KIBIYA RATSA MAZA!!!
Littafi Na Biyu (2)
Part A
A CAN BAKIN DAJIN TSAUNIN
LAUHUL-FARRAS
kuwa runduna ce ta sarakai,matsafa
,jarumai da
manyan bokayen duniya suka kakkafa
sansani
tsubi tsubi a wurare dabn
daban.Kowace runduna
ta fito ne domin farautar Jaruma Safirat
ta kasheta
sannan ta rabata da wannan baka data
dauko a
kan tsaunin Lauhul Farras.Wannan
shine kura da
shan bugu gardi da kwashe kudi.Daga
cikin
rundunar sarakan da suka zo har da
sarki Safwan
tare da dakarunsa na yaki mutum dubu
goma
kuma suma sun kafa sansaninsu wanda
shine mafi
kusanci da tsibirin Lauhul
Farras.Lokacin da rana
ta fadi ne sarki Safwan tare da
shugaban
dakarunsa wani barde da ake kira
Barha na tsaye a
bakin tantin sai sarki Safwan ya dubi
Barha yace
amma nayi mamakin abinda yasa har
yanzu Safirat
bata fito ba daga cikin wannan daji na
tsibirin
Lauhul Farras.Koda jin haka sai Barha
yayi gyaran
murya yace haba ya shugabana ai bai
kamata kayi
mamaki ba tunda ka sani cewa babu
wani
mahaluki daya taba hawa kan tsaunin
Lauhul
Farras ya sauko kasa a raye.Babu
mamaki itama ta
mutu ne a lokacin hakan.Sarki Safwan
ya girgiza
kai yace Safirat bata mutu ba kuma nayi
bincike a
cikin madubi tsafina naga cewa zata
rayu bisa duk
irin gumurzun da zatayi da dakarun
dake kan
tsibirin har ta sami nasarar dauko
wannan
sihirtaccen baka na mahaifinta.Sa'adda
barde
Barha yaji wannan batu sai yayi ajiyar
numfashi
sannan ya dubi sarki Safwan cikin
alamun tsananin
damuwa da karayar zuciya yace ya
shugabana
yanzu dai da idanunka kaga runduna
sama da
guda arba'in a bayanmu ta manyan
sarakan
duniya,matsafa da jarumai masu ji da
kansu.Yanzu
koda ka sami nasarar kashe Safirat ka
dauko
wannan baka dake hannunta ta yaya
zamu iya
ficewa daga cikin dajin nan da bakan ta
gaba
wadannan miyagun rundunoni alhalin
suma abinda
suka zo farauta kenan?Dajin wannan
batu sai sarki
Safwan ya bushe da dariya.Al'amarin
daya kara
baiwa barde Barha mamaki kenan.Daga
can sai
sarki Safwan ya hade fuskarsa yace ai
raba Safira
da wannan baka yafi tsare bakan
wahala.Duk
wadannan rundunoni da kake gani na
banza ne
muddin daya daga cikinsu bata rigamu
karbar
bakan ba.Bisa wannan dalili ne yasa
kaga ni nayi
kundunbala nazo daf da bakin dajin
tsaunin Lauhul
Farras saboda ya zama nawa da zarar
Safira ta fito
ya kasance nine mutum na farko da
zatayi arba
dashi.Ninasan cewa indai zamuyi GABA
DA GABA
da ita to saina rabata da bakan tunda
bata finin
KARFIN DAMTSE ba dana tsafi kuma
bata fini iya
yakio ba.Duk abinda take takama dashi
nima ina
dashi ko mafiyinsa.Kuma muna haduwa
zan shaida
mata cewa ubanta ne ya kashe
mahaifina don haka
ina son na dauki fansa a kanta,kaga
bata da ikon
cewa naci amanar soyayyarta.Kao bari
na gaya
maka gaskiya,koda Mahaifinta bai
kashe nawa ba
zan iya zuba idanu ba ina kallonta ta
fini matsayi
ba da daukaka tunda nine sarkinta.Dole
ne ka
kawar da batun soyayya na ceci
mulkina da kasata
tare da duk al'ummata.Babu sani ba
sabo a
tsakanina da Safira saidai KAIFIN
TAKOBI ya
rabamu.A yanzu haka ina zargin cewa
Safirat zata
iya fakar numfashinmu ta fito daga cikin
dajin
Lauhul Farras a cikin wannan dare ta
sulale ta
gudu ba tare da wani ya gantaba.Koda
jin wannan
batu sai Barde Barha ya gyada kai cikin
alamun
shakku yace haba ya shugabana ta
yaya Safirat
zata iya wucewa ta gabanmu ba tare da
ka ganta
ba tunda bata da wani sihiri na bata
wanda baka
da shi.Nidai kawai shawarar da zan
baka itace
kada ka kuskura kace zakayi bacci a
cikin daren
nan domin ta bakin kane a ko yaushe
zata iya
fakar numfashi ta fito din.Koda jin haka
sai sarki
Safwan yayi murmushi yace tabbas
maganarka
dutse ce.Dole ne hakura da bacci gaba
daya a
daren yau.Ai kuwa sarki Safwan bai
yarda ya kara
shiga cikin tantinsa ba.Kujera aka kawo
masa ya
hau ya zauna a waje yana mai fuskantar
cikin dajin
tsaunin Lauhul Farrs kuma takobinsa
nakan
cinyarsa ya dafeta da hannunsa guda
sannan kuma
yasa wata kuyangarsa ta dafa masa
shayi aka zuba
masa sinadaron hana bacci a ciki
yasha.Har gefen
asuba idanun sarki Safwan a bushe
suke ko
alamar bacci babu a tare dashi.
*Al'amarin Jarum Safirat kuwa tunda ta
kwanata a
cikin tantinta ta kama bacci ko
kyakkyawan motsi
bata sakeyi ba har asuba tayi.Kawai sai
ji tayi ana
tashinta kamar a mafarki.Safirat ta
mike tsaye
Zumbur a dan firgice.Tana bude
idanunta sai taga
ashe Bandaru ne tsugune a gabanta
kansa
sunkuye don biyayya.Ba tare daya dago
kansa ba
ya dubeta yace ya shugabata yanzu ne
daidai
lokacin daya kamata ki shirya ki fice
daga cikin
dajin nan ki durfafi hanyar da zata kaiki
can Dajin
Sarkif domin ki isa kogon mutuwa don
dauko
kuttun kwarinki.Kamar yadda na gaya
miki a baya
cewa masifar dake cikin dajin Sarkif ta
ninka wacce
ke cikin wannan daji namu sau goma
don haka
saiki jajurce kuma kiyi matukar juriya da
hakuri.Duk tarin rundunonin makiyan da
suka
biyoki izuwa nan ba zasu iya binki ba
izuwa dajin
Sarkif amma ina zargin cewa mutum
daya zai iya
binki.Koda Bandaru yazo nan a
zancensa sai
Jaruma Safirat ta tari numfashinsa tace
nasan
kowane ne ba wani bane face sarki
Safwan babban
masoyina a da yanzu kuma babban
makiyina.Koda
jin haka sai Bandaru yayi murmushin
murna yace
ina farin ciki da kika fahimci hakan duk
da cewa
har iyanzu nasan zuciyarki tana miki
wasu wasi
akan hakan.Amma dai na san cewa
lokaci zai
tabbatar miki da gaskiyar alamari.A
yanzu haka
tuni dakaru arba'in da nayi miki
alkawari sun gama
shirin tafiya ke suke jira.Kamar yadda
na gaya miki
a baya,kada ki fita daga cikin dajin nan
goye da
bakanki tsirara face kin lullubeshi cikin
mayafi
saboda hasken sane zai fara
™Abubakar Haleefah Physicist™
tona miki asiri.Yanzu ga mayafin da
zaki lullube
bakan na kawo miki.Nan take Bandaru
ya daga
hannunsa sama saiga wani bakin
mayafi ua
bayyana tsulum a hannun nasa kawai
sai ya mika
mata ta karba yace wannan ne kadai
mayafin da
zai iya boye hasken wannan kwarin
naki.Maza ki
lullubeshi yanzu.Ba tare da wata
gardama ba kuwa
sai Safirata ta mike tsaye ta ciro Bakan
daga
bayanta wanda ta daureshi tamau
kuma ta kwanta
a kansa tayi bacci tun a daren
jiyaSafirat na ciro
bakan sai ta lullubeshi da wannan
mayafi.Nan take
kuwa taga hasken nasa ya bace
bat.Cikin sauri ta
mayar da bakan bayanta ta goyashi
kuma ta
daureshi tamau.Faruwar hakan keda
wuya sai
Bandaru ya sake daga hannunsa guda
sama saiga
wani takalmi fade na fatar damisa ya
baiyana
tsulum akan hannun nasa.Kawai sai ya
mika mata
yace ungo wannan ki sanya a
kafafunki.Indai har
da wannan takalmin a kafarki babu
yadda za'ayi
wani yaji sautin tafiyarki ko
gudunki.Abinda nakeso
dake shine daga nan ke da dakarun
dana baki
guda arba'in zaku fice da gudun tsiya
ku nufi
arewa nan ne hanyar da zata kaiku
izuwa dajin
Sarkif.Kiyi gudu iya karfinki da
iyawarki.Ta gaban
makiya zaku wuce amma babu mai iya
cimmaku
saidai a riskeku a can dajin Sarkif inda
kowa zai
shiga cikin tararrabin rayuwarsa.Ni
kaina ba zan
baku tabbacin cewa zaku tsira da
rayuwarku ba
acan.Da wannan furuci nake yi miki
bankwana
yake sarauniyar Duniya ta gobe.Kuma
inayi miki
fatan sa'a da nasara bisa wannan
gagarumin aiki
dake gabanki.Ina fatan zaki zamo mai
cika alkawari
a gareni bayan bukatarki ta
biya.Bandaru na gama
fadin hakan saiya juya domin ya fice
daga cikin
tantin amma sai Safirat ta kira sunansa
da sauri
tace nagode bisa duk irin wannan
taimako da ka
bani kuma lallai zan zamo mai cika
alkawari a
gareka.Koda jin haka sai Bandaru yayi
murmushi
ya fice.Fitarsa keda wuya sai itama
Safirat tayi yan
kintse kintsenta kuma ta sanya
wadannan takalma
da Bandaru ya bata sannan ta fice da
sauri daga
cikin tantin.Tana fitowa tayi arba da
wadannan
dodanni guda arba'in.Kowannensu ya
goya jakar
guzurinsa a gadon bayansa sai kace
sun kasance
mutane ba dodanni ba.Al'amarin daya
baiwa
Safirat dariya kenan yayi
murmushi,kawai sai ta
juya ta nufi arewacin dajin ta dagawa
dodannin
arba'in hannu tana mai yi musu inkiyar
su biyo
bayanta.Nan fa Safirat ta falfala da
azababben gudu
izuwa cikin dajin dodannin arba'in na
rufa mata
baya suma sunayin gudu na ban al'ajabi
don har
tashi sama sukeyi saboda karfin gudun
nasu.Amma duk da haka Safirat ta
basu yar tazara.
*** A*H*P ***
Sarki Safwan na zaune akan kujera ya
zuba idanu
izuwa cikin dajin Tsaunin Lauhul Farras
a lokacin
da alfijir ya keto sai ya fara
gyangyadi.Nai ankara
ba sai baccin ya kwashe shi gaba daya
har da
minshari.Ashe suma sauran rundunonin
da suka
fito farautar Safirat basuyi bacci ba da
daddare.Abin kamar hadin baki sai
suma suka
kama gyangyadi a wannan lokaci da
alfijir ya
keto.A sansanin sarki Safwan barde
Barha ne kadai
baya yin bacci a wannan lokaci saboda
a daren
jiya kwanciya yayi ya hantse
abinsa,amma gaba
dayan sauran dakaru da hadimansa da
kuyanginsa
duk bacci sukeyi.Koda Barde Barha
yaga kowa
bacci yakeyi hatta sarki safwan kuma
shi kadai ne
idonsa biyu sai hankalinsa ya
DUGUNZUMA
saboda tsoron kada jaruma Safirat ta
fito a daidai
wannan lokaci daga cikin dajin Lauhul
Farras
saboda yasan cewa shi kadai bazai iya
cimmata ba
ya tare ta.Sannan kuma sai yaji tsoron
kada ya
tashi sarki Safwan daga bacci ya zamo
ya aikata
lafin katse masa baccinsa.A karon
banza ya
fuskanci hukunci mai tsananin.Nan fa
barde Barha
ya kama kai kawo a gaban sarki Safwan
wanda ke
fama sharar bacci akan kujera yana
tunanin abinda
zai fishshe shi.Kwatsam sai barde
Barha yaga
giftawar wani abu shuu!Ta gabansu
tamkar giftawar
tauraruwa mai wutsiya.Kafin ya juyo
yaga ko mene
ne tuni Jaruma Safirat da dodanninta
guda arba'in
sun bazu tazara mai yawan
gaske.Barde Barha ya
wangame bakinsa ya kuma ya takarkare
ya kurma
wani uban ihu mai tsananin kara da
firgitarwa.Take
sarki Safwan da sauran dukkanin
jama'arsa suka
farka firgigit a dimauce.Sarki Safwan ya
zare
takobinsa koda ya kallo gabansa sai ya
hango jelar
daya daga cikin dodannin kan tsaunin
Lauhul
Farras ta kule izuwa cikin daji.Kawai sai
sarki
Safwan ya falfala da masifaffen gudu
izuwa
arewacin dajin domin ya gane cewa
Safirat ce tazo
ta giftasu yana bacci.Nan yake kuwa
Barde Barha
da sauran dakaru suka ruga suka hau
dawakansu
suka bi sawun sarki,su kuwa hadimai
da kuyanci a
firgice suka shiga hada kaya sannan
suma suka bi
sawu.Kamar yadda su Jaruma Safirat
suka gifta su
sarki Safwan suna bacci haka suka
gifta sauran
sansanin na sarakai,jarumi da
matsafa,sai bayan
sun wuce sannan ake farga dasu a bi
bayansu.Nanfa aka kasa uban tsere a
tsakaninsu
ba sassauci.Amma aka rasa wanda ma
zai kusanci
su jaruma Safirat.Sai gashi mutum
daya jal yazo
yana ta wuce jarumai,matsafa da
sarakai rike da
zabgegiyar takobi a hannunsa.Nan da
nan ya
baiwa kowace runduna tazara mai
yawan gaske har
ya bace musu bat da gani saboda
masifaffen
gudun da yakeyi amma duk da haka
shima da
kyar yake iya hango dodo na karshen
baya daga
cikin dakarun Jaruma Safirat masu
tsaronta.Haka
dai aka cigaba da tseran gudu tsakanin
su jaruma
Safirat da sarki Safwan tun daga fitowar
alfijir har
rana ta take a sannan ne kowa ya gaji
ainun.Tsananin yunwa da kishirwa suka
addabesu.Amma saboda naci anki a
daina
gudu.Safirat da dakarun nata har
tangadi sukeyi
kamar zasu fadi kasa.Shima sarki
Safwan
haka,wani lokacin ma har faduwa
yakeyi amma
kuma har a san
™Abubakar Haleefah Physicist™
nan takobinsa na hannunsa bata
subuce masa
ba.Ana cikin wannan hali ne Safirat taga
uku daga
cikin dodanninta sun sare sun fadi kasa
suna haki
kamar ransu zai fita,kawai sai ta
sharesu ta cigaba
da gudunta abinta suna kara yin dan
gaba sai
dodannu biyar suka sake sarewa suma
suka zube
kasa.Faruwar hakan keda wuya sai
hankalin
Jaruma Safirat ya dugunzuma domin ta
fahimci
cewar indai aka cigaba da gudun a
haka to za'a
kai munzalin da zata rasa gaba dayan
dodanni,alhalin kuma tasan cewa akwai
lokacin da
zasuyi mata matukar amfani.Bisa sa'a
kuwa sai
Safirat ta hango wata fadama(korama)
a gabansu
kadan.Cikin farin ciki ta karasa gaban
koramar ta
tsuguna ta jika kanta ta sha ruwa.Ai
kuwa sai
suma sauran dodannin suka rugo izuwa
cikin
fadamar suna murna suka kama shan
ruwan.Adaidai wannan lokaci ne Safira
taji takun
sawu da gudu an tsaya a bayansu.A
nutse Jaruma
Safirat ta mike tsaye ta juyo a hankali
saboda
dama tasan wanda ke biye dasu din.Ai
kuwa tana
waigowa tayi arba da sarki Safwan a
tsaye rike da
sharbebiyar takobinsa yana haki kamar
ransa zai
fita.Ga tsananin kishirwa na
damunsa,lebansa ya
bushe sai kallon wannan ruwa na cikin
fadamar
yake.Nan fa aka fara kallon kallo
tsakanin sarki
Safwan da jaruma Safirat.Kawai sai
dodannin suka
yunkura zasu kaiwa sarki Safwan
farmaki amma sai
jaruma Safirat ta daka musu tsawa tace
wannan
yaki ba naku bane shi kadai ya iso nan
don haka
mutum daya ne zai yakeshi kum NI CE!
Koda gama
fadin hakan sai jaruma Safirat ta cire
battar
ruwanta daga kwankwasonta ta
tsomata cikin
fadamar ta cikata da ruwa sannan ta
tsuke bakinta
ta cillawa sarki Safwan ya cafe.Dama
tazarar dake
tsakaninsu bata wuce taku ashirin
ba.Safira ta dubi
sarki Safwan a lokacin da hawaye ya
subuto mata
cikin tsananin takaici tace bazan yaki
masoyina a
lokacin da yake jigace ba,kasha ruwa
ka gusar da
kishinka.Koda jin haka sai sarki Safwan
ya bude
battar ruwan ya kafata a bakinsa ya
kama
kwankwada har saida ya koshi sannan
yayi jifa da
ita.Ya dubi Safirat fuskarsa a murtuke
tamkar yana
kallon kumurcin maciji mai shirin
saransa.Har ya
budi baki zaice wani abu sai ta tari
numfashinsa
muryarta tana rawa tace ashe zaka iya
sayar da
soyayyarmu saboda abin duniya?Ina
kaunarmu da
amanar dake tsakaninu?Shin laifin
mahaifina ne ya
shafeni har da kakeson ganin bayana?
Koda sarki
Safwan yaji wadannan tambayoyi sai
zuciyarsa ta
karaya kuma kunya ta kamashi sannan
hawaye ya
zubo masa shima ya budi baki cikin
rawar murya
yace,yake Safirat ki dauki
soyayyarmu,kaunarmu,
shakuwarmu da kuma amanar dake
tsakaninmu
tamkar wani abu daya faru a mafarkin
daya shude
tuntuni a baya.Ki sani cewa a halin
yanzi bani da
wani abokin gaba wanda ya fiki domin
mahaifinki
ne ya kashe ubana kinga dole ne na
dauki fansa
akanki.Abu na biyu dole ne na rabaki da
wannan
KWARI DA BAKA naki domin ceto
Rayuwar kasata
da jama'ar da kuma mulkina.Idan harna
barki kika
mallaki wannan kwari da baka tofa sai
duniya gaba
daya ta koma hannun mata.Sai maza
su koma
hannun bayin mata.Kinga kuwa duk
ranar da
mulkin duniya ya koma hannun mata sai
komai ya
lalace.Zaman lafiya da kwanciyar
hankali sun rushe
kenan.Saboda haka yanzu bani da wani
zabi
wanda yafi na kashe ki na dauke
wannan baka
tunda gaba daya sarakai,jarumai da
matsafan
duniya hankalinsu na kan baka.Kafin
sarki Safwan
ya gama rufe bakinsa tuni Jaruma
Safirat ta daka
masa tsawa tace kaje ka binciki
mahaifiyarka kace
kana son ta gaya maka ko wanene ya
kashe
ubana.To ka sani cewa ubanka ne ya
siye
amintacciyar baiwar ubana ta zuba
masa guba a
shayinsa.Shin rama cuta ga macuci
laifi ne?Hatta
uwata bata san nasan wannan sirri
ba.Koda jin
wannan batu sai jikin sarki Safwan ya
sakeyin
sanyi a karo na biyu.Amma sai
zuciyarsa ta
kekashe ya sake murtuke fuskarsa
yana mai gyara
tsayuwa alamar cewa a shirye yake a
gabza
yakin.Koda ganin haka sai Hawaye ya
sake
subutowa Safirat tace tabbas yau ne na
tabbatar
da cewa NAMIJI BA DAN GOYO
bane,kuma namiji
butulu ne!Idan har nayi nasara kanka
kuma na
sami nasarar dauko tuttun kwari na,na
rantse da
jini ubana saina sa gaba dayan mazajen
duniya
sun zubar da hawaye.Sai na sauke
gaba dayan
sarakunan duniya daga kan karagarsu
ta mulki na
dora mataye akai.Sai kowace matar
aure ta daina
kwanciya a kasan mijinta,sai dai a
samansa.Sannan sai kowace mace ta
daina dafawa
mijinta abinci tare da yi masa sauran
hidima,saidai
shi yayi mata ya zamo bawanta.Saina
maishe da
dukkan mazajen duniya tamkar
karnukan farautan
mata sai yadda suka so zasu
sarrafasu.Safirat na
gama fadin haka sai ta dubi dakarun
dodanninta
tace dasu ko sarki Safwan zai samu
nasarar
kasheni kada ku tayani yakarsa.Duk
wanda ya
tayani yakarsa zan kasheshi da
hannuna.Nan take
Jaruma Safirat ta zare takobinta ta ruga
izuwa kan
sarki Safwan tana mai kwarara uban ihu
da
kururuwa,takobinta na kartar kasa tana
tashin
kura.Suna haduwa suka kacame da
wani masifaffen
yaki mai tsananin ban tsoro da ban
al'ajabi.Nanfa
suka rinka kaiwa junansu sara da suka
cikin bakin
zafin nama,juriya da bajinta.Su kuwa
wadannan
dodanni sai suka zuba musu idanu
kawai suka
zama yan kallo saboda tsoron saba
umarnin
jaruma Safirat.
Toofah!!Nima ganin ana wannan
masifaffen yaki
yasa na tsaya domin na more kallo.
Don't just read and pass,Commenting
and Liking Necessary.
A yanzu ne labari ya fara dadi fiye da
08161272634
KIBIYA RATSA MAZA 🎿
Littafi Na Biyu (2)
Part B
Post
By :----Man Bash ----
Ana cikin wannan hali ne Safirat taga uku daga
cikin dodanninta sun sare sun fadi kasa suna haki
kamar ransu zai fita,kawai sai ta sharesu ta cigaba
da gudunta abinta suna kara yin dan gaba sai
dodannu biyar suka sake sarewa suma suka zube
kasa.Faruwar hakan keda wuya sai hankalin
Jaruma Safirat ya dugunzuma domin ta fahimci
cewar indai aka cigaba da gudun a haka to za'a
kai munzalin da zata rasa gaba dayan
dodanni,alhalin kuma tasan cewa akwai lokacin da
zasuyi mata matukar amfani.Bisa sa'a kuwa sai
Safirat ta hango wata fadama(korama) a gabansu
kadan.Cikin farin ciki ta karasa gaban koramar ta
tsuguna ta jika kanta ta sha ruwa.Ai kuwa sai
suma sauran dodannin suka rugo izuwa cikin
fadamar suna murna suka kama shan
ruwan.Adaidai wannan lokaci ne Safira taji takun
sawu da gudu an tsaya a bayansu.A nutse Jaruma
Safirat ta mike tsaye ta juyo a hankali saboda
dama tasan wanda ke biye dasu din.Ai kuwa tana
waigowa tayi arba da sarki Safwan a tsaye rike da
sharbebiyar takobinsa yana haki kamar ransa zai
fita.Ga tsananin kishirwa na damunsa,lebansa ya
bushe sai kallon wannan ruwa na cikin fadamar
yake.Nan fa aka fara kallon kallo tsakanin sarki
Safwan da jaruma Safirat.Kawai sai dodannin suka
yunkura zasu kaiwa sarki Safwan farmaki amma sai
jaruma Safirat ta daka musu tsawa tace wannan
yaki ba naku bane shi kadai ya iso nan don haka
mutum daya ne zai yakeshi kum Nice Koda gama
fadin hakan sai jaruma Safirat ta cire battar
ruwanta daga kwankwasonta ta tsomata cikin
fadamar ta cikata da ruwa sannan ta tsuke bakinta
ta cillawa sarki Safwan ya cafe.Dama tazarar dake
tsakaninsu bata wuce taku ashirin ba.Safira ta dubi
sarki Safwan a lokacin da hawaye ya subuto mata
cikin tsananin takaici tace bazan yaki masoyina a
lokacin da yake jigace ba,kasha ruwa ka gusar da
kishinka.Koda jin haka sai sarki Safwan ya bude
battar ruwan ya kafata a bakinsa ya kama
kwankwada har saida ya koshi sannan yayi jifa da
ita.Ya dubi Safirat fuskarsa a murtuke tamkar yana
kallon kumurcin maciji mai shirin saransa.Har ya
budi baki zaice wani abu sai ta tari numfashinsa
muryarta tana rawa tace ashe zaka iya sayar da
soyayyarmu saboda abin duniya?Ina kaunarmu da
amanar dake tsakaninu?Shin laifin mahaifina ne ya
shafeni har da kakeson ganin bayana?Koda sarki
Safwan yaji wadannan tambayoyi sai zuciyarsa ta
karaya kuma kunya ta kamashi sannan hawaye ya
zubo masa shima ya budi baki cikin rawar murya
yace,yake Safirat ki dauki soyayyarmu,kaunarmu,
shakuwarmu da kuma amanar dake tsakaninmu
tamkar wani abu daya faru a mafarkin daya shude
tuntuni a baya.Ki sani cewa a halin yanzi bani da
wani abokin gaba wanda ya fiki domin mahaifinki
ne ya kashe ubana kinga dole ne na dauki fansa
akanki. Abu na biyu dole ne na rabaki da wannan
KWARI DA BAKA naki domin ceto Rayuwar kasata
da jama'ar da kuma mulkina.Idan harna barki kika
mallaki wannan kwari da baka tofa sai duniya gaba
daya ta koma hannun mata.Sai maza su koma
hannun bayin mata.Kinga kuwa duk ranar da
mulkin duniya ya koma hannun mata sai komai ya
lalace.Zaman lafiya da kwanciyar hankali sun rushe
kenan.Saboda haka yanzu bani da wani zabi
wanda yafi na kashe ki na dauke wannan baka
tunda gaba daya sarakai,jarumai da matsafan
duniya hankalinsu na kan baka.Kafin sarki Safwan
ya gama rufe bakinsa tuni Jaruma Safirat ta daka
masa tsawa tace kaje ka binciki mahaifiyarka kace
kana son ta gaya maka ko wanene ya kashe
ubana.To ka sani cewa ubanka ne ya siye
amintacciyar baiwar ubana ta zuba masa guba a
shayinsa.Shin rama cuta ga macuci laifi ne?Hatta
uwata bata san nasan wannan sirri ba.Koda jin
wannan batu sai jikin sarki Safwan ya sakeyin
sanyi a karo na biyu.Amma sai zuciyarsa ta
kekashe ya sake murtuke fuskarsa yana mai gyara
tsayuwa alamar cewa a shirye yake a gabza
yakin.Koda ganin haka sai Hawaye ya sake
subutowa Safirat tace tabbas yau ne na tabbatar
da cewa NAMIJI BA DAN GOYO bane,kuma namiji
butulu ne!Idan har nayi nasara kanka kuma na
sami nasarar dauko tuttun kwari na,na rantse da
jini ubana saina sa gaba dayan mazajen duniya
sun zubar da hawaye.Sai na sauke gaba dayan
sarakunan duniya daga kan karagarsu ta mulki na
dora mataye akai.Sai kowace matar aure ta daina
kwanciya a kasan mijinta,sai dai a
samansa.Sannan sai kowace mace ta daina dafawa
mijinta abinci tare da yi masa sauran hidima,saidai
shi yayi mata ya zamo bawanta.Saina maishe da
dukkan mazajen duniya tamkar karnukan farautan
mata sai yadda suka so zasu sarrafasu.Safirat na
gama fadin haka sai ta dubi dakarun dodanninta
tace dasu ko sarki Safwan zai samu nasarar
kasheni kada ku tayani yakarsa.Duk wanda ya
tayani yakarsa zan kasheshi da hannuna.Nan take
Jaruma Safirat ta zare takobinta ta ruga izuwa kan
sarki Safwan tana mai kwarara uban ihu da
kururuwa,takobinta na kartar kasa tana tashin
kura.Suna haduwa suka kacame da wani masifaffen
yaki mai tsananin ban tsoro da ban al'ajabi.Nanfa
suka rinka kaiwa junansu sara da suka cikin bakin
zafin nama,juriya da bajinta.Su kuwa wadannan
dodanni sai suka zuba musu idanu kawai suka
zama yan kallo
Saboda tsoron saba umarnin Jaruma
Safirat.Wohoho!Idan jarumtaka ta hadu da
takwaranta,naci da juriya suka game tofa dole ne
yayi yayi tsamari ainun.Saida Safira da Sarki
Safwan suka shafe dakiku masu yawa suna wannan
artabu amma dayansu bai samu nasarar koda
lakutar jikin daya ba.Al'amarin daya dugunzuma
hankalin kowannensu kenan.Shidai sarki Safwan
burinsa shine ya kashe Safirat kafin ragowar
rundunonin makiyanta su karaso wajen ya dauke
bakan dake goye a bayanta ya gudu.Itama Safirat
kokarinta shine ta gama da sarki Safwan kafin
sauran makiyan nata su karaso domin ta isa cikin
dajin Sharkif in yaso su sameta a can.Koda
kowannensu yaga wankin hula zai kaishi dare sai
suka sauya salon fada a lokaci guda suka hada da
kaiwa juna NAUSHI DA BUGU.Nan take kuwa labari
yasha bambam ya zamana cewa sun fara hadawa
kansu JINI da MAJINA.Nanfa suka fara
galabaita.Lokaci guda kowannensu ya fara ja da
baya cikin tsananin fushi sukayi nazarin juna suna
mamakin yadda karfin damtsensu yazo daya gami
da iya yakinsu.Kamar hadin baki sai kuma suka
sake rugowa da gudu izuwa kan juna a karo na
biyu suna masu kwala ihu.Koda ya rage saura taku
uku kacal su hadu sai kowannensu ya daka tsalle
sama ya kaiwa dan uwansa mugun sara.Duk da
cewa kowannensu yayi yunkurin kaucewa harin da
aka kawo masa,amma sai da hakan ya faskara
domin sarki Safwan ya sami nasarar saranta a
gadon bayanta,ita kuma ta samu nasarar saransa a
kirjinsa.Lokaci guda duk su biyu suka rusa ihu
sakamakon tsnanin zafi da zogin da sukaji a
lokacin da jini yai tsartuwa daga jikinsu suka fado
kasa a matukar galabaice suka kasa koda mikewa
tsaye.Adaidai wannan lokaci ne suka jiyo sukuwar
dawakai a bayansu.Suna waigawa suka hango
rundunonin daruruwan mahaya sun tunkaro su
daga can nesa sai kara yiwa dawakansu kaimi
suke domin su riskesu cikin kankanin
lokaci.Sawayen dawakan nasu na tashin
gagarumar kura.Koda ganin haka sai daya daga
cikin dodannin ya suri jaruma Safirat ya dorata a
gadon bayansa,ya falfala da wani azababben gudu
irin nasu.Ai kuwa sai sauran yan uwansu suka rufa
masa baya.Kafin rundunonin abokan gabar Safirat
su iso wajen tuni dodannin sun kule a cikin dajin
tamkar basu taba wanzuwa ba a wajen.Koda sarki
Safwan yaga Safirat ta tsere saiya kurma uban ihu
na bakin ciki kuma ya dafe raunikan kirjinsa mai
bulbulo da jini.Adaidai wannan lokaci ne ya bingire
kasa sumamme.Koda dakarun sarki Safwan suka
iso sukaga halin da yake ciki sai suka
dimauce.Nan tahe aka kafa tanti aka shigar dashi
ciki,likitansa ya kama aikinsa.Sauran sarakuna da
jarumai da mayakan da suka iso kuwa suka cika
da tsananin bakin ciki saboda sun san cewa koda
ma sunbi bayan Safirat a yanzu ba lallai bane su
risketa kafin ta isa cikin dajin Sarkif.Dajin da babu
wani mahaluki da baya tsoransa a duk fadin duniya
walau MUTUM ko ALJAN.Nan take gaba daya
sarakunan kimanin su arba'in gami da manyan
bokaye su ashirin da takwas da kuma
zakwakwaran jaruman da suka fito daga manyan
birane na duniya su talatin da biyu suka shirya
taro na gaggawa aka zauna ana tattaunawa.Sarkin
Misra ne ya fara da fadin cewa a halin yanzu babu
abinda ya kamata muyi face mu jira farfadowar
sarki Safwan na birnin Kisra tunda shi kadai ne a
cikinmu ya sami nasarar cimam wannan
takadariyar yarinya har suka fafata.Kuma dama
shine mafi sanin siriinta tunda tun suna yara suke
tare.Shine kadai zai iya bamu shawara da wannan
baka kafin ta dauko kuttun kwarinsa.Koda sarkin
Misra yazo nan a jabawabinsa sai wani shahararren
boka na kasar Yemen ya tari numfashinsa yace kai
bazai yiyu ba,domin a bari ya huce shike kawo
rabon wani.Kuma da zafi zafi akan bugi karfe.Ba
muki ta shawararka ba amma ga wata
shawarar.Kowacce runduna ta zabo wakilanta guda
goma goma a turasu subi bayan jaruma Safirat da
dakarun dodanninta,su cimma kafin su shiga cikin
dajin Sarkif.Tunda dai itama Safirat akwai rauni
babba a jikinta yanzu,nasan ba zasu shiga cikin
dajin Sarkif da ita a wannan hali ba.Dole ne su
tsaya suyi jinyarta ta farfado kuma ta dawo cikin
haiyacinta.Boka Inzuba ne yayi wannan
jawabi.Koda jin haka sai sansanin ya rude da
shewa kowa na cewa ya amince da shawarar boka
Inzuba.Nan take kowace runduna ta zabo dakaru
goma daga cikin mayakanta wanda take takama
dasu.Kuma ganin cewa ta yarda dasu,zasu iya yin
duk abinda ake ganin ba zai yiyu ba,kowane
badakare kallo daya zakayi masa ka tabbatar da
cewa ya cika gwarzon mayaki abin kwatance
saboda suna da kwarjini,haiba da cikar zati gami
da sura irin na manyan jarumai.Kuma kowannensu
na dauke da mahaukacin makami.Har wadannan
zababbun dakaru sun yunkura zasu bi bayan su
jaruma Safirat sai sarkin birnin Farisa ya tsaida su
yana mai daga hannu sannan ya dubi gaba daya
jama'ar dake wajen yace yanzu a misali idan
wadannan wakilan dakaru namu suka sami nasarar
karbo wannan baka a hannun Safirat wa za'a barwa
Bakan?Koda jin wannan tambaya sai kowa ya
shiga taitayinsa aka kama muzurai ana kallon
juna.Aka rasa wanda zaice kala.Da ganin haka sai
sarkin Farisa yace tunda an rasa mai bada amsar
tambayata ni zan baiwa kaina amsa.Amsar itace da
zarar an zo da bakan,sai a shirya GASAR
JARUMTAKA a tsakanin dakarun jaruman
namu,wanda suka yi nasara su za'a barwa
bakan.koda jin haka sai aka dada rudewa da
shewa kowa na cewa ya amince da wannan
tsari.Nan take dakarun wakilcin suka zaburi
dawakansu da gudu izuwa cikin daji domin su
riske su jaruma Safirat kafin su isa dajin Sarkif.
Bayan tafiyar wadannan dakarun wakilci da kamar
kimanin rabin sa'a ne sarki Safwan ya farfado daga dogon suma da yayi. habawa ai kwa sai .........h'm
Sai tomorrow kuma in sha'allah amma kafin wannan
Nidin ne dai Man Bash Nake cewa Asuba ta gari
08161272634
KIBIYA RATSA MAZA 🎿
Littafi Na Biyu (2)
Part C
Post
By :----Man Bash ----
Yana bude idanunsa yaga raunin kirjinsa a dinke kuma ya tsinci kansa kwance a
cikin tanti.Take ya gane cewa dakarunsa ne sualka
iso suka ceci rayuwarsa.Kawai sai ya tuno da
yadda Safirat ta kubuce masa,nan fa bakin ciki ya
turnuke shi ya rasa abinda ke masa dadi a
duniya.Cikin tsananin karfin hali sarki Safwan ya
yunkura domin ya mike zaune daga kwance amma
saiya kasa bisa tsananin zafi da zogin da yaji
tamkar kasusuwan kirjin nasa zasu kakkarye.Bisa
dole ne ya koma ya kwanta.Faruwar hakan keda
wuya saiga likitansa ya shigo cikin tantin da sauri
saboda dama yi kiyasta iya tsawon lokacin da
sarki Safwan zaiyi ya farka daga bacci.Da shigowar
likitan yana duban sarki ya gane cewa yayi
yunkurin mikewa zaune don haka saiya dubeshi
cikin alamun tsananin damuwa da fargaba yace ya
shugabana ka sake yunkurin zauna zaka iya rasa
rayuwarka gaba daya domin kuwa dukkan
kasusuwan jikinka ne zasu kakkarye saboda
jijiyoyin dake rike da kirjin naka ne zasu
tsintsinke.Kayi sani cewa ka auna arziki daya
zamana cewa saran da jaruma Safirat tayi maka
baikai ga datsa kasusuwanka ba,naman wajen ya
dare kuma ya dan taba kashin kadan.Dole ne a
kallah ka sami kwana tara a kwance kana jinya
kafin kashin ya hade ka iya motsi sosai ko ci gaba
da tafiya.Koda jin wannan batu sai zuciyar sarki
Safwan ta kama tafarfasa kamar zata kone saboda
bakin ciki domin yasan cewa kafin cikar kwanakin
tara jaruma Safirat zata iya dauko kurtun
kwarinta.Idan kuwa har haka ta kasance tofa babu
wani mahalukin da ya isa ya tare da yaki don ko
mutanen duniya ne da aljanunta zasu hadu a kanta
sai ta karar dasu.Koda sarki Safwan ya gama
aiyana hakan a cikin zuciyarsa sai sabon bakin ciki
ya turnukeshi har kwallar takaici ta cika masa
idanu yayi sauri ya kauda kansa ga barin kallon
likitan nasa don kada ya gane damuwarsa.
Al'amarin Jaruma Safirat kuwa itama tun sa'adda
ta fadi kasa sumammiya daya daga cikin dodannin
ya sureta ya aza a bayansa suka ruga izuwa cikin
daji bata farka ba sai bayan sa'a uku da rabi,tana
bude idanunta ta tsinci kanta kwance akan wata
bishiya mai yawan duhuwar ganyaye kuma a cikin
wani irin daji wanda ko a labari bata taba jinsa
ba.Da farko saida Safirat ta shafa gadon bayanta
taji an dinke rauninta kuma an shafa mata wani
magani a kansa me maiko.Koda ta dubi gabas da
yammanta sai taga ashe akwai wadannan dodannin
kimanin su goma akan bishiyar sun yi mata
KAWANYA suna gadinta.Bisa mamaki sai jaruma
Safirat taga ta iya mikewa zaune alhalin a zatonta
ba zata iya mikewa ba zaune sai bayan yan
kwanaki.Koda taga ta mike zaune daram ba tare
da taji wani ciwo ko wani zogi ba a bayanta sai ta
dubi dodannin tace,maza kuzo mu wuce izuwa
cikin dajin sarkif saboda na tabbatar da cewar
makiya suna biye damu,kuma idan suka riskemu
anan ban san yadda karshen gumurzunmu zai
kasance ba.Koda jin wannan batu sai wannan dodo
wanda ya goyata a bayansa ya dubeta yace,ya
shugabata ai dama ba wani abu bane yasa muka
yada zango ba anan face ganin halin da kike ciki
na suma da wannan rauni dake jikinki.In badon
mun kware akan ILMIN LIKITANCI ba da ba zamu
iya ceto rayuwarki ba har ma ki iya mikewa
zaune.Kuma gani mukayi idan ma muka shiga
cikin dajin Sarkif dake a cikin wannan mugun hali
babu abinda zaki iya bisa batun dauko kuttun
kwarinki.Kinga kenan shigar tamu bata da wani
amfani.Koda jin haka sai Safirat tayi murna kuma
ta yiwa dodannin godiya bisa ceto rayuwarta da
sukayi.Nan take ta duro kasa daga kan bishiyar
suma sai suka duro.Nan take taga ragowar
dodannin suna fitowa daga inda suka lallabe don
tabbatar da TSARO.KAfin Jaruma Safirat tayi
yunkurin cigaba da tafiya sai kawai sukaga
wadannan dakarun wakilci sun durfafo su a guje
bisa dawakai su da yawa suna masu zare
takubbansu suna kwarara uban ihu mai tsananin
firgitarwa.Kuma tazarar dake tsakaninsu bata wuce
taku goma ba.Har jaruma Safirat ta yunkura zata
zare takobinta sai wannan dodo daya goyata yai
wuf ya sureta ya sake° goyata a bayansa yace ya
shugabata bai kamata kiyi yaki ba yanzu domin
raunin gadon bayanki bai gama hadewa ba da
warkewa.Dinkin raunin zai iya warewa idan kikayi
kyakkyawan motsi.Ki kyalemu da wadannan dakaru
zamu iya dasu.Kafin wannan dodo ya gama rufe
bakinsa tuni sauran yan uwan nasa sun ruga izuwa
inda dakarun wakilcin suke suka tare su.Nanfa aka
ruguntsume da azababben yaki sai gashi dodannin
suna daka tsalle sama suna shawagi akan dakarun
wakilcin suna kai musu yakushi,sara da suka da
miyagun faratan hannayensu.Su kuma suka wanzu
suna karewa gami da maida martani.Nanfa kowa
ya zamewa kowa alakakai domin babu bangaren
dake samun wata nasara.Duk saadda makaman
dakarun ya hadu da jikin dodannin saikaga
tarwatsin wuta na tashi.Da yake suma wadannan
dakarun wakilci sun cika jarumai masu karfin
sihirin tsafi gami da matukar juriya da tsagwaron
iya yaki sai karfi ya kusan zama daya.Koda
donannin suka ga haka sai suka rinka huda cikin
dawakansu suka rinka faduwa kasa matattu suna
kayar da mahayansu.Nanfa aka bude kasuwar
KASUWAR YAKI ta gaba da gaba.Abinda ya
dugunzuma hankalin dakarun wakilcin shine ganin
yadda KAIFI da TSINI baya tasiri a jikinsu.Duk
wannan abu dake faruwa dodon dake goye da
Safirat yana ta kokarin samun hanyar da zai tsere
da ita ne ya nausa cikin dajin Sarkif amma ya kasa
saboda dakarun wakilcin sunyi musu kawanya
ne.Saida aka shafe sa'a daya da rabi ana yin
wannan bakin artabu ba tare da kowane bangare
sun sami wata nasara ba.Kwatsam bisa tsautsayi
sai tsinin takobin
daya daga cikin dakarun wakilcin ya soki idon daya
daga cikin dodanni.Faruwar hakan keda wuya
dodon yayi wani uban ruri a lokacin da jini ya
kama feshi yai tsalle ya runtuma da kasa ya kama
kakarin mutuwa.Koda dakarun wakilcin suka ga
haka sai suka cika da murna saboda sun gano
lagon dodanni ai kuwa sai suka kara kaimi wajen
yakarsu.Sai gashi sun cigaba da soke musu idanu
suna zubewa kasa matattu tamkar ana sassabe a
gona.Nan da nan cikin kankanin lokaci suka kashe
kimanin dodanni ashirin da bakwai su kuwa
dodanni da kyar suka iya kashe ashirin da daya na
dakarun wakilcin.Koda Safirat taga irin mummunar
barnar da dakarun sukayi musu saita fusata ainun
bata san sa'adda ta daka tsalle sama ba daga kan
gadon bayan dodon daya goyata.Tana saman iska
ta zare takobinta ta afka cikin dakarun wakilcin ta
hausu da sara da suka ba kakkautawa.Take salon
yaki ya sauya domin a cikin dakika arba'in ta
shaftare makogwaron dakaru kusan hamsin suka
zube kasa matattu.Ana cikin haka ne wani
badakare mai mugun naci ya sadado ta bayan
Safirat ya doki gadon bayan nata da kafarsa guda
da dukkan karfinsa.Jaruma Safirat tayi tsalle sama
tamkar an janyeta da majaujawa a lokacin data
kurma uban ihu sakamakon mugun zafin da taji a
gadon bayanta kuma sai fuskarta ta gwaru da jikin
wata bishiya ta fado kasa sumammiya.Kafin daya
daga cikinsu ya sami damar cafkarta tuni wannan
dodo ma'abocin goya Safirat ya dauketa daga
wajen ya sake goyata ya falfala da azababben gudu
ta tsakiyar dakarun wakilcin yana tarwatsasu da
karfin tsiya su kuma suna yi masa lugudan sara da
suka suna kokarin hallaka Safirat da dauke
bakanta.Amma sai suka kasa saboda dodon yafi
gaba dayansu zafin nama da karfin gudu da kuma
tsananin karfin damtse.Kafin su ankara tuni ya fice
fit ta tsakiyar tasu ya basu tazara mai yawa.Nanfa
suka bi bayansa da gudu a lokacin da tsirarun
dodannin ma suka rufa masa baya.Haka dai
dakarun wakilcin suka cigaba da bin wannan dodo
mai goye da Safirat suna karawa dawakansu
kaimin gudu wanda gudun nasu gudu ne na SIHIRI
amma har dodon ya iso bakin dajin Sarkif basu
sami damar riskarsu ba.Koda sukaga dodon ya
fada cikin dajin Sarkif da kafafunsa sai suka ja
linzamin dawakansu sukayi turjiya da haniniya.Jin
turjiyar dawakan nasu ne yasa dodon ya tsaya cak
ya waigo yana yiwa dakarun wakilcin murmushin
mugunta sannan ya yafutosu da hannu yana maiyi
musu nuni da cewar idan sun isa su biyoshi cikin
dajin sarkif din.Amma dukkaninsu sai suka noke
aka rasa wanda zai saida ransa.Ta gaban dakarun
wakilcin sauran dodannin suka zo suka wuce da
gudu suka fada cikin dajin Sarkif suka bi
dan'uwansu a baya lokacin daya juya ya cigaba da
tafiya a hankali cikin Izza,Kasaita da kwanciyar
hankali. bayan Kulewar Dodannin ne a Cikin dajin sai
dakarun wakilcin suka dubi junansu cikin tsananin
takaici.Daya daga cikinsu ya dubi sauran cikin
alamun matukar damuwa yace bamu da ilimin
komai akan dajin Sarkif,duk wanda yayi gangancin
shigarsa a cikinmu tabbas mutuwa zaiyi.Yanzu
kuzo mu koma sansaninmu wajen shugabanninmu
mu sanar dasu duk abinda ya faru,amma dole ne
mu dauki gawar dodo ko guda daya ne domin su
gasgata zancenmu su tabbatar da cewar munyi
iyakar kokarinmu.Gama fadin hakan keda wuya sai
dakarun wakilcin suka juya da baya da gudu izuwa
cikin dajin da suka baro,wato can inda suka fara
yin gumurzun farko dasu jaruma Safeerat.
Al'amarin su jaruma Safirat kuwa lokacin da aka
shigar da ita cikin dajin sarkif sa'adda take cikin
suma na biyu goye a bayan wannan dodo,tafiyar
dakika dari biyu da sittin kacal akayi ta farfado
daga suman da tayi.Amma sai taji gadon bayanta
yana yi mata mugun radadi da zogi sakamakon
naushin da akayi mata wanda ya zama ya fama
mata raunin,amma sai taji cewa zata iya yin tafiya
da kafafunta,Sai ta budi baki tace ka ajiyeni na taka
da kafafuna.Koda jin muryar Safiray sai farin ciki ya
kama dodon ya tsaya cak ya sauke ta saboda
tsawonsa.Koda ya direta kasa a gabansa yaga ta
fara kallon dajin Sarkif tana murmushi saboda
ganin irin ni'imar dake cikinsa ta korayen
ganyaye,ruwan duwatsu dake kwaranya wanda ya
kasance garai garai gwanin ban sha'awa da kuma
yayan itatuwa irinsu inibi,baure da sauransu sai
yace ya shugabata kyawun wannan daji ya daina
birgeki domin kyan dan maciji ne.Idan kinsan
masifun dake cikinsa da bakiyi sha'awar shigarsa
ba.Mu kanmu a yanzu ba karamin ganganci mu
kayi ba da muka biyo dake izuwa nan kawai,don
bamu da yadda zamuyi mu kawo kanmu GIDAN
MUTUWA,kuma ako yaushe a ko ina ajali zai iya
zuwa ya shammacemu a cikin wannan daji.Koda
jin wannan batu sai mamaki ya kama jaruma
Safirat tace to wai shin menene abin tsoro a cikin
wannan daji?Ni tun da muka shigo cikinsa ko
mugun kwaro guda daya ban gani ba.Gama fadin
haka keda wuya sai safirat taji wani irin huci a
bayanta mai dumi kamar an kunna gagarumar
wuta sannan kuma taji wani irin gurnani mai
matukar ban tsoro.A firgice ta waiga bayanta da
sauri,koda tayi arba da abinda ke bayanta sai taji
kamar ta saki fitsari a tsaye saboda tsananin
razanar da tayi duk da jarumtaka irin tata kuwa.Ba
komai jaruma Safirat ta gani ba face wata irin
katuwar macijiya mai girman gaske,amma kuma
kanta irin na macen bil'adama ne rafkeke tamkar
tunkuyar girki irin ta mutanen da.Tna da idanuwa
manya manya kamar tulu,hancinta wawakeke za'a
iya zura mutum a cikin kowane kofar
hancin.Bakinta kuwa kamar kofar shiga wani
gari.Hakoranta gabza gabza ne kamar hauren giwa
ne aka jera sama da kasa kuma guda dari ba daya
ne.Saboda girman jelarta da nauyinta ko yaya ta
motsa sai dajin gaba daya yayi girgiza.Tunda
Jaruma Safirat tazo duniya ko a mafarki bata taba
tunanin cewa akwai wata halitta mai mummunar
siffa irin wannan ba.Nan take sai jikin Safirat ya
kama karkarwa.Su kuwa wadannan dodanni
abokan tafiyar Safirat tuni sun arce daga wajen sun
shige cikin kogunan duwatsu da cikin ramuka sun
buya suka bar Safirat ita kadai a tsakiyar dajin a
gaban wannan muguwar Macijiya 🐍 Nima fah na feceee kar tayi loma daya dani lol 😜 😜
Sai tomorrow kuma in sha'allah amma kafin wannan
Nidin ne dai Man Bash Nake cewa Asuba ta gari
Suleiman zidane kd
KIBIYA RATSA MAZA 🎿
Littafi Na Biyu (2)
Part D
Post
By :----Man Bash ----
Lokacin da macijiyar taga yadda jaruma Safirat ta firgice kuma
ta dimauce sakamakon yin arba da ita sai ta bushe
da wata irin mahaukaciyar dariya mai kama da
saukar kwaran kwatsa sannan ta hade bakin a
lokacin da wani irin turirin dafi ke fita ta dakawa
Safirat tsawa tace ke karamar kwaruwa wane irin
taurin kai gareki gami da ganganci da rayuwa har
da zakiyi tunanin shigowa cikin wannan daji domin
ki dauki wani abu?To ki sani cewa ko shi kansa
mahaifin naki boka Saiham daya tabbata shugaban
bokayen duniya bai taba shigowa nan ba,saidai ya
aiko da abu ta hanyar sihiri shi kansa yasan ya
turoki ne izuwa AJALINki.Kafin macijiyar ta gana
rufe bakinta tuni jaruma Safirat ta tari numfashinta
tana mai cewa ke tsohuwar azzaluma,ki sani cewa
koma girman halitta,komai jin kanta da karfinta sai
an sami wadda ta fita komai.Tabbas na firgita da
ganinki saboda shi tsoro wajibi ne,amma dana
gane cewa ke azzalima ce sai naji duk tsoronki ya
gushe daga cikin zuciyata.Duk abinda yai farko a
cikin wannan duniya yana da karshe,babu mamaki
zuwana nan ya zama sanadin karshen
zaluncinki.Nayi imani cewa sai na sami abinda
nazo nema a cikin dajin nan kuma sai na fita a
raye don haka ke baki isa ki hanani daukar abinda
nazo dauka ba.Koda Safirat tazo nan a zancenta
sai Macijiyar ta wangame katon bakinta ta bushe
da dariya a karo na biyu,iskar bakin nata ta daga
Safirat sama har saida ta daina dariyar tsuke
bakinta sannan Safirat ta fado kasa tim.macijiyar ta
dubeta cikin kallon raini tace hakika yaro bai san
wuta ba sai ya taka ta.Tunda kikayi mini rashin
kunya yau saidai uwarki ta haifi wata amma dai ke
taki ta kare.Idan kina da wasiya ta karshen rayuwa
ki fadi kafin ki sheka barzahu.Kuttun kwari da
bakan da kika zo nema bama ke ba wasunki ma
basu isa susan inda yake ba a cikin wannan daji
bare su dauka daga nan har izuwa rayuwa idan
akwaita.Kafin Safirat ta bude baki tace wani abu ko
kuma tayi wani yunkuri tuni majiyar ta shammaceta
ta wangame bakinta.Take wata irin iska mai karfi ta
fito daga cikin bakin ta zuke Safirat ta
hadiyeta.Kawai sai macijiyar ta rufe bakin nata
sannan ta daka tsalle ta tsunduma cikin wani
tafkeken kogi tayi nutso izuwa karkashinsa.A
ka'idar wannan macijiya duk abinda ta hadiye a
cikin dakika biyar kacal yake narkewa ya zagwanye saboda
tsananin zafin dake cikin cikinta,amma sai gashi
Safirat bata narke ba kuma bata mutu ba amma
tsananin zafin cikin macijiyar yasa jikinta yayi luguf
kuma numfashinta ya fara sarkewa saboda rashin
shakar iska.Koda Safirat taji zata hallaka saita
mike tsaye a cikin cikin macijiyar ta zare wata
wuka dake daure a jikin cinyarta ta hagu ta kama
saran hanjin cikin macijiyar.Ai kuwa sai macijiyar
ta rinka jin kamar zata mutu don haka bata san
sa'adda ta wangame bakinta ba tayi wata irin
muguwar kara wacce tasa gaba dayan halittun
dake cikin karkashin tekun suka mace nan
take,wadanda ke saman kogin suka sume,wadanda
ke cikin dajin bisa turba dole suka toshe
kunnuwansu,wasu kuwa suka rinka tona kasa suna
binne kansu da kansu a karkashin kasa.Safirat ta
cigaba da saran hanjin cikin macijiyar duk da cewa
kuwa hanjin baya katsewa amma macijiyar bata
daina mutsu mutsu da juye juye ba tana ruri da
ihu tana gwara jikinta a jikin duwatsun dake cikin
karkashin kogin.Sakamakon haka ne Safirat ma ta
rinka faduwa tana gwara kanta da jikin macijiyar
amma saboda tsananin naci da juriya sai ta cigaba
da mikewa tsaye zumbur tana ci gaba da saran
hanjin macijiyar,nanfa ya zamana cewa da ita da
macijiyar duk sun wahala sun jigata ainun.nan da
nan idanun macijiyar suka kada sukayi jawur,suka
fara zubar da hawayen wuya,kai da bala'i yai bala'i
macijiyar taji cewa tabbas hallaka zatayi sai ta taso
sama daga karkashin kogin ta fito bakin gabar
kogin ta fito bakin kogin ta kama kakarin amai
domin ta watso Safirat waje daga cikinta ta huta da
azabar da take ji.koda Safirat taji an zukota za'a
wastota waje daga cikin macijiyar don haka saita
saki jikinta ta taho da gudu tana fitowa bakin
macijiyar saita wurkila jikinta ta haye saman kan
macijiyar ta zauna daram.Kafin macijiyar ta wurkila
jikinta ta jeho Safirat kasa tuni ta daga wannan
wuka dake hannunta ta caka mata ita a tsakiyar
madigarta.Nan take jini ya kama tsiri sama a
lokacin da macijiyar tayi wani irin uban ruri wanda
bata taba yin kamarsa ba.Kawai sai ta langwabe
kasa tayi wanwar ko shurawa batayi ba.Ashe ruhin
wannan macijiyar a cikin tsakiyar kanta yake cikin
madiga.Ita kanta jaruma Safirat da taga ta sami
nasarar kashe macijiyar tayi matukar mamaki
domin bata san cewa ruhinta a tsakiyar kanta yake
ba kawai dai tsananin sa'a ne da rabo ya kaita ga
samun wannan nasara.Saboda jikin Jaruma Safiray
ya hadu yayi lugub sakamakon tsananin zafin da
cikin macijyar yake dashi saita yanke jiki ta fadi
kasa sumammiya.Adaidai wannan lokaci ne
wadannan dodanni suka fito daga cikin ramuka da
kogunan duwatsun da suke boya da gudu suka
rugo izuwa inda take kwance.Nan dai suka fara
kokarin ceto rayuwarta.Saida suka shafe kusan
rabin sa'a suna yi mata fifta da dan yayafa mata
ruwa amma bata farka ba.Al'amarin dayai matukar
dugunzuma hankalinsu kenan suka fara tunanin
cewa lallai ta mutu saboda babu alamar inda yake
motsi a jikinta.Nan fa dodannun suka kama kuka
suna zubar da hawaye na takaici da bakin ciki
saboda a ganinsa bai kamata ace jaruma kamar
Safirat ta mutu ba wacce tasha wannan bakar
gwagwarmaya tayi bajintar da ba'a taba samun
mahalukin da yayi taba a nahiyar gaba
daya,sannan kuma suna matukar bakin ciki bisa
ganin cewa duk wahalar da suka sha a baya ta
raka Safirat izuwa cikin dazuzzukan biyu da kuma
yan uwansu da suka rasa duk sun zamo a banza
kenan.Dodannin na cikin wannan tsananin bakin
ciki ne ma'abocin goyata a bayansa ya lura da
yadda jikin Safirat ya hadu yayi lugub har a sannan
tururin zafi bai daina fita ba daga cikin kofofin
gashin jikinta.Koda ganin haka sai yayi wuf ya
sureta ya azata a bayansa ya runtuma da gudu
izuwa wani bangare daban na dajin wanda shi
kansa bai san inda hanyar zata kaishi ba.A
dimauce sauran yan uwan nasa suka rufa masa
baya domin suga inda zai kaita.Haka dai dodon ya
cigaba da gudu dauke da Safira yana waige waige
da dube dube ko zai ga abinda yake nema wanda
yake ganin cewar shine kadai zai iya ceto rayuwar
Safirat.Duk da cewar wannan dodo da sauran yan
uwan nasa suna matukar tsoron wannan daji na
Sarkif sai gashi sunfi jin tsoron mutuwar Safirat
akan dajin.Burinsu kawai shine su ceto rayuwar
tata koda kuwa zasu rasa tasu rayuwar.Saidai
wadannan dodanni suka shafe sama da sa'a guda
suna guje guje a cikin wannan dajin Sarkif suna
fadawa cikin tsaunuka suna jin raunika a jikinsu
saboda komai na dajin daban yake basa iya kare
jikinsu.Nan da nan suka jigata ainun suka sha
bakar wahala.Duk wanda ya kalli wadannan
dodanni a lokacin da suke cikin wannan hali dole
ya tausaya musu kuma babu abinda zai burge
mutum face yadda suka nuna tsananin tausayinsu
da kaunarsu akan jaruma Safirat.Sai bayan sun sha
wannan muguwar wahala ne kwatsam suka hango
dusar kankara a gabansu a bakin wani kogi.A guje
suka karasa wajen wannan dodo dake goye da
Safirat ya sauketa daga kan gadon bayansa ya
turbutsata a cikin dusar kankarar ya binneta a ciki
yabar iya fuskarta a waje sannan suka ja da baya
suka tsuguna suka tsurawa gangar jikin Safirat
idanu suna jiran tsammani,ba don komai ba kuwa
sai saboda sunsan cewa idan Safirat ta shafe
kamar rabin sa'a a cikin Dusar kankarar bata
farfado ba to ta mutu kenan ba zata taba tashi
ba.Koda rabin sa'a ta shafe kuwa sai zuciyoyinsu
suka karaya suka fashe da matsanancin kuka kai
kace mutane ne su ba dodanni ba.Cikin tsananin
bakin ciki suka mike tsaye tamkar wadanda suka
tashi daga zaman makoki suka nufi inda Safirat ke
kwance da nufin su cirota daga cikin kankarar su
haka kabari su binneta.Da isarsu gabanta
wannan dodo ma'abocin goyonta yakai hannu da
nufin ya zarota sai kawai yaga idanunta sun bude
nan take ta yunkura ta taso zaune daga cikin dusar
kankarar.Koda dodannin sukaga haka sai suka
kaure da shewar farin ciki suka kama tsalle
tsalle.Koda Safirat taga yadda wadannan dodanni
ke murnar ganin ta rayu bata mutu ba sai itama ta
kamu da tsananin farin ciki,nan take ta mike tsaye
ta daka tsalle ta fada kan kirjin wannan dodo
ma'abocin goyata suka rungume juna kuma sai
suka fashe da kukan farin ciki.Saida suka dan jima
a kankame da juna sannan dodon ya ajiyeta kasa
tamkar ya ajiye yar tsana saboda kankantarta akan
girmansa.Kawai sai Safirat ta dubeshi cikin
murmushi tace waishin menene sunanka ne?Koda
jin wannan tambaya sai mamaki ya kama dodon
ya maida mata martani da murmushi yace,ke kuwa
menene dalilin da yasa tuntuni baki san suna ba
tun a farkon haduwarmu sai a yau?Sa'adda Safirat
taji wannan tambaya sai ta sake yin murmushi tace
saboda ayau ne na tabbatar da cewa kai masoyina
ne na kwarai domin kuwa ban taba haduwa da
mahalukin daya taba nuna mini tsantar kauna ba
kamarka hatta masoyina sarki Safwan kuwa.Domin
shi ya kasa hakuri da komai na duniya a kaina.kai
kuwa gashi ka sallama rayuwarka don ceton
tawa,kayi kuka ka zubar da hawaye saboda ganina
a cikin mugun yanayi.Inda ace kai mutum ne
kamarni da babu abinda zai hanani aurenka face
mutuwa.Amma duk da haka zan nemi alfarma daya
a wajenka inaso idan har na sami nasarar dauko
kuttin kwarina zan fara karbar karagar mulkin
Safwan na zama sarauniyar Birnin Kisra.A sannan
ne nake son ka zama shugaban dakaruna ma'ana
ka zama sarkin yakina amma lallai ka koma can
mazauninku ka dauko matarka idan kana da
ita.Idan kuma baka da mata to lallai kayi sabon
aure.Koda Safirat tazo nan a zancenta sai dodon
ya bushe da dariya yace suna nan Gargus kuma
dama can nine mataimakon shugabanmu
Bandaru,Ban taba aure ba amma saboda na faranta
miki rai bayan kin cimma burinki zan koma can
dajin tsaunin Lauhul Farras na auri daya daga cikin
irin matayenmu.Ya shugabata ina ganin zaifi kyau
mu nemi inda zamu kwana a cikin wannan daji
tunda yanzu dare ya soma yi gashi babu hasken
FARIN WATA.Kin sani cewa wannan daji na Sarkif
yana da tsananin hadari kuma babu wanda yasan
iyakar mugayen abubuwan dake cikinsa.Koda
Gargus yazo nan a zancensa sai Safirat tayi
murmushi tace na aminta da wannan shawara taka
dari bisa dari.Nan take suka dunguma gaba
dayansu suka kama neman inda zasu kwanta su
huta kuma suyi bacci.Cikin sa'a kuwa basu dade
ba suna nema suka sami wani kogon dutse.Saida
suka shiga cikin kogon suka cajeshi tsaf suka
tabbatar da cewar babu wani mugun abu a
cikinsa.Sannan suka yiwa Safirat shimfida ta
kishingida.A sannan ne Gargus ya shiga duba ko
ina a jikin Safirat domin yaga yadda raunikan
jikinta suke yayi mata magani.Bayan ya gama
nazarin raunukan ne ya kwanto jakar guzurinsa ya
ajiye a gabanta ya shiga yi mata magani a lokacin
ne ta kura masa idanu ta shiga zancen zuci.Ba
komai bane ya fado mata a rai face tunowa da
cewar Gargus shine kadai namiji daya taba jikinta
itama ta hada jikinta da nasa hatta sarki Safwan
kuwa.Waishin yaushe ne zatayi aure ta sami mijin
da zai iya sallama rayuwarsa domin tata kuma ta
sami magaji tare dashi?Koda Safirat tazo nan a
tunaninta sai hawaye ya zubo mata,takaici ya
turnuketa ta sami irin wannan masoyi.Haka dai
Safirat ta cigaba da wannan tunani har Gargus ya
gama aikinsa bacci ya saceta bata sani ba.Safirat
bata farka ba daga bacci saboda tsananin gajiya
da jigata saida gari ya waye har rana ta
kwalle. Nima dai sai a lokacin na fara yin gyangyadi har wayar ta fado ta fashe ban sani ba lol 😂😂
Sai tomorrow kuma in sha'allah amma kafin wannan
Nidin ne dai Man Bash Nake cewa Asuba ta gari
Suleiman zidane kd
08161272634


0 Comments