Mahaukaci ko boyayyen masoyi hausa novels cmplt

 [11/03 11:44 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-1

        BY

MARYAM YARMAMA

*DEDICATED TO*

 MY FANS


_INTRODUCTION_

this is a interesting story that teach us more moral lesson about life,this,story has came with so many life styles and aloof our life leaving,i believe this long story will entertain readers



*APOLOGY*

AM SO SORRY MY FOLLIWERS I CANT CONTINUE ,THE STORY *CAPTAIN SHAYEEDA BUT I WISH ONE DAY I WILL CONTINUED,I NEED UR PRAYER


*starring*

Adorable minal

Stubborn gal aziza

Hansome guy annur

Play boy safwan

Ummi

Saudat

Hasiya

AND OTHERS..........



*VOTE OF THANKS*

zahrah bukar

Asykhaleel

Salma ali wada

Halal dady gal

Hauwa mamee

Maman hafsy(hajara)

Lubna(lalata writter)

Miss xoxo

Raz

Aisha gana

Pretty minnah

And others friends




*KANO CITY*

Kuka minal ta saki sakamakon mafarkin datayi na mahaukacin masoyi,kuka tafara tana wai yaushe zanga mahaukacin masoyina iye,mahaukacin masoyi ka nunamin kanka,meyasa kake firgitani a mafarki,wlh ina matukar kaunarka.


Aziza dake faman sharar baci tasha tsaki tace nifa minal kina damuna,da wannan banzan mafarkinki,haba dan Allah akanki akafara soyayya mutunmin ma dabaki taba ganiba amafarki kila ganshi,dan Allah kiyi mana shiru ko kuma inje inkira umma




Rufe baki minal tayi tana kuka mai tsuma zuciya tace yar uwata bazaki gane son danakewa mahaukacin masoyinnan bane,wallahi inna hadu dashi agaske wallahi kinji na rantse da Allah ko ya yake saina auresa




Razane ido aziza tayi tace yar uwa kina da hankali kuwa lalle kuwa zaki dakko ruwan dafa kanki ba kadan ba iye lalle ma,kinga kwanciyata saida safe


Minal ta doshi hanyar waje ta dauki ruwa a buta tadauki buta tayi alwala tazo tafara nafilfila tana rokan Allah ya bayyana mata mahaukacin masoyinta,




;::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::

Washe gari,gidansu minal ko sanwar abinci babu,auta da yake bata jurw yunwa yarinyar shekara hudu,sai kuka take tana,wayyo cikina,zan mutu yunwa nakeji


Minal uwar tausayi ta fashe da kuka,ta kalli umma datayi tagumi tace umma yazamuyi ne,nifa nafi tausayin auta,kuma kinga tanada sickler karya tashi wlh ina tsoro




Umma cikin taurin zuciya tace to minsl yakikeson inyi mukune,saidai inzakije gidansu hasiya wajen baffa ki tambayo mana kudin gadonmu,insinki subada sai mu barsu da Allah



Hawaye yafara kwaranya a idonuwan aziza tace a a umma abarsu kawai,neye gado,mutum ma yana mutuwa yaba barin gado balle gado,ai kayan duniya na shedanne?a tsirara mukazo a tsirara zamu koma meye zai damemu,Allah zai sakamana kawai abar maganar gadonnan



Idon autane ya fara kakkafewa da sandarewa.


Minal ta rungumo auta tana ihun auta auta karkiyimin haka,umma mutafi asibiti,




Saka hijjabi minal tayi ta fita dagudu kan titi yana rungume da suta da numfashinta yake sama sama,


Su umma ne suka rufa mata baya


Adaidaitasau suka tara suka shiga,nasarawa hospital suka nufa,sunashiga aka karbi auta aka shiga dakin emergency da ita.




Likitane ya kira minal yana lashe baki,umma zata bishi yace a a umma ita kadai nace zatayi signing a office dina



Aziza tace anya umma likitannan akwai Allah a lamarinsa ,daga ganinsa dan iskane




Umma tace kul kidaina fadin zarcenan,ai Allah yana tare damu





Minal tsayawa tayi acikin office din,




Kanne ido likitan yayi yace baiwar Allah kizauna mana 



A tsorace minal ta zauna,tana kallon kyakyawan likitan,matashi tace ina 

...kwana




Murmushi yamata lfy matsowa kusa da ita yayi har suna iya gogon juna,minal a tsorace tace pls kaban takardan dazanyi signing mana




Lashe lebe ya tashi kamar zaije ya dakko takardan ,bayan minal yabi ya dafata,




Kuka tafara rusawa tana dan Allah likita banson irin wannan kuda aka sanku da taimakon al,umma 



Kokarin sa bakinsa yake abakin minal,yana zura hannu a hijjabinta,kuka minal tasa;tayi iya karfinta ta hankadasa gefe,tafita da gudu





Karo sukaci da aziza,da take faman sharbar kuka tace kema minal yanaga kina kuka likitan ya gaya miki auta ta rigamu gidan gaskiyane?




Cikin mamaki,minal ta kalli aziza tace da gaske,auta ta ta tafi,


Aziza tace tabbas ta mutu saidai hakuri,yanzuma gawarta zamu dauka mu koma dashi




Kukan zuci minal take tana mudai haka rayuwarmu zai kasance ina umma




Jawo hannunta aziza tayi tace tana dakin da gawar auta take,bata wani tashi hankalintaba,Allah ne ya daukewa auta karshen wahalarta naciwon sickler dinnan





Minal kukanta yafito fili dataga wannan likitan kamar mutumin kirki yanata bawa umma baki,

Mamaki ya cika minsl to tawani kofa yashigo,har ya iso dakinnan





Yana  ganin su minal ya kallesu da alaman tausayi a fuskarsa yace sannu yanmata sai hakuri,zaro dubu goma yayi yabasu yace gashi wannan asiya abin sadaka.


Aziza uwar son kudi ta kawo hannu da niyar ansa,minal ta amshe ta watsawa likitan kudin a fuskarsa tace munafukin Allah bama bukatar kudinka,meyasa tun wuri baku taimaki rayuwar yan uwataba sai yanzu zaka taimakemu



Ji tayi an bata mari tas,batason lokacin da ajijiya ya kamataba tafada jikin likitan da tafi tsana aduniya



Taku kulllum

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*02

By

Maryam yarmama

Dedicated to

All my fans




_wannan shafin nakine *aunty yar mitsila* saboda kaunar da kikewa littafina,kina karamin karfin gwiwa,you are in tha part of my heart,i wish you more happiness and beautiful life and age_






Umma ce cikin kunar rai tace ke tsabar ke shedan ce anmana kyauta kinki ansa,to kisani gidanmu bada halinnan muka tashiba,har Mahaifinki ya koma ga mahallacinsa kullum mutane kyakyawar sheda akemai,




Tashi minal tayi ta durkusa agaban umma tace umma ki share hawayenki indai akaina ne bazaki sake kukaba,zakiyi alfahari dani,zanyu biyayya agareki har karshen rayuwata,ta kalli likita tace kayi hakuri mungode da kyautar da kamana



Likita safwan nan yaji yarinyar kaunarta ya kara dilmuwa azuciyarshi yaji gaskiya bazai iya rabuwa da itaba,yace bakomai muje insa a saukeku agida



Umma tace haba dannan kai da wahala haka ashe kanada kirki haka,

Minal azuciyarta tace,tab umma dakinsan me yake shirin yiminba





Haka suka fito daga asibitin suna kuka,safwan ya bude musu bayan haddaden motarsa,umma da aziza suka shiga,har minal zata shiga umma tace a a minal kishiga gaba,mana,nan yayi kadan kuma ga gawar auta


Minal tanajin an ambaci gawar auta ta rushe da kuka tana ashe dagaske auta ta mutu



Safwan ya kalleta da idonsa mai narkar da yanmata yace yanmata kishiga mana sai hakuri wanda ya mutu ya riga yamutu,sai hakuri



Takasan ido,minal ta gallamai harara tace ina ruwanka da kuka,kallon kafanta tayi sai yanzu ta lura kafarta ba takalmi,buzu buzu yake,kunyane yakamata tashiga motar shima safwan yashiga yana tukawa a sannu a hankali,yana satar,kallon kyakyawar fuskar minal daya rine da hawaye


Jin kukanta yake har ransa,amma ba yanda zaiyi yahanata



Minal kallon titi take,gano wani kyakyawan mahaukacin masoyin datake  mafarki tagani,gashinsa yayi luf luf kamar ns indi,a ga idonsa dara dara,yana dauke da faffadar kirji,dogo;fari kal dashi,ga hanci har baka,amma kash daga ganinsa bashi da hankali,kai duk inda ake neman namiji,in aka cire safwan to mahaukacin masoyi yakai,domin  safwan ba baya bane awajen kyauba.



Kara minal tasa tace likita ka tsaya ka tsaya dan Allah,naga wani abun dana dade ina muradi da nema



Cin burki safwan yayi,da gudu minal ta bude murfin mota,ta duba hagu da dama sama da kasa bataga abin sontaba,hawayene ya fara shatata a idonta,ta dawo cikin mota jiki asanyaye


Umma dake bayan mota takalli aziza tace wai meye minal ta tsayar da motane?


Aziza tace oho ita zataki tambaya,don inaga minal takusa zaucewa

Umma tace Allah ya kyauta



;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;,;;;;,,,;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;




A kofar gidansu minal likita safwan ya tsayar da motarsa,yana kallon rubabben gidansu cikin tausayawa da jimami,duk gidan ne yafi kowa muni a layin gabaki daya,



Bude musu motar yayi,ummi suka gani atsaye a kofar kyakyawan gidansu,tana ganinsu ta fara murmushin jin dadin ganinsu minal ta taho,ta dafa minal tace besty nashiga gidanku naga shiru lfy




Fashewa da kuka minal tayi,ta fara nunawa ummi gawar auta tana ihu da kukan auta ta mutu auta tabarmu aduniyar nan mai cike da wahala da kuncin rayuwa


Salati da ihu ummi ta zunduma ta nufi wajen umma dake rike da gawan auta,jijjiga auta take tana auta auta abokiyar kowa,auta akwai ki dashiga rai meyasa kika barmu innalillahi wa,innahilaihi raji,un


Makotane sukafara fitowa wasu nakukan rashin auta,wanda duk cikin yayan umma tafi shiga rai,da son wasa,kowa natane



Haka akafara zaman makoki


Umma da takejan chasbahana tacewa aziza taje gidansu abba ta gayamai rasuwarnan tunda yanzu shine uba,


Safwan sai hidima yake,komai shi yayi agidan mutuwarnan



Can anjima saiga aziza tashigo gidan da kuka tafada jikin umma tace umms wallahi ba Allah a zuciyar abbansu hasiya,haka yace bashi ya kashetaba balle yaxo,indai don abin sadakane wai saidai mu mutu bamuyi sadakarba,wai ahaka zamh kare ba rayuwar kwanciyar hankali



Yan gidan mutuwa suka fara jimami suna ta Allah ba tasaba saidaishi ya mutu badai kuba




Haka aka share zaman makoki ,komai safwan ne yakeyi,ya canja kamannin gidansu umma,an mai gini mai kyau,ya zuba kujeru da fridge,da t.v da jennareto,yacika store da abinci da komai.


Umma sai shimai albarka take,minal ko ajikinta ta tsani safwan,itadai burinta ta karacin karo da mahaukacin masoyinta



Abbane kanin babansu ya tako gidan ranar yazo da rashin mutuncinsa,yaga gida yayi kyau,nan ranshi ya sosu yace lallema matar nan,tafara tura yayanta duniyar karuwanci kenan




Shiga gidan yayi ba sallama,ga gidan an chanja shi harda tyles,wani uwar ashar ya dura yace ke karya ina kike kifito 


Aziza dake goge tyles da mopping stick tace karka kara cewa uwata karya saidai na tsayanne bakin  kare



Nufota yayi yace wallahi zanga uban daya tsaya miki agidannan kike cemin kare,


Aziza ta dankaramai harara tace to tsohan najadu inajiranka 



Minal dake girki a kitchen tafito ta durkusa har kasa tace abba ina wuni



Abba yace ban wuniba munafuka yar iska,karere



Dafe kirji minal tayi tace abba nagode,ta kalli aziza tace haba yar uwa yakikeson karya umarnin mahaifiyarmu kinsan tashiga,gidan hajiya tace duk wanda yazo ya takelemu da fada karmu biye masa,pls ki daure kibi umarninta




Aziza tace to shikenan taci gaba da aikinta,minal takoma kitchen tanata girki




Abba sai zage zage yake,dayaga bawanda ya kulasa,yayi tafiyarsa

By

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: _PERFECT WRITTER FORUM_(P.W.F)

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*

BY

MARYAM YARMAMA

*DEDICATED TO*

MY FANS




*WANNAN SHAFIN NAKINE MAMAN HAFSAT,INA FATAN ZUMUNCINMU ZAI DORE HAR ABADA,KINA RAINA*






bayan kwana biyu umma ta aiki minal zuwa gidansu,abba ta karbo mata ankon bikin hasiya


Hijjabi ya wuce gwiwa minal tasa,tana cike da farin ciki yau,tayi mafarki tayi zata hadu da mahaukacin masoyinta mai kaunarta




Ta tsantsara kwalya dama gata chocolate colour ga hanci har baka ,ga ido ,tayi masifar kyau,minal nada hakuri,gason karatu,da saukin kai,batta da surutu so silent zaka ganta,



Tafiya take a sannu a hankali,kamar tana tausayin taka kasa,ji tayi an rike mata hijjabi ta baya,faduwar gabanta ya tsananta



Wani murya mai uban dadi taji abayanta yana anty ki gaya musu su daina tsokanata sunacemin mahaukaci


A hankali ta juy karo taci da wanda take muradi wanda koda yaushe yana manne a birnin zuciyarta,ya kara kyau dahaske,rufe ido tayi tanajin sansayar iska yana kadawa sonsa nakara narkuwa azuciyarta



Firgigit ta farka daga dogan tunanin da take sakamakon jin ya kara ambatar anty ki gayamusu su daina tsokanata



Kallon gefensa tayi,yarane sunfi ishirin sun tsaya suna kallonsa,dayan yaronne yace kash gaka kyakyawa amma ba hankali



Tabule fuska yayi yace anty ki gayamusu ni wlh




Minal ta kyalesa cikin sanyin murya tace,to ka sakeni zan gaya musu ,kallon yaran tayi tace haba kukuwa idan yayankune kodan uwanku ya ke da wannan laluran yazakuji iye?



Jikinsu yayi sanyi a hankali suka fara watsewa suna barin wajrn



Kallonta yayi yace aunty nagode zaki aureni,ki dinga korar min yaran



Dariya minal tayi tace hmmmm mai kyau ya sunanka?


Cikin alamun jin kunya yace sunana annur sunana aunty kiyi alkawari zaki aureni muryarki da dadi



Minal tace,a-a ni  kadaina cemin aunty minal sunana ba auntyba ai zan aureka in Allah ya yarda




Ihu gami da tsallen murna yayi yace wooo aunty nagode dafatan zaki dingamin wanka kisamin pampers





Kunyane ya rufe minal tace kaga sai anjima ma hadu kasan gidanmu nan bayan layi kazo ka dinga karban abinci



Murna annur ya fara yafece aguje.




Jikin shaukin kauna minal takallesa tana in Allah ya yarda sai na auri annur na maidasa mutum kamar kowa



Tafiya taci gaba dayi abba ta tadda a kofar haraban gidansu maikyau yana ganinta tundaga nesa ya fara  yar maula ki koma ai yau ba jumma,a ba





*pls my fans am so sorry ,this is a short page ,am so sorry,am studying*



By

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: _PERFECT WRITTER FORUM_


*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-4

By

Maryam yarmama

Dedicated to

All my fans





Kunya ta kama minal,domin akwai dandozon mutane awajen,



A sannu a hankali ta iso wajen abba ta durkusa tace abba ina wuni,abba yace ban wuniba yar mace meya kawoki gidanmu?

Minal tace dama munji haseeyace zata yi aure,abba ya amshe zancen shine kikazo ki rusa ko to ta Allah batakuba,minal tace aa anko nazo amsar mana naga bikin saura sati biyu,washe baki abba yayi yace ai bama kusaniba mai kudi sosai zata aura,anya zaku iya siyan ankon don ankon kala biyar ne?


Minal tace in Allah yayarda ko kala dayane zamuyi,bari inshiga ciki



T

Tashi tayi abba nata yada mata bakakken maganganu.



Shiga ciki tayi tana kallon gidansu nada wanda aka kwace musu karfi da yaji lokacin da abbansu ya mutu,hawayene ya subuto mata amma tayi saurin gogewa



Su haseeya da luba suna zaune da kawayensu a harabar tsakar gidan suna cin kaza a plate



Suna ganin minal kowacce ta hade rai daga,dariyar dasuke



Minal tace sannunku


A yacine luba tace yauwa ya akabar tsohuwar yar bariki



Minal tayi murmushin takaici tace hmmm ,ta kawar da zancen da cewa hasiya Allah ya sanya alkhairi Allah ya doramu a danshinku


Rangada buda sukayi luba. a amshe zancen tace ai Allah bazai taba doraku a danshinmu ba ,ahaka zaku kare kuna rayuwar kunci da bin maza



Minal tace kema binta kinsan  da azizace tazo nan saikunyi dambe,ni Allah ya doramin hakuri dayawa kullum burina muja juna ajiki



Haseeya ta kalli dayar kawarta datasha bleeching tace kinga wannan mabaraciyar metake fada,wayake tsoran azizar,ai suk ruwan bala,in aziza bata kainiba,kidai shiga ciki kar a mana halin bera mama tana ciki




Minal jikinta tayi sanyi lukus,tashiga kofar dazai sadata ga falo,


.shiga tayi mamace a falon ta dora kafa daya kan daya,ga katon naman kaza a filet,


Hadiyar miyau minal tayi ,tace ina wuni mama,



Tsawa mama ta dakamata,firgita minal tayi ta rakube agefe,mace tace to diyar mayu maiya kawoki gidanann

Minal tace dama mama nazo ansar ankon haseeya ne



Mama tadan saki murmushi,don duk maison bikin hasiya bakaramin dady takejiba ,tace ok Allah yasa zaku iya anko din, bari in dakko miki,kima daina tunanin zantafi in bar kazata,don dashi zan shiga ciki,bazanma  nuns muku lefenba,karkuje ku nuna halin bera.




Shiru minal tayi,mama tashiga ciki

Idon minal ta sauka akan wani jaka mai kyau rataye a falon,ahankali tatashi ta dauki jakar,tana budewa abinda taci karo dashi yasata razana,sarkan gwal din da agogon gwal din da lokacin da babansu yake darai ya siyawa ummansu a dubai ta gani



Daukewa tayi ta aje jakar a inda yake ta sa sarkar da agogon a cikin rigarta ,faduwar gabanta ya tsananta,sai ta tuna lokacin da babansu ya mutu yana rashin lfy umma ta nemi sarkar da agogon ta rasa,abinda aka siya kimamin,miliyan biyu,shine su mama suka sace



Mamace tafito da kyallen ankon ahannunta,saida ta karewa falon kallo taga komai daidai yake,sannan ta wurgawa minal ankon tace kussan bikin saura sati biyj don haka ana saura sati daya zakuzo saboda akwai ayuka diyawa ,sora kuki zuwa wlh saina muku rashin mutunci



Minal tace in Allah yayarda zamuzo Allah ya kaimu lokaci sai anjima

Ko bata amsa mama batayiba taci gaba dacin namana


Tashin da minal zata tashi sarkan ya fado,mama bata luraba ,minal ta wullar da yadin tayi kamar kyallen ne yafadi ta dauka ,tayi hanyar waje


.su hasiya suna ganota suka kwashe da dariya suna ihun inna ta gaida assha




Minal fita tayi tana tafiya taga motar safwan ya tsaya,zuge glass yayi ya fito yace gimbiya sarautar mata


Minal ta hade rai



Safwan yace nidai saidai duk abinda namiki ki yafemin,don gobe zan tafi kasar england karo karatun shekara hudu,gashi iyayena ba,anan suke ba balle kisansu



Minal taji ba dadi ,duk tsanar da takewa safwan taji yabata tausayi ,shirrin kuka tafara tace yanzu bazakuje kuyi bankwana da ummaba



Safwan yace a a saura hour biyu ,girgin mu yadaga,but tunda na ganki ga sako ku bawa su umma,miko mata leda yayi mai nauyi,da wani envelope



Safwan yace wallahi minal i will miss you,wayarsa ta dakko tana tamata hoto


Kuka minal tafara tana tunanin wannan shine haduwarsu ta karshe



Safwan shima yaji hawaye ya tahomai,yace karki soma ki daina kuka nidai ki jirani,zakiga wasika daya naki daya na umma



Shiga mota yayi yana daga mata hannu


Minal ta kara fashewa da kuka,safwan ma dake mota shima yakara kukansa kamar yafasa tafiyarnan,tunda ya fuskanci minal ta fara kaunarsa




Minal barin wajen tayi,tayi hanyar gida tana shiga ta fara zubar da hawaye safwan ya musu hallaci sosai,sai yanzu take missing din muryarsa da kalamansa da kamahin turarensa da  kyawun fuskarsa



Aziza ce tafito daga daki,daga ita sai best da ta dora zani da alamu daga bacci ta tashi,ta kalli minal datayi tagumi ta kuka ga katon leda ahannnta,tace yar uwa badai wayannnan yan iskan bane suka tabamin ke




Kara rushewa da kuka minal tayi ta labartawa azixa labarin safwan


Zama turus aziza tayi jikinta yayi sanyi lukus;shikenan wahalarsu ya dawo,tunda gatansu ya  f

Tafi


Minal ta kalli aziza tace a a Allah zai kawi mana chanjin rayuwa  tunda naga sarkan gold din umma da ta dade tana nema.

*labari yanzu aka soma karku damu da gajertar page,labarin tanada tsaho*

Da yanma zancigaba


By

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: _PERFECT WRITTER FORUM_

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-5

By

Maryam yarmama

Dedicated to my fans





Ihun murna aziza tasaki,umma data fito daga bayi,itama butar dake hannunta ya subuce ya fadi tace dagaske kinga tsarkan dana dade ina nema iye



Minal ta kwashe labari tabawa umma,murna umma tafara tana godiya ga Allah,haka rami sukayi auka binne sarkar 



Bude ledar safwan sukayi,makudan kudine aciki zasukai dubu dari biyar,ga katon hotansa mai kyau wanda yayi elajiment tafkeke


Sai wasiku biyu masu kyau suka fado,minal ta dauki wanda taga ansa sunanta radau ra fara karantawa kamar haka;



_assalam hasken annuriyata_


_minal ina kaunarki kaunar da banawa kaina,tunda na seta idona akanki naji ina kaunarki,minal ki rikemin alkawari ko badade ko ba jimawa zan dawo gareki muyi aure,inaso ki fara karatu mai nisa ,ki daukar min alkawari bazaki gujeniba_


_zanyi kukan. Rashinki,i love you minal_

_by_

Safwan hamza sadauki




Tsaki minal tayi ta faki idonsu ummata yaga  wasikar



Azizace tafara karanta letter umma kamar haka


_assalam ya ummata,dafatan kina lfy,kiyi hakuri tafiyata tazo ba tsammani,pls ga amanar minal ki rikemin zan dawo in aureta,ki rike alkawari umma ina kaunar minal,zan dawp gareta nan daba jimawaba_

By

Safwan hamza sadauki



Umma tace hmmm Allah ya bamu damar rike alkawari



Kwafa minal tayi ta shige daki tana gunguni




Ba,a  jimaba sukaga abba yashigo gidan shida wasu kartin maza hudu 



Umma dake zaune tana karanta al,qur,an ta rufe kur,anin ta aje acan nesa takalli abba tace baban yara lfy badai minal taje ta muku wani abunba



Cikin masifa abba yace yimin shiru munafuka kawai karuwa



Azizace tafito daga kichen hannunta rike da chokali ta kalli abba tace karka kara cewa uwata karuwa


Baffa ya nufi wajrn minal dake buya a bayan umma ya damko gashinta iya karfinsa,ya gwarata da bango ji kake jini yana shatata a goshinta



Yace dan ubanki ina tsarkar gold din da kikaje gidana kika dauka iye?



Zafi da radadin fashewar goshi yasa minal tace abba kayi hakuri ban daukaba



Umma tazo ansar minal,cikin zafin nama abba ya daddage ya wankawa umma mari,umma ta kife akasa tana kukan zuci



Aziza ta fusata tana zuwa wajen ta kwadawa abba chokalin akai,ihu abba yasa yace lalle yarinyar nan nikika kwadawa,chokali abisani ya kalli yan dabansa ya basu umarnin suwa aziza fyadan daukar rai



Kuka aziza tasa tana ja da baya tana wallahi kar wanda ya tabani,da gudu yan daban suka iso wurin,suka rirrike  aziza dake ta faman kuka da neman agaji



Da yake unguwar na masu kudine,ko yakake ihu bawanda zai jika akaton gidanshi


Sai kuka suke,uma

 tana rarrafe;ta matso kusa da abba tabashi hakuri



Kara minal tasa tace annur kazo ka taimakemu




Wannan yayi daidai da tsayuwar annur akofar gidansu minal



A guje yashigo hannunsa rike da katon icce yana zuwa ya dinga rafkawa yan daban da abba

Aguje suka fice daga gidan,annur ya rufa musu baya


Cikin mamaki umma tace wannan waye kuma bawan Allah yazo ya taimakemu


Murmushi minal tasaki ta kalli umma tace shine *mahaukacin masoyina wanda nake burin mallaka*




By

Ur lovely maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: _PERFECT WRITTER FORUM_

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-6

By

Maryam yarmama

*Dedicated to my fans*






Rike baki umma tayi tace mahaukacin masoyi kuma?



Aziza data gyara xama tace tabbas umma minal tana yawaita adu,a da mafarkin samun mahaukacin masoyi,kullum tana rokan Allah ya bata shi,har rantsuwa tayi in Allah ya bayyanashi zata auresa



Salati umma tasaki ta kalli minal tace ke yanzu rantsuwar da kikayi kenan,lalle kam kin dauro ruwan dafa kanki





:::::::::::;;;;;;::::::::::::::::::::::::::::::::::::

Bikin gidansu asiya ya matso,su ummi da su aziza sunyi anko,ummace ta matsa musu karsu rike kowa a zuciya,ko bakomai yan uwansune




Tun ana biki saura kwana biyu su,asiya suka shirya tafiya


Minal ce take shirya musu kaya a ghana must go


Ummi ce tashigo dakin ta tuntsure dadariya harda rike ciki tana nuna ghana must gon tace minal ai wannan zubar da mutuncine kina nufin da ghana must go zamu tafi



Murmushi minal tayi tace to meye aciki wasuma nema suke sun rasa

Aziza ta shigo rike da kwalayan takalma guda uku ta jefa akan gado ta kalli minal tace kekuma meye haka,haba ai wannan kauyancine ya zaki tafar mana da ghana must go,dallah cire mana kayanmu akazamin ghana must go dinnan



Rike baki minal tayi tace haba yan uwa bai kamata kukai kanku inda Allah bai kaimuba,don munje da ghana must go meye aciki



Tsaki aziza tayi tace dallah matsa chan saikace bakiyi makarantaba,ummi jeki gidanku ki dakko mana akwatinnan


Tashi ummi tayi tana dariyar keta,yayinda minal ta daka mata harara tayi zamanta akan gado,tana karewa tafkeken hoton safwan kallo,ko yana ina oho,ko yana raye oho


Hawaye taji yana malala a idanuwanta,saurin gogesu tayi


Aziza dake kallonta tace dama kinsan kinason safuwan kika bari ya tafi baki nunamai ba?kinga yanzu bakisan inda yake ba kuma kin kamu da kauna.


Jijjiga kai minal tayi tana hawaye tace yar uwa ba haka bane,ina tuna ranar da safwan zai dawo ya ganni nayi aure ina tare da annur mahaukacin masoyina




Aziza tace haba yar uwa yakamata ace kin daure ki jira safwan



Minal tace a a dason mahaukacin masoyina na rayu dasonsa zan dauwama,shinake buri in aura duk danasan yanada larura haka nake sonsa



Aziza tace hmmmm bazaki taba fahimta bane,namiji badan goyo bane,kinsan mahaukaci baya da hankali zai iya miki illlah




Minal tayi murmushi tace hmmmm zanso haka,indai wanda nakeso ne yamin illah ko ya nakasani ba damuwa



By

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: *_(P.W.F)_*

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-7

By

Maryam yarmama

Dedicated to my fans




*TUSHEN SU MINAL*



Alhaji imran.a.maigari dane ga maigarin adammawa,a rugar fulani,su biyu iyayensu suka haifa shida abubakar (abba) saboda kasancewarsu yaya tilo maigari yadasu a makarantar boko da arabic, maigari yana kaunar imran saboda yakasance mai hangen nesa da taya mahaifiyarsa acikin gida saboda batta da mace,abba yanajin haushin son da akewa imran,shine ya dauki tsanar duniya ya doramai,basa jituwa,abba baya kaunar karatu kokadan,yafi kauri a lalata yayan mutane ya sato kudin maigari ya bawa yarinya yayi lalata da ita,yan mata basa kinsa domin ba baya bane wajen kyau,shiyasa mata suke rubibinsa suke sallamamai komai,rashin lafiya yakama maigari,imran yafi kowa shiga tashin hankali,duk ya fice a hankalinsa,shiko abba ba abinda ya damesa Allah Allah yake mai gari ya mutu yaci gado don ya hango garken shanu da gonaki,ana cikin haka mai gari ya amsa kiran mahallacinsa,imran ya firgice sosai,mahaifiyarsu halima tanajin maigari ya mutu zuciyarta ya buga itama ta fadi ta mutu,imran yafi kowa shiga tashun hankali


Haka aka musu rabon gado sauran aka bawa dangi,imran ya tafi birni ya fara sana,ar siyar da dankunne yari,yazo yafara kaurin suna haryana fita dubai dakko kaya,gwala gwalai,dasu atampopi,bawanda baisan imran da taimakon al,ummaba,haka ya gina tafkeken gida,yana zuwa kasar saudiyya sukaci karo da hindy nan suka kulla soyayya,amma dakyar aka dauramai aure da hindy kyakyawar mace,dayake ta fito daga gidan talakawa,akayi biki ,suka dawo gida nigeri,a da zama.





Imran ya tafi kauye yaga duk abba  ya addabi gari da lalata yan mata har yawa wata yarinya ladi ciki,iyayenta suka kekeshe saiya aureta



Agaban imran aka daura auren ya biya komai suka tahi birni,tunda ladi ta bude ido taga,hindy ts dauki karar tsana ta dora mata,haka imran ys siya musu gida maidan kyau flat,abba ya dau aniya azuciyarsa indai yana raye sai ya raba imran da dukiyarsa




Ladi ta zubar da cikin,abba bai mata maganaba



Cikin hindy yashiga wata tara ta haifo danta santallele,imran kamar ya mutu don dadi,ya gayyaci yan uwan hindy yan saudiyya ya biya musu kudin jirgi



Tunda babbar yayansu hindy taga dan ta kwallafa rai,dayake tayi aure bata taba haihuwaba,ran suna ya zagayo dangin imran sunzo,sa,biyu aka yanka ansha shagalin suna da yaci sunansa,shamsudeen



Da yan saudiya zasu tafi, babban yayarsu ta dinga ihu da kukan abata shamsi zata kula dashi



Imran yaki yarda amma daga baya ya bata shi badan yasoba,saboda bayason ran hindy ya bace



Haka da murna suka bar gidan suka hau jirgi suka tafi kasar saudiyya amma a hanyar zuwa sukayi hatsari,bawanda ya rayu acikinsu,hindy tayi sumar tagaji,haka sukaje saudiyya suka ginawa iyayenta gida?imran yabawa iyayenta jari




Ba,afi shekaraba hindy ta kara samun ciki, bayan wata tara ta haifi mace kyakyawa fara kamarta,ranar suna aka samata hadiza amma anace mata aziza,ana cikin hidimar suna ladi tahaifi yarta ya mace lubabatu,amma ana ce mata luba




Haka rayuwa yaci da tafiya ,aziza tana wata biyar umma ta karasamun cikin minal ta haifo minal a kyawu aziza bazata kami minal ba saida ta nunamata fari kawai



Itama ladi minal nada wata daya ta haifo hasiya,fara kyal da ita






Arzikin imran sai kara habaka ykk,haka yadauki su aziza da minal dasu,lubaba yasasu a makaranta mai shegrn tsada,a makaranta kullum cikin fada suke,saboda dukansu aji daya akasasu,minal da aziza sunfi kowa hazaka da kokari,lubaba kuwa kullum sai an jibgeta



Abotar ummi da minal tasamo asaline amakaranta sun shaku,har agida ansan abotarsu ummi da minal da aziza



Ko antashi wataran agidansu ummi suke zama,har sukaje ss1 

Inda minal take da burin zama likita,yayinda aziza take burin zama bussiness woman,ita kuma ummi *yar jarida*



Nan mahaifinsu minal ya fara ciwo mai tsanani ciwon suger,duk dukiyarsa abba ya mallake,ko ance ya kawo kudin magani sai yace ai yasamu karayar arziki,sai abba ya tabawa mahaifinsu minal,abincin da likitoci suka hana abasa,su minal nada shekara goma sha uku a duniya Allah yawa mahaifinsu rasuwa sun shiga tashin hankali bakadan ba,


Karantunsu ya tsaya,ga umma ta laulayi,haka abba ya musu korar kare ya mallake gidan,maman ummice hajiya ta bawa su minal karamin fillin ta wanda yake fuskantar gidanta ,

Umma sukayi ginin gidansu daidai gwargwado,da taimakon hajiyar ummi,akayi komai,



Umma duk ta rasa kadarorinta,duka,hajiya tana taimaka musu sosai,har aka haifi auta,(jawahir)itama hajiya bawani karfine da itaba,yayanta uku Allah yawa mijinta rasuwa,daga yayansu ummi nasir da ke karatu a kasar waje,sai yayar ummi dake auren d.p o a abujah,sai ummi data kusa ta kammala karatunta a yanzu,

Su minal sun ga kuncin rayuwa da wahala,haka wataran suke hakura basacin komai


Har auta data mutu kwanaki da suka wuce,wannan shine takaitaccen labarinsu minal


Ayanzu ahaka minal tanada shekara goma sha bakwai a duniya,takasance doguwa wankan tarwada ga dara daran idanuwa,ga hanci har baka,tanada diri;gason kwalya da faran faran da jama,a ahakuri minal ta dakko halin umma,yayinda aziza take fara kal harta zarce minala diri,tana da dan jiki kadan,ita burin aziza ta auri maikudi,duk saurayin dayazo wajenta bata kulasa,saidai tamai bala,i ta koresa,batta da hakuri samsam ,aziza tana shekara goma sha takwas,

Itama ummi fara ce kyal saidai batta da hanci sosai but amma akwai kyau da iya ado,yanzu ummi haka tanada mijin dazata aura lawyer,sainanda shekara daya akasa ranar



*wannan kenan*


*DAWOWA LABARI*



BY

MARYAM YARMAMA

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: *_(P.W.F)_*

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-8


By

Maryam yarmama

Dedicated to all my fans



;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;,;;;,,,;;;;;;;;;;,,,;;,,,;;;;;;;;;;;;


Haka su minal suka shirya,sukayi sallama da umma,ankon dogon riguna sukasha,na kanti,sunyi matukar kyau,duk inda suka dara kowa saiya kallesu


Gaban minal ne yafadi dataga sansanyar iska yafara kadawa,wannan ya nuna alamun mahaukacin masoyinta zai bayyana



Waige waige tafara, ido hudu sukayi da mahaukacin masoyinta,duk kayansa ya yayyaga,rike yake da taya ya nufota yana kwalla mata kira aunty aunty



Murmushu minal tasaki,ta gyara tsayuwa


Ummi tace wayeshi,kafin minal ta bata amsa aziza tace wai shine wanda take da burin aura



Ummi ta dake kirji munshiga uku minal kuwa bata samu tabin hankaliba kuwa,mahaukaci kike da burin aure 



Harara minal ta dankara mata tace ai mahaukacin mutumnr Allah ne yayisa



Annur ne ya nufo wurin aguje haryana neman hankade aziza yace aunty kizo in rage muku hanya



Cikin bacin rai aziza ta dakamai tsawa tace kai kaga munyi kallar yan uwanka,yar uwata ba sa,ar auranka bace,kaje ka auri mahaukaci ya kamar ka



Ran minal ya bace tace aziza!


Daga mata hannu aziza tayi tace dakata,in banda abinki wannan wawan zaki aura maiya sani arayuwar aure,iye sannan ta kalli annur ta dakamai tsawa tace barnan sauna ba amfani



Idon annur yayi jaa,hawaye ya fara malala a idonsa ,ya juya da niyyar tafiya,minal tasha gabansa tace annur ni inasonka,lafiyanka kalau karya suke kai ba mahaukaci bane.


Hankade minal yayi,yayi tafiyarsa yana share hawaye



Aziza ta kalli minal tace Allah ya kara ,ai indai wannan dutsen. Kikayi rantsuwa zaki aura yanzu kika fara gani

Aziza zatayi magana taji an zura mata bulala a duwawu zuwet,saboda zafin bulalan tayi ihu wayyo mamana,suna juyawa suka gano,annur ne rike da katuwar dorina sharbebiyya,aguje suka fanna



Yayinda minal tatashi ta ruko bulalar annur tace a a annur masoyina hasken idaniyata kayi hakuri ,ka kyalesu



Girgiza kai annur yayi yajuya yayi tafiyarsa

Minal ta kyallesa tana zuzuta kyan halitarsa,



Acan nesa ta gasu aziza sai maida numfashisuke,minal ta matse dariyarta ta nufi  wajen aziza sai faman harararta take



Minal ta kyalkyale da dariya tace,a a kike hararana bani naja mukuba bakinkune ya jawo miki




Ummi tace munji muguwa kuzo mukarasa gidan bikin



Abbane zaune da abokansa sunfi ishirin anaci anasha,sai rahs ake


 Ga. An daure shanaye biyu awaje


Yana hango su minsl ya hade rai,amma yana. Hango wasu bare,ya saki. Murmushi harda gaishe gaishe,karasowa wajen sukayi minal ta durkusa har kasa ta gaisheshi amma aziza,tana tsaye ta kwashi gaisuwa



Abba ya kalleta yace ke wace yar iskan yarinyace ,kin tsaya akaina ko haka kike zatonzan baki. Sadakar.  Ne? Banza. Sakarai



Tabe. Baki aziza. Tayi,ta. Kallesa shekeke tace nidai ba yar iskabace,kums inma ka bamu. Sadakan. Ai da kudin mahaifina kake bushasha.




Abba dayaga aziza zata. Bashi kunya,yayi shiru




Azixa ta gama yadamai bakaken magagganu,tashige ciki





Bin bayanta sukayi ,suna shiga asiya ta taresu damurna,abin ya basu mamaki ko din zatayi aure tayi hankali




AZiza ta hade rai yayinda hasiya ta dafa minal suna tafiya harta kaisu masaukin yan mata




Yan matane a dakin birjik. Sai kwalyan. Kamu ake.



Lubaba. Sai yarfa mata fulawa ake tana. Ganinsu aziza ta fara harare harare ta daga murna tace to jama,a kowa yayi hankali da jakarsa akwai masu. Halin bera



Amshe zancen aziza tayi tace to Allah ya rabamu. Da masu halin jaba ma




Yan mata suka. Amsa amin





Lubaba. Ta dinga yada habaici iri iri,har sukaso suyi. Dambe. Da ummi




Hasiyace tashigo tace aziza wai kuzo inji mama zaku gaisa da su dangi dasukazo daga kauye



Tsaki aziza tayi tace wlh ba inda zani waya taba zuwa ya dubamu ba wanda yasan darajarmu. Don haka ba wanda zanje in gaisher




Minal hawaye na. Zuba a idanunta tace aa yar uwa in mukaki zuwa umma taji labari,bazaji. Dadiba,ko bakomai danginmune




Lubaba ta rangada buda tace wama zaije wajenku abinda bakuda abin  hannu


Ummi tace ai arziki nufin. Allah ne bawanda aka haifa da kudi ko mulki




Lubaba ta fusata,tace to karere yar kallan dangi muna maganar mu na dangi meye zakisa mana baki iye?




Minal ta jawosu ummi da aziza suka nufi dakin mama,minalne taga yan uwan mahaifinta,kwasar gaisuwa sukayi


Nan yan uwa aka dauki kukan,mutuwar alhaji imran




Minal. Ma tarushe da kuka


Aziza ta tsaya yana musu kallon munafukai


Mama tace ke me zuciyr fir,auna ke ko kwalla bazakiyi ba ,waya. Saniko ke. Kika. Kashe. Mahaifinki



Aziza tace. Kece. Babbar fir,auna.  Wallahi ma aka bincika akwai sunanki ajerin yan wuta,ai wanda ya danne hakkin marayu shida rahamar Allah. Har abada,da kike cewa mahaifiyata karuwace,ai. Indai  karuwa ake nema aka samu kamarki an gama



Mama. Ta fashe da kukan munafurci




Dangin. Mahaifinsu suka tunzura suka dinga zagin aziza suna tsine mata albarka,


Minal ta. Rushe da kuka yayinda.  Aziza ko ajikinta ta kalli yan uba tace dallah chan ba wanda yakaiku mugunta ai da mahaifinmu yananan ba yar. Iskar data isa ta mana kallon raini,



Daya. Tsohuwatace aziza nice mune. Yan iska?



Aziza tayi dariyar keta tace and sowhat ai. A duniya bawanda  na tsana kamarku. Ayanzu





By

Maryam yarmama

[11/03 11:44 am] salmah💍💍: *(P.W.F)*

*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*_9



mama ta tashi ta fashe aziza da mari



Har aziza zata rama,minal tayi saurin rike hannunta ,suda ummi suka jata waje,suna bata baki,dakyar aziza ta huce ba kukan data tsana ta gani irin kukan yar uwarta minal,washe gari aka shirya tafiya dinner,minal tayi matukar kyau da tsari sunsa ankon kawaye,sun daura blue din rosis da takalmi blue komaima blue,dama ankon swiss less ne pink,aziza sai mita take tana danasan anko kawaye mukayi da banyiba


Abokan angone suka fara zuwa kwasar yan biki,minal suda aziza da ummi sun tsaya,wani hadden mota ya faka a nesa da su,yace minal tazo,a sannu a hankali take tafiya ta nufi wajen hadadden gayen maijini ajiki


Cikin yanga gayen yace sunana yusif shehu abukakar,ni dane ga shugaban custom,nagankine kuma kinyimin sosai in ba damuwa inasonki da aure


Minal tayi yar murmushi tace ai saidai kayi hakuri anmin miji ,indai kana kaunata ga yar uwata chan aziza sai ku daidaita


Yusif yace amma banji dadyba,amma inason yar uwarki tunda naga kuna kama sosai farine ya rabaku dadan jikinta,minal tace to bari inkirata,nufar wajen tayi tawa aziza magana,aziza ansamu abinda takeso ,ta nufi wajen suka gabatar da kansu ga juna,ya kwashesu;dukansu taje ya siya musu dankareriyyar waya ya basu kudin niki,aziza ana gaban mota anata zuba soyayya.



Minal suda ummi sai dariya suke abayan mota,dama haka aziza ta iya soyayya take wulakanta samari,



Taro yayi taro,ashe ma mijin hasiyan tsohone sa,an abbane ma


Aziza tace lalle kuwa auren kudi su mama sukawa hasiya,minal tace Allah yasa ta zauna



M.c taji yana cewa to jama,a yan mata da samari saidai kuyi hakuri prince annur adams saraki bazai samu hallataba amma yabada gudunmuwar miliyan daya



Gaban minal ya fadi tace waye mai irin sunan masoyina kuma,prince annur adam saraki? Inason ganinsa 



Wasu mata tagani suka fashe da kuka wata tace wlh saboda prince annur nazonan ,na aro kaya naci ado amma baizoba,meye wannan abin dan Allah,wlh sonsa zai kasheni,

Minal zuciyarta ya fara bugawa da sauri tana tausaya musu lalle daga ganin prince dinnan ya hadu,tunda gashi rabin yan matan wajen basuji dadiba




Aziza ta kyalkyale da dariya ta kalli minal tace wa ummi kinga minal yanda ta kame kamar kunki inaga ta tuno da masoyintane


Ummi tace shareta indai akan wannan mahaukacinne wanda bashida kyan gani zatayi zata gaji,duk fuskarsa yayi baki kamar anshafa baki tsabar rashin wanka



Minal kota kansu batabi ba


Haka akayi taro aka watse yusif ya maidasu gidan biki



Washe gari aka daura aure,aka chashe su umma da hajiya sukazo suka tafi,aka kai amarya ring road,



Wanke wanke tuli awaje



Mama tashigo dakin taga su minal nata hada kaya,mama ta rike kugu tace me kuke nufi tafiya zakuyi bakuyi wanke wankeba eye?



Harara aziza ta dankarawa minal dataga tatashi tayi hanyar waje da nufin taje tayi wanke wanken,bashiri minsl ta koma ta cigaba da hada kayan



Mama tace au bazakuyiba,to wallahi baku isa kubar,gudannanba dole kuyi 



Aziza suka gama hada kayansu aziza tace wlh bawanda ya isa yasamu wanke wanke,a tsakiyar daren nan,



Bangajeta sukayi sukayi wucewarsu suna zage zage ummi da aziza



Mama ta ce wallahi zamu hadu daku yayan mace kawai.



Yusif ne ya daukesu ya saukesu a kofar gida,minal da ummi suka fita motar suka shiga cikin gida suka,umma suka tadda batanan,gidansu ummi suka shiga suna tambayar hajiya umma tashigone,hajiya tace ai muna dawowa daga gidan biki muka rabu kuje ku duba bayan gidamana



Minal tace to inaga tafita muje dai mukara dubawa umman da bata yawa daganan gidan sainan gidan



Shiga cikin gidan sukayi,wata farar takarda suka gani ga takalmin umma a yashe a wajen,

Minal ta fara karanta takardar kamar haka

*dafatan kuna lfy yayan umma*



_mu barayine masuyin asiri da garkuwa da mutane,mun dauke ummanku kuda ganinta sai a lahira_

*daga boyayyen mutane*




Ihu minal ta saki ummmmma ta zube a wajen sumammiya


Yayinda ummi ma tasaki kara ta nufi waje da gudu aziza na zance da yusif,suka fara tambayar lafiya?



Kuka ummi tasako tace ansace umma



Aziza tace dagaske banson wasa



Ummi ta rusa kuka tace wlh dagaskene minal ma ta suma




Ihu aziza tasa ta shga gidan aguje,tana minal umma namu ya kare,itama ta zube awajen ba numfashi😭😭😭




By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-10


By

Maryam yarmam

*dedicated to*

*all my lovely fans*


😭😭masoya kunji shiru kwana biyu ko,wlh karatu nake,ku dinga mana adu,a masoyana ,adinga hakuri damu



_wannan shafin nakine kawata rabin jiki,ba abinda zai ce miki saidai ince nagode sosai *my salmati Ali wadah*nagode sosai Allah yabar zumunci_






Kuka ummi ta rusa yayinda yusif yaje motarsa da sauri hankalinsa a tashe ya dakko faro bottle water,ya shigo cikin gidan ya rasa takan wazai fara jikinsa sai rawa yake ya kwarawa ,minal,sannan ya kwarawa aziza,ajiyar zuciya minal tayi,itama aziza ba,a jimaba ta farfado,kuka suka dinga rusawa




Hajiya ce tashigo gidan tana lfy lfy nakejin ihu da kukanku ummance har yanzu bata dawoba ko




Yusif ya gaishe da hajiya yace eh yanzu nake tunanin muje police station,muyi reporting don abin nan bana zama bane ace an sace umma 



Dafe kirji hajiya tayi tace dagaske sace umma akayi tayaya haka ta faru,duniya ina zaki kaimu



Minal tace dan Allah mu tafi police station har gidan radio a yada ta kara rushewa da kuka




Yusif yace haka za,agi ku taso mu tafi






Anyi cigiya an sa jami,an tsaro abu yaci shirya shiru kakeji,saboda basu da karfi donma yusif yananan,gashi saura sati biyu ya tafi coursw


Aziza ta damu matuka shikenan basu da gata yanzu,minal tayi hakuri ta dangana kullum acikin adu,ar take Allah ya bayyana umma





Minal na zaune a tsakar gida tayi tagumi gidan ya mata fadi,ba umma,kallon aziza, minal ta fara da taga hawaye na zuba a kwaryan idanuwanta 




Minal zuciyarta yayi rauni ta fashe da kuka ,ba tsammani sukaga baffa ya shigo da wasu mutane guda biyu sun sha malin malin



Cike da tsoro minal bakinta na kakkarwa tace abba ina wuni,


Abba ya nunata ya murtuke fuska yace ni ba abbanku bane abbanku yana kasa,inaso kafin sati biyu ko wacce shegiya ta fito da mijn aure in mata aure kokuma kubi uwarku wanda ta fantsama duniya yawan karuwanci,donni siyar da gidan zanyi



Kuka minal ta fashe dashi tace wayyo umma ina kikene abba ka tuna mu marayune bamu da komai gidannan ne ya rage mana



Abba ya kyalleta yace to marainiya nima ai marayannan ne,kuma ai ubanku ni ya barwa dukiyarsa kafin ya mutu



Aziza ta mike tsaye tace to azzalumi kasani komai mai karewane,inka siyar da gidan sai me?kuma kace babanmu yana kasa karka manta kulli nafsin za,ikatul maut,kaima kana tunanin bazaka shiga kasar bane,kokuma kana tunanin da gida da mota da gwagwalai za,a binneka


Kafin aziza ta karashe kalamanta,taji an tsinka mata mari,dagowar da zatayi taga daya daga cikin alhazawanne wani kato dashi baki kirin,yace ke bakki da kunya kike zagin tsohonnan



Aziza ta dafe kunci tace nika mara to wallahi ka tsinkawa uwarka mari,banza azzalumi bakin mugu,da gudu aziza ta shige dakinsu tasa sakata tana zage zage



Abba ya durkusa yana bawa mutanen hakuri harda daukan alwashin dukanta



Minal tana kuka tace abba  nidai inada tsayayya zance ya turo magabatansa ayi auren



Cikin sauri abba yace dan waye,a garinnan,bafa zaki auri maikudiba fa


Murmishin takaici minal tayi tace abba badan kowa bane mahaukacine mai bin bola,yana neman abnci kuma bansan asalinsaba



Abba yaji kamar ammai albishir da gidan aljanna yace maxa maza kice ya turo da magabatansa ai dama yar karuwa sai mahaukaci,ku da kuka gama zubar da mutuncinku a kwararo wani dan arxikin ne zai tsaya ya aureki saidai mahaukacin



Kuka minal tasaki,yayinda aziza dake daki ta ce aikune mahaukatan da kukecin hakkin al,umma




Ran abba ya bace ya karbi makulli a hannun dayan alhajin,ya karkame kofan dakin da aziza take aciki,yana kya dandana kudarki yau





*masoya captain shayeeda amin afuwa gobe zan cigaba*


Daga taku mai debe muku kewa

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁* -11

By

Maryam yarmama

Dedicated to

*All my fans*




Aziza dake garkame da kwado bata sadudaba tace ai zanso ka kasheni inka isa sunanka abba,




Minal ta durkusa tace dan Allah abba ka budemin yar uwata ,karta mutu ita kadai ta ragemin ka taimaka ka budeta wallahi tana da asma kuma chronic ne



Abba yace mai ruwana da asmarta tsabar karya waya bata asma ai inyana dashi zamu sani,kinga tafiyata dakey din



Har kofar gida minal tabisu abba tana kuka da basu hakuri,daga bisani ma abba ya hankadeta ta fadi kasa wanwar har bakinta yadan fashe ,minal kuka tasa dataga sun shiga mota sunja sunyi tafiyarsu




Taimakon wa xasu nema,bayan su hajiya sun tafi abujah hutu,kuka ta kara fashewa dashi,ji tayi an wullo mata abu ya fadi kasa makulli tagani da dan karamin takarda ansa

_daga boyayyen masoyinki banson kina kuka ki share hawayenki_



Dafe kirji minal tayi tace waye kuma wannan inaga ma wucewa yazo yi kokuma ma makullin karyane,jefar da makullin minal tayi tana neman mafita ga aziza tana ta faman sheka uban tari.



Ba shiri minal ta dauki makullin tana adu,ar Allah yasa ya budu,kafin kace me kofa ya bude,da gudu minal ta fada dakin tana aziza,


Aziza dake faman sheka tari tace minal dakko min drug dina in shaka yi sauri,da gudu minal ta fita daga dakin ta nufi dakin umma inda umma take aje magunguna ,abin mamaki tana daga robar maganun ya kare,ihu ta kwalla tace ya Allah ka kawomin agaji kar in rasa yar uwata 



Minal ta fito daga daki cin karo tayi da maganin irinshi,ba tantama ta dauka ta kaiwa aziza,aziza tana shaka tana fesawa abakinta tayi ajiyar zuciya cikin nishi sama sama tace wlh sai naci uwar abba dan bantan ubansa



Cikin damuwa minal tace yanzu aziza kina nufin baki sadudaba kenan,



Aziza ta gyara kwanciyarta tace ai wlh sainaga bayansa ta sanadinsa muka rasa babanmu ta sanadinsa karatunmu ya tsaya muna ss2 gashi har ummi ta kusa zama nurse amma mu sai zaman gida,ta sanadinsa muka daina jin dadi da walwala muka rasa auta muka rasa umma,tayaya zan saduda in Allah ya yarda sai yayi mutuwar wulakanci,bazan taba yafe masaba.



Minal tace haba aziza ki dinga godewa Allah ai Allah ma yana yafewa mutum balle mu yan adam ajizi,ni yanzu na tsani auran maikudi da in auri maikudi gwanda na zauna ba aure har abadan abada



Zaro ido aziza tayi tace ke wace irin sokuwace ke ana neman inda za,a huta ai munfi kala da matan manya,nidai in bamai kudiba wlh bazan auri kowaba



Subhanalllah minal take fadi tace anya kinada hankali kuwa meyasa kike da hangen dala,



Tunzura aziza tayi ta wanke minal da mari tace ai gwandani ban tare a gindin mahaukaciba dan uwarki



Kuka minal tasa tace yar uwa nikika mara kika zaga,ko wanine ya zageni saikin dau mataki,ko kin manta amanata yana hannunki a yanzu,kece uwata kece ubana kece gatana,ke yakamata ki nunamin madaidaiciyar hanya amma tunda bakya sona gidannan bari in kwashe kayana in tafi in barmiki gidan,minal ta tashi da niyyar fita aziza ta ruko hannunta tana hawaye tace a a yar uwata ba inda zaki,kiyi hakuri ki yafemin





By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-12


By

Maryam yarmama


Dedicated to all my fans






Kuka minal tasa ta rungumi aziza suna kuka mai tsuma zuciya





Bayan kwana biyu minal zaune da kyakyawan mahaukacin masoyinta a tsakar gida ,sai gabzar lomar abinci yake yana santi kai aunty haka kika iya abinci dama 


Kallonsa minal take komansa burgeta yake


Dago ido annur yayi,dara daran idonsa suka hadu dana minal nan minal ta kara dumaucewa duk kwarjininsa ya cika mata ido sunkuyar da kanta tayi,

Annur ya kyalkyale da dariya,yace kai aunty ke matsoraciyace idona kike tsoro iyeh kika sunkuyar da kai kamar munafuka



Minal batasan lokacin da dariya ya subuce mata aziza ma dake waya a kuryar daki saida ta dinga dariyar data dade batayiba



Minal tace kaga nidai abinda nakeso kaje gida ka gayawa umma da abba,su kawo lefe a daura mana aure



Ihu annur yayi ya rufe fuska yayi waje da gudu,dariya minal ta fashe dashi aziza dake waya a daki hawaye ya zubo mata shikenan yar uwarta mahaukaci zata aura,oh yanzu yar uwarta zata shiga sabon rayuwa,




;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;



Washe gari minal tana sharar tsakar gida,taji sallama,amsawa tayi baki uku tagani tsofaffi uku mace daya, duk kayansu yasha ruwa gasu rike da karamin akwati daya tal


Minal ta gaishesu cikin ladabi da biyayya ta shimfida musu taburma ,aziza dake bacci ta farka fitowa tayi ta gaishesu, ta zauna a gefensu



Wata farar tsohuwar tace mudai mune iyayen annur wanda yake yawan bamu,labarin minal wacece amaryar tamu



Sunkuyar da kai mainal tayi


Tsohuwar taci gaba da cewa shine yazo mana da magana gadan gadan wai kince ya kawo kayan auransa,muka karyatashi yana da larura wazai auresa,kuka ya dinga mana harda zazzabi gashi muba haline damuba,annur marayane iyayensa sun mutu.mu muka rainesa tun yana karami yake tare da laruran nan,shine muka hado akwati daidai karfinmu ku kira ummanku da abbanku


Aziza jikinta yayi sanyi tace ai mu ma marayunne



Jinjina kai dattijan sukayi ,sukace Allah yaji jansu to waye zai wakilci auranne



Minal ta musu kwatancen  gidansu abba,aziza takaici ya kusa ta kasheta dataga an bude dan karamin akwatin sarka dan saba,in guda uku,dan kunne dan goma goma dozin biyu,turare dan dari biyu da hamsin guda biyu,takalmi dan dari uku guda daya tak,bacilin da gyalle daddaya,sai turmin atampa biyu.



Aziza kamar ta rusa ihu takeji,ai wannan gwanda basu kawoba ko sadaka albarka minal taja musu zagi agari shikenan sun zamo abin nuni agari



::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::;::::::::


Abba yaji dadin wannan auren minal da dan talaka atake ya yanke aure kwana uku masu zuwa



Minal kullum bata rabo da mutane,yan tsokana mata da maza,suna mata gorin auren mahaukaci,


Minal ko ajikinta,hajiyace suka dawo daga abuja taji labarin minal zata auri mahaukaci,ummi kamar tayi hauka tsabar takaici dama ashe minal bata sadudaba



Hajiya ta kasawa minal magana data ganta cikin farin ciki da annashuwa kawai ta mata adu,ar Allah ya kawo Zuriya masu albarka,sannan ta siya mata katifa da kayan kitchen da taburma makeke



Kuka aziza da minal suka dingahi suna godiya,hajiya tazama uwa agaresu



By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*13



By

Maryam yarmama

Dedicated to my fans




Aziza suka yanke shawarar daukat gwal din dasuka taba boyewa da umma,da nufin siyarwa amma suka nemesa suka rasa abin ya basu mamaki,


Jikinsu yayi sanyi kodai barayin dasuka sace umma sun tafi dashi 


Kuka minal tafara tace wai sai yaushe zamu daina kuka da bakin cikine rana tayi zafi inuwa kuna babu sanyi


Aziza tace muyi hakuri mu dangana,muje amana kunshi da fulawa kawai kinsan gobe daurin aurenki ke da masoyinki annur



Murmushi minal tayi yayinda taji takun takalma lubabace tsaye suda mama ,mama ta rangada buda tace ahayye kaikayi ya koma ga mashekiya andaiji kunya anrasa mijin aure an fake da auran mahaukaci ,wanda baisan gaibuba



Lubaba ta anshe zancen ai saura ke aziza in Allah ya yarda dan maye zaki aura yata lakada miki duka 



Aziza tayi tsaki duk jikinta yayi sanyi,aziza dana sani da rashin kunya da raina mutane bata kyalewa taja bakinta tayi shiru hawaye na malala a idanunta tace duk mai kukamana duniyace ta ishi kowa riga da wando



Lubaba suka rangada buda suka tafa da mama sai kace kawaye mama tace su kanwar fir,auna baki ya mutu kenan ai kadan ma kuka gani banzaye jakuna



Ba wanda ya tanka musu har suka gama sambada rashin mutuncinsu sukayi tafiyarsu ba wanda yace kala acikinsu minal





Rana bata karya saidai uwar diya taji kunya,yau mutane shida suka shaida auran minal da annur akan sadaki naira dubu biyu,wanda suka hallaci daurin auren saga abba sai abokinsa sai,baban annur da liman,ana watsewa abba yasa dubu biyun a aljihunsa yayi gaba abinsa



A gida minal dasu ummine a zaune sunhi dan girki,yusif ya kawo wa minal gudunmuwar kayan abinci su shinkafa lemo faro,katon din taliya biyu,turmukan atamfa sabulu dadai sauransu



Yusif ya sanarwa da aziza zai tafi course zuwa port harcour zai yi wata biyu in yadawo zasuyi maganar aurensu



Aziza jikinta yayi sanyi gani take kamar karshen haduwarsu yazo ,anya yusif ba guduwa zaiyiba ,wata zuciyar tace a a bazaimin hakaba 




Da daddare akasa dan kayan minal a kura su katifa dasu abubuwan da take bukata,a kafa su ummi suka kaita  kwarbabben gida kuma na jar kasa



Kuka aziza ta fashe dashi suka jera gadon minal aciki da yan kayanta



Minal kuwa sai farin ciki da annashuwa suke saida aziza sukazo tafiya ta fashe da kukan rabuwa,dakyar suka banbare jikinsu daga jikin juna suna kuka



Ba,a jimaba aka kawo nepa haske ya gauraye dakin, ya gauraye da haske,dakin yadanyi kyau,dauro alwala minal tayi tayi sallah ta,cire riga daga ita sao dan singlet saboda zafin da ake tafkawa,kwanciya ringingin tayi.



Annur ne ya taho da bataliyan yara,yana kuzo kuga mata ta yara,minal ta kokarin saka hijjabi suka danno kai dakin


Rufe ido annur yayi sakamakon ganin rabin dukiyar fulanin minal awaje yace laaaa dama aunty ke yar iskace?




By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-15

_BY MARYAM YARMAMA_



_MASOYAN LITTAFINA_

Ina muku dimbin godiya ba abinda zance muku saidai godiya


_this page is dedicated to adorable *my ummie jafar,awesome salma ali wadah,my sweet and beautiful hauwa mamee*_

_thank you for ur special love and care you guys you are in ma heart_






♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥


Annur yace anty,nizanyi wanke wanke karki damu jeki kwanta na iya



Murmushi minal tayi batason ,ta musamai ta nufi,daki tana gyarawa,annur yasamu bayan tukunya ya lakuta ya dauki wani kofi fari kal yace kai kofinnan yayi fari diyawa yakamata ace, nachanjamai kala zuwa baki



Duk fararan kwanukan minal annur ya lanbata baki akai suka dawobaki , ya dauki dish da nufin wankewa ,yaran jiya sukashigo,tashi tsaye annur yayi ya saki dish din ya fadi ya tarwatse,yana murnar ganin abokansa



K'aran ne ya  jawo hankalin minal dake faman gyara dakin,a guje ta fito hartana tuntube tace dear mezan gani haka iyeh,haba dear wannan ne iyakacin dish mukuma .



Annur  ya zaro ido kai anty,yanzu akandan wannan abun ranki ya bace to yahakuri bansaniba bazan karaba,anty bakiga na maida kwanukan da kofinnanba sun dawo baki abin sha,awa




Minal ta zaro ido tace mezan gani,nashiga uku ni minal




Annur ya ,hankade minal suka shige daki suda abokansa sunata tsalle tsalle da ihu akan gado



Minal cikinta ya duri ruwa,tace nadakko ruwan dafa kaina


Ihun annur minal taji yana fadin anty nayanke kizo wayyo zan mutu


Aguje minal ta fada dakin kukatasa,ta zauna a kan gado ta rike dan yatsan daya yanke wanda jini keta zuba,tausayinsa ya kama minal itama tafashe da kuka ta rungume annur ,duka dakin yadauki kukan abokan annur da minal dashi annur din kansa,




Sai rusa uban kuka suke,minal harda shessheka,azizace tayi sallama ta fado dakin tana waye ya mutu?


😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂




By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-14


_by_

_maryam yarmama_


_wannan shafin nakune masoyana saboda kaunar da kuke nunawa littafina ,masu bugomin waya masu yimin text da fadin sunanku kuna diyawa,naga sakonku kuyi hakuri next page zan fado sunanku kuna diyawa i love you too😍😍_




Dafe kirji minal tayi yayinda tayi saurinsa hijab,tayi yake dataga dandozon yaran sunata lalata mata risho,



Minal cikin sanyin murya tace ku bari mana annur ka gaya musu


Annur yace haba anty ai abokainane dasu muke wasan langa awaje,shiru minal tayi ,annur yace anty ina kazar da ake bawa angwaye tunda nima angone,minal ta kyalkyale da dariya tace ai amare ake bawa badai angwayeba




Annur yacewa yaran abokaina ku fita ku tafi gida gobe ma hadu ayi langa,ku zo gobe muci abincin anty



Ihu yaran suka dingayi suna sai gobe sai gobe


Minal tatashi taje ta rufo kofa,ta cire hijjabin tace ana zafi,wlh baxan iya jurewaba



Annur ya kalli shayeeda ya kawar da kai ,matsowa daf dashi minal tayi tana kallonsa,shafo fuskarsa tayi tace haba dear meye nacemin yar iska bayan kasan ni matarkace sai yanda kayi dani na zamo mallakinka,ina kaunarka kai nake mafarki kaine uban yayana




Matsawa gefe annur yayi ya murtuke fuska yace a a anty ki daina shafani karki iskantani,nidai yarone badan iskaba



Minal taji dariya ya subuce mata ta dingayi harda tsugunawa tace ai kai ba yaro bane ka wuce shekara talatin



Annur ya zaro ido yace amma ummata tacemin shekara biyar nake shine take bani biyar,tunda yanzu shekarata talatin nera talatin za,a dinga bani daga bisa ya kwanta a gado ,nan take barci ya daukesa.



Dariya minal tasa tace oh na hadu da masoyi,gyara mai kwanciya tayi itatama ta kwanta tana shafamai laulausan gashin sa daya kwanta kamar indi,a 




Washegari minal ta tashi ta hura wutar murhu ba kalanzir a risho tanason daura wa annur shayi



Iccen danyene ,duk gidan ya kaurw da hayaki sai hawayene yake ta zuba a idanunta



Annur ne ya fito daga daki, ya nufi wurin ya kalli idon minal duk yayi jajur,kamar, gauta yace sannu anty in nemo miki makamashi

Murmushi minal tayi. Tace daka kyauta my dear



Da gudu  annur ya shige dakin ya dauki wuka ya yanki rabin sabuwar taburman minal😂😂 dagudu ya fito ya cusa a murhun nan wuta ya tashi fuuuuuu



Tambul minal tayita koma gefe dafe. Kirji minal tayi tace  dagaskene gizo idona yakemin taburmata a wuta?



Annur yace ai anty saiki godemin , nasha wuya wajen yanko taburman,ma




Ko daya minal bataji haushiba,ta yi murmushi tacenagode ta dora tunkunya akan wutar dake ci


Tahadamusu. Shayi sukasa,




By

Maryam yarmama

[11/03 11:45 am] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-16

By

Maryam yarmama



*wannan shafin nakine maman hafsat(sayyada hajara)i love you so much*




Minal ta kara rushewa da kuka tace yar uwa mijina ya yanke wlh ya yanke,ki taimakamin kar,in rasashi,kinga jini yanata zuba a hannunsa ,minalta dago hannun annur masu laushi da taushin bala,i




Aziza ta rike ciki😂ta rinka sheka dariya harda hawaye saida tayi mai isharta ta kalli minal da ranta ya sosu tace dame ya yanke,banza minal tayida ita,yayinda aziza ta dauki tsumma,ta kulla a hannun annur


Ihu annur ya kwalla anty a cire zafi ,aziza ta kara kyalkyalewa da dariya harda faduwa kasa tace haba angon minal kaifa namijine ba mace ba ko kunya bakaji ga minal azaune kana kuka aisaita rainaka



Rufe ido annur yayicikin alamun kunya yace nidai anty ki bari nadena kuka,yanzuma wasa zamu tafi 



Zaro ido aziza tayi tace la ai ango baya wasa,sai amaryarka ta rainaka ta dingama wanka,ai azamanin nan  ka dinga zama agida tana koyawa a.b.c d 


Annur yace la aiko inason in iya a.b.c d.don yanamin dady duk abokaina sun iya nikadai na rage ban iyaba



Aziza tace laaikwa gwara ka koya donwata rana in baka iya a.b.c diba ba wanda zai yi wasa dakai




Annur yace. Dagaske anty bari in dawo daga wasan taya,sai antyna ta koyamin



Aguje ya fyace yayinda abokansa suka rufamai baya




Aziza tace lalle kam minal sannu da hakuri




Minal tace ai abinda kakeso shi yake wahalar dakai sai hakuri haka duniya ta gada mu dingahakuri, wai ya ake ciki har ne 



Aziza tace ai nasiyar da duk wata abubuwanmu na amfani,najena bude mana account na zuba,bakiga akwatina a wajeba,na dawo gidannan. Da zama na barwa. Baffa gidan


Gobe su hajiya ma zasu yafi abuja final

By

Maryam yarmama

[11/03 5:31 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-17

By

Maryam yarmama


*After a long break yarmama is back,for the countinuty of this novel,my fans thanks you for ur patience*



Minal tace ayyah yanzu hajiya tafiya zasuyi,sune fa yanzu gatanmu,ya takene abba ya tafi,umma bawanda yasan inda take,su hajiya zasu tafi,shikenan namu ya kare mun zama marayu karfi da yaji,bamu da kowa



Annur ne ya bankado labulen ya shigo yace anty ki daina kuka kuna dani ni jarumine,innayi kudi zan siya miki mota 



Aziza tayi dariya tace nifa annur


Annur ya noke kai yace a a banda ke ke,bakya dariya saina mugunta



Aziza dariya takarasa saki tace oh munada catoom a gidannan,tabbas annur shine farin cikinmu yanzu,yusif kona bugamai waya bata shiga,inagama a black list yasani



Annur yace anty anty ki koyamin a.b.c d


Aziza tace a a nidai kace minal ta koyama badai niba,ni bacci nakeji



Annur ya murtuke fuska yace anty dama kinzone ki cinye mana abincinmune?to bamu yardaba ki tashi ki koma gidanku


Minal tace a a yar uwatace anan zata zauna tare damu


By

Maryam yarmama

[11/03 5:31 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*-18

By

Maryam yarmama




Annur yayi murmushi yace hmmmm anty dafatan ba taci kamar shanuko


Aziza tace aini buhun shinkafa nakeci arana

Kuma acikina yake dafuwa



Annur ya zaro ido yace anty mekike nufi kina nufin hadiyewa kikeyi kamar gara iye kai anty ki dai rageci



Aziza tayi bamza dashi tayi kwanciyarta,minal ma ji tayi tanajin bacci itama ta haye kan gado ta kwanta



Annur ya tsaya ya kurawa kyakyawar fuskar minal ido,yana godiya ga Allah,dariya ya kece dashi


Kuka ya fara kuma yana anty yunwa nakeji zanci abinci anty zanci abinci



Aziza ta tashi tace ohhjj kaidai kafiya takura wollah,zama kusa dakai gwanda zama kusa da toilet


Annur ya dinga ihu wayyo anty minal,ki tashi ta kirani da mahaukaci



Minal ce tatashi ta fara aikin lallashi tace haba nawan jaruman maza basa kuka,ka koyi juriya



Annur kokari ya fara ya tare kukan,amma chan ya kara fashewa da kuka yace anty anty bazaki gane bane,buhun shinkafarmu nake tunani,yanzu muka yi bacci,anty zata hadiye,niko wallahi bazanci tuwoba


Fashewa da dariya su minal sukayi harda tafi minal tace ai bazata cinyeba,tasanni zaneta zanyi sosai


Ka kwanta anjima na dafa mana shinkafa mai dadi 




Dariya annur ya fashe dashi ,ya rufe ido da tafukayen hannunsa,ys fita a guje kamar zai tashi sama



:::::::::::::::;;;;;::::::::::::;::;;;;

Abbane zaune awajen boka yana fadin ya bokana kamar yanda nayi sanadiyar mutuwar babansu ,nawa uwarsu kuruciya tabi duniya,ta shige daji,nasasu sukayi bakin jini,nasa kanwar ta auri mahaukaci

To haka nakeso awa fitsararriyar nan asiri,duk wanda ya nufeta da niyyar auranta fuskarta sai ya zamemai wata dodanniya,kuma inason tayi bakin jini awajen kowa,inason dukansu daga ita har yar uwarta suyi bakin jini kowa yakisu



Kyakyalewa da dariya bokan yayi yace angama kasan yaran akwai ibada,inason ka debo kasar kabarin mahaifinsu da gashin yaran,in sunyi tsifa sun taje sai ka dakko warin takalminsu,shikenan an gama,zasuga bakin cikin da basu taba ganiba a rayuwarsu;a wahala zasu kare 



Abba yace gaskiya saidai kasa aljani kamus ya dakko amma ni bazan iyaba


Boka ya sheke da dariya yace wannan ba damuwa bace,ajiye kudi kaga aiki da cikawa.



Damin kudi abba ya aje yana murmushin mugunta,




By

Maryam yarmama

[11/03 5:31 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYYAYEN MASOYI🦁*-19→20

By

Maryam yarmama


Minal ce zaune a tsakar gida tanawa wa aziza tsifa,tajewa aziza kai takeyi,wata guguwa ta taho,gari yayi bakikirin

Takalminsu da gashin dasuka taje yayi sama,


Aziza da gudu tayi daki,yayinda minal taja baya bakinta ya furta ayoyi 


A hankali guguwar  ta lafa ,ta tafi da takalmarsu



Aziza ta fito daga daki tace minal kenan ta tafi da takalmarmu lalle da sake wannan guguwa haka


Minal tace hmmmmm Allah zaimana maganin komai,zomuci gaba da tsifar da mukeyi saimu dora girki



Wani almajirine yazo yayi sallama wai aziza tazo inji yusif


Ihun murna aziza tayi tace da gaske?


Yaron yace eh

Tace jeka cemai ina zuwa,kawai yanzu shafshaf



Aziza ta shiga cikin dakin tasa hijjab ta shafa hoda daman lebe


Minal ma murmushin murna take tana kallon yar uwarta yanda take dokin,ganin sahibinta tace Allah yasa a fita asa,a



Aziza tana taku daidai tana fita taci karo da yusif.


Yusif kara yasaki yanufi mota da gudu,ya ja da karfi yabar layin


Ran aziza ya bace tace aha,yusif dama zuwa yayi yamin wulakanci lallema bari inkirashi



Daukar wayarta tayi ta kirasa bugu daya ya dauka,

Aziza ta haushi da masifa yusif wannan wani irin wulakancine daga ganina saika kama guduwa saikace kaga dodo


Yusif yace haba aziza yazakiyimin wasa da fuskar dodanni ba kyan gani



Aziza ta cika fal da mamaki tace wallahi ba abinda nasa a fuskata ina ganin gizo nama



Yusif yace wannan ba gizo bane gaskiya indai hakane to kina da shafar aljanu



Aziza tawani lankayo ashar ta duramai tace yusif inkasamu wata basai ka tsaya kanamin wulakanciba,



Yusif yace bawa minal wayar nasan zatafi fuskantata


Gida azixa tashiga ta mikawa minal wayar a sanyaye,tace yar uwa gashi inji yusif



Minal ta amsa bayan gaisuwa yusif ya kora mata bayani


Mamaki ya cika minal ta tuna mafarkin datayi da abba shekaran jiya ya biyosu da wuka yana nuna aziza itada samun aure har abada,sudajin dady har abada



Kashe wayar minal tayi tana zubda hawaye ta kwashe mafarkin datayi ta gayawa aziza


Wani ihu aziza tayi tace shikenan burin abba yacika ya lalata mana rayuwa,aziza tashiga daki ta dakko kalanzir a galan,ga maganin kwari a hannunta



Minal ta kuka ta tashe tsaye ta tashi tace yar uwa mezakiyi,dashi


Ran aziza a bace tace sha zanyi inmutu in huta da wannan wahalar,wai me mukayiwa abba bayason ganinmu iyeh,wallahi gwanda nasha kalanzir na mutu,in huta,galan ta dauka ta kafa abakinta tanata kwankwada.



Ihu minal tafara ta taho da gudu,amma tayi latti aziza ta sha mai isharta,tafadi akasa kumfa na fita abakinta.



Kuka minal tasa tana aziza karki mutu kibarni awannan duniyar,mu biyu muka rage aziza ,,jama,a taimako yar uwata


Da gudu ta tashi da niyyar fita karo sukaci da wani yaro,hannunsa rike da madara caton yace wai gashi inji *boyayyen masoyi*



Ayar tambaya shin wanene boyayyen masoyinman mai taimakansu,

Shin aziza tamutune?


Jama,a labari yanzu aka soma kuta bibiyarmu



By

Maryam yarmama

[11/03 5:31 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYYAYEN MASOYI🦁*

By

Maryam yarmama


Minal ce zaune a tsakar gida tanawa wa aziza tsifa,tajewa aziza kai takeyi,wata guguwa ta taho,gari yayi bakikirin

Takalminsu da gashin dasuka taje yayi sama,


Aziza da gudu tayi daki,yayinda minal taja baya bakinta ya furta ayoyi 


A hankali guguwar  ta lafa ,ta tafi da takalmarsu



Aziza ta fito daga daki tace minal kenan ta tafi da takalmarmu lalle da sake wannan guguwa haka


Minal tace hmmmmm Allah zaimana maganin komai,zomuci gaba da tsifar da mukeyi saimu dora girki



Wani almajirine yazo yayi sallama wai aziza tazo inji yusif


Ihun murna aziza tayi tace da gaske?


Yaron yace eh

Tace jeka cemai ina zuwa,kawai yanzu shafshaf



Aziza ta shiga cikin dakin tasa hijjab ta shafa hoda daman lebe


Minal ma murmushin murna take tana kallon yar uwarta yanda take dokin,ganin sahibinta tace Allah yasa a fita asa,a



Aziza tana taku daidai tana fita taci karo da yusif.


Yusif kara yasaki yanufi mota da gudu,ya ja da karfi yabar layin


Ran aziza ya bace tace aha,yusif dama zuwa yayi yamin wulakanci lallema bari inkirashi



Daukar wayarta tayi ta kirasa bugu daya ya dauka,

Aziza ta haushi da masifa yusif wannan wani irin wulakancine daga ganina saika kama guduwa saikace kaga dodo


Yusif yace haba aziza yazakiyimin wasa da fuskar dodanni ba kyan gani



Aziza ta cika fal da mamaki tace wallahi ba abinda nasa a fuskata ina ganin gizo nama



Yusif yace wannan ba gizo bane gaskiya indai hakane to kina da shafar aljanu



Aziza tawani lankayo ashar ta duramai tace yusif inkasamu wata basai ka tsaya kanamin wulakanciba,



Yusif yace bawa minal wayar nasan zatafi fuskantata


Gida azixa tashiga ta mikawa minal wayar a sanyaye,tace yar uwa gashi inji yusif



Minal ta amsa bayan gaisuwa yusif ya kora mata bayani


Mamaki ya cika minal ta tuna mafarkin datayi da abba shekaran jiya ya biyosu da wuka yana nuna aziza itada samun aure har abada,sudajin dady har abada



Kashe wayar minal tayi tana zubda hawaye ta kwashe mafarkin datayi ta gayawa aziza


Wani ihu aziza tayi tace shikenan burin abba yacika ya lalata mana rayuwa,aziza tashiga daki ta dakko kalanzir a galan,ga maganin kwari a hannunta



Minal ta kuka ta tashe tsaye ta tashi tace yar uwa mezakiyi,dashi


Ran aziza a bace tace sha zanyi inmutu in huta da wannan wahalar,wai me mukayiwa abba bayason ganinmu iyeh,wallahi gwanda nasha kalanzir na mutu,in huta,galan ta dauka ta kafa abakinta tanata kwankwada.



Ihu minal tafara ta taho da gudu,amma tayi latti aziza ta sha mai isharta,tafadi akasa kumfa na fita abakinta.



Kuka minal tasa tana aziza karki mutu kibarni awannan duniyar,mu biyu muka rage aziza ,,jama,a taimako yar uwata


Da gudu ta tashi da niyyar fita karo sukaci da wani yaro,hannunsa rike da madara caton yace wai gashi inji *boyayyen masoyi*



Ayar tambaya shin wanene boyayyen masoyinman mai taimakansu,

Shin aziza tamutune?


Jama,a labari yanzu aka soma kuta bibiyarmu



By

Maryam yarmama

[12/03 9:33 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*26-30

BY MARYAM YARMAMA


_IN DEDICATION TO_

*MY BESTY SALMA*





aziza ta dauki kudin taje ta biya,


Akayi treating din minal,

Minal ta shafe saati uku tana jinya,kamar bazatayi raiba

Itadai burinta taga. Sanyi idaniyanta annur



Aziza tayi fadan tagaji,ta fidda damuwa,ahaka aka sallamesu


Abin mamaki suna dawowa gidasukaga gidan ya kone kurumus



Minal da azizasuka fashe da kuka dasuka shiga gidan sukaga komai ya kone


Minal ta dora hannu aka tace nashiga uku annur dina


Harara aziza ta dankara mata tace kekika damu dawani annur  ni ta kayana nake



Minal tace haka aziza raifa akace miki,ko kiyashima yana darai balle mutum,niban damu da in rasa rainaba indai annur zairayu wannan ba matsalata bane,kafin ta karasa maganar ta taga yara suna shigowa dadirka dirkan akwatuna guda hudu,ga kayan masurufi da sauransu


Ajewa suka farayi ,minal tace kuko wani irin sabani kukayi haka?


Dayan yaron yace basabani mukayi ba wanine waishi boyayyen masoyi yace in kawo muku


Dayan yaron yamika wasikar yace wai gashima yace abawa wata minal



Sahannu minal tayi ta ansa,ta sallami yaran,bubbude kayan sukafarayi,kayanemasu shegen kyau adinke suke,ko wanne da gyallensa,harda bedshit


Rawaa azizata fara tana murna,yayinda minal tayi tsaki tace aini bai burgeniba.




Fara karanta wasikar tayi kamar haka

 Assalamu alaikum



Kiyi hakuri dear natafi da mijinki,amai aikin kwakwalwa nanda sati biyu zan dawo miki da mijinki;lafiya kalau,saiya sakeki ni in aureki



Kuka minal tasatace. Wallahi bawanda ya isa ya rabani da mijina har abada,


Aziza dariya ta sheke dashi tace aigwanda ki auri *boyayyen masoyi* ya fiye miki alkhairi akan wannan mahaukacin,ki godewa Allah ma yamiki hallaci


Minal tace wallahi ba abinda. Yamin wani hallaci yamin bayan yarabani da abin kaunata?




Kwalin chocolate aziza ta bude ta dauki daya ta faraci tana santi




Yayinda minal tayi tsaki tayi tagumi.




Aziza tace inmazaki dauka ki dauka kici inta mutuwane mu mutu tare.




Minal tayi. Rau rau da ido itama ta dauka suka. Dinga ci.


Shigar dakayan sukayi daki,suka kulle,dakin suka fito tsakar gida kamar sunsan abba zaizo

Suna hira abba,ya shigo gidan yana tafiyar kasaita



Kallo daya sukamai kowacce ta dauke kai,aziza harda guntun tsakinta



Abba yace,to shedanun bariki saiku shirya kubar gidannan domin nasiyesa zan gyarasa sabuwar amarya zanyi




Aziza tace kutumar chan wai abba mai mukama bakason ,kaga mundan fake,kafiso mu zauna atitin Allah to wallahi kayi karya ubangiji Allah yafi karfinka tsohon najadu


Tattabata minal take alamun tayi shiru aziza tace ke dallah sokuwa kyaleni inciwa wannan wanda yafi fir,auna muganci mutunci kuma in kwana lfy ,kasan ba tsoranka mukejiba wallahi ko yanzu akan wuka saina lumama




Tafi abba yayi yace good niko nayi rantsuwa saina ga bayanku,keda aure har abada,kekuma minal ke dajin dadi kinyi hannun riga dashi



Minal ta fashe da kuka ta durkusa tana ta rokan Allah ya yaye masu bakin cikinan



Yayinda aziza ta dauki tabarwa tawani duro uwar ashar ta nufi wajen abba ta kwalamai akafa


Ihu abba yasa yayinda aziza ta kara kwalamai akafa tace bari in karya kafar zuwa gidan boka,



Da gudu abba ya fice rai abace aziza ta nufi daki tana kuka 


Minal ce tashigo tace aziza meye kike kuka



Aziza ta hargitsa gashin ganta tace minal bazaki gane yanda nakeji bane naso ace na kashe abba a take inyaso nima a kasheni



Subhanallah minal ke fadi tace haba aziza ki dinga sawa ranki ruwan sanyi,mekike ci nabaka na zuba,karki manta watara sai labari ,God time is the best



By

Maryam yarmama

[12/03 9:33 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*31-35

By

Maryam yarmama


This page goes to my unique fans,i gave you a vote of thanks for ur love and caring about this novel







Aziza ta share hawayenta tace shikenan yar uwa nabarwa Allah,in umma ta raye Allah ya bayyanata

Minal tace ameen sannan ta dora da ya Allahu,ya rabbi mai sammai da kassai,mai kowa da komai,ina rokanka da sunanka tsarkaka kuma kyawawa,ka kare umma duk take,in tana raye ka bayyanata,inya mutu ya ubangiji ka mata rahama kasadamu da ita a aljannah firdaus,ya ubangiji ya Allah ka nuna ikonka akan mijina ka warkar dashi,kabawa aziza miji nagari wanda zaizamo gatanta nikuma ina rokanka ka dawomin da mijina





Shafa sukayi a tare,yayinda ,aziza ta fara danne danne awayarta,a group dinsu sai hirar prince ake 




Kullum minal cikin kuka take Allah ya dawo mata da mijinta lfy



Kwatsam tana zaune atsakar gida tana zaune ta wanke kayanta ,wani yaro yashigo ya bata wasika ya tafi,karba tayi ta fara karantawa


*daga boyayyen masoyi*


_ki godewa Allah mijinki ya warke_

_garau yake yanzu,sai sunanki yake ta ambata_

_gaskiya yana masifar sonki, sati daya masu zuwa zai dawo,don haka ki dingacin abinci ki maida jikinki,kiyi kwalyar tarbarsa_


Minal bata karasa karanta wasikarba tayi ihun murna,aziza dake chatting ta fito tana tambayar meye faru?



Rungume aziza minal tayi tana wayyo dady kasheni annur ya warke ya warke nanda sati daya zai dawo



Itama aziza cike da murna tace dan Allah kai Allah abin godiya,wayayi wannan sai Allah



Minal tace kwarai kwarai farincikina yadawo amma naso umma tananan



Nan jikinsu yayi sanyi, aziza tace Allah yabamu hakurin jure rashin umma 



Minal tace ameen yar uwa



Minal mikewa tsaye tayi tana ta adu,a dacin abinci tayi kyau,da kiba tayi bul da ita




Saura kwana daya mahaukacin masoyi yadawo,minal anje an shiga saloon anyi gyara,anyi lalle



Tayi masifar kyau,tun dare suka fara toye toye,dama akwai raguwar kudin da boyayyen masoyi yabasu



Minal sai walwala take jira take gari ya waye,amma daren yayi nisa



Aziza sai tsokanarta take amaryar annur ,sai doki kike



Minal tace nadole inyi dokiba  inason in ji muryar mijina,muyi magana mai dadi ta fahimta,mu shaku da juna,annur din da da yanzu ba daya bane;annur din da yaro karami ne but annur din yanzu babban mutum ne mai hangen nesa




Dariya aziza ta sheke dashi tace lalle kam



By

Maryam yarmamat

[12/03 9:33 pm] salmah💍💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*36-40


By

Maryam yarmama

*DEDICATED TO*


_SALMA ALI WADAH_♥






Yau take sallah awajen minal,ta chaba ado cikin wani material mai shegen kyau



Itama aziza taci kwalya cikin wata atampa an kashe dauri


Minal tun safe take zuba idon ganin annur,harta fara fidda rai da zuwansa,harta fara fitar da kwallah

Aziza tace ke meye haka saikin bata kwalyarki?



Kara da horn din mota taji


Hadadden gayene yafito a motar ya nufo gidansu minal



Tsaye yake kekem ,suit ne blue ajikinsa,yayi masifar kyau,

Tashi minal tayi kamar tasha ruwa akasa


Miko mata hannu annur yayi alamun tazo


Kunyane ya rufe minal a hankali ta taho ta shige jikinsa ta fashe da kuka mai tsuma zuciya


Kara maidata yayi ta kwanta luf akirjinsa yace meye haka dear ki daina kuka,ni nakine har abada,gaskiya nayi sa,a Nagodewa Allah daya bani ke



Aziza farinciki ya kamata tace yaya annur sanda zuwa



Shima yana murmushi yace yauwa auntynmu,pls ki hado kayayyakinku,ku raba abincin da kukayi,sauri nake



Ba musu aziza tafara,harhada kayansu,ta wucesu ta kira almajirai ta raba musu abubuwa


Annur ya bude bayan boot din  sabuwar motarsamotarsa yasa kayansu minal,suka kulle gidan,suka zauna shida minal agidan gaba,yayinda aziza ta zauna a gidan baya



Annur ya kalli minal data zubamai ido ko kiftawa batayi,yakashe mata ido daya yace my soulmate kallon ya isa haka ko?



Kunyane ya rufeta ta sunkuyar dakai tana kallon fulawar datayi,kama hannunta yayi,wani yarr taji ,


Bai basa shafa fulawarba yana zuzzuta kyan dayayi,

Hanyar airport suka nufa





Airport suka shiga kwasar gaisuwa aka fara,nan minal tafara shan jinin jikinta





Suna fitowa,annr suka gaisa da pilot din ya saramai,ya rungume minal ta dora kanta akafadarsa,tana tsoron hawa jirgi(😂abinka da sabon shiga)aziza tana biye dasu abaya suka shiga jirgin,suka zauna asit dinsu


Minal sanyi takeji ta kwanta acinyar annur ,annur yace ki tashi ki dora belt jirgi zai tashi



Dora mata belt annur yayi,minal ta kyallesa tace waikai wanene annur *kuma ina zamuje*



Murmushi annur yayi yace asannu zaki gane kiyi hakuri



Aziza tayi shiru tayi jigum,har jirgin yasauka a airport din abujah



Annur ne ya rike hannun minal suna sakkowa daga matattakalar bene,aziza tana biye dasu,wani kyakyawan rug caper dogo aka shinfida ansa *WELCOME BACK PRINCE ANNUR*


Mutane cike a airport din suna tsammanin sakkowarsa,sai watsa fulawa masu kyalli da shekki ,sai busa sarewa da algaita ake masu gangaga nayi



Kusan sumewa minal tayi dataga annur yana daga musu hannu

Mominsa wata kyakyawa hamshakiyar mace ta nufo wajen,da gudu annur ya nufi wajenta yana oh my mum i really miss you


Dadynsa  yayi shaking hands dinsa suka gaisa yace my son congratulation ashe kun cinye gasar kallon kafa aturai,amma prince kayi kokari,yan jarida suna son magana dakai



Momy ta nuna minal tace wanne itace kake bani labarinta taho nan ya ta



Zamewa minal tayi tafadi kasa sumammiya.


Dama annur yaudararta yayi ba mahaukaci bane,dan sarkine?wanda taji labarinsa ya cika gari shararren footballer dinnan




Jama,a kuci gaba da bibiyata labari yanzu akasoma



By

Maryam yarmama[15/03 6:12 pm] Maryam Yarmama: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*41★45

By

Maryam yarmama


*Dedicated to*

_my sweet salma Ali wadah_



_i gave this page to my fans ,thank you for ur support and caring_




Annur cikin sauri ya tarota yana ambaton sunanta ,minal minal ki tashi



Mummy tace kaga sata a mota inmukaje gida awa saudat bayani

Mummy ta kalli aziza dake zare ido tace amma ke yayartace ko wow kunada hankali dafatan zaki zauna a wurina


Aziza tadan ritsina ta gaishe da mom,momy ta kamo hannun aziza,daga bisani akashiga motoci sama da talatin aka nufi katon haddeden estate dinsu annur da ake kiransa da king estate,gate ne ya bude da kansa,motocin suka kutsa kai ciki


Aka budewa annur mota,aka shimfidamai cafet,kuyangi suna watsa fulawa,annur rike yake da minal da har yanzu bata farfadoba




A katon falo akayi masauki wanda fadin haduwar falon nan karyane,yan uwa da dangi suka zauna anata gaisawa da annur,anamai murnar samun mata ta kirki


Saudat ce tashigo daga ita sai dogan riga mai hannun singlet,tayi buzu buzu da gashinta;sai taunar cingum take,


Mamakine ya cikata da taga wata matasshiyar budurwa a cinyar annur,tana bacci,wani uwar ashar ta dibo tace kai annur aina kasamo karuwa ,daga bisani ta kalli mai martaba tace dad kana kallonsa da wata daba tasaba amma kayi shiru shiyasa nace an tsaneni wallahi antsaneni



Tsawa momy ta daka mata tace ke saudat ki shiga hankalinki,kamar yanda kike matar prince annur haka itama take awurinsa don haka kimana shiru kizauna,ko akwai sa,anki anan dakike mana shouting



Ihu saudat ta zunduma ta dora hannu akai tace nashiga uku anci amanata an hadamin munafurci wayyo dadyna



Cikin lallashi mai martaba yace saudat yahakuri ki zauna a warware matsalar nan



Harara saudat ta dakawa mai martaba tace anki azauna din wallahi dolema ya saketa donni ba,ayi ni don in zauna da wata yar talaka ba.



Annur ransa ya bace,amma yasan yana magana mai martaba zai taresa,yayi shiru yana shafa fuskar minal,


Dakyar aka roki saudat ta zauna tana kumbure kumbure da daukar alwashi iri iri



Mai martaba yace son inaso ka bani labarin yarinyar nan yar wacece,aina ka sameta kuma tayaya akayi ka aureta?kasan a tsarin gidannan ba auran yar talakawa ko wata bare ko?



Annur yaja doguwar zuciya yace,lokacin naje kano,don koyawa kano pillars wasan buga kwallo ina cikin motata,na hangeta tana tafiya,binta nayi har kofar gidansu na gani,na nemi labaribta naji,nasamu,tausayinsune yakamani,sai na fito mata a siffar mahaukaci,abin mamaki yarinyar nan bata kyamaceni ba,tanada hangen nasa haka ta aureni,namata abun bacin rai kala kala bata damuba,komai tasamu nawane,haka annur yabasu tarihin minal da yanda mahaifiyarsu ta bata,da yadda rayuwarsu tazama,da zaluncin da abba ya musu



Kuka aka dingayi,har mai martaba,banda saudat data tabe baki sai harare harare take tana magana kasa kasa wayasani ko karyama yake



Mai martaba yace allahu akbar gaskiya yarinyar nan yar kirkice don haka annur ka lura da ita sosai,ita kuma yayarta intana da burin cigabada karatu,saita zabi kasar da takeso ta tafi karatu duk abinda takeson karanta



Nan falon ya dauki tafi da sowa yayinda aziza ta fashe da kukan farinciki,dama akwai ranar da burinta zai cika?na karasa karatunta


Momyce ta rungumota tace yata karki damu wannan kadan daga cikin karamcin king estate house.





Mai martaba yace annur dauketa ku tafi gidanku,inyasa saudat tabiyoku daga baya ,Allah yamuku albarka.


Annur ya dauki minal cak,wani tsalle saudat ta daka tace wallahi ba,a isaba tab,lallema ,wallahi baza,a hadani dayar talakawa ba tab haka kurrum ta shafamin talauci ina.


Bawanda ya kulata,annur ya fita daga falon,bin bayansa aziza zatayi,momy tace a a kidawo daughter bazaiyu ki barni ni kadaiba daga yau kin zama yata tajini



Murmushi aziza tayi ta dawo tazauna akusa da momy tana tunanin ya yar uwarta zata tsinci kanta,i tunda tanason annur yana sonta aishikenan ba damuwa



Ahaka falo ya watse aka bar saudat sai zage zage take,momy tana danasanin auren annur da saudat diyar sarkin gombe





By

Maryam yarmama

[15/03 6:15 pm] Maryam Yarmama: Y *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*46☆50

By

Maryam yarmama


*Dedicated to*

My salmaty





Tukasu ake,motoci bibbiyu gaba da baya,hmmmm jinin sarauta,mai martaba,ne yakira annur yace prince ka shirya gobe akwai hadadden party dana hada muku,donhaka ku shirya

Murmushi annur yayi,yace Allah yaja zamani dad,godiya nake.

A hankali minal ta fara bude kyawawan idonta tana karyata,lamarin anya ba mafarki takeba,yakamata dai ace ta farka,kara bude ido tayi,sanyin a.c din motar ne,yasa jikinta ya fara kyarkyarwa,annur ya ciro suit dinsa yasa lulluba mata


Tashi tayi cikin kunya tace annur meyasa ka yaudareni?meyasa  ka zabi kasamu farin cikinka fiye da nawa why annur,?kamin karya ka dora wa kanka ciwon karya



Annur yace minal nasan ku yayan talakawa ba kasafaffai kukeson auren masu kudiba,shiyasa na taho miki awannan sirfar kuma gaskiya nayi dace nasameki yanda nake bukata,kina da tawwakali,hakuri juriya,kin nunamin soyayya dan Allah,badan kudinaba?kuma saidai kiyi hakuri inada mata masifaffiya yar sarkin gombe ce sunanta saudat,saidai kiyi hakuri da halinta domin gida daya zaku zauna,


Murmushi minal yayi tace Allah ya bamu zaman lfy mai dorewa ,to dan Allah waye *boyayyen masoyin da ya taimaki rayuwarmu dana yar uwata*wlh inason ganinsa inmai godiya,



Murmushi annur yayi yace hmmmmm zagi ganshi watarana .


Minal tace wallahi inason ganinsa,Ubangiji yasamakai da alkhairi,nima in Allah ya yarda saina yimai fiye da yadda yamin




Dariya annur yayi yace ameen my wife


Rufe ido minal tayida tafukayen hannunta,


Wani tafkeken gida gari guda naga an nufa,gate ya bude da kansa,sojojine suke gadin gidan,sai sarawa annur ake,shiko yana daga musu hannu yana murmushi,harabar gidan abin kallone


Wajen ajiye motoci suka yi parking,bude musu akayi,minal ta kalli annur dayake taku daidai tace annur pls ka daina sawa ana budema mota,da kuruciyarka. Za,a dingama hidima yakamata ace komai kanayi da kanka,ba wanda yasan gobe, daukaka daga Allah ne,mulki daga Allah ne, yakan bawa wanda yaso,



Murmushin farinciki annur yayi,har hawaye ya ziraro a idanunsa yace ya Allah nagodema da ka bani minal,minal nagode da tunatar dani da kikayi,



Riko hannunta yayi yasa pasport a kofar dazai sadasu ga general falo,sunan minal ne a falon tafkeke ,a katon glass din hoton da akayi elergiment da sunan minal,minal tacika da mamaki



Haduwa iya haduwa falon yahadu,


Bangarenta annur ya kaita komai lemon green and orange colour ne part din ya mata kyau sosai,wanka ta fada ,tsullum taga annur a bathroom,kara tasaki ta tsuguna ta annur dan Allah ka fita,



Annur ya shagwabe fuska yace uhummm nima nazo anty tamin wanka,anty nifa badan iska bane



Minal dai tana rakube acikin bath tub,amma dariya take kasa kasa,bata ankaraba ya fado bathtub din,wani kara tasaki,



Amma ahaka ya mata wanka tana mammake jiki,ya goyota yana ai my wife yanzu babu kunya atsakinmu mun zama jini daya



Minal ta tuno littafin data karanta na ma,aurata,kissa da kissina dashagwaba



Murmushi tayi tana bayansa daure da tawul,dan cizo ta gantsaramai a kunne,kara yasaki,tazame tafada kan gado tana dariya kanta a sunkuye,


Annur yace taho in shafamiki mai


Hararar wasa tamai tace tab sai kace wata baby anki wayon


Karbar man tayi tanashafawa,ta je wardrobe kaya tagani sunfi miliyan ajere,wani doguwar riga ta hango pink mai adon fari da dankwalinsa sawa tayi,wow yayi masifar kyau ,fadin annur


Gaban katon madubi ta nufa,ta fara tsantsara kwalya,tana kallon annur daya kafa mata ido yana murmushi,martani ta maidamai,tadan sunkuyar da kanta alamun kunyatace dan Allah kaje kasa kayamana annur


Annur ya matawani kallo yace a chanzamin suna in bahakaba zamu shekara anan

Minal a hankali tace to *my husband*




Annur ya noke kai yace a a ba wannanba,


Minaltace to heart beatfa


Annur yace good ficewa yayi daga dakin yaje yasako riga t_shirt shima pink colour da farin wando



Shigowa yayi,minal tace kai yamukayi anko nidakai

Murmushi annur yayi yace aiduk kayan da kike dashi anan gidan inadashi,zo mudanyi hoto mana dear,kamota yayi,suka dinga daukar selfie,sannan ya mata ita kadai,kunyane ya cikata dama haka annur yake da iya soyayya?in Allah ya yarda ba wanda ya isa ya rabani da mijina


Karar fashewar abu sukaji  a general parlour



Minal ta tsorata ainun,annur ko ajikinsa yace zamuje dear nasan bazai wuci mahaukaciyar nan ne tazoba don kadan daga aikinta


Annur ya rungumi minal suka wuce general falo,aikwa saudat ce dauke da katon wuka a hannunta,gashi tayi raga raga da hotan  minal da akayi elergiment da sunanta



Annur yace ke dabbar inace kishi haukane,ko mamanki ita kadaice a gidanku,ai itama alfarmar wata taci



Saudat tace ni kake ciwa mutunci annur ta ubanka mai martaba kake zagi,tsohon najadu,mugu azzalumi



Annur yace zanso saudat ki fadi abinnan agaban mai martaba,yaji dama albarkacinsa kike ci,kuma tunda kika zagarmin mahaifi saina babbalaki a gidannan



Cikin karaji da takama tace bismillah inda jini aka haifeka kazo ka tabani wallahi dagakai har yar iskarnan da kuka gama wattsakewarku a titi sainayi ajalinku


Zuciya tadauki annur da nufin zuwa yawa saudat mugun duka,minal ta rije hannunsa tana kuka tana jijjiga kanka tace dan Allah karkaje,bakaga wuka bane a hannunta kar ruddun shedan yadauke ta yima illah



Annur yace kinga minal sakeni innunawa yar iskarnan kura kurenta



Saudat ta nufo wajen da kudu ta fara jibgar minal,tana yakushinta da dogayen faratanta na kanti,annur ya hankade saudat shima ya dinga jingarta



Kokuwa kakeji ,saudat tana ihu,da kukan saita illata minal,wuka salma ta dauka tana bin minal dashi,sai zagaye falon suke minal taga tashin hankali sai kuka da ihun kiran azizatake 



Annur ne ya sha gaban minal ya boyeta abayansa,yana inkin isa ki kasheni tunda ke mahaukaciyace



Cikin huci saudat tace ka matsamin ko in hadaku tare in kasheku



Da gudu saudat ta nufi wajen ta cakawa annur wuka







By[19/03 11:14 pm] salmah pinky💅🏼💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*51-55

By

Maryam yarmama

Dedicated to

My salmaty






Cikin zafin nama,annur ya rungumi minal suka tsuguna,wukar tabi iska


Ran saudat yabace kamar tayi hauka tace wallahi kayi karya annur kaci amanata kazaba niko ita.



Annur ya wanketa da mari kyawawa guda uku yace nazabeta akan mahaukaciya irinki,aini ko zanyi butulci bai kamata inwa minal rabin rayuwata butulciba tasoni ina mahaukaci banda komai.

Amma kefa na tabbata da kece na rike miki hijab kamar yanda na rikewa minal da tuni zakisa a shekeni bakida asara


Ran saudat yabace cikin bambamin fada tace wallahi inkasan wani bakasan wataba,saina kashe minal din inyaso nima akasheni saime?



Minal dake faman rusa kuka tana bayan annur,annur ya juyo gareta yace masoyiyata kiyi hakuri nan gaba zan raba muku gida kizabi,state din dakikeso in rabamuku gida





Saudat tace a a ba gida zaka raba mana ba ranka zaka rabama asararre rago kawai,aini nazata zakamin tsinannen duka ashe zuciyarka a muce yake irin ta ubankane.



Ritse ido annur yayi dabadan alkawarin daya daukarwa mahaifinsa na rashin dukan yarinyar nanba dasai yaci ubanta da duka kuma ya duki banza abanza.,hannun minal yaja sukabar saudat awajen tana ta zage zage.






Tare suka shiga kitchen ,minal tayi shiru sai hawayene ke tsiyaya a kwaryar idanuwanta ta kalli,annur da fuskarsa alamun damuwa tace annur shikenan mun rabu da aziza kenan?



Annur yace kiyi hakuri karatu zata tafi kasar waje amma ai zata dinga zuwa hutu karki,damu da wannan zancen annur ya kwantarwa da minal hankali tadinga walwala





Ahaka suka dirji amarcinsu cikin jin dadi da kwanciyar hankali,minak tayi fresh tayi kyau,duk hantarar da saudat take mata bata damuba,ko wucewa minal tazoyi sai saudat ta bangajeta tayi wucewarta tana zaginta da nuna kyama a gareta





Minal ce zaune akan dinning,annur ya tafi kasar waje buga ball,tana danne danne wayarta *iphone*tanacin abinci fried rice a hankali,ji tayi an dauki abincin an watsa mata ajiki 


Saudat ce tsaye tace ke yar talakawa jikar talakawa da akwai abinda yafi talauci dana kiraki dashi,anzo an zauna anacin abinda ba,a saba ba ,to ga wankina chan kije kimin





Minal tace zanyi karki damu da wannan but kisani talaka da maikudi duk ubangijin talikaine yayisu,kuma yayimu talakane bawai don baya kaunarmuba,bawanda yafi wani awurin Alllah,sai wanda yafi imani da tsoransa,don haka ki daina nuna bambamci dukanmu yayan adam ne da mamanmu hau,wa,u




Rike baki saudat tayi tace Allah?i see idon mage ta waye donhaka inzakiyi wa,szinki kije chan kofar massallaci ki dauki loudspeaker kiyi zakifi samun lada banza a banza kawai




Haka kullum daban rashun mutuncin da saudat take shukawa har annur ya dawo bata fasa halintaba




By

Maryam yarmama

[19/03 11:14 pm] salmah pinky💅🏼💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*56→60

By

Maryam yarmama


*DEDICATED TO*

SALMA ALI WADAH





®online hausa writters




Minal ce zaune a main parlor tana kallon zee aflam an sako wani film mai dadi yatafi da hankalinta,ji tayi an zagayota bayanta an, rufe mata idanuwa.



Tasan waye murmushi tayi tace nawan harka dawo kenan.



Aziza tace to yar soyayya bashi bane nice nan.



Tsalle minal ta daka tajuyo,cikin murna tace oyoyo yar uwa ashe da rabon zamu hadu kafin ki tafi london?


Murmushi aziza tasaki tace kinsan gobene tafiyarfa shekara bakwai zanyi,kinga lokacin saidai inzo in tadda yarki ko dangi dan shekara shida 




Minal jikinta yayi sanyi tace aziza shikenan nida ganinki sainan da shekaru bakwai sai mai rai.



Aziza tayi murmushi tace meye zaki damu bayan ga farincikinki a kusa,abinki kwadeshem



Dariya minal ta kyalkyale dashi,saudat ce tafito daga shashinta tana tafiyar kasaita,ta kalli minal tace ke yaki kizo ki wankemin inner weaes dina.



Har minal tatashi azixa ta daka mata tsawa ta koma ta tashi taje gaban saudat ta nunata dadan yatsa tace ke ba baiwarki bace ,kuma bakida iko akanta mijinkune yake da iko a kanta bawai ke ba,kuma kisani kinyi nafarko kinyi na karshe karki karasata aiki



Saudat tace keeeeeh kinsan wacece nikuwa au minal din bata baki labarinaba?



Dariya gami da tafi aziza tayi tace tabbas nasanki ke mara kunyace,mai zagin iyaye ,yar rainin,hankali,raina miji,saike,kuma saidai ki nuna mana dukiya that all



Ran saudat yabace tunda take ba wanda yataba jefarta da munanan kalamai sai aziza daga hannu tayi da niyyar dauke aziza da mari,aziza ta yarfar da hannun tace keeee?karki kuskura ki taba lafiyar fuskata inbahaka saikinyi nadama.



Minal cikin kuka tace aziza zoki fice ki tafi banson tashin hankali


Cikeda mamaki aziza ta kalli minal tace minal ina matsayin ysr uwarki kike korata kin zabi ki zauna kita bauta,?





Cikin kuka minal tace eh tunda mijina yanasona aishikenan bazan damuba na rokeki aziza ki tafi banson rigima.



Saudat ta kalli aziza tasheke da dariya tace aike ko mayyace yaci ace kintafi tunda yar uwarki da kuke uwa daya uba daya ta koreki,minal taji zafin kalmar nan amma ba yanda zatayi


Haka tanaji tana gani aziza tadauki jakarta ta nufi hanyar kofa,sai alokacin minal tace aziza,daga mata hanni aziza tayi ta fice daga gidan


Kuka minal take saudat ta kalleta tace malama tashi ba kuka zakiyiba ki tashi kije ki wankemin kayana.




Jiki a salube minal tatashi ,saudat tace tsaya malama anan in dakko miki karki shafamin farar kafa,shiga ciki tayi ta dakko,su kayan abokiti tace ,to gasunan sora amin halin sata don ranar dakikamin wanki breziyana daga aka kawomin daga dubai banganiba kawai nayi shirune,kuma karki wankemin a machine.




Bude baki minal tayi tace nida sabon sharri,haka ta dauki wankin ta nufi bangaren washing machine,tafara zanzage kayan kwayoyin maganin zubar da ciki tagani kala kala,abin yabata mamaki badai saudat zubar da cikin annur tadingayiba,tausayin annur ne yakamata yanda yake matuwar son yara.



Amai taji yataso mata kwararawa tadingayi,nan ta fuskanci tanada ciki,murnane yakamata tana bazata gayawa annur ba harsaiya gane da kansa,kuskure bakinta tayi taci gabada aikinta tana murmushi ya annur zaiyi inyaji wannan batun,



By

Maryam yarmama





Minal ce sai jibgar

[19/03 11:14 pm] salmah pinky💅🏼💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*61→65

By

Maryam yarmama

Dedicated to 

My besty salmaty





*this page is given to my sweet friends, _seemaluv,sunhera,ummy agos,dijah waziri,cwtjiddah,mixx xoxo,asykhaleel,zahrah bukar,autar hajiya and others_*






Minal ce kwance a cinyar annur yana mata tsifa,annur tace my wife wai meye naga saiwani fresh kike kinyi bul bul dake abinki kodai na girba abinda na shukane?



Fari minal tayi da ido tace idon matambayi?



Annur yace haba wife ki gayamin mana har yanzu bakiji wani alert ba.



Minal tace niko naji alert tunda yau watana biyu nayi batan wata


Wani uwar ihu annur ya daka yace dagaske?alhamdudillah dole su mom suji labarinnan,wow mezan siya miki,



Minal ta tabe baki tace zuciyarka nakeso,ina bukatar kulawarka dear,nidai kabari incikinnan yayi kwari saika gayawa duniya ka godewa Allah ma baibani wani wahalaba.



Annur yace tab lalle dole mutafi asibiti yanzu duk likitan daya faramin albishir shi zan bawa kyautar gida bari in kira abokina likita safwan da jiya ya dawo daga london



Jin an ambaci safwan gaban minal ya fadi sai yanzu ta tunada safwan tsohon masoyinta wanda yafara,taimaka musu arayuwa dariyar yake tayi tace Tom Allah ya kawoshi lfy



Annur yace gaskiya dole inmiki wani abu daga yau bake ba aiki acikin gidannan 


Minal tace kaidai da naiman rigima kake sokake in nazo haihuwa insha wahala ,ai ana son mace tadinga exercise




Annur yace banson mussu kiyi abinda nakeso banson ki wahalarmin da babyna.


Karar takalmin saudat sukaji tashigo tanacin cingum kas kas tace annur inada wani magana dakai in bazaka damuba



Annur yace maizai hana ki gayamin anan kinga yanzu ina busy.


Saudat tace auhakane?ta kwalla kira yar labai kashigo.



Wani matashin saurayine yashigo yasha kayan alfarma ya kalli minal yace wa annur  dama wannan matarkace?


Annur yace bangane me kake nufiba mallam matatace ta sunna mana.




Mutumin ya kalli minal yace minal kinci amanata dama baki da aure kike zuwa hotel din danake,muna aikata sabon Allah mukayi alkawarin aure?


Cikin rudu da mamaki minal tace ni?gaskiya to bani bace 



Mutumin yace haba minal abin yaudarace ke da har waya mukayi dake inzo gidanku kina dauke da cikina?


Annur ya tashi tsaye yace what?karyane wannan zancen wallahi karyane na yarda da matata.


Saudat tayi murmushi tace kaito bawan Allah ka nuna mana shaida mugani mana,

Mutumin yace hakane kinyi gaskiya,hotuna ya dakko sama da goma ya mikawa annur.





Hannun annur yana karkarwa ya anshi hotunan,minal ce kwance ajikin wannan mutumin,minalce a club daga ita saidan kanfai da bra,hannunta dauke da barasa,sauran hotunan kuma minal ce da wannan mutumin suna aikata masha,a ,wullar da hoton annur yayi ya zube a kujera yana numfashi sama sama innalillahi wa,innahiraihi  raji,un kalmar da minal take nanatawa daukar hoton tayi taje ta durkusa agaban annur tace mijina wallahi sharrine hadani akeso ayi dakai,wallahi bazan taba cin amanarkaba cikinnan da yake jikina nakane shi kuma wannan bawan Allah bansan shiba karya yakemin



Saudat tace wai borin kunya sharare sharare gashi munga abu baro baro ai saiki rufawa kanki asiri ki  auri mutumin nan tunda yana sonki





Annur rike yake da kirjinsa yana numfashi sama sama,ihu munafurci saudat tasa ta nufi wajen da annur yake kwance tana annur karka mutu ka barni wayyo minal zata kashemin mijina,ritse ido annur yayi shi yasan zafin da yakeji dama ashe saudat ce mutuniyar kirki ashe minal mutum a fuskace?




Tsugune minal take tana rizgar kuka,saudat sai gwalo take mata gami da harara,mutumin yace nidai natafi minal inkin haihu ki bawa mijinki na yafe dan ko yar





Saudat ta rushe da kuka tace ina mijina bazai rike shegeba  ina wallahi



Mutumin yace oho dai nidai kunga tafiyata,fita yayi daga falon minal yayi tafiyarsa





Kukan minal ya tsananta annur yaki magana ya ritse ido ya rasa wani hukunci zai dauka,a hankali ya bude ido 



Ya kalli minal yace minal kinyi daidai duk hallarcin danamiki ki rasa abinda zaki sakamin dashi sai cin amana dabin mazan waje,banyi mamakiba dama ai ance ku yayan talakawa bakuda tabbas ,zan kyaleki har sai ranar da kika haihu sai agwada ko jininane wallahi indai ba jininabane sai na daureki har  karshen rayuwarki,kuma bani bake komai nagidannan ke zaki dingayi 





Saudat bataso hakaba taso ya jibgeta yamata saki uku amma zataga sharri kala kala wannan ma kadan tafara gani


Kuka minal tasa yayinda annur yace minal kitashi daganan bana kaunar ganinki na tsaneki



Kuka mai tsuma zuciya minal tasa hartana tuntube ta nufi dakinta ta dauro alwala tayi sallah da adu,o,i. Da neman mafita da rokan Allah ya bayyana gaskiyar lamari







By

Maryam yarmama

[19/03 11:14 pm] salmah pinky💅🏼💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*66→70


By

Maryam yarmama


*IN DEDICATION TO*

_MY SWEET BERRY SALMA ALI WADAH_






_WANNAN SHAFIN NAKUNE MASOYANA,NAGODE DA ADU,ARKU,SAKONKU YANA ISOWA GARENI AMMA KU DINGASA SUNA DON,INNA GANI NAYI REPLY,AYYUKA SUNMIN YAWA KU DINGA HAKURI DAMU WASU BANA SAMUN DAMAR AMSA MUKU,AMMA INA GODIYA SOSAI KARKU DAMU ZAN LISSAFOKU,CIKIN WANNAN LITATAFIN,DOMIN KUSAN NAGA SAKONKU_





minal ce ke girki a kitchen ,soya miya take saudat tashigo ta mata kallon karamar awaki tace ke jeki ki dakkomin wayata a falo.



Minal tace bari in sauke miyar tunda yayi



Saudat ta. Daka mata tsawa tace ke wanni irin taurin kaine dake kamar akuya zaki wuce ki dakkomin ko sai ranki ya bace

Dasauri minal tawuce yayinda saudat ta yi murmushin mugunta tadauki gishiri ta zuba amiyar tadauki yaji tasa amiyar ta juya


Ba,a dadeba saiga minal tashigo tace aunty banganiba



Saudat tace antyn gidan uwarki wallahi munanan dake saina fitar dake agidannan snatcher kawai.


Jikin minal yayi sanyi,tasauke miyar ,sauke miyar ta zuba duka a kula.ta kashe gas



Wuce saudat tayi ta nufi dinning annur yana zaune yayi tagumi,yana ganin minal ya daka mata harara,

Saudat yagano tanufo wajen sai kwarkwasa take ajiyar zuciya yasaki da murmushi yace gimbiyar mata zoki zauna muci abinci



Zama saudat tayi tana fuskantarsa tace anya zan iyacin abincinnan honey wallahi tashin zuciya nakeji sosai


Zaro ido annur yayi yace da gaske watanki nawa bakiga al,adarkiba



Saudat ta yamutse fuska tace one month kenan.



Wani fusata annur yayi yadaga gabjejiyar salma yana zagaya dinning da ita yana kissing dinta da sumbatu



Saudat dariya take tayi azuciyarta tace kaji sauna uban son yaya to karya nake



Minal ta tsaya tana kallon ikon Allah annur ya daka mata tsawa ke mayya kizuba mana abincin karki lashemin matata


Cikin shagwaba saudat tace eh wallahi honey,


Jiki asanyaye minal tafara zuba musu abincin ta tura musu 



Annur da kamshin abinci ya isheshi yadauki spoon yakai chokali daya ,tufarwa yayi yadauki ruwa yasha ,afusace ya tashi ya shako minal yayi sama da ita ya dire yayi ball da ita yadinga taka ruwan cikinta Allah sarki minal kokarin kare cikinta take,yayinda annur yace dan ubanki kasheni zakiyi duk ciwon zuciyar da kikasamin bai ishekiba



Kuka minal take tatashi da gudu ta nufi  shashinta amatukar galabaice,ta rufo tana kuka 



Annur yace wallahi saikin gand kuranki,cikin kissa da kissina saudat tazo wajrn ta jashi dakinta tana lallashinsa




Washegari saudat tasa aka nemo mata jinin karya,ta shafa a kafafunta ta fadi a falo tana ihu da neman taimako,minal tashigo falon hankalinta atashe tana aunty mai yafaru?

Saudat ta kalleta tace ubankine yafaru taci gaba da ihu da kururuwa

Annur ne yashigo dagudu ya na neman akasi yanda yaga jini na malala ajikin saudat jini nabin kafafunta hankalinsa yatashi badai cikin daya kallafa rai akaiba yazube



Saudat tace wayyo mijina ka taimakeni minal tagama dani tazubarmin da ciki .


Cikin mamaki annur yace agarin ya?


Saudat tace lemo nace takawomin ashe tasa magani aciki ka kaini toilet mijina


Annur yace mutafi asibiti kawai ai wallahi minal dole in kira policawa a daureta tayi sati biyu acell dan ubanta



Mamaki yahana minal magana sai zaro ido take yawunta yakafe




Annur yatashi saudar suka nufi toilet ta gaggayara jikinta tana kukanzubewar jikinta.




Ran annur yakare bacewa yakira policawa akayi arrest din minal data kasa kuka sai kukan zuciya



Ran saudat yayi fari kal ,tanacin karenta ba babbaka,bayan sati biyu saudat ta takurawa annur yaje yayi belling ta 


Saudat har daki ta biyota tace oh su salihai ansha zaman cell

Murmushin takaici minal tayi tace kisani aunty duk abinda kashuka shi zaks girba komin daran dadewa gaskiya zaiyi halinta ko bana numfashi aduniya zamu tsaya agaban Allah yamana hissabi tsakanina dake




Tsawa saudat tadaka mata tace yimun shiru jaka aladiya dabba munanan dake ni yar jinin  sarautace donhaka mu family dinmu ba,a mana kishiya asannu zanfuddaki daga gidan annur in mallake annur da dukiyarsa gabaki daya











Haka minal ta dinga fama a gidan sharrin yau daban nagobe daban har cikinta yakai wata bakwai lokacin damuna ne. kullum cikin yi mata azaba suke,tarame tayi baki ,kullum cikin tunani da damuwa take,ranar tana fitowa daga wanka daure da tawul da katon hijab


Mutumin ranar tagani azaune dagashi sai singlet akan gadonta yace babyna ykk


Cikin mamaki minal tace wai menama bawan Allah kakeson shiga rayuwata




Annur ne yashigo da belt yana dan ubanta ina take saudat tana biye dashi,mutumin yana ganin haka yabi ta dayan gefe yafita aguje



Annur yace lalle minal kin tabbata yar iska to wallahi yau sainamiki abinda bazaki manta daniba





Minal tana kuka tace annur ka yarda dani wallahi bansan wani namiji arayuwataba inbakaiba wallahi bansanshiba



Saukar duka tadingaji ajikinta ihu take gami dagare jikinta,wani wawan duka annur yamata aciki,saudat kokari take a kashe abinda yake cikinta 


Annur yace minal bazan iya zama dakeba nasakeki saki daya 



Minal taji cikinta ya murde wani azababben ciwon mara yakamata,kara tasaki 


Saudat data fuskanci minal nakuda ne yakamata da kissa taja annur suka fita daga dakin suka banko mata kofa




Nakuda mai tsanani minal take tana ihun neman ceto dariyarsu takeji a main falo,haka minal tanajan gwiwa ta je wajen sif tadauki reza din data tanada ,tanajan ciki tanufi toilet sai nishi take


Kaffara tayi jariraya santalelliya ta fado kyakyawa da ita,cancara kuka tadingayi,mahaifa mata fado,minal tagyara jaririyar tadora ruwa zafi tamata wanka tasamata kayan da annur yasiya guda daya tal,awani super market dasukaje

Dama yace a dubai za,akawo kayan jaririyar



Wanka minal tayi,tafara harhada kayanta tana kuka,



Wani zoben gwal tadakko tasawa jaririyar ahannu,ta nanadeta a shawul



Minal ta dauki jaririyarta ta sa mahaifar a leda babba,tagyara dakin tsaf



Tanajin kaunar jaririyar harcikin kogon ranta ta dauketa ko tsinke minal bata dauka gidanba kuka take tazo ta iskesu afalo





Annur dayaji kukan yar ji yayi kamar ya kwaceta ahannun minal danso



Saude ta kalli minal tace ashe an haifar mana shegiya ko shege agida to a kaita gidan ubanta in bata da uba a nufi gidan marayu


Minal tace hmmm saudat kenan burinki yacika nabarmiki gida yanzu meye ribarki ,kaikuma annur sai nangaba zaka gane gaskiya inka shirya nemana saika nemeni kazo ka karbi yarka inkuma ka yafe na rungumi kaddara in riketa.



Tafiya tafarayi,annur jiyake kamar yadawo da ita ya anshi yar



Amma tayi nisa,tafiya minal take a tsakiyar dare shiru,ga hadari ya hadu yayi baki kirin



Kuka minal tasa tana ya Allah ka dubeni da idon rahama ,ya Allah ka taimakemu




Ruwa aka barke dashi tamkar bakin kwarya,jaririyar sai cancara kuka take


Kuka minal take tana adu,ar Allahya kawo musu agaji 



Kwatsam saiga mai adaidaitasau ya haskesu da fitila,tsayar dashi tayi tace gidan marayu zaka kaini



Dasauri tashiga,sai rawar sanyi take ,muryar jaririyar ya dashe takasa kuka da alamu mura ya kamata


Rudewa minal tayi aiko mai adaidaitasan ya nufi gidan marayu da ita ,abakin gate din ya ajiyeta


Shiru tayitana tunanin ina zata samu kudi tabashi ,kamar mai adaidaitasahun yasani yace kibar kudin nasan ke marainiyace ku abin tausayawane



Godiya minal din tayi ta gaishe da securities din tace tanason a kaita office din shugabar gidan marayu




Aiko wani hadadden office aka kaita,wata hadaddiyar matace zaune sanye take da glass tana bawa wasu yara abinci abaki tana musu wasa,dago da kyawawan idanuwanta tayi,ta kafa akan minal tayi murmushi tace sannunki da zuwa baiwar Allah




Ahankali minal ta amsa mata tagaisheta zama tayi 



Matar tace ke wacece meya kawoki gidan marayu





Labarin rayuwarta minal tabata,matar ta dunga zubar da kwallah ta karbi jaririyar tace wa minal daga yau kinzama yata karki damu zan kula dake sosai,zan gayawa duk wandayake gidannan ke yatace ,zan hadaki da kawaye nagari Du husna da khadijah suma marayune




Kuka minaltasaki tana godiya yayinda hajiya mairo takira docton yara akayi treating din jaririyar minal.




Watan minal biyu agidan marayu tacanza ta murmure,hajiya mairo ta maidata tamkar yarta ita take raba abincin marayu,kowa yana bala,in son minal







Wani hamshakin attajiri matashi yazo yana bawa yara dubu goma goma



Minal ce  tafito suda hajiya mairo da sauran shugabannin gidan marayu da niyyar yimai godiya,yar minal da sukawa lakabi da malika tana hannun khadeeja yarinyar ga kyau dashiga rai sai dariya take da wangale baki tana kallon hajiya mairo




Dagowar da minal zatayi abin da kwakwalwarta yakawo mata shine *safwan*tabbas shine tsaye yana rabawa yara kudi ya kara  kyau ya goge 





Shima juyowar dazaiyi da mamaki a fuskarsa yagoge idonsa yace kamar minal masoyiyata nake gani







By

Ur perfect writter

Maryam yarmama[21/03 6:34 pm] salmah pinky💅🏼💍: *🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*71-75

By

Maryam yarmama


*IN DEDICATION TO*


_MY SALMA ALI WADAH_



_*MASOYANA KUYI HAKURI SAKAMAKON SHIRUN DA KUKEJI,KUNSAN SHA,ANIN JIKI DA JINI*_






malikace tafara cancara kuka,ansarta minal tayi ta jijjigata


Tunanin safwan ya tsaya cikin mamaki gami da tsoro da fargaba yace minal badai kinci amanata kinyi aureba,minal ina kikeso insa raina,to mai yakawoki gidan marayu ina umma da aziza?




Ihu minal tasa ta fashe da kuka 


Hajiya mairo tace a a minal meye abin kuka tunda kinsansa saiki bashi amsa,kije wani wuri indai akwai sirri a tsakaninku




Safwan yace tabbas maman marayu akwai sirri a tsakanina nida minal munyi alkawarin aure da ita,kuma nazo naganta da ya'kuma sunyi kama sosai shiyasa abin ya dauremin kai



Hajiya mairo tace kabiyoni office akwai magana,hajiya mairo taja hannun minal dake shesshekar kuka suka nufi office,safwan yana biye dasu





Zama sukayi minal ta zauna a kujerar datake fuskantar safwan malika na sharbar barci acinyar hajiya mairo


Hajiya mairo tace alhaji safwan naji anacema gaskiya minal ta auri dansarki 


Dafe kirji safwan yayi yace nashiga uku minal badai kinci amanataba yazanyi da rayuwata 



Kuka minal tafashe dashi tafara bashi labari har batan umma



Safwan ya zubda kwallah ajiyar zuciya yayi ya durkusa agabanta yace minal dan Allah zaki aureni ?nayi alkawari ni zan zame uban yarnan,zan nuna miki gata zan taimaki rayuwarki zan nemo umma duk inda tashiga 



Kuka minal take tana girgizakai tace bazan iya aurenkaba maza

Macutane .


Hajiya mairo tace haba minal da hankalinki da tunaninki,ki tuna aure ibadane,akwai wanda suka fiki shan wuya,inma baki auri safwanba,ai kuka hadu da wannan dan iskan tsohon mijinki zaiyi takamar shine dama wanda yake sanki



Safwan cikin kalan tausayi yace minal ki tausayamin kin san yau nakai shekara shida inadauke da sonki karkimin haka kitaimakamin kinji



Minal tana kuka tace  safwan nagoge da kaunar daka nunamin,kayi hakuri kozan iya auranka sai malika tayi shekara biyu,kayi hakuri



Hajiya mairo takasa magana itama tana tausayawa minal,hawayene yakefita a idon safwan yatashi yana gogewa yafita yaje yadauka bandir bandir din kudi ya aje a teburin hajiya mairp yace maman marayu ga wannan dubu dari uku ne asiyawa malika madara da dubu dari biyu sannan dubu dari nakine



Godiya hajiya mairo tafara tana shimai albarka


Juyawa yayi da niyyar tafiya muryar minal yaji tace mallam kazo kadauki kudinka bama bukatar taimakon kowa yatace itakadai banson kowa yatabamin ita ni nasan wahalar danasha wajen haihuwarta


Murmushin takaici safwan yayi,yadawo yace,hmmmm minal kenan ashe kinada tsiwa



Minal tace eh inadashi kuma sanadinkune maza .



Safwan yace good ai shedanne yake mayar da hannun kyauta baya nidaina bawa yata bake nabawaba




Sallama sukayi da hajiya mairo,yayinda minal tabishi da harara,hajiya mairo itama yabitada wa,azi





Washegari malika tatashi kowa da kuka,minal tabata nono takisha sai rusa kuka,take anyi lallashi ankaji kukanta sai daduwa yake



Minal itama ta rushe da kuka,hajiya mairo ta ansheta amma sai kara cancara kuka take 




Motar safwan ne ya danno kai,parking yayi  da sauri yafito daga mota




Kukan malika yaji,dasauri yanufi office din da kowa yayi cirko cirko anrasa mai za,a bata tayishiru



Sallama safwan yayi



Amsamai sukayi,dasauri ya anshi malika daga hannun hajiya mairo,cillata yayi sama,ahankali kukan ya ragu ,jijjigata yake yana hura mata kunne,aiko yarinya ta murmusa



Abin yaburge kowa,minal tashagala a da kallon safwan tana inama shine uban malika dataji dadi 


Khadijah ce ta dakkowa safwan kujera yazauna,yakarbi feedern dayake cike da milk yafara bawa malika,harta koshi tafara wasa



Hajiya ta kalli dayar shugaban tace hajiya hanne kinga ikon Allah lalle kam malika tasamu uba





Hajiya hanne tace i wallahi bari in koma bakin aikina tunda uwata tayi shiru,dukansu suka koma bakin aikinsu



Office yarage daga hajiya mairo sai minal da safwan







By

Maryam yarmama

[21/03 6:34 pm] salmah pinky💅🏼💍: ●●●●●●●●●●●●●●●●●●●


*🦁MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI🦁*76★80


By

Maryam yarmama



*dedicated to*

_my salma Ali wadah_←



*®H.O.W*♣


_wannan shafin sadaukarwane ga kawaye na yan *HIQIYA ONLINE WRITTERS*_

_Shugabarmu *billyn abdul,classic feedoh,first lady,salma Ali wadah,eshart saleh,sweet jiddah,sunhera,Allah yakara mana dankon kauna da soyayya ,Allah yarabamu daga sharrin mahassada_







→☆Safwan yace hajiya mairo amin alfarma inaso aban aran minal da malika zanje muwa malika shopping din kaya



Minal ta dakamai harara tace ba inda zani ,kuma wallahi ko kasiyo bazatasaba



Hajiya mairo tace minal indai kin daukeni uwa kije kiyi wanka nizan shirya malika kuje



Jikin minal ne yayi sanyi a hankali tatashi tana gallawa safwan harara,shiko murmushi yake mata tawuce gidan hajiya dake xikin gidan marayu katan gida ne wanda babu abinda babu aciki,tayi wanka tasa atampa,tadanyi makeup maishiga rai,tasanya hijjabinta mai hannu tayi masifar kyau




Mota sukashiga safwan nadauke da malika,minal nabiye dashi sunyi matukar dacewa dajuna



Zama minal tayi agaban mota,maman marayu da sauran kawayen minal da yara suna dago musu hannu,minal ma dago musu takeyi,suka fita daga gidan marayun



Minal sai gunguni take ita kadai ambi an takurawa mutum saikace shi kadaine,



Safwan yace hmmm matata kina burgeni wallahi zanso muyi aure mu tallafi rayuwar yarmu malika



Minal tadakamai harara tace minal ba yarka bace yatace,gwandama kayi shiru kadaina zancenta


Safwan yadanyi dariya yace amma tafisona kuma dazu kinga example.



Shiru minal tayi  har akaje tafkeken shop mall dinnan wanda sai dan wane da wanene ke shiga mall din M&H & UMMAH SHOPPING MALL


Safwan ne yafaka mota,yafito anata chaje mutane ,amma shi dayazo wucewa security suka dinga risinawa suna kwasar gaisuwa


Safwan yace minal yakikaga shoprite dinnan



Tabe baki tayi tace yayi kyau mana aiko makawo yashafa yasan kyanshi balle ni



Dariya safwan yayi yace yanzu in akace nakine yazakiyi ?


Minal takara tabe baki tace zanji dadi in taimaki marayu


Safwan yace to minal dawowana nigeria nagina shoprite dinman danaje gidanku naga anzamr dashi tafkeke nayi tambaya bawanda yace yasan inda kuke,nayi kuka da bakinciki,shine nazo abuja nagina shoprite mall mai sunanku nayi alkawari duk randa na ganku yazama mallakinku dake da ummah da aziza yanzu shoprite dinman ya habaka,bankinki dana bude muku shima yahabaka,har kamfanin motoci da gidan  gona na bude muku,gashi ana ana siyar muku da gwala gwalai akasar waje ,kudin dayake bankinku,har jikkokinki sai sun mallaka,kuka duk acikin shoprite dinnan kuka samu daukaka yanzuma shirein bude muku asibitoci nake



Hawaye ne zirara suka fara zuba a idaniyar minal tarasa kalmar dazatayi amfani dashi



Safwan yadanyi gaba yace karkice komai banson godiyarki,ya miko mata hankerchief mai bala,in kamshi yace gashi ki share hawayenki kar mushiga ma,aikatanki su rainaki.



Dariya minal tayi,suka shiga katon short din bangare bangarw suna zagawa,malika tana kafadar safwan minal nabiye dashi,ma,aikata sunata aikinsu da kwasar gaisuwa,harda cinema da katon restaurant da wajen ice cream da wajen wasan yara a shoprite din



Su annur ne saudat suka shigo,minal tana wa annur magana,safwan yana waya,minal ta juya tana kallon kaya,ba abinda babu aciki

Malika tasaki kuka,annur ne yajiyo yakalli safwan sukayi musahaba yace a a abawa uwarta mana,kasan niko inason yara


Saudat tace eh wallahi dama kubamu


Minal takasa juyowa sakamakon muryar annur dataji wanda yanzu tafi tsana aduniya shi yakewa safwan magana.


Cikin harzuka ta dauki wata riga maikyau tajuyo  tana yake tayi kamar bataga annur ba tacedarling kaga wannan rigar zaiwa babynmu malika kyau.





Annur ya cire gilashin dake manne a idonsa da mamaki akan fuskarsa yace you?minal dama kinanan


Minal ta kallesa ido cikin ido tace mallam bansankaba kai waye dazakamin magana?



Annur yace annur nefa minal dama yar dake hannun wannan yatace bansaniba?



Saudat tayi rau rau da ido nan take taji kaunar kyakyawar jinjiran ya shiga ranta(Allah da iko,to kwalelenki) yayinda minal tace au har wani yarka kake kiranta? ta nuna safwan to ga uban daya dace da ita ,shine mijina,wanda yasadaukar da rayuwarsa akan malika,kai ko kunyar fadar cewa yarkace bakajiba




Annur yace wallahi sai anban yata ko mutuwa zakiyi saina karbi yata


Safwan mamaki da kishi suka cikashi fal ,ji yayi minal takamo hannunsa tana honey zomubar nan mahaukacine ,wani shock safwan yaji ya kankame malika sosai bayason kowa yarabashi da ita



Shan gabansu annur yayi yana zakuban sana kosaina kwata da karfi 


By

Maryam yarmama



Post a Comment

0 Comments