KARUWAR GIDA cmplt

 *KARUWAR GIDA*







*STORY WRITEEN BY✍*


*_AMENAT KABER KIRU_*




*I'M BACK 🤒DUNIYAR MARUBUTA SALAMU ALAIKUM* *ina yiwa d'aukacin Al'umman musulmi na duniya baki daya barka da sallah muna fatan Allah ubangiji ya karbi ibadun mu .👏*


*SADAUKARWA:*


_*WANNAN LITTAFIN SADAUKARWA NE GA HJY ZALIHA YOLA(MMN AHMED)*_



*GODIYA*

_Duk kan godiya ta tabbata ga ubangiji talikai wanda bai haifa ba kuma ba'a haifeshi ba,salati da daukaka da aminci ka qarasu ga dan Amenatu manzo tsira wanda babu tamkarshi,alaye da sahhaban gidanshi tsarkaka._


*TSOKACI*


*wanna labarin bai shafi wata ko wani ba  na rubuta shine domin gani yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamanin duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zu'katan mu, ba nayi ne dan yad'a bad'ala ba,a'a zanyi ne saboda na zakulo wasu halaye da suka shiga gidajen aure. Duk wanda yaga abinda bai masa ba yana da kyau ya bude dogon shafin zagina kofa  a bude take domin karbar hakan daga ko waye,zagi danzagawa ne nasan baya tabo🤷‍♂Azagi kowa normal ne🤪*





*PAGE🅾1⃣*



Da sauri Mariya ta juya ta kalli mahaifiyar ta wacce ta ke 'kokarin fita daga 'karamin dakin nasu ta kira sunanta a hankali tace UMMA dan Allah ki saurareni mana" kallon yar tata tayi galala wacce bata wuce shekara goma sha d'aya a duniya ba, tare da fad'in ina jinki, nisawa tayi da cewar UMMA ina zaki tafi a wannan daren ki barmu bai kamata ki tafi ki barni nida ANAS a wannan halin ba. daka mata tsawa tayi hadi da cewar ni zakayiwa nasiha?" Girgiza kai MARIYA tayi hadi da cewar A'a UMMA kawai naga tunda kika dawo dazu ko magani baki bashi umarnin ya tashi yasha ba gashi zaki 'kara komawa..... katse y'artata ta 'karayi da cewar naji ke din tunda har kinfini sanin abinda ya dace ki tasheshi ki bash mana. tana fad'in haka ta kad'a kanta tayi waje ko sauraren MARIYA bata 'karayiba duk da tasan MARIYA gaskiya ta gaya mata amman ta kasa tsayawa ga yaran nata, ita kuwa tunda mahaifiyar tata ta fita ta koma kusa da inda kaninta yake kwance ta dagoshi da cewar ANAS tashi kaci abinci ka sha magani,da kyar yaron ya dago daga kwanciyar da yayi yace toh yaya, amman ina UMMA?" Kwallace ta fito daga idon MARIYA sannan ta amsa da cewar ta sake fita yanzu, kad'a kai kawai ANAS yayi duk da 'kan'kantar shi a matsayinshi na karamin yaro yace kai UMMA kai UMMA mai kikeson zamane adacan idan ance UMMA zata iya fita nan da k'ofar daki ta barmu zanyi mamaki amman yau mune UMMA take gudu a matsayinta na mahaifiyar mu. kafin ya karasa maganarshi tuni kuka yaci karfinshi daga shi har yar uwarshi watau MARIYA hakuri ta shiga bashi da rarrashin qanin nata. Sai da sukayi kuka mai isa,sannan ta mik'e ta dauko abinci ta Zuba musu, ta fita waje ta dauko roba da ruwa ta umarci kaninta daya tara hannunshi ya wanke a cikin robar, bayan ya gama ta dauki robar da ruwan ta fita dasu itama ta wanke nata hannu sanna ta dawo sukaci abinci tare"bayan sun kammala ne ta dauko magungunanshi ta bare ko wanne ta bashi ta qara gyara mishi gurin kwanciyarshi sannan ta fita ta dauro alwala ta dawo daki,tayi sallah tare da kara gyara nata makwancin hadi da yin addu'a ta shafejikinta ta kwanta amman ta kasa bacci sakamakon tunanin ina mahaifiyar tasu take zuwa babu dare babu rana?" Juye juye tai tayi tana tunanin sauyin halayyar da suke gani a tare da mahaifiyar su, A dan tsakanin nan. Sabida karancin shekarun MARIYA bata iya gano amsar komai ba a haka dai taita juyi har mahaifinta ya shigo jin shigowar tashine yasa ta mike tsaye zumbur daga kwanciyar da tayi hadi da cewa sannu da dawowa ABBA" a ciki ya amsa hadi da cewar ina ZAINAB  ta tafi ne?"bata damu da rashin nuna ko in kula da mahifin nata yayi ba tace yanxu ta fita babu dadewa,kwafa yayi da cewar toh,kawai ya nufa  inda abinci yake a ajjiye ya dauko ya ajje shi daga gefe hadi da umartar MARIYA data dauko mishi abin zubawa"mikewa tayi ko tsoro bataji domin idan da sabo ta saba da halin mahaifin nata,na rashin tausayi ko jin k'ai a garesu ita da qanninta fita tayi ta hado komai tazo ta ajje masa komai sannan ta koma gefe ta zauna tana ta kallonshi yana muzurai haka ya zuba abincin ya fara ci ko wanke hannu bai fita yayi ba,ya fara ci kenan MARIYA tayi farat da cewar au ABBA na manta ban gaya ma jikin ANAS ya kara tashi ba. Wurga mata ido yayi hadi da kai lomar hannunshi baki yace toh sai akayi yaya? ZAINAB ce ta ce ki gayamin haka  da zarar na fara cin abinci ko?  dan ku hana zuciyata sukuni toh bari kiji sabida ku wallahi bazan kashe kaina ba'" girgiza kai MARIYA tayi hadi da cewar A'a ABBA, tare da matse kwallar da ta rufe idonta,tsawa yayi mata hadi da nuna mata makwancita da ta tafi ta kwanta, tashi tayi a hankali ta nufi shinfidar ta ta kwanta cikin kunar zuciya,da mamakin anya kuwa ABBA shine ya haifesu ita da qaninta?AMMA ce mai tausaya musu tai musu komai amman yanxu itama ta sauya a yan tsakanin nan bata san menene yake faruwa a tsakanin iyayen nasu ba, a haka bacci yayi awan gaba da ita, Ita kuwa ZAINAB tun fitar ta bata zame ko ina ba sai gidan kawarta Hajiya Rukaiyya tayi sallama tayi aka amsa mata daga ciki ta karasa tayi sa'a Hajiya ta dawo ba kamar dazu da tazo tai ta faman jiranta bata dawo ba,da fara'a Hajiya Rkaiyya ta karbi ZAINAB da cewar kawata kece a yanzu haka?"amsawa ZAINAB tayi hadi da zama kan daya daga cikin kujerun falon, kawata  da cewar ai nazo daxu bakya gida UMAR bai gaya miki ba?" Har yace bakiyi nisa ba"nan nayi ta zaman jiranki da naga rana tayi sosai shine na koma gida na daurawa yara abinci na danyi aikace_aikacen gida, yanzu ma harsashe nayi da cewar duk inda kika tafi kin dawo gida tunda yace ance min ba dadewa zakiyi ba,dariya Hajiya Rukaiyya tayi da cewar hakane qawata kuma da na dawo nayi kamar nima na bi ta gidan naki sai kuma dai naji nagaji na bari da safe kamin na fita na shigo ta gidan na duba ANAS da jiki, murmushi ZAINAB tayi da cewar ai yanxu ma matsalar jinkin nashice ta tasoni shine nazo na sanar miki hadi da qarin neman taimakonki akan dan Allah qawata ki tallafi rayuwata ki qara taimakamin da aron kudi zan kaishi asibiti, murmushi Rukaiyya tayi da cewar ai kawata tunda na ganki a wannan lkc nasan damuwa ce ta kawo ki gareni Amman dan Allah ina RABI'U yake ne da yabarki kike ta fakan2 din neman kudin kai yaro asibiti? "Murmushi ZAINAB tayi da cewar ai tunda ya fita sallah asuba bai kara dawowa gidan ba har na fito din na" nisawa Hajiya Rukaiyya tayi da cewar gaskiya ZAINAB baza rufeki ba kin sakarwa mijin ki fuska da yawa har ya samu damar wulakantaki haka, amman babu komai sai ki cigaba da hakuri da shi haka nan tunda da yara a tsakanin ku, mikewa tayi daga falon ta shiga dakinta, ta dauko naira dubu biyu ta mikawa ZAINAB tace mata gashi ba ranta miki nayi ba, zanzo muje asibitin tare da safe sai muga yadda Allah zaiyi ko kawata" toh ZAINABA tacewa Hajiya Rukaiyya" ta amsa da babu komai amman yana da kyau kije ki sanarwa da iyayen ku halin da kike ciki keda mijinki,shawara na baki bawai dan na gajiya da baki wani abu nawa ba,toh ZAINAB taqara cewa qawarta  hadi da yi mata godiya sukayi sallama ta kamo hanya tayo gida.Koda tazo kofar  gidanta sai ta tarar har mijinta ya rufe kofar gida nan ta hau bugun kofa, takai kimamin mitin talatin tana bugun kofar kamin yazo ya bude mata a fusace ya bude yana faman hucin da cewar daga ina kike,?" Shiru ZAINAB tayi kamar bata ji ba ta wuce ta barshi a tsaye  ta shige ciki abinta" mayar da kofar yayi shima ya rufe ya bi bayanta hadi da kara tambayar ta daga ina take?" Amman shiru jin bata da niyyar amsawa yasa shi ya kara bude murya ya shiga zazzaga masifa a wannan  dare ko kallonshi batayi ba bare ta tanka mishi haka dai yai ta zagi da gori da jifanta da bakaken maganganu amman tayi shiru, ta shiga daki ta cire hijab dinta sai kuwa ya hango k'yalin kudi nan fa ya kara gyara sai ya shiga rarrashita da cewar ai baki gaya min zaki fita bane shine dalilina, na yi miki fada amman kiyi hakuri ZAINABUWATA ai nasan bazaki wuce gidan Hajiya Rukaiyya ba toh ya kika barta?" Shiru ZAINAB tayi kamar bataji abinda yace ba hadi da waye kudin ta dauresu a ha6ar zaninta sanna ta nufi gado ta kwanta, biyo bayanta yayi shima ya kwanta gefe, yana jiran yaji abinda zata ce masa amman shiru, tashi yayi ya cire kayanshi ya dauko wata dukunku_nanniyar jallabiya ya saka kana ya qara hayowa gadon ya kwanta yana faman huci," haushine ya kara kama ZAINAB ta kara juya mishi baya ta kama bacci, bata farka ba sai ji tayi zakara na chara, sauri tayi ta mike tsaye tayi waje ta dauro alwala tayi sallah shi kuwa gogan naka ai bata farka ta ganshi a d'akin ba tuni ya fice, tashin MARIYA tayi dacewar taje tayo alwala, da sauri MARIYA ta mike ta bi umarnin mahaifiyar tata da cewar to" tayi waje ta d'auro alwala tazo tayi sallah.


 Bayan ta idar ta gaishe da mahaifiyar tata " amsawa ZAINAB tayi cikin kulawa tace mata lfy qlu" mamaki ne ya kama MARIYA duba da yadda taga mahifiyar tata kwana biyu bata sakar musu fuska sai tayi tsammanin ko wani abu tayi mata," murmushi ZAINAB tayi ganin yadda yar tata har ta saki jikinta a wannan lkc, ta qara muskutawa gefe ta kwanto zanninta da zata bawa MARIYA kudin da tasamu jiya ta sayo musu gasarar koko a ciki ta shafa babu su,ta juya ta koma kan gadon bata ji su ba, shiru ta yi hadi da zubar hawaye da sauri ta goge kar MARIYA tagani,duk da haka yarinyar ta fuskancin chanji da tagani daga mahaifiyar tata, sai tace mata UMMA tunda bakiga kudin ba ai ABBA ya rage abinci jiya ki barshi kawai maci haka. Toh kawai ZAINAB tace ta koma gun da ANAS yake kwance ta daga shi tayi waje dashi ta sashi yayi fitsari kana ta wanke masa bakinshi ta dawo dashi daki ta fita ta hada wuta ta dumama musu abincin sanna ta daura musu ruwan wanka. Bayan sun gama cin abin tayiwa ANAS wanka ta hadawa MARIYA nata ruwan wanka ta kaimata" sanna ta dawo ta gyara ko ina sanna ta debi nata ruwan wanka" tana fitowa sai ga kawarta Hajiya Rukaiyya ta karaso gidan kamar yadda ta al'qarta mata, tana shiga MARIYA  ta  gaisheta,Sai ta tashi ta fita tsakar gida, tabar mahaifiyar tata  suna gaisawa  da kawarta,bayan sun gaisa ta tambayeta jikin ANAS ta amsa da yaji sauki,can tace toh ki shirya muje asibitin ko, shiru ZAINAB tayiwa Hajiya Rukaiyya hadi da zubda kwallah tace ai babu damar zuwa" amsawa Hajiya Rukaiyy Tayi da cewar kamar yaya, RABI'U ne ya hanaki zuwa kai yaron asibiti?" Girgiza kai ZAINAB tayi da cewar A'a,mamaki ne ya kama Hajiya Raukaiyya tace toh menene?" Amsawa ZAINAB tayi da cewar ai ya sace kudin da kika bani jiya" ta6e baki Hajiya Rukaiyya tayi tana mamakin wanne irin sauyin yanayin ne yazowa ZAINAB haka?" Ace mijinta shine yake neman tagaiyyarata ci gaba tayi da tafe hannu tayi ta kara tambayar ZAINAB sata fa?" Daga mata kai ZAINAB kawai tayi, ta cigaba da kukan da takeyi duk maganar da sukeyi MARIYA na tsakar gida tana jinsu,a sanyaye itama Hajiya Rukaiyya tacewa ZAINAB toh kiyi hakuri ki barshi kizo mu tafi kawai mu kaishi ai baza'abar yaro hakaba"  toh ZAINAB tace ta dauko hijjab hadi da rungumo ANAS ta rufo kofar dakin nata"suka rankayo har MARIYA sai da ta sakashi cikin motar kawar tata, sannan ta juya tace mata bari nayiwa makofciyata sallama" toh Hajiya Rukaiiya tace mata kawai ta bude mota ta shiga tana jiranta" , juyawa tayi da saurinta ta cewa  MARIYA muje gidan su Haiidar ko nayi musu sallama,ta shiga ta bayar da ajjiyar MARIYA hadi da yi musu sallama,ta dawo ta bude motar kawar tata ta shiga,ita kuma taja mota suka dauki hanyar asibiti, sai da sukayi nisa sannan Hajiya Rukaiyya ta dan nisa ta kalli ZAINAB da cewar wai yaran nan duk sun daina zuwa Makaranta ne?"murmushi ZAINAB tayi da cewar yace bazai iya biya musu kudin makarantar ba, ta gwamnati ya mayar dasu,ita madin ya daina biyan komai nasu nice nake biya toh nima yanxu ta ritso banida kudin shine dalilin da yasa basa Makaranta,wallahi kawata banida jari jarina duk ya kare banida yadda zanyi,shine dalili, ko jiya da kikayimin maganar na saka manya cikin maganata da babansu nayi nayi,abin yakiyi Ke kisan yadda nake da shi  a dacan ban taba tsamanin zai min abinda yake min a yanzu ba, daga ni har yarana,amman babu yadda zanyi da halayyar da ya sauya min, naje na sami iyayenshi akan suyi masa fada,wallahi goya masa baya ma sukayi da cewar ai bashida sarari wanda ni nasan ba haka bane son zuciya ne irin na wasu iyayen mijin, da na dawo na sake yanke sahwarar naje na sanarwa da nawa iyayyen domin su shigo cikin lamarina amman abin duk yaci tura sun kirashi dan jin abinda nake masa yace babu komai, anyi mana fada gaba daya kamar zai gyara amman ya sake komawa kan halinshi wallahi kawata yanxu tsakanina da BABAN ANAS babu abinda ya sani nawa sai bukatarshi zuwa gareni,kinga kuwa dole zan fita hayyaci na,duk lokacin da naje gida hakuri ake bani, ace na dawo kan yarana ,nima duk lkc da so mu rabu idon yaran nake kallah sai naji na kasa tabuka komai a kanshi Amman yanxu tausayin yaran ya fara gushewa daga zuciyata domin bansan me zanyi ba, matukar hakan ba hakuri ne ba,kawata" nisawa hajiya Rukaiyya tayi da cewar kawata babu komai kedai ki cigaba da hakurin da ake cewa kiyi ai baya karewa, shiru ZAINAB tayi hadi da goge kwallar da ta cika mata ido ta amsa da cewa insha Allah kawata zanyi komai kike cemin,a haka dai suka cigaba da tafiya har suka zo dai_dai inda danja ta tsayar dasu suka tsaya nan fa ZAINAB ta dan bude glass din gefenta sakamakon dan zafin da aka fara na dagawar hantsi tana budewa taji ana kiran Sunanta daga motar da take gefenta takara lek'o da kanta tayi domin ta tabbatar ita din ake kira ko wa? Tana dubawa sai ta hango mai kiran nata hakan yayi dai2 da basu hannu da danger tayi domin su wuce, da sauri ta cewa Hajiya Rukaiyya kisan mai kirana kuwa?"A'a tace mata hadi da cigaba da tukin motarta tana kallon gabanta,"ZAINAB tace ai HAFSAT AL'AMEN ce a motar, kaminta karasa maganar tuni ta zo saitunsu ta yi ma Hajiya Rukaiyya nuni da su sami guri suyi parking nan fa suka dan tsaya a gefen hanya suka gaisa hadi da tambayar su ina zasu?"ZAINAB ce ta amsa mata da cewar zamuje kai yaron wajena asibiti ne"da sauri HAFSTA ta leqa sit din dake baya motar ta gano ANAS da yake a kwance yana ta faman bacci, kallo daya HAFSAT tayiwa ZAINAB ta tabbatar ko ba'ace mata komai kanta ba tasan tana cikin wani hali komawa tayi cikin tata motar ta dauko jakar hannuta ta bude ta debo kudi masu yawa ta mikawa ZAINAB hadi da kara jajanta mata rashin tafiyar ANAS din godiya tayi mata, a lokacin Hajiya Rukaiyya itama ta kara saka baki a maganar tasu tayiwa HAFSAT godiya, har sun juya zasu koma mota ta kira sunan ZAINAB hadi da tambayar ta number wayarta tace ko dan sanin halin da kike ciki Sosa k'eya ZAINAB tayi da cewar ai banida waya a hannu na yanxu,mamakine ya kara kama HAFSAT da cewar toh bari na baki card dina duk duk lkc da kika sami dama sai ki kirani ta miqa mata, ZAINAB ta karba ta rike hadi da kara yi mata godiya, sukayi sallama ta shiga motar ta suma suka koma tasu suka dauki hanyarsu ta zuwa asibiti. Basu wani kara bata lkc ba suka karasa wani karamin clinic wanda suka shiga suka karbi kati a inda suka wuce sunga likita ya duba ANAS da kyau inda ya sanar musu cewar ba wani ciwo ne mai tsanani ba,  garkuwar jikinshi ce tayi laushi sakamakon rashin samun wadatacan abinci mai gina jiki, hakan shine yasa yake yawan zazzabi mai zafi, cikin kwarewa Dr ya rubuta musu magunguna karin jini da na cin abinci da basu shawara akan su ringa bashi abinci mai gina jiki,suka amsa hadi da yiwa Dr godiya suka fito gurin zama Hajiya Rukaiya ta nuna ma ZAINAB da cewar ta zauna ta jirata taje ta sayo magungunan da Dr yayi umarnin su saya...... 



*Comments dinku shi zai sa insan kuna son Inci gaba da rubuta muku wannan labarin*









~AMENAT KABER KIRU~






*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.Duk wanda yaga  abinda bai masa ba yana da kyau ya bude shafin zagina k'ofa a bude take domin karbar hakan daka ko waye zagi d'an zagawa ne nasan baya tabo🤷‍♂azagi kowa normal ne🤪*



*🅾2⃣*




Amsawa ZAINAB tayi da toh, ta sami d'aya daga cikin kujerun da suke gurin ta zauna hadi da rungume ANAS," ita kuwa Hajiya Rukaiyya pharmacy  dake cikin asibitin ta nufa kai tsaye domin sayo magungunan da aka rubuta musu," tafiyarta kadan ZAINAB ta fada duniyar tunanin baya yadda rayuwar ta kasance tsakaninta da mijinta uban 'ya'yanta wanda take kallon a matsayi sanyin idon ta a wancan lkc ba yanxu ba,tunawa tayi da irin soyayyar da ta nuna mishi had'i da bashi kulawa haka shima daga nashi 6angaren sam baya son abinda zai bata mata zuciya,rayuwa ce mai ban sha'awa  mai cike da kaunar juna tunda ZAINAB ta auri RABI'U bata taba kai k'ararshi ba haka shima bai taba kai tata k'arar ba sai lkc da ta sami cikin MARIYA ne aka fara samun matsala domin kuwa cikin yazo mata da wani irin yanayin laulayi mai daga hankali komai taci sai ta amayar dashi,aman yakan zo matane a ko wanne yanayi babu dare babu rana,wannan ce tasa RABI'U ya fara tsanarta da hantarar ZAINAB a ko wanne lkc hakan ce tasa duk abinda ZAINAB ta ta6a RABI'U baya iya amfani dashi ga k'yara da hantara a duk lkc da ta fara amaye_amayenta haka zai tsallake ya barta babu tausayawa ya fita , tun abin baya damunta, har ta fara tsangwamar kanta da cewar ko RABI'U ya daina sonta ne? take ta k'aryata zuciyar ta akan abin da take zargi" duk abinda ZAINAB tace tana marmari a matsayinta na mai ciki bazata samu daga gareshi ba, tun tana iya tashi tayi komai da kanta har hakan ta gagara wannan hujjar ce tasa ZAINAB ta nemi izinin RABI'U da ya barta ta tafi gida tayi jinya acan" Katseta yayi da wani wawan mari hadi da daka mata tsawa na cewar ai daman ba d'aureki nayi ba ko an gaya miki cewar zamanki anan yana da wani muhimmanci a gareni ne?" Dafe kumatu ZAINAB tayi hadi da kallonshi cikin mamaki duba da irin yadda ya rufe ido yake ta faman masifa kamar bai san da wacce yakeyi ba ya fice ya barta anan  tsugunne kan gwaiwuyinta ,can kuma sai ta tuna ai dole zaiyi masifa duba da yadda ta saba masa da mi'ka mishi  jikinta a koda yaushe, kamin cikin ya samu, tayi iya yinta itama wajan taga tana iya jure masa a duk lkc da yaso hakan amman abin yak'i domin kuwa duk lkc da RABI'U yazo kwanciya da ita ji take yana mata wani irin wari wannan ce take k'ara sa ambaliyar amai da zarar ya nemata" shi kuwa sai yake ganin ai ta raina shine hadi da wulak'anci shi yasa ko tausaya mata baya yi a duk lkc da yaganta a irin wannan halin. tashi tayi da k'yar Ta mike ta goge hawaye da yake fuskarta ko wanka batayi ba ta sake kaya ta dauki kudin mota ta nufi gidansu,"tun daga sallamarta mahaifiyar ta tabbatar ba lfy ba, duba da yadda taga ZAINAB cikin tashin hankali hakan ne yabata damar tambayar ZAINAB ko lfy?" Asmwa ZAINAB tayi jiki a san yaye da cewar lfy qlu MAMA, ta tsuke bakinta daga haka ta k'arasa dakinsu inda k'anneta suke, duk suka tashi da murnar ganin yayar tasu"ta amsa fuska babu walwala ta nemi gefen gado ta kwanta ba tare da ta kara cewa kowa komai ba a haka bacci yayi awan gaba da ita." Sanin halin mahaifin ZAINAB da mahaifiyar tata tayi ne yasa ko bin ta kanta bata k'arayi ba domin ba nisa yayi ba tasan da zarar yazo ya sameta tare da ZAINAB din zaice tana kitsa mata wani abune na rashin arziki tunda tun farko sai da ta nuna bata son ZAINAB ta auri RABI'U amman ZAINAB ta k'ek'ashe idonta da cewar shine za6in zuciyar ta."  ZAINAB bata fi minti talatin da kwanciyar ba mahaifinta ya shigo inda mahaifiyarta ta sanar masa cewar ZAINAB tazo"da kanshi ya k'arasa har kofar d'akin da take kwance yayi sallama yasa d'aya daga cikin k'anneta su taso ta,a firgice ZAINAB ta tashi domin tasan mahifinta mutune mai a k'idar gaske baya daukar raini, fitowa tayi da sauri wanda yayi dai2 da tashin zuciyarta nan fa ta dinga amai babu k'auk'autawa ganin haka shine ya hana mahaifinta yin fad'an daya saba. Ya koma dakinshi kai tsaye da cewar idan ta natsa yana jiranta ta sameshi can" kai kawai ZAINAB ta daga alamar toh ta cigaba da yin aman a inda ya barta. Mahaifiyarta yi tayi kamar bazata kawowa ZAINAB dauki ba, sai da taga abin ya ta'azarra sanna ta baro inda take zaune take aiki ta zo kanta domin tallafa mata" a hankali ta janyeta daga inda take ta samo ruwa da tsumma ta gyara wajan sanna ta sake komawa ta hada ruwan wanka takai mata band'aki, a sanyayye ZAINAB, ta mik'e tayi wanka,ita kuwa mahaifiyar tata dakin yaran ta koma ta kara gyrawa sannan ta koma kan aikin da takeyi, ta fahinci halin da ZAINAB take ciki watau na samun cikin nata ko daga yanayin sauyawar walwalarta da kuma daukewar da jikinta yayi ga uwa uba amai da takeyi," wannan ne ya tabbatar mata cewar yar tata ciki gareta., Ba wani 6ata lkc ZAINAB tayi ba wajan wanka ta fito ta koma dakin k'annen nata ta takure, kunun tsamiya mahaifiyar ta damo mata ta shigo ta bata tace tasha"ba qaramin dadi kunun yayiwa ZAINAB duba da yadda ta kasance cikin rashin jin dadin bakinta, a hankali ta ringa shan kunun sai gashi ta shanye shi kamar wasa  ga mamakinta kuma batayi amai ba, ganin ta sami natsuwa ne yasa mahaifiyar ta, shigowa ta sanar mata da cewar taje mahaifinta na jiranta" amsawa ZAINAB tayi da toh ta tashi ta nemi hijab dinta ta saka ta bi bayan mahaifiyar tata  dakin mahaifinta ,tayi sallama suka amsa mata"  zaune ta sameshi  mahaifin nata yana duba littafin addini, ya taso akan son yawan karatu k'ananun littafai na addini, sai da yakai k'arshen karutunshi ya dago ya kalli ZAINAB da cewar na tamabayi mahaifiyarki ko lfy kika zo gida? Tace min bata san dalili ba shine nace kizo naji daga gareki" amsawa ZAINAB tayi cikin rawar baki da cewar  daman banida lfy ne shine na taho" kallonta ya k'arayi cikin ido da cewar uhumm?" Tai shiru a karo na biyu" Ko RABI'U ne yace kizo gidan? Ta girgaza kai", ya k'ara da cewar toh mekike nufi? Tayi shiru nan fa ya ringa yi mata fad'a kamar zai doketa hadi da cewar shi gidanshi ba'a isa a ce anyo yaji har an zauna ba" dan haka ta tashi ta shirya ta koma dakinta, ganin yadda mahaifin ZAINAB yake ta fada babu sauki ko daga k'afa hakan ne yasa mahaifiyarta bata saka baki a maganar ZAINAB ba." Hakan ce tasa ZAINAB dole ta sake kamo hanyar dawowa gidan RABI'U  gwaiwa babu kwari ta dawo,ko data dawo haka rayuwa ta cigaba da tafiya a tsakaninta da mijinta yau da dadi gobe babu, gashi tana tsoran taje gida ta Sanar a haka dai har cikin ZAINAB ya isa haihuwa bata tsinke da al'amarin RABI'U ba sai a wannan daren da zata haihu da ta rok'eshi da magiyar yaje ya sanar da mahaifanta halin da take ciki" ya amsa,  fita yayi ya nemi mai mashin ya daukeshi yaje  gidan su  ZAINAB yayi sallama a lokacin yayi sa'ar mahaifinta ya dawo daga masllaci ya sanar masa da cewar ZAINAB tana gida tana nak'uda aje kanta, da sauri malam AUDU watau mahaifin ZAINAB ya koma ya sanarwa da mahaifiyarta halin da ZAINAB take ciki hadi da yi mata umarnin ta shirya taje gareta," toh kawai tace a hanxarce ta koma dakinta, ta dauki hijab, " bai tsaya jin ta bakin matarshi ba yasake dawowa kofar gida domin neman shawarar sirikin nashi kan yadda za'ayi da ZAINAB  ga mamaki yana fitowa baiga dan mashin da yakawo RABI'U  gidansu ba bare RABI'UN mamaki ne ya  rufeshi amman sai ya kawo ko firgicine hakan tasa ya koma cikin gidan domin kara SA mahaifiyar ZAINAB tayo hanzari su tafi tare, A soron gidan yayi kaci6us  da mahaifiyar ZAINAB din yace mata yawwa kin taho?" Ta amsa da cewar eh" yace hanzarta muje na rakaki mamakine ya kama mahaifiyar ZAINAB ganin yadda MALAM AUDU ya keta rawar jiki, batayi tsammanin hakan daga gareshi ba tunda tasan mutum ne mai tsatsauran ra'ayi" tafiya suka cigaba da yi har suka k' arasa titi motar ta ratsa ta tsakiyar unguwar tasu, suka yi sa'ar samu mai texi din da zai kaisu unguwar da ZAINAB take, a hanya ne MALAM AUDU ya roki mai motar ya taimaka ya kaisu har kofar gida  yar tasu da sanar mishi halin da suke cikin ya tausaya musu matuk'a driver, sanna ya karfafa musu gwaiwar zai taimakesu zuwa gidan yar tasu."   ita kuwa  mahaifiyar ZAINAB jinsu kawai takeyi amman bata fashintar maganar da malam yakeyi da driver sabida hankalinta baya tare da ita, har suka k'araso kofar gidan yar tasu," koda sukazo a bude suka sami kofar gidan ZAINAB kamar yadda sukayi tsammani, kaitsaye mahaifiyar ta kutsakai cikin gidan bata tsaya jiran umarnin mai gidan na taba, sallama tayi tun daga tsayar gidan amman shiru har ta kusa k'arasawa d'akin Sai taji ZAINAB ta amsa da k'yar hakan ne yasa ta k'arasawa cikin dakin da saurin inda ta sami ZAINAB kwance cikin jini kware_kaware a gigice ta dagota tana yi mata sannu,kai kawai ZAINAB ta d'agawa mahaifiyarta, da sauri ta jinginar da ita jikin gado takoma waje wajan MALAM AUDU domin ta sanar mishi halin da ZAINAB take ciki" tana fita ta sanar mishi, tambayarta ya farayi da ina sirikinshi?"amsawa mahaifiyar ZAINAB tayi da cewar ai babu kowa a gidan sai ita kad'e  mamaki ne ya kama MALAM AUDU  amman sai kuma yayi tunanin RABI'U ko yaje kiran likitane" duk abinda akeyi driver taxi din nan yana tsaye bai tafi ba, yana jiransu ya ji idan asibitin zai kai su toh  ya jirasu" nuni MALAM AUDU yayiwa matarshi da cewar ta koma ciki gashi nan zuwa"komawa mahafiyar ZAINAB tayi ba tare da tacewa mijin nata komai ba'  tana shiga sai ga mai gidan nata ya shigo shima ya shigo har tsakiyar d'akin ZAINAB din bai jira wata_wata ba ya kalli matar tashi da cewar HALIMA mai zamu jira garinyi?" Ai kawai kamomin ita muje asibiti tunda naga alamar tana jin jiki"toh kawai mahaifiyar ZAINAB tace domin ta dade bataji mai gidan nata ya ambaci sunana ta, sabida tsabar kawaici" daukanta sukayi chas har mota suka sakata,sanna mahaifiyar tata ta dawo ta gidan nata ta  dauki zannuwa ZAINAB ta janyo d'akin nata ta fito ta fad'a mota,shigar su mota ke da wuya sai ga RABI'U ya dawo da sauri MALAM AUDU ya fito ya tareshi da cewar munzo gidan ne tunda nazo bamu ganka ba,gashi ZAINAB tana buqatar taimakon gaggawa shine zamu kaita asibiti" yak'e RABI'U yayiwa MALAM AUDU hadi da juya yar bak'ar ledar hannushi da cewar babu damuwa, kuje kawai zan biyo bayanku, bari na shiga na ajje ledar hannuna daman magani naje sayo mata"toh kawai MALAM AUDU yace ya koma mota a tunaninshi abinda RABI'U ya fada gaskiya ne,suka ja mota suka tafi amman ko lek'awa baiyi yace wa ZAINAB y jiki ba" haka suka nufi asibiti suka kai yar tasu babu RABI'U babu dalilinshi bare bare wani nashi duk da dare ne" a haka har Allah yasa ZAINAB ta haihu lfy ta sami santaleliyar budurwa duk da tsammaninsu ko RABI'U bai sami abin hawan da zai hayo ba tunda dare ya shura, MALAM AUDU ya buga wayar RABI'U arufe  daga baya ya yanke shawarar bari ya jira gari ya k'arasa wayewa ya kira ta mahifin RABI'U ya sanar mishi, haka Kuwa akayi domin MALAM AUDU yana fitowa daga masallacin asibitin ya latsa lambar mahaifin Yayi sa'ar mahaifin na RABI'U wayarshi na bude yayi sallama a ka amsa daga can 6angaren ,bayan sun gama gaisawa ne cikin girmamawa sannan ya sanarwa da mahifin sirikin nashi cewar ZAINAB ta haihu tun daren jiya ta sami mace amman suna asibiti tare da ita,yayi murnar matuk'a shima mahaifin RABI'U sanna ya k'ara da cewar basuda labarin rashin lfy tata, domin kuwa d'an nasu bai sanar musu ba,koda mahaifin RABI'U yazo kan wannan maganar sai MALAM AUDU ya nuna mishi babu komai hadi da sanar mishi da sunan asibitin da suke watau SAUDAT clinic wanda yake bayan katangar B.U.K a nan unguwar kabuga Jan bulo daman nan ZAINAB ta sanar musu tana zuwa awon ciki, anan k'awarta  RuKAIYYA SHITU ta sami aiki shine har ta bude mata file anan," basu wani bata lkc ba suma iyayen RABI'U suka hallaci asibitin da kayan baby kaca_kaca nan fa dangin suka shiga yiwa juna murnar haihuwar da ZAINAB tayi, amman har a wannan lkc gogan naku baizo asbitin ba bare  yazo yaji halin da ake ciki, duk gwaje_gwajen da za'ayiwa ZAINAB da baby anyi sanna aka sallamesu daga asibitin kai tsaye ZAINAB gidatan aka mayar da ita ta bakin mahaifin nata, wai bayason wata bid'ar tafiya gida wanka hakan baiwa mahaifiyar ZAINAB dadi ba,amman su iyayen RABI'U sai sukaji dadi kalmar MALAM AUDU domin kuwa suna ganin baya kyau tuwa ayi sunan surukar tasu a gidan iyayaenta, tunda daga asibiti MALAM AUDU yayi ma su mahifin RABI'U sallama yace zai koma gida ya shirya yaje kauye domin sanar da danginshi ya dauko wacce zata kula da ZAINAB wajan yi mata wankan jego godiya, suka k'ara yi masa da yabawa bisa hallacin da yayi musu  sannan ya tafi,. Ita kuwa mahaifiyar ZAINAB kafarta kafar yarta har gidan ta,inda suka rankawa tare da iyayen mijin ZAINAB din ,suka tarar da RABI'U yana gidan yanata sharbar bacci abinshi har wannan lkc,mahaifiyar ZAINAB batayi mamakin abinda yayi musu ba tun daga daren jiya har kawo safiyar yau din" shi kanshi RABI'U tashi yayi a kunya ce bisa ga abinda yayiwa iyayen matar tashi, koda ya fuskanci basu sanarwa mahaifanshi ba sai ya marzaye idon shi kamar bashi yayi wannan rashin mutuncin ba. Da mahaifiyar ZAINAB da tashi, haka da sauran dangin haka suka hadu suka gyara ZAINAB da babynta kana suka gyara komai wanda ya lalace tun farkon fara nak'udar  ZAINAB ta fara a gida" daga k'arshe mahaifiyar ZAINAB tayi musu sallama itama ta koma gida domin ta sanarwa nata dangin da mak'ofta cewar ZAINAB ta sauka lfy, "Tana isa gida ta fara aikawa makwaftanta cewar ZAINAB ta sauka lfy" nan fa gida  ya cika da jama'a duk da ba ta sami natsuwar da zata aikawa da sauran  danginta da suke nesa ba,amman anyi mata kara iya mutuk'a" shi kuwa MALAM tun bayan dawowarshi daga asibitin shima gida ya dawo ya shirya ya tafi kauye su watau GULU domin sanar da yan uwanshi cewar ZAINAB ta haihu lfy, ko da ya isa ya sanar musu da hakan sunyi matuk'ar farin ciki da jin yar tasu ta sauka lfy,haka dai sukai ta aikawa 'yan uwansu  na kusa ana sanar dasu cewar ZAINAB ta haihu" MALAM AUDU bai baro kauyesu ba sai da yayi duk wata shawara da yan uwanshi kan cewar INNA TALATU ce  zata zaunawa ZAINAB  tai mata zaman da6aro" sakamakon ita kade ce  mace a gurin mahaifan su MALAM AUDU" tana zaman  gida ne sakamakon rasuwar mijinta wannan hujjar ce tasa koda suka sanar mata da kudirin yayan nata,batayi musu ba,  batada miji bare ta buk'aci jiran umarni" a yammacin ranar suka taho da yayan nata hadi da kayan sha tara ta arziki wanda yan uwa da dangin suka hado aka fara yo gaba dasu kamin su biyo bayan su kashe gari Domin ganin lfy maijego"

bayan  saukar MALAM AUDU gida da shi da y'ar uwanshi, gaisawa kawai tayi da matar yayan nata,  tayi musu sallama da cewar ta tafi kula da tafiyar yarta watau ZAINAB" zo kaga rawar kai gurin angon karni watau RABI'U domin shima kayayayaki ya sayowa jaririyar da ZAINAB masu kyau da tsada, sai shiga yake yana fita shima kamar bashine yake nuna halin ko in kula da ZAINAB din ba"Ita kanta tayi mamakin yadda taga cikin k'ank'anin lkc mijin nata ya sauya kamar bashi ba".

 "Dangin mahaifinta dana mahaifiyarta duk sunzo ganin lafiyarta kashe garin da ta haihu kamin yan suna su zo suna".

Haka dai  RABI'U yayi ta hidima shida iyayenshi da sauran dangin da abokanan arziki" Suma a nasu 6angaren dangin mijin na ZAINAB sunyi duk abinda ya dace sannan domin kuwa tunda suka dawo daga asibiti lbr ya ishe sauran danginsu haka sukaita zuwa ganin jaririya da kayayayyakin su na barka"Abufa yakai Abu domin kowa yasan mahaifan RABI'U mutane ne masu kara da zuminci shi yasa duk wanda yaji matar d'ansu ta haihu baya k'asa a gwuiwa sai yazo yaga lfy ZAINAB da 'yart haka dai 'yan uwa da abokanan arziki sukai ta zuwa  da abin arzik'insu".

Acan ma gidan su ZAINAB haka iyayenta da danginta suka kawo nasu kayan sha tara ta arzik'in suka kawowa ZAINAB,"

"har akai suna yarinyar taci suna MARIYATU sunan kakar RABI'U ce ta wajan uwa gidan baya yankewa da jama'a wannan ce tasa RAB'IU ya mayar da hankalinshi sosai kan ZAINAB da 'yarsu gudun kar aga wani bak'on yanayi daga gareshi lbr ya sami iyayenshi wannan ce tasa ya mantar da ZAINAB duk wata cusgunawar da yayi mata a baya"..............






~AMENAT KABER KIRU~










*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan mu,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan auren mu a wannan zamanin*


*🅾3⃣*


"Ko dan idon k'anwar mahaifin ZAINAB  tasa RABI'U ya sauya taku?" haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya ZAINAB da RABI'U cikin basu kulawar gaske, kamar wasa kwanci tashi har yarsu ta cika shera biyu chif babu wani abu na cutarwa da RABI'U ya cigaba da nunawa ZAINAB" bayan an d'auke  MARIYA ne zuwa gidan su ZAINAB yaye" RABI'U ya shiga rayuwar ZAINAB da wani salo na nuna kulawa da kyautata mata,baya son yaga wani abun da zai 6ata mata zuciya ko ranta, kullum a  gida yake kusan yini ko gurin sana'arshi bai ciki fita ba yana manne da ita"fahintar da ZAINAB tayi na cewar RABI'U d'anson biyan buk'atane da jin dadi daga mace, wannan ce ta bata damar daura dammarar yi masa duk abinda yake so shima," ko kadan bata nuna gajiyawarta akanshi wajan jure masa akan duk wata buk'atuwa tata zuwa gareshi"ko kadan shima RABI'U baya gajiyawa da jikin na ZAINAB domin kuwa hakan yafi so tunda yanxu babu wani abu da zaiyi masa birki 'ya ce an dauke ta,tana hannun kakanninta, abu kamar wasa dai ZAINAB batayi wata biyu da yaye MARIYA ba wani cikin ya sake shigarta haka ta fara amaye_amaye kamar dai lkcn da tasami cikin MARIYA" nan fa RABI'U ya fara jin haushinta  had'i da cin zarafinta" kullum fada da masifa babu kama hannun yaro" Haka RABI'U ya dinga gara ZAINAB,daga kashe ya bijiro mata da cewar lallai sai ta zubar da cikin jikinta" ZAINAB kin yadda tayi da kudirin RABI'U" shi kuwa ya fita harkarta" ganin hakan tasa ZAINAB ta shirya ta je gidan iyayenshi domin sanar musu da halin da suke ciki ita da mijinta, koda ZAINAB taje kasa gaya musu tayi duba da yadda  dan nasu yake kyauta ta musu tasan idan tagaya musu ba lallai su yadda ba kuma kamar ta ragewa kanta k'imane a idon surakan nata,duk da mu'amalar da yake nuna mata daban wacce yake nunawa iyayenshi daban" wannan ce tasa ZAINAB ta rasa kwarin gwiwar gaya musu komai"sai da yamma likis ta koma gida yammar da bazata manta da ita ba a rayuwar ta ,tana komawa gida ta tsinci kanta a wani irin yanayin mai ban  tausayi domin kuwa wani irin jiri ta ringa gani hadi da ciwan kai mai tsanani har wani Kore_Kore take ganin garin yana juya mata, da k'yar ta k'arasa shiga d'akinta ta sami guri ta kwanta,tana faman kiran sunan ALLAH, batafi mutuna goma da shiga wannan halin ba sai ga RABI'U ya dawo gida" yana shigowa ya sameta a wannan halin yi yayi kamar bazai bata agaji ba domin gani yake kamar karya take ganin ciwan nata yana qara ta'azara ne yasa ya budi baki ya tamabayeta ko lfy?" Amsawa ZAINAB tayi da cewar batada lfy hadi da sanar mishi irin yanayin da take ji" sannu kawai yace mata ya sake kada kanshi waje ya fita" koda ya fita chemist ya wuce yaje ya sayo mgunguna ya kawowa ZAINAB yace ta tashi tasha" a gwaugwauce tasha maganin ido rufe domin ji take kamar ranar zata bar duniya" ALLAH sarki ZAINAB shan maganin nata ke da wuya baifi mitin biyu zuwa uku ba ciwo ya k'ara tsananta tun tana iya fahintar inda kanta  yake har ta daina ganewa" tana cikin wannan halin ne jini ya yanke mata ya fara zuba ganin zubar jinice ta kara rikitar da jikin ZAINAB kamin kace wani Abu tuni ta sume a inda take ko motsi ta daina!" ganin halin da ta shigane yasa RABI'U fita daga gidan a gurguje yayi waje ya samu motar da zata kaita asibiti cak ya dauke ta ya fitar da ita zuwa kofar gida ya jefata jikin motar da ya samo ba tare da ya sanarwa kowa ba"da zuwansu aka kar6esu cikin gaggawa duba da irin halin da su kaga ZAINAB na ciki"  nan da nan likitoci suka zo kanta aka fara kokarin ceto rayuwarta, cikin k'aramin lkc" koda ZAINAB ta farfado batayi mamakin ganinta a asibiti ba domin tasan komai zai iya faruwa da ita, koda kuwa mutuwa ce a yadda ta tsinci kanta,"ba wani ciwo da yake damun ZAINAB illa rashin kwarin jiki da takeji ko da ta farfado" Da sauri RABI'U ya k'araso kusa da gadon da ZAINAB take kwance yayi mata sannu!" Amsawa tayi ba tare da ta kalli fuskarshi ba tace yawwa! Ta mayar da kallonta xuwa ga silin din dake saman d'akin, suna cikin wannan halin ne wata nurse ta shigo dauke da faranti wanda yake cike da allurori ta k'araso inda ZAINAB take kwance tayi mata sannu hadi da yi mata nunin ta gyara zata yi mata allura" amsawa ZAINAB tayi tare da gyara wa lkc guda,"Nurse din  tayi mata allurorin har guda biyu,bayan ta gamane ta kalli ZAINAB da RABI'U a tare ta fara yi musu tambayar menene dalilin da yasa zasu zibar da ciki wanda a sakamakon haka   da kyar suka sami ceto rayuwar ZAINAB din?" Kallon2 suka fara a tsakanin su wanda yasa ZAINAB kasa jure hakan domin batasan amsar Da zata bayar ba" shi kuwa RABI'U da yasan komai shima kasa bud'e bakinshi yayi, ya yiwa Nurse bayanin shine ya bawa ZAINAB k'wayoyin da yasa ta  cikin ya zube,wani gumine ya fara karyo masa tare da bayyana fargabarshi na furta shine ya bawa ZAINAB maganin a sarari" jin basuda niyya bata amsa yasa ta fara yi musu masifa tare da yiwa ZAINAB gargadi hadi da Jan kunne da nuna mata idan bata son ta dauki ciki kar ma ta bari ta dauka bare har taje tana shan maganin da zai k'arar da rayuwatar"tun kamin takai k'arshen maganarta ZAINAB ta saki salati hadi da wata irin k'ara tana fadin RABI'U ka cutar dani idan baka sona ka sakeni na huta ba sai ka kasheni ba ,ka kashe abinda yake cikina ba!!!" Jin wadan nan kalaman da suke fita daga bakin ZAINAB yasa Nurse din ta tabbatar bada sanin ta cikin ya zube ba, rarrashin ZAINAB ta shiga yi da nuna mata muhimmancin yadda da kaddara" kukane yaci k'arfin ZAINAB da take kwance a kan gado mai ban tasauyi da rikita zuciya" wannan dalilin ne ya hana RABI'U ko motsi a inda yake yana dai kallon su yana kuma sauraron duk abinda yake wakana" banda kugin kukan ZAINAB babu abinda yake tashi a d'akin" jin hakan ne yasa Nurse din tayiwa RABI'U nuni da tafiya waje" amsawa yayi kawai da toh ya fita." bayan fitar shine ta k'ara gyara murya ta kira sunan ZAINAB a hankali" ZAINAB ta dan saurara da kukan da tayi ta amsa da mata" jin dadin hakan Nurse tayi da taga ZAINAB din har ta kawo hankalinta gareta sai ta k'ara yi mata nasiha hadi da rarrashinta da bata shawarwari akan yadda zata kauracewa duk wani abu da zai daga mata hankali dangane da irin hakan idan ya taso, ta nuna mata abu mafi mahinmmanci shine idan kinsan zaki sami ciki da mai gidanki yazo yana baki k'wayoyin da zasu jefa rayuwarki cikin hadari to karki fara daukan cikin ma sai ki dauki matakin daukan baki daya,duba yadda rayuwar nan ta sauya mafi akasarin maza basa buk'atar haihuwa gaskiya abinda nake so na sanar miki kenan ina fatan zaki karbi shawarata?" kai kawai ZAINAB ta daga mata domin kuwa jinta kawai takeyi tunda ta fara maganganunta ita ba fashimta take ba sabida tsananin bugar zuciyar da take ji" fuskantar hakan da tayi daga ZAINAB yasa ta ci gaba da bata bakin tayi hakuri akan duk abinda ya faru da ita"toh kawai ZAINAB ta cewa Nurse din ta kara kwantar da kanta gefe tana  cigaba da zubar da hawaye" jin zainab tayi shiru ne yasa nurse ta k'ara tambayar ZAINAB ko tana jin wani ciwo?" A'a zaina tace kawai " hakan ce tasa nurse din fita daga d'akin inda tayi kacibus da RABI'U ya k'osa ya shigo domin kuwa ya kosa a wajan da ya fita shima" Domin kuwa gani yake kamar Nurse din zata matsa ma ZAINAB da tambayoyi shine dalilin kosawarshi"murmushi Nurse din tayi masa hadi da cewar ka gaji ta jirana ko?" Amsawa yayi  da cewar ko kadan likita" sake murmushin tayi a karo na biyu da cewar bari na dawo ai yanzu zamu sallameku duba da yadda abin yazo da sauki kuma tace min babu wani ciwo da take ji a halin yanzu wannan dalilin yasa zamu sallameku yanxu amman jirani k'adan dan Allah ina zuwa" toh RABI'U yace cike da gwarin giwar jin kalaman Nurse din" yasa kai ya shiga d'akin fuska a sake kamar bai aikata komai ba" ganin haka yasa ZAINAB tamke tata fuskar a gareshi" yi yayi kamar bai san tanayi ba ya k'ara matsawa kusa da gadon da take kwance hadi da kamo hannunta" fizgewa ZAINAB tayi had'i da dakatar dashi da dayan hannun da cewar dakata MALAM bakada wata magana da zaka gayamin maha'inci kawai" hakan shine yayi dai2 sallama Dr tare da nurse da sukaji yasa tayi shuru amsawa RABI'U yayi fuska a sake" k'arasawa Dr yayi jikin gadon ZAINAB ya duddubata sosai sanna ya karbi katin ta a hannun Nurse din take biye dashi yayi rubuce2 da zaiyi sanna ya mik'awa RABI'U" karba yayi jiki na rawa hadi da yiwa Dr karin godiya" Dr ya amsa hadi da mika masa hannu sanna ya kara jaddada masa cewar lallai yasa yi magungunan da ya rubuta musu sanna ya ringa saya mata kayan fruit wadanda zasu kara mata jini"amsawa RABI'U yayi da insha Allah" sanna Dr ya koma kan ZAINAB da bayaninshi da cewar ta ringa yawan shan abu mai dumi banda mai Sanyi koda wankane kar tayi da mai Sanyi har sai bayan sati biyu ta kuma daure ta ringa shan magani duba da yadda ta zubar da jini mai yawa"toh kawai ZAINAB ta cewa Dr" shima bai jira yaji wani k'arin bayani daga bakin ZAINAB din ba tunda ya fuskanta tana cikin wani yanayi na rashin jin dadin zuciya" kallon RABI'U ya k'arayi da cewar babu komai kwa iya tafiya idan ta Dada hutawa" godiya RABI'U yayi da cewar toh likita mungode da shawarar ka" OK kawai Dr yace suka juya suka fice daga dakin. Suna fita ya sake komawa jikin gadon da ZAINAB take kwance yace mata ta tashi ta shirya kamin ya samo mota su tafi" shiru tayi kamar bata ji shiba ta cigaba da zubar da hawayen da tacigaba dayi tun bayan fitar Dr" bata k'ara cewa komai ba, kallonta yayi hadi da zama daga gefen gadon ya kamo hannunta da cewar magana nakefa kinmin shiru" yi tayi kamar bazata amsa ba" sai ji tayi ya k'ara kama hannunta had'i da dago kanta da cewar haba ZAINAB me yasa kika kasa fahimtar abinda nakeso ne? Kinsan ni dai ba mutum ne mai damuwa da haihuwa ba amman kin kasa ganewa wallahi ZAINAB ina matukar kaunarki da zaki yadda ki gane hakan da lfy k'alau zamu zauna muyi rayuwa idan har kika bi abinda nakeso zan nuna miki duk wata kulawar da ta dace" koda yazo dai2 nan sake d'aga masa hannu tayi tana magana cikin shashekar kuka tace ya isa MALAM nidai nace ka sakeni daga nan ma na wuce gidan iyayena" wani irin kallon rashin fahinta yayi mata da cewar ZAINAB kece kike fad'an wannan kalmar da bakinki? Toh bari kiji  yanzu na shirya zama dake dan kiji kuma babu inda zaki daga nan da ya wuce gidana" fasa fita yayi ya samo motar kawai ya mike ya tattara duk wani abun da yake nasu ya fizgi hannunta kamar yarinya yayi  waje da ita,ganin da gaske yake ga rashin kwarin jiki da yake damunta  gashi daga fitowarsu daga d'akin da aka kwantar da ita har mutanen dake gefensu sun fara lekowa shine yasa tace ya sakar mata hannu taji zata iya tafi ba sai yajata da karfi ba"ganin hakan shima yasa ya biye matan ya saki hannunta suka jera a hankali har suka isa bakin get din asibitin bai tsaya jiran mota ba ya tarar musu kafi babur suka hau suka nufi gida. Da Isar su gida ya hau gaganiyar dorawa ZAINAB ruwan wanka duk tana jinshi har yayi ya gama sannan ya shigo daki ya Sameta a kwance tana faman zubar hawaye  ya sami guri ya zauna daga gefe, ba tare da yace mata komai ba, hannunshi yasa ya tallafota hadi da dora kanta a kan cinyoyinshi, itama ZAINAB din zamewa tayi ba tare da d'aga ido ta kalleshi ba. Bai wani tsaya jin sautin kukanta ba ya kara cewa haba ZAINAB sai hawayenki ya kare? Ina sai nake ganin duk abinda Allah ya kaddara babu makawar ketareshi ina mai baki hakuri bisa duk abinda nayi miki wallahi, wallahi ZAINAB dan bakisan yadda nakejin kukan nan naki ba har cikin zuciyata amman kin kasa fuskanta hakan sai k'arawa ma kikayi ko?" Shiru ZAINAB tayi kamar wacce ruwa ya cinye sabida bata san amsar da zata bashi" ganin batada niyyar cewa komai yasa RABIU tashi ya kara komawa kitchen ya zauna sai da ya tabbatar ruwan yayi zafi dai_dai wanka ba tare da ansurka ba ya kai bayi ya hada mata komai na wankan sannan ya  dawo ya cewa ZAINAB ta tashi ya rakata tayi wanka kar tayi wasa da jikinta"wani irin kallo ta bishi da shi ba tare da tace masa komai ba" ganin batada niyyan tashi yasa ya dauke ta chak yayi bayi da ita,  sannan ya shiga cire mata kaya" sake d'aga masa hannu tayi da yabar mata kayanta ita zata cire da kanta" babu yadda ya iya haka yabarta a cikin bayin ya fito"..........




~AMENAT KABER KIRU~







*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*



*🅾4⃣*



Ya na fita ya rufeta, ta waje yasaka makulli domin gudun kar tayi yunk'uri guduwa daga gidan. kayan ciye2 ya sayo mata da duk wani abu da zata buk'ata wanda  yasan tana so ya haďo mata da magungunan da Dr ya rubuto musu ya dawo. Koda ya dawo sai ya iske ZAINAB tayi bacci haka ya aje komai ya shirya duk wani abu da yasan ba gurin zamansa bane a d'akin sannan ya tashe ta daga bacci yace taci abinci." wani irin kallon tuhuma ZAINAB ta k'ara binsa dashi ta mayar dakai ta koma" baiyi zuciya ba ya shiga rarashinta kamar wata yariya ganin ya nace yasa ta tashi ta ci komai kadan2 ta ture duk da yunwar da takeji amma haka nan tabar masa kayanshi ya cinye wadanda yake ganin zasu lalace kamin safiya.

"tunda RABI'U ya fuskanci ZAINAB tana fushi dashi taki sakin jikinta yaita faman bata kulawa babu ji babu gani komai shi hatta birni da wasu aikace2 gida ya hanata  tayi, ko fita yayi  baya dadewa yake dawowa  gudun kar ZAINAB  ta sami damar fita bada saninshi ba ko wani yazo ta sami damar gaya masa." Lamfa ZAINAB tayi wa RABI'U da nuna mishi ta hakura da duk wani wulak'anci da yayi mata a baya har  jikinta  ya warke sarai" ganin haka shima RABI'U sakin jikinshi da'ita kamar babu wani abu da ya shiga tsakaninsu hakan ce tasa ZAINAB bayan ya fita wajan neman kudinshi ta shirya kayana tsaf ta gudu gidansu a karo na biyu" koda ta isa gida kuwa babu sa'a kamar zuwana na farko domin tun kamin ta k'arasa gida  ta hange MALAM yana fitowa daga gidan nasu da alama fita zaiyi.tana hangoshi kuwa gabanta ya fara daukan uku2!!"yi tayi kamar ta yasar  da akwatin  da take rike da shi a hannunta ta juya da gudu ganin irin kallon tuhu MALAM din yake mata tun kamin ta k'araso  inda yake tsaye chak,"durkusawa tayi haďi da cewa" ina kwana MALAM baki na rawa" "ya amsa tare da cewar muje ciki" "tashi ZAINAB tayi tsam ta shiga MALAM na yabi bayanta" tana yin sallama d'akin mahaifiyarta ta shige hadi da sallama" mahaifiyarta dake cikin dakin tana ninke kayan wanki ta amsa" shiga ZAINAB tayi ta sami gefe guda ta zauana tare da akwatinta a gefe ba tare da tacewa mahaifiyar tata komai ba"itama bata tambayeni ta ba taji dalilin zuwanta gidan ba" MALAM ne yayi sallama suka amsa a tare" sanna ya shigo ya wuce gefen gado ya zauna sanna ya dubi ZAINAB da cewar lafiya? Amsawa ZAINAB tayi da cewar eh MALAM" sakae kefa mata wata tambayar yayi da cewar ina zaki da kaya toh?" Ji ZAINAB tayi bakina yayi nauyi da tambayar MALAM din" shiyasa tayi shiru kamar wacce ruwa ya cinye, bude baki tayi yana rawa da cewar MALAM wallahi na gaji da halin da RABI'u yake min ne"  MALMA ya amsa da uhumm" tun kamai takara  cewa wani abu ya sake cemata kashe auren kikayi" girgiza kai ZAINAB tayi kawai da cewar A'a" toh mekike nufi da tahowar da kikayi?" Shiru ZAINAB tayi" domin ta rasa rasa ta inaza zata fito da maganar abida RABI'U yayi mata ,ganin haka yasa  MALAM ya dinga yiwa ZAINAB fada ta inda ya shiga ba tanan yake shiga ba, jin ZAINAB bata kwakwaran dalili yasa MALAM ya cewa ZAINAB ta tashi ta koma inda ta fito" jin haka yasa mahaifiyar ZAINAB saka bakin cewa haba MALAM!" Ai yana da kyau mu tsaya muji ta bakinta duk da karin maganar 'yan Hausa suna cewa (karfe daya baya amo) amman yana da kyau mu saurareta don jin salin dalikinta na zuwa garemu".Katseta MALAM yayi da cewar dakata HALIMA baki isa ba!! Domin na ciki sanin wacece ZAINAB tun daga yarintar ta har zuwa girmanta, kuma nafiki sanin me duniya take ciki domin ina yawo lungu da sak'o ina ganin matan da suke gantali a titunan garin nan babu aure, kanaso ta zama d'aya daga ciki ne?" Girgiza kai mahaifiyata tayi da cewar a'a ba haka nake nufi ba yana da kyau da ka duba"amsawa yayi da cewar ni ba shashan uba bane wanda da 'ya'yansa sun gaya masa magana ya hau ya zauna, na fuskanci da saka hannunki ta taho gidan ma kenan" amsawa mahaifiayar ZAINAB ta sakeyi da cewar babu saka hannu na,amman dan Allah MALAM ka saurareni yana da kyau ka san cewar zamani ya sauya akan komai musamman zamantakewar auren yanxu,da dacan da yanxu akwai banbanci...." katseta yayi da cewar" naji haka iyayen yanxu da na da can akwai banbanci ko?."Shiru tayi bata ce masa komai ba."ya cigaba da cewar  ai mu a yadda mukasan auare hakuri da juriyace kawai a ciki,kuma abin kunya ne ace kana Raye 'ya ka na gantalin yaji zuwa gida" toh_toh  naga alamar idan na daka ta taku ke da ita ba zatayi zaman auren ba."ya sake hutawa ga ZAINAB da cewar ke kuma Daga yau daga rana irin ta yau idan na sake ganin kinzo min gida da zummar yaji wallahi sai na 6ata miki rai mara musaltuwa,ki tashi ki koma inda kika fito, kuma ko gidan wani dan  uwana  idan naji lbr kije da  niyyar yaji wallahi sai kinyi mamakin hukunci da zan yake miki.,sanin halin zuciyar MALAM ne ya k'ara kada hanyar ZAINAB" sannan ya k'ara juyowa ya kalli mahaifiyar ZAINAB yace kema daga yau karna k'ara  jin kinje gidanta babu dalili ko naji wani daga cikin yaran nan yaje sai na 6ata miki!" Shiru  mahaifiyar  ZAINAB tayi kamar bata d'akin sabida takaicin d'anyen hukunci da MALAM ya yanke."ita kuwa ZAINAB tashi tayi ta sake Jan yar akwatinta ta bar gidan tana kukan abinda MALAM din yayi mata." Haka ZAINAB ta fito daga cikin gidan nasu cike da k'unar zuciya ta koma gidan ta" ta dawo babu RABI'U ya shigo yakawo mata kayan cefene rana ko kadan ZAINAB bata nunawa masa taje gida ba" alamar da ya gani ne a idonta kamar tayi kuka yabata tambayarta dalilin da yasa idonta yayi ja" amsawa tayi da babu komai."shiga dakin yayi da sauri ta duba sai yaga akwatinta a tsayar d'akin a ajiye fitowa yayi tsakar gida ya sake tamabayarta cewar"ina zata?" "Ta amsa da cewar" babu ko ina" murmushi yayi da cewar. "ZAINAB manya wai a tunaninki kina ganin zan iya rabuwa da ke ne? Ko kadan karma kiyi tunanin hakan wallahi !wallahi!!wallahi!!! rantsuwar musulmi kenan bazan iya rabuwa da ke ba dalili kuwa babu yadda zuciyata zata jure hakan, ke bari na taka ita miki ko wani namiji kika aura bazan barki ki rayu dashi cikin jin dadi ba, dan haka ki sauya tunani akan yadda zaki zauna dani cikin jin dadi da kwanciyar hankali,idan kikayi haka toh babu shakka zaki ji dadin rayuwa tare dani. ZAINAB kin kasa fashinta waje ni!!  Bare ki gane abinda nake so hakan yana gasa min zuciya amman babu yadda na iya da halinki" shiru tayi masa domin kallon mahaukaci ta ke masa tunda ya fara maganar shi toh wanne irin hali yake ciki wanda bata fuskanta ba?" Tambayar da tayiwa kwanta,ko kadan ZAINAB batayi mamakin ganganun RABI'U tunda tasanshi akan mace amman kuma na banza tunda baya iya bata kulawarka da tace" kamin ta Ankara tuni ya sureta yayi daki da ita bai dire da ita a ko ina ba sai kan gado" wantsal2 take tayi hadi da sakar mishi kuka tana cewar "nidai banaso dan Allah kabarni naji da kaina." ko kadan bai saurara mata ba ya fara danna harshen shi a bakinta yana fana k'ok'arin shafa tsakiyar kanta" kulle bakinta tayi 6am amman duk da haka sai da yayi nasara bude mata zip din rigata tabaya nuna karfinshi yayi sosai ya k'rasa bude rigar sannan ya zaro nonuwanta ya fara wasa da su" kukane ya kara cin karfin ZAINAB tana ta faman fisge2" amman hakan bata sa RABI'U ya daina abinda yake ba,binta yayi da rarashi hadi da dadin bakin cewar ZAINAB da kinsan yadda nake kaunarki da sonki da ba kiyi kukun da kikayi ba akan na rasaki gara na rasa komai a rayuwata kin kasa fuskanta ta haka dear na" kukanta ta cigaba dayi bata saurareshi ba" shima duk da hakan bai fasa abinda yayi niyya ba wasa ya shiga yi da jikinta kamar wani mahaukacin zaki haka ya dinga wujijiga ta babu yadda ZAINAB ta iya da halin mijin nata domin yafi karfinta idan tace bazata tsaya ya biya bukartashi  cikin sauki ba tasan zai iya yi mata rauni a banza wannan dalilin yasa tabarshi har yayi abinda yaga zai iya ya barta" koda ya gama abinda yake bai k'ara bin ta kanta ba ya tafi yayi wanka abinshi ya dawo ya saka kayanshi ya fita ko sallama bai mata ba, abin ya yiwa ZAINAB ciwo wanda ya k'ara tsananta mata radaddin zuciya mara musaltuwa" kuka ta yini tanayi ko girki batayi ba a wanna ranar sabida zazzabin da ya rufeta a wannan ranar." Haka dai ZAINAB ta cigaba da rayuwa da RABI'U da dad'i babu dadi tunda kullum baik'i yayi sex da ita kamar sau biyar ba, har ta ciki wata uku da yin barin wancen cikin da ya zubarmata dashi" Allah mai kyuata da k'ari ba tare da yayida shara da bayinshi ba,ya sake bata wani cikin  shima dai irin wancan babu wani abu da ZAINAB zata ci sai ta amayar dashi koda kuwa ruwane, wnana ce ta k'ara hargitsa zaman su da RABI'U idan zata kwana ta amai bazaiyi mata ko sannu ba bare ya taimaka mata, hakan ya k'arasa ZAINAB ta fita haiyacinta kamar ba ita ba, tun tana iya jurewa  tayi komai da kanta har takai da gargarar sai da nemi agajin  makwafciyat ta taimaka mata da yarinya daya daga cikin 'yayanta ta riga zuwa tana dan rage mata wasu ayukan na gida", tunda ZAINAB  ta k'ara samun cikin nan RABI'U ko ( p.c.m) bai ta6a shiga tsakanin ta dashi ba,duba da yadda salon wannan cikin na daban ne, domin kuwa bata iya yadda ko shinfinda ta hadata da RABI'U bare wani sex."



K'wanci tashi babu wuya tun cikin ZAINAB na farkon har ya tsufa bata taba zuwa awo ko sau daya ba, babu ruwan RABI'U da ita ya zuba mata ido domin shi a tunaninshi duk wata d'abi'ar ciki bai yadda da ita ba,wannan ce tasa ya watsar da lamarinta ko harkarta ya daina shiga"tasha yi masa magaiyar ya barta taje asibiti a duba lafiyar ta amman sai yayi kamar baiji ba,  yayi burus da al'amarinta" hakura tayi da maganar zuwanta asibitin dole,  tunda bara da sararin kudin motar zuwa asibitin bare kudin sayan magani. Ganin babu sarki sai Allah haka ZAINAB ta shirya kanta duk da nauyin cikinta tunda ya fara tsufa ta nufi shinfidar mijinta a wannan ranar" har ya fara bacci ta tashe a hankali" shi kuwa yana jinta yayi shiru da ita kamar baiji ba" jin nacinta yayi yawa ne yasa ya tashi zaune ya bude ido hadi da tambayar ta ko lfy?" In'ina,ZAINAB ta shiga yi sabida batasan ta ina zata fara magana ba" shirun da yaji tayi ne ya sake bashi kwarin gwaiwar komawa ya kwanta yace tunda ba tada ta cewa" ganin haka yasa ZAINAB sakin kuka ta fada kanshi da cewar dan Allah darling me nayi maka ne?"Ka fita sha'ani na sam babu ko kulawar kirki bare tausayawarka a gareni ko dan abun da yake jikina ai naci arzikin kulawarka" tashi RABI'U yayi zubar ya zauna hadi da dakatar da ita da hannu da cewar Malama kin isheni bana son takura da hana bacci ki bari idan zakiyi mitarki kya yi da safe" kara kutsa jinta ZAINAB tayi cikin nashi tana kuka hadi da yi masa magiyar ya sanar mata da laifin da tayi masa" jin fadawarta ZAINAB jikin RABI'U kuwa sai yaji kamar wanda aka bai taba riskar kanshi a irin wannan yanayin ba,yaso ya cireta daga kirhinshi amman ya kasa,sabida jinshi yake tamkar baya raye, dago kanta yayi da cewar sorry dear laifin nawa ne ba naki bane domin ni yakamata na dau matakai kamin komai ya faru sai banyi hakan ba" bude baki ZAINAB tayi tana mamakin kalamanshi sabida batayi tsammanin hakan ba" d'aga mata hira yayi da cewar eh nine mana domin da na nemi shawararki kila bazaki lamincewa kuduri na ba sai kuma banyi ba yana magana yana shafa wuyanta har yakai ga ya fara kokarin cire mata rigar bacci da take jinta duk da nakai nauyi bace kuma daman bata 6oye duk wani abu da yake jikin ta ba,ita kuwa ji take tamkar yana sassoka mata allura a jikinta amman babu yadda ta iya domin kuwa ita takai kanta domin samun masalahar zaman su, ko da yaji ZAINAB ta saki jikinta dashi zagewa yayi akanta ko tausayamata baiyi ba duba da tsufan da cikinta yayi haka ya kwana yana sex da ita tun tana iya gane ina kanta yake har ya kasance bata iya ganewa, nonuwanta kuwa tashi tayi dasu duk sun kunbura kamar ba a jinkinta suke ba,da kyar ta iya tashi ta nemi ruwan zafi ta basa jinkinta sanna tayi duk wani d'an gyare 2 da zatayi, shi kuwa gogan yana ta bacci tunda ya kwana yana aikin abu daya, bai farka daga bacci ba sai wajan tara na safe sanna ya tashi fuska a murtuke babu wal'wala koda ta gaishe shi da kyar ya iya amsawa" wannan ce ta k'ara rukitawa ZAINAB zuciya, wanda har sai da ta tambayi kanta da cewar anya kuwa RABI'U ne jiya da dare yake ta faman bata hakuri har da bata hakurin da nuna mata laifi ad gareshi ne?"  Amman da mamaki menene yake damun shi?" Me yake so a tare da ita? Wanne matakine bai dauka ba? Shin anya soyayarsu ta gaskiya?.................

Wani irin hawaye ne ya gaszayo mata daga ido zuwa kan fuskarta domin kuwa ta rasa amsoshi da take wa kanta, take taji duk wani kwarin gwaiwarta ya yake bare ta k'ara zuwa ta ji abinda tayi masa" RABI'U kuwa koda yayi wanka ficewar shi yayi ba tare da yace mata komai ba ya ko yabi ta kanta, batayi mamakin fitarsa babu magana ba duba da yanayin da ya tashi kenan" komawa itama tayi ta kwantar tana ta faman aikin kuka daga kashe ta yanke shawara cewar fita dag safgashi gabaki daya a haka bacci ya kwashe ta. Bata farka ba sai wajan karfe sha daya da rabi na rana"  sallamar dawowar  RABIU gidance tasa ta farka kayan cefene ya kawo ya ajje fuska a sake babu wanna kunci da yafita dashi a dazu, mamakine ya k'ara kama ZAINAB kamar zata tambay sai kuma tayi shiru" a dai2 lkc ne taji sallama yan uwar mahifiyar ta suna shigowa" amsawa sukayi a tare ita da mijin nata" bakin suka shigo rik'e da hannu MARIYA yar su,  sauran matan suna rike da kayayyakin yarinyar da kayan garar ta ta yaye" suka ka k'araso ciki RABI'U ya durkusa har k'asa ya gaishe su sanna ya fita yabar gidan" dadin ne ya kama ZAINAB gani yan uwan mahaifiyar ta sunzo haka ta tashi ta debo musu ruwa sanna ta dawo suka gaisa" suna cikin hira RABI'U yayi sallama a kofar dakin suka amsa ya shigo ya ajje musu ledar da take hannushi ya sake saka  hannunshi a aljihu ya ciro kudi a aljihunshi ya mik'awa ZAINAB hadi da cewar ta basu suyi kudin motar komawa" karba ta mika musu" sukayi godiya hadi da samishi albarka" ya amsa da amen sanna ya juya ya fita" mamakin halin RABI'U ZAINAB kawai takeyi a zuciyar ta idan yaga baki kamar bashi ba" tashi tayi da niyya zata darawa bakin abinci suka ce su ba zama zasuyi ba tafiya zasuyi iya lemukan da RABI'U ya kawo ya ishe su"suka raba kayan garar daa sukazo dashi gida biyu suka matsarmata danata gefe" wannan rabin kayan garar da sukace  zasu wuce dashi sukaiwa iyayen mijinta" taji dadin hakan da sukayi domin tasan idan dan ta mijinta ne sai dai kayan su ru6e bazai karba ya kaiba har kofar gida ta rakasu sanna ta dawo gida ta fada keching wanjan girki tunda yar yaye ta dawo hannunta.........





*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*



*🅾5⃣*


Haka ta tsara aiki babu ji babu gani tuwon shinkafa miyar d'anyar kub'ewa tayi tunda tasan Rabi'u yana so sosai,duk da tsufan da cikinta yayi tana yi tana hutawa har ta gama. Bai dawo ba Sai da magrib ya shigo fuska a daure tayi masa sannu da dawowa."RABI'U ya amsa ba tare da ya kalli inda take, baya shege daki abinsa" da gudu MARIYA tabi bayanshi tana kira ABBA! ABBA!!ABBA!! amman ko ya waigo.yana shiga ta k'wak'umeshi ya zareta daga jikinshi a cewarshi kar ta shafi bakin da yake jikinshi na kanikancin motar da yakeyi" hakan ce tayi dai2 da shigowar ZAINAB ta janyeta gefe" shi kuwa yi yayi kamar baisan ta shigo d'akin.da kanshi yaje ya hada ruwa yayi wanka ya fito ya shirya, bayan ya gama "ZAINAB ta gabatar"mishi da abincin shi ya zauna yana ci kamar ba shi ba ganin haka yasa"ZAINAB ta rok'eshi da rana son tayi magana dashi idan ya gama cin abinci" kai kawai ya daga mata alamar toh ya cigaba da abinda yake gabanshi"koda ya gama ci a zaton ZAINAB zai bata lkc suyi magana sai gani tayi yana wanke hannushi bai dawo ciki ba fita ya sake yi ya barta na turus da tsohun ciki a zaune" yunk'urawa ZAINAB tayi da k'yar ta tattaren kayan da RABI'U yaci abinci ta kai kitchen ta aje sannan ta dawo ta gyara wa MARIYA makwanci wanda ta dade da yin bacci tun bayan hantarar da RABI'U yayi mata tayi bacci"  ZAINAB ta dade a zaune tana zaman jiran mai gidan nata amma shiru har ta gaji tayi bacci bai dawo ba sai sha biyun dare har da rabi" haushine yasa ZAINAB kinyi masa magana koda ta farka taganshi juyawa tayi ta k'ara gyara kwanciyar ta ba tare da tace komai ba."shima hakan bai dameshi ba tunda baya buk'atar wani abu daga gareta. Ko kayan jikinshi bai cire ba ya kwanta abinsa ya kama tirk'ar bacci" ko da safiya tayi bai tsaya sauraron ZAINAB ta bashi abin karyawa ba yayi ficewarshi ya barsu ita da 'yar ta" haka dai ZAINAB tai ta gani wasu sabbabin d'abi'u daga wajan RABI'U uwa uba ko 'yar tashi baya kulawa bare ya jata a jiki" wannan ce ta k'ara d'agawa ZAINAB hankali tun tana kukan hakan har ta fara sawa zuciyar ta hakuri domin tasan kukanta bazai bata amsar da take neman sani ba, daura aniyar jiranshi tayi komai dare idan ya dawo yau kam zata tambayeshi abinda yake nufi da ita.sai dai RABI'U ya kara sauya wani halinda tsiro dashi na fita yawo dare, domin kuwa sai ya fita tun takwas na yamma amman bazai dawo  gida ba, sai karfe dayan dare ko biyu tun yana kaiwa sha biyun dare abin baya damunt sosai yanxu ya sauya taku ,tashi tayi zaune tayi tagumi haďi da tambayar kanta shin RABI'U ya daina kaunata ne ko kuwa ya daina marmarin kwantawa da ita ne?" Bata dade a zaune ba taji shigowar shi, sannu da dawowa tayi masa" ya amsa a ciki" ganin ya amsa shine abinda yasa ta sami kwarin gwaiwar yi masa magana" mik'ewa tayi ta k'araso inda yake zaune tace darling dan Allah ina da magana da kai" amsawa yayi da uhmmm sai ki fada naji" shiru ta d'anyi sannan tace daman wasu tambayoyi ne zanyi ma idan bazaka damuwa ba" toh kawai RABI'U yace ina jinki bana son takura da hana bacci" nisawa tayi da cewar daman naga ka k'ara sauyawa ne bisa yadda na sanka dan Allah idan akwai laifin da nayi ma ka sanar dani, nayi al'k'awarin gyarawa, bana jin dadin zaman mu a haka ba ni kadeba harta yar da muka haifa baka kulata  wanne laifin nayi da har ya shafeta haka?" Wani guntun murmushi ya saki wanda bai kai zuci ba, sannan yace tunda har kina neman sani yanzu saki san dalilin sauyawata, a gaskiya bana zaman k'arya da ko waye ZAINAB ya kamata ki san da hakan, why not zanyi miki bayanin abinda nake so tun kamin muyi aure amman ki kasa?" Na sanar miki ni ba mutum ne mai son tara iyalai ba amman kin kasa daukan mataki,ko kinason kullum sai na gaya miki kamar karatu?" A gaskiya ZAINAB bazan boye miki ba matuk'ar kinason zama dani toh ki dauki mataki akan duk abinda nakeso ayimin shi,baya yuwa matan waje mu kafa musu doka subi amman matarka ta gida ka gaya mata tak'i bin umaranin ka,idan kin shirya daukan matakin sai ku sanar dani gobe muje a cire cikin da yake jikinki nan" wani gumine ya dinga zubowa daga fuskar ZAINAB tunda RABI'UN ya fara bayanin bata tsinke da al'amarinshi ba sai akan kalma biyu watau matan waje da cire cikin jikinta" nisawa tayi da cewar gaskiya bazan iya cire, cikin da yake a jikina ba dalili kuwa duba da yadda cikina ya gota wata tak'was ya shiga na tara a gaskiya koda daga waje nayo bazan iya haka ba bare d'ansinnah" kuma kana maganar daukan mataki ai babu wani bawa da ya isa ya k'etare k'adararsa, banga dalilin daukan mataki ba,a maganar shigar ciki tunda kudurar Allah ce!!" Murga mata wata uwar harara yayi da cewar sai kije kiji da kudurar Allah ke k'ade basai na kara kusantar kiba ma bare hakan ta faru!!" Aikin banza kawai ga matacan masu jajayen cinyoyi a waje, kwanciya sai irin yadda yakaso akeyi ma ita, ni ina zan zauna ina batawa kaina lkc akan matar da bata ilimi zamantakewar rayuwa?" Ya juya ya kwanta yana ta faman zazagawa ZAINAB bak'ak'en maganganu" taji bakin cikin maganganunshi matuk'a" Wani kukan bakin ciki ZAINAB ta rushe da shi mai fauna zuciya da tausayawa, mik'ewa tayi ta koma gurin kwanciyarta tacigaba da yin kuka a haka ta yi mai isarta ta gama har kusan asuba bata rintsa ba,haka bata sami shawarar yadda zatayi da  RABI'U ba,dalili idan ta daka ta tashi akeje cire ciki ta mutu fa? mai zata gayawa ubangijinta"domin kuwa tasan ba'ayiwa abokin hallita biyayya a sa6awa mahallici, ta dai barwa zuciyarta ta rabu dashi har zuwa lkc da zata haife cikin kinga ayi duk maj yuwa" koda gari ya waye tan tangarau RABI'U yana ta kwasar bacci abinshi, yi ZAINAB tayi kamar bazata tashe shi ba, yadda MARIYA take ta kukan neman abinci kari,ta duba kuma basuda sauran kayan tea wanna hujjar CE tasa ZAINAB  kasa jurar kukun MARIYA,dole ta nufi har inda yake  RABI'U yake kwance ta ta6ashi a hankali tace ya tashi gari ya waye har karo uku, amman yana jinta, sai daga ta koma na karo na hudu ya sanar mata wani irin wawan tsaki" ko kadan bata ji bata jira ya kara cewa wani abu ba ta ce masa dan Allah ka tashi MARIYA ce take ta kukan zata sha tea shine dalilin sake dawowata" tashi yayi ya zauna ya bude idonshi tas sannan ya kalli ZAINAB da cewar anki a sayo kayan tea din, ke dakata kiji daga yau an daina shan tea a wannan gidan indai da kudina ne ban hanaki idan kinaso ki saya ba sai ki bata" mamakine ya kama ZAINAB bisa furucin RABI'U gareta, yi tayi kamar bazata tanka ba,daga kashe tace kana ganin hukunci da kaynake yayi dai2 kenan?" Amsawa yayi da cewar wannan kuma ruwanki nidai nagama duk abinda yake hannu ki bata taci ni ba shashabane da zan dinga asabar kudina akan wanna 'yar tsigigiyar yarinyar" shiru ZAINAB tayi ta fice ta bashi guri ta tafi ta nemawa MARIYA abinci da zata iya ci a keching mai sauki,"  ganin ta fita shima ya tashi yaje yayo alwala yayi sallah ya fice bai ko yi mata sallamar tafiya ba. Haka ta nemi dan abinda taga MARIYA zata iya ci ta dafa mata cikin irin kayan ganar da aka kawu musu,tun ZAINAB tana daukan halayen RABI'U da wasa,kamar zai sauya amman ina sam,ko abinci ta dafa ta kawo sai ya lankwasa chukalin domin ya lalace da wuri" inda RABI'U yaso arziki ya bata cefenan da zai ishesu Ita da  'yarta shi, idan yaso tsiya ya hana wanda zai isa, ZAINAB tasha kwanciya da yunwa ga tsohun ciki,amman RABI'U ko a jikinshi haka ZAINAB tayi ta fama da halinshi na yau da ban na gobe da ban'' har cikinta ya isa haihuwa. Tun yamma ZAINAB take jin ciwo mara yana karta mata amman haka ta daure tayi abinci dare tanayi tana hutawa, har ciwo yaci karfinta ta koma d'aki, daga ita sai k'aramar 'yarta haka ZAINAB ta haihu wajan sallah magariba ta sami santalelen d'anta namiji kyakykyawa dashi, babu kowa a kusa da ita haka taci murkusunta ta gama, ga ba waya a hannuta bare ta buga waya gidansu ta sanar da mahaifiyarta ta haihu, yunkurawa tayi da kyar ta sani bero da takkada tayi rubutu a ciki ta bawa MARIYA 'yarta duba da yake yarinya CE mai wayo tace tayi maza ta kaiwa makwafciyar ta" karba tayi tana murna ta fita da sauri duk da tafiyar yaro babu sauri amman kai da ganin yanayin tafiyar kasan itadin sauri takeyi" bata fi muti biyu da fita ba sai gashi sun shigo tare da makwafciyar tasu, ita kanta tayi mamakin juriyar da ZAINAB tayi har ta bari ta haihu ita kade ba tare da ta sakarwa kowa ba,sannu yayiwa ZAINAB hadi da jinjina mata bisa namiji kokarin da tayi na haihuwa ita kade!" Murmushi kawai ZAINAB tabita da shi domin batada ta cewa" k'ara lek'a jaririn tayi da cewa sannu ZAINAB kinsha aiki" amsawa ZAINAB tayi da yawwa ta sunkuyar da kanta k'asa" nan da nan makwafciyar ZAINAB ta cire hijab din ta kama aiki dora gawarwar wanka, bayan ta gama ta shigo ta fitar da duk kayan da ZAINAB ta bata da jini taje ta wanke sannan ta dawo ta goge d'akin tas ta samu gwaurashin wuta ta saka turen k'anshi, sanna ta yiwa baby boy din wanka, data gama ta cewa ZAINAB ta bayar da kaya asaka masa" nan fa ido ya raina fata domin tunda ta sami cikin ko wando RABI'U bai saya ba, bai kuma bata kudin da zata saya ba domin tanaji" mikiewa tayi ta dauko tun irin na MARIYA da ta rage ta bata haka tace asawa baby kamin yadawo ya sayo musu" kar6ar kayan kawai makwafciyar tata tayi ba tare da tace komai ba tasawa yaron ajiki ta kwantar dashi sanna ta mik'e ta koma keching ta juyewa ZAINAB nata ruwan wanka ta dawo ta sanar mata ta juye ruwan wankan" toh amsawa ZAINAB tayi da toh ta gode"  mikewa tsaye tayi da k'yar sanna tayi shirin  shiga wanka" inda tabar makwafciyar tata a d'akin tana k'arasa gyara inda ta tashi" bata jima a bayi ba tayo wankanta ta fito" ta gyara jikinta kamar ba ita ba,ganin haka yasan makwafciyar ta koma gida ta dauko kayan baby boy masu kyau sat biyu ta bawa ZAINAB" godiya ZAINAB ta k'ara yi dayatayi a sanna ta roketa aron wayarta idan akwai kudi a ciki zata kira gidansu ta sanar ta haihu"amsawa tayi da cewar akwai sanann ta mikowa ZAINAB wayar tata" ZAINAB ta sa hannu ta kar6a ta latsa lambar mahifiyar ta, bugu d'aya tayi aka daga kiran nata daga can bagaren Sallama ZAINAB tayi"mahaifiyarta ta amsa da cewar lfy dai ko?" Amsawa ZAINAB ta k'arayi da lfy qlu suka sannan ta sanarwa mahaifiyarta ta tasauka lfy" murnace ta kamata acan 6agaren hadi da mik'awa Allah godiyar ta a sarari' sannan ta tambayi lfy ZAINAB din da jariri"ZAINAB ta amsa da cewar lfy su lau" yanke wayar ZAINAB tayi ta k'ara latsa lambar mahaifiyar mijinta, itama ta dauka suka gaisa bayan gaisawa ZAINAB ta sanar mata ta haihu, murnace ta karad'e duk ka gidanje guda biyu kamin wani lkc gida ya ciki da yan uwa, basu bar gidan ba har bayan insha,magaifiyar RABI'U kuwa zama tayi da cewar sai zuwa safiya zata tafi ba zata iya barin ZAINAB ita kad'e a gidan ba,jin RABI'U shiru bai dawo ba har tsawan dare yasa mahaifiyarshi tambayar ZAINAB ina yaje ko yayi tafiya ne bai je ya sanar musu ba?" Murmushi ZAINAB tayi kamin ta bawa surukarta amsa,sanna tace ko kadan inaga aikine ya rik'eshi tunda kika ga haka" mata da miji sai Allah sam ZAINAB bata nunawa mahaifiyar RABI'U haka yakeyi ba gudun kar tajawa kanta wani sabon bala'in da yafi wanda take ciki a halin yanzu" sun dade suna hira kamin bacci ya kashe ZAINAB duba da yadda ta k'ago tayi baccin daman duk tagaji tunda akayi haihuwar bata kwanta ba. Barin surukarta ta tayi zaune inda ta kama bacci abinta,ita kuwa zama tayi domin ganin lkc da d'an nata zai dawo" ta kwashe tsawan mutuna a zaune bayan baccin ZAINAB har ta fara gyangyad'i ita kanta sannan taji motsin shigowar RABI'U ko sallama babu zubur tayi ta farka da cewar waye?" Jin muryar mahaifiyarshi ne yasa yaji wata irin fargaba kad'an sallama yayi a kofar d'akin da suke ciki, amsawa mahaifiyarta shi tayi" ya shiga ya durkusa har k'asa ya gaisheta,ta amsa fuskarta cike da annuri tace masa daga ina haka?" Sosa k'eya yayi kadan da cewar ina gareji  tun d'azu wallahi wata mota aka kawo min gyara gaf da zamu rashi daga aiki toh kuma mai ita zainyi sanmako da ita zuwa MAIDUGIRI shine na tsaya na sallameshi duba yadda motar ta wahalar damu,banda abokin harka ne ai da bazan tsaya nayi dare haka ba" murmushi mahaifiyarta shi tayi da cewar tunda ka sallameshi ai shikenan haba nayi mamakin ace tunda akayi haihuwar nan babu dadewa nazo gidan amman banga gelminka ko sau daya ba?" Nayi magana ZAINAB tace aikine ya rik'e ka kunyi waya  ita kamin na k'araso" sosa k'eya RABI'U yayi da yaji mahaifiyarshi tana gaya masa yadda sukayi da ZAINAB ya amsa dacewar eh wallahi"karbar maganar tashi tayi da k'ara nuna damuwar ta akan rashin shigowa tashi tayi da cewar"  dalilin da yasa na kasa bacci na zauna jiran shigowar ka kenan" tashi RABI'U yayi da rawar jiki kamar da gaske ya dauko jaririn da yake kwance a kusa da ZAINAB da take ta faman ware baccin gajiya" kallon yaron ya dinga yi yana shafa sumarshi" har wani lkc suka kai shida mahaifiyarshi suna shawarar yadda komai zai gudana bai mata musu ba ya amsa da cewar Allah ya kaimu zuwa safiyya duk za'ayi abinda kika lissafa" ta amsa da Amen itama" yayi mata sallama ya mike ya tafi shiga k'aramin da yake kusa da na ZAINAB ya kwanta. Ka shegari tun asabar fari ya baro k'aramin dakin da kwana ya dawo wanda ZAINAB take tare da mahifiyarshi suka gaisa da mahaifiyar shi cikin kulawa da girmamawa, fuskarshi cike da fara'a kamar bashi ba,ya k'arasa ihar bakin gadon da ZAINAB take zaune"ganin haka yasa mahaifiyar tashi fita daga d'akin tace zataje ta keching ta duba abincin karin da ta daura musu" amsawa ZAINAB tayi toh mama"shi kuwa zaunawa yayi a gefen gadon da ZAINAB take zaune shima hadi da mik'a mata hannu ya k'arbi jaririn da yake hannun ta" mik'a tayi ba tare da ta kalleshi ba,ya kar6a yayi masa huduba sanna ya cigaba da rikonshi a hannun tsawan mutuna bai bawa  ZAINAB yaron ba,sam batayi mamakin hakan daga RABI'U domin tafi kowa sanin waye shi din da zarar yaga idon mutane, makirine na k'arshe idan ana maganar karuwa a cikin maza toh RABI'U yana daga cikin kuruwai maza tabas baya ta6a barin wani bakon fuska ya fashinci irin zaman da yakeyi da ZAINAB,"  jin tayi masa shirune yasa shi tamabayarta da cewar ko taba buk'atar wani abu?"shiru ZAINAB tayi hadi da tamske masa fuska"yasan me ZAINAB take nufi dashi,tana son nunawa mahaifiyar shi akwai damuwa kenan" nunawa yayikamar baisan tanayi ba, ya fuske ya k'ara tamabayarta a karo na biyu" kamar bazata amsa ba, jin motsin dawawar mahifaryashi yasa ta saki fuska da cewar duk abinda ya samu,bata k'ara ce masa komai ba tayi shiru dashi" ya mike ya yayi wa mahaifiayashi bayanin sunan da ya yiwa yaron huduba dashi watau ANSA murmushi tayi da cewar haka Allah ya ciyar dashi kenan?" Amsawa RABI'U yayi da cewar eh ai tun jiya ban kwanta bacci ba sai da na kira wayar ABBA na shawarce shi, shine yace ya banmin za6in sunan da za'a saka.........



~MAENAT KABER KIRU~






*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*



                _not editing📵_


*🅾6⃣*



Wa yaro" d'adine ya k'ara kama mahaifiyarta shi dacewar toh Allah yaraya manashi bisa sunnah" amsawa  RABI'U yayi da amen, kamar gaske yana sunkuyar da kanshi k'asa kamar wani muminin gaske" duk abinda suke tattaunawa tsakanin mahaifiyar mijin nata da shi kanshi RABI'U ZAINAB taba jiyosu daga d'akin rana sauraron wani takaici ne yake ta cinta a inda take zaune ji take kamar ta fito ta zaiyanawa mahaifiyarta duk halin da suke ciki,can wani shashi na zuciyata ya kwa6eta da cewar karki zama silar rushewar farin cikin da mahaifiyarshi take ciki a halin yanxu,kuma kina ganin duk abinda kika sanar mata zatayi amanah da hakan?"ki rabu da harkar d'a da mahifi kawai."Wata  ajiyar zuciya ZAINAB ta sake wanda har sai da yakai kunneh mahifiyar mijina nata da shi kanshi RABI'U" atare suka shiga d'akin ZAINAB din da saurin su,hadi da tamabayrta ko lfy?" Amsawa ZAINAB tayi da cewar lfy lau" wani kallon tuhuma  RABI'U ya biya shi"  hakan ce tasa ZAINAB tsuke bakinta ba tare da ta kara cewa komai ba, rarrashinta surukarta ta ta shiga yi da cewar haba ZAINAB ki zuba wannan uban tagumi haka ga gajiyar zuciyar da kikayi wallahi sai da tasa hanyar cikina kad'awa,akan me zaki dami zuciyarki?" bayan Allah yasa kin haihu lfy,ai sai ji gode masa bisa ni'imar da yayi miki ,ko kinajin wani ciwo ne?" Sai a lkc ZAINAB ta girgiza kai alama babu wata damuwa,shi kuwa RABI'U tsayawa yayi ya kafeta da idanu hadi da yi mata muzurai duk a nashi tunanin yana yi mata barazana"shiruce ta ratsa tsakanin su tsawan mituna ganin haka yasa RABI'U sake budar baki shima yayiwa ZAINAB tambayar cewa idan kawai abinda yake damunki ki fad'a a kira likita ko muje asibiti" amsawa ZAINAB tayi da cewar babu abinda yake damuna" jin haka yasa RABI'U yiwa mafiyarshi magana ko da k'arin abinda suke so banda wanda ta lissafa masa a daren jiya domin fita zaiyi" amsawa tayi da cewar inaga shawarar da mukayi ai tayi" sai dai ko ka tambayi ZAINAB ko tana da wani abinda zaka sayo mata" juyawa yayi ya sake kallon ZAINAB da cewar kina buk'atar wani abune ne? Inason zanje nayo muku sayayya" zanwa ZAINAB tayi da cewar babu wani abu duk abinda ka sayo babu damuwa" toh kawai yace da cewar sai nadawo" ZAINAB ta amsa da Allah ya tsare"yace amen" mahaifiyarta shi ce ta k'ara jefa masa tamabaya da cewar tun yanxu zakafita bazaka jira ka karya ba?" Ya amsa da cewar eh inason zanje banki ne na ciri kudin bana son bin dogon layine ,sabida inason  shiga kasuwa da wuri,"toh kawai tace masa hadi da yi masa fatan dawowa lfy" amsawa yayi da cewar sai Allah yasa ya fita." Yana fita kai tsaye banki ya fara wucewa kamar yadda ya sanarwa da mahifiyarshi" bai wani dade akan layi ba duba da safiya mutane basu fara ciki bankin ba ya cire kudinshi masu yawa sanann ya tari dan adaidata sahu ya ka k'arasa dashi kasuwa" yayi siyayya kamar ba gobe har da abinda ba'a lissafi masa ba ma sai da ya sayo tun daga kan kayan baby har zuwa na MARIYA ita kwanta kala goma ya sai mata kama daga dogayen riguna zuwa masu dogon wando, ko wanne sat da takalmi, sanna ya juya kan na ZAINAB mai jego itama haka ya sai mata kaya har kala goma kama daga atamfofi zuwa les da shadda da material',har da takalma itama da jakarsu da mayafai" ita kanta mahaifiyar tashi bai barta haka ba sai da taci arzikin haihuwar da aka yiwa RABI'U kai abin ba'a magana domin drop din mota ya dauka ta kaishi har kofar gidanshi da wanna kayan haka ya rika daukar su d'aya bayan d'aya yana shiga dasu,sai da ya gama shigar dasu ya dawo ya sallama driver ya koma ciki" tunda mahaifiyashi ta ganshi niki2 da kaya ta dinga washe baki yak'i rufuwa kallon mamakin sayayyar da RABI'U yayi har da ita domin ko haihuwar ko haihuwar fari da akayi masa baiyi siyayyar da ta zarce hakan ba, nan fa ta shiga samasa albarka" yana amsawa kamar da gaske" ita kuwa ZAINAB tunda ya fara shiga da kayan batayi mamaki ba domin tasan halin RABI'U dan yaga idon duniya zaiyi sama da hakan bare yaga idon mahaifiyarshi,murmushi ZAINAB ta ringa saki mai kamar yak'e, domin kuwa idan zata shekara fad'an aibun mijinata ga mahaifiyarshi ba yadda zatayi ba." Yana fita kai tsaye banki ya fara wucewa kamar yadda ya sanarwa da mahifiyarshi" bai wani dade akan layi ba duba da safiya mutane basu fara ciki bankin ba ya cire kudinshi masu yawa sanann ya tari dan adaidata sahu ya ka k'arasa dashi kasuwa" yayi siyayya kamar ba gobe har da abinda ba'a lissafi masa ba ma sai da ya sayo tun daga kan kayan baby har zuwa na MARIYA ita kwanta kala goma ya sai mata kama daga dogayen riguna zuwa masu dogon wando, ko wanne sat da takalmi, sanna ya juya kan na ZAINAB mai jego itama haka ya sai mata kaya har kala goma kama daga atamfofi zuwa les da shadda da material',har da takalma itama da jakarsu da mayafai" ita kanta mahaifiyar tashi bai barta haka ba sai da taci arzikin haihuwar da aka yiwa RABI'U kai abin ba'a magana domin drop din mota ya dauka ta kaishi har kofar gidanshi da wanna kayan haka ya rika daukar su d'aya bayan d'aya yana shiga dasu,sai da ya gama shigar dasu ya dawo ya sallama driver ya koma ciki" tunda mahaifiyashi ta ganshi niki2 da kaya ta dinga washe baki yak'i rufuwa kallon mamakin sayayyar da RABI'U yayi har da ita domin ko haihuwar ko haihuwar fari da akayi masa baiyi siyayyar da ta zarce hakan ba, nan fa ta shiga samasa albarka" yana amsawa kamar da gaske" ita kuwa ZAINAB tunda ya fara shiga da kayan batayi mamaki ba domin tasan halin RABI'U dan yaga idon duniya zaiyi sama da hakan bare yaga idon mahaifiyarshi,murmushi ZAINAB ta ringa saki mai kamar yak'e, domin kuwa idan zata shekara fad'an aibun mijinata ga mahaifiyarshi ba yadda zatayi ba" Bare kuma wani wanda baiga san RABI'U da wata muguwar halaiyya ba' wannan ce take k'aryawa ZAINAB zuciya akan duk lkc da tayi yunkurin tunkarar iyayen mijin nata halin da take ciki da d'ansu."


Abu kamar wasa haka RABI'U ya dinga jifgowa ZAINAB kayan bukatun gida tun kamai ranar suna ta zagayo babu wani abu da bai ajjiye ba a gidan duk wani abinda yasan za'a nema sai da ya tanaza.Tun daga lkc da akeyiwa suna mahaifiyarshi bata bar gidan ba har sai da ZAINAB ta gama wankan jego a cewar ta gara ta bari kwarin jikin ZAINAB din ya dawo" ko kadan RABI'U da ZAINAB basu sake samun sa6ani ba haka ya dinga bawa ZAINAB kulawa ita da yaranta guda biyu watau MARIYA da ANSA dan jariri" sai dai tun bayan suna aka fashinci ANAS bashida koshin lfy" ko kadan RABI'U bai ta6a gajiyawa da sayan magunguba ,ko kai shi ganin likita."Duk wani hali da mahifiyarshi zata gani na banza ya dainasu kamar bashi ba,hatta kaiwa daren da yakeyi duk dainawa yayi" mahaifiyarshi tana  tafiya ya ciki gaba da gasawa ZAINAB gajiya a hannu" sauki da ZAINAB ta samu d'aya ne babu wani abu da zata nema dag RAB'U sai yarjewarshi zuwa kai ANAS asibiti" duk ranar da yaga dama ya barta ko kuma ya hanata" hatta yawo daren da yakeyi ya dawo da yin abinshi." Haka ZAINAB ta cigaba da hakuri da yanayin da RABI'U ya koma duk dan abinda yake hannuta haka ya tasama k'arewa dole ce ZAINAB sake shiga cikin wata damuwar" shi kuwa ko kadan baya kallon ZAINAB a matsayi mace tunda ta haihu gashi har ta tasama wata na uku da haihuwa, yanke shawara ZAINAB tasakeyi na tun karara mijinta ko dan ssauke nauyin da yake kanta nashi" tasa ZAINAB zaman jiranshi a wannan dare,koda ya dawo tayi masa sannu da dawowa"ya amsa a ciki kamar baisanta ba,ko kadan ZAINAB bata kiyeyeshi ba,sai da ta shigar da buk'atarta ta bashi hakkinshi" wata harara ya wurga mata da cewar Ashe ganin buzu a masallaci bazai sa tunkiya taji tsoran Allah ba?" Ke wai waje mara fashinta ce? Nace miki ina buk'atarki ne? Ko nace miki ina sha'awar kwantawa da ke ne?" Ni banza ne kenan da zan k'ara kusantarki"ai tun daga lkc da nace miki muje a cire cikin wannan yaron kika k'i naci alwashin daina kwanciya da ke" wasu zafafan hawaye ne suka ziyarci kumatun ZAINAB hadi da zafin rai dana zuciya"yi tayi kamar taci kwalar RABI'U tace ya saketa kawai ta huta,sai ta tunda da maganar mahaifinta na cewar ko da wasa taja sanadin da mijinta ya saketa ko bayan ya mutu bai yafe mata ba" wannan hujar ce tasa ZAINAB mik'ewa tsaye tsam ta har kusa da RABI'U  ta kuma yiwa kanta al'k'awarin ko zafin sha'awa zai zama shine ajalinta bazata k'ara zuwa gareshi ba itama" Ganin haka yasa RABI'U shima ya fita a rayuwar ta" duk abinda ya zama wajinbinshi ya daina bata sai yaga dama kama daga sabulun wanka da na wanki da dai duk wani kayan tsafta wanda ZAINAB zatayi amfani dashi ya daina bayarwa tunda yana ganinta dasu,kuma bai ta6a tambayarta waye wake kawo mata ba." Ko kadan ZAINAB bata gaban RABI'U abin har ya dain 6ata mata rai da zuciya'  fatan ta Allah ya dawo dashi kan hanya a kullum addu'ar ta kenan.


ZAINAB na cikin wanna gallazawar ta mijinta Allah ya saukar mata da maraicin rashin iyaye duk biyu dare daya,hakan ya farune sakakon annobar amai da guduwa da ta sami iyayen nata cikin daren da bazata ta6a mantawa dashi ba!!! ZAINAB tasha kuka ita da k'anneta da suka ragemata kamar basu daina ba". Haka dai sukayi ta kuka har suka hakura" bayan an k'are saman makokine dangin mahaifin ZAINAB da na mahiafiyar ta suka raba k'anneta a tsakaninsu,ranar ne ZAINAB ta k'ara tsikewa da labarin duniya!! Tun kamin kowa ya watse aka yanke shawarar zuba yan haya a gidan mahaifin ZAINAB din" kowa ya aminci tsakanin dangin duba da MALAM bashida d'a namiji babba duk mutuwa suka ringa yi,sai daga kan ZAINAB 'ya'yan nashi suka fara zama"gashi har sun koma ga Allah basu sake samun haihuwar namijin ba.

Haka dai aka yanke shawara,kowa ya amice ZAINAB tasha kuka mai isa gani za'a tafi da k'anne nata danginsu"ba iya ita ba hatta dayan sunyi kukan suma duk da ba wani wayo suka cikaba" haka dai suka rabo da juna kowa yana kuka. Ko kadan RABI'U bai tausaya ZAINAB ba bisa rashin iyaye da tayi haka ya cigaba da cisguna mata" dole tasa ZAINAB sake tunkararshi dan sanin matsayinta amman ko kallonta baiyi ba' wanna dalilin ne yasa ta shirya taje nufi gidan iyayenshi"ko da taje bata sami mahifinshi a gida ba ya fita, kunya da nauyi ya yabata zaiyanawa mahaifiyar mijinata komai, ta dai dan gaya mata wasu abubuwan da suke faruwa a tsakanin su" musamam janye hakkin kwanciyar aure a cewar ZAINAB tun kamin ta haihu rabinsu da juna" tafa hannu mahaifiyar RABI'U ta shiga yi da cewar haba ZAINAB na dauka wani gagarumin abune?" Ke ko kunya bakiji na kallona ki sanar dani laifinshi ba duk da irin kyautatawar da yake miki?" haka  zaki fara yawan kawo k'arashi daga muguwar iyayenki ko tausayi kanki bakya yi" toh ai sai kiyi hakuri ta wuyu ma tausayinki yake shi yasa ma ya kaurace miki badan wani abu ba,banda zamani ina ke ina iya fitowa kice baya kusantarki"wallahi mu adacan ko k'awace zaki iya sanar da ita wanna maganar ba,bare ni da nake a matsayin mahaifiyarshi,sunkuyar da kai ZAINAB tayi tana jin surukar tata tana ta faman motar maganar" hakance ta hana ZAINAB dadewa a gidan tunda ta fuskanci mahaifiyar mijjn nata bata son a fadi alaifin d'anta,ta baro mata gidan." Tunda ZAINAB ta baro gidan surukar tata,ko da wasa mahaifiyar RABI'U bata gayawa mahifinshi ba,bare yayi binke a matsayinshi na namiji" ganin babu sarki sai Allah yasa ZAINAB ta rungum k'addararta ta faulawa Allah" duk wani kaso dakesamu na  hayar gidan mahaifinta akan hidimarta da taranta ta ke k'arewa ko kadan ZAINAB bata k'ara gajiyawa da hakan ba tunda ya zame mata jiki duk da yawan rashin lfy da ANAS yakeyi" tana cikin wanna halin ne gwamnati ta bijiro da aikin titin da zai ratsa ta unguwarsu anyi ittifak'in gidajan da za'a ruguje cikin kuwa har da wanda mahifinsu ya bar musu gado" nan hankali ZAINAB ya kara tashi sosai, da taji wannan lbr." Bayan gwamnati ta rushe gidajan nasu ta raba musu diyya,idan aka raba musu ita da k'anneta"ita aka damk'a mata nata a hannuta,haka ta ringa d'ibar nata kudin da kadan_kadan tana yin hidmar yau da kullum saura ta k'ara a jarinta. Tunda  RABI'U ya ga ZAINAB ta kara samin wannan kudaden ya k'ara matse hannunanshi babu wani abun da ZAINAB zata gani na ciki ko n sha,ko na sha'awa  nata ko na yaransu" taiya tunkarshi da maganar ya sai musu' tsawan shekaru takwas kenan wannan ce ta k'ara kasaara ZAINAB din" duk lkc da tayi tunk'urin bijirewa wasiyar mahaifita sai ta kasa, ba wani abu take k'ara tunawa ba illa iyakar gamuwarta da mahillicnta uwa uba ga tausayin rayanta da taki a duk lkc da ta kalli idon yaran sai taji bazata iya barisu ba ita ma,wannan ce tasa ZAINAB daura dammara zama da RABI'U duk wuya duk rintsi. Tana cikin wannan haline Allah yasa RUKAIYYA kawata suka dawo gari ita da mijinta tunda duk su biyun ma'aikatane"cikin ikon Allahkusa dasu ma suka dawo run dag lkc RUKAIYYA ce take taimaka mata akan komai wanda baifi karfinta ba,hakan take k'ara bata shawarar duk rantse kar ta sake ta rabu da yaranta" tana kaiwa k'arshen tunanin ta tuni ta jike fuskarta da hawaye Sai a lkc ta lura da dawowa k'awartata tun tsawan lkc tana tsaye kanta...............




~AMENAT KABER KIRU~







*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*



*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*


*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 



*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*



*🅾7⃣*



Tsaiwar Hajiya RUKAIYYA bata hana ZAINAB cigaba da kukan da takeyi ba"  sunk'uyawa Hajiya RUKAIYYA tayi tatallafo kan ZAINAB da cewar haba kawata yaushe zaki daina wannan kukan naki?" Ya kama ace kin saba da halin da kike ciki duk da cewar manzo Allah sallalahu _alaihi_wasalam yace (babu wani bawa da jure cutar bayi yana ji, idan ba Allah ba.) Amman duk da haka inason karki manta da ubangiji mu,domin shine ya kaddara miki komai tun daga ranar da aka haifeki har zuwa ranar mutuwarki tsararrene a gurin Allah babu wani bawa da ya isa ya ketarewa k'addarasa" abibda nake so dake shine ki k'ara hakuri akan wanda kikeyi"cikin shashshek'ar kuka ta amsa da insha Allah zanbi duk shawarar da kika bani" Ganin ZAINAB ta d'an lafa da kukan da takeyi ne yasa RUKAIYYAN tace mata bari taje ta kaiwa Dr mugungunan da ta sayo wa ANAS a phamarcy ya duba"amsawa ZAINAB tayi da toh" wucewa RUKAIYYA tayi office din Dr" sallama tayi kaitsaye" Dr ya asma da sannan ya k'ara nuna mata gurin zama" RUKAIYYA ta zauna had'i mik'a masa  maganin da ta sayo" yasa hannu ya karba ya duba komai yabata amsa da cewar duk sunyi, ya k'ara da bata shawarar akan bawa ANAS kulawar da ta dace" amsawa RUKAIYYA tayi da toh mungode" tayi masa sallama ta fito" ta dawo inda ZAINAB take zaune da ANAS akan cinyarta da kanta ta sunkuya ta dauki ANAS din sannan ta kalli ZAINAB da cewar tashi mu tafi" toh kawai ZAINAB tace tana biye dasu a baya",har suka isa idan RUKAIYYA tayi parking din motarta ta,a hankali ta mikowa ZAINAB ANAS ba tare da tace mata komai ba" hannu  ZAINAB tasa ta karbeshi" sannan RUKAIYA ta bude musu motar ta koma nata 6angaren" ZAINAB ta shiga ta zauna tana cigaba da zubar da k'allah da ta cika mata idanu" itama RUKAIYYA bude gurin zaman driver tayi ta zauna kamar zata tayar da mota sai ta fasa ta waiwaya ta sake kallon ZAINAB da cewar k'awata ko baki dauki shawarata bane?" Da sauri ZAINAB ta d'ago runannun idanuwanta wadanda sukasha kuka, ta kalli RUKAIYAYA da cewar ko kadan wallahi ina dai tuna irin cutarwar da ake min ne" numfasawa RUKAIYYA tayi da cewar toh nagode amman dan Allah ki k'ara hakuri,sanna duk abinda zakiyi  ki kalli ubangijinki shine mai yayewa bawa duk wata damuwa" godiya ZAINAB tayiwa RUKAIYYA hadi da cewa zata cigaba da hakurin da takeyi" a sarari RUKAIYYA ta nuna jin dadinta bisa ka6ar shawararta da  take dauka koda yaushe." Sunyi tafiya mai nisa babu wanda yace wa kowa komai atsakanin su" sai daga baya ne ZAINAB tacewa RUKAIYYA ga wannan kudin da HAFSAT AL'AMEN ta bani ko zaki karbi wani abu daga ciki?" Murmushi RUKAIYYA ta sakarwa ZAINAB da cewa haba k'awata ko bansanki ba  ace yau na fara ganinki kika sanar dani halin da kike ciki ai na tausaya miki na bar miki kudinki bare kuma ina matsayin yar uwa a gareki domin kuwa bana kallonki a matsayi k'awa sam_sam, Allah yasamin soyyayarki da tausayinki a jinana,kinga kuwa idan na karbi wani abu daga hannuki banmiki  adalci ba,nifa duk abinda kika ga nayi miki daga Allah ne kawai domin nima ba iyawa ta bace". Godiya ZAINAB din ta k'ara yi mata" ta amsa da cewar ki godewa ubangiji mu baki daya" sannan ta ringa Jan ZAINAB da hira har sai da taga hankalin ZAINAB ya dawo jikinta" sanna ta shawarceta akan tayi amfani da kudin da HAFSAT ta bata wajan biyawa yaranta kudin Makaranta abinda yayi saura sai ta cigaba da amfani dasu" amsawa ZAINAB tayi da cewar kamar kin shiga zuciyata wallahi tunanin da nakeyi kenan" Ai insha Allah da zarar ANAS yaji sauki zasu koma karantarsu daga boko har islamiyya, domin bana jin dadin zaman su a gida ni kaina ai ilimi shine jigo komai" kullum sai nayiwa mahaifinsu magana akan yasan muhimmanci ilimin yarashin koda bai kula da sauran hakkoki ba,ta hanyar biyan kudin makaratarsu amman sai yayi min shiru ranar da yaso magana ne yake jefa min habaicin wai meye amfanin ka fashintar da yaran  da uwarsu bamai fashintar komai bace? Ai yasan suma haka zasu zama dan shi baiga amfani bawa mara fashintar ilimi, ilimi ba, ZAINAB ta k'are zancanta da k'afa" ko kadan RUKAIYYA batayi mamakin maganar ZAINAB domin kuwa agwagwarmayar ta ta gurin aiki tasha ganin maza masu irin halin mijin k'awartata, wannan ce tasa akullum take k'ara bawa ZAINAB shawara akan tayi hakuri da halin mijinta haka zalika take kokarin taimaka mata akan duk wani abun da taka ya dace tayi mata"ko kadan RUKAIYYA bata gajiyawa da gain akin ZAINAB din domin kuwa kallon yar uwa ta jini takewa mata kamar yadda ta sanar mata tun a baya, wannan dalilin ne yasa bata Shakkar bata duk wata kulawa daga ita har 'ya'yanta,"tasha hana idonta bacci domin tashi tayi sallolin dare hadi da rok'on Allah badan kowa ba sai dan ta yar uwarta rokon ubangiji yak'ara  tallafawa k'awarta ta hadi da nema mata mafita gurin ubangiji, aduk lkc da ZAINAB tazo da mtsalarta RUKAIYYA kan shiga matsanancin tashin hankali sabida tana ganin k" tana danne halin da take ciki domin gudun kar ta nuna mata damuwarta a sarari  fad'awa matsala." Haka suka tafi suna tattauna al'amuran rayuwa kamar yadda suka saba a kullum" hakaki RUKAIYYA ba k'aramin dad'i take ji ba idan ta tuna irin hallicin da mijinta yayi mata a rayuwa" shi yasa a ta tuna da hakan takewa k'ara yiwa Allah godiya domin ba duka maza ne suke da hali iri d'aya ba,wani yasan abinda ya kamata na wajibinshi ga ilyalanshi wani akasin haka shi yasa hausawa suka Allah d'aya gari banban. Haka suka isa har kofa gidan ZAINAB suna hira kamar yadda suka saba a tsakanin su"guri RUKAIYYA ta samu tayi parking da motarta sanna ta bude murfi ta fito ta zagayo inda ZAINAB take zaune da ANAS a rungume a hannuta,ta bude mata karfin nata 6angaren ta mik'a hannu ta kar6i shi " ZAINAB ita kuma ta dauko leda magungunan nashi suka shiga ciki tare" ba wani dadewa RUKAIYYA tayi a gidan ZAINAB ba tayi mata sallama hadi da k'ara bata shawarwarin da suka dace akan jikin ANSA din" amswa ZAINAB tayi hadim da k'ara yi mata godiya bisa kyuatata matan da keyi" juyawa RUKAIYYA tayi ta kalli ZAINAB din sanna ta sakar mata murmushi hadi da amsa mata dacewar daga safiyar gobe  aikinta zai juya morning ne kar taji shiru da zarar ta sami time zata iya zuwa duba su koda yaushe" asawa ZAINAB tayi da cewar kai haba babu damuwa"  har kofar  gida ZAINAB ta sake rako RUKAIYYA sai da taga tashin motarta sanan ta koma gida.

Tana komawa sake lek'awa dakinta tayi domin ganin ANAS ya farka daga baccin da yakeyi?"ko da ta duba sai taga ashe bacci yakeyi har wannan lkc hakane yasa ta fada keching da sauri ta wanke tunkuya ta daura sanwar fara shinkafa duba da babu komai a gidan sai ita kade" tana gamawa ta sake juyawa tayi waje ta shiga gidan makwafciyata Sallama ZAINAB tayi, mafkwaciyar tata da ke ta faman aiki a tsayar gida ta amsa hadi da tambayar ZAINAB sun kun dawo daman yaya ANAS din da jikin?" ZAINAB ta amsa da cewar eh yanxu muka dawo babu jimawa haba yaji sauki"  masha Allah makwafciyar ZAINAB ta amsa mata da shi hadi da cewar amman dai basu da sauki sosai ko?" Amsawa tasakeyi  da cewar da sauki ai dubashi sukayi sai magunguna da suka rubuta mana kuma mun saya tun a asibiti, shine ma karin jinkirin mu" itama amsawa tayi da cewar ai da naji shiru da har zan bugawa maigidana waya na gaya masa zan bi bayan ku,sai kuma na tuna ai babu waya a hannunki kema kuma bansan wanne asibiti kuka tafi ba" murmushi ZAINAB tayi da cewar karki damu tunda ba kwantar damu sukayi ba" duk maganar da sukayi MARIYA tana falon gidan tana ta kallon TV tunda duk yaran gidan sun tafi makaranta sun bayar ita kade, sai a sanna ne ta leko nacewa ZAINAB sannu da dawowa UMMA"amsawa ZAINAB tayi da cewar yawwa, sannan tace yawwa kizo gida yanxu zaki yomin cefene a bakin layi bayan ta gama gayawa MARIYA sakonta ta juya ga makwafciyar ta tayi mata godiya hadi da sallama ta koma gida" itama MARIYA komawa cikin falon ta dauko hijabinta ta bi bayan mahaifiyarta ta.Sallama  MARIYA tayi shigo  gidan nasu hadi da yiwa mahaifiyarta sannu  da gida tak'ra da tambayar jikin kanin nata?"   asmwa ZAINAB tayi da cewar yaji sauki, Sanna tayi mata umarni da tashiga d'aki ta dauko kudi ta aiketa" amsawa MARIYA tayi" ta wuce cikin hanzari ta dauko kudin tazo ta durkusa har k'asa ta mik'awa mahaifiyarta" ZAINAB tasa hannu ta kar6i kudin ta kirgo wasu daga ciki sanna ta lissafa mata duk abinda zata sayo musu na cefen miya ta mik'awa MARIYA kudin" hannu tasa ta karba ta fita da hanzari" tashi ZAINAB tayi ta cigaba da aikin da takeyi." Bayan fitar MARIYA baifi miti ashirin ba ta dawo ta kawo aikine da mahaifiyarta ta tayi mata" cikin hanzari suka hadu suka gama gyara komai tunda duk wani aikin gida tuni ZAINAB ta komawa yarta sai wanda baza'a rasa ba duk da k'aracin shekarunta" bayan komai ya kammala  ZAINAB ta shiga d'aki da kanta ta taso ANAS yaci abinci sannan ta bashi magungunanshi yasha ya ko wanne, sanna ta k'ara gyara komai. Shi kuwa RABI'U bai yana chan basan a wanne hali suke ba tunda ya fita tun safiyar da ya kwashe matawa ZAINAB yan kudadenta" shi yasa ko da tadowa da kudin hannuta ta gama zarar na cefenen da tayi musu guri mai nisa ta boye sauran domin gudun komawa gidan jiya,ta sani sarai mugunta irin tashi da baya son yaganta da ko naira biyar  a hannunta. 


Kamar kullum yauma sai da dare ya raba sannan ya shigo gidan a fusace gudun kar ZAINAB taga fuska ta tambayeni shi wani abu shi yasa ya shigo yana tsaki hadi da mak'osanai  tunda yanxu ta farga shine ya kwashe mata kudi da safe" ita kuwa ZAINAB tunda taga ya shigo yana malam zance ko kallonshi batayi ba bare ta tanka ta k'ara mayar da kanta ta kwanta kamar basan ya shigo gidan ba,bare dakinta" ganin haka yasa shi ya fara zage_zage da cewar ta rainashi tana ji ya dawo bazata kawo masa koda ruwa ba,bare tayi masa tayi abinci da zaici" k'ara gyara kwanciya ZAINAB tayi ta bawa banza ajiyarshi ganin bata da niyyar tashi yasa shi ya tafi keching da kanshi dan zubo abinci"yana zuwa ya bude tukunya yaga babu komai a ciki har an wanketa"  hakan ne  yasa shi ya daga tunkuyar ya maka da k'asa ya dawo d'akinya kama ZAINAB da masifa da bala'in wai ta rainashi" ita kuwa ko tari batayi masa ba bare yasan ta damu da abinda yakeyi" ganin haka yasa ya fara zazzaginta da cewar idonta ya fara budewar da har zata iya girka abinci ta hanashi" wata dariya ce da takaici suka zowa ZAINAB lkc guda,tama kasa jin 6acin rai bare ta tanka masa" ganin haka yasa RABI'U dagota daga kwance da take ya shek'a mata wani wawan mari hadi da tambayar ta wa kika mayar mahaukaci?............






*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*

*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*


*TSOKACI*

*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*


*~GODIYA TA MUSAMMAN GA:~*

*_DR KAMAL U. MAIKUDI_*

*_DR HUSSEN MOHMD YAK'IMA🤙_*



*🅾8⃣*



Dafe kuncinta tayi had'i da binshi da kallon mamakin da ya hanata furta komai bare tayi kuka bisa marin da yayi mata" komawa tayi da niyar sake kwanciyar sai ji tayi ya sake fezgota yana k'ara tambayar ta kamar yadda yayi a farko da was kika mayar mahaukaci?"shiru ZAINAB tayi hadin da sunkuwayar da kanta k'asa dugun kar ta d'ago ya k'ara mata wani marin" jin shirun tayi yawa ne yasa RABI'U kara matse mata  hannuta da gangan da ta furta wata kalma ya sami damar da zai jifgeta amman babu dama" fusukatar hakan ZAINAB itama daga gareshi shi yasa tayi shiru"bugu da k'ari dare ya shuda babu mai kawo mata dauki sai Allah shine babban dalilinta na kin tankam masa kamar kumar"  sai da taji zafin rokon tsaurin da yayi mata sannan ta fizge hannuta ta kwanta ba tare da tace masa komai ba" ganin haka yasa RABI'U ya k'ara zage dantse wajan zazzagin ZAINAB babu k'auk'autawa kamar wanda ya sha kwaya"  shiru tayi kamar mai bacci" tana jin shi har ya dan lafa da sage_zagen nashi ya sami guri ya zauna kamar mai gadi sam ya k'i kwanciya bare ZAINAB ta sami dama/dama" ganin bashida niyyar dainawa ne yasa ZAINAB ta mike jiki a sanyaye ta fita ta d'auro alwala duk da tsoran da take ji ta dawo dakin kenan zata tayar da kabarar sallah  sai jin wani irin ciwo tayi tunda tsakiyar kanta har zuwa tafin kafafuwanta duk sun  daure ga wani abu da yake mata zuge a gadon bayanta zuwa k'asan mararta banda rad'adin da takejin zuciyar ta tana yi mata"' salati ta fara a hankali ta sanna ta zauna akan daddumar da ta shinfida zata yi sallah takai wani tsawan lkc tana jin ciwan, bayan ya lafa mata ne ta mike a hankali ta tayar da sallah na filar da tayi niyya" ta dade tanayi tun tana iya lissafa iya raka'oin da tayi har ta daina"fatan ta ubangiji ya k'ara kawo mata dauki da kafita a koda yaushe,domin tasan babu wanda ya isa ya yaye mata damuwar da take ciki sai ubanginta mabuwayi gagara musali  tunda tasan yana sane da zamanta. Shi kuwa RABI'U ganin ZAINAB  ta kama salla ba tare da tace masa komai ba, gashi batayukukan marin da yi mata ba, kuma bata tanka masa ba shine abinda ya k'ara k'ular dashi ya dinga masifar ta mayar dashi shaidan kenan raba  daren wanna ranar yayi yanamasifa da aibatawa a gareta" ko kallonshi batayi ba ta mayar da kanta ta kwanta ba tare da ta kalli inda yake ba,hmmm ranar ZAINAB ta k'ara tsinkewa da lamarin RABI'U sosai"kuwa har ya kai hak'ark'arinshi makwancinshi ya sake tashi ya dawo kan ZAINAB ya k'ara ce mata yanzu kika fara ganin wulak'anci na,ai daman hausawa sunce babu mace mai wulak'antuwa gurin miji sai wacce ta yadda ta bude gindinta da haihuwa sanna ya dawo ya kwanta kamar shink'inkin kamar gawa" ZAINAB taso bashi amsar kalmarshi ta kashe sai ta fara domin tasan haka yakeso shi yasa ta fasa ta k'aleshi itama ta juya ta cigaba da juyayin halin da take ciki. Ka shegari ZAINAB bata fito da wuri ba tunda ta iddar da sallah asuba bacci ne ya dauke ta daga baya sai da rana tayi sosai sannan ta fito ta nemarwa yara abinda zasuci, sai da ta tabbatar yaran duk sun koshi sannan ta dauko maganin ANAS ta shi yasha ko wanne,sanna ta koma ta juye musu ruwan wanka su ta farayiwa ANSA da bai da lfy, sanna MARIYA taje tayi nata"ita kuma ta kama aikin gida ta kammala bayan tashi gama taje tashi yi nata wankan, sai da ta shirya ne ta sannarwa MARIYA ta zauna ita da k'anainta zataje ta dawo" ba dadewa zatayi ba"amsawa MARIYA tayi da toh" fita tayi ta barsu a gidan. Tana fita bata zame ko ina ba sai makarantar da yaran nata suke yi tana shiga ta tambayi office din shigaban makarantar aka nuna mata,sallama tayi" ya amsa sannan yayi mata umarnin ta shigo hadin da nuna mata gurin zama" shiga ZAIANB tayi ta zauan suka gaisa ya da shi sannan ta gabatar da kanta a matsayi mahifayar su MARIYA"shiru ya d'anyi kadan ya kalleta da cewar MARIYA RABI'U ko?" kai ZAIANB ta daga hadi da ce amsa eh ita" mamaki ne ya kamashi asarari yace ikon Allah ai  na dauka yaran marayune ko kuma basa tare da mahifiyarsu, duba da yadda yaran suke da hazak'a amman sam basa samun kulawar da ta dace tun daga uniform dinsu zuwa kayan karatunsu,duk babu wata kulawar kirki sai nake ganin kamar kin taka muhimmiyar rawa wajan tauye musu jin dadin karatunsu bai kamata yara masu hazak'a adinga watse da su ba" shiru ZAINAB ta d'anyi sanna tace hakane gaskiya amman ina iyar kokarin akansu a matsayina na mahaifiyarsu sai dai nak'ara, kuma insha Allah daga yanzu zan k'ara akan wanda nakeyi" shugaman makarantar yaji dadin alkawarin da ZAINAB tayi masa na bawa yaran kulawar da ta dace a sarari" godiya tayi masa itama" sannan tasa yayi mata lissafi kudin da ake binsu na Makaranta,ba tare da ya 6ata lkc ba ya janyo fayin yaran ya duba ya sanar mata da yawan kudin"  lissafo ZAINAB kudin tayi ta mik'a masa",  yasa hannun ya kar6a sanan ya rubuta mata rasit ya mik'a mata"ta karba tayi godiya" sannan ta sanar masa da cewar MARIYA ce  kade zata dawo a goben ba tare da k'aninta ba shi bashida lfy" amman da zarar ANAS din ya sami lfy shima zai dawo" amsawa shuban Makaranta yayi da cewar Allah kaimu ya kuma bashi lfy,ZAINAB ta amsa da amen. Sannan ta fito daga office din ta koma gida. Tana dawowa ta sanarwa da yaran inda taje" MARIYA ta kama tsalle hadi da murnar lbr baya musu kudin makaranta"ba ita k'ade ba hatta ANAS da yake kwance sai da yayi murnar lbr da mahifiyar tasu ta zo musu dashi, yayi fatan Allah yabashi lfy ya koma Makaranta" amsawa sukayi da Amen" wani sabon tausayi yaran ne ya k'ara kama ZAINAB domin tasan duk duniya basuda wanda yafita a gurin su"  wannan hujarce tasa take shanye  duk wani wulak'anci da cutarwar mahaifinsu domin tasan wata rana sai lbr,uwa uba basuda wata mafita daga ita har yaran wacce ta wuce suyi hakuri da halinsa har Allah ya ganar dashi. Haka dai ZAINAB taci gaba da bawa ANAS baya kulawa ta musamam da kudaden da k'awarta ta bata tunda ranar da suka gamu a hanyar kai ANAS asibiti" tayi hakan ne sakamakon bayanin da Dr yayi musu na yanayin ciwan da yakeyi". Tak'ara fita harkar RABI'U bata bi ta kanshi daga ita har yaran babu wanda yake shiga sha'aninshi" ganin haka yasa shima sai yaga dama yake kwana a gidan tun daga lkc." Babu abinda yafi damun ZAINAB face wani irin ciwo mara da rik'awar baya ga wani irin ciwo da take ji yana taso mata daga cikin (pravet part )nata watau farji ta" kasa daurewa ZAINAB tayi ta shirya bayan yara sun tafi Makaranta ta nufi gidan RYKAIYYA domin ta shaida mata irin yadda take ji a jikinta sai dai kash tana zuwa gidan ta tarar bata nan sai a lkc ta tuna tace mata zata shiga aikin safene awatan gabaki daya babu yadda ta iya haka tayi kwana ta nufi titi ta tare mai mashin din adaidaita sahu tanufi  clinic din da RUKAIYYA take aiki" a daddafe ta sakko daga mashin din ta mik'awa mai mashin kudin shi" ya kar6a"ya bata chanjinta" ta nufi office din RUKAIYYA take aiki tayi sallama"RUKAIYYA ta amsa sannan ta nunawa ZAINAB gurin zama" ZAINAB ta zauna fuska babu walwala ta kalli RUKAIYYA suka gaisa"kallo d'aya RUKAIYYA tayiwa ZAINAB tasan babu lfy a tare da ita, tasowa tayi daga kujerar da take zaune ta zagayo ta zauana a kujarar da ta take gefe ZAINAB ta k'arewa ZAINAB kallo da cewar yadai?" Cije leben ZAINAB tayi kamin ta bawa RUKAIYYA amsa da cewar k'awata banida lfy naje gida ki dubani bak'ya nan shine dalilin biyoki nan" sannu rukiyya tayi mata sanan ta tambayeta abinda yake damunta" bayani ZAINAB tayi mata da cewar tana jin ciwon mara da rikewar baya ga wani irin kai da kuma wani ciwo da take ji a farjinta" shiru RUKAIYYA ta dan yi kada'an da cewar na gane" amman ki tashi muje office din babban likita ya dubaki,ba wai bazan iya bane amman yana da kyau ayi miki bincike mai kyau tunda kin anbaci (pravet part) naki duba yadda kika fasalta ciwo,tunda abune da yake buk'atar duba na tsanaki" toh kawai ZAINAB tace ta mike a hankali" RUKAIYYA ta wuce gaba ZAINAB na biye da ita abaya" wucewa suka yi RUKIYYA ta kar6arwa ZAINAB kati sanna suka hanyar office din babba dr""daya daga cikin kujerun da suke gefe office RUKAIYYA ta nunawa ZAINAB tace ta zauna ta shiga ta nemi izinin ganin shi tukunna"amsawa ZAINAB tayi da toh ta zauna da k'yar sakamakon jin wani irin ruwa da ya fara zubowa daga cikin wandonta har ya fara sauka kan cinyoyinta amma sam bata gayawa RUKIYAYA ba gudun kar ta k'ara rikita ta kuma tunda sunzo inda za'a sami makarin abin" juyawa RUKAIYYA tayi ta karasa bakin kofar office din dr tayi sallama RUKAIYYA tayi hadi da kwankwasa kofar office din babban Dr" ya amsa da yes coming" RUKAIYYA ta bude ta shiga ta fara da gaishe shi"ya amsa da cewar ah Hajiya RUKAIYYA kece Kika bugu kofa kamar wata bak'uwa?" Murmushi tayi sannan ta masa da cewa nice sir" kallonta yayi ya da cewar lfy ko?"amsawa tayi da lfy sanna tace Dr sister ta ce bata da lfy shine na rakora domin ka dubata" murmushi yayi da cewar ai kema Dr ce mai hana ki dubata?" Murmushi tayi da cewar sir ai gaba da gabanta shine dalili?" Yaji dadin girmamashin da RUKAIYYA tayi ya amsa da cewar ko toh nagode jeki shigo min da ita" amsawa RUKAIYYA tayi da hakane mana Dr   amman bari naje na shigo da ita din" Dr ya amsa da okey" tana fita ta sami ZAINAB har ta sauka daga kan kujerar da ta barta ta durk'ushe kasa kamar mai nak'uda" da sauri ta k'arasa inda take ta dagota" hadi da cewa  sannu ZAINAB menene yayi zafi haka?" Sai da ta tallafota sanna taji danshin a jikin ZAINAB din" rikiwa tayi hadi da tambayarta menakeji haka a jiki jikin !!?" Amsawa ZAINAB tayi da k'yar hadi da cewar nima tunda kamin na zauna naji abin ya fara biyomin cinyoyi na tun ina zaune shine har zaman ya ga gara domin duk zubowar nan da yakeyi sai marata ta karta min da ciwo" sannu tayi kara yi kata sanna ta kamata suka shiga office din Dr" suna shiga ya nunawa RUKAIYYA gadon da yake cikin office din yace ta kwantar da ZAINAB akai" amsa tayi da toh" a hanzaarce ta karasa da ita inda gadon yake ta taimaka mata taho" ture tarin takardun da suke banshi yayi na marasa lfy da yake dubawa ya k'araso inda ZAINAB take kwance yace mata sannu" ZAINAB ta amsa da k'ayar" tambayarta ya fara da cewar menene abinda yake damunta?" amsawa ZAINAB tasakeyi da cewar ciwan mara da rik'awar ba hadi da ciwan kai mai tsanani ga wani irin ciwo da nake jin daga al'urata, yanzu kuma bayan shigo asibitin nan shine wani irin ruwa yake fitowa dag ciki" amsawa Dr tayi da cewar okay toh bari mu duba ko" juyo yayi ya kalli RUKAIYYA da cewar ta miko masa safar hannu a drower set din shi" ta amsa da OK ta tafi da sauri ta dauko ta bude kwalin ta ciro ta mi'ka masa" ya kar6a ya saka, sanna ya yi mata nuni da ta miko mishi sauran kayan aikin nashi" tasake komawa ta dauko masa su,ta ajje a gefe"itama ta koma kusa da kan ZAINAB ta tsaya tana kallon yadda Dr yake ta ta faman kokarin saka taimakawa k'awar tata" hannu shi guda daya wanda ya sakawa safar ya ware d'an yatsa daya ya zuwa a(pravet part) din watau farjin ZAINAB tana cije le6e yakai yatsa na biyu duk da ruwan da yake fitowa daga ciki da kyar ya zurashi ya shiga" wani k'aramin ihu ZAIANB ta saki sakamakon jin zafin da ta k'ara ji gun yanayi mata"hakuri ya Dr yabata da cewar sorry" kai kawai ZAINAB ta dan motsa tayi shiru domin kuwa ita kad'e tasan irin zafin da takeji domin ji take kamar k'ara mata zafin ciwan mara da takeyi da dr yake acikin jikin nata" sai da yagama duk wani bincike sanna ya ciro yan yatsunshi daga ciki,sanna ya dako kai ya kalli ZAINAB da cewar shekarki ki nawa rabonki da aure?" Mamakine ya kamata akan tambayar Dr me ya hada cutar ta da rashin aure"kamar yasan abinda take tunanin kenan"yes abinda nake nufi kenan cutar ki tana da alak'a da rashin aure" dururu da ido ZAINAB tayiwa lkita domin batasan masar da zata bashi ba"  yanjuyowa yayi ya kalli RUKIYYA ta cewar Hajiya tun wanne lkc ne yar uwar taki takai rabonta da namiji? Dan naga tana jin kunyar amsa min tamabayata?" Murmushi RUKIAYYA tayiwa Dr da cewar ai tana da aure" mamaki ne ya kamashi da cewar what?" Daga kai RUKAIYYA tayi da cewa Dr yes da gaske nake?" Asarari ya k'ara baiyana mamakinshi da cewar okey,babu damuwa binken da nayine a yanzu ya nuna kamar ta dade rabota da d'a namiji, duba irin ruwan da take fitarwa daga jikinta launshin ya nuna kamar na wacce ga rabo da namiji tsawan lkc, amman bari na k'arasa sauran sai nayi muku bayanin komai" toh kawai RUKAIYA tacewa Dr" ta cigaba da kallon yadda yake gudanar da aikinshi cikin kwarewa da ta sanin darajar ilimin kanshi, wannan ce k'ara bawa Dr wani matsayi na musama a idon sauran likitoci yan uwanshi" daukar abin gwaji yayi ya fara gwada (BP) ZAINAB sannan ya dawo ya bude idonta, ya bata umarni ta bude bakinta ya gani" ta bude" ya buda sannan yayi bata tambayar shekarunta na haihuwa" ZAINAB ta amsa da cewar sunkai 30 zuwa da d'aya" Dr ya amsa da okey"ya cigaba da yi mata tambayoyin yadda takejin yanayin nauyi jikinta" ZAINAB ta bashi amsa iyakar saninta" sai da ya gama yasaka d'agowa ya kalli RUKAIYAYY da cewar zanso ace kamin na baku masa da shawarrin da yadace wanda yar uwarki zata bi na fara tattaunawa da mijinta idan da hali"yana kai maganarshi ta k'arshe a tare ZAINAB da RUKIYYA sauka had'a ido da bakin ciwa baya gari matafiyi ne" da sauri dr ya d'ago ido da cewar amman nayi mamakin halin da take ciki koda yake matafiyin yana kaiwa shekara nawa ba yanan?" K'asa da kai kowacce tayi daga cikinsu daga ZAINAB din har RUKAIYYA" jin sunyi shiru ne yasa Dr shima yayi ya koma ya kan kujerarshi ya zauna sanna ya janyo katin ZAINAB yayi rubuce_rubece da zaiyi akai" sanna ya sake cewa RUKAIYYA ta taimakawa ZAINAB ta sako daga kan gadon ta dawo kujerar da masa lfy suke zama yayi musu bayanin komai a tak'aice hadi da bata shawarwarin da suka dace"toh RUKAIYYA tace wa dr" ta kamo ZAINAB a hankali suka k'arso har kujerar da take fuskantar tashi" Ya gyara zama yayi sosai ya kallosu su duka biyun sanna ya fara da cewar kunji ina Alak'anta ciwon da maganar aurataiya ko?"suka daga kai da almar eh?"ya cigaba da cewar ba abin mamaki bane idan na fadi haka domin kuwa bincike ne ya nunamin haka?" Domin nayi iyakar bincike na bata da( high BP)da ta ambaci ciwan kai mai tsanani,kazalika kuma binken ya nuna batada cutar (ucler)da ta ambaci rikewar baya d.s.......shine as abinda yasa na k'ara matsa mata da tambayoyi hadi da k'ara bincikar shekarunta na haihuwa da tambayar matsayi aure, nasan ke RUKAIYYA ba abun mamaki bane a tare da ke ammn ita dole zatayi" RUKAIYYA ta amsa da cewar hakane Dr" mumushi yayi da cewar insha Allah komai yazo da sauki tunda har an gano meye matsalar" amsawa sukayi su duka da masha Allah a tare"bayani ya fara kamar haka da cewar ita mace wata hallitace wacce Allah ya sirrita ta kamar haka,idan mace takai mamakin balaga tana da wasu(humous)a jikinta watau jiyiwon sex,mana'a jijiyon shawarta ga da namiji basa budewa sai ranar da ta fara sanin namiji a rayuwatar wanda da zarar tasan shi ne cikar matantakarta,kuma shine take sabawa da shi, a duk lkc da suka matse junansu basa buk'atar komai sai sex watau jima'i da zarar sun samu toh mace zata zauna lfy ba tare da sun takura mata da ciwo ba,idan basu samuba shine,mace zata ringa jin zafin sha'awa na firgata, har ta kaita da cin ciwon mara da rikewar baya hadin da ciwon kai mai tsakani wani, sometimes yakan haifar da sarkewar tunani ga macan da ta dade bata samu sex ba,watau saduwa da namiji a hausancen"duk bayanin da Dr yake ZAINAB da RUKAIYYA suna jinshi." Numfasawa yayi kadan da cewar wannan itace matsalarki a ta farko"matsakarki ta biyu watau zubar ruwan da kikeyi daga (pravet part)naki shima matsalace a likitance domin hakan ya faru ne sakamakon wancan bayanin da bayi miki ba farko,duk da kince gurin yana miki zafi amman na duba naka kina da lfy shi ciki da waje, domin kuwa lafiyyayyan farji yana farawa daga kamar yanayin haka...

 Kaminshi na mumsaman kamar haka(internal&external) a hausance shine kamar cikinsa da wajensa, yana da wasu tudai guda biyu daga waje(labio majerer& labio menorer) dunbarun gefe da gefe na sama kenan a hausnce,toh aduk lkc da farji yake lfy shine zagaka (labio majorer)yana da girma da gutu sosai, idan ya kassnce  farjin mace bashida lfy kuwa na wani abu kamar infection kenan, to zakiga(labio menorer) dinta yafi (labio majorer) din ta girma, a hausance ce, shine dun barun cikin farjinta k'aramin ya kumburo yayo waje ya bubude shi na sama kuma sai k'ankance ba tare da ta barga ba,shine har yakai kai ga ya kasa rike (Peri's) na namiji watau kan azzakari ko nace yankan hashafa ta d'an namiji. Shine zakiga namiji sam baya jin dadin (sex )watau saduwa da matar da take a wannan yanayin, sai dai kawai yayi kawai badan yana jin dadinta ba yana da kyau duk mace ta gane wannan koda tana jinta da lfy a jikinta" wani dogon nunfashi ZAINAB da RUKAIYYA suka k'ara saki a tare sannan dr ya k'ara juyawa ya kallesu shima yace sai maganar tambayata ta gaba shine maganar shekaru da nayi ko?"a tare suka k'ara daga masa kai kamar kurami domin bayanin nashi ya shigesu sosai barin ma ZAINAB da ba hurunmita ba gara RUKAIYYA ita daman ma'aikaciyar lfy ce.

K'ara musu bayani yayi da cewar babu shekaru masu h'adarin gaske ga mace da suka wuce guda biyu a matakinta na rayuwa, shekara ta farko ita 17years idan mace tana wannan mamakin tafi buk'atar najimi fiye da tunanin mai tunani,dalili kuwa shine a wannan ga6ar zata iya daukan samari majiya k'arfi kamar hudu zuwa biyar ba tare da taji wani rauni a farjita ko wata jinya ba,yana da kyau duk wata mace tasan wannan, sai shekaru na gaba sune suke farawa daga 30years zuwa da biyar,anan ne masen da tasan namiji itama sha'awarta take nukunwa zuwa rukun bukatarta ta itama zata iya daukan maza majiya k'arkfi da lfy kamar guda biyu zuwa uku,ya kalli ZAINAB  da cewar lake you,kinga kema kina cikin rukuni na biyu kenan"sunkuwar da kai ZAINAB tayi kamar bataji mai Dr yace ba" ta fara tunanin magana shi fa gaskiya ce domin ita ma taji wani sauyi a tare da ita a kwanakin nan,amman sai take ganin kamar shaidan ne yake son rikita lissafinta" maganar Dr ce ta katse mata tunani da cewar yana dakyau kowa wacce mace ta binciki kanta,kuma tayi kokarin kusantar da kanta ga mijita idan suna tare, domin ko mu a kimiyyance bamason mace da takai wannan shekarun ta wuce sati namiji bai motsa mata sha'awarta ba, domin kuwa idan yayi tsamari takan iya samun damuwa ta turuwar (spom) watau maniyya,dan ma Allah tayi ku da wata baiwa ta musamman tunda tana yin jinin al'ada,tana nan duk wani maniyyi mara amfani yake fita daga jikinta,da namiji ne ya tsinci kanshi a irin wannan yanayin zai iya rasa rayuwarshi lkc guda,  shi yasa da zarar mace tazo min da irin wannan matsalar nake fara tama bayar ta mijinta domin yafuskanci matsalar da matarshi take ciki, wannan shine dalilin tambayata ina mai gidan ki amman yana da kyau ki nemishi ku tattauna idan kin koma gida, domin cimma matsalar lfy yarki" toh kawai ZAINAB tace domin batada abin da ya wuce hakan" sai bincike bakin da nayi miki shima  duk yana daga cikin matsalon mata matan da suke da damuwa a farjinsu kamar yadda na sanar muku dunga farko,macen da take da lfy wata tun daga bakinta ana iya ganeshi dalili kuwa zakiga wata bakin ya d'ade ya sauya kala kamar bashi ba  zai dinga fitar da wani launin wari mara dad'in ji haka nana, toh yana iya komawa har cikin farjinta shima ya koma yana bayar da wannan launin warin ko nace bashi kamar karin nama d'anye alamu cututukan farji sun shigeta kenan, domin macen da farjita yake lfy zakiganshi yana fitar da wani irin kamshi wadda maishi ba lallale ne ta fuskanci kana ba,daman Allah yayi shine domin da namiji idan yakai hanci ko baki cikin farji,ko shigarta domin yin( sex) watau saduwa sometimes wasu matan sukan gane hakan da kansu suma din' har takai idan sunji wannan nau'in k'amshin ya chanza kiga sun dauki matakin ganin likita da sauri. K'ara dawowa yayi ya kalli ZAINAB da cewar bari na k'asa yi miki bayanin a hanzarce kinga marasa lfy suna jirana tsawan lkc" toh kawai ZAINAB tace ta k'arayin k'asa da kanta tasa sauraroshi" yace a gaskiya babu wani gani a likitance da magance miki matsalarki gaba dayanta a halin yanxu duba yadda abin sha'awa take kama mutum lkc guda bata tare da tayi shara da shiba kuma batada lizami sai dai na rubuta miki magagungunan da zasu rage miki jin zafin ciwan da ta haifar miki dashu abu na gaba kuma shine ki nemi mijinki ku tattauna akan yadda zai tafiyar miki da ita ba tare da da d'anku ya cutu ba,wannan shine gaskiyar lamari ya mik'a mata katin ta sanna ya ce Allah yabaki lfy" tare suka amsa da amen ita da RUKAIYYA ta take gefe wacce tuni ta narke da acikin karfin imani da k'ara mik'a wuya ga Allah tsarkakken sarki"  godiya sukayu Dr sosai bisa bayanin da yayi musu, RUKIAYYA ce ta fara mikewa sai ZAINAB da tade da daskarewa a zaune tunda Dr ya fara bayani,sallama sukayi masa sanna suka fito daga office.(ni kuwa nace saddak'ar rasulul Karim,domin kuwa manzo Allah yayi gaskiya da yace idan zafin sha'awa ya takura dayan ku toh yayi aure, idan bai samu damaba ya yayawita yin azumin shima warakace.) Bayan sun fito kai tsaye office din RUKAIYYA suka nufa,suka zauna babu wanda yawa dan uwansa komai domin kuwa kowa da abinda yake tunani a zuciyar shi,ita ZAINAB tana tunanin yadda zata fuskanci mijina da maganar saduwa domin kuwa tun tana da cikin ANAS yabonta dashi kimanin shekaru takwas kenan har da watanni,ita kuwa RUKAIYYA tana neman shawarar da zata baya ZAINAB din akan yadda zata shawu kan RABI'U ya dawo su daidai ta asamin masalaha..............



~AMENAT KABER KIRU~





*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*

*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*


*_JINJINAR BAN GIRMA GA:_*

*_HAUWA S.ZARIA,MARYAM OBAM,UMMU FATEE,_*


*TSOKACI*


*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*



*🅾9⃣*


Shiru ce ta cigaba da gudana atsakanin su tsawan lkc" sai can daga bisani RUKAIYYA ta dada gyara da cewar k'awata mubar komai a matsayin k'adda daga Allah"ina fatan duk kin gamsu da bayanin da Dr yayi miki ko?" ZAINAB ta gyad'a kai alamar eh" RUKAIYYA ta cigaba da cewar toh shawara ta farko shine karki manta da Allah a duk wani lamari da zaki shiga,haka zalika ki tuna da fadin Allah ta'ala da cewar ba iyakar yin imani ne yake hana a jarraci bawa ba,jarrabar ubangiji hakika zata riski ko wacce rai mai numfashi" dan haka ki k'ara sawa ranki duk abinda kike ciki jarafta ce daga Allah,shawara ta gaba ki dage da addu'oi da kaiwa Allah kukanki, kar ki gajiya akan hakan dominshi mabuwayine akan komai,kuma mai jin k'an bayine a ko wanne hali" dan haka nake k'ara tunasassheki girmanshi a kodayaushe nake kuma nuna miki yin hakuri bisa kaddara wata nasarace a rayuwa ga bawan da Allah yanufa da al'kairinsa, magana ta gaba kuma shine ki dage dantse  wajan ganin kin cito mijinki daga fad'awa hallaka mara iyaka,ta wajan ganin kin zama sanadiyar shiryuwarshi ya dawo kan hanya mai kyau, ki k'ara  juriya bisa duk wani abu da zakiyi karo dashi wajan ganin gyaruwartashi"ta haka sai kiga kinsami sassauci daga Allah ko dan kema ki ku6uta daga sharrin fadawa hanyar da Allah bayaso bayinsa mumainai subi" tana kaiwa dai2 nan ZAINAB tace mata ban tari numfashi kiba kawata wallahi duk abinda kaki zaiyana gaskiya ce amman karki min rashin fashinta akan rashin kusatar da kaina zuwa ga maigidana ko kadan ban ta6a kwana a raina da cewar bazan biya masa buk'atar zuciyarshi akodayaushe ina kokarin bashi hakkinsa na aure, shine yaga baya buk'atar hakan daga gareni ya share tsawan lkc"amman nasha kai kaina gare  ko kallon arziki bayayi min bare har ya saurareni koda da hirar bakisance bare kwanciyar aure hmmm!!  Ya' ilahi yaya kikeso nayi dashi?gani nayi shi kanshi da yake namiji bai damu da yabiya buk'atar kanshi ba bare ni mace tun tsawan shekara takwas kenan da watanni a haka muke nida shi ko kadan hakan bai dameshi ba wannan itace hujjar wallahi, nasha zuwa da shirin karbar hakkina ni a karan kaian amman baya samuwa sai dai wani lkc ma na karbi hakkin duka daga gareshi ko nacin zarafi kinga kuwa ta ina zan takura mishi? toh yanzu sai nake ganin tunda har Allah yasa Dr ya rubuta min maganin da zansha dan rage rad'adin yanayin da nake ciki mai zai hana mubarshi har zuwa lkc da Allah zai dawo dashi kan hanya kawai inaga hakan zaifi kawata" d'aga mata hunnu RUKAIYYA tayi ta dakartar da ita da cewar wai meyasa wani lkc bakida fashinta ne?"sam bazai yuwu ba ina a kina nufin kin hakura kenan da shi har abadan?" A'a ZAINAB tace ko kadan ba haka nake nufi ba sanin halinshi ne yasa nace mu jira" hmmm RUKAIYYA tace da cewar kamar kice da lokaci" amsawa ZAINAB tayi da cewar lkc na Allah ne amman yana da kyau ki hango min matsalar da zan shiga idan na ce zan tunkareshi da maganar nan san RABI'U ba mutum ne kamar kowa ba" amsawa RUKAIYYA tayi da cewar hakane, amman ai gabanki Dr yace yana da kyau koda mijinki ba mazauni bane ki nemi masalaharshi ki ta yadda zaidawo inda kike ko? Ko ke kije gareshi meyasa wani lkc kike kasa fashintar matsalar da ke ake hange miki? badan komai yasa haka sai dan samun lafiyarki shiyasa akace keje gareshi kodan farin cikin ya dawo da na yaranki ya zama dole ki daura damar ganar da mijinki, uwa uba ga halin da kike ciki a halin yanzu domin shawa'awa batada linzami" zaro idon ZAINAB tayi da cewar ta yaya!? Murmushi RUKAIYYA tayi da cewar kwantar da hankalin ki Hajiyata bawai zuwa zakiyi ki tareshi gaba da gaba ki gaya masaba A'a ta hanyar hikima da basira zaki shige shi,shi da kanshi zai sakkko ya gyara tare da ya fusata ba,koda bai dawo 100% ba ai ansamu sasauci duk da nasan halinshi da kafiya da taurin kai amman ai baiyi i fir'auna ba, kuma ki dage da rokon Allah kina binshi da addu'a kamar yadda dai da na gaya miki safe da maraice" numfashi ZAINAB ta sake saki da cewar toh banki ta taki ba zan jaraba nagani domin hausawa sunce mai d'aki shi yasan inda yake masa yoyo!! Amman bana jin RABI'U zai fuskance ni bare matsalata" katseta RUKAIYYA tayi da cewar ai kinji ki toh bari kiji ko ubangiji zaka rok'a da yak'ini ake rokarshi ki tabtarwa kanki Allah dai shine Allah shine maji6anci lamuran bayi kuma ki tabbatar yana sauraronki zaiji ya amsa miki rokonki"bare dan Adam mutum?har ki dinga cin alwashin bazaiyi kaza ba, ki nufaci Allah da abin sai ya jiyarmiki kuma ya isarmiki ya tafiyar da lamarin cikin sauki,fatana shine kiyi duk mai yiwuwa ki daidaita da mai gidanki domin kuwa duk duniya babu wanda yafishi kusanci dake a yanzu shine rayuwarki, Toh kawai ZAINAB ta k'ara cewa RUKAIYYA"domin kuwa ita tafi kowa sanin halin RABI'U" domin kuwa tasan ba lallene tami kallon arziki da gareshi ba,sai bare har takaishi ya kusance ta"wannan shine gaba kura baya shayak'i  sharad'in  tayi kaico da sharadin da MALAM ya  gindaya mata tun yanada raye,har yanzu gargad'inshi gareta yana nan ya na aiki a kwakwalwarta a kullum kwanan duniya da cewar duk rintsi kar ta yadda ta nemi wani sanadin saki daga mijinta" ta k'ara na damar biyewa za6in zuciyata,domin sai da MALAM ya gargad'e da cewar kada wata matsala ta biyu baya ta tuna tana dasu,yau ga karshen kunne k'ashi ya kata,wannan hujjarce tasa MALAM din taka mata burki tun farko" tabiyewa kyawun fuska ta fad'a tarkon namiji"uwa uba ga matsala na tunkarota."numafshi ta sakeyi ta kalli RUKAIYYA da cewar babu damuwa insha Allah zanbi duk wata shawara da kika bani, amman wallahi banda sharadin da MALAM ya kafamin tun kamin rasuwarshi da tuni na rabu da mijina,sai dai kash kaddara ta riga fata!ta kare maganarta tana mai zubar da kwallah" da sauri RUKAIYYA ta ce haba kawata kar kice haka mana ai yiwa iyaye biyayya akan wasiyarsu bayan sun mutu wajibi ce ga mai neman haske rayuwa, ki dai yadda da k'addarar amman kar kiji haushin MALAM domin su iyayye suna da wani girma na musamman wanda Allah yace mu basu kuma mu girmama maganar su kada  ganin k'asa ta lilli6e idansu yasa ki kasa cika wasiyyar da ya bar miki haka zalika kada hakan yasa ki k'iyi musu adda'ar Allah yaji kansu"shiru ZAINAB tayi kamar bazata tanka ba daga k'arshi ta nisa da cewar hakane nagode da tunasarwarki gareni" amsawa RUKAIYYA tayi da babu komai k'awata." Mikewa ZAINAB tayi a hankali kamar mai tsohu ciki ta dafa bango ta kalli RUKAIYYA d cewar ni zan tafi gida na barki kiyi aikin ki" amsawa RUKAIYYA tayi da cewar ai aikin nawa mai saukine yau din sai dai d'an abinda baza'a rasaba, muje nayi miki rakiya zuwa get kawai da ace ma na had'a aikine sai muje na ajjeki a gida ni kuma na k'asara gida daga can" murmushi ZAINAB tayi da cewar a'a kar ki damu wallahi ai nasan aikine zai hana mu tafi tare ke amman babu komai zan lalla6a haka" RUKAIYA ta amsa da toh muje"a tare suka fito daga office din har zuwa get din asibitin ta tare ma ZAINAB mai adaidaita sahu ZAINAB ta shiga sannan RUKAIYYA ta k'ara jaddada mata ta sayi maganin da aka rubuta mata ta sha",toh tace mata da zarar ta koma gida zata je chemis ta sayo"daga mata hannu RUKAIYYA tayi da cewar gobe kamin ta fito aiki zata zo gidan ta ji yadda sukayi da gogan nata" toh sai kinzo ZAINAB tace mata" mai mashin yaja suka tafi,ita kuma RUKAIYYA ta ko ma cikin clinic.

 Fad'awa tunaniZAINAB tayi da ta ina zata fitowa RABI'U  akan buk'atar ta? domin kuwa tasan halin kayanta tas sai dai ta bawa wani lbr amman bawani yabata, duk wata hanya tabi tun acan baya ba ma bataci galaba ba bare yanzu da take ganin yayi nisa baya jin kira" haka taita kulle2 yadda zatayi amman sai ta kulla sai ta kwance a haka har mai mashin din adaidadita shu ya kawota unguwarsu bata sani ba,sai da taji yace mata Hajiya a ina zaki sauka?" Shine abinda ya dawo Ita daga duniyar tunanin da ta tafi" amsa masa tayi da sauki nan ma yayi" ya tsaya ya sauketa ta mika masa kudinshi yasa hannu ya kar6a"ta dauki hanyar da zata kaita gida.

Tun kamin ta k'arasa  kofar gidanta ta hango k a bude,gabanta ne ya hau dukan uku2!!da kyar ta k'ara domin tasan yara basu isa dawowa daga Makaranta ba,asanyaye ta shiga tayi gidan tayi sallama"RABI'U  ta tarar a tsakar gidan amman yana jinta bai amsa mata  sallama ta ta ba, yana tsakar gidan a zaune ya kafa kujera yana jiran yaga ta ina zata bullo"kallo d'aya tayi masa a sace tayi k'asa da kanta domim tasan babu mutunci a yanayin da ta ganshi" kamin ZAINAB ta k'ara daga k'afarta daga inda tayi sallamar sai ji tayi ya daka mata wata uwar tsawa hadi da tambayarta daga ina take!!? Yi ZAINAB tayi kamar ta nutse a inda take don tsoro! Da kyar tayi karfin halin amsawa da cewar daga asibiti nake!! kaga ma katin da suka rubuto na magani"ta nuna masa duk dan gudun kar yaci mata mutunci"amsawa yayi da toh uban wa kika tambaya kika fita?" Ashe bata tsira ba" "Amsawa ZAINAB tayi da cewar babu kowa amman kayi hakuri ji nayi ciwon yana niyar cin k'arfi na shine dalili da yasa ban jira sai ka dawoba amman baza'a k'ara ba" sake daka mata tsawa yayi da cewar dama haka kike fita gantali da zarar bana nan kenan?" Girgiza kai ZAINBA tayida da lamar cewa a'a" toh bari kiji daga yau duk lkc da na dawo na tarar bakya gida wallahi sai jikinki ya gaya miki" shiru ZAINAB tayi ba tare da ta k'ara cewa komai ba" ta godewa Allah a zuciyarta tunda a iya masifa ya tsaya ba tare da ya ta6a lfy jikinta ba ta wuce ta barshi a inda yake zaune ta shiga daki domin zage kayan jikinta,batafi muti biyu da shiga ba ta fito da kayan da ta cire tazo ta wuceshi a inda ta barshi zaune tun dazu ta zubu ruwa ta wanke kayan tas duk yana zaune yana kallonta ba tare da ya k'ara ce mata komai ba har ta gama ta koma d'aki ta kwanta da tunanin ta ina zata bullowa RABI'U." Tana kwance tana wannan tunanin sai ji tayi RABI'U yana k'ara kwad'a mata kira" a gigice ta amsa ta fito da sauri ta k'arasa inda yake ta ce gani" wani banzan kallo ya sakar mata da cewar ashe ke har yanzu bakisan ciwan kanki ba?ai tunda kika ganni na dawo yanzu da rana ai ina da dalilin dawowa ta ko?kin dawo kin sameni a gida amman ko ruwa baki baniba bare abinci sai kika cigaba abinda yake gabanki kawai" amsawa ZAINAB tayi da cewar kayi hakuri na shafa'a ne ban baka ruwan ba, abinci kuwa babu domin komai ya k'are na dangane da kayan abinci bangirka ba" kwafa yayi da cewar ubanwa kika gayawa bakida kayan abinci?"shiru ZAINAB tayi dashi domin tasan duk hanyar da zai jifgeta yake nema,kuma ina ta ganshi a gidan bare ta gaya masa wata matsala? mutumin da kwanan shi biyu baya gida sai yau ya, dawo shine zaiyi masifar ba'a bashi komai ba a can k'asan zuciyarta take wannan maganar" shiru tayi tana jinshi yana ta faman masifa amman tayi masa banza"  tashi yayi ya fita daga gidan" sai a lkc ta mike da daga inda ta tsuguna"baifi miti uku da fita ba ya dawo hannu rik'e da leda ya shiga yana kiranta cikin isa da tak'ama" amsawa tayi ta fito da cewar gani" miko mata ledar yayi da cewar gashi nan Saura ki wulak'anta min kayan abinci" karba  kawai ZAINAB tayi ta shige d'aki da ledar da ta karba a hannun shi ba tare da tace komai ba"sai da ta shiga ta bude ledar ta duba ta ga abida yake ciki,ba wani abu bane illa tsurar shinkafa ko magi babu bare k'arin wani abu akai amman har yake zafga takarar kar ta lalata masa"ko da yake ta godewa Allah domin ya dade bai ma zayo mata shinkafar ba ko a chokali bare har yayi takarar sai yau. Fasa kwanciyar da tayi niyya tayi ta fito ta shiga kitchen ta hada wuta duba da yadda lkc dawowar yara daga Makaranta yana k'aratowa,shine dalilin da yasa ta tsiri aiki cikin sauri babu k'auk'autawa kamin wani lkc ta gama dafa farar shinkafa da RABI'U kawo duk da rikewar da mararta ta takeyi amman haka ta dage ta dafa abincin" inda ZAINAB ta godewa Allah shine tana da soyayyen manja da dakkaken yaji shine dalilin da yasa tana  gamawa ta zubawa RABI'U nashi abinci takai masa"ta ajje masa ta debu ruwa ta ajje masa sanna ta koma ta cigaba da aikin da ya rage mata a tsayar gida tanayi tana cijewa" duk RABIU yana kallonta yana dariyar k'eta a zuciyarshi yana cewar kadan ma nayi miki yarinya keki ga zaki iya shanye duk wani wuk'anci na." Sallama su MARIYA ta jiyo ta amsa" yaran suka shigo sukayi mata sannu da gida" ta amsa ta saki aikin da takeyi ta mek'e daga inda take aikin ta shiga kitchen ta zuba musu abinci ta ajje gefe sannan ta fito t umarce su da su shege k'aramin dakinsu, su cire kayan makarantarsu" toh sukace mata a tar suka wuce"sannan suzo su wanke hannu ga abincisu ta zuba musu su dauka" toh yaran su k'ara cewa"cikin hanzari suka  gudanar da komai kamar yadda ta zaiyana musu,haka sukayi komai a tsanake bayan sun gama ta zubawa kowa ruwa yayi wanka, sannan tace su wuce suyi sallah su zo su wuce islamiyya lkc ta yayi, amsawa sukayi da toh" sukabi umarninta kamar dai yadda suka sabi kullum, dalilin kuwa gabaki d'aya tsakalinin dawowarsu daga makarantar boko zuwa lkc tafiyar su islamiyya baya wuce miti talatin" suna gama shiryawa suka sake yi mata sallama suka tafi" domin basu babansu yana gidan ba bare su saurari inda yake,ko da sun sani ma ba Sabin tatashi kamar yadda ya nuna bayason su ra6eshi suma basa zuwa inda yake". Ita kuwa ZAINAB tunaninta RABI'U ko bacci yake yi shine dalilin da yasa bata barsu su shiga dakinta ba bare ma susan yana gidan,bayan fitarsu ne yasa ZAINAB ta shigo d'aki da nufin ta dan kwanta ta huta sai ta tarar ashe RABI'U ba bacci yake ba tunda ya gama cin abinci ya kashingid'e yana ta chat da wayarshi ganin ta shigo ta tarar yana murmushi shine dalilin da yasa ZAINAB ta fasa kwanciyar dayi niyya"zuwa tayi ta zauna da gefenshi nesa kadan tace masa au ashe ba bacci kakeyi ba na dauka bacci ne ya kwasheka tun dazu" shiru yayi kamar bazai amsa ba sannan yace mata eh banyi ba cin ba,akwai damuwa ne?" Jin RABI'U ya fadi hakane yasa ZAINAB gyara zama ta amsa da cewar eh a'a ah daman da naje asibiti d'azu ne likita yace na nemeka mu zauna muyi shawara akan wata matsala da take shirin tunkaroni shije dai maganar tawa!!" d'ago ido yayi ya d'an kalleta da cewar cigaba ina jinki kamar wacce?koda yake ai ke ta shafa ma tunda ke kikace matsala na shirin tunkara har nake ma k'ara tambayarki" ZAINAB bata damu da yanayin amsarshi ba da kuma tambayar da yayi mata a hade ba, ta cigaba da rattaba mishi bayanin yanayin da take ciki da kuma bayani likita da kuma shawarar da yace tabi, wani wawan mari ya watsa mata a fuska da cewar ni kika mayar dan iska kenan?" Wanne likitan kikaje yayi miki wannan gwajin da har kika bude mashi gindinki ya gani?"amsawa tayi da cewar ba budewa nayi ba fa"  tareta yayi da cewar toh yaya  akayi ya sani?" shiru ZAINAB tayi  kamar kurma ta dafe kuncinta tayi ba tare da tace komai ba" huci ya kama yi kamar mahaukaci da cewar anki a kusanceki din dan uwarki, ni zaki kawowa wulak'anci?da iskanci? Bari kiji ba yanxu nayi niyya kwanciyar da ke ba har sai na cika sharadi da wa'adin da na d'ibarwa zuciyata zanyi, har sai kin cika mace mai aji da yanchin da zata sami wannan damar, akin baza kwai,ba irin wanna gindin nake buk'ata  wanda da ancishi sai haihu kamar kanya ,ki bari sai ya zama kalar yayi irin na matan da sukan Kansu sai ki kawo naci kinaji na ko?" Tunda ZAINAB ta dafe kuncita bata tayi k'asa da kanta bata k'ara d'agowa ba, duk maganganun da yake yi tanajinshi amman babu damar mayar mishi da martani domin kuwa bakasan me zatace masa wani kukan baki ciki ZAINAB ta saki rushewavdashi hadi rike k'afafun RABI'U gwaiwarta a durkushe tana kuka tana yi masa magiya dan Allah ya fashinci halin da take ciki" san RABI'U bai tauya magana ya tureta  gefe ya cigaba da latsa wayarshi, jin ta isheshi da kuka ne yasa ya fara kiran wata lamba yayi hansfree da cewar hello!!" daga can akan d'aga da cewar ina jinka" magana yayi da cewar yawwa JAMCY kinga irin abinda nake gudu ko?" Ta amsa da cewar kamar yaya?"eh sai da na gaya miki cewar ba yau na shirya dawowa gidana ba kika takura min sai na dawo gashi daga dawowata har an fara 6ata min rai da zuciya!"amsawa tayi da cewar ayya sorry dear ai naga kamar kar mu shiga hakkin madama ne shi dalilin da yasa nace kaje ta ganka, tsawan two days fa ai babu dad'i ko?" Tsaki yayi da cewar kina wani maganar madam da ma madam din da tasan kanta ce irinki" murmushi tayi wanda har ya fito da yar siririyar dariyarta ta cikin waya tashi"ta amsa da ko?" Yace eh mana" duk maganganu da sukeyi ZAINAB najinsu tana gefe tuni ta daskare a durkushe sabida takaicin abinda kunneta yake jiye mata" shi kuwa RABI'U ko a jikinshi ya cigaba da wayarshi "da cewar Allah kuwa da ga gaske nake mai sanyi na wallahi idan bana tare da ke sai naga duniyar duk tayi min duhu" karba zancan tayi da sauri da cewar da gaske?" Yace wallahi kuwa" amsawa tayi da cewar nima bana gajiya da kai wallahi kan dole nake hakura nabarka domin babu yadda na iya tunda nasan bani kad'e ce da kai ba" tareta yayi da cewar injiwa!kamar wani zai rigashi yace ina sam ai babu wata mace a gaba wallahi sai ke"  dariya tayi da cewar nagode toh" bata rai yayi kamar tana kallonshi yace toh yanxu ya za'ayi in dawo kin lamincemin ko yaya?"  Amsawa tayi da cewar zaka iya tahowa mana ai ni I'm free"godiya yayi kamar wanda akayiwa albashir da aljanna yace toh gani nan zuwa yanxu"OK kawai tace" shi kuma ya yanke wayar ya dawo kan ZAINAB da cewar kinji irin matan ga suka isa nan masu gidin da sirkin ruwan zinare  amman ba irinki banza ballagaza mara class, kauce ya sa k'afa ya ham6are duwawunta tayi gefe ya fita............




~AMENAT KABARE KIRU~






*KARUWAR GIDA*




*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*

*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 


*TSOKACI*

*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*




*ban manta da kuba yan karuwar gidan fans ina yinku over hakika ina jin dadin comment dinku gareni ku cigaba da gashi suya sai ma ranar bani na fad'i wannan kalmar ba Rabe ne yasen😆?🤪⛹,shalele maman (mama many)raggon namiji, kema ban manta da ke ba kina kasheni da irin naki salon😍*



*1⃣🅾*



Wani irin kuka mai ban tausayi da daskarar da zuciya ZAINAB ta k'ara yi wanda har sai da ya haifar mata da ciwan kai mai tsakani" fashe da kuka tayi hadi da zake tunano maganganu RABI'U babu  kalmar da tafi tsaya mata iyllah ta kiranta da yayi da ballagaza, da cewar matan waje ne masu gidin mai dauke da surki da ruwan zinare!!! Abin da ya k'ara yafasa zuciyar ZAINAB kenan wanda ya hanata sukuni a duk harbarwa zuciyarta."A wannan ranar ZAINAB ta k'ara tabbatarwa kanta da waye RABI'U" domin kuwa ta k'ara fadawa kogin nadamar saninshi da tayi a rayuwarta",shi kuwa yana fita bai tsaya ko ina ba sai ibedi wani dandalin yan hamsin ne da yake a cikin sabon garin ta KANO domin kuwa duk wata karuwa mai lasisi a nan take karuwanci ta,shima anan ya sami daya daga cikin irin su watau JAMILA (JAMCY) karuwa ce wadda ta shahara a fannin karuwancinta da duniyanci ko kadan batada mutunci domin kuwa duk wannan rawar k'afar da RABI'U yake akanta,ita sam baya burgeta tana biye masa ne kawai dan kudin da take samu daga gareshi" amman haka baya hana idan rashin mutuncinta ya motsa ta rufe ido taci mutuncinshi a idon duniya,"a hakan RABI'U yake binta kamar yayi mata sujada sabida tsakanin bukatarta da yakeyi" amman ita hakan sam baya burgeta"yana isa d'ankin nata ya sameta  da wani k'aton namiji a kwance suna ta harkokinsu na nishad'i" haka RABI'U ya zauna daga waje har sai da wancan ya gama duk abinda zaiyi shida JAMCY ya fito sannan shi kuma ya shiga ya zauna na jiran abinda zata ce masa"yaso yayi mata magana, amman sai ya tuna rashin mutuncita hakan yasa ya share domin yasan ba kyaleshi zatayi ba da zarar yace zaiyi masifar ma" a zaune take a gefen katifarta ta d'ago idanu hadi da yi masa far dasu ta kashe ido guda d'aya hadi da d'age girta ta gefe tace yadai nawan?" Murmushin yayi da cewar na k'araso" amsawa tayi da OK" sai kuma kazo ka tarar nayi bak'o wani tsohun costomer na ne,ya cika naci wallahi, shine dalili babu yadda na iya dashi tunda dasu na fara, kaga kuwa tuna baya shine rok'o inji yan Hausa" mirmushin k'arfin hali RABI'U ya k'ak'alo domin yasan da ya nuna mata yaji haushi zasu 6ata, ya k'ara da cewar ai daman son samun mutum ace a sashi da wanda suka dade tare amman fa kinyi kyan kai,takunki yana yana burgeni kullum, kina kashe zuciyata da sakonki" amsawa tayi da ko" d'aga mata gire yayi da cewar yeah" tasowa tayi daga inda yake ta zo inda yake a zaune ta kwanta akan cinyarshi cikin shwagwa6a ta fara shafa wuyanshi" wani gauron numfashi RABI'U ya fara saki kamar tsohun  amale"haka dai JAMCY ta ringa bin jikinshi da jagwalgwalo lugu da sak'o "shi kuma yayi sundundun a zaune kamar gunki"haka tai ta bin jikinshi da lasa kamar mayayya tana k'are shfeshi har n tsawan lkc ba tare da ya kwanta da ita ba, daga k'arshe ta shagalar dashi ya kasa tabuka komai da ita dole ya kwanta suka kama bacci a tare domin itama ta gaji, daman duk lkc da ta gaji bata gaya masa ta dauka maza da yawa sai dai ta nuna masa  hakan a aikace"...

Ita kuwa ZAINAB yadda taga rana haka data dare domin Allah_Allah take gari ya karasa wayewa taga shogowar RUKAIYYA k'awarta tazo gidan domin sanar mata da yadda suka kwashe da RABI'U" tunda ta gama shirya yara suka wuce Makaranta ta tashi ta yi duk wani cikinta na gida duk da zuciyata babu dad'i haka ta zauna tana kallon hanyar shigowa domin jiran RUKIYYA amman shiru haka har yara suka dawo daga makarantar boko babu RUKAIYYA babu dalili haka har suka sake shiryawa suka koma islamiyya bata zo ba,kai har magariba ZAINAB tana zuba ido shiru,haka taita sak'e2 a zuciyata amman dai bata sami amsa ba,tunani ta ringa yi ko ta shirya taje ta duba RUKAIYYA ta gani ko lfy? Taso hakan amman sai ta tuna idan ta fita komai zai iya faruwa domin kuwa RABI'U zai iya dawowa ba tare da ta zataba tunda bashida tabbas wannan hujarce tasa ZAINAB ta fasa zuwa gidan RUKAIYYA taji dalilin rashin zuwana gidan nata da tace zatazo." Haka dai  ZAINAB ta zauna tana jiran tsammani,ganin dare yayi sosai yasa ta sawa zuciyata cewar RUKAIYYA bazata zo ba,haka ZAINAB tayi kwanan zaune tunanuka kala2 ta shiga yi babu abinda zuciyata bata gaya mata ba akan yadda zatayi da RABI'U, amman ta share domin ita batada wani za6in da zatabi a yanzu sai abinda K'awarta ta yanke mata gashi bata zo ba." Shi kanshi wanda take tsoro idan ta fita ya dawo yayi mata masifar bai dawo ba, da amala yau ma ba'a gidan zai kwana ba ya koma inda ya fito a zai kwana ya raba musu kwana da matan waje kenan"k'ara fadawa ZAINAB tayi kogin tunanin yadda zata dauki mataki akan abibda yake mata amamn ta kasa samo hanya, domin kuwa duk wata hanyar da ta sak'awa zuciyata sai taga ba hanyace mai 6ullewa ba, sabida RABI'U ya wuce tunaninta,haka dai ta sake wayar wani garin babu amsar yi." A haka har wata ranar ta k'ara takewa ga yamma na k'aratowa amman babu RUKAIYYA babu dalilnta, a ranar ZAINAB tayi Allah wadaran da rashin wayar hannu wacce ta rasa ta a dalilin mijinta na cewar bazara rike waya ba" ganin babu sarki sai Allah yasa ZAINAB ta yake shawarar fita ko ta halin k'ak'a domin dubo RUKAIYYA a wanne hali take"wannan dalilin ne yasa ta shirya bayan yara sun dawo daga islamiyya ta tafi gidan RUKAIYYA domin ganin halin da take ciki, duk da rashin kuzarin da takeji a jikina ga rashin kwanciyar hankali uwa uba ma bata iya cin abinci kwata2 haka dai ta daure ta dauki hanya sai gidan RUKAIYYA, tana zuwa ta yi sa'ar RUKAIYYA na gida"tayi sallama"RUKAIYYA wacce tuni ta runca6e cikin aikin kwalima ta fito da kaya ta amsa" hadi da a ajje kayan da ta debo kayan da suke hannunta,tace k'awata sannu da zuwa" ZAINAB ta amsa da cewar yawwa" hadi da samin gurin zama ta zauna tana yiwa RUKAIYYA kallon rashin fashintar hada kayan da taga tanayi" kamar RUKAIYYA tasan tunanin da ZAINAB takeyi ta katseta da cewar kinga ina had'a kaya ko?"ZAINAB ta amsa da eh mana ko lfy?" Murmushi RUKAIYYA tayi da cewar eh lfy" wallahi jiya bayan rabuwar mu dake mai gidan yayi min waya da cewar anyi transfer din  shi zuwa jihar IMO shine ya sanar min da cewar na shirya komai nawa yana hanya zaizo mutafi nan da gobe babu yadda banyi da shi ba ya barni zuwa wani watan ma tafi gabaki d'aya ya nunamin bai yadda da ba,,dole haka naje na shigar da duk wani bayani a gurin aikina nima duk da pravet clinic nake aiki,amman banso barin aikina ba sai dai muhimmancin aurena yafi aikina na,wallahi k'awata dolece zata da ayi hakan,shine dalilin jina shiru da kikayi daman jira nake na kammala wanna aikin da nakeyi yau komai dare sai nazo gareki sai kuma gaki wallahi duk aikin ana da nakeyi zuciyata bata tare da ni dominni  kaina  bana son barin garin nan ko dan ke kaide" sai da tazo nan sannan ZAINAB ta d'ago idona wadda tuni ya cika da hawaye tace k'awara ya zamuyi hakan Allah yaso A haka har wata ranar ta k'ara takewa ga yamma na k'aratowa amman babu RUKAIYYA babu dalilnta, a ranar ZAINAB tayi Allah wadaran da rashin wayar hannu wacce ta rasa ta a dalilin mijinta na cewar bazara rike waya ba" ganin babu sarki sai Allah yasa ZAINAB ta yake shawarar fita ko ta halin k'ak'a domin dubo RUKAIYYA a wanne hali take"wannan dalilin ne yasa ta shirya bayan yara sun dawo daga islamiyya ta tafi gidan RUKAIYYA domin ganin halin da take ciki, duk da rashin kuzarin da takeji a jikina ga rashin kwanciyar hankali uwa uba ma bata iya cin abinci kwata2 haka dai ta daure ta dauki hanya sai gidan RUKAIYYA, tana zuwa ta yi sa'ar RUKAIYYA na gida"tayi sallama"RUKAIYYA wacce tuni ta runca6e cikin aikin kwalima ta fito da kaya ta amsa" hadi da a ajje kayan da ta debo kayan da suke hannunta,tace k'awata sannu da zuwa" ZAINAB ta amsa da cewar yawwa" hadi da samin gurin zama ta zauna tana yiwa RUKAIYYA kallon rashin fashintar hada kayan da taga tanayi" kamar RUKAIYYA tasan tunanin da ZAINAB takeyi ta katseta da cewar kinga ina had'a kaya ko?"ZAINAB ta amsa da eh mana ko lfy?" Murmushi RUKAIYYA tayi da cewar eh lfy" wallahi jiya bayan rabuwar mu dake mai gidan yayi min waya da cewar anyi transfer din  shi zuwa jihar IMO shine ya sanar min da cewar na shirya komai nawa yana hanya zaizo mutafi nan da gobe babu yadda banyi da shi ba ya barni zuwa wani watan ma tafi gabaki d'aya ya nunamin bai yadda da ba,,dole haka naje na shigar da duk wani bayani a gurin aikina nima duk da pravet clinic nake aiki,amman banso barin aikina ba sai dai muhimmancin aurena yafi aikina na,wallahi k'awata dolece zata da ayi hakan,shine dalilin jina shiru da kikayi daman jira nake na kammala wanna aikin da nakeyi yau komai dare sai nazo gareki sai kuma gaki wallahi duk aikin ana da nakeyi zuciyata bata tare da ni dominni  kaina  bana son barin garin nan ko dan ke kaide" sai da tazo nan sannan ZAINAB ta d'ago idona wadda tuni ya cika da hawaye tace k'awara ya zamuyi hakan Allah  Karki damu" hmmm kawai RUKAIYYA tace" sanna tace ai damuwa ta zama dole domin kuwa sabo akewa kuka"itama ZAINAB ta dangane ne domin a sarari taga damuwar RUKAIYYA tunda tasan duk wani abu da take ji bai wuce akanta ba, amman ai mijinta shine mafi mahimmanci a gareta, banda abin yazo haka da tasan babu wani abun da zai rabasu sai mutuwa" wanna dalilin ne yasa ta danne nata tashin hankalin domim ta bata damar shiryawa tabi mijinta cikin kwanciyar hankali domin hakan shine zaisa taga ta yi mata sakaiyya ta kwarai" ba" ba ZAINAB ce kade ta fashinshin RUKAIYYA ba ita kanta  tasan karfin hali ZAINAB din take, dan taga ta faranta mata rai amman tasan cikin zuciyar ZAINAB d'anfare take da tashin hankali kala2 sai dai babu yadda zasuyi da kaddara ubangiji, shine ya tsaro hakan"duk wata magana da ZAINAB taje da ita domin gayawa RUKAIYYA haka ta barta  a zuciyarta ta hakura da gaya mata komai, tunda ma abin yazo da haka a cewarta idan ta fadama babu wata mafita tunda duk wata gamana daga yau ne, domin gobe zasu rabu" wanna ce ta k'ara SA ZAINAB a cikin matsananci tashin hankali domin kuwa ko tantama babu tunda har zata rasa RUKAIYYA akusa da ita tata tazo k'ashe tabbas bakin cikin RABI'U ne zai kasheta nan zancan zucin da takeyi ashe har ya fito sarari"da sauri RUKAIYYA ta k'ara dago da ZAINAB da cewar wanne subatu kikeyi haka yar uwata?" Shiru ZAINAB tayi ta cigaba da yin kukan da takeyi" nan RUKAIYYA ta tattara duk wani hankalinta da nutsuwarta ta fara yiwa ZAINAB nasiha ankan yadda da k'addar da hakuri a kar6weta yadda tazo, hakan shine cikar mumuni na gari" karki manta da duk wani baki da Allah ya hallita shine yake hore masa yadda zaiyi ya rayu ba tare da dabararshi ba ko wayonshi dan haka ki yadda da Allah ki rikeshi sau da k'afa sai ya iyamaki domin hausawa sunce dogaro ga Allah jari ne" haka dai RUKAIYYA tsira bin ZAINAB da nasihohi masu ratsa jiki da zuciya,har sai da taga ZAINAB din ta dan saki jiki sannn ta tashi ta tayata hada kayyayakin da takeyi." RUKAIYYA  da kanta ta ware kaya masu yawa na sawa da na mafanin gida da ku dade masu yawa ta bawa ZAINAB tace ta rik'e ta bar mata kamin taje garin da aka turasu taga yanayin zama da zarar taga hanya zata ringa zuwa tana ganin ZAINAB tana komawa" ZAINAB ta karba tayi mata godiya, sunsha kuka kamar basu daina ba,lkc da RUKAIYYA ta rako ZAINAB gida motarta ta da duk kayan da tabata sannan ta rubuta number wayar ta ta bawa ZAINAB da cewar gashinan duk lkc da take da buk'atr wani abu ta buga mata ta sanar mata, insha Allah zata sami hanyar da zata ringa yi mata sako" godiya ZAINAB tayi hadi da k'ara fashewa da kuka"da kyar RUKAIYYA ta rarrasheta tayi shiru" sannna suka damu damar da  sukayi sallama da cewar gobe da sassafe RUKAIYYA zata zo su k'arayin sallama." Toh ZAINAB tace mata suka k'arayin sallama sannan ta tafi. Ita kuwa ZAINAB ta kashe duk kayan da RUKAIYYA ta bata da kudaden ta Adana, sanna ta shige d'akinta ta cigaba da aikin kukan da ya zame mata jiki, har yara suka dawo daga islamiyya ta basu ambinc tana ta kallon hanyar dawowar RABI'U amman shiru" haka dai ta sake zaman ba tare da ta runtsa ba har aka fara kiraye2 sallah asuba bata ritsa ba mikewa tayi ta tafi ta tafi ta daura alwala tazo tayi nafiloli, da baya ta mike ta kawo farillah bayan ta idar ta kwanta ta rintsa kadan ta fara baccin kenan taji ana bugun k'yauron kofar gida, a firgice ta tashi ta fito ta nufi kofar gidan,tana zuwa ta bude bata jira tambayar waye ba ta bude,ganin wanda yake a tsaye ne a kofar gidan bayan ta bude gidan yasata cikin firgice, domin kuwa shi kanshi a gigice yake lkc da ta ganshi ba wani bane sai UMAR dan mijin RUKAIYYA ne a tsaye ido jawur yace kuka ga murya ta disashe ya ce baki na wara yace AUNTY ......"amsawa ZAINAB tayi da cewar lfy UMAR?" Da kyar ya budi bakin cewar AUNTY na ce Allah ya karfi rayuwata, ko jira batayi ya kara fadeba taci kwallarshi da cewar karya kake wallahi RUKAIYYA ta bata mutu ba garin yaya zaka ce ta mutu menene ya Sameta ka gaya min gaskiya nace ka gayamin gaskiya!!!" ganin ta gigicene yasa ya cire hannuta daga kan kirjinshi, cikin kuka yace wallahi da gaske nakeyi ta rasu !!!!a dalilin bugawar zuciya da yasameta  cikin daren jiya!! bayan nadawo daga gurin abokaina ne nashiga domin sake tayata harhade kayan da bata k'arasa hadawa ba shine na  sameta akwance tana  wani irin nishi da fitar da dafara daga bakinta ,nayi korin kiran likitan da zai dubata ta kamin yazo ta rigamu gidan gaskiya" koda likitan yazo shine ya tabbatar min da dalilin mutuwar tata,tun a daren aka sakarwa da kowa da kowa dangin na kusa da na nesa wasu tuni sun hallara a gidan, ganin ban ganki a gidan ba yasa na taso yanzu na zo gaya miki" wani irin kuka ZAINAB ta sake saki tare da ihu wanda hakan har sai da ya taso makwaftanta suka fito domin jin ihun kukanta, haka suka ringa bata hakuri da" shi kuwa UMAR tunda ya gama mata bayani ya  juya gida domin komawa su yi Jana'izar RUKAIYYA( ALLHU AKBAR KABIRAN)." Komawa cikin gida ZAINAB tayi ta tashi su MARIYA tace suje makwafta su jirata zataje gidan rasuwa RUKAIYYA ce Allah ya karbi rayuwarta" su Kansu yaran da suke kananu sai da suka koka bisa maganar da sukaji na rasuwar aminyar mahaifiyar tasu." Amsawa sukayi da toh cikin kuka" itama ta shirya ta fita zuwa gidan rasuwa koda ta k'arasa kofar gidan ta tarar ya cika mak'il da jama'a da kyar ta sami hanyar da ta ra6a ta shiga cikin gidan tana zuwa ta tarra da gawar RUKAIYYA lallibe da zani a kwance a tsayar falon ta" tana budawa ta fada kan kirjita ta na wani irin kuka mai ratsa zuciya, hakika ZAINAB ta gigice da ganin gawar k'awarta ta sosai ta girgiza mutar ta domin kuwa gani take tamkar ita kade akayiwa mutuwar" nan fa mutane da yan uwan RUKAIYYA suka janye ZAINAB da kyar sannan a ka dauke gawar akayi mata wanka aka hada ta domin kaita makwancin ta,sai da aka dauke gawar aka fitar da itane ZAINAB ta k'ara yinkewa da maganar mutuwar RUKAIYYA gaskice domin da duk gani take tamkar mafarki take" wanna ne ya k'ara hasgitsa tunaninta da nutsuwarta domin gani take itama tata tazo k'arshe tunda ta rasa iyayenta bata kallon kowa a matsayinsu sai kawarta RUKAIYYA yau itama Allah ya amshi kayarshi," subatu ZAINAB ta riga yi mai ban tausayi babu wanda bai tausayawa ZAINAB ba a gidan mutuwar nan" domin kuwa kaiwa take tana kawowa tana surakatai tana juya hannu kamar wacce take shirin zarewa" ganin haka ne yasa wasu daga cikin matan da suke gurin suka kama ZAINAB suka zaunar da ita aka dinga yi mata nasiha da bata hakuri har ta ta lafa da subatun da takeyi" amman sam taki daina  kukan da takeyi yaki tsayawa domin kuwa jinta take tamkar tsirara take a rayuwata ta duniyar yanzu" haka dai tacigaba da kuka mai tsuma zuciya da ban tausayi matuka" ana ta bata bakin tayi hakuri"............... 


~AMENAT KABER KIRU~




*KARUWAR GIDA*



*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*


*SADAUKARWA GA:*

*HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMAD)*

 


*TSOKACI*

*wannan labarin bai shafi wata ko wani ba,na rubuta shine domin ganin yadda rayuwar mata ta sauya a wannan zamani duba da yadda kwadayi da son zuciya yayi yawa a zukatan ku,ba nayi ne dan son yad'a bad'ala ba zanyi ne saboda na zak'ulo wasu halaye da suka shiga gidan aure.*


*GAISUWAR BAN GIRMA*  

*_TA MANYAN HAMSHAK'AI MANDIYOYI  BILKISU ABBAS SA'ID KIRU DA UMMU FATI MUTANE SAUDIYYA, BAN MATA DA KE BA UMMU ABDULLAHI KD,MMN AHMED KD (BAGOBIRA) MY SISTER UMMU MUHAMMAD, GA IRIN TAKU🤙_*



*1⃣1⃣*



Haka dai ZAINAB ta gaji har ta hakura. Tunda ta fara zuwa gidan karbar gaisuwa RUKAIYYA har sai da akayi sadakar bakwai da ita amman har a wannan lkc RABI'U bai dawo gida ba tun abin baya damuna har ya fara damunta haka tai ta rama da k'arewa a tsaye duka goma da goma" sai da RABI'U ya cika sati biyu Chif a waje ba tare da ya lek'o gida ba sannan ya dawo" koda ya dawo bai fasa halinshi ba haka zalika bai tausayawa ZAINAB halin da take ciki na rashin da ta shiga ba haka yayi ta kunsa mata taikaici na yau daban na gobe daban. Allah sarki duniya mai yayi haka ZAINAB ta kasance cikin rayuwar ban tausayi ga rashin kwanciyar hankali da miji" 


Akwana a tashi RUKAIYYA ta cika wata hudu da mutuwa anan ne fa rayuwar ZAINAB ta k'ara tuzarta da wulak'anta domin kuwa idan ba kallon tsanaki mutum yayi mata ba zai ganeta ba duk da dacan din ma ba dadi take jiba amman da dama2" shiga d'aki tayi tana kwaso yan kayayyakin ta nasawa wadanda suka rage mata masu daraja a cikin werdrop dinta kawai sai ta arba da wata takada rubuce da number waya an rubuta HAFSAT AL'AMEN da sauri ta k'ara juyata takardar domin kuwa ta manta da ita tsawan lkc wanna da sauri ta janyo hijaf dinta ta ratayashi a wuya ta fita sai makwafata ta fada tare da yin sallama" makwafciyarta ta amsa" ko gaisawa ZAINAB ta jira sunyi ba ta tambayi makfciyarta ta ko wayarta da kati?" Amsawa tayi da cewar eh da kawai hadi da miko mata wayar kai tsaye" ZAINAB tasa hannu ta karba" tana karba ta fara latsa lambubin da suke rubuce a takardar da take hannunta cikin hanzari kamar wani zai kwance wayar tana gama loda lambobin ta tura kira hadi da karawa a kunneta,ta nasawa taji ta shiga sai tana k'ara amman ba d'aga ba har tagaji da gunji  kiran ya yanke ba tare da an d'aga ba,haka ZAINAB ta sake kokarin sake tura kiran a karo na biyu har sai da ta kusa katsewa sanann taji an daga da cewar hello" jin haka yasa ZAINAB itama tayi sallama aka sake amsawa da tambayar wayem?" Da sauri ZAINAB tace nice ZAINAB ABDUL dan Allah ko da HAFSAT AL'AMEN nake magana?" Wata dariya taji an sakar mata da cewar eh itace shegiya kawata sai yau zaki nemeni ai nayi fushi"da sauri ZAINAB tace ko kadan wallahi tun lkc da kika bani number na rasa inda na jefa ta shine dalili yanzu ma da kika kirana wallahi banfi mutu biyu da ganinta ba cikin kayana shine dalilin da yasa na nace bari na gwada naji ko zata shigo" amsawa tayi da cewar OK karki damu ai komai yin Allah ne, yanxu gashi ya nufeki da ganinta kuma kinyi sa'ar ta shigo kashe na kiraki"ZAINAB ta katse layin" HAFSAT ta sake bugowa hadi da tambayar ZAINAB da cewe wanna ne layin naki na ajje shi" girgiza kai ZAINAB tayi kamar tana ganinta da cewar a'a banida wata ai har yanzu"wani tsaki HAFSAT ta saki da cewar ban gane ba, bakida ra'ayine ko kuwa lalacewa tayi?" A'a ZAINAB tace babu d'aya daga ciki banida ita ne gabaki d'aya"mamakin ya kama HAFSAT daga can bangaren da cewar daman har yanzu akwai wadanda basuda wayar hannun a wannan lk duk saukinta? haba kawata  karki bada mata mana" murmushi ZAINAB ta yi da cewar k'awata kenan ai nima ba haka naso ba" tamabayarta HAFSAT tayi da cewar toh lefin waye gayamin? Da kina da ita ai da gaisawa batayi wuya ba.sun dade suna hira anan ne ZAINAB ta sanarwa da HAFSAT rasuwar RUKAIYYA nan HAFSAT ta jajantawa ZAINAB bisa rashin da sukayi da cewar insha Allah gobe zatazo da yamma da zarar ta gama uzuririkanta" ba karamin dadai ZAINAB taji ba domin kuwa hakan ya nuna a sarari" amsawa tayi da cewar babu damuwa Allah ya kaimu goben"HAFSAT ta masa da amen"sannan sukayi sallama juna ta yanke wayar ta."itama ZAINAB ta mikawa makwafciyarta wayarta tayi godiya"ta amsa da babu damuwa"ZAINAB ta fito ta koma gida zuciyarta  cike da farin cikin albishir din da taji daga bakin k'awarta wacce suka rabu tun tsawan lkc. Haka dai ZAINAB ta zauna tana ta jiran kashe garin ranar tazo kamar ta k'arawa lkc gudu,har dare haka takai tana jiran tsammanin gari ya waye." A wanna daren ne kuma ZAINAB ta k'ara fadawa tsaka mai wuya domin kuwa a cikin daren ne ANAS ya farka da wani irin mugun ciwan ciki haka yayi ta murkusu!!"ba ZAINAB ba hatta MARIYA da take yarinya sai da ta kokawa ANAS din" sakamakon yadda taga yaron yana wata irin zambarma hadi da koka mai ban tasauyi"ga gida babu namiji domin kuwa yanzu RABI'U sai ya ga dama yake zuwa gida ya dubasu babu abinda ya damesu da a wanne hali suke yana can yana sharholiyarshi ba tare da yasan halin da iyalanshi suke ciki ba." Haka dai ZAINAB da MARIYA sukayi kwanan zaune ba tare da d'ayansu ya ritsaba,a ranar ZAINAB taci kuka kamar idonta zai tsiyaye sabida tsakanin kuka da tunanika iri da kala, domin kuwa a daren RUKAIYYA ce ta bijiro mata domin kuwa tasan ita kayiwa mutuwa ba kowa ba,hakika da tana raye tasan tashin hankalinta kadane koda zatayi bazai kai kamar wanda take ciki ba" haka dai tai ta tuna al'kairin RUKAIYYA gareta lkc da take raye." A haka har gari ya dauko waye was sannan ANAS ya samu ciwon ya dan lafa masa yayi bacci" ganin ya rintsane yasa ZAINAB tashi ta gabatar da sallolinta sannan ta dawo tacewa MARIYA itama taje tayi tata sallah" toh tace sannan ta mike ta fita"bayan ta dawo tayi sallah itama ta koma ta kwanta ta koma bacci domin ta dan rintsa." Ita kuwa ZAINAB tashi tayi bayan ta gama lazimi ta shiga kitchen ta huwara wuta domin Samar musu abin kalaci a gurguje"bayan ta gama ta daura musu ruwan wanka,ta koma ta tashesu ta sannan ta fito da ANAS ta fara yi masa wanka"bayan ta gama masa ta umarci MARIYA da taje tayi nata wanka" toh tace" ta fita cikin k'aramin lkc ta dawo" ZAINAB ta hada masu abin kari sannan ta fita ta yi shara itama ta shiga nata wankan batafi muti sha biyar ba ta fito ta dan goga mai kadan sannan ta saka yan kod'add'un kayanta ta zauna tana nazarin yadda zatayi da ciwan ANAS duk da ya farka jikin nashi da sauki amman dai ta firgita matuk'a domin kuwa ko kudin chemis batashi bare na motar da zata hau taje ta kaushi suga likita" haka dai ta zauna tana ta sake2 a zuciyata babu amsa daga k'arshe dai ta mika wuya ga Allah tana kallon hanyar domin sauraron zuwan bakuwarta." 

Karfe goma dai2 HAFSAT ta yiwa gidan ZAINAB tsinke domin kuwa kugin tsayawar motar HAFSAT ce tayiwa kunne ZAINAB tsine koda bata leka ta gani ba amman tasan babi wanda zaizo kofar gidan ta a wannan lkc da mota har kofar gida, domin kuwa mai zuwa da motar da can RUKAIYYA ce kuma Allah ya karbi kayarshi" da sauri ta mike tsaye daga inda take zaune tun tsawan lkc domin kuwa Jin sallamar HAFSAT tayi a tsakar gida" cikin farin ciki da murna ta fito ta tafi da gudu ta rumgume k'awarta ta,hadi da yi mata sannu da k'arsowa"amsawa HAFSAT tayi hadi da daukan kafadar ZAINAB da cewar yimin a hankali k'awata kar ki kayar dani" murmushi ZAINAB tayi da cewar wace ni? Na kayar da manya irinku" dariya HAFSAT tayi da cewar ke kuka bakya ganin takalman da na sako ne?" Sai a wannan lkc ZAINAB ta kula da uban tsinin takalmin da yake kafar HAFSAT domin kuwa tsininshi ya kai tsini matuk'a gashi da kyau da walwali kalashi daya da yar karamar jakar hannuta wanda ta cikashi da awarwaron gold da zubuna suna duk na gold kai tsayawa ma lissafa tsaddadun kayan jikin HAFSAT 6ata lkc ne." ZAINAB ca tacewaw ZAINAB oh yi hakuri ai sam ba kula ba kisan abinka da wanda idonshi ya rufe da ganin k'awarshi sam bazai kula da abida yake a gabanshi ba" murmushi HAFSAT ta k'ara yiwa ZAINAB da cewar ai na lura kin shiga da yawa k'awata farin cikin ki yaki 6uyuwa a fuskarki naga alamar hakan" amsa ZAINAB tayi da ko? Toh mushiga daga d'aki man,kya cigaba da yankata k'awata" amsawa HAFSAT tayi da cewar ba wani yanka muje dai" ZAINAB ta shiga gaba HAFSAT na biye da ita a baya tana k'ara yiwa gidan kallon tsanaki tana mamakin yadda ZAINAB take iya rayuwa a cikinshi kuntattace ga rashin iska ga wani irin kauri da take Jin yana taso mata kamar ana k'ona taya ga wasu tarin kayan wanki daga can gefe abu dai babu dadi kallo" ZAINAB ta lura da irin kallon da HAFSAT takewa gidan amman ta share har suka shiga d'aki ta shifida mata sallaya tace mata ta zauna"nan fa HAFSAT ta k'ara tsinkewa da lamarin da ZAINAB take ciki sai da taga  d'akin da take ciki babu uwar komai sai tari shirgin tsumo karan da suka cikashi" zama HAFSAT tayi akan sallaya ta kalli ZAINAB da cewar k'awata ya kwana biyu toh?" Amsawa ZAINAB tayi da cewar sai kairan ,hadi da cewar bari na debo miki ruwa duk da dai har yanzu da sauran safiya" amsawa HAFSAT tayi da cewar a'a basai kin debo ba wallahi na gode, zauna muyi hirar ta abota ta kalli ZAINAB" zauna ZAINAB tayi tana fuskantar HAFSAT da cewar k'awata wallahi nayi mamakin ganinki a wanna yanayin domin kuwa da wani ne ya gayamin cewa zanyi k'arya ne ke kuwa yaushe kikayi auren da har zaki mayar da kanki tsohuwar dole? haba k'awata karki bayar da mata mana, ina RABI'U yana kallonki haka kika lalace kuma baiyi yun kurin yi miki magana ba ke kuwa?" Murmushi ZAINAB tayi da cewar ai shine ma silar lalacewar komai nawa da kika gani" amsawa HAFSAT tayi da cewar kamar yaya? Yanzu fisabilillahi shine zai zauna yayi miki gyaran gida da na daki da sauran kulawarka da duk ta dace?" Hmmmm kawai ZAINAB tace sanna ta dora da cewar da dai banyi niyyar gaya miki hujjar hakan ba, amman yanxu tunda har kina gani baki yadda ba toh bari kiji dalilin da yasa nace hakan kwashe lbr komai da yake guna tsakaninta da RABI'U tayi tun daga lkc da ta fara samun matsala da shi har kawo wannan lkc da take ciki duk wata cutarwa da yake mata ita da yara babu abinda ta boyewa HAFSAT har zuwa yau da take bata lbr" koda ZAINAB tazo karshen lbr ta ta dago ido domin tambayar HAFSAT meye nata laifin sai tayi arba da ita tana ta faman zubar kallah da share majina" bude baki tayi da kyar ta cewa ZAINAB sannu a gaskiya ko kwatar hakurin da kikayi ni bazan iya ba amman ki barshi idan yasan wata, ai biasan wata ba ,ba dai shi karuwan namij ba? toh da hannushi zaiyi nadamar abinda ya aikata miki a rayuwar shi ta duniya" zaro ido ZAINAB tayi da cewar a'a k'awata nifa tsoro gareni domin wallahi RABI'U ya wuce inda kike tunani ni dai ki rufa min asiri" amsawa HAFSAT tayi da cewar ai rufin asirinki kenan ki tashi tsaye tun kina raye basai takaici ya kasheki ba,irisu zuma ne sai da wuta, idan kina ganin zai baki matsala kiyi k'arshi zuwa kotu mana"sake zaro ido ZAINAB tayi da cewar kin manta da sharad'in da nace miki MALAM tayi min tun kamin ya rasu?" Amsawa HAFSAT tayi da cewar haka naji kince a cikin lbr da kika bani,toh ya zame miki wajibi tunda girmanki, ki samarwa kanki mafita tun kamin dare yayi miki domin hausawa sunce mace kamar ruwa take idan aka tsare mata hanya sai yiwa kanta, dan haka ki shirya d'amarar yak'ar bakin ciki d'a namiji daga zuwaciyar ki" wani dogon numfashi ZAINAB tayi da cewar toh ta yaya k'awata" hmmmm HAFSAT ta fara cewa sanna ta budi bakin tace toh ki zama karuwar gida mana domin yanzu wanna harka ita ce Sana'a mafi sauki domin majority matan yanzu ita suke dalili kuwa a matan da suke gidajan aure25% ne suke zaune da mazajen su lfy sauran duk rubabine kinga kuwa idan nace miki 75% karuwar gida ne kar kiyi mamaki domin maza basuda tabbas sune silar jefa matansu zuwa ga neman kudi ko ta halin k'ak'a" dafe k'irji ZAINAB tayi da cewar haba kawata sam wannan kalmar bata kamaceki ba domin wannan shawarar taki sai nake ganin bayi ba" amsawa HAFASAT tayi da cewar OK sai ki zauna zafin sha'awa ya kasheki da taikaicin d'an namiji wallahi kawata sam baki san yadda rayuwa ta juya bane" wani sabon numfashi ZAINAB ta k'ara saki da taji maganar HAFSAT kamar al'mara ta rasa bakin magana" ganin haka yasa HAFSAT tace ai k'awata ko dan ki rama abinda RABI'U yayi miki kya aminta da magana ta kuma ai karuwanci gida shine domin kuwa ko cinki aiki babu wanda zai gane tunda da aurenki,ke nifa wallahi matsalar da na samu da nawa mazajan sam bata doshi irin taki ba amman na nuna bazanyi zaman auren ba akan me zan zauna takaici ya kashe ni?shine dalilin ma da kika ga yanxu banida aure karena nake ci babu babbaka banida wanda zai matsamin nayi" amsawa ZAINAB tayi da cewar gaskiya k'awata bazan iya ba" jin haka yasa HAFSAT fusata tace ai sai ki zauna takaici ya kasheki!! hadi da mikewa ta bude Jakarta ta zaro kudi yan dubu2 ta mikawa ZAINAB hadi da yi mata sallama tace ta tafi" karba ZAINAB tayi tai mata godiya ta kara da tambayarya sai yaushe?"tabe baki HAFSAT tayi da cewar sai na sake samun time zan kewayo ku" godiya ZAINAB ta k'ara yi mata sanna tayi mata rakiya har zaure.


Shikuwa RABI'U tunda ya 6usa yaga da jini ai can ya tare gurin JAMCY ko waiyayar ZAINAB bayayi daga ibedi sai garesu na gyaran mota haka rayuwarshi ta sauya ko tsoran Allah bayayi bare tausayi maraicin ZAINAB" suna zaune a garejin su masu aiki nayi masu hira nayi irin wacce aka saba ta yau da kullum,guda daga cikin su ya nisa da cewar kai bari na tashi na shiga kasuwa tun kamin na shagala da hirar na" farat kuwa RABI'U ya amsa da cewar me zakayo a kasuwa yanzu? kamar wani mace" amsawa tayi da cewar wallahi tunda zan fito iyalina ta sanar min da cewar kayan abinci mu sun taho k'arewa"shine yanxu na tuna da maganarta toh kaga ai na hanzarta naje na sayi komai tun kamin dare yayi ko?" Wata dariyar mugunta RABI'U ya saki ya kalli na gefenshi da cewar kaji mutumin ka fa wai har wani rawar jikin shiga kasuwa yake madam ta gaya masa kayan abinci ya kusa k'arewa amman dan shine kaluluwa sarkin d'oki bazai jira ya k'are din ba amman kaji zaije ya sake sayo wasu"wancan ya bushe da dariya mugunta yace ai kasan mijin tace ne" mik'o hannu RABI'U yayi suka tafa yace wannan bai san mata ba abin tausayi bane wallahi ai mace tsakani ka da ita shine ta biya ma buk'ata malam amman da zarar ka nuna kana tausayinta babu d'an iska rinka kasan Allah ni dai yanzu a gidana bazan iya sayan kayan abinci da za'ayi sati ana ci ba" mikewa wancan din yayi da cewar oga RABI'U duk naji dalilanka dan haka kayi rayuwarka da iyalainka yadda kaga dama, nima ka barni nayi yadda nake so ya juya ya barsu ya tafi" yana juya suka sake kallon juna suka bushe da dariyar RABI'U ne har da cewar a haka zaka k'ara d'an wahala.



Ita kuwa ZAINAB tunda HAFSAT tabar gidan ta take ta tunanin maganar ta hadi da jinjina al'amarinta na ko kadan bataji nauyi irin shawarwarin da take bata ba? Wanna ai gurguwar shawarce ta yaya ma za'ace ita din tayi hakan, domin a ganina tuni mahaifinta yake guje mata faadawa rayuwar da batada ammafani,a tunanishi rashin aurene yake haddasawa ashe ba anan gizon yake sak'ar ba.........


~AMENAT KABER KIRU~







*KARUWAR GIDA*


*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*



*SADAUKARWA GA:*

*_HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMED)_*



*_Kuna Raina Kamar kudin haya yasen🤾‍♀_*

*yadomma mohmd Bello,my zuk,Sadiya I. Baso matar kirki, zainab sarki Mustapha Kiru, zainab b. Sani kiru(ta rabe), 🤭yar yola karuwar gida fans,Fatima Abubakar abaza life,Hauwa'u Umar Mohammed karuwar gida fans, Abdul h2, my bro amaccid'o Abubakar, Yaya hayat, Bashir sardauna mashek'i & mawasgi😜Ina gaisuwa kamala Bala yaron kirki Ina yinku over Kuna k'albina😘🥰*



*12*


Kadai ZAINAB ta wani tana juya maganar HAFSAT a zuciyarta............ Domin kuwa yanzu abin ya wuce tunanin duk wani mai tunin"haka dai ta yini tana jinana maganar Kawarta ta. "Allah sarki rayuwa (Ina ya Allah babu ya Allah sarkin iko da buwaya k'asaitaccan sarki gagara misali) a cikin wannna daren ranar ne Allah ya sake sakkowa da ANAS cutar ciwan ciki ya sake damk'arshi haha dai  ZAINAB ta sake kwanan zaune har gari ya waye basuyi bacci ba daga ita har yaron " Kamin gari ya waye ANAS ya suka kusan sau hudu zuwa biyar wannna ce tasa ZAINAB ta Kara rikicewa da shiga rud'u domin batayi tsammanin ciwan nashi har zai kaishi ga suka ba" k'agara tari gari ya waye domin ta kaishi asibiti"tun ZAINAB tana kuka a sarari har yakita da tana na zuci domin kuwa ji tayi ruwan idonta ya dauke baya iya zubowa ko kadan, haka dai tai ta zarya da yaron a hannuta daga d'aki zuwa tsakar gida"a haka har gari ya waye..... 



Gari na wayewa ta shirya ta fita domin Kai ANAS asibiti" tana zuwa cikin gwaugawa likitoci suka kar6eshi ba tare da sun tsaya neman wani bayani daga bakin ZAINAB ba."domin kuwa tana shigowa dashi cikin asibiti ya sake someway, wanna ce tasa aka wuce dashi emergency domin duba lfy sh"wani irin kukan zuci ZAINAB takeyi domin kuwa ta rasa yadda zatayi sau kinda MA Allah yasa jiya HAFSAT ce ta Bata  kudin da tazo asibitin dasu wannna ne ya takaita tashi hankalinta"shi kuwa ANAS tun bayan da aka tafi da shi dakin gwaugawa  likitoci ne suka taro akanshi domin ceto lafiyar shi"bayan ya farfado daga suman da yayi ne babba Dr yace ta kaishi dakin bincike na musaman domin yana son ya k'arayin bincike akan matsalarshi duba da yadda cikinshi yayi wani irin girma Kamar ba cikin k'aramin yaro ba." gani  an sake fito dashi daga 6angaren da aka kaishi yasa ZAINAB tayi saurin zaburowa daga inda take zaune tana tamabayar likita da cewar Dr ya jikin nashi? "kallonta yayi Shima cikin tausayawa yace ai yaji sauki zamuje dashi d'akin bincike na musamman ne domin sake dubashi dan gano asalin matsalar shi" amsawa ZAINAB tayi a hike a sanyaye da cewar toh Dr Allah yasa a gane din" amsawa yayi da cewar amen" Sanna yaruba yabi bayan k'ananun likitoh cin da yabasu umarnin sukai mass ANAS din d'akin bincike"bayan sun shigar da ANAS din suka daurashi a Kan gadon daya daga cikin gadajen da suke d'akin Kai tsaye sukai wa ANAS (x_ray)watau hoton cikin ya dauka"Kamin wani lkc Dr ya fitar da sakamakon da aka samu daga hoton cikin nashi da akayi." Bayan ya fitar ne ya Bawa daya daga cikin k'ananan likitocin da suke gefenshi yace ta Kai masa office gashinan zuwa"toh tace ta fita a hanzarce"shi Kuma Kuma ya k'ara komawa inda ANAS yake kwance yasa a aka dagoshi daga kwanciyar inada ya k'ara tamabayarshi ya yake jin yanayin nauyi cikin nashi da Kuma yanayin murdawar da yake masa?"amsawa ANAS yayi da cewar baya jin wani ciwo a halin yanzu dai dai Yana jin  cikin Kamar ansaka masa dutse a ciki " sorry Dr ya k'ara cewa ANAS Sanna ya ce wa sauran litocin su dauko shi su kawo masa shi office" amsawa sukayi da toh sanna ya fita " Yana fita kuwa sunayin arba da ZAINAB wacce ta taho a sukwane gaba Dr" da sauri tace Dr Yaya jikin Nasha dai?"amsawa ya sakeyi cike da kulawa yace haba ai ya ji sarki " wata ajiyar zuciya ta saki da fad'in masha Allah" kallonta yayi cikin tausayawa Dr ya k'ara da cewar ki biyoni office yanxu"toh ZAINAB tace sanna ta bashi. "

Yana shiga office din nashi itama ta shiga hadi da yin Sallama" amsawa yayi hadi da nuna mata gurin zama",, ZAINAB ta zauna tana sauraron abinda zai ce mata"Kamin ya fara bata bayanin dalilin cutar ANAS sai gashi sauran likitoci sun shigo dashi tare da yin sallama"a tare suka amsa"musu sallamar tasu"suka k'araso inda ZAINAB take zaune suka mik'o Mata ANAS din"tasa hannu ta karbeshi ta daurashi akan cinyartahadi da rumgumeshi tayi musu godiya"suka amsawa suka fita."Bayan fitar su ne Dr Shima ya dawo da hankalinshi zuwa ga ZAINAB wacce ta k'ago taji abinda Dr zaice mata akan cutar ANAS din"farawa yayi da cewar bisa bincikin da mukayi akan ciwan cikin da yaronki yakeyi, ba wani abu bane ila(Ascites) na taruwar wani ruwa a cikin shi hakan Yana faruwa ne Idan mutum ya kamu da wasu irin cuttutuka Kamar haka cutar k'ada da Saifa, da hanta,a jimalance muna Kiransu da shine(Abdominal da cavity)shine yake tara ruwa a wani 6angare na cikin mutum, Shine dalilin da yasa yaronki ya kamu daya daga cikin cuttutukan da na lisafa Miki a Fargo watau(chronic liver disease) a turance"toh wanna ita ce karshen nan bi ma'ana ciwon hanta, itace take haifar masa da wanna cowan cikin mai tsakanina Wanda ya hada har da taruwar ruwa a cikin cikin shi, toh Kinga yana da kyau a bashi jinya ta musamma mai domin tarar ciwon da wuri  sabida Kar yazo yana samun damuwar da tafi wacce yake ciki a halin yanzu"ya daga Kanshi yana kallon ZAINAB wacce tuni ta gama kid'imewa da bayanin da yayi mata"wata irin ajiyar zuciya ZAINAB ta saki sannan tacewa Dr duk na gane bayabinka sai dai na karshen ne bangane da kace jinya ta musamma"eh Dr yace abinda nake nufi shine zaku zauna anan dashi domin bashi kulawar da tace"murmushin karfin hali ZAINAB tayi da cewar Dr Kamar yaya? " Amsawa Dr yayi da cewar eh Ina nufi Idan kina da sarari sai mu baku gado anan domin yayi jinyarshi Koda kuwa ta kwana biyu ce, Idan Kuma babu sai na rubuta miki ganin da duk ya dace yasha tare da dokinkin da za'a kikaye"amsawa ZAINAB tayi da cewar gskiya Dr banida sararin da zan biya kudin d'akin da za'akatar damu domin bashi jinyar ta musamam sai da a rubutamin maganin da kuma gayamin dokokin da zanbi domin bashi Kariya " Dr ya fuskanci iyar gaskiyar ZAINAB Kenan wanna dalilin ne yasa ya janyo katin ANAS ya rubuta mata magani yace taje pharmacy ta sayo su ta dawo" kar6ar katin tayi hadi da godiya ta dauki ANAS din ta fita." ko dar ZAINAB bataji ba wajan tunkarar pharmacy da yake cikin asibiti tana zuwa ta mik'a musu Kamin " suka karba tun Kamin su hado mata magungunan suka gaya mata kudin da batayi tsamani ba, domin kuwa ce mata sukayi kudin ya kama 15k Ina magani da allurori da aka rubutu" wani irin Jeri ZAINAB taji yana shirin damk'arshi, da kyar ta samu ta iya bude baki tayi musu bayanin cewar ita fa iya 6k ne a jikinta sai d'ari biyu da ta rage mata zata hau adaidaita sahu ya mayar da ita gida, dan haka ta roki alfarmar su Bata Wanda zaifi muhammanci subar sauran ta Saya daga baya " nuna mata sukayi da cewar ko wanne mai amafani ne, dan haka ta ciko kudi su Bata magani kawar shine yafi sauki" magiya ZAINAB ta shiga yi musu da cewar su fuskanci halin da take ciki ita da yaron duk duniya iya abin da take dashi Kenan " ganin magiyar tata tayi yawa yasa dole suka bata iya na kudin ta suka rabu da ita" karba tayi taimusu godiya ta juya ta koma office din likita sagale da ANAS a kafad'arta. "tana shiga tayi sallama" Dr ya amsa hadi da dakatar da rubuce2 da yakeyi ya kalleta da cewar kin dawn? "ZAINAB ta amsa da cewar eh nadawo ga magungunan ta mik'a masa" yasa hannu ya kar6a hadi da cewa ta zauna bayan ta zauna ya cirosu daya bayan daya, sanna ya d'ari ido ya Kalleta da cewar ai basu cikaba"sosa k'aya ZAINAB tayi da cewar eh Dr wallahi duk kudin hannuna sun k'arene shine nace su bamu iya wadan nan daga baya Idan na samu sai da sayi wadan da ban Saya ba " kallonta yayi da cewar haba madam ya kike saka wasa a cikin al'amuran ciwon yaron nan naki ai nagaya miki ba cuta ce Kamar saurancuttutuka ba yana da kyau Idan anyi muku bayani ciwo toh ku tsaya ku hankanta ku kuma yak'i cutar ta hanyar shawarrarin likita da sayan maganin da aka rubuta muku, ganin halin da kike cikine yasa ban bari an rubuta miki duk wani kudin gwaje2 ba amman yanzu kuma ga magani yana neman gagara ki Saya gabaki daya"murumushi karfin hali ZAINAB ta k'akaro da cewar Dr nima nasal kayi naka kokarin kuma nagode!! Amman yana da kyau ka fuskanceni wallahi banida sararin Sayan maganin duk kansun wannna shine dalili"amsawa Dr Yaya da cewar Ok amman yana da kyau kayi kokarin samun kudin da zaki sayi sauran kamin nan da kwanan uku ace suma sauran ya fara amfani dasu, Kamin lkc da zaki dawo mana dashi muga yadda jinkin nashi Yaya idan har ruwan da ya taru a cikin nashi bai tsiyaye ba ta hanayar shan maganin da aka rubuta muku toh sai ta kai ga matakin zuke Masashi da na'ura ta hanyar yi masa aiki na mustafa, Shima kuma ba abune mai sauki ba, shi yasa nake mai baki shawarar da ki gaggauta sayan sauran magaungunan kamin lkc dawowarmu Yayi nan da sati uku masu zuwa"jinjina Kai kawai ZAINAB ta shiga da tayi bayanin da Dr yayi mata tace toh insha Allah za'a Saya ta amsahi maganin hadi da yi masa godiya ta fita....... 


~AMENTA KABER KIRU~






*KARUWAR GIDA*


*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*



*SADAUKARWA GA:*

*_HAJIYA ZALIHA_*

*_YOLA(MMN AHMED)_*


*_KUNA BAWA ZUCIYATA SHAUKI A KODA YAUSHE_*

*_AMENA SALES, UMMU USANAISA_*



*13*


Tana fitowa ta tare dan mashin din adaidaita sahun da zai mayar da ita gida."



Shi kuwa RABI'U yana ta bacci a d'akin JAMCY sai ji yayi tana zungurar kafarshi" a gigice ya tashi duk ya shar6a da gumi ya kalli JAMCY da jajayen idanunshi da cewar wai dan Allah bazaki barni nayi bacci ba Kenan!!"kalloshi tayi a wulak'ance da cewar ai kuwa bazakayi bacci cikin jin dadi ba a yau Kam, domin ai nasanar kama cewar Ina son zanyi gyaran d'akin nan tun wanccan watan amman kayi shiru dani matuk'ar baza bani  kudin da na buk'aci kabani ba,toh wallahi zan dauki mumaman mataki na hanaka shigomin daki gaskiya"jin hakan daRABI'U yayi yasa ya k'arayin ya zaro kudi a aljihunshi na gefe da cewar wallahi banida abinda ya wuce 35k din kud duk duniya nace ki kar6i wannna din da zarar na samu zan cika miki sauran a sati nan"murguda baki tayi Wanda ta cikashi da cingum tace haba Kai kuwa ta Yaya zan yadda na kar6i 35k bayan hidimar da zanyi ta zarta Hakan ka duba ko(AC) kad'e a nawa zan Sayota? Inason sayan kayan kallo ma ga sauran gyare2 da zanyi, kudin da nake son kashewa d'akin nan nawa ai ya tasamma 120k amman sai ka bani 35k me zan Saya dasu?"kallonta tayi da cewar ai nace kiyi hakuri zuwa k'arshen sati duk matsalar da ta kawo min rashin kudi a tsakanin nan  bata wuce ta k'arancin aiki da muke fama dashi a garejin muba amman kiyi hakuri nayi al'k'awarin baki duk kudin da kike so da zarar aiki mai tsoka ya samu" murgud'a masa baki tayi" hadi da yin far da idanunta sannan ta sunkuya ta kwashi kudin da ya ajje akan katifarta ta ta"tawuce ta dauko kwadan rufe d'akin ta Zane mukullen ta wurga masa hadin da ce masa Idan ya gama baccin nashi ya rufe mata d'akin ita zata fita " dole tana Shima ya tashi ya saka kayanshi ya shirya ya fita ya rufe mata dakinta gudun Kar ya k'arayin wani bacci da yawa ta dawo ta k'ala mishi Sharri tace bata GA wani abu nata ba, allura ta tono garma, hakance ta yasa ya bar gidan da sauri.


Yana fitowa ya tare mai mashin din adaidaita sahun bai zame ko Ina ba sai gidan Shi." yana sauka ya ciwo kudi ya biya me adaidaita kudin shi ya fada gida ko sallama babu, ganin ya shiga a fusace yasa ZAINAB tayi banza dashi Kamar bata ganshi ba, wucewa yayi d'akin ta kanshi tsaya " ZAINAB tafi mutuna biyar a waje Kamin ta shiga d'akin, tana shiga d'akin abinci RABI'U ya fara tamabayrta"amswa masa tayi da cewar banyi ba nima yanzu na dawo gidan"kallon yayi hadi da cewar Ina taje?"ko kadan ZAINAB bata ji shakkar gaya masa cewar daga asibiti take ba"mikewa yayi ya fara masifar uban me tajeyi asibiti? "masha ZAINAB tayi da cewar ai naga dad'i baya Kai mutum asibiti ANAS ne bashida lfy sosai Ina na ganka bare na nemi izininka?ko kuwa sai zafin ciwo ya kasheshi nemanka kazo gurin binne ga warshi ko"? Wani mamakine yaymamashi ji yake Kamar ba daga bakin ZAINAB wannna maganganun suke fita ba"daga mata tsawa yayi hadi da daga mata hannun tayi masa shiru"ko kadan ZAINAB bata razana da tsawar tashi ba bare ta fasa gaya masa duk abinda yake bakinta " Shi kanshi yasha mamakin ZAINAB din daga a wannna ranar domin jar barazanar dukanta yaso yayi amman yaga ta dake taki ko motsi daga inda take tsaya wanna ne yasav ya kama borin Kunya yayi hadi da cewar duk abinda zata fada bazai saiwa ANAS magani ba sai dai taje gurin Wanda ya bata shawarrar zuwa asibiti yabata"amsaa tayi cikin sarkewar murya da cewar Ina addu'ar Allah ya ganar da Kai, ya nisanta 'yarana da fadawa cikin jarabawar ubangiji a dalilin ka!!"kwafa yayi da cewar ke dan uwarki ni kike was fatan jarabawar ubangiji ta sameku! !? kanta ya  Karayi da niyyar zai daketa amman yaga tayi sauri ta fito ta nufi keching ta dauko tabarya itama"ganin haka yasa RABI'U ya kyale ZAINAB ba tare da ya daketa ba ya fice ya bar mata gidan."



Ganin ya fita ne yasa ZAINAB ta koma keching ta mayar da tabaryar hannuta ta koma d'akin ta ta tasa ANAS gaba tana ta faman Kuka" Shi kuwa ya samu yin bacci abinshi"fadawa duniya tunanin Ina zata Sami kudin da zatayiwa ANAS magani!! domin kuwa babu wani gurin da take ganin zata of samu tallafi a yanzu, haka ta zauna tana ta faman Kuka domin a ranar ta k'ara ganin muhimmnaci marigayiya RUKAIYYA a ranar ZAINAB tayi Kuka Kamar ranta zai fita domin kuwa tasan da Allah yasa tana raye babu wani abu da zai gagara akan ANAS sai inda k'arfinta ya k'are"goge hawayenta ZAINAB tayi ta mike ta saka hijab dinta ta shiga gidan makwafciyar ta watau SAMIRA tayi sallama" SAMIRA ta amsa"k'ara rok'ata tayi da ta bata aron wayarta"komawa SAMIRA tayi falonta ta dauko wayar ta mik'awa ZAINAB " ta kar6a tayi da cewar dan Allah ko Zaki ganemin lambar da nakira kwanakin baya?" kar6a wayar SAMIRA tayi ta lalubo mata lambar Sanna ta sake Mika mata" ZAINAB ta Karba ta tura kira wayar HAFSAT bugu daya tayi HAFSAT ta daga kiran ZAINAB tayi sallama" HAFSAT ta amsa da cewar waye? "ZAINAB ta amsa da cewar k'awata nice ZAINAB ABDUL ce" dariya HAFSAT tayi da cewar oh ZAINAB gabaka zakicemin!!"dariya ZAINAB ta sakeyi da cewar toh naji ba wanna ba Ina son zuwa gidanki gobe ko zan sameki? "amsawa HAFSAT tayi da cewar eh da dai Ina son fita amman tunda kince zaki zo sai na fasa bakida damuwa kizo kanki tsaye kawata Ina farin cikin sauraronki" murmushi ZAINAB tayi da cewar nagode da bani lkc da zakiyi nima" amsawa tayi da karki damu ai kayan mu a hade suke""dariya ZAINAB ta k'arayi da cewar toh sai nazo din"amsawa HAFSAT tayi da cewar OK " daga karshe dai ZAINAB ta yanke wayar itama" ta mik'awa SAMIRA wayarta tayi mata godiya ta juya ta koma gida. "


Shi kuwa RABI'U tunda ya baro gida Bai zame ko Ina ba sai garejin su duk da yammar da tayi haka ya tafi ya zauna yana jiran tsammanin ta Ina aiki zai bullo ya Sami na kalaci tunda ya dandak'awa kare ciyawa da wancan kudin na hannu shi." Kashe garin ranar ZAINAB ta shirya da wuri haka ta shirya MARIYA da ANAS tai basu abin Kari, bayan sun gama ta tattare magungunan ANAS ta zuba a leda ta shiga gidan SAMIRA makwafciyar ta ta sanar mata da hali da take ciki amman dan Allah kar ta gaji ta da ajiyar yaran da take kawo mata zataje neman rance kudin da zata sayawa ANAS sauran magungunashi"amsawa SAMIRA tayi da cewar babu komai ai d'a na kowa ne"asarari ta baiyana tausayinta ga ZAINAB, Sanna ta sake amsawa da cewar toh ki kawosu mana ai babu inda zanje"toh ZAINAB tace Sanna ta juya ta koma gida ta rungumo ANAS ta fito dashi MARIYA na biye da ita a baya suka sake shiga gidan SAMIRA ta nuna mata yards zata bawa ANAS magani Idan lkc bashi yayi",amsawa SAMIRA tayi da toh Allah yasa adace sai kin dawo" ZAINAB amsa da amen ta fita." Tana fita ta tare mai adaidaita sahu tahau sai unguwar hotoro watau gidan HAFSAT"tunda mai mashin ya sauketa dai2 inda HAFSAT din tayi mata  kwanan ta gane gidan HAFSAT ba tare da ta tambayi kowa ba. Tana k'arasawa jikin get din gida ta Kwan kwankwasa bata fi mutu uku da tsaiwa HAFSAT ta tazo ta bude mata gidan " tana ganin sanye da kananun Kaya tiri kwatan Wanda ne a jikin HAFSAT da yar k'aramar riga ta daure gashin kanta da ribars kalar kayan jikin nata" da sauri ta k'akaro ta rungume ZAINAB ta saki ihu da cewar kisan Allah ban zata Zaki zo tun yanzu ba" kallota ZAINAB tayi da cewar ko? " eh HAFSAT tace da cewar ai na dauko sai yamma" murumshi ZAINAB tayi da cewar Idan na bari sai yamma kika gaji da jirana kika fita fa? Ai Kinga nayiwa kaina domin nazo da magana mai kauri a bakina"kallonta HAFSAT tayi da cewar toh mu shiga cikin gidan mana, ai samu tattuna maganar taki" jerawa sukayi suna hira irin tasu ta k'awaye har suka isa falon HAFSAT"dan matsaikaci ne ba mai girma ba Wanda ta cikashi da kayan alarm hadi da baibayeshi turaruka masu tashi kanshi mai kwantar da hankali"zama ZAINAB tayi a daya daga cikin kujerun da suke falon"bayan ta zauna ne HAFSAT ta gabatar mata da lemuka kala2 hadi da kayan lashe2 dana tande2,duk dai bayan ta gama taba ko wanna, daga ciki HAFSAT tazo ta dauke faranti da ta kawo wa ZAINAB kayan lemukan ta mayar ta dawo ta zauna kusa da ZAINAB ta mayar da hankalinta tace kawata Idan kin natsa Ina sauraronki naji maganar da kikazo da ita Allah yasa alkairi" Kashe garin ranar ZAINAB ta shirya da wuri haka ta shirya MARIYA da ANAS tai basu abin Kari, bayan sun gama ta tattare magungunan ANAS ta zuba a leda ta shiga gidan SAMIRA makwafciyar ta ta sanar mata da hali da take ciki amman dan Allah kar ta gaji ta da ajiyar yaran da take kawo mata zataje neman rance kudin da zata sayawa ANAS sauran magungunashi"amsawa SAMIRA tayi da cewar babu komai ai d'a na kowa ne"asarari ta baiyana tausayinta ga ZAINAB, Sanna ta sake amsawa da cewar toh ki kawosu mana ai babu inda zanje"toh ZAINAB tace Sanna ta juya ta koma gida ta rungumo ANAS ta fito dashi MARIYA na biye da ita a baya suka sake shiga gidan SAMIRA ta nuna mata yards zata bawa ANAS magani Idan lkc bashi yayi",amsawa SAMIRA tayi da toh Allah yasa adace sai kin dawo" ZAINAB amsa da amen ta fita." Tana fita ta tare mai adaidaita sahu tahau sai unguwar hotoro watau gidan HAFSAT"tunda mai mashin ya sauketa dai2 inda HAFSAT din tayi mata  kwanan ta gane gidan HAFSAT ba tare da ta tambayi kowa ba. Tana k'arasawa jikin get din gida ta Kwan kwankwasa bata fi mutu uku da tsaiwa HAFSAT ta tazo ta bude mata gidan " tana ganin sanye da kananun Kaya tiri kwatan Wanda ne a jikin HAFSAT da yar k'aramar riga ta daure gashin kanta da ribars kalar kayan jikin nata" da sauri ta k'akaro ta rungume ZAINAB ta saki ihu da cewar kisan Allah ban zata Zaki zo tun yanzu ba" kallota ZAINAB tayi da cewar ko? " eh HAFSAT tace da cewar ai na dauko sai yamma" murumshi ZAINAB tayi da cewar Idan na bari sai yamma kika gaji da jirana kika fita fa? Ai Kinga nayiwa kaina domin nazo da magana mai kauri a bakina"kallonta HAFSAT tayi da cewar toh mu shiga cikin gidan mana, ai samu tattuna maganar taki" jerawa sukayi suna hira irin tasu ta k'awaye har suka isa falon HAFSAT"dan matsaikaci ne ba mai girma ba Wanda ta cikashi da kayan alarm hadi da baibayeshi turaruka masu tashi kanshi mai kwantar da hankali"zama ZAINAB tayi a daya daga cikin kujerun da suke falon"bayan ta zauna ne HAFSAT ta gabatar mata da lemuka kala2 hadi da kayan lashe2 dana tande2,duk dai bayan ta gama taba ko wanna, daga ciki HAFSAT tazo ta dauke faranti da ta kawo wa ZAINAB kayan lemukan ta mayar ta dawo ta zauna kusa da ZAINAB ta mayar da hankalinta tace kawata Idan kin natsa Ina sauraronki naji maganar da kikazo da ita Allah yasa alkairi" amsawa ZAINAB tayi da cewar alkairine kawata"kallonta HAFSAT yayi da cewar Ina jinki"gyara zama ZAINAB tayi ta fara bawa HAFSAT lbr abinda ya faru da ita bayan barowarta gidanta ta numa mata kuma a shirye take da dauki shawarar da ta bata a baya domin tana ganin babu Wata mafitar da ta wuce hakan".............. 



~AMENAT KABER KIRU~







*KARUWAR GIDA*


*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*



*SADAUKARWA GA:*

*_HAJIYA ZALIHA YOLA (MMN AHMED_*



*_yar tuna tarwa kadan, akan masu sharshin yadda akayi ZAINAB zata zama karuwar gida, toh mu koma ga adding, fadi (manzon tsira, s. a. w) ne da cewar mu nisanci zinah, domin ita mugun aiki ce kuma musiface ga al'umma, domin duk Wanda yayi da yar wani shima za'ayi da tashi haka uwar wani ko matar wani,koda da kantargar gidan wani kaje ka fake ka aikata hakan toh sai anyi da taka!! yana da kyau muyi kallon tsanaki ga ZAINAB ba laifinta bane, jaza mata akayi, ba kowa bane face RABI'U_*


~*KWARZANTA GWARZUWATA MARYAM OBAM*~

              *up*

*Up*

_*my daughter MARYAM OBAM Allah ya kara hasken kwakwalwa da hange hadi da basira da hazak'a a ke har da zalak'a, na tayaki murna kammala book dinki da kikayi mai suna bariki na fito, fatan mu Allah ya kara daukakaki yasa abinda kika rubuta duniya ta amfana dashi. Sai mun sake jin ki a book dinki na gaba💃🕺*_

        *UP*

                  *UP*

_*AMANAR JIDDA USMAN DA ASIHA BAGUDU🚴‍♀*_


*14*


Da sauri HAFSAT ta rugumo ZAINAB da cewar yaushe kikayi tunanin zama karuwar gidan kuma!!? Ai daman nasan zakizo gareni Koda ba yanzu ba kawata dalili kuwa nasan yau da gobe taki wasa haka zalika babu wayaiye a mutane sai wanda ya  fuskantar matsalarshi da sauri kuma ya maganceta ba tare da shiga tashi hankali ba, tun farko kikayi sake domin kuwa a yanzu babu wani wanda zai jure taimakonka, sai wanda yake da rabon samun lada gurin Allah"duba da yadda zuminci ya lalace ai ni matsalar da na shiga bata Kai taki ba amman gani kowa ya juyamin baya yasa na dauki matakin magance matsalata da kaina abinda nake ta faman nuna miki Kenan kika k'i fuskanta ta sai yanzu da kikaga uwar bari!""wani dogon nufashi ZAINAB taja hadi da tambayar HAFSAT yadda za'ayi ta shigo gari itama?" murmushi HAFSAT tayi da cewar ai shigowarki gari nauyi hakan a wuyana yake domin kuwa ni zan nuna miki yadda ake shiga gari, haba ZAINAB ai ko badan matsalar kudi kya shiga gari, dan kisan dadi d'a namiji wanda zai ciki lungu da sak'o, ko gan rage kaifin shawa'a ai kya nemi namiji, duk da yanxu mata ne suke cin maza dalili kuwa su kansu maza suna suka tara " domin kuwa majority su sun sami damuwa a dalilin yawan shiga gwagwarmayar rayuwa ga uwa uba cin kayan maik'o ko likitoci sunyi binciken Kan hakan shine ma suka fitar da cewar abinda yake bawa maza damuwa bai wuce(hire amount of protein)" Kinga yanzu mune da sama watau kici namiji kuma yabaki kudi"murmushi ZAINAB tayi da cewar ai duk na fashinta nidai yanzu ki sani a hanya domin wallahi ina da damuwoyi masu yawa a tare dani" kirki damu HAFSAT ta cewa ZAINAB ta kara da cewar ai ni zan dauki nauyi komai ko dan gurzawa RABI'U takaici" amsawa ZAINAB tayi da cewar ta yaya? "murmushi HAFSAT ta karayi da cewar Idan mashayi giya yaje gurin sayarwa randa  bai da kudi ya ake masa?" hmmmm ZAINAB tace da farko sannan ta k'ara da cewar karo2 ake masa har sai yasha ta isheshi"toh ashe kin gane Kenan kawata kema yanzu abinda zan miki Kenan har sai kinci bura kin gaji da ita"bude ido ZAINAB tayi da cewar toh fa!! ta ina zan samu?" dariyar mugunta HAFSAT tayi da cewar ai kinzo inda cutarki zata wake, yanxu dai nawa kike so kudin maganin ANAS?"amsawa ZAINAB tayi da cewar saura 14k sune nake buk'ata Kade " tashi HAFSAT tayi ta shiga bedroom dinta ta dauko damin kudi ta zube a gaban ZAINAB ta wari wasu daga ta mik'a mata da cewar kudin maganin ANAS kenan" ta k'ara waro wasu ta sake mik'awa ZAINAB tace ki rikesu a hannu su kuma"karba kudin ZAINAB tayi baki na ruwa hadi da magyagya6a na ganin irin mahaukatan kudin da HAFSAT ta bata ne yasata rudewa har ta rasa ta ina zata fara gode mata!! "rawar baki ZAINAB ta shiga you tana godewa HAFSAT din" amsawa tayi da Kai haba tsakanina mu babu godiya ai"ta cigaba da lissafa kudaden da suke a hannuta tana ware wasu daga ciki gefenta" fuskantar rudewar da ZAINAB tayi ne yasa HAFSAT ta aje kudin hannuta ta fara tafi da cewar yaro nemi kudi tun abin saye bai zo ba,  hadi da sakarwa ZAINAB dariyar mugunta tace ai nayi makinki a ranar da nayi miki tayin harkar nan kika k'i Kar6a" dariyar ZAINAB din itam tayi da cewar ai yanzu gani gurfane a gabanki na kawo kaina" kalloshi tayi da cewar shakka babu na shaida hakan dan haka yanzu abinda yarage miki shine kibayar da Kai bori ya hau"amswa ZAINAB tayi da cewar ai tun dazu na bayar, yanzu wuka da nama duk naki ne" dariya HAFSAT tayi da cewar ai ba'a bori da sanyi jiki, kinga wanna kudin da na baki na daga baya ai dasu ne zama zuba jarin mu"mamakine ya kama ZAINAB da cewar jarifa kikace!! ?" Amsawa HAFSAT tayi da cewar kwarai Kuna ai Idan naso a tuno mijici daga raminshi sai an mishi turamin magani, toh suma maza macizai ne sai da hayaki dole sai an baki wani sarrin d'aki wanda Zaki fara dashi Kamin ki fada fagen dagar yana da kyau kisan wani abu dangane da karuwancin gida" maganar gaskiya dole Idan kina son shiga wannna harkar sai kin koyi rike sirrin Kanki da na abokin harkarki abu na farko Kenan, sai maganar iya furta kalamin, hadi da iya hila da yiwa maza dadin baki, (domin kuwa hausawa sunce magana iya wace)sai uwa uba shine gyaran jiki da iya kwanciya"kasa kunne ZAINAB tayi tana jin HAFSAT domin kuwa duk abinda ta lissafa bata iya ko wannne daga ciki ba" Kamar HAFSAT ta shiga zuciyar ZAINAB ta katse mata tunina da cewar da wuya ko?"amsawa ZAINAB tayi da cewar a'a kawai dai ina tunanin ta Ina duk zan zama hakan?"dariya HAFSAT ta sake sakarwa ZAINAB da cewar ke k'awata duk fa macen da kika gani tana da irin baiwar da Allah ya hore mata sai dai ita ta kasa gane hakan, amman yana da kyau ki lura ki gano taki sai ki k'ara da ta wani ma ki mori duniyar ki tun lkc bai Kure miki ba" maganar gaskiya ZAINAB kedin mace ce rashin samun kulawa ce tasa kike ganin Kanki Kamar bakai mace ba amman zaki gane hakan da zarar time yayi" dariya ZAINAB ta saki da cewar Allah k'awata?"amsa mata HAFSAT tayi da cewar da gaske" yanxu dai mu fara da maganar abubuwan da zakiyi amfani da su domin jininki ya sauko"toh ZAINAB tace hadi da cewar Ina jinki"abu na farko shine ki sami waken suyar ki mai kyau da tsafta ki ajjeshi kullum ki dinga dibar dan kad'an kina markad'awa kina yin madararshi kina Sha zakisha maman, Sanna ki dinga yawan yin shayin zogale da yawan cikin kwakwamba da kuli_kuli tana cikowa da mace gabanta, Sanna ki ringa markad'a kwakwambar da kankana kina Sha da madara Koda yaushe Zaki Sha mamaki, dalilin da yasa na baki wannna kudin Kenan nace ki rik'esu a hannuki,sai abu na gama shine ki zama ma'abociyar amfani da kannufari wajan tafashi da yin tsarki dashi haka da zubawashi a bakinki koda yaushe yana kawar da cuttutukan baki hadi da bayar da kanshi ga bakin MA, sannan ki yawaita yin lalle a kafarki hadi da wanka da ruwan shi ki dan dinga zuba madarar turare a ciki, yana k'arawa mace danshin jiki da bata Kariya mara iyaka sai magana ta haba shine ki yawaita amfani da turaruka masu kyau wajan shafawa jikin ki."amsawa ZAINAB tayi da cewar nagode da shawararki gareni kuma duk zanyi insha Allah sai maganar da kikayi ta iya kwanciya itace ta dan sani a duhu"murmushi HAFSAT tayi da cewar kar ki damu ai ba gudu akeyi ba yanzu dai tashi muje wani guri mu dawo"toh ZAINAB tace hadi da mik'awa"itama HAFSAT mik'ewar tayi ta kuma shiga bedroom dinta ta sake wasu kayan hadi da daukar mukullin Mozart, sannan ta kalli ZAINAB da cewar muje ko."............ 



~AMENAT KABER KIRU~







*KARUWAR GIDA*


*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*



*SADAUKARWA GA:*

*_HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMED)_*



*15*



Amsawa ZAINAB tayi da toh" suka fita  HAFSAT ta wuce gab ta bude get sannan ta dawo ta bude wa ZAINAB gaban motar ta shiga, itama ta koma nata 6angaren ta bude ta shiga" ita tuka su zuwa wajen get din sanannta fitar da motar ta dawo ta rufe get din ta suka tafi."Da wani katafaren gurin shoping suka fara zuwa HAFSAT tayi parking a harabar gurin suka fito daga motar a tare, HAFSAT na gaba ZAINAB na biye da ita a baya haka suka shiga ciki" bayan shigarsu ne suka wuce guri da aka jera turarukan jiki da na wanka hakaHAFSAT ta ringa za6a tana zubawa a kwando, bayan da ta gama za6a tazo Kan kanatar kantin ta mik'awa Wanda yake kuwa da baggage aka lissafa mata kudinsu take tabiya su kudadensu aka zuba matasu a leda wacce take dauke da tamabarin kanti" ta Karba suka fito ta k'ara jan motarta sai sabon gari market, shagon wani mashahurin masanin fatar dan Adam tanufa" zuwa tayi ta sake yin parking da motar ta a gaban Shagon ta fito hadi da yiwa ZAINAB Jago Ranch tana tafe ZAINAB din na biye da ita Kamar rakumi da Ayala suka shiga."Suna shiga cikin Shagon Kai tsaye HAFSAT ta nufi gurin shugaban shagon baki daya watau NATO ta sami kujerar da take gefeshi suka zauna suna jiran ya sallami wacce suka tarar yana yiwa bayani yadda zatayi da Maya-mayan da ya hada mata" bayan ya sallemata ya dawo da hankalinshi Kan su ZAINAB da cewar HAJIYA HAFSAT barka da zuwa Ina fatan dai lfy da na ganki a wannna lkc? Domin nasan ba a irin wanna time din kike saba zuwa"amsawa tayi da cewar lfy lau OGA NATO" amsawa yayi da OK" HAFSAT ta k'ara da cewar na kawo k'awata ne ka hadamin ita"kallon ZAINAB ya k'arayi da cewar barkan ki da zuwa HAJIYA"  amsawa tayi da cewar barka ka dai" tamabayar ta yayi da cewar Kamar me kike buk'ata dan gane da gyaran jiki?" rasa amsar da zata bashi ZAINAB tayi domin bata masaniyar abinda yake nufi" shine dalilin da yasa ta kalli HAFSAT da cewar kinaji fa k'awata!!"dariya HAFSAT tayi da cewar lamarine irin na OGA NATO banda haka ai ni yakamata ya tambaya yaji yadda za'ayi domin kuwa ni na rakoki"dariya yayi da cewar oh HAJIYA HAFSAT kenan dad'ina dake gajan hakuri ai naga itace za'ayiwa aikin nan ba keba" ya k'ara da cewar idan tana jin yunwa kece kike jiyemata? ko ita take ji acikinta?"dariya HAFSAT tayi da cewar a'a amman ai al'amarin bana jin yunwa bane, OGA NATO amman kaji hausa da yawafa zama cika tararka"dariya yayi da cewar kaina bisa wuyana yanxu dai muyi maganar abinda za'ayi mata ko?domin mutane na jinana" amsawa HAFSAT tayi da cewar ba wani abu mai wahala nake son ayi mata ba face gyaran fata shine dalilin zuwan mu nan" amsawa yayi da OK babu damuwa Ina zuwa" ya tashi yayi ya dauko wata roba karama wacce take dauke da wani irin sinadari ruwa a ciki mai kama da man gyad'a hadi da yago audugar ta take Kan tebir dinshi ya dangwalo sinadari da ita sannan ya kalli ZAINAB da cewar mik'ashi hannuta ya gani" toh tace masa hadi mika masa hannu nata"ya goga mata sinadari a hannu sannan yace ta bar hannu a haka kar ta ta6a"ya koma ya zauna hadi da zolayar HAFSAT da cewar HAJIYA kunyi kudi kun huta"dariya tayi da cewar ai kune silar samun kudin name OGA NATO domin kune silar komai " dariya yayi da cewar kefa bakya rabo da sharri" amsawa tayi da cewar gurinka na koya domin yanzu ka gama yiminshi"dariya yayi hadi da tasowa ya sake dawowa inda ZAINAB take zaune ya ce tabashi hannun ya duba" mika masa hannuntayi tana kallon abinda zanyi, gumin da ya tsatso a jikin hannu nata ya sake goga a jikin wata adugar ya ajje  a gefen tebir Dinah hadi da sake komawa mazaunin shi ya zauna, sannan ya dauko wata yar karamar na'ura ya saka audugar da ya gogi gumin hannun ZAINAB a ciki " yakai tsawan miti biyar yana dube2 a cikin na'ura bayan ya gama ya dago ido ya kalli su ZAINAB da cewar HAJIYA HAFSAT ai Kawarta ki batada wata matsala komai" basai anyi mata wankan inji ba abinda take buk'ata bai wuce a hada mata man da zai k'arawa fatarta sheki da santsi ba " amsawa HAFSAT tayi da cewar babu damuwa kayi duk abinda ya dace shi yasa ai na kawo ta gareka domin masan duk fadi kasuwar nan banida kamar ka" dariya yayi da cewar nasan da hakan Hajajo" dariya HAFSAT tayi da cewar sai magana ta gaba za'a yashe mata kaushin fuska da na kafa hadi da wankin hakora" ok NATO yacewa HAFSAT."Sannan ya tashi hadowa ZAINAB man da zata ringa amfani da shi wajan shafawa kulu Idan wanka" bayan ya gama ya kawo musu ya mikawa HAFSAT da cewar gashi HAJIYA tunda kece kibayar da 15k Kwai" "Karba tayi hadi da yi masa godiya ta bude jakar hannuta ta mik'a masa kudin" yasa hannu ya kar6a"asarari ZAINAB ta nuna mamakinta ganin yadda HAFSAT ta biya kudin man da bai wuce kalbar k'aramin verselin din da bai wuce girman 250mg ba amman shine ta bayar da 15k ashe abin bana wasa bane!!" Yankewa ZAINAB tunanin HAFSAT tayi da cewar muje can 6angaren za'ayi miki wanki hakora dana yashe kaushi"toh kawai ZAINAB tace ta mike ta sake binsu HAFSAT a baya tana kalle2 yadda gurin yake ashe Kato ne babu abinda ba'ayi na gyaran jiki hatta yankan farce kafa da gyaran shi da take ganin shi karamin abu akwai 6anrenshi a gurin." Gurin zama NATO ya sake basu sannan ya Kara tafiya gurin wata katuwar kanta ya debo kayan aiki sannan ya bude wani dogon glas mai kama da akwaku ya cewar ZAINAB ta shiga da yashe kaushi ya fara tunda daga na fuskanceni har na k'afafuwanta bayan ya gama ya wanke mata hakora"ya bude murfin glas din ya fito ya juya da sauri  ya debo wasu samfulan maya_mayai ya mik'awa HAFSAT da cedar sune wanda ZAINAB zata ringa amfani dasu a kafa da fuska da daddare kamin ta kwanta, hadi da bata wani turare na daban wanda yake hadi da man wanki baki yace shima ta ringa wanke bakinta dashi, turaren shima ta ringa fesawa abakinta" kar6a HAFSAT ta sakeyi hadi da yabawa da aikin da yayiwa k'awata ta cikin karamin lkc" tamabayar shi kudin aikin HAFSAT tasakeyi da cewar wannna aikin fa nawa zan biya? "amsawa NATO ya sakeyi da cewar kibayar da 10k duk da Kaya sun tashi amman ki bayar hakan" sake zuge jaka HAFSAT tayi ta debo kudinsa ta mika mishi hadi da yi masa godiya" ya amsa da babu komai ai ana tare"ya juya ya shiga wani k'araminfi d'akin da yake gefenshi su."ita kuwa ZAINAB da take zaune cikin glass din  mamakin 6arin kudins da HAFSAT takeyi akanta ne ya k'ara kamata!!"Bayan Kamar miti bayar NATO ya fito daga d'akin da yashiga hannushi dauke da wasu tab da syrup da wata injection ya kalli ZAINAB yace ta fito daga cikin glass din da take ciki"  amsawa ZAINAB tayi da toh" sannan ta bude murfin glass din ta fito tazo dinga yake tsaye tace gani"duwawunta yace ta bude zai mata allura" waigawa tayi ta kalli HAFSAT Kamar wata mara wayau"nuni HAFSAT tayi mata da hannu Kamar wata kurma alamar babu matsala"bude masa tayi hadi da kawar da kanta gefe alamar jin Kunya " Shi kuwa NATO allura yayi mata hadi da cewar kar ta likiya gurin domin idan ta liliyawa b aikin da akeso allurar tayi baza tayi mai kyau sosai ba" toh ZAINAB tace hadi da tahowa inda HAFSAT take itama ta zauna a gefenta"ko mawa cikin yayi d'akin da ya dauko allurar da yayiwa ZAINAB.


Ita kuwa  HAFSAT Kallon ZAINAB kawai takeyi domin daga k'aramin gyaran har ZAINAB ta koma kyakyawar gaske "dariya tayi da cewar lallai hausawa sunyi gaskiya da suka duk mace_mace ce sai dai Idan bata samu yadda takeso ba kin ganin kuwa!! ? Hmm abin ba'a magana wallahi ashe dai k'awartawa wutar kyauce" dariya ZAINAB tayi da cewar bana son zolaya fa kawata"gyra zama HAFSAT tayi da cewar Sam ba zolaya bace amman bari ki gani Ina zuwa"tashi tayi taje gaba kantar da NATO kayan aikinshi ta dauko k'aramin kudubi ta kawowa ZAINAB da cewar duba kiga!!"Karbar mudubin ZAINAB tayi da cewar mugani!!"tabbas maganar HAFSAT gaskiya ce babu karya domin kuwa gani tayi Kamar an sauya hallitar fusakarta, mamaki ta dinga yi da cewar Kai k'awata banida bakin gode miki a gaskiya kin fito dani dariya HAFSAT tayi da cewar ban fito da ke ba sai ranar da kikaji shigar bura a jikin ki shine zaki fito sosai"murmushi ZAINAB tayi da cewar kai k'awata bakya gudun fadan sunan wanna abar"dariya HAFSAT tayi cikin zolaya tacewa ZAINAB wacce abuce haka Kamar sunan surukar kike buyewa!?"fitowar NATO ce ta katse hirar tasu"ya kalli HAFSAT da cewar HAJIYA na gama aikina yanzu sai maganar wandannan syrup din hade da tabs dinnan yadda zatayi amfani dasu shine kullum ta ringa shan syrup din cikin murfin kwalabar sau uku haka shima tabs din sau uku zata ringa Sha a yini amman mafi ingancin shawar Idan tana son yayi amfani a jikine sosai sai ta ringa shan kunun gero komai na wani abu mai maik'o Kamar alkama da Aya, wannna maganin suna da ingancin sosai domin ban tana shigo da irinsu ba sai wannna Karon yana da kyau matuk'a tabi dokar shi, Idan tayi haka cikin kwanaki kadan duwawumta da nunukanta zasu baki mamaki sai kunzo kunyi min godiya har ku kawo wani ma duk da naga tana jin Kunya ta amman bayani ya zama dole"godiya HAFSAT tayi masa hadi da tamabayrshi kudin wannna aikin shima ta k'ara da cewar itama zata dawo ya sake yi mata irinsu"amsawa yayi da cewar karki damu shima kibayar da 15k din"ko kadan HAFSAT bataji shakkar sake mika masa wannna kudin ba" NATO shima ya Karba yayi godiya hadi da mika mata magungunan da suka a hannushi" karbar maganin tayi ta saka a jaka sukayi masa sallama suka fito.......



~AMENAT KABER KIRU~






 *KARUWAR GIDA*


*STORY WRITEEN BY✍*

*AMENAT KABER KIRU*



*SADAUKARWA GA:*

*_HAJIYA ZALIHA YOLA(MMN AHMED)_*




*BAN MANTA DA KUBA*


*_ZAHRA ASEEM AK'IL,UMMU UNAISA,SIFFINUR AISHA JAFAR, AISHA MAGAJI KD, KARUWAR GIDA FANS, TARE DA YAN HAUSA NOVEL GROUP,UBAIDA MRK, FAUZAH ABBA MA'AJI, UMMU AFRA, UMMU SADEEQ DUK NA GAISHEKU KYAUTA, INA YINKU OVE💃🕺_*




*16*




Bayan fitowarsu daga kasuwa  basu zame ko Ina ba sai gidan ZAINAB sabida lkc ya Kure musu ba tare da sun gama siyayar da zasuyi ba, gashi ta bar ANAS a gida babu lfy ga yamma ta kwace musu wannna hujjar ce tasa dole HAFSAT tadawo da ZAINAB gida" bayan faka motarta ta da tayi ta a kofar gidan ZAINAB fitowa tayi duk siyayar da tayiwa ZAINAB din daga ciki motar,ta mik'a mata wasu ita kuma ta rik'e mata wasu, suka shiga gidan a tare suna k'ara tattaunawa akan yadda zasu kamo bakin zaren a haka suka Karasa shiga ciki"ZAINAB ta bude d'ai suka shigar da kayan sannan ta HAFSAT ta sami gefen gadon ZAINAB ta ta zauna da cewar ai k'awata kwanan na zakiyi mamakin yadda jikin ki zai koma, yana da kyau ki mayar da hankaliki akan duk abinda Zaki koya daga gareni"amsawa ZAINAB da tayi da cewar ai k'awata bakida matsala dani domin kuwa ai babu guda babu ja da baya tunda har mun shigo fagen dagar"dariya HAFSAT tayi da cewar  bana jinki domin kuwa tun daga yau kin nuna min zaki iya komai domin kuwa kin bawa mara d'a Kunya"dariya itama ZAINAB tayi da cewar ba'a yabon dan kuturu dai!! har sai ya shekara arba'in da yatsu"dariya HAFSAT ta karayi da cewar ai wanna dan kuturun tun daga haihuwarsa ya nuna zai zauna lfy, kedai a juri zuwa da tulu rafi, kin kusa hadewa da i'waje"dariya ZAINAB tayi da cewar wacca kalmace haka ta k'arshen da kika fada?"kashe ido HAFSAT tayi da cewar yarenmu ne na yan bariki Idan kinji wannna kalmar dana fada toh wani abune Wanda ya shafi sirri shine muke buyewa musamman ta batsa Idan Bama son fade kowa ya gane shine muke karantata da i'waje ko muce masa ja'e ta k'arasa maganarta da kwarkwasa"dariya ZAINAB tayi da cewar toh ai naga bakinki baya haila ya akayi kika sututurta maganarki yanzu" "dariya tayi da cewar ai akwai abinda basai an fadi sunashi ba amman Kai daga jin kalmar da zata wakilce shi ka gane, ba gashi daga fad'ar hakan kema kin gane ba yanzu?"dariya ZAINAB ta karayi da cewar zan dai gane hadi da cewar toh ki Kara yimin bayanin akan kayancan da muka shigo dasu" oh HAFSAT tace sannan tace gara da kika tunanin, miko ledojin mu gani" mikowa mata ledojin ZAINAB tayi Kamar yadda ta buk'ata"budesu HAFSAT tayi daya bayan daya ta fara da magagugunan da NATO ya basu ta kalli ZAINAB wacce tayi zaman dirshen tana sauraronta tace kinga wannna kwayoyin magannin shine zai so na  nononki su cure Kamar dutse cikin yan kwanaki, wannna syrup din kuma da kika gani shine mahadin allura da NATO yayi miki domin ita amfaninta yana da ga jiki itace zata bawa k'wank'wansoki damar budewa yayi 6akeke cikin yan kwanakin shima, haka ya karawa duwawunki tudu da girma hadi da laushi Kamar kitsen da aka zuba a ruwa, abinda yasa nace haka domin ni ganauce akan hakan ba ciyau ba kuma kema kisan da ba haka nake ba " amsawa ZAINAB tayi da cewar tabbas k'awata" nisawa HAFSAT ta sake cewar toh ki kula domin kuwa duka maganin nan da kika gani basa sakawar mace k'ibar irin mai ciki da ruwa ko kod'an basu da wata matsalama dan haka sai ki daure dan Allah ki riga amfani da ko wanne kamar yadda kaka ji NATO yayi miki bayani"insha Allah ZAINAB tace hadi da sake cewar nagode" amsawa HAFSAT tayi da cewar babu komai"sai wannan turarukan na wankane da na shafawa Idan kin fito daga wankan da kuma na fesawa fatana dai kinsan ga6an da ya dace mace ta shafawa turare ko?"amsawa ZAINAB tayi da cewar a'a sai kin fada"murmushi HAFSAT tayi da cewar muhimman guraren da akafi amfani dasu wajan sex sune mafi mahimmanci mace tafi kulawa dasu wajan sama musu k'arnshi, kamar bayan kunne sabida namiji yana kai hancinsa da bakinsa nan wadan, haka k'warmin cibiya shima namiji yana Kai hancinsa da bakinsa nan wajan, haka ga6ar yuwa da k'asa nonowa da tsakankanin cinyoyi uwa uba hammata da k'warmin duwawu domin zakiga mata da yawa basu san wajan yana tara dauda da annakiya ba, yana da kyau mace koda bazatayi amfani da turare ruwaba wajan safawa matsematsinta ba, toh ta dimanci saka turare wuta a agarwashi tana tsugunawa akanshi kullum domin kanshi ya kama mata jiki,haka yana k'ara matse farjinta, dalilin dasa na tambayekuwa yana da nasaba da sakacin da matan sukeyi da gurarincan dana lissafa miki,a gaskiya na kyau ki basu kulawa gaske kawata"nisawa ZAINAB tayi da cewar lalle duniya makaranta ce ai ni bansan da wannna gurare bama wallahi nidai nayi wanka na sawa hammata ta turare kawai na sani amman duk bansan da wasu kofofin sex ba ma sai yanzu dana ji daga bakin ki, amma fa k'awata kin hadu"dariya HAFSAT tayi da cewar bazaki gane haduwata ba sai ranar da na had'aki da namijin da zai lashe miki duri"kai dan Allah k'awata ZAINAB tace da gaske ana lasar gaban mace daman?"dariya HAFSAT ta kyakyace da ita tace hmmm zaki sanine sai nan gaba" Nisawa ZAINAB tayi da hmmm Allah ya kaimu dai" HAFSAT ta amsa da amen" sannan tace sai maganar karin ni'ima domin bazai yuwu mace tasan wadancan abubauwan ba amman bata san yadda zata inganta ni'ima jikinta ba, yana da kyau mace ta dimanci shan tsumin Wanda akayishi dabino duba da yadda dabino yake da magance tutukakkan jiki da Adam,  yadda ake yin tsumin dabino kuwa shine ki nemi dabino mai kyau ki 6are cikinshi ki cire kallon ciki sai ki wake ki zuba a tukunya mai kyau sai ki sami garin sanemon ki zuba ki sami  kanunfari da citta da zuma ko mazarkwaila sai ki zuba Idan kika gama had'awa sai ki hada wuta kiyi ta dafawa har sai ya narke ya zama Kamar Kuna wanna shine tsumin dabino yana da kyau da inganci dalilin da yasa nace asaka sanemon kuwa yana magance cutttukan sanyi kuma yana hanshi tasiri a jiki ga bawa jijiyon sex Kuzari,abinda yasa naba ki, kudi masu yawa Kenan nasan zaki kashe kudi inda kinaso gyarasu mai kyau"nisawa ZAINAB ta sakeyi da cewar k'awata nagode,Ashe a zaune nake da tarin rashin sanin kaina tun tuni" amsawa HAFSAT tayi da cewar kin cika abun dariya wallahi" sai magana tagaba ki sami waken soya da alkama da aya da gayada  ki gyarasu a nika miki su ki ringa damawa Kamar koko da sauri zakiga yadda ni'imarki zata ringa fita, sai kuma ki sami "ya"yan hulbaki tafasa da kanunfari ki zuba madara da bourvita da zuma kiringa Sha Kamin kici komai zakiyi mamaki k'awata" dariya murmushi ZAINAB tayi da cewar k'awata nagode da hadimtamin da kayi uwa uba ga tarin ilimin da nasamu daga gareki"dariya tayi da cewar ba da wannna muryar nake son ki godemin ba"zaro ido ZAINAB tayi da cewar toh da wacece kalar muryar zan miki godiya!!?" "amsawa tayi da cewar irin ta mata masu class nake son ki gode min" hamm!!! ZAINAB tace lalle lamarin babbane toh ya suke mata masu class din? "dariya tayi da cewar nifa nafison naga kin hadu ta ko ina shine dalilin da yasa nake son ki kware Kamin ki shigo daga ciki!! Domin bazan so ki zama yar buyajin karuwar gida ba, nafi son naganki da manyan al'hazai 'yan birni domin sunfi bayar da fefe" dariya ZAINAB tayi da cewar bak'uwar kalma ta uku meye fefe kuma?"amsawa HAFSAT tayi da cewar kudi mana masu gidan rana wancan yarenmu ne na karuwan gida kawai " oh!! ZAINAB tace hadi da sake cewar nagane" kallonta HAFSAT tayi da cewar gaskiya k'awata sai kin chaza sosai Kamin hakan su samu domin mace mai class bata yawan dariya ga namiji Ko da abin dariyar ne yazo dan muskutawa take gefe sai tayi gajeren murmurshi ta fuske"toh ZAINAB tace kawai"ta cigaba da sauraron jawabi da HAFSAT take sake yi mata da cewar mace mai class bata kurawa namiji ido komai kyanshi da haduwarshi Idan ba haka ba sai ya raina ta, sai dai ki kallah shi kadan ki marzaye, Idan ya masa da kallonki sai ki dage girarki daya hadi da kashe idonki ta gefe da zarar yaga haka yasan kedin ta musamnace dan haka ki kula da wannna abubauwan su kansu suna bawa mace damar kiran namiji gareta musamman karuwar gida,irin wannna kallo  shine alamtawa namiji ke yar hannuce ba sai yaji daga bakinki ba, Dalili kuwa macen da zatayi karuwancin gida bai kamata ta mayar da kanta Kamar rijiyar Kan hanya ba kowa yayi mata tofin Ala tsine aka ita take zama tayi tsarin yadda zata tafiyar da harkarta cikin sauki tun daga Kan haduwarta da na mijin da taga zata iya bawa fusaka wajan mu'amalata, sabida ita tana da aure kuma bazata so kowa yasan tana karuwancin gida ba, wannna hujarce tasa zan baki sahawara kar ki taba yadda wani ko wata da kika sani ya ganki da mijin da ba naki ba, ko da kuwa a gurine, ko kuma kayi kokarin gayawa abokin harka uguwar da kike ta Sali, Idan ta kama dai zaki iya gaya masa gari Idan bak'one, amman ba kowa ake bawa fusakr hakan ba."Jinanawa ZAINAB tayi da cewar duk nagane kuma nagode" "amsawa HAFSAT tayi da cewar Kai haba dan Allah godiya bata k'arewa?ta Kara da cewar Idan kina neman shawara akan abinda baki gane ba ki tamabayeni a shirye nake na sanar miki da duk abinda kike bukata" toh ZAINAB tace insha Allah babu abinda zai shiga min duhu"amsawa HAFSAT tayi da cewar Allah ya nufa ni zan tashi haka sai gobe da yamma zan sake dawowa gareki yanxu muje naga yadda jikin ANAS yake sai na wuce daga can " toh ZAINAB tace hadi da tashi ta dauko takin asibitin ANAS tace muje nima sai ki saukeni a bakin titi na sayo masa sauran magungunan shi tunda kudi sun samu ai bana zauna ba kedai an gode miki kawata" murmurshi tayi da cewar babu damuwa muje kawai " fita sukeyi a tare suka shiga gidan SAMIRA makwafciyar ZAINAB din a daki suka tara da ita tana kallon TV ita da yaranta da su ANAS da yake kwance a daya daga cikin kujerun falonta" gaisuwa HAFSAT tayi da SAMIRA hadi da yi mata godiya bisa namiji kokarin da takeyi akan ZAINAB da yaranta " SAMIRA ta amsa da cewar babu komai amfani Zaman Kenan ai"  karasawa inda ANAS din yake kwance HAFSAT tayi ta duba shi " sannan ta cewa ZAINAB ni zan tafi gida" amsawa ZAINAB tayi da toh nagode " sannan ta kalli SAMIRA da cewar dan Allah zan bita ta saukeni a bakin titi na sayo sauran maganin ANAS na dawo" amsawa SAMIRA tayi da cewar sai kin dawo hadi da cewa HAFSAT ta gaida gida"atare suka amsa mata da toh Sannan suka fito."Bayan sun fitone HAFSAT ta Kara kallonta ZAINAB da cewar ammanfa kinyi dace makawfciya k'awata"murmushi HAFSAT tayi da cewar ai batada matsala wallahi " amsawa HAFSAT tayi da cewar toh kinga Koda ita kar kibari tasan kina wata harka bare ki gaya mata halin da kike ciki dan haka ki Iya takun ki domin karuwancin gida ba wasa bane" toh ZAINAB tacewa HAFSAT kawai OK!!! HAFSAT tace sannan ta bude musu mota suka shiga ciki suka tafi suna Kara tattaunawa da juna"suna zuwa bakin titi HAFSAT ta sami giru ta tsaya ZAINAB ta sauka hadi da yin sallama da junasu HAFSAT taja motar ta tafi, ZAINAB ta wuce ta shiga chemis ta sayowa ANAS sauran maganinshi sannan ta juya gida zuciyarta ciki da farin ciki......... 





~AMENAT KABER KIRU~



Post a Comment

0 Comments