dawo ya Biya ya Siyo Furanshi yana Shigowa,kafin ya Shiga Dakinsa ya Fara Biyawa Dakin Su basma ya Tarar dasu suna kallon Cartoon Oyoyo Sukayimai ya Rumgumesu yana Tambayansu ko Sunci Abinci Tsaraban Furan Daya Siyo ya basu kulli Daya kafin yayi musu Saida Safe Daganan ya Shiga Wajen Su bassam ya samesu Shida Muda Suna buga Game,nan Suma Suka Tashi Suna mai oyoyo Shafa kansu yayi yana Tambayansu lafiyansu Suma Furan Guda Daya ya basu kafin Daganan ya Fito yaja musu kofa,Dakin Mufeeda ya kallah har zai Wuce sai kuma ya kasa Cikin Sanyin Jiki yanufi Dakin Nata yana Tura Kofar yaganta Kwance Kundundune chan Tsakiyar gado Cikin bargo Tana barci Bai Shigo ba Daga Kofar Dakin ya Tsuramata ido yana kallon Karamar Fuskarta Cike da Tsausayi Wani Abu na Tasomai Daga Kasan Zuciyarsa Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin ya koma Da baya ya jamata Kofar.


Yana Shirin barin Falon ne yaji Muryan Iya na Gaisheshi Da Sauri ya Waigo yana amsawa Cikin Sanyin Murya Iya tace"Alhaji Naila na Wajena Saboda ganin yanayin Mufeedam.."Gyada kai kafin yace"Bakomai kin kyauta.."Har ya Juya ta Sake Fadin"Amh Alhaji dama Ina son mgana dakai in ba Damuwa.."Cikin mamaki Tahir ya Waigo kafin yace"Mgana kuma...? Toh Shikenan iya Kibari da Safe kafin na Fita Ki Tunamin yanzu Dare yayi.."Jinjina kai Tayi kafin Tace"Shikenan Allah ya Tashe mu lafiya.."Da Ameen Ta amsa Har ta Juya zata Tafi ya Kirata ta Waigo ya mikamata Fura guda Daya karba Tayi tana mai Godiya Daganan ya mata sai da Safe ya Haura sama ko kallon Dakin Farida baiyi ba.


Sai da yagama Duka al"adansa na Kwanciya kafin ya Dauko Laptop dinsa  ya Dora Bisa Gado ya Haye Tsakiyar gadon ya Cigaba da aikinsa Lokaci bayan Lokaci yana Kurban Furar Daya Tsiyaya Cikin karamin Kofin glass bai kwanta ba sai Wajen 1pm kana ya Kashe komai ya koma ya Kwanta bayan yayi Addu"ar barci.




*Don"t Forget to Vote,Share,comments and like..*



*SHAKIRA*

A.ALTO*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*


_Don"t Forget to Follow us on Wattpad:Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


      *BABI NA GOMA SHA SHIDDA*


"""Tahir Ya Fito Cikin Fitanshi na Zuwa Office yana Sanye Cikin American Suit Dinsa,Black and White ya matse Wuyansa da Tie yana Dauke da Brifcase Dinsa Lokacin daya Sauko Kasan Falo Ya Iske Basma da Laila da Bassam da Mudu suna zaune Bisa Dinining Suna Breafsat Suna ganinshi Kowanne ya Washe baki Suna Fadin"Daddy gud Mrning...?


Karisowa yayi yana Fadin"Mrning my Childreen How was Ur Nite.."Suka amsa da Fine Kan Basma da Laila ya Dafa kafin yace"Laila da Mudan Hutunku ya kare Fa Tun last Week ko .? Kai Suka gyadamai alamar Hakane Numfashi ya Sauke kafin yace"Ok Bari na Dawo Kila ko Zuwa Gobe Ko Jibi Saturday Sai mu maida ku gida ko..? Kallon Junansu Sukayi kafin Suce"Toh Daddy.."Suka Fada Suna Dariya Jin Harda Bassam zasu Rakasu gida.


Teburin yabi da Kallo kafin yace"Ina iya da Mufeeda Bazasu karya bane..'Basma ce tace"Bamu sani ba Daddy ammh iya Ta Dibarma Mufeeda Ta kaimata Daki Tundaga nan Data Fito sai Ta Koma Dakinta Bamusan Abunda Ya Faru ba.."Basma Taa Fada Tana kallon Tahir din Kafin ya samu Zarafin Mgana Bassam ya karbe da Cewa"Eh mana Daddy Gidan Duk ba Dadi Mufeeda bata Fitowa yanzu Iya ma kamar Akwai Abunda ke Damunta yau Duk kamar ba Ita ba.."Yafada cike da Kewa Irin Abun bayamai Dadi.


Shuru Tahir yayi kafin ya saki Ajiyar Zuciya yace"Ikon Allah Meyafaru ne..? Basma tace"Bamu sani ba Daddy Kila Ita da Momy ne kafin Tatafi.."Da kallo yabi Basma Baki bude kafin Yace"Tatafi..? Faridar bata nan ne..? Ina taje..? Ya jero musu Tambaya Lokaci Daya.


Basma ta Zakuda kafada kafin Tace"Bamu sani ba Daddy Tadai Tafi Har iya ta mata mgana Ta kusa Zaginta.."Ido ya zaro yana kallonta ganin Haka yasa ta Shiga maidamai Abunda ya Faru,Jinjina kai ya Hau yana Jin Wani Bakinciki na Ratsashi,Wato Duk Bayan Rusamai Rayuwa da Farida Tayi bai Isheta ba sai Tabi gari Ta gama Tonamai Asiri ko..? Domin yana da Tabbatacin Bata je Kano Domin bada Safenan ya samu Wayar Umma,bayan Sun gaisa Ta kara bashi hakuri game da Farida Tare da Fatan zasu zauna Su Rungumi kaddaransu kuma yanzu bads Dadewa ba Suka kara Mgana Da Abba duk da Mganar Business ne ammh da Farida Taje kano Jiya Dayaji lbri,Shi ba Wannan bama Damuwarshi naga Goggo Abu Domin Innaro da Ashe Sun Kirashi Awaya Suna Sanar Dashi ya Kokarta yazo Domin Baba Hakimi yayi mugun Fushi da goggo Abu baya Shiga Dakinta kuma yahanata Shigowa Turakarsa kuma Baya Shiga Sabgarta Tayi kuka Tanuna Nadamarta Ammh Baba Hakimi yayi Burus Da Ita Innaro ma Data Nemi Shiga Mganar Hakimi yaja mata Kunni da Kakkausan Muryan Kan in Ta sake ta Kara Shiga Mganar Itama zai Jingine ta Gefe Kamar yadda ya Jingine Goggo Abu..


Jin Haka yasanya Goggo Abu Ta Rikice sai Zazzabi da Ciwon kai Kafin kace kwabo ta Kwanta Ciwo koda Likita yazo Dubata sai Iske Jininta yayi bala"in Hawa nan Dai ya Dubata ya bata Mgunguna,ammh Duk da Haka Baba Hakimi bai Sakin ma Ra"ayinshi ba Koda ma akayi Haka ko Shashen Goggon Abu bai leka Ba gefe Daya kuma Inna Fulera na gida kwance ba lafiya Tun bayan Dawowarsu Hakimi ne Dayaji Lbri yasa Innaro da Ashe Suka Tafi Suka Dubata itama nan Suka Isketa jiiki yayi Zafi Maman lantana ke Kula da Ita Koda Suka zo suka Fada Hakimi bai Bata Lokaci ba ya Saka Aka kaita Asibitin garin Danbatta,Itama dai Damuwar ne ya Rafketa Hawan Jininta ya Tashi Gado Aka bata sai da ta Kwana Daya da Wuni kana aka sallameta Saboda Haka gabadaya Hankalinshi ba"a Kwance yake ba yana Jin Damuwarsa na Saka Ahali Dadama Damuwa gashi ya Lalatama Mufeeda Rayuwa da Farincikinta Gabadaya Saboda Shi bata da Sakewa kamar baya.


Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace"Umh..Bari nayi mgana da Iya Tukunnah.."Yafada yana Sauke kanshi kasa Cike da bakinciki mai yawa yakama Hanyar Dakin Iya kenan Basma tace"Daddy..." Ya waigo yana kallonta cikin Dankwabe kai da Marairaicewa Tace"Ka fara Shiga Wajen Mufeeda First Daddy..."Tafada Tana Hada Hannuwanta alaman Roko..


  Tsam yayi yana kallonta Cike da Mamaki kafin yace"Alright..."Juyawa yayi zuwa Dakin Mufeeda ammah Kuma Acikin gangar Jikinsa babu karfin Gwiwa Turo kofar yayi Ya Shiga da Siririyar sallama bata Jishi ba Tana Zaune Dirshan Akan gado Naila na kan Cinyarta Kanta ba Dankwali sai Kitson Shikon Dake kanta Wata doguwar Rigar Roba ce ke Jikinta Kirar Bhrain,Kofin Shayi ne Ahannunta Tana Sha gefenta kuma Farantin Silba ne Cike da Kwai da Dankwalin Turawa Wanda Iya ta Kawomata Naila ce ke mika hannu Tana yafiton kofin Shayin Cikin Sanyin muryanta tace"Nailata zaki Sha Shayi ne.."Kamar tasani ko Ta daga kai Dariya Tayi Har Fararen Hokoranta Suka bayyana Kofin takafa mata abaki Tana bata kadan Kadan Tana Sha,Gefe Daya kuma tana gutsurin kwan Tana bata Tana Fadin"Zan Cigaba da baki Abincin aboye Nailata bana so kiyi Rama.."Itako Naila batamin Jinta malulan kwanta Take Cike da Jin Dadi.


Tahir Dake Tsaye bakin Kofa ya saki baki da Hanci yana Kallonsu Gefe Daya Wani Tsausayin Mufeeda ke kara Tasiri Acikin Ranshi ga Naila Wacce in ya kalleta sai yaga ko Hakkinta Allah ya kama Farida dashi bazata Taba Jin Dadin Duniya ba,Ganin Basuji Shigowarsu ba ya Sanya yayi gyaran Murya da Sauri Mufeeda Ta Dago Daga bama Nailan kwai abaki ganin Tahir Tsaye sai ya kara Rikita ta Rude,Ta Riko Naila Lokaci Daya Tana Kokarin Ijiye Kofin Shayi bisa Side Drower sai bai zauna Dakyau ba Da Hanzari Tahir ya Isa Wajen ya Rike Kofin Lokaci Daya yana Dauke Farantin kwan Tsurama Mufeeda ido Cikin Cikin Sanyinsa yace"Shiii..Is ok..Relax.."


  Ya Fada yana Daidaita Natsuwarsa yana kuma kara gyara zaman Brifcase dinsa Dake Hannunsa,Cikin Kunya da Wani Nauyi Mufeeda ta sadda kai Tana Fadin"Ina..ina kwana Daddy..."


Bai amsa ba sai da ya Ijiye Brifcase dinsa gefen gadon Mufeeda ya mika Hannu ya Dauki Naila Wacce Tunda ya Shigo Take mikomai Hannu kafin ya amsa yana Fadin"Lafiya lau kin Tashi lafiya..? Ya fada cikin Kunya kadan Domin bayason ma yana kallon Kwayan Idanuwanta.


Itama Kunyar Takeji Shiyasa Bata Dago ba tace"Lafiya lau.."Shuru ya biyo bayan Mganar Mufeeda,Wacce kanta ke Kasa Duk kunya Ta gama kamata na Halin da Tahir ya Isketa Wata Zuciya tace"Me zaki boye Abunda Yagama Dake.."Dam Take taji Hawaye Sun Cikamata ido Shi kuma cikin Nazarinta ya Furta"Ya Jikin ki..? Kina jin Wani Ciwo Acikin jikinki..?


Shuru Tayi kafin ta girgiza mai Batayi mgana Illah Hawayen Data Rikewa ne Suka zubomata,Tsam yayi yana kallonta tana Share Kwallah cikin Tsausayawa ya Durkusa kan Gwiwoyinsa yana Rike da Naila yace"Don Allah kiyi Hakuri mufeeda kiyafemin laifin Dana aikata agareki Hakika na zama azzalumi Kuma naci Amana,Ina Jin kunyar kaina Mufeeda.."Yafada Cikin Rawan Murya.


Dagowa Tayi ganinshi Durkushe agabatan Yasa Tace Da Sauri."A"ah Daddy Meye Haka..? Don Allah katashi Ni Tun Daren da Abunda ya Faru Zuciyata ta yafemaka bayan ta tabbatar bazaka Taba aikata Haka da gangan ba.."Tafada kai Tsaye Tana Dauke Hawayenta Mikewa yayi Jikinsa Asanyaye kafin yace"Nagode Mufeeda,Ki sanar da Iya duk sanda Kikaji Wani Chanji Ajikin ki kinji ko .? Cikin Ladabi Ta Daga kai Da cewa"Toh Daddy.."Dan Mirmishi yayi kafin yace"Gud gal..Kuma kiyimin Alfarma zaki saki Jiki kamar baya,Kinga su Basma basajin Dadin ganinki Haka.."Kanta na Kasa Ta Dago da Niyyar mgana Suka Hada ido yadda idanuwansa ke Narkar da Zuciyarta yasa Tayi Saurin Sadda kai Tana Fadin"Insha Allahu Daddy.."


Mganarta Tamai Dadi Cikin Farinciki ya Furta.."Allah yayi miki albarka,ga Diyarki zan Fita aiki kada na Mkara.."Yafada yana  mika mata Naila Wajen saka Hannuwanta ta karba Hannuwansu Suka Hadu Waje Daya Wanda Dukkansu sai da Sukaji Wani Shock Atare,Mufeeda Tayi Saurin Jan Hannunta Tana barin Jiki Shi kuma yayi Saurin Doramata Naila kan Cinyarta,Lokaci Daya yana Daukan Brifcase dinsa ya Fice Daga Dakin da Sauri da Kallo Mufeeda ta bishi Zuciyarta na Bugawa batasan Dalili ba Tun Zuwanta gida nan Indai zata ga Daddy Toh Zuciyarta Ta hau buguwa kenan da Sauri Sauri kamar Wacce Tayi Gudun Tsere..


Yana Fitowa yaci karo da Iya Dauke da Ghana must go Cike da Kaya Su basma na Tambayata ina Zata,taci ko Lullubinta Cikin Mamaki ya Karisa Kusa Dasu sai Dai Sukaji Muryanshi yana Fadin"Iya lafiya kuwa..? Ina zaki da Wannan kayan..?


Jin Muryansa yasa Iya Ta Durkushe Kasa Tana Fadin"Alhaji kayi Hakuri da Abunda zan Fadamaka,Na yanke Shawaran zan bar aiki agidan nan bawai Dom kun Saba min ba ko kuma kuna min Wani abu A"ah sai domin Tsira da Mutumcina.."Cikin Wani Haushi Tahir ya Furta.."Kan Issues din Farida ne ko..? Yafada Cikin bacin Rai bai bama iya Zarafin mgana ba yace"Tunda Muke Zaune Dake Acikin Gidan nan Iya na Taba Saba Miki..? Iya ta Girgiza kai Tana Sharan Kwallah Ya cigaba da Fadin"Su basma fa..? Nan ma ta girgiza kai ya kada kai yana Fadin"Toh Tunda babu Daya iya babu Inda zakije matukar Ni Tahir Mansur Danbatta ina Raye,Koda Farida Take Takama Ta Dalilinta Kikazo Gidan nan bata da Ikon Koranki Saboda Nima karkashin Ikona Take,saboda Haka mganar Gaskiya babu Inda zakije kina Tare damu Mudin Rai.."Yafada kai Tsaye kafin yace"Basma,Laila ku kama Jakar iya ku maida mata Ciki ni na Fita sai na Dawo .'Yafada kai Tsaye yana Wucewa Cike da Haushin Farida ji yake kamar ya yanke Duka alakan Dake Tsakaninsu Wata Zuciya tace"Not Now Tahir..Juz leave her to pay Wht She Didt For u.


Iyya bata da yadda Ta Iya Su Basma Suka ja jakarta Zuwa Cikin Dakinta Suna Murna Harda Su bassam Ihunsu ya Fito da Mufeeda Ita da Naila Tana Tambayan Lafiya nan Basma Ke Sanar Da Ita Itama Murnan Tayi Jin Tahir ya Hana Tafiya Tana ji Acikin Ranta In iya Tatafi ai Ta kara Shiga bala"i Fitowar Mufeeda yasa gidan ya kara Dadi Tun Tana Dari Dari dasu Basma Har Ta sake ganin basu kyamaceta ba sai ma Kafa kafa Da Sukeyi Da Ita Hakama iya Motsi kadan Sai Sunje meke Damunta Ita Tsausayi Su basma Ke bata ganinsu yara ammh Susan Matsalolin Rayuwa Da yawa.


******


*DANBATTA*


Ranar Asabar Tun Safe Tahir Da Basma,bassam da laila da Muda Garzali ya Debesu Zuwa Danbatta bayan Tahir ya cika Muda da laila da Sabbin kaya da Kayaan kwalama,gefe Daya kuma an Cika Booth da kayan Abinci Aka bar Mufeeda Da Iya agida da Naila, Wacce da zasu Tafi idanuwanta Suka Cika da Kwallah ganin Haka sai Tahir yace in zata Ta Shirya Harda Iya Su Tafi Gabadaya ammh Sai Mufeeda Tace bazata jeba Ta Shige Daki da Gudu Tana Dannen Kukanta Domin Tana Tunanin Da zarar Taje Danbatta Nunata Za"ayi Tayi na Cewa Tayi Cikin Shege kuma Inna Fulera yanzu batazatayi murna da Zuwanta ba Shiyasa Tace bazata Je ba Ta koma Daki Tana Kuka Abun ya Taba Ran Tahir Har Suka Isa Danbatta kanzil bai ce ba Gabadaya Rayuwarsa batamai Dadi Daya Tuna da Abunda ya Aikata ma Mufeeda sai yaji Duk ya Tsani kanshi.


Baba Hakimi na Waje da Jama"arsa Motar su Tahir Ta Tsaya Tunda Hakimi yaga Tahir yazo Aranshi yace mganar Zainabu ne,Shiyasa Ko Fuskar bai Sakarmai ba bayan Yaran Sungama gaisheshi Suka Shiga Cikin Gida Shi kuma ya Tsaya Waje Suna gaisawa da Jama"a Kafin ya karisa gaban Hakimi ya zauna yana Tankwashe kafa,Yau din yana Sanye ne Cikin Wani yadi kalan Sararin Samaniya Da Hulansa Zannar Bukar kallon Farko zakamai ka Fahimci yayi Rama Sosai sai Dogon Hanci Kai Tsaye ya mika ma Hakimi Hannu yana Fadin"Barka da Safiya Ranka ya Dade..".


Musabaha Sukayi kafin Hakimi yace"Yauwa sannunku da Zuwa..,lafiya nagangu Duka gidan Kuna Tafe da Safe Ina Ita Faridan..?Sunkuyar Dakai yayi kafin yace"Lafiya lau Baba Hakimi Dama na Dawo Dasu Muda ne Hutunsu ya kare Shine Muka Taho Tare dasu Basma.."Gyada kai Hakimi yayi kafin yace"Masha Allah..Allah sa akbarka ya Wajen Ita Mufeedan ince dai ba Wata mtsala.."Kai yagyada mai kafin yace"A"ah Babu Wata Mtala,Sai dai Dama Dalilin Zuwan nawa kai nake son gani Ranka ya Dade..".


Kai Tsaye Baba Hakimi ya kalleshi kafin yayi mirmishin Takaichi yace"Dama na sani Tunda na Ganka nasan kazo kan Mganar Sakaryar Uwarku ce,Uhmm.."Yafada yana Kallon Gefe Dayake babu Kowa saman Tabarman Tunda Tahir ya kariso Aka Watse aka barsu Su Zanta,Gaban Tahir ya Fadi ya Dago Yana kallon Baba Hakimi Cike da Firgici Domin Tunda yake da iyayensa bai Taba jin makamacin Wannan mganar yana Shirin Bude baki yayi Mgana Baba Hakimi ya Dakatar Dashi bayan ya Dagamai Hannu yace Cikin kakkausan Murya"Tashi ka Shiga Ciki zan Shigo yanzu Tunda kaima ka zama Sakarai mata na Walagigi Dakai baka iya Katabus.."Kunya Ta kama Tahir ya Sosa keya kafin ya mike yana Fadin"Ashigo lafiya..'"Ko kallonsa Baba Hakimi baiyi ba Domin Shima Haushinsa yakeji yadda ya biyema Shirmen Mata baizo ya Sanar Dashi Mtsalanshi ba,Da kallo ya bishi har ya Shige Gidan Idanuwansa Suka kada kamar yayi ma Tahir Kwallah Shikenan gareshi kwara Daya Tal kamar Dubu ammh Abu Tayi Sanadiyar Jefa Rayuwarsa Cikin Garari Bazai kyale ba Dole ne ya Nuna mata Kuskuranta Iskancin banza Wautar Wofi Zumunci me?na Cuta da Rashin gaskiya,Haka Hakimi keta Fada Shikadai Acikin Ranshi.


Tahir Sashen Innaro yafara Zuwa Sai ya Tarar Bata Ciki Tana Shashen Goggo Abu kai Tsaye ya Nufi Shashen Goggo Jikinsa Duk ba Dadi na Abunda ke Faruwa Tsakanin iyayen nashi Ta Dalilinshi,Da sallama ya Shiga yana Kokarin Tube Takalmin kafanshi Ashe Dake Zaune Gefen Goggo Abu Dake Kwance Kan Cafet Ta Tada kanta da Filo Ta mike Tana mai Sannu da Zuwa sai Innaro Dake gefenta ,su Basma Kuwa nadaga Gefe Sun Jeru kamar masu karban gafara,


Karisowa yayi yana Amsa ma Ashe Cikin Kulawa gefe Daya kuma yana kallon Goggo Abu Dake Kwance Duk Ta Rame kamaer ba Ita,yana Kokarin zama Kusa da Ita Innaro Tace"Sannu Attahiru..? Dago da kansa yayi yana kallon Innaro Cikin Kunya Domin Kunyar Kanshi yake da Abunda ya aikata Hatta Ashe bai iya Hada Ido da Ita ba,Kansa ya Sadda kasa bayan ya saka Hannu ya Rike Hannun Goggo yana kallonta Tana Kallonshi Itama Idanuwanta Suna Taruwa da kwallah.


Innaro Tace"Karka damu Attahiru kadai jin Wani Iri mu iyayenka ne Munfi kowa saninka Mu bar Haka amatsayin Gaddara mu Fuskanci gaba,Domin Hakimi yayi Fushi Sosai kan Goggo Wlh har yau bai Tako Falon nan ba Balle yazo ya Dubata Nayi mgana abanxa Daga Karshema yace In ban Cire baki na ba sai ya sabamin.."Tafada Kamar Tayi Kuka,Dago da kansa yayi kafin yayi mgana goggo Ta Fara Kokarin Tashi Da Sauri Ya Saka Hannu yana Taimaka mata Ita kuma Ashe ta saka mata Filo Abayanta ta Jingina Suna Jeramata Sannu Atare 


Kai goggo Abu Ta gyada Tana Share Hanci Tafara Mgana"Attihiru Don Allah ka Yafemin Na cutar da Rayuwarka na Zama Sanadiyar Fadawarka Wani,Hali Wlh bansan Abun ya Wuce Misali ba Na zata Farida mai Jin mgana ne,Gashi Ta sakani Cikin Fitina nayi Sanadiyar da D'ana yayi Zina yayi ma Wacce ke kallonsa matayin Uba Ciki..Kaico na Ni Abu gashi Babanku na Fushi Dani Ina zan Saka Raina naji Dadi.."


Tafada Tana Kuka Sosai,Tahir yayi Shuru yana kallon Goggo Zuciyarsa na Gudu Bayansa ya Waiwaya da Niyyar yama Su Basma mgana su basu Waje sai yaga wayam Sun Dade da Ficewa Tun Sadda Innaro Ta Fara mgana,maida Hankalinsa Yayi kan Goggo Abu kafin ya Saka Hannu ya Riko Hannunta Cikin Tsausayawa yana Fadin"Bakomai Goggo Don Allah kidaina bama Kanki laifi,Nima ina da Laifi Tunda na bari Tuntuni Farida Tafi karfina ban Isa na gayamata Taji ba,Abunda ya Faru Tsakanina da Mufeeda goggo bamu Isa mu Tsallakeshi ba Domin Rubutattace ne Daga Rabbil Izzati,Kidaina damun kanki kinga Jininki ya Hau,ki,Daina damuwa Indai Mganar Baba Hakimi ne Abunda ya Kawoni Kenan zan mai mgana Kuma Insha Allahu zai ji mganata Kinji.."Yafada yana Kallonta LokaCi Daya yana Sanya Hannu yana Share mata Hawaye,Hannunsa ta Riko Tana kallonsa kafin tace"Nagode Attahiru Allah yayi Maka albarka.Allah ya Kare Gaban ka da Bayanka ya Raya maka Zuru"a,.."Da Ameen yake amsawa Su Innaro na Tayashi.


Cikin Alhini goggo Abu Tace"Ina Mufeedan? Fatan dai bawata mtsala..? Itama Inna Fuleran Sai da Ta Kwanta Asibiti.."Tahir yace"Lafiyanta kalau goggo ba Wata Mtsala sai Abunda ba"a Rasa ba,Eh Ashe ta sanar dani kafin na Wuce zan Shiga na Dubata kuma na Nemi Izinin Hakimi kan ya bari na Tafi da Inna Fuleran Kaduna Kila Dukkansu In Suna ganin Juna Hankalinsu ya Kwanta."


"Kul..karka Fara Ban Amince ba Kuma Ban lamunta ba.."Sukaji Muryan Hakimi Daga Bakin Falon yana Shigowa Gabadayansu Suka Mike Banda Goggo Dake Zaune Tana kallonshi Cikin Fada Baba Hakimi yace"Ka Barta anan,Kawai ka kyaleta zata Warware Damuwa ce Kuma Ta zama Dole Domin barin Fulera garin nan Zargi zai Hau kan Mutane Har Daganan lbrin ya Shigo Gari Abunda bana Fata kenan.."jinjina kai Tahir yayi kafin yace"Hakane Ranka ya Dade An bar mganar.."


Gyada kai yayi kafin yace"Yauwa...Kuskure ne ya Riga yafaru ba Yarda zamuyi,Tunda ka Hadu da Shashashar Uwa Mara Lissafi Tayi Dalilin bata Rayuwar Mutane Dama Ciki harda D'anta kan Dalilinta Mara Tushe ballatana Makama.."Yafada yana Hararan Goggo Abu Data Sadda kai Tana Sharan Kwallah.


Tahir da Ashe Suka kalli Juna Cikin Rauni Tahir zai yi Mgana Kenan Innaro Ta Rigashi Da Fadin"Haba Ranka ya Dade sai Hakuri,Tunda Abunda Ake Gudun ya Riga ya Faru..."Ke Salamatu Rufemin baki.."Hakimi ya Katseta Cikin Fada Da Fushi.


Shuru Tayi Tana Kallonshi Cikin Nunata Da Yatsa yace"Kul Ki kama bakinki Kan Wannan mganar in ba So kike na Saba Mii ba,kina Wata mganar Banza Inda Tun Lokacin da D'anta yazo mata Bukatarsa Ta Saurareshi Haka Zata Faru..? Nace Haka zata Faru..? Yafada Cikin Tsawa kafin ya Cigaba Da Fadin"Dalilin Rashin Sauraranshi Shi ya Jawo komai,Banta ba Jin inda kaki naka kaso bare ba Zumunci Iskanci ko na Cuta Tunda Ita Faridar batasan Ciwon kanta ba Su kuma Iyayenta Sun saka mata ido toh mu sai mu bar Rayuwarmu Da'nmu Ta lalace ..? Ammh Saboda Sakarci,Kina babba Ki Haifi kamar Attahiru,Da Aisha ammh baki da Wayau ko kadan,Zumuncin Dakike Mgana Ba Dalilina Kikasan Ibrahim din da Aliyan ba..? Haka Kurum Saboda baki Daukeni Da Daraja ba, Kika Dakatar Dashi Wai kada ya sanar Dani Sai da Abu ya Kwabe Kana kizo kina Kuka kina Nadama Lokacin bata da Amfani.."Yafada yana Nuna goggo Da Yatsa Cikin Fada.


Ashe da Tahir dai ba Baki Domin yau kam An kure Baba Hakimi ba Kasafai Yake Fada ba Sai an Kureshi,Hakurinshi Tahir ya Kwaso yana Saba Babban Rigansa yace"Ke ni bari ma Kiji Haushinki nakeje Wlh kamar na Makeki Abu,Shiyasa na Kyaleki ki Girbi Abunda Kika aikata Kin Cucu kanki ne Domin Ita Farida ba Ita kika batama Rayuwa ba Marainiyar Allah kika saka Cikin Gararin Rayuwa kuma sai Allah ya Sakamata akanki Domin Duka Laifin na Attahiru ya Rataya a Wuyanki ne Zainabu.."


Yafada Lokaci Daya ya Juya yana kokarin Ficewa Daga Falon Goggo Abu ko Banda Kuka Babu Abunda Takeyi Innaro na Tsaye Ba bakin mgana Tahir ne ya Bi bayan Hakimi yana Fadin"Baba...Ka Tsa..."Kai Saurareni nan Attahiru.."


Hakimi ya Katseshi bayan ya Waigo Sagale Tahir yayi yana Kallon Hakimi Wanda yakallesa Shima yana Fadin"Bari kaji na Fada maka zaka batama kanka Lokaci ne Indai Akan Mganar Abu ne,Gwara Tun Wuri kazo ka Wuce Sabgar ka zaifi maka in kuma ka Dameni Wlh Allah Harda kai zan Hada na ci Muku Zarafi Domin kaima ina Cike dakai yadda ka zauna mata na Kwallo da Rayuwarka kajima na Fada maka.."ke Aisha...? 


Yafada yana kallonta da Sauri Tace"Na"am Baba.."


"Fitio Maza Ki Tarkata ya"yanki ki Wuce gida kaima ka Tarkata naka ka koma bakin Aikinta Ku barta Ta Shiga Nadamarta Ita kadai.."Yafada yana Ficewa Daga Falon.


Gabadayansu Jikinsu yayi Sanyi bamai Kwakwaran Motsi sai Kukan Goggo Abu Dake Tashi Kasa kasa.


*Don"t Forget to Vote,comments, Share and like...*


*Shakira*.

Anitha*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


      *BABI NA GOMA SHA BAKWAI*


""""Riƙe ƙugu Tahir yayi yana Sauke Ajiyar Zuciya, gefe Ɗaya kuma Zuciyarsa na Gudu Sosai Saboda Damuwa, Ashe ce Dake gefe Ta ƙarasa Kusa da Goggo Abu Ta Zauna Kusa da Ita Kafin Tace "Goggo..."


Ta faɗa Tana kallonta Innaro Dake Tsaye Ta Ɗora Hannu Bisa Haɓa Tana Faɗin "Wai Hakimi meke Damunshi ne..?Tunda nake Dashi ban taɓa ganin yayi irin Wannan Fushin ba.." Tahir ya waigo ya Fara Taku Zuwa Kusa da Goggo Yana Faɗin "Ranshi yana ɓace...Dole a saurara mai Har ya Sauko Da kanshi.."


Ya faɗa yana Zama gefen Ashe, Dayan Hannun ya kama yana Faɗin "Goggo Don Allah Kiyi Haƙuri kibar kukan nan Haka nan Nayi miki alƙawarin Komai zai Daidaita Insha Allahu..." Ya faɗa yana Kallonta Goggo Ta Murmusa Tana kallon Tahir da Ashe kafin tace "Bakomai...Allah yayi muku albarka Ku Tashi ku Tafi kubi Umarnin Mahaifinku.." Ta faɗa Tana ƙoƙarin Ɓoye Hawayen Da Suka Taru acikin ƙwayan Idanuwanta.


Innaro ta saki Numfashi Tana Faɗin "Shine kawai magana Don Rashin Tafiyar Naku ma Matsala ne, ku Tashi ku Tafi Insha Allah komai zai zo da Sauƙi, maganar Mufeeda kuma Iya ta Dinga Kula da Ita Saboda yarinya ce..ko Goggo ya kika gani..?" Hannunta Ta zare cikin na Tahir kafin ta saka Hannun ta Share Ƙwallarta Tana Faɗin "Eh Hakan ma yayi Innaro, Allah ya Sauketa lafiya kabiya ka gaida Fuleran karka manta.."


Gyaɗa kai yayi kafin yace "Insha Allahu.." Har ya Miƙe Innaro Tace "Ya ita Faridan...? Ina Fatan ba Wata matsala...?" Jinjina kai Yayi kafin yace "Eh Innaro ba Wata Matsala..."


Sauke Numfashi Tayi kafin tace "Masha Allah...Ko jiya naji Mahaifinta suna Waya da Hakimi kan mganar ne, Allah Ubangiji ya kawo mana Komai Da Sauƙi..."..


Gaba ɗaya Suka amsa da Ameen Kafin Ashe da Tahir suyima su Goggo Sallama Suka Fice Suka barta Tana Share Ƙwallah Fita Sukayi Inda yabama Garzali Umarnin ya Shiga da kayan Abinci Zuwa Cikin Gidan Hakimi, A ƙasa Suka Taka Shida Ashe Har Zuwa Gidan Inna Fulera, Wanda Suna Tafe Tahir na Faɗama Ashe Abunda ya Faru da Wanda yake Faruwa yana gaya mata kamar ya Zubar mata Da Hawaye, Cikin Tausayin Ɗan'uwanta Take Lallashinsa Take bashi Shawaran karya Damu, kuma ya ƙyale Farida Duk inda Zataje Zata Dawo ne bayan Duniya ta koya mata Hankali ya yarda Da Shawaran Ashe Duk da A lokacin Farida bata da wani Fari Acikin Zuciyarsa.


A haka suka isa Gidan Inna Fulera, Ashe ce Ta fara shiga Suka Gaisa da Inna Fulera da Maman Lantana kafin tace musu Tahir zai Shigo Cikin Sauri Maman Lantana ta gyara Tabarma Tahir ya Shigo ganin Maman Lantana ne Awajen yasaka Daga Ashe Har Tahir ba Wanda ya Tada maganar Illah Sunkuyar da kai Da Tahir Yayi kunyar kansa na Ƙara kamashi ganin yadda Inna Fulera ta Rame Lokaci bayan Lokaci Tana Share Ƙwallah...


Basu Wani Daɗe ba Tahir ya Miƙe zai Tafi bayan ya bama Ashe 30k yace Tabama Inna Fulera, Ashe na Bata taƙi karɓa Sai Ta Fashe da Kuka Lokaci Ɗaya Ta Ɗago ido Tana kallon Tahir bayan ta Ɗago Daga Kwancen Datake Maman Lantana Tana gyara Mata Filon Kanta Saboda Taji Daɗin Zaman Sosai.


Cikin Muryan Ciwo da Kuka Inna Fulera tace "Alhaji....."Ta faɗa Muryanta na Sarƙewa, cikin Sanyin Jiki Tahir ya Tsaya cak kafin ya Waigo Zuciyarsa na Tsinkewa Sosai Cikin Muryan Sanyi da Roƙo tace "Bana Buƙatar Kuɗinka Alhaji Abu Ɗaya Nake da Buƙata Awajenka.." jikinsa na Rawa ya Dawo ya Duƙe agaban Inna Fulera yana Faɗin "Ki Faɗi Abunda Kike Buƙata komai kike Buƙata matuƙar na Mallakeshi zan baki Shi Inna.." Ya faɗa Cikin Karaya..


Muskutawa Tayi kafin tace "Ba komai nake Bukata ba Illah ka Riƙe min Mufeeda Tsakani ga Allah...Ka zama gatanta..!kaji ƙanta..! Ka jibanci lamarinta...! Ka zama garkuwa a gareta Alhaji Domin Duk Duniya Mufeeda bata da Wani gata bayan kai..Don Allah kar ka barta tayi kukan maraici In kamin Wannan Abun Ka gamamin komai kuma Bana Buƙatar Wani kuɗi ko Kawan Duniya Farin cikin Mufeeda kaɗai Shine Burina Alhaji.." Ta faɗa Tana Rushewa da Kuka, Maman Lantana Dake gefe kanta ya Ɗaure amma bata kawo komai ba sai ta barshi a ƙila zafin Ciwo ne ke Damun Inna Fuleran.


Ƙuri Tahir yama Inna Fulera da Ido kafin ya maida kallonshi kan Ashe Wacce Idanuwanta Suka Cika da Ƙwallan Tausayin Inna Fulera Iska mai Zafi ya Furzar kafin yace "Girman alƙawari Inna Ba Abu bane mai Sauƙi, Amma Duk Da Haka Nayi miki Alƙawarin zama Gatan Mufeeda, Nayi miki alkawarin bazan bari Mufeeda Ta ƙara kukan Wani Abu ba...Sai na zama Silan Murmushinta anan gaba.." Ya faɗi Haka Idanuwansa Sun kawo Ruwa kafin ya miƙe da Sauri ya Fice Saboda Yadda Inna Fulera Ke kuka Tana Godiya sai yaga Kamar Bazata Tashi ba, Lokaci Ɗaya kuma Kunyar Abunda ya aikata ke Dawo mai Har Ashe ta Fito yana Tsaye yana Maida Hawayen Idanuwanshi Haka Suka Jero Har Zuwa gidan Hakimi ba Wanda ya ƙara magana, bai koma Cikin gidan ba Ashe ya umarta data cema su Basma Su Fito Tare Suka Fito Dasu Laila sama sama yayi ma Hakimi sallama suka Shiga mota Har da Ashe Har gidanta Suka kaita Kafin su Sauketa ita dasu Muda da Tsarabansu 20k yabama Muda da Laila ita kuma Ashe ya kara mata 10k ta ƙara Da Wanda ya bama Inna Fulera Taƙi karɓa Haka Motarsu Ta Ɗaga Ashe Ita da 'ya'yanta Suna Daga maSu Hannu Har Suka ɓace ma ganinsu.


Sai yamma Suka Shigo Kaduna Tahir na Sauri Ko Gida bai Shiga ba Garzali ya Juya Dashi kamfani ya samu Kiran gaggawa bai Dawo ba sai Dare Lokacin kowa yayi barci iya kaɗai ya Tarar Farke, Mufeeda Ita da Naila Sun Daɗe da yin barci gaisawa sukayi sama sama, kafin ya Haura Zuwa Ɗakinsa Ransa Duk babu Daɗi ko yayi Wani Motsi sai ya Tuna da Alƙawarin Inna Fulera wanda Maganar da Suka gama Tattaunawa da Ishaq kenan kafin Su Rabu gaba daya Abubuwa sun mai yawa yanzu Farida bata gabanshi Matsala Goggo ce Sai Tausayin Mufeeda Daya ƙi barinshi Su sukafi Zama Cikin Ranshi Suka Hanashi Sukuni.


****


Farida kuwa Tana gidan Bilkisu Wajen Kwananta Uku amma basu ci karo da Mijin Bilkisu ba mai Suna Aliyu Saboda Tun Safe yake Fita kuma sai Dare yake Dawowa, Sai ya Fita Farida ke Fitowa Haka Kuma kafin ya Dawo Bilkisu zata san yadda Tayi Ta Hillaceta ta koma Ɗaki Abunda ke bama Farida Mamaki yadda Bilkisu ke Rawan Jiki da Abban su Walida in ya Dawo Haka zata Tsala Wanka, Taci Gayu Tana Kwakwarsa, In ko Ta mata sallama bata ƙara sakata a ido sai Washegari bayan ya Fita, Amma kuma Tana Daga Cikin masu bata Shawara ko Acikin group ɗinsu na makaranta Kan Mace ta Daina sakarma Namiji amma Ita gashi Bata Iya Haɗa komai da Mijinta.


Wani Abunda baima Farida Daɗi ba Shine yadda Bilkisu Ta Dinga yaɗa Abunda ya Faru Wajen Sauran Ƙawayensu Waɗanda basu san Meke Faruwa ba Haka Suka Haɗu agroup ɗinsu na Classic Ladies Sukayi Ta Tsinema Tahir Aciki Harda masu bata Shawaran Takaishi ƙara Kotu, yaƙe kawai Farida Keyi amma Bata jin Daɗin yadda Billy ta Fallasasu A duniya ba Ko ba komai Tana Son Tahir Kuma Har gobe yana Matsayin Uban 'ya'yanta ne, Kuma Mijinta.


Ɓangaren su Umma kuwa basu san Abunda ke Faruwa ba Don Daga Faridan Har Tahir ɗin ba Wanda basa Waya Dashi amma ba Wanda yace ga wani Abu, Ita Farida Tsoron Su Umma ne Domin Tasan Ranta sai ya ɓaci Balle Abba dayayi Fushi da Ita don Musamman ya Kirata ya Zageta Tas, Balle kuma tace Ta Baro Gidan Tahir ai kila sai Abba ya Kusa Tsine mata, Shiko Tahir Faridan ne Kwata Kwata bata gabanshi Baya Fatan ya ƙara Buɗan baki ya Faɗi Wani Abu Daya Danganceta ya Ratayeta Gefe ne Domin Ahalin Da yake Ciki yafin Jin Tsananta da Haushinta Fiye da Kanshi Shiyasa Ko Umma ta tambayeshi Suna Zaune lafiya yake cema ta ba wata matsala Domin Kaucema Duk Abunda zai Dawo Da Farida Yamafi Jin Daɗi da bata nan Ko ba komai bayasan Abunda zai Dinga Takura Mufeeda.


  Sai Ranar Data Kwana A cikin Gidan Kana Suka Ci karo da Abban su Walida, Ranar bai Fita ba Kwata kwata yana gida, Lokacin Daya ga Farida yayi Mamaki sosai nan yake Tambayanta Yaushe tazo..? Sai tace mai ta kwana biyu ma..Ido ya Zaro yana kallon Billy Wacce Tayi Fiƙi Fiƙi da Ido Zuciyarta na Tsananta Bugu Wani kallo yabi Farida Dashi bai dai yi magana ba Amma Acikin Ranshi yana Tunanin Wani Shirme kenan Mace da Gidan Mijinta Kuma Tazo Gidanshi Ta tare, Ina bazai Ɗauki Wannan Iskancin ba.


Bai mata magana ba sai da Suka Shiga Cikin Bedroom Ɗinsu kana ya Tsareta da Ido yana Faɗin "Da wani Dalili Farida Tazo nan gidan Harta kwana uku ban sani ba..? Ke dama wani Manufa Matar Da take da Mijinta..?"


Ya faɗa yana Hararanta Sanin Halinta na Shanshanci Shi bai Sake mata ba Shiyasa Duk yadda Billy taso tayi Iskanci bata samu Dama ba, Cikin Rawan Murya tace "Dama..Dama..Umh..." Tsawa Ya Daka mata yana Faɗin "Dama Menene..? Baki zaki Buɗe kiman magana Yadda zan Fahimceki kinsan bana son Raini ko....?"


 Kai ta gyaɗa kafin tace "Matsala suka samu da Abban su Basma..." Kallonta yayi A ɗage kafin yace "Matsala..?" Ya maimata da Sigan Tambaya kai Ta gyaɗa mai alamar Hakane, Cikin Dariyan karki Raina min Wayau yace "Kuma Shikenan Don Sun samu Saɓani ita da Tahir sai kuma akace tazo gidan Aurenki ta tare ko..? Ke gaki Uwarta ko kuma Mai bata Shawaran karta koma gidan Mijinta ta cigaba da zama agidan naki Mijin..?" Ya faɗa yana kallonta Cikin ɓacin Rai..


 Jikin Billy na Rawa Ta Riƙo Hannunshi Tana Faɗin "Don Allah ka Tsaya ka Saurare Abban Walida Wallahi Tahir ya chanchanci Farida Data barshi Amanarta fa yaci Shida yarinyar Datake mata Renon Naila.." Ta faɗa Lokaci Ɗaya Tana Zaunar Dashi gefe Ɗaya Kafin ta Fara Rattaba mai yadda Akayi Billy Saboda Sharri Harda ƙari kamar Agabanta Akayi 


 Haba Aliyu ya riƙe Kafin yace "Ke Bilkisu bana son Ƙarya fa..? Shi Tahir ɗin..? Haba Don Allah ya za'ayi mutum mai Daraja ya aikata Haka, Tahir fa Yana da Kima Sosai a idanuwan Waɗanda Suka sansa.." Ya faɗa yana Tantama Rantsuwa Billy Ta fara Jera mai, Domin ya yarda Da Ita, Bai yarda ba Miƙewa yayi yana Faɗin muje naga Faridan, Jiki na Rawa Tamai Jagora Zuwa Ɗakin data Sauke Farida, Cikin Tsare gida yake Tambayanta gaskiyan lamarin Cikin Kuka Farida ke labarta mai Hadda Hukuncin da Iyayenshi Da nata Suka bashi goyon Baya.


 Tana Faɗa tana Share Ƙwallah, Jinjina kai Aliyu yayi kafin yace "Lallai ba Shakka In ko Hakane Tahir bai kyautama kanshi ba ya Cuci kanshi kuma ya Tozarta iyayensa Da kuma Zuri'arsa..Ya bani kunya Sosai, kuma sai na kirashi na mai magana.." Da Sauri Farida tace "Don Allah Abban Walida ka ƙyaleshi ko kayi mai magana bazai Saurareka ba baya ganin Abunda ya Aikata amatsayin laifi Tunda Haryana Ikirarin data bar gidan Gwara ni na Fita na bar mai gida.."


Miƙewa Aliyu yayi Daga kan Sofa yana Faɗin "maganar banza kenan Har office ɗinshi Zani Wallahi..Sai na gaya mai gaskiya sai dai ko karyaji Daɗi.." Daga Haka ya Fice Daga Ɗakin Cike da Mamakin Tahir ɗin Duk da ba wani Kusanci Suke da Juna sosai ba, amma Suna Taɓa Juna Lokaci bayan Lokaci Saboda ƙawancen Matansu Da ba yanzu yake ba, Yana Fita Farida Ta Miƙe zatama Billy magana tayi Saurin Dakatar da Ita tana Faɗin "Kinga Farida Bar maganar nan sai gobe..Yanzu lokacin Abban Walida ne kada mu Shiga Hakkinshi Nasan, Halin yan kaya na.." Daga Haka ta Fice Ta bar Farida Riƙe da baki Tana Binta da Kallo.


****

Washegari kuwa Da Misalin Ƙarfe 3:00pm na Rana Aliyu ya ƙwanƙwasa Ƙofar Office d'in Tahir inda ya bashi Umarnin Shigowa Suna Tare da Ishaq lokacin Suna Wani Lissafi ganin Aliyun sai da yayi mgana Cikin Fara'a Ya Tarbeshi yamai iso Zuwa Kujeran Dake office d'in Ruwa ya kawo mai Ya Zuba mai ya Mika mai ya karɓa yana Mai Godiya sai da yasha Ruwan ne ya Miƙawa Ishaq hannu suka gaisa Cikin Sakin Fuska ya kalli Tahir yana Faɗin "Alhaji Tahir Wajen ka nazo, Wata maganace mai Muhimmanci ke Tafe dani.."


 Shiru Tahir yayi kafin yace "Allah Sarki ba komai ina Jinka.." Ya faɗa Cike da Mamaki Lokaci Ɗaya yana zama agefensa, Kallonsa Aliyu yayi kafin ya maida kallonshi kan Ishaq, Tun kafin yayi magana Tahir yace "Karka damu ka faɗi maganar Ishaq Tamkar Ɗan'uwa yake a gareni.." Zakuɗa kafaɗa Aliyu yayi kafin yace "Kana da Labarin Matarka Farida na gidana Tun Ranar data bar gidanka..?"



Tahir ya Ɗago ya kalli Ishaq shima ya kalleshi kafin  Duka su maida Hankalinsu kan Aliyu Lokaci Ɗaya Tahir yace "Ah...Ina zan Sani kuwa Alhaji Aliyu.." Ya faɗa Cikin Halin Rashin Damuwa, Gyara zama yayi kafin yace "Toh Tana gidana nima bansani ba sai jiya na sani Shine na Turke Ita Bilkisun Shine Take Sanar dani Wani Labari mara Daɗin Ji ban yarda ba sai da Na Kira ita Faridan Na ƙarajin Ta bakinta Wai Alhaji Da gaske ne Maganar da Suka Faɗa min..?"


Miƙewa Tahir yayi yana Kallon Aliyu kafin yace "Wata magana kenan..?" Ya faɗa Jijiyoyin kansa Sun Fara Tashi Saboda Ɓacin Rai Cikin Jimami Aliyu yace "Na kama yarinyar Da kuka Ɗauko Daga Garinku tana muku Rainon Naila Ciki.." Ya faɗa yana Sakarma Tahir ido, Runtse ido Tahir yayi Zuciyarsa na Tafasa kamar tayi Bindiga Haka Shima Ishaq yana Tsinema Farida ne a Cikin Ranshi, shi Wallahi ko Zahra bai yarda ya bata wannan Labarin ba balle ke ace Mijinki amma baki da Buri sai na Tona mai Asiri ki tozartashi.



Taku Tahir yayi Zuwa bakin Window Office ɗinshi ya yaye labulen Wajen Cikin Juya baya yace "Eh Da gaske ne Aliyu..Nama Mufeeda Ciki, amma Duka Abunda ya Faru ba laifina bane Laifin Farida ne Ita ce Sanadiyar Jefani Cikin Halaka amma Wallahi bayan Matata Farida ban taɓa Keta Gonar da ba Tawa ba sai akan Mufeeda Wacce Ƙaddara ta Hau kanmu.." Ya ƙarashe Faɗa Cikin Muryan Kuka, Miƙewa Aliyu yayi yana Faɗin "Ashsha Kaji ko..? Abu baiyi Daɗi ba.."


Tahir bai bashi Zarafin ƙara magana ba, ya Shiga bashi Labarin irin zaman Wulaƙancin Dayayi da Farida da yadda ta banzatar da Rayuwarsa da Ƙoƙarinsa na ƙara Aure da yadda Goggo Take Dakatar dashi har Zuwa Faruwan komai Ya ƙarashe yana Faɗin "Wallahi Tallahi..Farida Ta Cutar dani Cutar da Allah ne kaɗai zai sakamin, Sai Farida tayi Wata Huɗu bata kalleni A shimfiɗa ba, Ku gayamin Ni Dutse ne ko Gunki da bazan Buƙaci mace ba..?" Ya faɗa lokaci Ɗaya yana Juyo da Fuskarsa Wacce Hawaye suka Wanke mishi ita.


 Daga Ishaq Har Aliyu Jikinsu yayi Sanyi Sosai Aliyu ne ya ƙarasa Kusa Dashi ya Dafa Kafaɗarshi yana Faɗin "Cool Down Ka daina Kuka, Haƙiƙa Wannan Abun da ya faru ƙaddara ne ko Kuma nace Darasi ne ga Farida da Goggo, Amma fa maganar gaskiya kana da babban Laifi Tahir na yarda kabar Farida ta Rainaka take yarda taga Dama bayan Kai kake Aurenta aiko Min gatan da iyayenta Suka bata Tunda tabar Gabansu Ta Dawo ƙarƙashin Ikonka ya kamata ka Nuna mata ƙwanjinka na Mulkinka Amatsayinka na Namiji mai Cikakken Iko Agidanshi.. Maganar gaskiya kayi Kuskure.." Ya faɗa yana Murza Kafaɗarsa.


Numfashi Tahir ya Sauke kafin yace "Tabbas maganarka Hakane... Haƙurina da girman Iyayenta Danake gani Da kuma Nasihan Goggo Akaina da Kuma 'ya'yan Dake Tsakanina da Farida yasanya Bana iya Mata Wani abu, In tayi ba Daidai ba Shine Kuskure na barta ta saba da Komai tayi Daidai ne Tabbas nima ina da Laifi ba komai Ake ma Haƙuri ba Gashi Haƙurina yajamin naje na Afkama Marainiyar Allah Daga Ƙarshe na zama Abun YaɗaWar Farida Kamar bamu Haɗa komai da Ita ba, ba komai...Haka Allah ya Tsara min.." Ya faɗa yana Share Hanci kamar Wani yaro.


Kafaɗarsa Aliyu ya Daka kafin yace "Kazama namiji Abokina ka ganni nan bana ma Bilkisu da Wasa Tunda na Lura tana da Rawar kai Ubanta Nakeci tasan Halina ko yanzu ɗin ma ina komawa zan Koro Faridan Dole ta Dawo Tunda bata da Wajen Zuwa..."

 

 Da Sauri Tahir yace "No..no plz ka ƙyaleta Ka barta ta Zauna Da kanta zata Dawo ba sai kamata magana ba ai zataga Abunda saɓanin Shi Suke gaya mata zata ma kanta Faɗa Tun kafin Wani ya mata.." Ishaq yace "Shawara mai kyau Tahir..."


Aliyu ya Saki Hannu yana Faɗin "While Tunda kace Haka zan saka musu ido.. Amma True Tak, Yarinyar nan ta Haihu ka Aureta Wallahi Sweet Sixtyn suna da Daɗin Sha'ani, Tuni Farida zata Rena kanta Ta Dawo Tana begenka Lokacin Da ka mata Nisa.." Dariya Ishaq ya saka kafin yace "Shawara mai kyau..Dama Shi ya Chanchanta yayi Wuf da Ita.." Hararanshi Tahir yayi Bai yi Magana ba, Shima Aliyu Dariya yake kafin su Cigaba da Tattauna maganar Tare Suka Fito Sai da Sukayi sallar La'asar Cikin Jam'i kana suka Rako Aliyu ya Hau Motarsa Zuwa gida, su kuma suka koma Office d'in Tahir Ishaq bai Dawo da Maganar ba ganin Tahir ya basar da Zancen ya Ɗauko Lissafinsu suka cigaba dayi amma Cikin Ran Tahir Tsanar Farida ce ke ƙara Ninkuwa in ya Tuna Tana chan tana Yawo Dashi Acikin Duniya kamar babu Igiyan Aurenshi Akanta.



******


*BAYAN SATI ƊAYA*


Lokacin Tuni Har Su Basma Sun koma Makaranta Hadda Itama Mufeedan Don Da Tahir ya nuna kamar Ta Haƙura da Karatun Saboda Gujema idon Mutane sai Ta Fara Share Ƙwallah Shi kuma ƙwallar Mufeeda kamar dalma yake Acikin Ranshi, dole ya barta ta cigaba da Zuwa Makaranta amma bayan yaje yama Shugaban makarantan Bayanin Cewa Mufeeda matar Aure ce, Kuma tana Ɗauke da Juna biyu So School Authority Su kula da Ita, basu Tsaya Tambayan Waye Mijin Ba Illah Suka yarda da maganar Tahir Suka kuma Rubuta Cikin Record Book.


 Hatta da Islamiyya ta koma Abunta kamar ba Ita ba, sai dai Tayi Kiɓa Sosai, Ta ƙara Fari ta Cika ta Ko'ina Saboda tana samun Abunda Take so Abincinta Dama Shine Faten Wake, sai ƙosai da Koko sai kayan kwaɗayi Irinsu Goriba, yalo Sai Ice cream Wanda In Mufeeda bata Sha ba kamar Cikin zai ɓare, Shiyasa Tahir kullum zai Dawo sai ya Shigo mata Dashi, Ba laifi Iya na Kula da Ita sosai su Basma ba'a barsu Abaya ba Lokaci kaɗan Mufeedan Ta Saki Ranta sai dai Tunanin Innarta Dayaki barin Ranta.


Ɓangaren Su Goggo Abu kuwa ba Wani Cigaba, Tahir Sau Ɗaya ya Kira Baba Hakimi Awaya Tunda yaji ya fara mai maganan Goggo Abu ya Datse Kiran, Tun daga Ranar ko ya Kirashi baya Ɗauka Dole ya Haƙura sai dai yana Kiran Goggo Akai akai Yana ƙara bata Haƙuri amma ya Ɓoye mata Shima Saboda Ita Baba Hakimi ya Daina ɗaga Wayarsa sai dai ya Dinga Nuna mata ta kwantar da Hankali komai xai Daidaita.


*******


Yana Toilet yana Wanka, Akayi ta Kiran Wayarsa bai ji ba sai da ya gama Wanka ya ɗauro Alwala ya Fito Ɗaure da Towel A ƙungunsa Ƙaramin na Saman kansa yana Tsane Ruwan Jikinsa, Yaji Kiran Wayarsa Cikin Sassarfa ya isa Kusa da Wayar, Abunda ya bashi tsoro ganin Kiran Baba Hakimi, Da Asuban Fari Domin Lokacin Wajen ƙarfe 4:43am ne.


  Cikin Firgici Da Tsoro ya ɗaga Kiran yana Faɗin "Salamu Alaikum Baba..?" Ya faɗa Cikin Rawan Murya banji me akace ba Sai dai naji Tahir ya saki Salati yana Faɗin "Innalillahi Wa'inna Alaihirraju'un..Allah ya Jiƙanta da Rahma Allah yasa ta Huta..."


Ya faɗa kafin ya Ɗauke Wayar A kunnensa Cikin Mutuwar Jiki ya Faɗa gefen gado yana Dafe kanshi Ko'ina na Jikinsa na Rawa, lokaci ɗaya Yaji Hawaye Sun Cika mai ido Har Sun Fara gangarowa.






*Shakira*

*Aisha Alto*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


      *BABI NA GOMA SHA TAKWAS*


........Ya Daɗe Zaune a gefen Gado yana Dafe da kanshi yana Jimamin Abunda Baba Hakimi ya Sanar Dashi, Tausayin Mufeeda na Ƙara Cika masa Zuciya. Rashin Mahaifiya Akwai Ciwo balle Ita Daba Uwa ba uba..


Ya daɗe Zaune Baisan Iya Adadin Lokacin Daya Ɗiba yana Tunani da Kuma Tausayin Mufeeda ba, Kiran Sallah ya ƙara Jiyowa Daga Masallatan Dake Kusa Dasu Zabura yayi ya Miƙe Lokaci Ɗaya yana Duba agogon Wayarsa yaga 5:10am Da Sauri Ya Nufi Wardrope ɗinshi ya Buɗe ya Ɗauko Wata Jallabiya mai Ruwan Toka ya Zura Hula ya sanya kafin ya Ɗauki Carbin sa ya Fice Daga Ɗakin.


Ƙasa ya Sauko Zuwa Ɗakin Bassam Shi ya kuma Tashi Su Basma, Iya kuma Koda ya Leƙa Ɗakinta Ta tashi sai yace Ta tashi Mufeeda Lokacin Sallah yayi, Daga nan Suka Wuce Masallaci Shida Bassam sai Wajen Bakwai Saura Suka Dawo Suna Shigowa Falon Suka Iske Basma Tsaye da Uniform A jikinta Cikin Girmamawa Ta Duƙa ta gaishe da Tahir, Cikin kallonta yake amsawa yana Faɗin "Ku Saka kayan gida ne Basma Gaba ɗayanmu yau Ɗanbatta zamu.." Tare da Bassam Suka Kalleshi Cikin Murna Suka ce "Da gaske Daddy..?" Kai ya gyaɗa musu alaman Hakane Tsalle Suka Farayi alamar Murna Cikin Dakewa yace "Ku ɗiba kayanku koda Kala Uku uku ne sai bayan Kwana Uku zaku Dawo.." Jin Haka yasa Suka Zura da Gudu Zuwa Ɗakunansu da Kallo ya bisu Acikin Ranshi yana Faɗin Kurucci Dangin Hauka.


Yana Shirin Haurawa Sama Iya ta Fito Daga Kichen ganinshi yasa Ta saki Fuska Tana Faɗin "Ah...Alhaji Barka da Safiya.." Cikin Sanyi ya waigo yana Faɗin "Ina kwana Iya..?" Ta amsa da lafiya lau bai bata Zarafin magana ba yace "Ahm Iya Ki Shirya kayanki ki kuma Saka Mufeeda Ta Shirya Kayanta Ɗanbatta zamu yanzu da Safen nan." Iya ta Ji Zuciyarta ta Tsinke da Sauri Tace "Ɗanbatta kuma Alhaji..? Allah sa lafiya..?"


Shiru yayi kafin yace A hankali.. "Mahaifiyar Mufeeda ce Allah yama Rasuwa Jiya da Daddare yanzu Baba Hakimi ya Kirani yake Faɗa min.." Dafe Kirki Iya Tayi kafin tace "Innalillahi Wa'inna Alaihirraju'un..." Ciwo Tayi Alhaji..?" 


Kai ya gyaɗa mata kafin yace "Eh har ta kwanta Asibiti ma, Ki Taimakama Mufeeda Don Allah Iya, Kuma karki Sanar da Ita Domin batasan Halin Da'ake Ciki ba.."Jinjina kai Iya Tayi Tana Faɗin "Allah Sarki Haƙiƙa Mufeeda Tayi Rashi babba..Allah Ya Jiƙan Inna Fulera, Insha Allahu Alhaji yanzu zamu Shirya.." Ta faɗa Cike da Tausayawa.


Gyaɗa mai kai yayi kafin ya Haura sama Ita kuma ta Koma Kichen Ta Cigaba da Soya Dankali, cikin Jimami da Tausayin Mufeeda sai da Ta kammalah Duka Abun karyawan Ta kwaso Zuwa Dininng kana Ta Shiga Ɗakin Mufeeda Ta Isketa Tayi Wanka Har ta shirya Cikin Uniform ɗinta Naila ma Ta mata Wanka Ta Shiryata Cikin Riga da Wando, Tana gefen Gadon Tana Riƙe da Hannun Naila wacce Ke Tata tan Tafiya, cike da Tausayin Mufeeda Iya ta Shigo Ɗakin Tana Faɗin "Mufeeda Ki Cire kayan Makarantar ki saka na gida kuma ki Haɗa kayanki Cikin Akwati Naki dana Naila yanzu Alhaji ke gayamin Ɗanbatta zamu Tafi Dukkanmu sai mun kwana Biyu A chan.."


Da Sauri Mufeeda Ta Ɗago Tana kallon Iya Cikin Fitar Magana tace "Ɗanbatta kuma iiya..? Na Shiga Uku ko Gida Daddy zai maidani..?" Ta faɗa Idanuwanta na Cikowa da Ƙwallah Saurin girgiza kai Iya Tayi Tana Faɗin "Ko Ɗaya inaga dai Hutu Alhaji ya samu yakeso muje chan Muyi Hutun.." Ta faɗa Tana Ƙara Jin Tausayin Mufeedan, jin Haka ya saka Mufeeda Ta Washe baki Tana Faɗin "Da gaske Iya..? Yau zan kwana A ƙirjin Innata.." Ta faɗa Cikin Farin ciki Lokaci Ɗaya Tana Ijiye Naila kan gado ta isa Wajen Akwatinta ta Ɗauko, Iya Fita tayi Tana Sharan Ƙwallar Tausayin Mufeeda.


Shiko Tahir kafin ya Shirya sai da ya Kira Ishaq ya Sanar Dashi Cikin Tausayawa Ishaq yace Ya Jirashi gashinan Zuwa Su Tafi Tare Haka ko Akayi, ƙarfe 8am da 'yan Mintina Gaba daya Sun gama Shirinsu Sun karya Tahir ne ma bai Karya ba, Lokacin da Suka Fito sai ga Ishaq ya ƙaraso, musabaha Sukayi da Tahir Su Basma kuma Suka Ranƙwafa Suna gaisheshi ya amsa yana Shafa kansu, Nan da nan Suka Shiga Mota bayan Garzali ya Zuba kayansu Cikin Booth d'in Motar, Harda Tahir Shima da Jakar kayansa, Cikin gida kuwa Iya sai da ta kashe komai na Wuta Kana Suka Fito, Motar Garzali Su Iya da Basma da Bassam da Mufeeda Suka Shiga Tahir  wanda ya ke Riƙe da Naila, da ishaq suka Shiga Motar Ishaq ɗin, Tara da Wani Abu na Safe Suka Ɗauki Hanya bayan Tahir ya Kira Baba Hakimi yace Atsahirta da Jana'izar Inna Fuleran Har su Iso ko Mufeeda ta samu ganin gawar Mahaifiyarta Suna Tafe Suna Janjanta Abun Shida Ishaq, Lokaci Ɗaya kuma suna Gudu ba Sosai ba.


******


Ƙarfe 11 da 'yan Mintuna Motocinsu Suka Yada zango A ƙofar Gidan mai girma Hakimin Ɗanbatta Inda Suka Tarar da Al'umma Tsaye, wasu kuma Suna Zaune da alaman dai Isohuwarsu Ake jira, Mufeeda Kuwa Tunda Suka Shigo garin Ɗanbatta gabanta ke Faɗuwa Zuciyarta bata Tsinke ba Sai da Suka Tsaya A ƙofar Gidan Duk da Ƙofar Gidan Hakimi ba'a Rabashi da Jama'a amma na Yau Daban ne, Sukansu su Basma Sunyi Wani Iri balle da Suka Firfito Daga mota Sunji Ana gaisawa da Tahir Ana mai gaisuwa, Umarni ya basu kan Su Shiga Cikin Gida, Shi kuma Idanuwansa na kan Mufeeda bayan ya Miƙawa Iya Naila. 


A cikin gidan ma Cike yake da Mata Tunda nan Aka kawo gawar Inna Fuleran Bayan ta cika Akayi mata Wanka da Suturu Tunda Suka Shiga gidan Mufeeda ke Jan Ƙafa, kamar Mara Lafiya, barinma yadda jama"a ke Binta da kallon Tausayi Basu Dai Tsaya ba sai da Suka Shiga Falon Goggo Abu Inda Suka Iske Goggo Abu zaune da Hijabi Da Carbi Ahannunta gefenta kuma Innaro ce sai Ashe da Maman Lantana Dake gafe Daga Tsakiyarsu kuma gawar Inna Fulera ce Lulluɓe Cikin Likkafani Tunda Suka Shigo Ɗakin Maman Lantana Ta ɗago Tana Kallon Mufeeda Idanuwanta na Zubar da Ƙwallah Tun daga Lokacin Jikin Mufeeda ya fara Rawa Saboda yadda gabanta ya fara Tsinkewa Lokaci Ɗaya.


Basma ganin gawa ne yasa Ta koma bayan iya Tana Rawar Jiki Ita ko Mufeeda Maman Lantana ta Nufa Tana Faɗin"Maman Lantana lafiya naga kina kuka..? Waye nan kwance ya Rasu..? Ina Innata naga banganta bane.." Ta ƙarashe Faɗa Cikin Fitan Hayyaci Hannunta Mama Lantana Ta Rik'e kafin Tajata har gaban gawan Inna Fulera ta saka Hannu ta yaye Farin likafanin Da'aka Lulluɓeta Dashi Dayake Tana Cikin Makara ne, Fuskar Inna Fulera Ta bayyana Kwance Bata Numfashi.


Daskarewa Mufeeda Tayi Tana bin gawar da kallo Cikin Rashin Hayyaci Kafin Ta Sulale ƙasa Ta Duƙe Gaban Gawar bakinta na Rawa Muryanta na Tsinkewa Take Faɗin "Inn... Innata..Ta..na barci ne ko..?" Ta faɗa Lokaci Ɗaya Ta Ɗago kai Suka Haɗa ido da Maman Lantana Hawaye Sun Fara Wanke mata Fuska Jikinta na Rawa ganin Tana Taɓa Inna Fulera ba motsi gashi Duk An Nannaɗeta Ciki Likafani Zuciyarta Ta Tabbatar mata da Sai Mutum ya Mutu Za'ayi mai Haka Kenan Innarta Ta Rasu..? Zuciyarta ce ta karye Ta Faɗa jikin Gawan Tana Faɗin "Innata ki Tashi...Nasan kina Jina..? Nice 'Yarki Mufeeda ki Tashi ki ganni nasan Wasa Kike man baki Mutu ba.." Ta Faɗa Tana Kuka Wurjajan Su Goggo Abu Saboda Tausayi Sai Sharan Ƙwallah Suke na Tausayin Mufeeda Maman Lantana ne ta ƙaraso kusa Da Ita ta Riƙota Tana Kuka Take Faɗin "Bar Kuka Saman gawa Mufeeda Fulera ta tafi..Sai dai muyi mata Fatan Dacewa Ta Cika Da Kalmar Sunanki Abakinta bayan Ta Jaddada albarka agareki.." Ƙyam Mufeeda Ta Tsaya Da Kukanta Tana kallon Maman Lantana Cikin Fitan Hayyaci Take Faɗin "Da gaske ne dama Inna ba barci Take ba..? Innata fa Ta Rasu kika ce..?" Na Shiga uku ni Mufeeda ina zan Saka kaina..?" Ta faɗa Tana Sakin Wani Marayan Kuka, kamar zata Shiɗe Lokaci Ɗaya Tana ƙara Sulalewa kan gawar Iya da Basma na waje Ɗaya Suna Sharan Ƙwallah Hatta Naila Datake yarinya Ganin Mufeeda na Kuka Itama sai Ta Fashe da Kuka ganin Yadda Mufeeda ke ƙanƙame gawar Inna Fulera ne Tana Kuka Tana Faɗin Inna Ki Tashi ya sanya Innaro Tashi Ta Riƙota da Ƙarfi Cike da Tausayi amma sai Mufeeda Ta Turje domin Wani ƙarfi ne yazo mata ta ƙwace kanta ta koma ta ƙara kwanciya kan gawar Inna Fulera Tana Kuka Daidai lokaci kuma Su Tahir Suka Shigo Dashi da Ishaq da Wasu mutane su Shida Sunzo Daukan Gawar, Tun Shigowar su Mufeeda Cikin gidan Tahir ke Cikin Zullumi yanzu ma yana Shigowa Idanuwanshi na kanta Gaba ɗaya Jikinshi na ƙara Sanyi Kusa da Ita Suka Isa kafin ya Sanya Hannu ya Dafa kafaɗarta yana Faɗin "Mufeeda..." Ya faɗa Cike da Rauni.


Jin Muryansa yasa ta Ɗago da Sauri Ganinshi yasa Kawai Tayo Rimi ta afka mai Har sai da ya zauna kan Cafet ɗin bayan yayi Saurin Riƙeta Cikin Kuka Take Faɗin "Kagani Wai Daga Innata na barci suna cewa ta mutu, Zata Tashi ko Daddy kace mata Ta tashi gani nazo.." Ta faɗa Tana Zubar Hawaye Zuru yayi mata da Ido kamar ya Fashe mata da Kuka Cikin Fitar magana yace "Kinga Kwantar Da Hankalinki, kinji ko..? Kin Taɓa ganin Wanda ya Mutu ya Dawo..?" Girgiza kai tayi kafin ya cigaba da Faɗin "Toh ki saka Aranki Inna ta tafi bazata Taɓa Dawowa ba...Yanzu Addu'arki kaɗai Take buƙata ba Kukanki ba.." Tsuru tamai da Ido Hawaye na Zuba mata Shar kafin tace "Bani da Kowa...Inna itace gata na...Ya zanyi na Shiga Uku.." Baki ya Rufe mata yana Faɗin "A'ah kina damu...Mune gatanki Mufeeda nayi ma Inna Alƙawarin zan zamo garkuwarki Har Ƙarshen Rayuwarki ki daina Kuka Tashi ki bari Aɗauki gawarta Amata Sallah zamu kaita gidanta na gaskiya.." Ya faɗa yana Ɗagota Tsaye kafin yama Su Ishaq alama da Ido kan Su Ɗaga gawan Gaba ɗaya Falon ko Mamakin yadda Tahir ya Iya Shawo kan Mufeeda Akeyi, wacce Tun Taga Da Gaske za"a Fita da Gawan Inna Fulera sai ta ƙara Tuburewa Tana Kuka Tana Ƙoƙarin Ƙwace kanta Tana Faɗin "Wayyo ku Dawo min da Innata Ku Dawo min da Ita.." Take Faɗa Tana kuka Tana miƙa Hannu Har Aka Fice da Ita Agaban Idanuwanta Luu kawai Tayi Ajikin Tahir alamun Ta Sume, Fuskarta yake Shafawa yana Kiran Sunanta, Innaro da Ashe Suka Taso da Sauri Suka Riƙota Suka Shiga da Ita Uwar Ɗakin Goggo Abu Mama lantana kuma Ta bisu da Ruwa Shi kuma Tahir Da Sauri ya Fice yana Ji kamar Shima ya share Ƙwallar, Da kallon Tausayi Goggo Abu Ta Bishi Itama Ƙwallar Take Sharewa Domin Har yanzu bata Ishi Baba Hakimi kallo ba.


Har Aka kai Inna Fulera gidanta na Gaskiya Mufeeda bata ƙara magana ba Bayan Ta Farfaɗo Tana dai Zaune Zuru Hawaye na Zubar mata Kowa yazo ita yake Tausayi ba Uwa ba Uwa Gashi ba wani ƙwaƙƙwaran Dangi, Mutane sai magana Suke Wasu na Faɗin Ai Taimakonta Ma gidan su Hakimi, Sune gatanta, gida ya cika da 'yan Zaman Makoki Hakama Ƙofar Gida Cike da Mutane Ciki Harda Su Tahir da Ishaq Harda Garzali Direba Wanda Tahir yace ya Koma gida yace ya barshi ya samu Jana'iza Mutane da Kuma alhinin Mutuwa ya saka ba Wanda Ya Lura ba Farida balle Har Ya Tambayeta Goggo Abu ne ke Damuwa Da Ita, Toh Itama Tana Ta kanta ne Ba wanda Ya Tuna Da Ita sai Washegari Da Umma Suka zo gaisuwa Ita da Abba,Tun Ajiya Ishaq ya koma Shida Garzali inda Tahir yace Ranar Uku ya Dawo ya Ɗaukesu.


Tahir ya Shiga Cikin Gida Da Rana gaida Umma Naila na Hannunsa bayan Tagama ma Tahir gaisuwa Shiko Rabin Hankalinsa naga Mufeeda Wadda Cikin Kwana Ɗaya Ta Fita Hayyacinta Kukan Zucci Take Wanda Sai dai Aga Hawaye na Zubo mata Ta fita Kamanninta Fuskarta Ta Kumbura Idanuwanta Sunyi Jawur Tana Kusa Da Goggo Zaune ta Tsurama Cafet Ɗinta ido Yana Nazarinta ne Umma Tace "Wai ni kam Ina Farida ne Tunda na Shigo ban Ganta bane ko Tana Shashen Innaro ne..?"


Gaba ɗaya wajen Aka Zuba ma Tahir Ido, dama Cikin Uwar Ɗakin Goggo Abu ne, Daga Umma sai Mufeeda sai Goggo Abu Innaro ma Tana Falo Ita Da Ashe da Sauran Jama'a Cikin Dakewa Da Rashin Damuwa Tahir yace "A'ah Umma bata zo ba.." Cikin mamaki Take Faɗin "Bangane bata zo ba? Tahir Mutuwa fa Akayi Shine ka ƙyaleta Taƙi Zuwa..?"


Murmushi yayi kafin Yace "Nifa Umma Tun Washegarin Tafiyarku Farida ta saka ƙafa Ta bar gidan Batare Dana san Inda Taje ba.." Salati Umma ta Saki Kafin Tace "Na shiga uku ni Aliya Farida Zata Kasheni Lokacina bai ƙare ba Haba Tahir Shine Duk Tsawon Wannan Lokacin Baka Taɓa Sanar damu ba..?" Kansa ya Sunkuyar batare Daya ce komai ba Mamakin Goggo Abu yake Yadda Ko ƙanzil batace ba Lalle Goggo Taga Rayuwa.


Cikin Ɓacin Rai Umma Ta Ciro Waya Ta Dokawa Farida Kira, lokacin da Kiran Umma ya Shigo Tana Zaune Afalon Na Billy Tana kallon Ikon Allah, domin Abban Su Walida ne yayi Tafiya yau zai Dawo Shine Billy Ta kasa Sukuni da Zama Tsakanin Kicthen da Falon ƙayataccen Girki Take mai Tana Rawan Jiki, Farida Abun na bata mamaki In Taga Abunda Billy ke Aikatawa kamar ba da ita Cikin masu Zugata kan ba'a Sakarma namiji Fuska Balle kai mai Rawan Jiki Itako Tunda Tazo Gidan Matuƙar Taga Billy Afalo Toh Abban Walida ya Fita ne In ko yana nan bata da Lokacin kowa bayan An Chaɓa Ado An Shiga Kichen Anyi Girki Ta Tuna Sanda Billy ke Bata Shawaran Ta Ɗauko mai aiki Kada ta zama baiwa mai abinci, Abun bai ƙara Ɗaure mata kai ba, sai da taga yadda Billy ke Rawan Jiki ko Muryan Abban Walida Taji, kenan Itace Suka Maida Sakarya da Suke Sanar Da Ita Tsakaninta da Namiji bawani Ragowa in Tanaso ta ƙwaci 'Yancinta..?


Tana Cikin Wannan Tunanin Wayarta Ta Shiga Tsuwa, ganin Sunan Umma sai da gabanta ya amsa Tana Ɗagawa Umma tace "Kinci Ubanki Farida.." Cikin Mamaki Farida Tace "Kai Umma me nayi kuma..?" Umma tace "Ubanki kikayi Nace Ubanki kikayi..Ashe Farida Baki da Mutumci bansani ba? Kina gidan Uban waye Bayan kinbar gidan Mijinki...?" Tura Baki Farida Tayi kafin Tace "Umma ina gidan Billy...."

"Billyn ubanki Sakarya mara Tunani Wato ita Tana Gidan Aurenta Ke kuma Ta barki ki Zauna Tunda baki da mafaɗi, Toh maza ki Haɗo Yanaki yanaki Kizo Ɗanbatta yau ɗin nan muna Jiranki Nida Abbanki munzo Gaisuwar Rasuwar Mahafiyar Mufeeda.." Daga Haka Umma Ta Katse Kiran.


Sororo Farida Tayi Ranta na ƙuna da Sunan Mufeedan Da'a Aka Ambata Amma Haka Ta tashi ko kallon Ɓarayin da Billy Take bata yi ba Wacce ke Jera Kuloli bisa Dinning Ɗakin Da'a Aka Sauketa ta Shiga Tana Hawaye Ta Haɗa kayanta Tsab Ta Ɗauko Mayafinta da Akwatinta ta Fito, A falo Suka ci karo da Billy Cikin mamaki tace "Ah Farida Ina Zuwa naganki da Akwati Haka..?"


Kai Tsaye Farida tace "Ɗanbatta zani..." Sheƙeƙe Billy ke Binta da kallo kafin tace "Wai koma ma Tahir ɗin zakiyi Don Rashin Zuciya..?" Cike da Haushinta Farida Tace "Eh zan koma ma Mijina Tunda na lura masu bani Shawaran yadda zan Tafi da gida Su basu amfani da Shawaran ko Kaɗan.." Sororo Billy Tayi Domin Tagane magana Farida ta yaɓa Mata, Ɗaure Fuska Tayi kafin tace "Au Haka zaki ce...? Ke kika sani Ai 'yanci Ake Neman ƙwatar miki Mutumin daya Tozartaki yama 'Yar aikinki ciki ai magana ta ƙare.."


Farida Takama Hanyar Fita Take bama Billy Amsa Cikin Dakewa tace "Eh 'Yanci Abarni na ƙwatarma kaina kamar yadda Kuma naga kuna Ƙwatarma kanku, kuma maganar yama 'Yar Aikina ciki Gwarashi nashi ya bayyana Mijin Wata Fa.? Uban wa yasan Wani Ta'asan yake Aikatawa Adai yi Sha'ani.." Baki Billy Ta kama kafin tace "Kambu...! Amma kafin ta Sake Wata Magana Farida Ta Fice da Kallon Mamaki Ta Bita Kafin Ta taɓe baki tace A fili.. "banza.Allah sa Kin Fara Wayau kenan.."


Itako Farida Motar Ta ta Ta Shiga Taba ta Wuta sai da Ta Fahimci Lafiyarta kana Ta saki Hon Megadi ya Buɗe mata Ƙofa ta Fice da Gudu Cikin Lokaci kaɗan Ta Ɗauki Hanyar Ɗanbatta Zuciyarta Cike da Fargaban Wani Irin Hukunci Zata karɓa Wajen Umma da Abba.




*Aisha Alto*

*Shakira*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️


*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕


_Don't Forget to Follow us on Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_


       *BABI NA GOMA SHA TARA*


Ƙarfe 2:40pm. Ta isa Ɗanbatta, Tahir da Hakimi da sauran mutane suna zaune a ƙofar gidan suna karɓar gaisuwa gurin jama'a masu zuwa musu ta'aziyya, haka ta ratsa tana sunne kai ta shige cikin gidan, tana shiga direct ɗakin Goggo Abu ta dosa.


Tana shiga da Umma suka fara haɗa ido, rass taji gabanta ya faɗi tana turo baki ta ƙarasa ciki ta zauna a kusa da Goggo Abu ta duƙar da kai taƙi kallon kowa dake ɗakin, Mufeeda kuwa tana ganin Farida ta shigo tayi maza ta miƙe ta fita falon Goggo ta zauna, don bata son abinda zai haɗasu da Farida guri ɗaya, gani take zata iya rufeta da duka don haka take jin tsoronta.


Miƙewa Goggo Abu tayi itama ta fito falo gurin Mufeeda ta zauna akabar Umma da Farida kaɗai a cikin uwar ɗakin, ɗagowa Farida tayi tana kallon Umma tace "Umm..." Da sauri Umma ta dakatar da ita tana watsa mata harara take faɗin "Uban me ya kai ki gidan Bilkisu Farida...? Wato dai ke har yanzu bazaki natsu kiyi hankali da duniya kisan me take ciki ba ko Farida.? Yanzu da kika je gidan Bilkisun uban me kikaje tayi miki? Me ma yasa kika saka ƙafa wai kika bar gidan mijinki da 'ya'yanki bayan duk irin faɗan da nayi miki ranar kafin mu tafi? Wato baki ji ba shine kika shure kika tafi gidan ƙawa har na tsawon kwanaki huɗu kina can a zaune saboda gaki ballagaza ko...? To uban me kika je yi gidan aurenta tayi miki..? Tana zaune da mijinta lafiya ke da baki san mutunci da darajar naki mijin ba shine kika kwashi jiki kika tafi gidanta tayi miki maganin taki matsalar ko?" Ta faɗa a hasale tana ji aranta kamar ta tashi ta rufeta da uban duka saboda takaicinta, ita ko Farida wani bala'in haushin Bilkisu ta ƙara ji a zuciyarta, take wasu hawaye suka fara zubowa daga cikin idanunta Umma na kallonta tace "Ai kuka kam yanzu kika farashi Farida..tunda dai kince ke ba mai hankali da tunani bace balle kisan ya kamata, na ɗauka zaki yi nadama ne saboda abinda sakacinki da toshewar tunaninki ya janyo muku ke da mijinki, ashe ba haka bane, ke inda tunaninki yake daban, abinda kika ɗaukarwa zuciyarki tun farko shi zaki ci gaba da yi. To kiyi Farida, bance ki  fasa ba kici gaba..." Haka Umma tai tawa Farida faɗa, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, Farida kuwa in banda kuka ba abinda take yi har da shassheƙa, sai yanzu ne ita da kanta take ganin aibun abunda tayi a rayuwarta, bata kyautawa kanta da 'ya'yanta ba, uwa uba kuma mijinta, bata tashi sanin babban kuskuren data tafkawa rayuwarta ba, sai data je gidan Bilkisu taga yanda take yiwa mijinta take kaffa kaffa dashi, bata haɗa komai da mijinta ba. Ita yanzu wace riba zata ce taci na irin halayen dasu Bilkisu suka dinga zigata suna ɗorata akai kuma tana bi...? 


Umma ce ta katse mata tunanin da take da faɗin "Yanzu a irin waɗannan abubuwan da kike yi wace riba kika samu? Me kuma zaki ɗorar? Miji ya gaji da halinki, har ya daina damuwa da duk wasu lamura da suka shafeki, kin kaisa bango halayenki sun gama isarsa, kin tafi kin bar gidan mijinki da 'ya'yanki kin tafi gidan ƙawa kin zauna har tsawon kwanaki, kin gama fallasa kanki da zuri'arki a gaban ƙawayenki, sirrin gidanki da komu bai kamata mujishi ba kin gama tallatashi a titi ga wasu can kinyi terere da mijinki, don nasan sai kin gaya musu duk abinda yake faruwa, tunda tunaninki ya gama toshewa..." Ta faɗa tana murmushin takaici, wani kukan baƙin ciki Farida ta fashe dashi tana girgiza kanta, kafin ta ɗago hawaye na tsirarowa daga cikin idanunta tace "Umma don girman Allah..." Sake dakatar da ita Umma tayi da faɗin "Komai kika yi fa kanki kika yiwa, nidai zanci gaba da tayaki addu'a Allah ya shiryeki yasa ki gane gaskiya. Don haka maza ki tashi kije ki yiwa Mufeeda gaisuwa..." Ta faɗa tare da miƙewa, itama Faridan tashi tayi tana share hawayen fuskarta tabi bayan Umma suka fito falo, inda Goggo Abu da Mufeeda suke sai Nailah da Iya da Maman Lantana, Umma zama tayi a kusa da Mufeeda tana kallon Farida da tayi tsaye tana kallon Mufeeda a sace tana turo baki alamar bazata iya ba an takura mata, wani kallo Umma ta watsa mata ba shiri ta dubi Mufeedan data sunkuyar da kai ƙasa tana wasa da bakin hijabinta, sai data zabga mata uwar harara kafin ta ɗauke kai tana faɗin "Ya ƙarin haƙuri...Allah ya jiƙanta ya gafarta mata.." Ta faɗa a tare tana zama a kujerar dake falon. 


A hankali Mufeeda ta ɗago ba tare da data kalli inda take ba tace "Alhamdulillahi...Momy mun gode Allah, Ameen na gode.." Ta faɗa ƙwalla na taruwa a cikin idanunta, janyota Goggo Abu tayi jikinta tana share mata hawaye, taɓe baki Farida tayi tana kallonsu kafin ta ɗauke kai tana sakin siririn tsaki.


Ranar a nan Umma ta kwana yayinda Abba kuma suka juya shida direba suka koma wanda sai ranar addu'an uku sannan zai dawo bayan anyi addu'an uku da safe sai su koma tare da Umma.


************


Yau akayi addu'an ukun Inna Fulera, bayan mutane duk sun watse yayi saura sai yasu yasu a gidan, suka taru dukkansu da Baba Hakimi da Goggo Abu da Innaro da Tahir da Ashe dasu Basma da Bassam sai Farida da Mufeeda da Umma da Abba.Sai Ishaq da Zahra da Suka zo Suma, Sai da suka haɗu gaba ɗayansu kafin Baba Hakimi yasa Tahir yayi addu'a aka shafa, sannan ya fuskanci Mufeeda wacce ke zaune a ƙasa ta duƙar da kanta ƙwalla na zubo mata, nan ya shiga yi mata nasiha sosai da nuna mata ta dinga yiwa mahaifiyarta addu'a ta daina mata kuka, kanta ta gyaɗa masa kafin ta ɗago tana share ƙwallar tausayin kanta. 


Umma ce ta gyara zamanta tana kallon Abba take faɗin "Gata nan Alhaji ka tambayeta inda ta tafi tabar gidan mijinta da 'ya'yanta tsawon kwanaki bata gidan aurenta...ba tare da tazo gida ba, ba kuma tazo nan Ɗanbatta ba..." Ta faɗa tare da nuna masa Farida da tayi tsuru tsuru tana raba idanu, wani kallo Abba yayi mata yana faɗin "Au wato bayan mun tafi shine tabar gidan tayi wani guri, saboda bata ji maganar da mukayi mata ba..?" Gyaɗa kai Umma tayi tace "Ai kuwa babu abinda ta ɗauka a faɗan da akayi mata.." Ta faɗa tana kallon Farida.


Gizgiza kai Baba Hakimi yayi yana faɗin "A'a bafa kusan dalilinta na barin gidan ba, ƙila dai akwai abinda shi Attahirun yayi mata ne..." Da sauri Abba ya katseshi da faɗin "A'a Mansur, karka ce haka, ai yana gaba da ita, kuma ko ba haka ba ai mijinta ne shi, kuma kome zaice mata ai bai kamata ace tayi fushi tabar gidan ta tafi wani guri daban inda ba'a sani ba..." 


Baba Hakimi na kallon Abba yace "Ka bari muji abinda ya faru a bakinta tukunna..ke Farida faɗa mana abinda Attahiru yayi miki da yasa kika bar gida..?" Ya faɗa yana kallonta, ƙara sunkuyar da kai tayi ta shiga rattabo abinda ya faru ranar bayan tafiyarsu tana haɗawa har da sharri tana ƙullawa, tunda ta fara maganar kawai Tahir ya girgiza kai yana sakin murmushi bai ce komai ba, har ta dasa aya... 


A harzuƙe Abba yace "Wato a ranar da muka gama magana akai miki faɗa a ranar kika sake shuka wata tsiyar ko Farida..? To ki sani wallahi tallahi babu inda Mufeeda zataje tana nan zaune daram a gidan anan zata zauna ta haihu, sai dai ke kibar gidan don ubanki kije duk gidan ubanda zaki amma banda gidana, kuma wallahi duk ranar da kika sake fita kika je wani waje bada yawun mijinki ba ko kika fita saboda nuna kinfi ƙarfinsa Allah ya isa bamu yafe miki ba, tunda ke bazaki taɓa yin hankali ba..." Ya faɗa a zafafe yana sauke numfashi, sake rushewa da kuka Farida tayi har tana jan numfashi kamar zata shiɗe saboda baƙin ciki, nan Umma ma ta ƙara dasawa sukayi mata tass, abin mamaki Goggo Abu na zaune tayi laƙwas sai bin kowa da kallo kawai take ta kasa magana.


Baba Hakimi ma yayi mata faɗa sosai sannan ya haɗa har da Tahir shima yayi musu faɗa kafin ya ɗora da faɗin "Kiyi haƙuri Farida ki rungumi Mufeeda ki tausayawa rayuwarta, ki zauna da ita lafiya kinga marainiyace, ki ƙara riƙeta kamar yanda kika fara riƙeta ada..idan cikinta ya isa haihuwa watan ya tsaya Innaro zata zo can gidan naku ta zauna don ta riƙa kula da ita har ta haihu.." Ya faɗa yana ƙara lallashin Farida kan ta zauna lafiya da mijinta ta kula da 'ya'yanta.

Daga ƙarshe dai Baba Hakimi ya saka musu albarka tare da yi musu fatan alkhairi da gamawa lafiya dukkansu.


Nan Tahir ya matso gaban Abba ya duƙar da kai bai ce komai ba, lura da hakan da Abba yayi yasa yace "Me yake faruwa ne Tahir.? Ko akwai wata matsala ne kuma...?" Jinjina kai Tahir yayi alamar Eh.. Abba na gyara zama yace "Ka faɗa min ko mene ne Tahir insha Allahu indai inada dama Allah ya bani iko zanyi maka maganinsa..." Cikin jin daɗi Tahir ya ɗago yana faɗin "Dama Abba inaso ne ka roƙi Baba ya yafewa Goggo Abu.." Ya faɗa yana jin ƙwalla na taruwa a cikin idanunsa, saurin ɗagowa Abba yayi yana kallon Baba Hakimi, kafin yayi magana Baba Hakimi ya rigasa yana murmushi yace "Na riga na yafe mata duniya da lahira, Allah kuma ya yafe mana baki ɗaya ya kiyaye gaba.." Da Ameen duk suka amsa, kafin Tahir ya fara miƙewa Shida Ishaq  suka  fita daga ɗakin suka nufi ƙofar gida gurin Sauran Jama"an Dake Wajen Wadanda Suka zo Addu"arku Uku ba Dadewa sai ga Su Abba Suma Sun Fito Suna Tattaunawa shida Baba Hakimi.


A ranar Umma da Abba suka koma Kano, da yamma suma su Tahir da Farida da Iya da Mufeeda da yara duk suka tattara suka yi shirin komawa Kaduna, mota biyu sukayi Tahir da Farida da Mufeeda suka shiga motar Ishaq, su kuma Basma da Bassam suka shiga motar Tahir da Garzali ya tuƙo suka ɗauki hanya, bayan sun bar motar Farida a nan gidan Baba Hakimi akan washegari Garzali zai dawo ya ɗauka.


******


A hankali abubuwa suka fara daidaita, sai dai Farida tana tsananin kishin Mufeeda, amma tana ƙoƙarin dannewa bata son a gane, don irin tsantsar kulawar da Tahir ke nuna mata kwata kwata bata so, amma tana yi tana dannewa, bata so a gane tana jin haushi.


Haka a ɓangaren Tahir shima kwata kwata baya ganin hasken Farida, don ta gama sire masa gaba ɗaya a ransa, daurewa kawai yake yana nuna kulawarsa a kanta, kuma yana ƙoƙarin sauke hakkinta dake rataye a wuyansa, amma duk ɓoyewarsa sai data gane, don a komai ya ƙara canza mata sosai, kusan rabin kulawarsa gabaki ɗaya yanzu duk ya ɗorata akan Mufeeda ne.


A lokacin ne kuma su Mufeeda suka shiga Jss2 suna ci gaba da karatunsu, bata da matsalar komai ta ƙara wani kyau da haske, sai dai kusan kullum kafin tayi barci sai ta tuna da Innarta, idan tai kuka sai ta share hawayenta kuma tayi mata addu'a.


Haka rayuwa taci gaba da tafiya wani lokaci aji daɗi wani lokacin kuma aji akasin haka,Farida Bata Kaunar Ta Bude Ido Taga Mufeeda da Ciki Acikin gidannan Tsoronta Daya ne Abba da Umma Tasan yanzu Abu kadan Zatayi Suyi Fushi da Ita Sosai,Abunda kuma ke karamata Kishin Mufeeda Shine ganin yadda Tahir ya Watsar da al"amarinta bai Cika damuwa da Al"amarinta ba,gasu Bassam Sun ki marata baya Sun bi Bayan Mahaifinsu,Haka Suke Kafa kafa da Mudeeda kamar su lasheta komai take bukata tana samu Koda yaushe Cikin Tallalinta Sukeyi.


Tuni Farida ta Watsar Da Shawaran Kawayen banza,Tunda Agroup Dinsu Billy Taje Tana bada Lbrin Zata kwatar mata yanci Ta gayamata mgana Ranta ya baci,ta Shiga group din Ta maida mata martani Tamata Wankan Tsaki Billy Tasan bata da gaskiya Sai ta kama kame kame,anan Akayita bata Hakuri Daga karshe Fitama Farida Tayi Daga Group Wasu Dadama Sun Bita Suna bata Hakuri Suna Fadamata Kowa Data gani Anan yana lallaba Aurensa ne,ba wani mai Sakaci,sai Lokacin Farida Tagane tayi Wauta babba..Wato Duk Acikinsu itace Sakarya Tayi Kuka Sosai kamar Ranta zai Fita Tayi Nadama sanda bashi da amfani,Tadaina Fita kwata kwata Wanda Ta gyara Domin Shi ko kallo bata Isheshi Ba Domin yafi Nuna kalawarsa Akan Mufeeda Fiye Da Ita,Abunda yasa Farida Rama kenan Atsaye Duk tayi Wani Zuruzuru Da Ita.


***********


   *BAYAN WATA SHIDA*


Cikin Mufeeda ya ƙara fitowa sosai yayi girma gwanin ban tausayi, Tun yana Wata Hufu Tafara Zuwa Awo Anan Iyali Hospital,kuma shi yake kaita watarana In yana da Lokaci Ranar dai bai samu Zuwa ba sai Garzali ya kaita ita da Innaro,tsufan cikin nata ne, yasa Tahir ya hanata zuwa islamiya yace ta riƙa zama a gida makarantar boko zata rinƙa zuwa kaɗai, duk ranar da ba makaranta tana zaune a gida, hakan yana ƙona ran Farida sosai ya baƙanta mata zuciya, don ta tsani ganin cikin bata ƙaunar tayi tozali dashi kwata kwata a rayuwarta, jira take kawai Mufeedan ta haihu Tahir ɗin yasan nayi da ita.


Baba Hakimi ya cika alƙawari Tahir na sanar Dashi Cikin Mufeeda ya Cika Wata Tara yace ya Aiko Garzali ya Ɗauketa, nan da nan kuwa ya aikashi sai ga Innaro Ta Iso Abunda ya ƙara baƙantama Farida rai ganin Ɗakin Mufeeda Tahir yace A sauketa Suna Murna kamar ba Ɗan Shege za'a Haifa ba, Haka Tazo da Jiƙe jiƙe Saboda Maganin sanyi, Take Ta bama Mufeedan Ita da Iya ba'a san Wanda yafi Wani kula da Mufeedan ba, Goggo Abu kuwa Batama ta Farida yanzu Domin Da ƙyar ta samu bayan Abba ya saka Baki Hakimi ke Kulata Ko a hakan ba kamar baya ba, Shiyasa Take ƙoƙarin gyara Kuskuranta ta kuma Ƙudirci Wani Abu A ranta Jira kawai Take Allah ya Sauke Mufeedan lafiya Ta Aiwartar da Ƙudirinta Domin yanzu Tausayin Mufeedan Take Kullum Cikin Kira Take awayar Innaro Ana bama Mufeeda Tana Tambayanta Me take ji..? Wani Lokacin Dariya kawai Mufeeda keyi bata cewa komai Domin Yawanci Tambayan Tahir kenan Inya Shigo Dubata da Safe da Kuma bayan Ya Dawo ko Shi bata bashi Amsa sai dai ta Sunkuyar Da kai Aranta Tana Jin Daɗin yadda Daddy ya fara maida Jikinshi ba kamar Farkon Al'amarin ba.




*Anitha...*

*Aisha Alto...*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


       *BABI NA ASHIRIN*


""Ɓangaren Kayan Haihuwa Kuwa Babu Abunda Tahir bai gama Siya ba Kuɗi masu yawa ya Ware ya bama Matar Ishaq Zahra ta sayo komai da komai Kayan jariri kuwa komai Biyu ta Siyo na Mace Dana Namiji Tace Saboda Tahir bai yarda an mata Scanning ba, balle aga mai Zata Haifa.


Kuma Zahran Da kanta ta kawo Kayan Gidan, Abunda Ya ƙarama Farida Ciwo yanzu Har Takai matsayin da Bata da Wani amfani Wajen Tahir, ya maida kanshi dashi da 'yan'uwansa da Iyayensa Wajen Tattalin Mufeeda, Sai dai Tayi Wuni Cikin Ɗakinta Taita kuka bamai lallashinta Ita baga kulawan Miji ba Haka Zalika ma Su Bassam banda Gaisuwa babu Abunda Ke Haɗasu Koda yaushe Suna Ɗakin Mufeeda suda Iya da Innaro Wani Lokacin Tana Falo sai dai Tajiyo hirarsu Da Dariyansu Mufeeda kuwa Ko ta ganta ta gaisheta Farida bata amsawa Sai dai Ta bi Cikin Jikinta da kallo Cike Da Kishi ganin yadda yayi Girma yana Neman Rinjiyan Mufeedan, Burinta da Fatanta Allah Ya Sauke Mufeedan Lafiya ta ƙara gaba Allah barshi abunda Zata Haifa In Ta gama Shayarwa akaisa gidan Marayu Domin ba Wanda Zai Gurɓata mata 'ya'ya dana Shege 


******


Yau ɗin takama Jumma'atu Babban Rana ce, Misalin ƙarfe 9 na Safe Duka suna Zaune A falo Suna Hira Innaro, Iya da Basma sai Bassam Dake wasa da Naila Wacce Take Tafiyanta yanzu Sai Mufeeda dake Zaune kasan Cafet Ta Buɗe ƙafa Hannayenta na Baya ta Dafa ƙasa Ga Cikinta nan Wani Randa guda yayi girma sosai har yayi ƙasa, Ta kumbura Ko'ina na Jikinta ya Buɗe ya ƙara Girma, In ka kalleta Farat Ɗaya kamar ba Mufeeda ba Domin Ta Cika Ciki ya sakata tazama ƙatuwa, su Basma suna Hutun Ƙarshen Shekara in suka koma zasu Shiga jss3 hadda kawai Suke Zuwa yanzu da Islamiya.


Aya ce agabanta Tana ci Tana Dariyan Labarin da Iya ke basu na Matar ƙaninta da Ta faɗa masai, Basma Saboda Dariya Harda Riƙe Ciki, Mufeeda ma Dariyan Take lokaci Ɗaya tana Cin Ayanta, Farida Data Sauko Daga Sama ta bisu da kallon Takaichi Da ƙyar ta iya Buɗe baki Ta gaida Innaro, Iya ta gaidata Hakama Su Basma Duk ta amsa amma Mufeeda na Gaisheta tayi kamar bata jiba ta Shige Kichen Abunta Mufeeda bata damu ba Domin Inda Sabo ta Saba da Hallayar Farida.


Ruwa ta Ɗauko Kafin Ta sake Haurawa Sama Ƙofar Bedroom D'in Tahir Tabi da kallo, Tun Jiya Daya Dawo Daga Lagos bai sake Fitowa ba, Buɗe Ƙofar tayi Ta Shiga ta Iskeshi kwance Cikin Bargo yana barci Ƙyalesa Tayi Ta Fito Daga Ɗakin Tana Tunanin gajiyace Domin Wajen Satinsu Daya achan Shida Ishaq ne Suka Tafi Taran Sabbin Motocinsu da Zasu zo ta Jirgin Ƙasa, Toh basu iso ba Sai Shekaran jiya Da Daddare Su kuma jiya suka taho Zuwa Kaduna.


Ɗakinta ta koma ta Sha Ruwa kana Ta Koma ta kwanta Tana Tunanin Da Zarar Mufeeda Ta Haihu Ta bar mata gida Zata gyara Duka mu'amalanta da Mijinta Harda 'ya'yanta Batasan Cewa Lokaci Tuni ya Ƙure mata ba.


Mufeeda Dake Dariya Ƙasa ƙasa, Taji kamar bayanta ya amsa Da Sauri ta gimtse Dariyan Tana jin Lokaci Ɗaya maranta ya Ƙulle, Cije baki tayi ganin ba Wanda ya lura da Halin Data ke ciki Ta Dafa Kujeran Ta Miƙe A hankali Tana Cije baki Lokaci Ɗaya Innaro da Iya Suka kalleta kafin Innaro taceb"Mufeeda lafiya..? Ina zaki Haka..?"


Saurin Sakin Murmushi Tayi kafin tace "Bakomai Innaro Toilet zan Shiga.." Innaro tace "Ayyah..Jeki Dawo.." Ta faɗa Tana kallonta da Sauri Mufeeda ta Fara Taku Zuwa Ɗakinta Tana Daurewa amma Fa Cijewa kawai take saboda yadda Ƙugunta ya Riƙe ga Maranta ta Ƙulle Waje Ɗaya,bHar ta Shige Ɗakinta Innaro na Binta da kallo kamar tana so Ta Ɗago Wani Abu...


Mufeeda Da ƙyar Ta iya kai kanta Tsakiyar Ɗakinta kafin ta Durƙushe Tana Riƙe gadon Hannu Biyu Jin Ƙugunta kamar zai Tsage gida Biyu, Zufa ce ke Keto mata kamar Wacce Ake Gasawa Salati Mufeeda ke Saki Cikin Ranta Lokaci Ɗaya Hawaye na Wanke mata Fuska ko Bata sani ba Wannan Azaban Data keji Ta Gane Naƙuda ce, Tun Abun na Ƙasa ƙasa Har ya gagari Tunanin Mufeeda Kuka Take Wurjajan da Majina Domin Tagama Yanke Kauna wallahi  Mutuwa Zatayi domin Wannan Azaba Ta mutuwa ce.


Innaro ce Taga Shirun na Mufeeda Yayi yasa Ta kalli Basma Tana Faɗin "Ke Basma Maza Tashi ki Dubo min Mufeeda najita Shiru ne.." Da Hanzari Basma Ta Miƙe Ta Nufi Ɗakin Mufeeda Halin Data Tarar da ita ya bata Tsoro Cikin Firgici Tace "Innaro kuzo kuga Mufeeda.." Ta fada da Ƙarfi Jin Haka yasa Innaro da Iya Suka fara Rige Rigen Shiga Ɗakin Mufeeda Hankalinsu a Tashe, Bassam Dai Naila ya Ɗauka Wacce Ta Fashe da Kuka lokaci Ɗaya bai bisu Ɗakin ba ya dai Tsaya A falon yana Tunanin ko lafiya...


Kallo Ɗaya Innaro Tama Mufeeda Ta Fahimci Tana kan Gwiwa Basma Ta kallah Wacce Har Ta fara Hawayen Tausayin Mufeeda tace "Maza kije ki kira min Daddynki.." Da gudu Basma Ta Fita ta Haura sama Tahir na kwance Cikin Barci Yaji Basma na Faɗin "Daddy Daddy...Ka Tashi Innaro na Kira Mufeeda Zata Haihu Tana ta kuka.." Take Faɗa Tana Kuka Itama.


Zumbur ya Miƙe Daga Kwancen Yana Kallon Basma Ido ya Zaro yana Faɗin "Zata Haihu kika ce Basma..?" Kai ta gyaɗa mai tana Share Ƙwallah da Hanzari ya Dirko Daga kan gadon Da gashi sai Dogon Wando Jallabiyansa ya Laluba ya saka ya zari Key ɗin Mota ya Fita Da Sauri Basma Tabi Bayanshi Fitowarsu Da Hanzari ya Fito Da Farida Daga Ɗaki Ganin Tahir da gudu ya Sauka Ƙasa yasa Itama Tabi Bayansu da Sauri Tana mamakin Me ya Razana Tahir Lokaci Ɗaya Haka..?


Tahir ko na Shiga Ɗakin Mufeeda Yaga ba yarda Take Innaro na mai magana bai Saurareta ba kawai ya Cicciɓi Mufeeda Zuwa Waje yana Faɗin "Innaro ki Ɗauki Mayafi mutafi Asibiti.." Farida Dake Ƙoƙarin Shiga Ɗakin Mufeeda Tayi Baya ganin Tahir ya Ɗauko Mufeeda Tana Faman kuka tana Yarfa Hannu, suman Tsaye Tayi Cike Da Takaichi da Kishi Wai Tahir ne ya Ɗauki Mufeeda da Hannunsa Niko Nace Yamata Cikin ma balle Ɗauka.


Bata gama Mamaki ba Iya da Innaro Da Suka Rufa mai baya Da Gudu Mayafai A hannu Saboda Zullumi sai ga Basma Ita ma da Hijabi Ta Runtuma tabi Bayansu, baki ta Riƙe Cike da Baƙin ciki Lokaci Ɗaya kuma Falon ya ƙara Ɗaukan Kukan Naila, Daga Nailan Har Bassam D'in Da Harara Ta Bisu kafin Ta Saki Tsaki ta koma Sama Tana Ƙunƙuni Ita kaɗai.


Tahir ko Garzali bai Saurara ba ya Kai Mufeeda Bayan Mota, Ya Dawo Gidan Gaba Mazaunin Direba ko Su Innaro Dake Fitowa Haraban Gidan bai Jira ba ya Kunna Mota yayi Reverse da Ƙarfi lokaci Ɗaya ya saki Hon ya Fice Da Gudu, Su Innaro basu Tsaya ba Suka Faɗa Mota Basma Ta Shiga Gaba Innaro Tace "Garzali bi mana bayan Attahiru..." Cikin Bin Umarni Garzali yaja mota Yabi Bayan Tahir Daya Nufi Asibitin Iyali Hospital Dake Kusa Dasu.


****

Koda Tahir ya gama Faka Motarsa Cikin Haraban Asibitin Bai Jira Wani ba, Ya Fito Daga Mota ya Buɗe Baya ya Cicciɓo Mufeeda Dake kuka Wurjajan Lokaci Ɗaya Da Salati Domin Ji Take kamar Zata mutu da Gudu ya Nufi Cikin Asibitin Da Ita ganinshi Haka ne ya saka Nurses Da Gudu suka gungoro Gadon Ɗaukan Marasa Lafiya Zuwa Gareshi ganin kamar ya Fita Daga Hayyacinsa yana Kiran Likita.


Kan Gadon ya Ɗora ta da Hanzari Suka Shiga Turata yana Bin Bayansu cikin Tashin Hankali Labour Room Suka Shiga da Ita Suka Rufo ƙofa Dole Tahir ya Tsaya Awaje yana Safa da Marwa sai ga Su Innaro Sun Shigo Asibitin Hankalinsu Tashe Cikin Fargici Innaro Tace "Attahiru Ya Ake Ciki...?" Numfashi ya Sauke yana Faɗin "Bansani ba Innaro Sun Dai Shiga da Ita Ciki..." Gefe Suka Koma kowa na Addu'a Cikin Ransa Basma ko Hawaye Take Sharewa Suna nan Tsaye Wata Nurse Ta fito da Gudu Ta Wuce Office d'in Likita, Sai gashi Sun Fito A tare Cikin Hanzari Sun Koma Cikin Ɗakin Daga Wajen Suna Jin Salatin Mufeeda Da Kukanta Lokaci Ɗaya Tahir yaji Jikinsa ya Saki Ƙwalla Ta Cika mai ido yana Fatan Allah ya Sauki Yarinyar nan lafiya kada ta Mutu Da Cikin nan ya Shiga Uku.


Tsawon Awa Ɗaya Likitoci na Shige da Fice kan Mufeeda Haihuwa Shiru nan da nan Suka mata Scanning Nan Suka gano yan Biyu ne A cikinta amma Sun Galabaita, yunƙurin Fitowarsu da kansu Matsala ne, Nan da nan Wani Likita ya Fito Yana Faɗin "Ina Mijinta...?" Da Hanzari Tahir ya Isa Gabanshi yana Faɗin "Gani Dr..Hop ta Sauka lafiya.." Kai ya girgiza mai kafin yace "Biyoni Office da Sauri bamu da Lokaci.." Jin Haka yasa ya bishi da Hanzari, Zuwa Cikin Office Ɗinshi Suna Shiga Ciki ko zama baiyi ba ya Miƙa mai Wata Takarda yana Faɗin "Muna Buƙatar saka Hannunka anan, zamu Shiga da Ita Aiki ne yanzu Domin Ceto Rayuwarta data yaran Dake Cikinta.." Tahir na Zufa ya karɓa Takardan Haɗe da Biron ya Rattaba Hannu, kafin Likitan ya karɓa yana miƙa mai Wata ƙaramar Takarda yana Faɗin "Ka biya Kuɗin Aiki yanzu..." Tahir bai Tsaya ba ya Fito da Sauri su Innaro Dake Zaune Suka miƙe Suna kallonshi Kanshi ya Shafa yana Faɗin "Sun ce aiki zasu mata yanzu...Ku zauna anan Bari naje na Biya Kuɗin Aikin Na Dawo.." Innaro tace "Toh kana da Kuɗi A hannunka..?"


Yana Tafiya yake Faɗin "A'a Sai dai Atm ɗina zanyi Amfani Dashi.." Ya faɗa yana Ƙara Sauri Cikin Minti goma Sai gashi ya Dawo da Resit ya Riga ya Biya Kuɗin Aikin bai Daɗe da Isowa Wajen ba Sai ga Mufeeda An Gungurota Zuwa Ɗakin Tiyata an Chanza mata kaya, Kuka Take da Salati Lokaci Ɗaya Suna kallo Aka Shiga Da Ita Gefe Suka koma Kowa Da kalan Addu'an Dake Ranshi barin ma Tahir da Abun Duniya Suka Taru Suka mai yawa...


Shuɗewar Awa Biyu Kafin wasu Nurses Guda Biyu Su Fito Daga Ɗakin Tiyatan Ɗauke da Yara Guda Biyu Cikin Wasu Showels, da Hanzari Suka miƙe Suna kallonsu Cikin Fara'a Ɗaya Tace "Congratulation ta Sauka An Samu Twins, mace da Namiji..." Gaba ɗayansu Suka Haɗa baki Wajen Faɗin "Alhamdulillah." Innaro Ta karɓi Namijin Iya kuma Ta karɓi Macen Dukkansu bakinsu yaƙi Rufuwa Shiko Tahir Hamdala yake Acikin Ranshi kafin yace "Ina ita Maman Yaran..?" hope tana lafiya.." Ɗayar tace "Eh ana gyarata ne da Zarar an kammalah zamu maidata Ɗakin Hutu.." Daga Haka Suka Wuce, Chan sai ga Likitocin Suma Sun Fito Suna Cire Safan Hannu, Musabaha sukayi da Tahir Suna mai Murna, Bakin kowa yaƙi Rufuwa, Bai Ɗauki yaran ba Domin Wani Tausayinsu ne ya Tsirga mai na Ya samar Dasu Ta Hanyar da bai dace ba, Ashe Dalilin Daya sa ya Afkama Mufeeda Kenan Rabon samun Waɗannan ne ya Kawo Haka.


Ba ɓata Lokaci aka Gunguro Mufeeda Zuwa Ɗaki na Mussaman Domin Hutu, Suka ce Kar wanda ya Shiga Inda Take Sai ta Farfaɗo bayan Awa biyu da wani Abu, Yanzu aje azo da kayan Jarirai da Kayan Tea d'in da Mai Jego zata Buƙata in ta Farfaɗo, Tahir ne ya barsu anan ya Koma gida, Farida na Jin Dirin Mota ta Zabura ta Fito Falo Suka Ci karo da Tahir Cikin Rawan Baki Tace "Ta Haihu..?"


Bai kalleta ba yace "Eh amma C.s Aka mata an Ciro 'Yara Biyu mace da Namiji.." Dafe ƙirji Farida Tayi kafin Tace " 'Yan biyu fa kace...?" Ta faɗa Tana kallonsa Bai mata magana ba illah binta da Kallo Da yayi kafin yace "Eh Abunda Kunnenki ya jiye miki..." daga Haka ya Wuceta ya Barta sama ya Koma ya Ɗauko Wayarsa ya Sauko, Ɗakin Mufeeda ya Shiga Inda ya Tatarro Duka kayan Babies, Sai kuma Dogayen Riguna da Riga da Zani, ya Fito Nan ya Wuce Farida Tsakiyar Falon Tana Binshi da Kallo, Bassam ne ya Biyosa yana Tambayansa Mufeeda Ta Haihu Cike da Fara'a Tahir ya Ɗaga mai kai kafin yace "Kun samu ƙanne Bassam 'Yan'uwanku ne Twince ne Suma.." Washe Baki Bassam yayi Harda Tsalle yana Faɗin "Daddy Zan Bika.." Bai ce mai komai ba sai ma Miƙa mai Jakar Kayan Mufeeda da yayi Suka Fice Daga Falon.


Sai da Tahir ya kawo Kayan Kana Aka maida Yaran Ciki aka Sake Gyarasu aka Shiryasu Cikin kayan Sanyi pick masu kyau Ɗakin da Mufeeda Suke Suka maidasu, suka ce suma abarsu Su Huta Haka nan, Bakin Basma da Bassam yaƙi Rufuwa saboda Murna Sai Lokacin Tahir ya samu Damar Kiran Baba Hakimi yake Sanar Dashi Baba Hakimi Dake Shirin Fita Sallar Azahar ya Washe Baki yana Faɗin "Kai Masha Allahu...Allah ya inganta.." Daga nan Abba ya Kira Shima ya Sanar Dashi, Shima ya Saka albarka, Daga Abba sai ya Kira Ishaq ya Sanar mai, Wanda ke Zuba kabbara Cikin Waya kafin Kace me Haihuwan Mufeeda Ta isa Kunnan Wanda ya kamata Farin ciki kamar bata Gurɓattaciyar Hanya aka samesu ba.


****

Baba Hakimi Na gama Waya da Tahir ya Shiga Cikin Turakarsa ya Ɗauko Huhun Goro da Dabino Cikin Wata Leda Waje ya Fita Zuwa Masallacin Kusa da gidan nashi Lokacin Har An Tada Sallar Jumma'a Domin Babban Masallaci ne Wanda ke Jikin Gidan nashi Inda Suke Gudanar da Sallar Jumma'a.


Bayan An idar da Sallah Baba Hakimi Ya bada Sanarwan Akwai ɗaurin Aure nan da nan ko Kowa ya Matso kuɗi ya Fito Dashi Duba 30k ya bama Liman yana Faɗin "Ina so kazama Wakilin Ɗana Tahir, ni kuma zan zama Wakilin Mufeeda A Ɗaura musu Aure.." Liman ya Washe baki ba tare Da bata Lokaci ba nan Take Shaidu Suka Shaida Ɗaurin Auren Tahir Mansur Ɗanbatta da Mufeeda Bello Ɗanbatta, Auren Daya bama Kowa Mamaki Domin Mutane Da dama Sun san Mufeeda A matsayin Wacce ke Reno A gidan Tahir, Cikin Fari ciki Taro ya Watse bayan an Raba Goro da Dabino Baba Hakimi ya ɗibi Wasu ya Shiga Dasu Cikin Gida Har Ɗakin Goggo Abu Wacce ke Cike da Murnan Wayar Da Tahir ya mata yanzu Yana sanar da Ita Haihuwan Mufeeda, goro da Minti ya miƙa mata yana Fadin "Na Ɗaura ma Tahir Aure da Mufeeda Yanzu bayan Mun Sauko Daga Sallar Jumma'a..." Baki Goggo Ta Washe kafin tace "Mallam kamar kasan Abunda Ke Raina kenan...Allah ya basu zaman lafiya.." Da Ameen ya amsa Cikin Jin Daɗin Haɗin kanta Duk Da yasan bazai Samu Matsala ba.


******


Har Yammah Su Innaro na Asibitin Sun cika Ɗakin da Mufeeda Take bayan ta Farfaɗo, Basma da Bassam Sun ƙanƙame yara Ko Tahir basu Bari ya Ɗauka ba, sai da Innaro ta karɓe Macen Ta Hannun Basma Ta Miƙa mai ya karɓa Cikin Jin kunya Lokaci Ɗaya yana Tsurama Jaririyar Ido Sak Basma Tana Jaririya, Lokaci Guda Idanuwansa Suka kawo kwallah yayi Saurin Mayar Dasu Mufeeda Dake Jingine da Gado Tana kallonshi yana Dagowa Suka Haɗa ido sai tayi Saurin Kauda kai Murmushi yayi ya ƙarasa Kusa da Ita yana Faɗin "Mufee ya Jikin..?" Kanta na Ƙasa Tace "Da Ɗauki Daddy..." Kai ya gyaɗa kafin yace "Masha Allah...Allah ya ƙara baki lafiya.." Da Ameen Ta amsa Ƙasa ƙasa, kan Jikinta ya Ɗora mata Jaririyan Yana Faɗin "Kina Sonta...?" Kallonsa Tayi kafin tace "Kaifa kana Sonsu...?" Kai ya Gyaɗa mata kafin yace "Ina sonsu Sosai kuma Zan Cigaba da Ƙaunarsu Har Ƙarshen rayuwata.." Murmushi Ta Saki kafin tace "Nima ina sonsu...." Dariya yayi yana kallonta kafin ya Miƙa Hannu ya karɓi na Hannun Bassam ya Ɗora mata Bisa Jikinta yana Ƙoƙarin Zama Kusa Da ita Wayarsa ta Shiga Ƙara Miƙewa yayi ya Zarota Ciki Aljihu sai yaga Hakimi ne Da Hanzari ya Fice Mufeeda ta Bisa da Kallo Cikin Wani yanayi. 


Fita yayi Haraban Asibitin kana Ya Ɗaga Kiran Cikin Farin ciki Baba Hakimi yace "Ya Wajen Maijegon da Sabuwar Amarya don bazan Tambayi sabon Megidan Salamatu ba Tunkafin ya Fito Duniya Take Nuna min Son kai.." Dariya Tahir yayi kafin yace "Duk Suna lafiya Ranka ya Daɗe.." Baba Hakimi yace "Madallah kafin ya Zarce da Faɗin "Attahiru na yanke Wani Hukunci ba tare Da nayi Shawara Da kai ba Domin ina ganin Hakan Shine Daidai.." Tahir ya Jinjina kai yana Faɗin "Ka isa ne Ranka ya Daɗe kowani Hukunci ne zan karɓa Hannaye Bibbiyu.." Baba Hakimi ya saki Murmushin Jin Daɗi yana Faɗin "naji Daɗin Haka ba Komai Illah Ɗazu bayan sallar Jumma'a Na Ɗaura maka Aure da Mufeeda yanzu Haka tana Matsayin Matarka ne Attahiru..Bata da wanda ya fika ku Haɗu ku Rungumi 'ya'yanku Karsu Tashi suga bakwa Tare Su Tuhume ku Wata rana.." Ajiyar Zuciya Tahir ya Sauke kafin yace "Hakane Baba...Allah ya bani ikon Adalci.." Da Ameen Baba Ya amsa kafin Su yanke Kiran Bayan Baba Hakimi ya tabbatar mai Suna Tafe ko yaushe.


Bai koma Cikin Asibitin ba yayi Tsaye yana Tunanin Wannan Al'amarin Guda Biyu Lokaci Ɗaya Haihuwa da Aure, Dafe kansa yayi yana Faɗin "Alhamdulillah...Allah ne Abun Godiya.." Yana Cikin Wannan Halin ya hangi motar Ishaq Ta Shigo Cikin Asibitin Bai Matsa daga Wajen Ba Har Suka ƙaraso Shida Zahra ta gaisheshi Bayan Ta mai barka, Shi ya musu Jagora zuwa cikin Ɗakin Suka Gaida Mufeeda Suka kuma Ɗauki Yaran Bayan Sun gaisa da su Innaro Nan Suka bar Zahra Tahir yaja Ishaq suka Fita Waje Cikin Damuwa ya labarta mai Abunda Baba Hakimi ya Kirasa ya gaya mai Baki Ishaq ya Washe kafin yace "Finally...Baba Hakimi ya gama maka Komai Friend...Mufeeda Ta Chanchanci Haka Domin Bata da Wani Gata Nan Duniya bayan kai...Gaskiya Allah sakama Baba Hakimi da alheri Yayi Abunda ya Dace.." Tahir dai Shiru yayi yana Jin Ishaq Shi kuma yana Cigaba da Bashi baki basu koma Cikin Ɗakin ba sai da Sukayi sallar Mangariba, suna komawa Tahir yace Su Basma Su Shirya su Koma gida, Harda Iya gobe da Safe sai su Dawo Innaro kaɗai Aka bari zata kwana da Mufeeda, Zahra tayi musu sallama Bayan ta ijiye musu kwandon Abincin Da tazo Dashi. Tare Suka Fita Bayan Tahir yayi musu Sai da Safe Mufeeda kuwa na Kwance Tana Binsu da kallo har Suka Fice Daga Ɗakin.




*Anitha..*

*Aisha Alto..*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*


_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


    *BABI NA ASHIRIN DA DAYA*


"""Suna Shigowa gidan da Farida Suka ci karo tana Zaune Afalo Tana Zare ido Domin gama wayarsu kenan da Umma tana Tambayanta ya Wajen masu jego tace suna lafiya tanama Asibitin ne Tafito amsa waya ne,Umma taji Dadi tace mata suna nan Zuwa Cikin Satin nan Ita da Abbanta......


Daga Tahir har ya"yansa Babu Wanda ya Tankata Kowannensu Dakinsa ya Nufi Haka Shima Tahir ya Haura sama ya Fada Dakinsa A matukar gajiye yake Shiyasa yafada wanka,Iya ce kadai ta iya tsayawa tana gaida Faridan wacce Tabi su Basma da kallon Mamaki,Tahir ta Daina Damuwa dashi Domin baya Shiga Harkanta Tuni.


Bayan ta amsa gaisuwan Iya ne ta kalleta tana Fadin"Wai iya da gaske ne Mufeeda yan biyu ta Haifa...? Gyada mata kai Iya Tayi Lokaci Daya tana Washe baki tace"Eh Hajiya mace da Namiji yara nan kamar su Basma suna Jarirai inji innaro.."Harara Farida ta Zabgamata Lokaci Daya Tana Fadin"Kul kar na sake ji...Ni ya"yana na Sunnah ne karki kara Hadasu da Shegu wanda ba ya"yan Sunnah ba.."Cike da mamaki Iya ke kallonta bata samu Zarafin mgana sai ma gyada kai Datayi ta juya Zuwa Daki bayan ta kalli Naila dake barci kan kujera tagaji da kuka Barci ya kwasheta.


Da Harara Farida ta Bita kafin ta koma ta Zauna tana karkaɗa ƙafa, Iya tana Komawa ɗaki ta Fito ta Shiga kichen domin sama musu saukakkan Abinci da zasu ci Shiko Tahir Bayan ya Fito Wanka yayi sallar Isha'i da Shafa'i da Wuturi ya koma ya kwanta domin Haka kurum yaji Cikinsa ya Cika baya Sha'awan Cin komai kwance yake kawai yana Tunanin Wai shi yanzu mijin Mufeeda ne, Lalle Allah ne mai Tsara komai kuma ya aiwatar yana Fatan Allah yasanya alheri yabashi ikon kwatanta Adalci Domin baya ta Farida Ita yanzu bazai ƙara Ɗaukan Wani Iskancinta ba, Itama ta sani.


Da Iya ta gama Dafa musu macaroni da Kifi, Su Basma kaɗai Suka ci sai Iya ko Farida bata ci ba ɗaki ta koma tana kukan Bakin ciki da Takaichin Wai Mufeeda Ta haihu har 'ya'ya biyu lalle ma wato zata Haɗa kafaɗa da ita, ba wanda yabi ta kanta Har Washegari da Safe Tahir ya Tafi Office Su kuma Iya da Basma da Bassam da Naila data saka Rigimar sai ta tafi Tahir baima sani ba Ya bari sai zuwa yammah su koma Tunda ya tafi musu da Abun karyawan da Iya tayi musu Ashe su kuma suna Gama Dafa na Rana suka tafi dashi Keke Napep Suka Shiga Zuwa Asibitin Suka bar Farida agida tana kallon ikon Allah.


Sanda suka isa asibitin ma Sun Iske Zahra matar Ishaq itama ta kawo Abinci Mufeeda na Zaune Innaro na bata Tea abaki Taji Sauƙi ba kamar jiya ba, Namijin ne ke Hannun Zahra Shine mai Rigima macen na kwance Tana barci Naila Haka ta saka Rigiman sai an bata Ta Ɗauka ganin Su Basma Sun Ɗauka harda kukanta Su Iya na mata Dariya, cikin ikon Allah Ruwan Nonon Mufeeda ya Fara Zuwa ba laifi Tunda Dukkansu suna samu Suna Sha Duk da baya isarsu Da Safe ma da Tahir yazo Likita yamai maganar za'a Haɗa musu da madara saboda kada yunwa ta kamasu.


Kumburin Jikin Mufeeda ya Ragu amma ba Sosai ba, Sunyi Waya da Baba Hakimi da Goggo Abu Awayar Innaro Kunya Mufeeda keyi Jin Suna Tambayanta Ya Jikinta bata magana sai dai Murmushi Suna nan har Dare nan Ishaq da Tahir suka samesa bayan Sun Dubata Suka Wuce gida Gaba ɗayansu bayan ya kawo musu Kayan marmari da Nama gashasshe saboda Mufeeda Ta maida Jikinta.


Haka Suka Din gayi Har Tsawon Kwana Biyar, amma Farida bata taka Asibiti ba sai Ranar da Mufeeda ta cika kwana Shida taji Sauki ma, har ta fara Zuwa Bayi da kanta aikin ya fara Bushewa, Farida kunya taji Yasa ta Shirya taje Asibitin Aikwai Tayi Nadama Sosai Domin ba wanda ma yabi Ta kanta Bata Raina kanta ba sai da Yammah Bayan Tahir ya Shigo Asibitin yana Shigowa Ɗakin Su Basma da Iya da Innaro Suka Fice Suka barshi amma ita sai ma gyara zama Datayi kuma Abun Haushi ko Yaran bata Ɗauka ba Daga Cikin gidansu ta leƙasu Idanuwanta na kawo ƙwallah ganin Tsabar kama da Tahir da yaran Suke ko Mufeeda Da ƙyar ta iya gaisheta ta amsa itama ta kauda kai saboda Nauyi Itako Hararanta kaɗai take Acikin Ranta tana Faɗin "Kin kusa bar min gida makira.."



Bata gama Jin Nadama ba sai Dataga Tahir ya Shigo ko ɓarayin Datake bai kallah Data gaisheshi ma Kansa na gefe ya amsa, amma yana isa kusa da Mufeeda ya saki Fuska yana tambayanta ya Jikinta ita kuma Munafukar tana Sunne kai Numfashinta bai kusa Ɗaukewa ba sai taga ya zauna gefen Gado ya Duƙa yana ma yaran Wasa Mufeeda kuma na kallonsa Tana Murmushi, macen ya Ɗauko yana Faɗin "Yarinyar taso ta ɗauke ki fa Mufee..? Ya faɗa yana kallonta.


Sunne kai tayi Tana Murmushi batace komai ba, sake kallonta yayi yana kallon Jinjiran kafin yace "Kila yau ko gobe ku koma gida, in kun koma sai mu Shawaran Wasu suna zasu saka musu.." Kan Mufeeda na ƙasa tace "Basai kayi Shawara dani ba Daddy Duk Sunan da ka saka musu Dai-dai ne.." Ta faɗa tana Wasa da Hannayenta Kallonta kawai yake yi Tausayinta na ƙara Shiganshi kaɗa kai yayi yana Faɗin "A'ah...zamu magana in kun koma gida kema kina da Hakki yaranki ne.." Bata sake magana ba illah Kallonsa Datake kasan Ido bataso ya Fahimci Tana kallonshi batasan kuwa yana Kallonta ta gefen ido sai dai yayi murmushi kaɗai 



Farida Dake Zaune ba tasan Sanda Ta miƙe A fusace ba tana Faɗin "Asirin mutum ya Tonu yace Ƙaddara ne, Kuma ko kunya Yazo yana Abu goɗai goɗai, Wlh mutum bai isa ba Zuwa za'ayi abar min gida Nida Mijina da 'ya'yana, bana son karuwancin Ƙauye.." Ta faɗa tana Ficewa Daga Ɗakin Daga Mufeedan Har Tahir da ido Suka bita Shiko Tahir ko Damuwa da kalamanta baiyi ba Mufeeda ce Idanuwanta Suka cika da Hawaye Tahir bai ce mata komai ba Cikin Ranshi Dariya ce Ke Cinsa na Tunanin yadda Farida zataji in Taji Mufeeda matarsa ce yanzu.


Haka ko akayi Washegari da Safe aka sallami Mufeeda suka koma gida kafin su Dawo Iya da Basma Sun riga sun gyara Ɗakin na Mufeeda suna Dawowa nan suka Sauketa ita da 'ya'yanta Aranar kuma sai ga Ashe da Tawagarta ita da Laila da Muda tazo da kayan Wanka Goggo Abu ta bata Sakon ta kawo Itama Data Ɗauki yaran Sai da tayi ƙwallar Tausayi da Jinjina ma Rabo, Nan ta kwana Washegari kuwa sai ga Baba Hakimi ya iso gidan bai jima da Zuwa ba sai ga Abba da Umma suma sun iso Tunda Farida Taga Haka Jikinta bai bata ba illai kuwa Domin Taro Aka Sake zama kamar na Farko harda Mufeedan Shiko Baba Hakimi na Rike da Jaririn Namiji Abba na Riƙe da macen Tunda Farida Taga an Kirata Gabanta ke Faɗuwa Tana Addu'an Allah yasa Tafiya da Mufeeda Zasu yi ƙauye.


Bayan Buɗe Taro da sallama da Godiya Ga Allah Baba Hakimi ya Fara Magana yana Cewa "Kowa anan yasan Abunda ya Faru Har Aka samu Waɗannan yaran Munyi Tawassali da Sunayen Allah kuma mun yarda da Ƙaddara..Gashi Ashe Rabon bana Ɗaya bane Rabon Har na 'ya'ya Biyu ne Hakan Kaɗai ya isa kowa yagane Ƙudurar Allah ne.." Kowa ya gyaɗa kai banda Farida dake kallon kowa ɗai ɗai.


Cikin Dattako Hakimi ya Cigaba da Faɗin "Magana Ɗaya zanyi Zuwa biyu dama Abunda Ya kawoni kenan, na Farko nazo ne naga Ƙaruwar Da aka samu na Biyu kuma na gabatar muku da Hukuncin Dana yanke ko nace Wanda na Zartar nasan Wasun ku sun sani kamar Kai Tahir da Ke Innaro Tare Da Aisha, toh ba wata Magana bace Illah Aranar da yarinyar ta sauka Attahiru na Kirana banyi ƙasa a Gwiwa ba na Biya Sadaki aka Ɗaura musu Aure..." Kowa maganar bata Razana Shi ba Umma da Abba da Iya Cikin Farin ciki Suke Faɗin "Masha Allah hakan yayi Dai dai.


Farida ko Kamar Saukan Aradu Haka Taji mganar Arzane ta miƙe Hannnunta Bisa Ƙirjinta tana Faɗin "Aure...? Mijin nawa kuka Aura mata kanbura uba..." Ta faɗa Tana girgiza jiki, Tahir Da yaji kamar Ta Tsikara mai allura na Zagin Data ƙunduma kafin ya Ɗauki mataki Umma ta miƙe ta Sharara mata mari tana Faɗin "Kinci Ubanki Farida Baban Mijin naki kike cema Kan Bura uba Saboda baki da Tarbiya..?" Kuka Farida ta Fashe Dashi Ta Duƙe tana Faɗin "Wayyo Allah na na Shiga uku ni Farida Ina zan saka kaina kowa baya sona." Umma ta Ɗuma mata Dundu Tana Faɗin "Eh ɗin ba'a sonki ɗin Uban waye zai soki Kina da Mugun Hali Tir Dake Farida iliminki bai miki amfani ba.." Kuka Farida take kamar Ranta Zai Fita kowa A falon yaji Daɗin Hukuncin Umma Barin ma Ashe da Haushin Farida ya cika mata Ciki Abba ko Kunyace Ta Hanashi Magana Shiko Baba Hakimi mamakin Rashin ɗa'ar Farida ne ya kamashi.


Basma da Bassam Dake gefe ko Ajikinsu basu damu da Kukan Da Farida keyi ba sai ma murnan Da Suke Daddynsu ya auri Mufeeda Zasu Dinga ganin Twince dama Fargabansu kar a ɗauke musu su suna sonsu sosai kuma suna son zama da ita.


Mufeeda kuwa kanta na Duƙe Tana Share hawaye Wai Abun Mamaki itace matar Daddy, Lalle Allah mai yarda yaso amma Maganar gaskiya ba' ajinta bane ya Fita komai da komai, Ta Daɗe tana Fatan Allah ya bata Miji Irin Daddy koda bai kaisa ba koda Rabinsa ne sai gashi shi ɗin Allah ya mallaka mata, Babu Abunda Zatama su Baba Hakimi sai godiya Domin Sun inganta Rayuwarta.


Hakimi ne ya Kaɗa kai yana Faɗin "Banzaci Haka Daga gareki ba Farida..Assha Abun bai min Daɗi ba..Karki manta Mufeeda yanzu amana take garemu, Tun mahaifiyarta na Raye take ƙarƙashin Ikon mu kuma in bai Aureta ba Alhalin Shi ya ɓata mata Rayuwa Wa kikeso ta Aura ga 'ya'ya baki Tunanin Watarana agoranta musu..? Saboda Haka Tahir shine Rufin Asirin Mufeeda Itama Shine Rufin Asirinta ina Fatan zaku zauna lafiya da Junanku Ku Rungumi ƙaddaranku Tunda Haka Allah ya Tsara muku.." Ko ɗago kai Farida batayi ba sai Gunjin kuka take Baba Hakimi bai Damu ba Illah maida kallansa Da yayi kan Mufeeda yana Faɗin "Kiyi Haƙuri Mufeeda kiyi ma Mijinki biyayyah kuma ki kula da 'ya'yanki na Tabbata Attahiru bazai barki kiyi Kukan Maraici ba.." Mufeeda kanta na ƙasa Tana Share Ƙwallah tace "Bakomai Ranka ya Daɗe...Bani da Bakin da zan mika godiyata zuwa gareku..Tun Mahaifiyata nada Rai kuke Jin ƙaina kuna Wahala dani, Daddy ya ingata Rayuwata ya Wahala dani ya Tarbiyantar dani kamar 'yar daya Haifa na yarda Ƙaddara ne ya Faɗa mana Babu Abunda zan ce muku Sai Fatan Gamawa da Duniya lafiya, Allah ya saka muku da Gidan Aljannah Firdausi.." Ta faɗa tana kuka Sosai kowa Afalon sai da kalaman Mufeesda ya Sakashi kwallah Shi kanshi kafeta da Ido yayi yana Jinjina ma Kaifin Tunanin Mufeeda Kukan kuwa kara Narkamai da Zuciya yake.



Baba Hakimi ya Jinjina kai yana Faɗin "Ameen Ameen...Allah yayi muku albarka...Allah ya albarkaci Aurenku ya kuma baku zaman lafiya.." Yake Faɗa yana Share Siririyar ƙwallar Data Zubo mai, Abba ne yayi gyaran Murya yana Faɗin "Masha Allah...Allah ya bada zaman lafiya Haƙiƙa Mansur kayi Tunani mai kyau Allah ya sanya alheri.."


Kowa ya amsa da Ameen Baba Hakimi ne ya kalli Tahir yana Faɗin "Ka sanya musu suna..?" Kai ya gyaɗa kafin yace "Eh jiya da Daddare nayi ma Namijin Huɗuba da Sunanka macen kuma na mata Huɗuba da Sunan mahaifiyar Mufeeda.." Kowa ya Washe baki yana Faɗin Masha Allah Mufeeda kuwa Ɗagowa tayi tana kallon Tahir Lokaci Ɗaya Tana Kuka tana Dariyar Farin ciki Shima Murmushin ya sakar mata.


Baba Hakimi yace "Kai...kai Naji Daɗi sosai nagode..Allah ya Raya Mansur da Hulairatu.." Kowa ya karɓa da Ameen kafin ya cigaba da Faɗin "In zaku yi taron Sunanku Ku haɗashi duka da Tarewar Mufeeda Tunda Duka gida ne, Bana son Bidi'a Komai kuyi shi Lokaci Ɗaya.." Ashe tace "Insha Allahu Baba Dama munyi magana da Yaya Tahir In Sati ya Zagayo za'a Yi Taron Suna sai A haɗa da Tarewarsa Allah ya basu zaman lafiya.."



Ta faɗa tana makama Farida Harara Wacce tabar kuka sai ajiyar Zuciya, babu wanda ma ya ƙara bi takan Farida aka Rufe Taro da Addu'a Baba Hakimi ya miƙama Innaro Takawaranshi Shi kuma Abba ya miƙawa Iya mai sunan Inna Fulera suka Fita Waje, Farida kuwa Umma ta jata ɗaki ta Zaunar da Ita tana Faɗin "Farida..Farida.Farida..!


Ta faɗa tana kallonta Cikin Muryan Ɓacin Rai tace "Farida Sau nawa na kiraki..?" Ta faɗa tana Murɗe mata kunne Cikin Hawaye tace "Sau uku Umma.." Sakin mata kunne Tayi tana Faɗin "Kinga Duk Abunda ya Faru ko..? Kinji kuma kin gani yadda kika zama bora banza a idon Mijinki da 'ya'yanki harda Dangin Mijinki...ko..?" Kai Farida Ta gyaɗa tana Kuka sosai Umma tace "Toh ya rage naki ki Zauna kima kanki karatun ta natsu In ba Haka ba Wlh Tallahi Tahir zai koreki Daga gidan nan Kina ji kina gani yarinya ƙarama ta ƙwace miki miji Tunda kin zama Sakarya Kina sane yanzu ba Da bane Wlh Tahir bazai ƙara Ɗaukan Abun da ya Ɗauka abaya ba, Ya Rage naki Farida Ki gyara Rayuwarki da Halayyarki in ba Haka ba Wlh Zaki Kwashi Nadaman Dayafi Wanda kike karɓa yanzu, Daga ƙarshe ina Fatan Allah ya Sausauta Zuciyarki ya Kori Sheɗan acikin Rayuwarki." Ta faɗa tana miƙewa kafin tace "Zamu Tafi..Sai an kwana biyu ƙila nazo Ranar Tariyan, Don Allah Farida ki maida komai ba komai ba, ki nemi Gafaran Mijinki ki kuma Rungumi 'ya'yanki Da Mufeeda Ko kimarki ta Dawo don Allah ba domin Halina ba..." Ta faɗa Tana Haɗa Hannuwanta Waje Ɗaya.


Farida ta miƙe ta Rungume Umma tana kuka take Faɗin "Insha Allahu Ummah naji maganarki...Nayi miki alƙawarin Zan Chanza Halina Umma zan Nemi gafaran Tahir dashi da Mufeeda Umma, Na gane kuma na Fahimta Duk Abunda ya Faru laifina ne.." Rungumeta Umma Tayi tana Bubbuga bayanta take Faɗin "Naji Daɗin Haka Allah yayi miki albarka.."


Ta faɗa tana Share mata ƙwallah, Har Falo ta Rakota Ta Shiga wajensu Innaro ta musu sallama ta Fice Haraban gidan inda Abba ke Jiranta Daga nan suka ma Tahir sallama suka Tafi, Baba Hakimi ko Tuni Garzali ya Miƙa Dashi Farida kuwa ɗaki ta koma tana kuka Cikin Zuciyarta tana Fatan Allah ya bata ƙarfin Gwiwan Gyara Rayuwarta.







*Anitha...*

*Aisha Alto..*

*NANNY..!*

_(Mai Reno..)_


*Alkaluman:*✍️

 

*AISHA ALTO*💞

*JAMILA UMAR(Janafty)*💕



_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_


_*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*_



     *BABI NA ASHIRIN DA BIYU*




_Assalamu Alaikum...Ina masoyanmu na nesa Dana kusa..Ku marmatso ga dama ta samu Kuna Buƙatar ku kece raini cikin Flat Shoes masu kyau da Tsari...Toh ga dama ta samu zaku samesu acikin Rahusa mai Sauƙi...Gamai Buƙatar Siyan Ɗaya ko Sari Zai iya Tuntuɓarmu ta wannan Nombobin kamar Haka 09069067488 ko kuma 08147672049 Mu na Maraba da masu siyan Ɗaya ko Sari zaku samesu kan Rahusa mai Sauƙi...Sai kunzo..Siyan Nagari mai da kuɗi gida...mai kasuwa kuma Shi ke da Riba..._


Sai da Farida taci uban kukanta ta gode Allah, sannan ta share hawayenta ta miƙe jiki a sanyaye ta shiga toilet tayo wanka ta fito ko mai bata tsaya shafawa ba ta zira doguwar rigar atamfa a jikinta ta zauna a bakin gado ta zabga tagumi ta tsurawa guri guda idanu tana saƙe saƙe a zuciyarta.


Bayan sallar Isha'i Tahir ya shigo gidan, tana jin motsin shigowarsa ta miƙe a sanyaye ta ɗauki hijabinta ta fice ta nufi ɗakinsa, yana ƙoƙarin shiga toilet ta shigo, kallo ɗaya yayi mata kawai ya ɗauke kansa gefe ya buɗe ƙofar toilet ɗin zai shige abinsa, da sauri ta isa gabansa ta riƙo hannunsa ƙwallah na taruwa a cikin idanunta ta marairaice gwanin tausayi tace "Don Allah don sonka da Annabin rahama kayi haƙuri kazo muje ɗakin Mufeeda...Akwai maganar sa nakeso nayi daku ne dukkanku...Don girman Allah Abban Basma kar kace a'a..." Ta faɗa da magiya ƙwallah na gangarowa daga cikin idanunta suna zubowa kan fuskarta, tsam yayi kawai ya tsura mata ido yana kallonta kamar ba zai je ba, can sai ya janye hannunsa a nata ya raɓa ta gefenta ya nufi ƙofa, da sauri tabi bayansa suka fice suka nufi ɗakin Mufeeda.


Suna shiga suka iske su Innaro da Iya dasu Basma da Bassam a ɗakin tare da Mufeedan suna hira, a hankali ta taka ta shiga tsakiyar ɗakin ta tsaya agaban Tahir daya tsaya ya zuba mata ido yana kallonta yayinda gaba ɗaya su Iya da Innaro dasu Basma suma suka zuba mata ido suna kallonta, a hankali ta durƙusa a gaban Tahir ta zube gwiwoyinta a ƙasa hawaye na zubo mata ta duƙar da kai cikin rawar murya tace "Don Allah don Annabi don girman Allah...Kayi haƙuri ka yafe min na tuba..Ka yafe min duka laifin dana aikata, bazan sake ba, na yarda nayi kuskure kuma zan gyara halayena..." Ta faɗa tare da fashewa da kuka, a hankali yace "Na yafe miki...Allah ya yafe mana baki ɗaya.." Wani sanyin daɗi taji ya ziyarci zuciyarta har sai da ta saki ƙaramin murmushi ta juya tana share hawayen fuskarta ta matsa gaban Mufeeda dake zaune ta duƙar da kanta tana wasa da farcenta, a hankali Farida ta riƙo hannunta tana kallon cikin idanunta take faɗin "Nasan nayi miki abubuwa da dama waɗanda bazasu lissafu ba Mufeeda..amma karki dubi munin abunda nayi miki ki dubi girman alkhairina agareki ki yafe min kuskurena..nasan na cutar dake sakacina ya jefaki cikin wani yanayi, na cuci rayuwarki...Kuka ya hanata ƙarasawa. Da sauri Mufeeda ta faɗa jikinta itama ta fashe da kuka tana faɗin "Bakiyi min komai ba Momy..kuma duk abunda ya faru dani daga Allah ne dama dole sai ya faru dani ban isa na kauce masa ba, kuma na ɗauki hakan a matsayin ƙaddarata, don haka ki daina cewa na yafe miki bakiyi min komai ba, nice ma zan roƙeki yafiya...Don Allah ki yafe min, kuma duk abunda kika yi min wanda na sani da wanda ma ban sani ba duka na yafe miki..." Ta faɗa tana ƙara ƙanƙame Faridan a jikinta, ƙara rungumeta Faridan tayi itama suna sharɓan kuka, Tahir dai na tsaye yana kallonsu jikinsa duk yayi sanyi, a hankali Farida ta janye Mufeeda a jikinta ta durƙusa agaban Iya itama ta roƙeta ta yafe mata sannan ta durƙusa agaban Innaro itama ta yafe mata sannan Basma da Bassam suma duk suka yafe mata. Nan take taji ta fayau zuciyarta tayi mata wasai taji kanta kamar an sauke mata wasu tulin kaya.


Haka a ɓangaren Tahir yaji daɗin abunda Faridan tayi sosai a ransa har hakan ya nuna a fuskarsa kuma yana fatan Allah yasa hakan ya zama gaskiya har a zuciyarta tayi tuban ba tuban muzuru ba.


Miƙewa tayi a hankali ta ƙarasa inda gadon jariran yake inda suke ciki a kwance luf abinsu ta tsaya tana murmushi ƙwallah na taruwa a cikin idanunta ta buɗe ta ɗauko macen ta riƙe sannan ta ɗauki namijin shima ta haɗasu ta rungume a jikinta tana jijjigasu kafin kuma ta cirosu daga jikinta ta tsura musu ido tana kallonsu har bata san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba, ƙarasa tayi gaban Tahir da fara'a a fuskarta tana faɗin "Abban Basma zoka gani, wallahi yaran nan tamkar Basma da Bassam lokacin dana haifesu suna jarirai.." Ta faɗa tana ƙarasawa gabansa, yana dariya ya karɓi namijin a hannunta yana kallonsa yace "Wallahi haka nace nima.." Innaro tace "Nima dai haka nace.."

Tahir yana murmushi yace "Ai kamarsu da 'yan uwansu ce ta fito sosai."  Ya faɗa yana miƙa mata yaron. Karɓarsa tayi ta miƙa masa macen tana faɗin "Yanzu da wane suna za'a dinga kiransu kenan..?" Ta faɗa tana kallonsa, yana dariya yace "Mufeeda wane suna za'a dinga ce musu..?" Ƙara sunkuyar da kanta ƙasa tayi cike da kunya tana faɗin "Duk abunda kuka zaɓa yayi Momy.." Ta faɗa tana murmushi. Farida tace "To shikenan, namijin zamu dinga kiransa da Ayman macen kuma mu ce mata Airah.." Da murna Basma tace "Yauwa Momy...Wallahi sunan yayi mana daɗi sosai..kuma ya dace dasu..Allah ya raya mana ƙannen mu.." Da Ameen duk suka amsa, kafin daga nan suka shiga hirar yanda taron suna da bikin tariyar zata kasance, kowa ka gani fuskarsa cike da fara'a da farin ciki take, har ta su Basma da Bassam ma walwalarsu ta ƙaru a wannan daren, sai farin ciki da annashuwa suke.


Sun daɗe sosai a ɗakin suna hira har ƙarfe 10:30pm kafin Tahir da Farida sukama su Innaro da Iya da ita kanta Mufeedan data fara barci sallama suka fice tare dasu Basma da Bassam kowa ya shige ɗakinsa bayan sun musu sallama suma, suka nufi bedroom ɗin Tahir.


Suna shiga ciki ta janyosa jikinta ta rungumeshi ta baya ta zagaya hannayenta a saman cikinsa tana shafo ƙirjinsa a hankali cike da wani irin salo, juyo da ita yayi gabansa ya tsura mata idonsa, kasa jurar irin kallon da yake mata tayi ta zame hannunta ta faɗa jikinsa ta ƙanƙamesa ta fashe da kuka mai tsuma rai da zuciya tana ƙara bashi haƙuri.


A hankali ya fara shafa bayanta alamar lallashi yana hura mata iskar bakinsa a cikin kunnenta cike da wani irin salo mai tafiyar da ruhi haɗe da zuciya mai ƙara azalzala wutar ƙauna, ƙara shigewa jikinsa tayi ta lafe tana karɓar saƙonsa, a hankali ya fara tafiya da ita zuwa gurin gadon dake ɗakin tana jikinsa a narke tana shaƙar daddaɗan ƙamshin turarensa mai sanyaya zuciya, a haka suka isa gaban gadon, cike da shauki ya ɗagata cak ya ɗorata a saman gadon ya kwantar da ita flat, sannan ya hau kai shima bayan ya zare rigar shadda dake jikinsa yayi saura daga shi sai dogon wandon kayan.


Wani irin shauki da tsantsar soyayyar mijinta Farida taji tana ƙara kamata, tana daga kwancen tana kallonsa ya hayo saman gadon ya fara ƙoƙarin zare mata rigar jikinta, wani irin daɗi da farin ciki mara misaltuwa Farida taji sun kamata lokaci ɗaya daɗi ya baibayeta ta ɗago ta faɗa jikinsa tana ji a ranta yau zata gwada masa tsantsar ƙauna wacce bata taɓa nuna masa ba, zata nuna masa tsabtatacciyar ƙauna mara iyaka wacce babu algus a cikinta, zata sa yayi alfahari da ita ta tsaya a ransa ya kasa gogeta a zuciyarsa. Cike da salo ta jawo makunnin wuta ta kashe wutar ɗakin, ɗakin yayi duhu kaɗan ta miƙe ta sauka daga kan gadon ta cire rigar da kanta yayi saura daga ita sai pant da bra suma a hankali ta zaresu ta koma saman gadon ta haye jikin Tahir dake zaune mamaki ya gama cikasa ya zuba mata ido kawai yana kallonta, ganin irin kallon da yake mata mai cike da mamaki yasa ta ƙara zagewa ta jawosa jikinta ta haye saman cinyarsa a hankali ta fara shafo fuskarsa zuwa leɓensa da wani irin salo kafin ta ɗago haɓarsa tana kallon cikin ƙwayar idanunsa ta haɗa bakinsa da nata, wani irin lumshe idanu Tahir yayi cike da jin daɗi ya ƙara matso da ita jikinsa sosai ya kamo tattausan harshenta ya fara mata wani irin tsotsa mai tayar da hankali dasa mutum mantar dashi kansa waye. 


Sake zagewa Farida tayi sosai ta kamo harshensa ta shiga aika masa da wani lafiyayyen kiss mai kashe jiki da zuciya, Tana yi tana shafar sumar kansa tana tura yatsunta ciki tana masa wani irin salo kamar tafiyar tsutsa, a haka ta sauka har kan gadon bayansa tana shafa bayan tana masa tafiyar tsutsa kamar tana masa susa, idan ta ja har tsakiyar bayansa sai ya gantsare ta dawo da hannunta sama tana shafo ƙeyarsa, in banda sauke numfashi da gurnani babu abunda Tahir ke yi, hakan ya ƙara mata ƙwarin gwiwa ta zage sosai ta dage ta shiga nuna masa tsantsar ƙauna mai cike da nuna tattali da tsantsar so mai tsayawa a zuciya.


Duk wani salo mai kashe zuciya da saka rai cikin tsantsar buƙatuwa, sai da Farida tayi amfani dasu gurin kashe jikin Tahir ta mantar dashi kowa da komai a wannan dare, ta zage ta nuna masa cikakkiyar kulawa da tattali.


Wani al'ajabi da mamakin Farida ne ya kama Tahir, sagale ya tsaya kawai yana kallonta a ransa yana tambayar kansa dama kenan ta iya komai take tsaya masa kamar gunki ta barsa yayi kiɗinsa yayi rawarsa? Ko ta nuna masa bata son komai da yake mata ita ta gaji bata iya ɗaukar lalurarsa? Lallai Farida yau ta bashi matuƙar mamaki, kuma yaji kimarta da darajarta sun fara dawowa a zuciyarsa.


Sosai Farida ta zage ta kafa tarihi mai tsayawa a zuciyar Tahir a wannan dare, tayi duk abunda tasan zai faranta ransa ya manta da komai da kowa sai ita. A ɓangaren Tahir kuwa shima tsayawa yayi tsam ya nuna mata tsantsar kulawa mai dasa farin ciki mara gushewa da walwala mai matuƙar tasiri a zuciyar duk wasu ma'aurata masu so da ƙaunar junansu.



Washegari da sassafe Farida ta tashi bayan sunyi wanka da Asuba sunyi sallah Tahir ya koma barci ta fice ta nufi ɗakin Mufeeda, lokacin ko tashi Mufeedan bata yi ba tana ta sharar barci abinta, sai Innaro dake zaune akan darduma tana lazumi Iya kuma na kichen zata dafa ruwan wanka, bayan sun gaisa da Innaro ne ta fice taje ta haɗo ruwan zafi a babban robar wanka, Innaro tace ta bari za suyi musu wankan taje ta kula da mijinta, amma Farida tace A'a su bari ita zata wanke 'ya'yanta tas. Haka kuwa akayi ta ɗauko jariran a cikin gadonsu ta fara yiwa Ayman sannan ta yiwa Airah itama, ta shiryasu tsab cikin lafiyayyun kayan sanyinsu masu kyau da tsada, Innaro na zaune tana kallonta gwanin sha'awa. Sai data gama musu sannan ta fesa musu turare mai sanyin ƙamshi ta sakasu a cikin shawul ta miƙawa Innaro su sannan ta miƙe ta ɗauke robar ta kai Toilet d'in Mufeeda ta zubar da ruwan ciki, sannan ta sake haɗawa Mufeeda ruwan wankan itama ta fito ta tasheta, ta cire kayanta suka shiga toilet. Farida Ita ta taimakawa Mufeeda tayi mata wankan jego tsab ta gasata sosai Mufeedan sai sunkuyar da kai take tana jin kunya amma ita Farida ko a jikinta ta zage ta gyarata tas ta rufa mata babban tawul suka fito..Suna fitowa ta zaunar da ita a bakin gado ta ɗauko mai ta bata ta shafa kafin ta buɗe akwatinta ta ciro mata wata atamfa riga da zani ta ajiye mata, ta koma ta ɗauko humra da kulacca da Innaro tazo mata dasu ta bata ta shasshafa a jikinta sannan ta saka kayan ta zauna ita kuma Farida ta fita. Bata jima da fita ba ta dawo ɗauke da babban kofi da kayan tea a hannunta, Mufeeda dai sai binta da kallo kawai take tana jin tsananin farin ciki a ranta, Farida kuwa tana jin bala'in kishin Mufeeda a ranta amma tana dannewa kada a gane, a haka ta haɗa mata tea mai kauri ta miƙa mata ta tura mata bread da filet ɗin soyayyen kwai ta tasata gaba sai da taci tayi dam zufa sai keto mata take, haɗa kayan Farida tayi ta fitar dasu ta kai kichen sannan ta dawo ta haɗa kayan da Mufeedan ta cire da waɗanda ta cirewa jariran ta fita dasu can bayan gidan ta wankesu tsab ta shanya sannan ta dawo lokacin ƙarfe 8:20am tace Mufeedan ta koma ta kwanta ta huta bari taje su gama haɗa breakfast da Iya, Innaro ta amsa tana sa mata albarka ta fita a ɗakin ta nufi kichen. 



Lallai Farida ta sauya sosai kuma duk wanda ya santa a ranar ya ganta dole zai gane hakan, Iya ma sai kallonta take suna aiki, tare suka gama haɗa komai suka jera a dinning table kafin ta nufi bedroom, tana shiga ta samu Tahir ya tashi yana Toilet yana wanka. Tuɓe kayan jikinta tayi itama ta shige toilet d'in don suyi wankan tare.


Mintuna talatin suka ɗauka a toilet d'in sannan suka fito ɗaure da tawul a jikinsu suna rungume da juna suna dariya, ita ta shafa masa mai ta shiryashi tsab sannan shima ya tayata ta shirya ta feshesu da turarensa mai daɗi da sanyaya zuciya ta ɗauko hularsa zanna bukar ta kafa masa yayi kyau sosai tana kallonsa tana jin wani kishi na taso mata tayi saurin kawar dashi ta riƙo hannunsa tana murzawa a nata cikin kwantar da murya ta fara faɗin "Abban Basma ya kamata fa a siyo kayayyakin da Mufeeda zata saka tunda tare za'a haɗa da taron suna da fitar biki..." Ta faɗa tana sumbatar tsakiyar tafin hannunsa, lumshe idonsa yayi ya kamota jikinsa yana faɗin "To shikenan, zan turo miki kuɗi ta account ɗinki sai ku sayi abunda ya dace.." Ya faɗa yana sakar mata kiss a goshinta, tana murmushi ta kama hannunsa suka fice daga ɗakin suka sauka ƙasa.


Sai da suka shiga ɗakin Mufeeda ya dubasu ita da yara suna ta barci suka gaisa da Innaro da Iya dake shirya Naila kafin suka fice bayan Farida ta ɗauki Naila tace su Innaro su fito Dinning suci abinci, suna fitowa daga ɗakin suka samu Basma da Bassam sun fito daga ɗakinsu wanda da alama sun shiga su gaishesu ne basu samesu ba, da murna suka nufesu suka faɗa jikinsu, Tahir ya ɗago Basma daga jikinsa yana murmushi yake faɗin "Karki kayar da Daddy mana..ko bakisan kin girma bane..?" Ya faɗa yana jan kumatunta, turo baki tayi ta duƙa ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska tare da shafa kanta, sannan ta juya ta gaishe da Farida dake kallonsu tana murmushin jin daɗin gyara rayuwarta da tayi, shima Bassam ya gaishesu kafin Tahir ya kama hannunsu yace suje Dinning su karya, da sauri Basma ta zame hannunta tana faɗin "Zanje na ga ƙannena da Aunty Mufeey tunkunna Daddy.." Ta faɗa tare da ƙoƙarin rugawa da gudu, saurin kamota Farida tayi tana harararta tace "To barci suke yi..baza kije ki tashesu ba.." Ta faɗa tana nufar dinning, ba don Basma taso ba tabi bayanta tana turo baki, Tahir dai na kallonsu yana murmushi bai ce komai ba.


Sai da suka gama karyawa sannan Farida ta rakashi harabar gidan ya shiga mota Garzali yaja har suka fice tana ɗaga masa hannu kafin ta koma cikin gida ta shiga bedroom ɗinsa ta gyarashi tsab ta fesa room freshener mai ƙamshi ta saka turaren wuta mai daɗi ta janyo ƙofar ɗakin ta fice..tana saukowa taji alert ya shigo wayarta tana dubawa taga transfern kuɗi ne masu yawa Tahir yayo mata tana murmushi ta nufi ɗakin Mufeeda tace Innaro ta shirya zasu fita kasuwa.


Haka kuwa akayi ita da Innaro suka je kasuwa ta narkowa Mufeeda siyayya sosai ita da jariranta ta haɗo musu kaya masu kyau da tsada, a nan kasuwar ta samu haɗaɗɗen shagon ɗinki ta bada kayan Mufeeda ta zaɓar mata ɗinkuna masu kyau da ɗaukar hankali, bayan ta biya kuɗin ya faɗa mata ranar da zata zo karɓa suka dawo gida.


Duk waɗannan abubuwan da Farida take yi kawai tana daurewa ne don tayi alƙawarin ta gyara halayenta, bazata ƙara yin abunda tasan zai sa wani yaga baƙinta ba balle mijinta da iyayenta da 'ya'yanta su tsaneta su dinga jin haushinta ba, saboda haka ma duk wasu ƙawayen banza tayi watsi dasu ta daina bi ta kansu, yanzu ta gyara rayuwarta zata tsaya ta kula da mijinta da 'ya'yanta.



Bayan kwana biyu da haihuwa Goggo Abu tazo duba Mufeeda da yaran taji daɗin yanda ta ga Farida ta koma ta saki jikinta tana ta kula da Mufeeda da yaranta nan ta tarasu tayi musu nasiha sosai mai ratsa jiki da zuciya. 



*BAYAN SATI ƊAYA...*



Ana gobe taron suna da yamma Farida ta ɗauki Mufeeda suka tafi cikin gari ta kaita wani haɗaɗɗen Saloon inda take zuwa aka tsantsara mata ƙunshi da kitso ta biya kuɗin suka dawo gida. Suna zuwa suka tarda Ashe dasu Muda da Laila sun zo, nan Ashe tayi ta yaba kyaun da Mufeedan tayi, ita dai Farida sai dai tayi dariyar yaƙe kawai tana ƙoƙarin danne abun data ji yana taso mata.


Washegari tunda sassafe Zahra matar Ishaq da 'ya'yanta suka zo. Nan suka haɗu dasu Innaro da Iya da Farida da Ashe suka shiga aiki baji ba gani, don ba wani taro za'ayi sosai ba, iya yasu yasu ne kawai suka cika gidan.

Farida da kanta ta kira mai kwalliya tazo har gida ta tsantsarawa Mufeeda kwalliyar data ƙara fito da ita tayi kyau sosai, ta ɗauko mata wani haɗaɗɗen leshi blue mai adon stones cikin waɗanda aka ɗinko mata ta bata ta saka tayi cacas a ciki, nan kyaun Mufeeda ya ƙara fitowa sosai ita da kanta Farida sai da ta kalleta ta ƙara kallonta don gani take kamar ba Mufeedan data sani bace a gabanta, Farida da kanta tayi mata lafiyayyen ɗaurin ɗankwalin daya sake fito da kyawun fuskarta tayi fayau abinta sai ɗaukar ido take tana ƙyalli. Haka jariran suma expensive kaya aka saka musu haɗaɗɗu masu kyau da tsada sai ƙamshi suke suna walwali abinsu, Basma da Bassam ma da Naila sunyi gayu abinsu sun sha kyau suna rungume da ƙannensu Ayman da Airah sun hana kowa ɗaukarsu sai dai ka gansu a hannayensu duk inda sukai dasu Naila na nan nane dasu itama.


Taro yayi taro an gama lafiya an tashi lafiya, sai dare Ishaq yazo ya ɗauki Zahra da 'ya'yansa bayan Farida ta haɗa musu kayan suna cike da leda ta rakasu har gurin mota sukayi sallama ta koma cikin gida, don yau duk a gajiye take ko hirar dare da suka saba yi a ɗakin Mufeeda bazata tsaya yau ayi da ita ba, wanka kawai zatayi ta haye gado kafin kuma uban gayyar shima ya dawo.



Washegari Ashe dasu Muda da Laila suka koma Ɗanbatta suma, nan Innaro da Farida da Iya suka cigaba da kula da Mufeeda da yaranta, Basma da Bassam kuwa indai suna gida kullum suna nan liƙe da ƙannensu haka Naila sai tasa rigima itama sai ta ɗaukesu.


Wannan kulawar da Farida ta gani kowa na ba Mufeeda shiya ƙara saka mata kwaɗayin son taga ta sake haihuwa itama, don taga duk wata kulawar Tahir da tattalinshi ya ɗorasu duka ne akan Mufeeda da 'ya'yanta.


Ranar da Mufeeda tayi arba'in a ranar Innaro tace bazata ƙara kwana a Kaduna ba, itama Ɗanbatta zata koma, haka kuwa akayi Tahir da Farida suka haɗa mata sha tara ta arziki da kaya niki niki Garzali ya maidata.





*Anitha...*

*Aisha Alto...*

*NANNY...!*

      (Mai Reno..)


*Alƙaluman:*✍🏻


*AISHA ALTO💞*

*JAMILA UMAR (Janafty💕*


_Don't Forget to Follow us On Wattpad: Janafnancy13 or Aisha Alto Alto_



*DEDICATED TO OUR SWEET UMMI💔*

*KHADIJA SALISU YUSUF..LVUSM💘*


      *BABI NA ASHIRIN DA UKU*


Ranar da Innaro ta tafi Farida ta samu Mufeeda a cikin Ɗakinta tana bama Ayman Nono Domin shiyafi Airah rigima, Gefenta ta Zauna Tana Faɗin "Kina nan Ashe..? Ina Airah take ne..?


Mufeeda tace "Wlh Ayman ya tashi Da Rigima ni nagaji da Tsotsan nan nashi Momy.." Hararanta tayi kafin tace "Kin me..? Lallai Awo ki Yarinya don sai sun Shekara 2 zaki yayemin yara.." Shagwaɓe Fuska tayi tana Faɗin "Kai Momy.."


Bata bi ta kanta ba ta fara faɗin "Kinsan Abunda Nake so Dake..? Mufeeda ta girgiza kai Farida ta cigaba da Faɗin "Yau zaki karɓi girki ma'ana Yau kece keda Abban Basma.." Ido Mufeeda ta Zaro gabanta na Faɗuwa Kallonta Farida tayi tana Faɗin "Eh Sai ki Shirya, yanzu tashi zakiyi mu shiga Kichen tare muyi Dinner, kinga ya kamata ace mun gyara komai bai dace ace yana da mata har guda biyu ba amma ace kullum Sai dai Iya ta girka ta bashi yaci ba sai na yanke Shawaran Duk wacce keda miji Ranar toh zamu Shiga kichen tare mu taimakama juna ko ya kika gani..?


Mufeeda ta Sadda kai ƙasa Tana Faɗin "Duk Abunda kika yanke Dai-dai ne Momy.." Kafaɗarta ta Dafa tana Faɗin "A'a karki ce Haka kema fa matar gidan nan ce kina da Hakki kan komai.." Mufeeda batayi magana ba Farida ta cigaba da Faɗin "Iya zata shi ci gaba da taimaka mana wajen kula da Airah da dai Sauransu.." Kai Mufeeda ta gyaɗa tana Faɗin "Hakan yayi Momy.." Sun daɗe suna hira kafin Ayman ya gama shan Nono Farida ta ɗaukeshi su Fito Falo, Su miƙawa Iya wacce ke goye da Airah tayi barci an samu 'yar Rigima Naila an tafi islamiya, Farida ce ta miƙa ma Iya Ayman ta faɗa mata Shawaran da suka yanke taji Daɗi sosai, Ko babu komai yanzu Tahir zai Fara Ɗanɗanan daɗin Aure.


Farida da Mufeeda Haka suka Zage suka Shiga Sukayi girki mai rai da lafiya, Tuwon Shinkafa suka yi miyar Agushi saboda Tahir yana bala'in son Tuwo ga miyar taji man Shanu da naman rago zuƙu-zuƙu, Zobo suka haɗa suka sanyashi cikin Fridge, Dai-dai Dawowarsu Basma Daga Makaranta suka gama komai har gyara kichen ɗin Farida ta Fita ta bar Mufeeda na wanke wanke Abun da suka ɓata, Su kansu yaran sunyi matuƙar mamaki ganin Duka iyayen nasu acikin kichen suma sun Nuna murnansu suna tsalle Cewa yau zasu ci girkin Momy dana Aunty Mufeeda.


Farida ta matsama Mufeeda taje tayi wanka itama Sama ta Haura ta Shiga wankan, Bayan ta Fito tayi sallar Magriba ta Shirya cikin wani ubansun Leshi Riga da zani batayi kwalliya ba amma Tayi kyau sosai Tana Fesa Turare taji Ihun yaran suna Faɗin Daddy oyoyo Murmushi tayi tana Ƙoƙarin Ɓoye Abunda ke Taso mata acikin ƙasan Ranta ta Fito Tun daga saman Steps d'in yake kallonta yana Riƙe da Naila harta ƙaraso tana Faɗin "Sannu da zuwa Abban Basma.."


Murmushi ya sakar mata yana Faɗin "Yauwa Umm Airah ko..? 'yar Dariya tayi Briefcase ɗinsa ya Miƙa mata ta maƙale kafaɗa tana Faɗin "Yau bani keda kai ba Mufeeda ce.." Duk da acikin Ranshi yaji daɗi domin wajen Wata goma kenan yana Fatan sake komawa wannan ƙorama amma sai bai nuna ba yawani Ware ido yana Faɗin "Bangane ba..? Baki ta murguɗa mai tana Faɗin "Baka gane ba ko..? Zaka gane anjima.." Dariya yayi yana kallonta saboda yarda tayi magana su Basma kuwa Tuni sun Wuce ɗakunansu, Farida ce ta Ɗaga Murya tana Faɗin "Mufee...Wai me kikeyi ne Haka bakiji Shigowar Megidan naki bane...? Ta faɗa tana Murmushi.. 


Mufeeda Dake laɓe Tun Ɗazu ta kasa Fitowa saboda kunya ta Fito kanta Sunkuye tana Faɗin "Gani Momy sallah na idar..." Ajiyar Zuciya Tahir ya sauke yana kallonta ƙasa ƙasa Tana Sanye cikin Riga da Siket na wata atamfa wanda yasan Mufeeda abaya ba wanda zai ce itace yanzu domin Mufeeda yanzu haihuwa da Namiji Sun Buɗata tayi kiɓa kamar ba ita ba hips da nonuwa kuwa sun cika ko'ina, ƙarasowan tayi ta ranƙwafa tana faɗin "Sannu da zuwa Daddy." Amsawa yayi yana kallon Fuskarta ido cikin ido Farida Dataga Haka sai ta wuce kichen tana Faɗin "Ki bishi Sama ki Taimaka mai yayi wanka Mufee, kafin ku Fito na Shirya Tebur.." Ta faɗa tana Shigewa kichen da Sauri kamar zata faɗi Domin bazata iya jurar irin wannan kallon Sha'awan da Tahir ke bin Mufeeda dashi ba.


Ganin ta tsaya tana Wasa da Hannunta yasa kawai ya juya ya fara Haura step Naila kuma Tun ɗazu ta sauka Daga hannunsa tabi Basma Ɗakinta cikin Sanyi jiki tabi bayansa yana jin takunta ya mata banza Har Suka Shiga bedroom ɗinsa, ko kallonta baiyi ba ya ijiye Jakar Briecafe ɗinsa da wayarsa ya Buɗe Ƙofar Toilet ya Shiga Haushinsa Ɗaya da Mufeeda Yadda komai wai sai Farida tace mata tayi Zatayi alhalin yana da tabbacin Daga Iya har Innaro basu barta Haka ba.


Kuma yayi gaskiya domin Innaro ta mata nasihan ta kuma ta bata wasu Shawarwarin, ƙara zama da Miji, Harda gyaran Jego Haka Innaro ta Tiƙe ta ma Mufeeda, kayan lambun nan Duk matsa mata take tana Sha Tsarki da ruwan zafi mai bagaruwa, shan madara da Zuma, kuma kafin ta tafi ta tarasu ita da Farida ta sake musu nasihan Zama lafiya, Amma Duk mufeeda tayi biris tana jiran komai sai Farida tace tayi kana zata Da Haushin Abun ya gama wanka ya Ɗauro alwala ya Fito Kansa Ɗaure da karamin Towel yana goge kansa Jikinsa kuma sanye da wani baƙin dogon wando Tana nan tsaye inda ya barta yana ganin Haka yace "Kinga ki Tafi kawai Nagode.." faɗin haka da yayi yasa ta Ɗago kanta suka Haɗa ido saurin kauda kai tayi ganin Ƙirjinsa yana waje ga gashi Duk ya kwanta cikin kasala ta ƙarasa kusa dashi tana Faɗin "Kayi haƙuri Daddy..."


Kallonta yayi yana Faɗin "Baki man komai ba Mufeeda Abu Ɗaya nake so ki gane yadda nake Mijin Farida haka kema nake Mijinki.." Gyaɗa kai tayi kanta na ƙasa tace "Bazan ƙara ba.." Ta faɗa Muryanta na rawa ganin Haka yasa ya Riƙo kafaɗunta yana Faɗin "Meye Abun kuka..? Kinga Zauna na gama Shiryawa mu sauka tare.." Ya faɗa yana Zaunar da ita Kan gado shi kuma ya juya yana neman kayan da zai saka Wasu Riga da wando ya saka ƙirar Armani ya Taje kansa sai gashi ya fito kamar ɗan Saurayi dan Shekara Talatin da Biyar, Tana ta satar kallonsa bai nata magana ba, sai da ya gama kana ya Riƙo Hannunta ya miƙar da Ita yana Faɗin "Muje ko.."


Kasa kallonshi tayi ta sadda kanta ƙasa, har suka Fito Daga Bedroom Farida na Saman Dining bayan ta gama Shirya komai ita da Basma da Bassam da Naila da Iya, Hangosun da yayi yasa ya saki hannun Mufeeda saboda idanuwan yaran, Farida ko Sau Ɗaya ta kallesu bata ƙara ba Har suka ƙarasa Saukowa, Farida Jikinta na rawa Ta ja musu kujeru suka Zauna yana amsa gaisuwan iya Cikin Fara'a yace "Ina su Airah...? Farida Tace "Har sunyi  barci kasan su Da sunji Ruwan zafi Shikenan.." Bai ce komai ba Illah Basma Da tace "Daddy yau fa girkin Momy zamu ci dana Aunty Mufeeda." Baki Tahir ya washe yana Faɗin "Realy...? Lokaci Ɗaya yana kallon Farida Ita kuma tana kallon Mufeeda Suna Dariya hannu yasa bisa Ƙirji yana Faɗin "Uhm..Lalle Tahir ya zama Ɗan gata.."


Ya faɗa yana Murmushi Farin ciki ya Cika ranshi, ba wanda ya ƙara magana har Farida ta sallami kowa suka Fara cin abinci, Tahir kuwa ya Zuba santi kamar ba gobe har Farida na saka mai Waigi Ranar Haka Suka gama cin abinci Cikin Farin ciki wanda Suka Daɗe basuyi ba bayan sun koma suka koma Falo Suka Zauna suna Hira da 'ya'yansu Har su Airah suka tashi Iya ta kawo ma Mufeeda ta basu Nono bayan ta gama ne Tahir ya Ɗaukesu yana Musu Wasa Farida bata bari Hiran yayi tsawo ba tace kowa ya wuce ɗakinsa yayi wanka yayi sallah kafin ya kwanta Tun da yau basu Fita sallah ba...


Ita ta karɓi Su Airah tana Faɗin "Allah tashemu lafiya...Ango Asha Amarci lafiya.." Ta faɗa ta Wuce da Sauri Jikinta na Ɗan Rawa Sabida yadda wani Duhu ya mamaye mata Zuciya, Da kallo Suka Bita Tahir ne kaɗai ya amsa mata da Allah tashemu lafiya.


Miƙewa yayi bai tsaya wata magana ba ya Riƙo hannun Mufeeda ya miƙar da ita Tsaye kuma bai yarda sun Haɗa ido ba suka Nufi Bedroom ɗinshi, Ita kuwa Farida kan gadonta ta kwantar dasu Airah Itama ta Sulale tana Sakin kukan Data ke Danewa wani kishin Tahir ne ke taso mata, Sheɗan na Zugata amma tana ƙoƙarin yakiceshi Da ƙyar ta miƙe ta Faɗa Toilet tana Rangaji.


Suna Shiga Bedroom ɗin Tahir ya saketa yana Faɗin "Ki shiga ki ɗauro alwala.." Bata yi musu ba ta Shiga ya bita da kallo yana Murmushi bata jima ba ta Fito tana Faɗin "Daddy na Fito.." Kallonta yayi kai tsaye kafin yace "Sallah zamu yi.." Kai ta gyaɗa kafin tace "Bani da Hijabi anan Ɗakin.." Bai mata magana ba illah Ficewa Da yayi har Zuwa Ɗakinta ya Buɗe Wardrope ɗinta ya Ɗauko mata Hijabi da wata Arniyar Rigar barci ya kawo mata Duk Farida najin Fitarshi da Dawowarshi tana Zaune kan sallaya bayan ta idar da sallah Hawaye na Zuba daga cikin idanuwanta..


Miƙa mata yayi Haɗe da Rigar barcin yana Faɗin "In mun idar sai ki saka wannan rigar barcin.." Ido ta Waro Tana Faɗin "Kai Daddy.." hararanta yayi ya wuce bai mata magana da Sauri ta kama bakinta tana Faɗin "Bazan ƙara ba." Murmushi kawai ya saki shima ya Faɗa Toilet d'in Mufeeda daban take, Komai tayi cikin bada Haƙuri take, Alwala ya Ɗauro Shima ya Fito kafin yajasu sallar sai da sukayi sallar Isha'i kana yajasu Raka'a Huɗu bayan sun idar ya dinga kwaroro musu Addu'ar zaman lafiya Mufeeda na amsawa da Ameen.


Tashi yayi ya isa saman Side Drower d'in gadon ya Ɗauko Madaran Hollandia ya Tsiyaya cikin Kofi ya cikashi yazo gabanta ya Zauna ya miƙa mata ta saka hannu zata karɓa ya Girgiza mata kai yana nuna mata bakinta ganin yadda ya Haɗe Rai, yasa ta buɗe baki ya shiga bata sai da tasha fin Rabi, kana ta kauda kai bai matsa mata ba shima sai ya ƙafa kai ya ƙarashe Shanyewa ya Miƙe ya maida komai inda ya Ɗauko kafin ya Dawo Agabanta ya Ƙara Zama wannan karon gwiwowinsa yana Gugan nata, Lokaci Ɗaya ya Riƙo Hannnayeta yana Faɗin "Kinga kalleni.." Ɗagowa tayi tana kallonsa Cikin kunya ganin yadda yake mata wani kallo yace "Ki saki jiki dani mana Mufeeda bana son Abunda ki kemin kinji..." Gyaɗa kai tayi tana Faɗin "Bazan ƙara ba.." Hannunta ya Sumbata yana Faɗin "In kika ƙara sai na Hukuntaki.." Jikinta ya mutu cikin Sanyinta ta langwaɓar da kai tana Faɗin "Allah bazan ƙara ba.."


Yana yar Dariya yace "Naƙi wayon..? Hukunci ne baki so ko..? Ta gyaɗa kai bazato ba Tsammani taji ya kama kanta ya Ɗora Leɓensa bisa nata ya Fara Tsotsa Lokaci Ɗaya taji jikinta ya ɗau kyarma jin Baƙon lamari ya Daɗe yana Tsotsan Leɓenta Cikin Fitan hayyaci ta saki Bakin nata har ya kama harshenta, cikin ƙwarewa yake Sumbatar ta lokaci Ɗaya yana maida Numfashi sun Ɗauki Tsawon Lokaci kafin ya saketa ya koma kuma ya Kwantar da kanshi Bisa Ƙirjinta yana maida Numfashi Itama jikin gado ta maida kanta tana Sauke Numfashi Cikin Shakewar Murya Tahir yace "Koda irin wannan Hukuncin ne Mufee..?


Ba tayi magana ba illah Runtse ido Datayi wani yanayi na Shigarta Jinsa Acikin Jikinta, bai ɗago ba sai da ya Daidaita kansa kana ya Tashi Lokaci Ɗaya ya Ɗagota Suka miƙe tare Hijabin jikinta ya Cire mata yana Faɗin "Ki saka Rigar barcin Mufee, I need u bazan miki ƙarya ba karki jamin Rai plz.." Ya faɗa yana ƙura mata Lumsassun idanuwansa Da Suka Fara Chanza Launi, Rigar barcin ya Ɗauko ya miƙa mata Shi kuma ya Buɗe Wardrope ya Ɗauki wata jallabiyarsa ya Shiga Toilet saboda ya bata daman Shiryawa, cikin Sauri ko ta kwaɓe tana yi tana kallon kofar Bedroom d'in, Tana ƙoƙarin Saka Hijabi ya Buɗe ƙofa ya Fito da Sauri ya ƙaraso yana Riƙo Hijabin Cikin Wani narkakken kallo yake Faɗin "A'a bana so.."


Ya faɗa yana marairaice Fuska jin haka yasa Jikinta ya Mutu ta sakar mai tana kare Ƙirjinta Tunda pant ta bari kaɗai hatta bra sai da ta cire, Nonuwanta da Suka cika da ruwa sunyi ɓul ɓul dasu Bai tsaya Sauraranta ba ya rungumota ta baya ya saka hannu ya Cire Hannayenta Daga kan Ƙirjinta ya Ɗora nashi Lokaci Ɗaya yaja Numfashi Cikin Shinshinar Wuyanta lokaci Daya kuma yana Shafa Ƙirjinta Zuwa Wuyanta Cikin Lokaci kaɗan ya Rikita kansa kuma ya Rikita ta Domin Mufeeda Haka Ta saki jikinta Sosai Tun Suna Tsaye Har Suka Danganta Da kan gado Cikin Dubara Tahir ya saka hannu ya kashe Wutar Ɗakin ya Kunna Dum light.


Cikin ƙwarewa Yake Sarrafa Mufeeda Ƙirjinta Su sukafi Jan Hankalinsa kuma suke Rikitashi, Itama banƙaro mai ƙirji kawai take tana jin Wani Daɗi na Tsirga mata Har ya Saɓule Rigar barcin bata sani ba kai Tahir ƙarshe ne ya kai makura wajen iya Sarrafa mace, Domin ko'ina na Jikin Mufeeda sai ya amsa Domin babu inda bai bi ya lashe da Harshensa ba Mufeeda ta Haukace sosai Lokacin da Bakin Tahir ya kai ƙasanta Haka ta Riƙe kanshi tana kukan da batasan ko na mene ne ba, Ya gama Rikita ta Shima ya Rikita kansa bata yi Aune ba Taji ya Sunkuyo da kansa yana karanta addu'ar Saduwa da iyali ya haɗe bakinsu Waje Ɗaya, kafin ya Danna kai sai Lokacin Mufeeda ta dawo Hayyacinta jin Azaba na cinta ta Shiga Tureshi amma Ina ta makara domin da ƙarfinsa ya Danna kai cikin magagi Tahir yace "Ya salam..." jinshi Tsundum cikin ƙoramar Daya Daɗe yana mafarki bai tsaya wasa ba ya Shiga Haƙarta cikin Zaucewa da Fitar Hayyaci, Kuka Mufeeda keyi Domin tasha gyara ta koma ta Haɗe duk da Azaban bai kai na Farko ba amma ta Ɗanɗana.


Sai da ya shafe minti Arba'in yana Abu Ɗaya kafin ya ƙanƙameta yana Sakin Numfashi, Haka ya ƙanƙame Mufeeda yana Kwarara mata albarka Tana kuka tana komai ya Ɗauketa suka Shiga Toilet ya gasata kana sukayi wankan Tsarki Suka Fito Domin Tun Mufeeda najin kunyarsa har ta ware Domin karatun Daddyn nata ya Girmi Shekarunta Naɗota yayi Cikin Towel Suka koma Suka kwanta Ya Rungumeta Yana mai Jin Wani farin ciki sosai, Barci Tuni ya sace ta Shima Daga baya barcin ya Tafi dashi mai Daɗi.


*****

Da Asuba ma tare sukayi wanka Mufeeda sai Zille zille take, Shiko ko Ajikinsa, wajen wanka ma sai da ya ƙara morewa son Ranshi kafin suyi wankan Su Fito, Ya barta shi kuma ya saka kaya agurguje zuwa masallaci yau ɗin ko Tsayawa Ma Sauraran Wa'azin da akeyima kullum Safiya bai tsaya ba jiki na rawa ya Dawo gida Mufeeda na cikin bargo ko kaya bata saka ba Tunda bata da kaya a ɗakin ya Sake Ƙwaƙumarta Mufeeda taga ta kanta Domin Duk Kukanta sai Da Tahir ya sake, Sai Da ya samu natsuwa sosai kana ya Rungumeta yana lallashinta ita ko Tana tamai Taɓaran Shagwaɓa Yana biye mata Abun na ƙara Rikitashi, kwanciya sukayi Daga nan kuma sai barci Sai Wajen 9 suka tashi, wannan karon kuwa Mufeeda taga Abun Da ya isheta Cikin Jazucci haka yake lasanta kamar zai Cinyeta Ɗayan Cikin Kunya da Nauyi tace "Kai Daddy..."


Yana wasa da Boobs Dinta da Suka Sake cika Yake fadin "U better stop calling me ur Dad...Ni ba babanki bane.." Cikin Tura baki tace "Kai Babana ne.." Bai bata amsa ba sai da ya Tsotsi bakinta kana yace "Babanki bazai miki irin Abun da nake miki ba.." Ya faɗa yana kashe mata ido Ɗaya ƙirjinsa ta faɗa tana mai Dukan wasa Da ƙyar yayi wankan Tsarki ya fice ya barta bayan ya gama latsata son Ranshi gasa kanta tayi kafin tayi wankan Tsarki ta Fito, Jin Nonuwanta nata Zuba ne yasa ta gane Su Airah sun tashi suna kuka Tahir ta kallah wanda ke murza Hulan kansa tace "Daddy su Airah sun tashi..?


Yana Ɗaure agogon Hannunsa yace "Eh Suna wajen my Farida karki damu muje.." Hijabi tasaka Bayan Towel na Daure Ajikinta Suka Fice Daga Ɗakin, Suna Zuwa Falo suka iske Farida na goye da Airah, Ayman na Hannunta tana ta Faman Jijjigashi yana kuka Tahir ne ya samu daman ƙarasowa gareta ta gaisheshi ya amsa yana karɓan Ayman Cikin Kauda kai Mufeeda ta gaida Farida ta amsa itama bata kalleta ba da Sauri ta Shige ɗakinta Sauri Sauri ta saka wata Riga da Zani na les cikin kayan Tariyar da Tahir yayi mata ne, Ta Fito Zata karɓi Ayman Farida ta Hana tace su Fara karyawa Tukunnah gidan babu kowa Sun Tafi makaranta Harda Naila itama an saka ta Iya ce kaɗai ke Kichen tana Wanke wanke, shi kuma ya kama Hannun Mufeeda suka Nufi Dinning d'in tana ta Zillewa amma Tahir yaƙi sakinta Farida Sau Ɗaya ta kallesu ta juya kanta tana ta Jijjiga Ayman dake Hannunta, Idanuwanta suna Fitar da Ƙwallah domin Daga yanayinsu ta san komai ya sake Faruwa Saurin koran Sheɗan Tayi.


Ko wajen cin Abinci Haka Tahir ya dinga tsokanar Mufeeda ita kuma kunya Duk ya kamata, Farida Data ga Haka sai ta koma sama kawai abunta bata son ganin Abunda zai sa Aga Rauninta, Tana Tafiya Mufeeda ta marairace tana Faɗin "Don Allah Daddy ka bari kaga Momy taji ba Daɗi har ta koma sama.." Shuru yayi kafin yace "Hakane...Bazan ƙara ba Cutie.." Ya faɗa yana lakace mata hanci Dariya tayi Suka Cigaba da cin Abincin nasu cike da ƙauna Lokaci Ɗaya suna aikama juna kallon Soyayyah da ƙauna mara yankewa.


Haka rayuwar gidan Tahir ya cigaba da kasancewa cikin Murna da Farin ciki da Zaman lafiya Abun sai wanda ya gani, duk wacce keda miji zasu haɗu suyi girki tare komai nasu gwanin ban sha'awa Wahalan Renon su Airah kuwa Farida ne da Iya Tsakaninsu da Mufeeda kuwa sai in zata basu Nono Farida na bala'in so wad'annan 'ya'yan gashi ita kuma Haihuwa Shuru Duk da taje Asibiti An buɗe mata bakin Mahaifa amma kuma Har Zuwa Wani Lokaci Shiru sai ta maida Hankalinta wajen Kula da Su Airah kamar ta lashesu Saboda yadda Take bala'in sonsu.


Zamansu gwanin ban sha'awa ko Su Umma suna alfahari da Chanzawar Farida, hakama chan Ɗanbatta Hakimi hankalinsa ya kwanta ganin Walwalar Ɗansa ta Dawo Awajen Aiki kuwa Ishaq sai ma Tahir Tsiya yake wai yaji daɗin Mata sai kiɓa yake yana Tumbi kuma da gaske ne Domin Tahir ya samu kwanciyar Hankali sosai, Duka matan nashi suna ƙoƙarin kyautata mai shima kuma yana ƙoƙarin kwatanta Adalci Baya nuna wanda yafi Wani Afili sai dai ya bar kanshi kawai Ɓangaren Mufeeda kuwa dama Akwai ɓoyayyiyar soyayyar Daddynta Cikin Lokaci ta Fito Dashi, Bata mai gardama komai ya keso shi take mai shiyasa Cikin Lokaci ƙanƙani ta mamaye mai Zuciya, gashi baya gajiya da ita kamar yadda itama bata gajiya dashi Farida kuwa Tana da matsayi sosai amatsayin ta na Uwargida kuma uwar 'ya'yansa Uwa uba kuma Dalilin ta ne Zaman lafiya ya Zauna a gidan Tahir Yanzu Zumuncinsu ya Dawo Sabo da Zahra matar Ishaq, Bilkisu har gida tazo tana Zugata wai ta zama baiwar Mufeeda ta zama mai mata rainon 'ya'ya, nan tayi mata Fata fata ta koreta Ta watsar kuma da duka ƙawayen banza ta riƙe Mufeeda da Zahra kawai domin Samun Sukunin Zuciya Tana ƙoƙarin Ɓoye Kishinta Saboda Tahir na kwatanta Adalci a tsakaninsu...


*******


*AFTER 5 YEARS*


Bayan Shekara Biyar Abubuwa Da dama sun Faru na Farin ciki da Akasinsa amma Aciki na Farin cikin yafi yawa Domin A shekarar Data gabata ne Iyalan Tahir suka tattara suka koma Lagos a Victoria Island, Inda ya gina wani katafaren gida Haɗe da katafaren Kamfani mai Taken *ƊANBATTA MOTORS LIMITED* da guminsa, Bayan ya barma Ishaq wanchan kamafanin na Abba a Kaduna yana kula Dashi, saboda amanarsa da Hazaƙarsa Duk da Dukkansu Cigaba ne ya Samesu amma Sunyi baƙin cikin Rabuwa da Juna.


A waɗannan Shekarun Tahir ya ƙara zama magidanci domin Arziki yaci uban nada, Baga iyalansa kaɗai ba Hatta ga iyayensa ma suna yabansa, Garinsa ko Ɗanbatta basu da abun alfahari sama dashi, yana ƙoƙarin Biya musu Buƙatunsu, ya gina musu Rijiyoyi da kuma Bohol, hadda k'aramin Asibiti ya gina musu mai suna MANSUR CLINIC, Abun sai wanda ya gani Ashe kuwa Yanzu ta zama Hajiya Aisha Tuni Tahir yayi ma Mijinta hanya ya samu aiki a kamfanin Abba Dake Kaduna in da ya bari suna aiki tate da Ishaq, Sun bar garin Ɗanbatta Tuni suka koma Kaduna da zama, Baba Hakimi babu Abunda ke Shiga Tskaninsa da Tahir sai godiya da Fatan Alheri, haka su goggo Komai na Jin Daɗin Rayuwa ya mallaka musu, Duk Da Baba Hakimi ya Tsufa amma yana gudanar da Sha'anin mulkinsa Domin ya Jiƙu da Hutu da Jin Daɗi Tuni Tahir ya maida Garzali makaranta yana Ɗaukan Nauyin karatunsa, Rayuwa tayi kyau Abun sai wanda ya gani.



Su Airah nada wata goma sha Biyar Mufeeda ta sake samun Wani Cikin Farida ta karɓi su Airah ta yayesu ita kuma Mufeeda ta cigaba da kula da rainon cikinta, Lokacin har ta yi Jsce ta koma Makaranta,Sai da cikin ta ya Tsufa kana ta daina Zuwa Makaranta lokacin tana Ss2 ne Achan ko garin Ɗanbatta kowa Ɗauka yake cikin jikin Mufeeda Shine na Farko su Airah kuma Farida Ta Haifesu Tunda ba wanda ya sani sai su kansu da komai ya Faru suna nan, Hajiya Iya kuwa 'yan'uwanta sun so su Ɗauketa amma Tahir ya hana yace Ai Iya Ta Riga ta zama tamu Dole suka yi Haƙuri Suka ƙyaleta.


Na ƙara Haihuwan mace Ta ci Sunan Goggo Abu muna kiranta Ayda, tana da Wata Takwas na ƙara Samun wani cikin wanda nayi ta kuka Farida ko da Tahir nata Murna ta karɓi Ayda ta yayeta Lokacin su Airah suna Ɗanbatta wajen Innaro, cikina na wata Bakwai suka Tafi Aikin Hajji Dukkansu, Goggo Abu, Innaro Ashe, Iya, Tahir, Ishaq, Zahra, Farida, sai Abba da Umma da Baba Hakimi, Ashe da Mijinta da su Basma.

Ni Kaɗai kawai aka bari agida sai Maman Lantana ita ta Zauna dani har Suka Dawo Wacce nake Kallo tamkar mahaifiyata Lantana ma tana Kano abunta muna waya sosai itama, ta cigaba da karatu, Lokacin da suka Dawo Cikina yayi girma kwana goma da dawowarsu na Haifi Santalelen yarona Namiji wanda yaci sunan mahaifina muna kiransa Walid, Duka 'ya'yana Ba zaka ce ni na Haifesu ba Domin komai nasu yana Ɗakin Farida ne, itace uwarsu, Tsakani na Dasu Aunty Mufeeda ne kaɗai, in ka kalleni bazakace nine keda 'ya'ya Har Huɗu ba saboda yanayin Jikina, Bayan na Haihu da wata uku Ciki ya Ɓulla a jikin Farida Murnan da mukayi ba kama Hannun yaro bamu tafi Hajji ba Nida Tahir sai da mukayi Jarabawar WAEC da NECO lokacin Walid nada wata goma Sha Uku Na yayeshi na Damkama Farida da Iya, Bamu samu Tafiya ba sai da mukayi Walimar Buɗe kamfanin Tahir da kuma Tariyarmu Asabon Gidanmu kana Muka Tafi Ni dashi, kwananmu Talatin agarin Makka muka Wuce England, Mukayi kwana goma, sai muka Dira a India saboda nacema Tahir ina son garin mune Har America munsha yawo, Honey Moon da bamuyi abaya ba muke Ramawashi yanzu, Sai da muka Shafe wata biyu da wani Abu kana muka dawo Gida, koda na Dawo na kwaso Tsaraban Honey Moon, Munyi kiɓa munyi jajir alamun munsha Hutu Sosai Farida da yaran sukaje Filin Jirgi Suka Ɗauko mu Lokacin Cikinta Har ya Fito, Duka duka kwanan mu goma ne da Dawowa Duka yaran da Suka Tattara suka Tafi Ɗanbatta Hutu suda Iya da Maman Lantana, Su kuma Basma da Bassam Dama Suna chan Tun bayan Tafiyarmu Farida kuma ta tafi Kano Duba jikin Abba Nida Tahir kaɗai suka bari agida naso na Bita Amma Laulayin Ciki ya Hanani Sukuni Dole na Zauna agida.

 

Tun muna India na Nuna ma Daaddy ina son na Cigaba da karatu na, nan ko ya nuna bai yarda ba kuma bazai taba yarda ba ya tambayeni a faɗin Duniya mai na rasa nace mai babu yace toh matuƙar ban rasa komai na Duniya ba maganar karatu na barta Karatuna kenan na Zauna na kula da mijina Haɗe da 'ya'yana Lokacin Kuma ina Cigaba da Zazzage mai kwansa A duniya.


Maganar gaskiya ban Rasa komai na Duniya ba, Ilimin nan dai-dai gwargwado ina dashi waye wa ma Haka domin yanzu na zama babbar mace babu Abunda wata macen zata Nuna min game da Namiji Daddy ya riga ya gama Zama malami na kuma bango na Shi ɗin da gaske garkuwa ne agareni bai taɓa bari nayi kukan maraici ba ko sau ɗaya Koda yaushe Cikin bani kulawa yake, Yana tattalina kowani Jin Dadin na Duniya yana bani ni kuwa mai Zan je na Tsinta in na cigaba da karatun mijina na sona, iyayensa naji dani kamar su lashe ni ina da 'ya'ya Me zan nema nan Duniya wanda Allah bai bani ba..? Babu domin Bayan Iyayena da suka kawoni Duniya Bani da kamar Daddy shine Mijina, kuma bango na kana kuma Shi ɗin wata Garkuwa ne agareni.



*****


Ina Zaune Ina Sauke Numfashi Bisa makeken gadonmu Tahir Dake kwance cikin blanket na Mintsina ina Sakin Kukan Shagwaɓa Cikin barci ya Buɗe ido yana kallona Hankalinsa tashe ya Miƙe yana Faɗin "Cutie wai lafiya kike ta ƙananun kuka Tun Ɗazu..?


Ya faɗa idanuwansa da barci, Kan Jikinsa na Sulale ina Faɗin "Toh ba cikin ka bane ke Wahalar dani ba...Komai naci baya zama sai na amayar dashi.." Murmushi ya saki yana gyara min kwanciya Lokaci Ɗaya yana wasa da gashin kaina yace "Umh..Wato na gane so kike kawai Dai na Taɓaki ko..? Ya faɗa yana Kallonta Kwaɓe Fuska tayi kafin tace "Ni..Yaushe nace kai dai Daddy kace zaka min wayau da ka saba.." Bata ankara ba taji ya maidata ƙasanshi yana Faɗin "Ni Wlh ke kemin wayau koda yaushe cikin amshe min Kuzarina kike, ke ɗin fa da ba domin ina ƙarawa da maganin ƙarfin maza ba da Tuni kinfi ƙarfina.." Ya faɗa yana mata Dariya baki ta Buɗe Tana Kallonsa Lokaci Ɗaya ta fara Tureshi tana sakin mai kukan Shagwaɓa Shi kuma yana dariya Lokaci Ɗaya ya Kama bakinta yana Faɗin "Muyi aikin lada Cutie bayan mun gama nayi lallashin Gaba ɗaya.." Ya faɗa yana haɗe bakinsu waje Ɗaya, cikin Sauri itama ta tallabi kanshi, Suka Fara Sumbatar juna cikin ƙwarewa Lokaci Ɗaya suna ƙara Rikita juna da Salon da kowanne yasan yana Kunno Ɗan'uwanshi Sai da Suka Ɗauki Tsawon Lokaci kafin Tahir ya saki bakinta yana kallon Cikin idanuwanta yace "Cutie ina Sonki...Ina ƙaunarki ƙaddarar Data Haɗamu ta Alheri ce..Allah yayi miki albarka.." Ya faɗa cikin Sanyin Murna Rungumeshi tayi tana Faɗin "Alhamdulillah...Kai ne garkuwata..Mijina Abun alfaharina..Ina matuƙar Sonka..."


Ta faɗa Lokaci Ɗaya tana Haɗe bakinsu Waje Ɗaya, Cikin Zalama kowannensu ke aikama da Ɗan'uwansa Saƙo.


          

        *ƘARSHE...*



*ALHAMDULILLAH...*


*Tammat bihamdullah...godiyata ta tabbata ga Allah ( SWA) Wanda yabamu ikon Fara wannan Littafin kuma ya bamu ikon gamawa lafiya..Muna fatan Kuskuran da mukayi Allah ya yafe mana...Laadan da muka samu Allah yayi ma Tarraya damu daku waɗanda sukayi ta jimirin bin wannan labarin Ameen.*


```Godiya ta mussaman ga Groups din da sukayi Jimarin Binmu Tun daga Farko Har Zuwa ƙarshe basu gajiya da Sharhi koda yaushe kamar su JANAF NOVELL 1&2,,AISHA ALTO NOVELS,TASKAR LITTAFAN HAUSA,NANNY CANSERVATION ROOM,NANY FANS GROUP,MARYAM NOVELS,ZAUREN JANAFTY,MASAURATAR SHAKIRA JANAFTY,ZAUREN KHADIJA CANDY,INTELLIGENT FANS,1&2,ZAUREN SAINA,FEEDHOM NOVELL, BENEFICIAL WRITER'S, MASOYAN SHALELE, Da duka Sauran groups d'in da bamu ambata ba Muna godiya gareku masoyanmu Wanda muka sani da wanda bamu sani ba Muna godiya Sosai Allah yabar Zumunci our wattpadians Fans ɗinmu kuma muna godiya sosai Da Soyayyarku muna ganin Vote ɗinku da Shairhinku Muna godiya Love u all....Allah ya bar Zumunci...One luv```



_Albishirinku Masoyanmu Muna tafe muku da wani albishir na Sabbin *SANYAYA BIYU* wanda zasu zo muku Daga Alƙaluman Tagwayen marubutanku ɗin nan Guda Biyu, Wato *MR BELLO...* na Jamila umar Janafty, wacce ta Daɗe tana Nishaɗantar da ku cikin Zafafan Littafanta, masu matuƙar Daɗi da Faɗakarwar, Kunsanta kuma ta sanku, kun gwada kuma kun gani ku zaku ba wasu labari, Labari ne mai cike da Cin Amana, Tausayi,da mugunta, haɗe da Soyayyah mai Zafi mai tsayawa azuciyar masoya, Domin kasancewa cikin Waɗanda zasu ci karo da wadanan Abubuwan zaku Biya kuɗin karatu akan Naira ₦300 kachal domin more karatunku cikin kwanciyar Hankali da Aminci._

_Itama Ɗayar gwanar taku Wato Aisha Alto itama tana tafe muku da Nata salon mai taken *MATAR NASEER...* ku Daga jin sunan kunsan namu ba irin nasu bane labari ne mai Shiga Zuciyar mai karatu yadda mata ke Shanye Takaichin ɗa namiji, gori da kuma Soyayyah mai Tsuma Zuciya Duk zaku samesu ne kan Farashi mai Sauƙi ₦300 kachal babu Tsada mai buƙatar guda biyun kuma Zai biya ₦500, zamu yi muku VIP shima wanda ke Buƙatar ƙarin bayani Zai iya Tuntuɓarmu ta lambobin wayar da zamu bada...Ina kuke masoyanmu ku Hanzarta, ku yunƙuro wajen Nuna mana naku salon Soyayyar wajen Siyan Sabbin Novels ɗinmu Mun san bazaku bamu kunya ba...Kar ku manta koda kuɗinka sai da Rabonka..._



Domin neman ƙarin bayani ko ƙorafi ko gyara Za'a iya Tuntuɓarmu ta waɗannan Nombobin wayar kamar Haka👇


09069067488

08147672049


*Saƙo mai amfani...Banda kiran Waya...*


*Anitha..*

*Aisha Alto*



Post a Comment

0 Comments