JINNUL ASHQUI cmplt

 Compiled By Umar Dalha Funtua.





[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹JINNUL

       AASHIQUE🌹


      _NA_

_HARIRA ALIYU_ ( *Yar Fillo*)



✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to aisha a ibrahim 


*Bissmillahirrah manirrahim*


Fatan alkhairi ga kowa inafatan za ayimin hakuri abisa ga wasu kura kuran da kila zanyi


Gaisuwa da jinjina ga GOLDEN PEN WRITTERS 



 🅿AGE📕  1⃣



Gid'ane madai-daici  dayike cike taf da jama'a idan kakalli kowa zaka fuskarsa dauke da farinciki da annashuwa banda wacce akayi taron da gayyar dominta


Datake makwabta tare da kawayenta anayimata lalle


Kallo daya zakamata kagano  tashin hankali da tsananin fargaba atare da ita


Batawuce seconni batare data duba agogon wayarta ba faduwar gabanta na dada tsananta 


Babbar aminiyarta ce tafahimci halin datake ciki ta matso gab da ita tafara magana ahankali 


"Rauda please kikwantar da hankalinki banaso jama a sufahimci halin dakikeciki"


 Kai kawai Rauda tagyada ma salma dantasan bazata fahimci tashin hankalin datakecikibane

Hakanma bakaramin dauriya takeyi ba


Tanaji kawayenta nayaba kyan lallen amma takasa tankamusu 


Wata yar makarantarsuce tashigo tana sallama

Suka amsa salma nafadin"munyi fushi saiyanzu"


Tazauna kusa da rauda tana yar dariya"nabiya kasuwane salma yanzukuma danashigo layin dakyar na iya kutsowa

Jama a suncika layin tundaga farkonsa har karshensa"


Rauda tayi saurin tambayar jamila

"kinga umar?


Jamila ta girgiza kai"gaskiya ban lura ba kinsan mutanen dayawa"


Tajinjina kai tare da kara lalubar numbansa amma har lokacin akashe


Takara duba agogo karfe biyu saura  hankalinta yakara tashi


Kallon me lallen tayi tace"dan allah kitakaita lallen haka"


"To"

Me lallen tace batafi minti biyar ba kuwa tace tagama


Mikewa tayi ganin mama tashigo suka shiga dakin matar gidan dasuke lallen


Mamar ma hankalinta atashe yike 

Rauda da jikinta yagama yin sanyi ta dubi mama tanacewa

"mama wayar umar tundazu nike kira akashe kuma bana tunanin yazo gurin daurin aurannan gashi yanzu biyu dai dai"


Mama tasauke numfashi 

 Dan tama kasa cewa komai


Kasa rauda tayi dakanta hawaye na gangarowa 

"mama idan aka fasa aurannan awannan karon bansan yaya zanyi da raina ba"


Mama takara sauke numfashi tare dacewa cikin kwantar da hankali


"insha allahu ba abunda zefaru"


Zaunawa kawai tayi amma ita ta riga da ta sadakar


Mama tafice zuciyarta cike da damuwa


Salma tashigo dakin tazauna kusa da ita tana karemata kallo

"haba Rauda meyasa bazaki kwantar da hankalinki bane bakisan wannan damuwar zata iya haifarmiki da wani ciwon na dabanba"


Wasu hawayenne suka kara gangarowa cikin shesshekar kuka tace


"Salma bansan yazanyi da rayuwata ba tundazu nike kiran wayar umar batashiga,gashi yanzu biyu harta gota amma banji alamun wani nasa yazoba bare maganar daurin aure ba

 

Salma inason umar bantaba son wani kamar yadda nike sonsa ba,idan narasasa bansan yazanyi da rayuwata ba......


Takarasa  maganar cikin karyewar zuciya 


Salma tasauke ajiyar zuciya hakika itama tagama karaya amma bataso ta nunama Raudan bataso hankalin raudan yakara tashi


 Cikin karfafa gwiwa tajanyota jikinta tanadan bubbuga bayanta


"kawata kukannan ya isa haka dan allah insha allah ba abunda zefaru"


Kuka kawai takeyi me cin zuciya


  Khadija ce  tashigo dakin aguje fuskarta dauke da tsananin farinciki

 Salma tace 

"lafiya"


Cikin sauri khadija  tace

"gasu umar can sunzo  da tawagarsu"


Dasauri Rauda tamike

"dagaske khadija?


Khadija tadaga kai

"dagaske wallahi"


yaye labulen dakin tayi dasauri wanda ke fuskantar cikin layin tafara hange hangen inda zata hangosa


Daga can nesa tahangosa cikin abokanansa yasha wata purple din shadda  abunka ga fari tas


Sai shaddar ta hausa  kyawunsa yakara futowa


Kuramasa ido Rauda tayi da jikakkun idanunta 


Tanajin wani sanyi da farinciki naratsa zuciyarta


Salma tadafa kafadunta tana dan murmushi

"kinga ni ba,bagashi yazo ba amma da duk kinbi kintada hankalinki nima kin tada nawa"


  Kallon salma tayi tana yar dariya "karkiga laifina kawata kinsan yadda nike sonsa kuwa?


Dariya salma  tayi itama sai lokacin hankalinnata yakwanta

"jibeki hawaye na zubowa kina kuma dariya, kuka da dariya alokaci daya"


Hannu tasa ta goge fuskarta dasauri tarasa


Ma mezatace saboda tsananin farinciki


"salma bazaki gane bane aure biyu anafasawa dole hankalina yatashi bare umar danike sonsa kamar raina"


Murmushi salma tayi tana girgiza kai


"allah dai yasa yadda kike son umar shima yana sonki haka"


Rauda ta jingina tana lumshe idanuwanta

"aganina salma ayanzu dai babu wanda yakai umar sona

Saboda kullum maganarsa batawuce idan babu ni baze iya rayuwa"


Dariya salma takuma yi 

"lallaikam kunason junanku dayawa,amma dai kada wannan son yasa kibada kanki da ankaiki ehe


Kija aji kidan bashi wuya tukunna


Bude idanu rauda tayi tanayima salma wani irin kallo


"lallai salma bakida saiti,tunda nike aduniya bantaba yima umar musu ba


Ko bani da lafiya nakasa cin abinci idan yacemin inci sainaci kobadadi


Haka bacci ma kobanaji idan yace inyi dole nikeyi alokacin


Anguwa ma haka idan yace kar inje to ko inason zuwa fasawa nikeyi


Kekomai idan Umar yace inyi atake nikeyi bana bata lokaci


Bare kuma abunda ya dade yana muradi sai kawai in hanasa saboda wani ajin banza......



"Ya isa ya isa mamar soyayya"

Salma tafada tana mikewa 

Sannan tacigaba  dacewa


Yanzu nasan ko rijiya Umar yace kifada fadawa zakiyi wannan soyayyar taki tayi yawa wallahi


Dariya Rauda tayi

"najidai koma mezakice dan haka kigayawa wa'ancan

(sauran kawayen)

Dannaji suna zancen kwana babu wacce zata kwananmin agida"


Baki Rauda tarike

"eyyeh lallaima Rauda yazune bakinki yabude ko?


Amma dazu ko ihin kasa furtawa kikayi

To kwana ko zamuyi yazama dole"


Waro idanu Rauda tayi tanajin kamar mafarki takeyi

Yayinda taji ana sanarwa


"andaura auran umar da Rauda bisa ga sadaki naira dubu dari


Cinta,shanta,suturarta duk sunkoma kan umar 


Jama a sunshaida 

Fatiha


Runkunkume salma tayi tanfadin

"kinji abunda kunnuwa na sukaji salma"


Salma tadaga kai

"naji andaura auran Rauda da umar"


Durkushewa Rauda tayi,tayi sujada ga ubangiji 

Tana fadin allah nagodemaka allah nagodemaka


Wayarta tafara kara tadago ahankali tana duban wayar


Salma tamikamata wayar tanufi hanyar fita tana cewa


"kinga bari naje muciga da shirye shirye tunda dai allah ya yadda"


Kallon wayar tayi ganin numban umar yasa tadauka

 

Cikin tattausar muryarsa mesata  natsuwa aduk sanda tajita yace


"madam yadai"


Fashewa tayi da kuka wanda batasan ko namenene bane


"haba madam kukan kuma namene?

Yatambaya yana sassauta muryarsa


Cikin kukan tace

"yau tunda natashi nike  kiranka amma wayarka akashe kasa hankalina yatashi...


Yakatseta"haba honey,kema kinsan hakanan dai bazan kashe wayata ba


Kinsan hidimar bikinnan jiya agajiye nakoma gida dasafe kuma  mutanene suka addabeni da kira 


Shiyasa nakashe"


Numfashi tasauke


"kasani cikin fargaba da tsoro bazan iya kwatantamaka tashin hankalin dashiga ba"


Murmushi yayi wanda tajiyo sautinsa 

"kiyi hakuri bama jina kadai ba yanzu gabadayana nazama naki

Mallakinki ke kadai


Murmushi ya subucemata zuciyarta har harbawa takeyi saboda tsananin farinciki


"jaana"

(sunan datake kiransa kenan)


Takira sunan ahankali sannan tacigaba dacewa

"ina sonka bazan iya kwatanta kaunar danike maka ba.....


Ya katseta

"chuchu inasonki fiye da yadda kikesona,


Inasonki fiyeda yadda nikeson kaina 


Zan iya yin komai akanki zan iya yin komai dan inga nakasance

Tare dake har abada

Kece farinciki


Lumshe idanuwanta tayi wasu hawayen farinciki masu dumi suka gangaromata


Anty larai ce tashigo dakin tana salallami


"wai dama amaryan tananan ko wanka batayi ba bare tashirya?

Ga jama a saikara cika sukeyi?


Murmushi Rauda tayi,tayi kasa da muryarta tare da kara matse wayar akunnenta


"jaana bari naje nayi wanka "


Yace to afito lafiya





Yarfillo

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹JINNUL

        AASHQUE🌹



            NA

HARIRA ALIYU( *Yar Fillo*)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to aisha a ibrahim




🅿AGE📕 2⃣



Cikin kankanin lokaci aka tsantsara mata kwalliya


Take kyawunta yakara fitowa 

Farinciki agunta kuwa baya misaltuwa bakinta yakasa rufuwa


Haka mahaifiyarta ma itama farinciki gareta baya misaltuwa


Karfe hudu suka kammala shirin zuwa reception


Motocine manya masu tsadan gaske sukazo daukansu zuwa gurin reception din


ansha shagali sosai saikarfe bakwai akatashi Harsu salma sunshigo motar datake 


Abokin umar yazo yace sukoma dayar motar


Wannan motar amarya da angone zasushiga


Basuyi musu ba suka koma dayar motar


Saida motocin suka gama tafiya sannan umar yashiga motar


Tanazaune tayi shuru tana tunani batasan yashiga motarba harsaida  yashafamata wuya


Tadanyi firgigit tana kallonsa


Murmushi yayi yanafadin

"matsoraciya tunanin mekikeyi?


Girgiza kai tayi

"babu komai"


Ya gyada kai

"ook fadamin wani hotel kikeso muje mukwana"


Danzaro ido tayi tana kallonsa

"hotel kuma?


Yadaga gira

"yes hotel ko da aurena zan kwana nikadaine?


Ta rausayar da kai

"dan allah kabar wasa mutafi gida"


Ya gyara zamansa yana fuskantarta

"allah dagaske nikeyi da aurena bazan kwana nikadai ba idan bazaki zabi 

Hotel din dakikeso  ba nizanzaba"


Ganin dagaske yikeyi yasa ta marairaice fuska


"haba jaana kaima kasan abunda bazeyuwu bane.....


"mene bazeyuwuba?


Yakatseta ya na hade fuska


Tasauke numfashi 

"tayaya bamu tare ba zamutafi hotel?


"keba matata bace?

Yawurgo mata tambayar


"matarka ce mana amma......


Yadaga mata hannu

"kinga dakata!

Banason wasu surutai marasa tushe ke matata ce ina da ikon dazanyi duk yadda naga dama dake


Zata kuma magana yakuma katseta

"nace taredake zan kwana idan kuma tunyanzu zakifara min gardamane sai inji"



Shuru tayi tana kallonsa tarasa tayadda zatamai magana yafahimta


Ganin zetada motar yasa tarike mai hannu tana langabar dakai


"jaana please kayi hakuri kasani bazantaba iya yima musu ba amma hakan badai dai bane


Duk da nasan ba haramun bane dan na kwana tare da kai 

Amma surutun mutane nike gudu


Kaga za a daukeni marar kunya


Kayi hakuri gobe iyanzu inadakinka duk abinda kaga dama saikayi amma kayimin hakurin yau please"


Bekara cemata komai ba yatada motar ya nufi hanyar gida da ita


Kallonsa kawai takeyi tasan ransa yabaci itama saitaji zuciyarta babu dadi


kwata-kwata batason ganin bacin ransa


"jaana.....


Zatai magana yayi saurin dakatar da ita tahanyar daga mata hannu batare da ya ko dubeta ba


"inace gida kikace inkaiki?


Tadaga kai


Yacigaba da cewa"to yanzu hanyar gidan nikeyi ai dan haka banason surutu please"


Jikinta yayi sanyi takuma kai hannunta tarike nasa


"muje hotel din inhar zuwan zesaka farinciki"


Fakawa yayi agefen titi yazuba mata manyan idanuwansa masu juya mata lissafi


"bazantaba yimiki abunda bakyaso ba chuchu,danhaka kibari kawai ba fushi nayi ba kawai dai banji dadi bane"


"amma....


Shhhhhhh yadora yatsunsa biyu akan dan karamin bakinta


"nacemiki banyi fushi bakarki damu,dayau da goben ai duk na allah ne


Kuma goben kaman yaune"


Yakarasa maganar yana sakin fuskarsa


Sai lokacin taji hankalinta yakwanta bata kaunar bacin ransa kwata


"nagode mijina dakafahimceni"


Yasakarmata murmushi tare da shafa gefen fuskarta


"bar wani jindadi gobe zaki gane kurenki ne yarinya"


dariya tayi tana kauda kanta



Washegari karfe goma nasafe sukabar kaduna zuwa garin abuja


Iyayenta sunyimata fada da nasiha sosai


Taci kuka kamar ranta zefita dan tanada kawa zuci sosai ko tafiyar kwana biyu tayi allah allah takeyi takoma inko tayi sati to dama wajibine saitayi rashin lafiya


To bare wannan da tafiyar dun-dun-dunce saidai takaima gidansu ziyara


Saiwajen karfe shabiyu suka isa birnin tarayya


Cikin wata hadaddiyar unguwa suka shiga wani kayatacce fankacecen gida me kama da gidan sanator


ko nawani gomna gidan yatsaru sosai  gaba d'aya wadanda suka rakota sakin baki sukayi suna kallon gidan


Wasu daga cikinsu suna fadin

"gaskiya Rauda ta dace"


Yan uwan Umar ne suka futo da ga ciki yayarsa me suna kaltum itace tazo tarungumota

Tana rangada buda 


Nandanan sauran suka fara yan wake-wakensu na buzaye 


Ahaka suka shiga  kayataccen falon dayasha kayan alatu


Atsakiyar falon anty kaltum tazaunar da ita inda sauran suka zagayeta


Anty kaltum tayaye lullubin da ke kan rauda fuskarsa ta bayanna


"masha allah"

Sauran yan uwansa suka fara fada suna yaba kyanta


Kasa tayi dakanta dangani takeyi kaman zaginta sukeyi yadda sukeda tsananin kyau har zasu dubeta su kirata kyakkyawa


Ba abata lokaci ba aka cika gabansu da abinci kala kala


Saiwajen karfe biyar yan kaduna suka fara shirin komawa


Fada suka kara yimata sosai sannan suka juyo


Suma yan uwan umar din fashewa sukayi yan kaduna suka juyo yan niger suka nufi masaukinsu 


Anty kaltum ce kawai tarage  itama kuma tanajiran zuwan angwaye ne takama gabanta


Wanka tasa Rauda takumayi taciromata wani leshi rantsatsse tasa


Sannan tazauna tatsaramata kwalliya kasancewar ta kware afannin kwalliya


Saida akayi sallar issha sannan umar yashigo tare da babban abokinsa zayyad


Nan itama takarayimusu tata nasihar sannan tamusu sallama shima zayyad yayimusu nasa 


Sannan yayimusu saida safe


Umar yarakasa yarufe kofofin


Tanazaune saman gado inda yabarta yashigo yana zuba kamshi


Yazauna kusa da ita yasa hannu ya tallabo fuskarta


Suka hada ido

Jitayi gabanta yafadi wanda batasan dalilin faduwar tasa ba


Yasakar mata murmushi

"yadai amarya kinwani yi shuru ko duk jimamin rabuwa da mamane?


Takakaro murmushi

"kaman kasani jinikeyi kaman intashi inkoma"


Yayi yar dariya har fararen hakoransa suka bayyana


"lallai yarinya bakiji dakyau ba keda zuwa kaduna saikin shekara kila ma da jariri zakijemusu"


Dariyar itama tayi  

"ai inayin sati biyu zanje"


Ya jinjina kai

"lallai kam"


Tashi kidaukomana plate muci abinci dannasan yau bakici komai



Tamike tabude kofar dakin tafara saukowa daga step tana karema falon kallo 

Azuciyarta tana yaba kyansa dakuma kokarin mijinnata


Ta murda kofar kicin din 

Komai ashirye yike tsaf-tsaf


Tayi guntun murmushin jindadi


Lallai umar yanasonta dayawa dan ko tsinke kinyarda ayimata yayi shi yayi komai


Tazaro plate daya acikin kitchenwire

Tajuyo zata fita


"kwaram"

Taji karar wani plate din yafado


Tajuya tana cewa garin saurina banciro ahankali ba


Tagyara su tsaf sannan takuma juya


Hartakai bakin kofa takuma jin karar faduwar plates din


Dasauri tajuyo plates biyu tagani akasa


Gabanta yafadi take taji tsoro yafara kamata


Bata koma dauke plates dinba gaba kawai tayi tarufo kofar kicin din


Tafara tafiya dasauri tahau step.


Tahau daya biyu uku tatsaya cak.


Wani fargaba da tsoro yakuma kamata


Jitayi kaman ana bin sawunta


Tayi karfin halin juyawa amma bata ga kowa ba


Dasauri tacigaba da hawa harda tuntube gurin shiga dakin


Kallonta yayi yana fadin

"lafiya madam?


Zama tayi tana dan sauke numfashi


"jinayi kaman wani yanabina"


Dariya yayi

"oh my dear tsoronki yayi yawa wallahi waye zebiyoki?bayan kinsan gidannan dagani saike?


Hmmmmmmmm

Tasauke ajiyar zuciya

"nidai yanzu bazankara fita nikadai ba saidai muje tare"


Yagirgiza kai yana murmushi

"to madam ai duk yadda kikace haka za ayi"



Ya amshi plates din yajuye gasassun kaji biyu aciki


Sannan yafara bata abaki 

Saida yaga takoshi dam sannan ya kyaleta 


Yakwashe kayan  yamaidasu gefe sannan yadauro alwala itama yace tadauro


Sallah raka a biyu sukayi yayimata tambayoyi game da addininta ta amsa mai


Sannan yadafa kanta ya dinga kwarara addu o i


Sunmike kenan yana ninke darduma wayarsa tafara kara


Ganin numban asibi ne yasa ya dauka 


Magana uku yayi yace "ook kubashi taimakon gaggawa ganinan zuwa"


Ya ajiye wayar yana dubanta


"baby kirane daga asibiti wai ankawo wani emergency"


Kallonsa tayi sosai

"toyanzu mekake nufi?


"zuwa zanyimana chuchu ceton raine fa?


Waro idanuwanta tayi tana kallon agogo sannan tamaida idanuwanta kansa


"yanzufa karfe shabiyu"

Yadaga kai

"nasani ai amma ai komin dare dole infita tunda aikinane 

"


Nan danan idanuwanta suka cicciko da kwalla


Matsowa yayi gab da ita yajanyota jikinsa


"please honey kiyi hakuri naje ance mutumin yana cikin wani hali please....

Dago kanta tayi daga jikinsa 


Tazuba masa fararen idanuwanta 


"amma kasan bazan iya kwana nikadai acikin gidan nan ba ko?saidai inmutafi tare"


Ya waro ido

"dawa?baze yuwu ba ba bu inda zakije acikin darannan


Nima dan yazamarmin dole ne


Danhaka kikwanta kiyi baccinki inagamawa zandawo


Zata kuma magana ya katseta


"chuchu bata lokacinnan danikeyi bawan allahn can ze iya rasa ransa da haka natafi 


Yakarasa fada yana ficewa da sauri


Bin bayansa tayi da kallo cike da tsananin damuwa dan ita ko agida batasaba kwana itakadai


Bare awannan katoton gidan


Zama tayi turus gefen gado yayinda taji tashin motarsa



Tayi shuru tana tunanin yadda zatayi 


 Ga iskar hadari tanata kadawa


Mikewa tayi ta janyo windon dakin dayike abude iska nata kadashi 


Rufe windon yayi dede da dauke wutar gidan 


Kirjinta yabuga dam take matsanancin tsoro yakamata 


Tayi karfin halin dawowa bakin gadon tasa hannu tana laluben wayarta


Jitayi antaba mata kafa dasauri tahaye gadon tana karanto duk addu o in da suka zo bakinta




Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹JINNUL

       AASHIQUE🌹



           NA

HARIRA ALIYU(yarfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/




Dedicated to Aisha Ibrahim



🅿AGE📕 3⃣


Dakyar ta iya lalubo wayar gabadaya firgici da tsoro sungama kamata


Hannunta na rawa takunna fitilar wayar,tahaska tsakar dakin inda takejin kaman akwai wani atsaye


Saidai bataga kowaba,ajiyar zuciya tasauke me nawi

Tajingina da jikin gadon tana maida numfashi.


Amma idanuwanta sunkasa tsayawa wuri daya kalle-kallen dakin kawai takeyi

Azuciyarta kuma tana karanto addu'o in neman tsari.



Dai-dai lokacin akafara ruwan sama wanda yataho da karfi kaman da bakin kwarya


Hankalinta yakara tashi dantasan yadda ruwan yataho da karfi,to lallai sai anyi tsawa,itakuma allah ya jarabceta da jin tsoron tsawa


Takurewa tayi guri daya ko motsin kirki takasa yi 


Ahankali taji karar bude kofar falon sannan taji anrufe


Daga bisani tajiyo karar tafiya kamar ana haurowa saman


Babu inda baya rawa ajikinta saboda tsabar tsorata,gabadaya ta daburce 

Addu'o inma sunbace mata


Inbanda ayatul kursiyyu ba abunda bakinta ke iya furtawa,itama din bata kaiwa karshenta take dawowa farko.



Jin karar sawun tafiyan daf da kofar dakin datakeciki,yasa ta cusa kanta cikin gwiwo winta 

Danbataso taga abunda ze shigo din tasan ba alheri bane



Murda kofar dakin akayi 


Da karfi tafara karanta ayatul kursiyyu,amma har lokacin takasa dago kanta bare taga me shigowar,


Jitayi andafata,takwala ihu tana fadin 

"inna lillahi wa inna ilaihi raji'un !


Muryar umar taji yana fadin

"lafiya madam meke faruwane haka?


Tabude idanuwanta da sauri,ganin shine yasa ta rungume sa dasauri gami da fashewa da kuka.


Zaunawa yayi tana rungume ajinkinsa

"meyake faruwane?fadamin mana"


Cikin kuka tafara magana tana girgiza kai

"bazan iya zama agidannan ba wallahi tsoro nikeji,bazan iyaba"


Yasauke numfashi yana dan bubbuga mata baya ahankali


Cikin sigar rarrashi yace

"ok..ok kiyi shuru hakanan banason kukannan please"


Saida tadan dauki lokaci sannan tadena kukan takomai sauke numfashi ahankali


Ya dagota daga jikinsa yazuba mata kyawawan idanuwansa


"chuchu,meyasa kikeda tsoro dayawane? Bakisan yawan tsoro babu kyau ba?


Ta ajiye numfashi tace

"to ba laifinka bane katafi kabarni a wannan daren,badole inji tsoro ba"


Shima numfashin yasauke 

"toyanzu da bandawo ba fa?dole fa kikoyi rage tsoronnan saboda kinsan aikina,

Ana iya kirana ako wani lokaci"


Ta jinjina mai kawai sannan tace

"waima ya akayi kadawo?bakace zakaje kaduba mara lafiya bane,kuma ya akayi banji tsayuwar motarka ba?


Yayi dan murmushi

"wallahi inazuwa natadda doctor zubairu a asibitin,yanata yima nurse din data kirana fada


Wai akanme tasan yaune natare zata kirani,shine yacemin injuyo shi zeduba marar lafiyan


Karar mota kuma ya zayi kiji?bayan kin sama zuciyarki tsoro,sannan kuma kinmanta ruwa akeyi?


Tagyada kai 

"hakane amma please jaana karka kara barina nikadai wallahi inajin tsoro sai intajin wasu abubuwan tsoro dayawa"


yayi murmushi dayakara bayyana kyan fuskarsa

"dama koda yaushe ni inatare dake,danhaka kirage tsoro kinji"


Ta gyada kai tana nata murmushin

"tom insha allahu zan rage"


Yakwanta gamida kwanto da ita jikinsa

"chuchu ina alkawarina na jiya?


Tadanzame 

"tomiye nasauri jaana,nifa takace"


Dariya yayi ya kashe fitilar wayartata



Misalin karfe uku da rabi,suna rungume da juna yana shafa sumar kanta


"chuchu allah yayimiki albarka hakika ke tadabance kinsanyani farinciki mara misaltuwa"


Murmushi tayi tanajin wani sanyi acikin zuciyarta 


"jaana inasonka,kayimin alkawarin bazaka taba rabuwa dani ba"


hannu yasa yadago fuskarta suna kallon juna


Tasauke ajiyar zuciya

"hmmmmmm hakika nayi dace da miji kyakkyawa wanda samun irinsa aduniya ze yi matukar wahala,amma ina fargaban kada watarana wata takwacemin kai"


ya girgiza kai

"bakisan irin son danakemiki ba chuchu,zan iyayin komai akanki kuma babu wacce ta isa takwace soyayyata agareki


Maganar yimiki alkawari kuwa,nayi ada kuma ayanzu ma zankuma yimiki


bazan taba rabuwa dake ba....."


Ta lumshe idanuwanta ahankali farinciki yakuma lullubeta 


Gani takeyi kamar ayanzu bata da wata sauran matsala arayuwarta


Kara shigewa jikinsa tayi bacci medadi yadauketa.



Washegari sai wajen karfe bakwai tafarka


ganin haske yagauraye dakin yasa  ta kalli agogo

Karfe bakwai harda mintoci.


Takalli gefenta inda yakwanta, baya wurin 


Mikewa tayi tashiga toilet tayi wanka tadauro alwala


Ta gabatar da sallar asuba,bayan ta idar ta ninke dardumar tanufi wardrop tanajin jikinta nayimata tsami dan gabadaya ciwo yikeyi.



Riga doguwa tadauko tasa,sannan tasauko daga saman dantasan yana kasan


Saidai bataganshi a falon ba,taduba kicin nanma baya ciki


"ina yaje"

Tayi wa kanta tambayar


Zuciyarta ce tabata amsa

"kila yaje siyomuku abun kari ne"


Tagyada kai dantasan baze wuce hakan ba


Falon tadawo tazauna adaya daga cikin kujerun


Tadanna kiran numban mama

Ringing biyu tadauka suka fara gaisawa.


Kwan-kwasa kofar akafara yi


Tamike da wayar akunnenta tabude


Umar ne tsaye rike da rigarsa ta likitoci


Suka sakarma juna murmushi


Katse wayar tayi tanacewa

"ina kwana"


Ya janyo hannunta tafada kan faffadan kirjinsa


"wayace miki haka ake tarban miji?kintsaya daga nesa kina wani cewa ina kwana"


Tayi kasa dakanta cike da jin kunyarsa


Suka karasa cikin falon yana rike da ita


A three seater suka zauna,ya ajiye rigar ahannun kujera yanacewa

"wallahi nagaji kokadan jiya ban runtsa ba,amma nasan ke barcinki kikai harda munshari"


Megadi ne yayi sallama 

Ya miko ya miko wani kwando cike da kayan karin kumallo yace anty kaltum ce ta aiko dashi


Umar yamike

"kinga jera abincinnan akan dining bari in watso ruwa"


Tadauki kwandon ta kai kan dining din ta jejjera komai,tazauna tana jiransa.


Befi minti goma da shiga ba yafito sanye da three-quater da T-shirt


Yazauna a kujerar dake fuskantarta suka fara karyawa yana janta da fira


"shine ko kitambayeni ya me jiki ko?


Yafada yana kai kofin tea bakinsa


"yihakuri yanzu nike shirin intambayeka"


Ya gyada kai

"ook ai bawan allahnnan ya jigata dayawa motarsa karkashin traler fa tashige da kyar muka iya ceto ransa danni banyi zaton ma zeyi rai ba"


Tadakata daga kurban tea din datakeyi tana kallonsa dan bata fahimci abunda yike nufi ba


Shima kalonnata yayi ganin takafashe da ido yasa yace

"yadai?naga kinayimin wani irin kallo,kamar bakigane abunda nike cewa ba"


Ta jinjina kai

"to gani nayi ba kai kayi aikinnan ba,doctor zubairu ne yayi amma kana cewa da kyar kuka ceto rayuwarsa


Kallon rashin fahimtar shima yafara yimata

"bangane ba,wani doctor zubairu kuma?


"doctor zubairu na asibitin ku mana"

Tabashi amsa atakaice


Yagyara zamansa yana maida hankalinsa akanta

"wai wani doctor zubairun kike magana akansa?

Doctor zubairun da watansa biyu kenan a kasar china"


Takauda idanuwanta akansa,tamaida kan wayar ta, tana duba sakon da aka turo mata



"to nidai bansani ba,kaida bakinka jiya kace doctor zubairu yace kadawo gida bekamata kafita aiki a daren jiya ba"


Har lokacin idanuwansa nakanta

"ayaushe nace miki hakan?


"a jiya da kadawo mana"

Tabashi amsa cikin kosawa da zancen dan dan tafahimci so yike yamaida abun wasa



"nifa bandawo gidannan jiya ba"

Yafada


Tadago kanta daga kan wayar suka hada idanu

"mekace?


Ta tambaya dan tabbatar da jin abunda yace


"nace bandawo jiya bani,tunda mukai natafi asibiti bandawo gidannan ba sai a safiyarnan"


Ganin fuskarsa ba bu alamar wasa yasa tace


"wai meyasa kaketa wasu maganganu da bangane bane,jiya bakadawo ba,misalin shabiyu da rabi?


Ta girgiza kai

"saidai in mafarki kikayi danni lokacin ma ina emergency room"



Ta gyada kai 

"dan allah kabar wasannan haka"


Hannunta yakama

"kedai zancema wa kibar wasan haka,nida na kwana asibiti zaki wani ce wai nadawo gida...........


Takatse shi

"jaana please wasan ya isa haka"


Ya jingina bayansa da kujerar dining yana kallonta


"chuchu i'm serious saidai in mafarki kikayi amma ni wallahi bandawo gidannan ba"


Jin yayi rantsuwa yasa gabanta yafara faduwa


"jaana harda rantsuwa?


Ya jinjina kai

"to nafadamiki mafarki kikayi baki yarda ba.......


"to dawaye na kwana jiya?

Takatsesa da sauri


"kwana kuma?banganeba"


Ta jinjina kai yanayinta yafara komawa na firgici


"jaana wallahi jiya kadawo kacemin doctor zubairu ya amsheka,kuma tare dakai muka kwana."



Wani kallo yayimata gami da cewa 

"kidawo hankalinki please,ban kwana agidannan ba..............





Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹JINNUL

       AASHIQUE🌹



            NA

HARIRA ALIYU(yarfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to Aisha Ibrahim


Wannan page din nakine anty nabila ina godiya da kokarinki gareni allah yabar zumunci



🅿AGE📕 4⃣



Dire kofin tayi,ranta yadan soma baci,akanmene yikeso yayi mata wasa da hankali?


"wai meke damunka ne? Indawo hankalina kamar yaya?tayaya munkwana dakai zaka cemin kai ba a gidannan kakwana ba........


Buga teburin yayi dan shima nashi ran yasoma bacin


"nace miki a asibiti nakwana!


Jikinta yasoma bari,zuciyarta tafara rawa


Zagayawa tayi inda yike ta durkusa tadafa gwiwowinsa 


"jaana kasan bama irin wasannan ko?dan allah kafadamin dagaske ne baka kwana  agidana?


Wani irin kallo yikemata nawacce tafara tabuwa


"chuchu wallahi a asibiti nakwana......


matsawa tayi arazane idanuwanta suka cicciko


Cikin rawar murya tace

"inna lillahi wa inna ilaihi ra'ji un.......



Kallonta kawai yikeyi


Maganar malan ce tadawo mata

"kirike wannan lemun tsamin kitabbatar dakin shiga dashi cikin gidanki


Aranar da kika kwana daya kibude kullin da lemun tsamin ke ciki


Idan kiga yananan akalarsa to tabbas munyi nasara a wannan aikin da mukayi na karshe


Idan kuma kiga yacanza kala zuwa ja,to tabbas akwai matsala


Wannan lemun tsamin yana dauke da magunguna masu karfin gaske kitabbata kinshiga dashi"



Mikewa tayi dasauri tafara hawa step dagudu 


Tanajin umar yana kiranta bata tsaya ba,harsaida tashiga bedroom dinta


Handbag din ta tadauko ta zazzage kayan dake ciki


Hannunta na rawa tadauki kullin lemun tsamin tafara kwancewa


Gabanta nafaduwa 


Saidai me,tana gama kwance kullin taga lemun tsamin yayi jawur


Ihu takwala ta wurgar dashi


Dai-dai lokacin umar yashigo dakin 


"chuchu me kikeyi ne wai.......


Kankamesa tayi dasauri jikinta narawa 


"Aasim!Aasim!"



Yadagota dasauri

"Aasim kuma?


Cikin kuka tafara cewa

"nashiga uku jaana Aasim yanatare dani haryanzu,wallahi jiya ba mafarki nayi ba shi yazomin a suffarka.........



  Kamata yayi suka zauna akan gadon yakura mata ido yana karantar yanayinta


"Aasim chuchu?ba malan yace anriga da ankullesa a kwalba ba?


Ta jinjina kai dasauri

"haka yace amma  lemun tsamin dayabani yacanza kala kuma.....kuma jiya inatajin anatsoratani sannan yazomin asuffarka"


Rungumeta yayi yana shafa bayanta


"okay,okay,kwantar da hankalinki please  bari inkira wayar malan din"


Yazaro wayarsa daga aljihu yadanna numban malan saidai kira biyu yana masa bedauka ba


Yakuma danna kiran a karo na uku,saida takusan tsinkewa sannan aka daga


Yayi sallama yana fadin

"ina kwana malan,antashi lafiya?


Daga can bangaren wani ne ya amsa

"ba malan bane,malan allah yayi masa rasuwa jiya da daddare yanzu haka muna shirin kaisa makwancinsa"


"inna lillahi wa inna ilaihi ra'ji un,ya rasu?hatsari yayi kome?


daga can bangaren ya amsa

"wallahi lafiyarsa lau ya kwanta saidai dubawa akayi akaga yarasu" 


Ajiye wayar yayi yana share gumin da ke keto masa a goshi


Itako kuka tafashe dashi tana fadin


"wayyoh allah na,nashiga uku!!


Be hanata kukantaba,zura mata ido kawai yayi zuciyarsa cike da damuwa


Da tarin fargaba,me yike shirin faruwa da sune?


Jiyayi kansa yayi wani dum

"la ila ha'illa anta subhanaka inni kuntu minaz zalimin"


Bakinsa ya furta ahankali

Sannan

Ya kira sunanta a sanyaye


"Rauda.....

Sanin kankine kukannan ba bu maganin da zemana face yajanyo miki ciwon kai,


Kiyi shuru kidaina kukan haka,munemi mafita......


Dagaowa tayi tana kallonsa da jikakkun idanunta


"mafita?a ina zamu samo mafitar jaana?gurin malan isah ne kadai muka sa ran zamu sami mafita,


Amma gashi,sanadiyyar taimakona har ya rasa ransa nasan.......


Ya girgiza kai

"malan kwanan sa ne yakare,kuma na tabbata zamu samu waraka awani gurin.



Abinda nikeso dake,ki kwantar da hankalinki kinji?


Ta jinjina mai kai kawai amma ita kadai tasan tashin hankalin datake ciki.


Shima din dauriya yayi kawai amma zuciyar sa cike taf da da damuwa.



Yarasa wani irin al'amarine wannan me cike da rudani


Ya kalli fuskarta,tayi kuka harta gaji bacci yadauketa.


Kwantar da ita yayi


Ya mike,yana zagagaye acikin dakin yana tunanin ta inda ze bullo ma al'amarin


Itako Rauda mafarki takeyi cikin barcinta,malan isa tagani zaune yana lazumi 


Saiga hayaki yafara shigowa dakin dayike,kan kace kwabo jijiyoyin wuyansa sun mummurde,idanuwansa sun kakkafe


Zuwa can taga yazame kasa,alamun numfashin sa yadauke


Dariya taji anfara yi me tsoratarwa daga bisani taga wani farin saurayi yabayanna 


Dariyar ya cigaba dayi,lokaci daya kuma ya murtuke fuska kamar bashi yagama yin dariyar ba.



Yakalli malan isa yana nuna sa da da yatsa

"kallesa,wai shi ze ja dani,ni Aasim"


Ya girgiza kai yana cigaba dacewa 


"bazaka iya ba! Bazaka iya ba!


Na gargadeka tun farko amma kayi taurin kai kana ganin kaman zaka iya ja dani......"


Yadan durkusa sai saitin malan isan 

"tashi mana! Tashi kaciga ba da aikin da kakeyi.........bazaka iya ba,bazaka iya ba ko?



Ya mike tsaye yana cigaba da yin dariyar sannan ya dubeta da razanannun idanunsa


"kinsa nayi abunda ban taba yi ba,tunda nike aduniya bantaba kisa ba


Amma gashi sanadinki kinsa nafara,kinsa naka sheshi.......


Yakara sa fada idanuwansa na kuma runewa 


"Kiyi babban kuskure a rayuwanki,da kika karya sharuddan dana gindaya akanki


Mafi girman kuskuren da kikayi kuwa,shine dakika bari na kusanceki azahiri..."


"kisani daga yanzu kinrabu da farin ciki,kwanciyar hankali sannan abunda zance miki na karshe shine


Idan har kinason rayuwar mijinki to  tabbas kada ki kuskura ya kusanceki dan duk ranar daya yi hakan to tabbas ze mutu kamar yadda wannan ya mutu!!!!!


Yakara sa fada yana nuna malan isa sannan yakuma fashewa da dariya



A razane tafarka jikinta nabari


Umar dake ta patrol acikin dakin yadawo bakin gadon dasauri


Rirrikesa tayi tana waige-waige

"shine yakashe shi,wayyoh allah na!!!


Bayi da bukatar tambayarta dan yasan mafarki tayi


Rungumeta yayi kawai,azuciyarsa yana jin tausayinta


"dan allah kada kabarni koda na minti dayane,cutar dani zeyi"


Tafada jikinta na kakkarwa  


Ya jinjina kai 

"zan kasance tare dake,akodayaushe,babu abunda zesameki da izinin allah"




Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹JINNUL

        AASHIQUE🌹



              NA

HARIRA ALIYU(yarfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to little  Hajjo




*_A kullum forum dinmu Kara bunk'asa yakeyi,mutanen cikinsa Kara basira da fasaha sukeyi,ina jinjina ma golden writters Allah yabar zumunci a tsakaninmu_*



_GAISUWA Ga *MATAN K'WARAI* group *yar fillo* na godiya da addu'o inku gareta,ina Kuma Jin dadin yadda kuke yaba labarina,ina godiya sosai_




🅿AGE📕 5⃣



Hannunsa takama,Tana kallonsa da jik'akk'un idanuwanta da suka yi luhu-luhu


"Jaana,kayi min alkawarin duk rintsi bazaka taba rabuwa Dani ba,nasan matsala yanzu muka fara ganinta......


Ya sauke numfashi Yana kallon cikin idanuwanta


"Chuchu kina tunanin akwai abunda ze bani tsoro har yasa nai tunanin rabuwa dake?”


Ya girgiza Kai sannan yaciga ba da cewa

"Son Dana ke yimiki,ba k'aramin so bane,kuma bana tunanin akwai abunda ze razanani akanki,nasan yayi hakane Dan yasanya shakku da fitina atsakaninmu Amma ni ina k'aunarki Kuma ko me zeyi sai dai yayi Amma tarayya dake yanzu nafara Kuma ashirye Nike da indauki duk wani abun da zezo dashi"



Ta maida kanta kan k'irjinsa,tanajin zuciyarta babu dadi



"Nasan  zaka iya jure komai,Amma ina Jin tsoro,nafi kowa sanin waye Aasim,abunda ze iya?da abunda baze iya ba.


Nasan ze iyayin komai domin yaga yarabani da kowa,baze cutar Dani ba,ina da tabbacin hakan Amma........


Tadan dakata Tana share hawayen dake ambaliya a fuskarta,sannan tacigaba


"Kai ze iya cutar da Kai,banason wani Abu yasameka abunda Nike tsoro kenan"


Murmushi yayi me dauke da damuwa


"Kinmanta da cewa Allah Yana tare damu?idan har muka rike addu'a,to tabbas muna tare da kariyar Allah a kodayaushe.


Dan Haka kikwantar da hankalinki,zankira zayyad akwai wani malami dayace yasani a k'auyensu,sai muji yadda za'ayi"



"A'a,banaso wani yak'ara rasa ransa a sanadina"


Tafara cikin karyewar zuciya 



"Hmmmmmmmmm!!

Yakuma sauke numfashi


"To Rauda zamu zauna hakane?dole mukuma neman mafita,tun abun beyi k'arfi ba"


Shuru tayimai kawai,Amma ita ta Riga da ta Gama karaya


Wunin ranar be leka ko kofar gida ba,Dan yasan a tsorace take,hatta salloli agida yayi.


Abincin Rana Dana dare duk anty kaltum ce ta aikomusu,Dan Basu da nisa sosai


Bawani cin abincin sukayi dayawa ba,Dan hankalinsu ba a kwance yike ba.



Suna zaune a kan kujera,da daddare,bayan sun kammala cin abinci,yamike Yana maida sauran kula


"bari in d'an watsa ruwa,yanzu zandawo"


Ta gyad'a mai,batare da tace komai ba.


Sama ya haura yashiga bedroom dinsa,yarage saura ita kadai a falon


 Tunanin Daren jiya kawai takeyi da abunda ya wakana atsakaninta da Wanda ba jinsinta ba,



Zuciyarta ce take ta haskomata lokacin,  gani takeyi Kamar mafarki takeyi.


Karar da TV d'in falon yikeyi ne yafara damunta,ganin hankalinta bama akan TV d'in yike ba,yasa tadauki remote d'in dake dake gefen kujerar takashe


Ko second biyu batayi da kashewa ba ya kunnu


Ta Kuma d'aukar remote d'in takuma kashewa,still ya sake kunnuwa.



Gajeren tsaki taja tamik'e ta zare socket din,tajuyo zata dawo kan kujerar


Karar TV d'inne yasa ta tsaya cak,tare da juyawa ahankali


Still TVn yasake kunnuwa


Takalli socket d'in da ta zare Yana nan akasa Amma Kuma TV Yana aiki


Tsoro yafara kamata,zuciyarta tafara rawa


Ta kalli cikin TVn,wasu mutane tagani a zazzaune  sanye da bak'ak'en Kaya  sunyi kasa da kansu suna karatu da wani yare


Zuwa can suka d'ago suka kalleta da manyan idanuwansu da yike bak'kk'irin babu wani alamar fari acikinsa.


Tayi baya dasauri jikinta yafara rawa 


Hannayensu suka d'ago sunayimata alamar Kira


"Ta'al huna Rauda!

Ta'al huna Rauda!"


Zuciyarta tafara bugawa da k'arfi kaman zata fito waje saboda tsananin razana


Matsowa sukeyi suna Kuma fadin

"Ta'al huna!



A razane tajuya da gudu,Tafara hayewa saman,maganganunsu kawai ke yimata yawo akunne tanajin sautin muryarsu yana dad'a k'aruwa


Ta banka k'ofar bedroom dinsa da k'arfi,tare da tura k'ofar bayin


Yana tsaye jikin shower,Yana sakar ma kansa ruwan sanyi


K'an-k'amesa tayi jikinta na kyar-kyarwa


“gasu can.......kirana sukeyi,d'aukata zasuyi,kataimakeni kafitar Dani daga cikin gidannan......


"Suwaye?”


Yatambayeta dasauri


Kasa bashi amsa tayi Dan ta rud'e sosai


K'aramin towel ya d'aura yakamo hannunta suka fito daga bayin


Addu'o I yadinga tofa Mata,zuwa can tadena sambatun datakeyi, Takoma sauke ajiyar zuciya


Ya dauko wani tawul din yafara gogemata gashin kanta daya jike yayinda tashiga bayin


"Aduk sanda kika ga wani Abu na tsoratarwa,ki rinka ambaton sunan Allah kikuma dungayin addu'a,


Tsoratar dakikeyi shizeba masu tsoratar dake damar cutar dake"


tadago kanta tana kallonsa har lokacin jikinta bedena rawa ba


"Bazan iya zama agidannan ba,bazan iya ba,ka maidani gida Dan Allah"


Hmmmmmmmmm yasauke numfashi


"Ko zaki iya gaya min yanayin da mama take ciki a halin yanzu?


Nasan tana cikin farin ciki,da jin dadin kinyi aure,abunda tadade tanason tagani,


Me kike tunanin zataji idan har ta fuskanci kina cikin matsala a halin yanzu?


Yad'an numfasa sannan yacigaba da cewa


"Nasan zata shiga damuwa,da tashin hankali,wanda ze iya tado mata da ciwonta,sam komawarki gida ba mafita bane 


Ta yayama daga yin auranki kwananki daya da tarewa ace kinkoma gida,me kike tunanin mutane zasu ce?


Nasan mak'iya dariya zasuyi,Dan haka kicire wannan tunanin a zuciyarki


Badai sai bana tare dake a ke tsorataki ba?


To bazan kara zuwa ko nan da can batare dake ba,ba abunda ze koma tsorataki ina tare dake"


Yak'arasa fada yana share mata hawayen dake gangarowa daga idanuwanta



Tabbas abunda yafada gaskiyane,mama tanacikin farin ciki a halin yanzu


Dole ta hak'ura ta danne damuwarta


Mik'ewa yayi yazaro mata rigar bacci ya mik'a Mata


"Kayan jikinki sun jik'e,kisanya wannan"


Amsa tayi tana dubansa,shid'inma ita yike kallo ganin nawin cire kayan takeyi agabansa yasa yace



"Kinajin kunya ko?to bari infita kisa kayan"


Yak'arasa fada yana juyawa


Da hanzari ta rik'o hannunsa


"Baka ce bakace bazaka k'ara barina nikadai ba?


Ya jinjina Kai

"Eh,Amma ai naga nawin cire kayan kikeji agabana,shiyasa zanfita"


"To nidai karkafita,zan canza ai"


Tafad'a tanayin k'asa da kanta


Ya gyad'a kai yana kafeta da kyawawan idanuwansa


"To canza"




D'ago kanta takumayi suka had'a ido


Ta marai-raice fuska


"To ka dena kallona"


"Aa,bari ma infita kawai"


Yafada Yana niyyar zame hannusa dake rik'e cikin nata


Kara matse hannun nasa tayi tana cewa


"Kayi hakuri"


Ya gyara tsayuwarsa yana k'ara kafeta da ido



Cikin sanyin jiki ta war-ware k'aramin gyalen da ke kanta tadan daura a k'irjinta



Sannan tafara yaye doguwar rigar dake jikinta,cikin sauri tacire rigar tasa hannu zata d'auki rigar baccin



Dakatar da ita yayi tahanyar rik'emata hannu


Kallonsa tayi da rinannun idanunta


"Menene kuma?


Ya sauke gauron numfashi tare dacewa


"Kitsaya ahaka,ina buk'atar ganinki ahaka"


Zatai magana,yajanyota tafad'a jikinsa


Gabanta yafara fad'uwa


"Jaana,kamanta damuwar da muke cikine wai?


Ya girgiza Kai

"Ina sane banmanta ba"


"Amma......


Yakuma katseta


"Chuchu duk wad'annan abubuwan dakika ga anayi,anayine dan ahanamu samun cikar burinmu,shiyasa aka biyo ta wannan hanyar dan aga ankauda tunaninmu akan abunda mukadad'e muna muradi"



Ta girgiza kai

"Amma ai ba ayau ba,kabari sai mundawo cikin natsuwar mu tukunna.......



Yatsunsa biyu yad'aura akan labb'anta


"Kada kibawa azzalumai damar cin galaba akan rayuwar auranmu,nasan da zarar mun cika burinmu to tabbas wannan tsoratakin da akeyi za Adena,Dan dama anayine Dan aga ancanza mana tunani



Maganganun Aasim ne suka fara dawo mata da yi mata yawo akunne


"Idan har kanason rayuwar mijinki to tabbas kada ki kuskura ya kusanceki Dan duk ranar da yayi hakan to tabbas ze mutu Kamar yadda wannan ya mutu"


Umar ya katsemata tunanin da takeyi


"Kada kibari maganganunsa suyi tasiri a zuciyarki,kibani dama zaki tabbatar da abunda Nike fadamiki.....



Yak'ara matseta a jikinsa


Hankalinta yak'ara tashi


"Aa kayi hak'uri Dan Allah,bazan iya ba!


Kallonta yayi sosai, daga bisani ya janye jikinsa ya kwanta agefen gadon yana juya mata baya



Hawaye ne yacigaba da gangaro mata,yaza tayi da rayuwarta ne?


Aduniya babu abunda ta tsana irin taga b'acin ran Umar,Amma yaza ayi ya fahimci irin abubuwan datake gani na razanarwa??



Durk'usawa tayi agaban gadon,cikin kuka tafara cewa


"Dan Allah kayi hak'uri.......



Juyowa yayi ahankali yana kallonta,ya sakar mata murmushin karfin Hali



"Kada kidamu kanki,ki hawo kikwanta,nima nasan ba dai-dai bane inbukaci hakan agareki awannan yanayin danike ciki


Amma idan muka ce zamu biyema wannan al'amarin haka zamuyita zama,kuma kimin uzuri kinfi kowa sanin hak'urin dana dad'e inayi"



Ta jinjina Kai 

"Nasani,amma ka gafarceni tukunna Dan Allah"


Ya gyad'a kai yana kuma yimata murmushi tare da dagota 


Suka kwanta suna fuskantar juna


"Karki damu,kiyi baccinki Amma kibari in rungumeki ki kwana ajikina,babu abunda zanmiki"


Ta jinjina mai Kai,ahaka suka kwana rungume da juna


Kowane da abunda yike sak'awa acikin zuciyarsa



Da Asuba,ita Tafara tashi,wani irin yunk'urin amai ne yatasheta


Bayi tashiga dasauri tanata kakarin amai


Sai dai babu amai babu labarinsa sai uban kakarin datakeyi


Tsayawa tayi tana maida numfashi


Ta kunna famfo Dan ta dauraye bakin da fuskarta


Sai dai me? A memakon taga ruwa saitaga jini nata bul-bulowa


Baya tayi dasauri tana murza idanuwanta Dan tabbatar da jinin datagani


Still jinin tagani harda guda-guda








Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

           AASHIQUE🌹




                NA

HARIRA ALIYU (yarfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/




Dedicated to little hajjo




Gisuwa da fatan alkhairi ga babbar Yaya hafsat aliyu




🅿AGE📕 6⃣



Bissmillahir rahmanin rahim



Hannunta na rawa takulle kan famfon  tafito daga bayin



Ta zauna bakin gadon tana kallon fuskar Umar


Bacci yikeyi sosai,tafashe da kuka tana dafa kanta datakeji yanayimata wani irin ciwo Kamar ze rabe biyu



***      ***   ***



Washegari 

Anty kaltum da yaranta anan suka wuni,hakan yasa tad'an saki sai yamma suka tafi


Bayan sun dawo daga yimusu rakiya,umar yakalleta yanacewa


"Kishirya mufita yawo"


Tayi murmushin Jin dad'i Dan dama zaman gidan ya isheta jitakeyi kaman akan k'aya take



"Yanzu,ko anjima?


"Yanzu mana,"


Ya bata amsa


Ta gyad'a kai

"To muje karakani d'akin"


Dariya yayi had'i da cewa


"Matsoraciya zanga yadda zakiyi innafara fita aiki"


Tafiya tafara yi Tana cewa

"Tare zamu rink'a zuwa ai Dan bazan taba zama nikadai ba Allah"



Bedroom d'inta suka shiga tasauya kayan dake jikinta zuwa ga bak'ar jallabiya


Tayana gyalen rigar tana d'aukar wayarta


"Muje nagama"


Kallonsa tayi jin yayi shuru


"Yadai nace nagama muje"



Janyota yayi gab dashi suna shak'ar numfashin juna


"Chuchu!


Yakirata da wata kalar kasalalliyar murya


Suka kalli juna,yasauke numfashi me nawi



Tare da kama hannunta yad'aura akan k'irjinsa


"Chuchu,zuciyata tana bugawa da k'aunarki ne,a duk sanda nakalleki inajin k'aunarki na k'ara bin jinina da dukkanin jijiyoyina......


Tayi guntun murmushi tare da kama nasa hannun tad'aura akan nata k'irjin tace 



"Nima haka, kodayaushe zuciyata bata wani abun da take ambato face sunanka,ina sonka fiye da yadda Nike son kaina,fiye da yadda nike son rayuwata,bazan iya rayuwa idan babu Kai na"



Rungumeta yayi yana k'ara sauke sassanyar ajiyar zuciya


"Ina alfahari da samunki danayi amatsayin Mata,zankasance tare dake har k'arshen rayuwata"


Har lokacin murmushi be bar fuskarta ba


"Muje,kada dare yayi"


Yakama hannunta suka jero zuciyoyinsu cike da begen juna


Saida suka shiga motar me gadi yabud'e suka hau Kan titi sannan yace


"Ina kikeson mujene,inda zesakaki nishadi?


Tad'an rausayar da fararen idanuwanta


"Uhm muje.......



Ya ketseta

"Wajen shan ice cream ko?



Dariya tayi tana kallonsa


"Ya akayi kasan abunda zanfad'a?


Hankalinsa nakan tuk'in yabata amsa


"Saboda nasan kinasan Ice cream sosai"



Ta jinjina Kai


"Hakane,kumafa na kwana biyu bansha ba,tun zuwan dakayi kaduna wancan karen dakazo mindashi"


Ya gyad'a Kai


"To yau zaki sha ki k'oshi harkiyi odarsa zuwa gida"


Basu dad'e suna tafiya ba suka isa katafaren wurin 



Wuri me kyau suka zauna aka kawo musu ice cream d'in,suna sha suna fira cikin nishad'i


Duk da k'asan zuciyarta akwai damuwa amma tayi k'ok'ori ta danne.


Basu suka bar wurin ba sai tara saura


Suna shiga falo ko zama basuyi ba,ya fizgota jikinsa yana shisshin shina wuyanta cikin wani irin yanayi 


K'ok'orin janye jikinta tafara yi tanacewa


"Jaana please"


Kuma matseta yayi yana k'ok'orin had'a  bakinsa da nata


   Yayi nasan cafkar labb'anta masu ban Sha'awa aduk sanda take motsasu gurin yin magana



Kissing d'inta yafarayi azafafe,yana shasshafata


Maganganun Aasim ne suka fara yimata yawo a kunne


K'arfinta tasa gabad'aya,ta turesa tare da janye jikinta tana maida numfashi



Yakuma janyota yana kallonta da idanuwansa dasuka canza launi


Cikin wata kalar murya me cike da buk'ata yace


"Rauda please kada kihanani,ayanzu ke matata ce babu wani shamaki atsakaninmu"



Girgiza kai tayi idanuwanta suka fara cikowa da hawaye


"Jaana dan Allah kayi hak'uri bazan iya ba........


Ya k'ura mata ido zuciyarsa na bugawa dasauri


"Chuchu idan kika hanani yin abunda zuciyata take muradi ahalin yanzu,wallahi zanshiga wani Hali,kitausayamin please......



Zuciyarta tafara karyewa,hak'ik'a tana tsananin k'aunarsa tana son tafaranta Masa, Amma yazatayi?idan wani abu yasamesa fa?


Kuka tafarayi  me cike da tsananin damuwa


Yasauke numfashi me nawi


Tare da jinjina kai

"Shikenan ya Isa,tunda bakyaso shikenan"


Yak'arasa fad'a Yana sakinta yakoma kan kujera yazauna,ya lumshe manyan idanuwansa shikad'ai yasan halin dayike ciki


Kuka takeyi sosai tarasa yadda zatayi da rayuwarta


Sun d'auki lokaci ahaka,daga bisani yataso yadawo inda take durk'ushe



Zatai magana ya katseta ta hanyar cewa

"Karkice komai,nafahimceki,bazan tab'a yimiki abunda bakyaso ba,akullum burina infarantamiki,danhaka kada kidami kanki zancigaba da hak'uri har zuwa sanda zakiyi niyya"


Takallesa da jik'akk'un idanunta da sukayi luhu-luhu tace


"Wallahi inason infaranta maka kaima kasani Amma...........



Yatsunsa biyu y d'aura akan lips d'inta


"Nace nafahimta,tashi muje kiwatsa

Ruwa kikwanta"


Tamik'e tanajin zuciyarta babu dad'i



Dakanshi yashiga yahad'amata ruwan wanka tashiga


Kafin tafito haryaciro mata kayan bacci,hakan yak'ara mata tausayinsa sosai


Bayan tasa kayan tazauna kusa da shi tare da kama hannunsa ta matse cikin nata


Cikin murya me taushi tafara magana


"Jaana kagafarceni,nasan hukuncin duk macen da tak'i zuwa shimfid'ar mijinta,nasan mala'iku ke tsinemata har gari yawaye


Amma.......


D'aga mata hannu yayi yace


"Nacemiki nafahimceki meyasa kikeson nanata abu d'ayane,alfarma d'aya kawai Nike so kimin"


Kallonsa tayi suka had'a ido


Yacigaba dacewa


"Inaso muraba d'aki wajen kwanciya,kikwana a naki in kwana anawa,saboda aduk sanda nike tare dake hankalina tashi yikeyi.........



Ta katseshi 


"Jaana amma kasan bazan iya kwana a d'aki ni kad'ai ba ko?


Ya jinjina kai


"Nasani amma hak'uri zakiyi, Kamar yadda kika rok'i alfarmar in k'yaleki nakuma k'yaleki



Nima kimin wannan alfarmar dan Allah ta wannan hanyarce kad'ai zansamu sa'ida"



Kasa cewa komai tayi, kallonsa kawai takeyi



Yamik'e Yana tambayarta


"Akwai wani abun da kike buk'ata ne?


Ta girgiza kai alamar aa


Yace


"To shikenan zanje inkwanta,kiyi addu a kafin kiyi bacci kinji?


Gyad'a Masa kai kawai tayi zuciyarta cike da fargaba


Ya durk'uso yanayimata murmushin k'arfin Hali tare da manna mata kiss a goshinta


"Good night''


Yafad'a yana ficewa daga d'akin tare da rufomata k'ofa


Ajiyar zuciya tasauke gabanta nafad'uwa,



Shiko Umar bedroom d'insa yashiga,yashiga toilet tare da sakar ma kansa ruwan sanyi



Dafa bangon bayin yayi ruwan na sauka ajikinsa 



Ya runtse idanuwansa yana tunanin yadda ze b'ullo ma al'amarin,shikad'ai yasan irin feeling d'in da yikeyi akanta


Zuciyarsa ta haskomata kyakkyawar k'irarta


Yakuma runtse idon yana dun'k'ule hannunsa yabuga a bango


"Why Rauda?meyasa bazaki fahimci yadda kike araina bane?


Yafurta ahankali


Janyo tawul yayi yad'aura ya janyo wani yana goge gashin kansa


A gaggauce yasanya kayan bacci yafad'a Kan gado


Yayi rub da ciki,tsananin sha'awarta na kuma taso Masa.



Itako tana zaune gefen gadon tana rarraba idanu,dan gani takeyi kamar zataga wani abun tsoro


Kallon agogo tayi k'arfe shad'aya da minti arba'in


Haka tacigaba da zama tana dube-dube ahaka bacci yafara d'aukarata


 

Sama-sama taji andafa mata kafad'a,tabud'e ido cikin yanayin bacci tana kallon kafad'ar,wasu dogayen yatsu tagani bak'ak'e sid'ik tare da zak'o-zak'on k'umbuna


Wartsakewa tayi dasauri tana k'ara kallon kafad'ar


Still hannun yana kafad'ar ta


Azabure tamik'e tana kallon kan gadon,babu kowa akai


Motsi tafara ji ak'asan gadon, hakan yatabbatar mata abunda yatab'atan yana k'ark'ashin gadon



Hanyar fita d'akin tayi,ta murd'a hannun k'ofar amma gam tak'i bud'ewa,



Tafara jijjiga k'ofar da ka k'arfi gabanta na wani mugun fad'uwa



Shafata wuya akayi tabaya


Ta k'wala ihu tare da juyawa a razane 


Wayam babu kowa,bubbuga k'ofar tayi tana kiran sunan Umar,amma shuru 


Tazame k'asa tana numfarfashi,


Wani kalan gurnani tafaraji me tsoratarwa yana fitowo daga cikin bayi


 

Bam!


Aka banko k'ofar bayin,runtse idanuwanta tayi dasauri tana ambaton sunan Allah Dan tasan shikad'ai ze kawomata agaji


"Habibty!


Taji anfad'a cikin wani irin salo


Tabud'e idanuwanta dasauri tana kallon inda tajiyo Kiran


Aasim tagani kwance kan gadon ya kishingid'a da fulo


Yanayimata wani irin kallo da idanuwansa masu d'auke da k'wayar ido kalar golden


 

Yacigaba da cewa

"Barka dai habibty,barka da dare"



Yarrr yarrr tsigar jikinta ta tashi,ba bu inda baya rawa ajikinta


Addu'a kawai takeyi


Dariya yafarayi yanacewa


"Nazo tayaki kwana ne bazaki yimin maraba ba?


"Dan.....Dan.....Allah...kayi.... hak'uri'


Tace cikin rawar murya da tsananin razana



Dariya yakuma yi akaro na biyu 


"Gabad'aya ni natsani kalmar hak'uri,dan haka kada kik'ara ambaton hak'uri agabana,kitaso ki hawo kan gadon"



Girgiza kai tayi jikinta na kyar-kyarwa kamar wacce akaciro daga cikin k'ank'ara



Yagyad'a kai yana murmushin k'asaita


"Kinfi kowa sanin bana nanata magana sau biyu,idan bazaki taso ba to akwai wad'anda zasu taso dake



Yana gama fad'a kuwa taji anciccib'eta and'agata sama amma kuma bata ganin wad'anda suka d'agatan


Tana ihu kuma amma ihun baya fita



Kan gadon aka direta, gabad'aya jikinta ya mutu bata da kuzarin dazata iya guduwa


Duk surar datazo bakinta karantawa takeyi


Yayi murmushi tare da cewa


"Tun kan asan za a haifeki nike karanta al'qur ani,yanzuma zanso ace ni nike karantamiki tunda naga arud'e kike wasu ayoyinma ba dede kike karantasu ba"


Cikin tsananin tsorata tace.

"Menayi maka ne da kake bibiyar rayuwata,meyasa bazaka k'yaleni nayi rayuwa kamar yadda sauran al'umma sukeyi ba,meyasa!



Yayi guntun murmushi


"Sabida ba'ayiki dan kowa ba,anyiki ne danni kad'ai,kuma dani kad'ai zaki rayu,ina sonki habibty bazan tab'a iya rayuwa babu keba.........



Cikin kuka tace


"Wannan ba so bane,zalunci ne.........


Bata k'arasa ba ya damk'o gashin kanta yana kallon fuskarta


"Kada ki kuskura,ki zageni,kinsan halina sarai"


Ya matso yana gogga fuskarsa me zagaye saje a wuyanta


"Hak'ik'a kinacin albarkacin son dankeyi Miki,shiyasa nike k'yaleki,amma da tuni na b'atar dake a duniya,Dan babu mahaluk'in da ya isa yafad'amin maka manciyar abubuwan dakike fad'amin batare dana shafe labarinsa ba!



Runtse idanuwanta tayi wasu hawaye masu zafi suna gangaro gefen kuncinta



"Rauda!!!!!!


Yakira sunanta


Tabud'e ido tana kallon sa


"Kicire tunanin cewa zanrabu dake arayuwa,Dan wallahi babu wani malamin da ya Isa yarabani dake"






Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

           AASHIQUE🌹



              NA 

HARIRA ALIYU (y'arfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu


_Kuna a raina yan uwana yan *Golden Pen*  hadin kanku na burgeni hakika kun cika Zinarai, kuma yan Amana, inama yan k'ungiyoyi zasuyi kuyi daku yan uwana, da tabbas zasu samu ci gaba, wlh *Golden Pen* kun hadu dari bisa milyoyi, bani da abunda zan baku shiyasa na baku wannan page  kuyi yan da kukeso dashi na bakushi kyau ta,👌_



🅿AGE📕 7⃣


Bissmillahir rahmanin rahim



"Rauda!!!!!!


Yakira sunanta


Tabud'e ido tana kallon sa


"Kicire tunanin cewa zanrabu dake a rayuwa,Dan wallahi babu wani malamin da ya Isa yarabani dake"


Tanaso tayi magana amma taji bakinta yayi mata nawi takasa motsashi,kamar yadda takasa motsa koda d'an ya tsanta



Yakuma yin murmushi yana shafa lip's d'inta da yatsansa


"Wani hukunci yakamata inyima wannan labb'an?dasuka bari wani ya tsotsesu"


Yad'an rausayar dakai cikin yanayin nishad'i


Bakisan cewa wa'annan kyawawan labb'an suna d'aya daga cikin manyan dalilan dana kasa rabuwa dake ba??


Hmmmmmm yasauke numfashi

Sannan yacigaba da cewa


"Kada ki sake,habibty kisani komai na jikinki mallakina ne nikad'ai"


Ya matso da fuskarta kusa da tasa,dan har lokacin gashin kanta na damk'e a hannunsa


Kallon lips d'inta yikeyi


"Hukunci d'aya zanyima labb'an Nan,zanta shansu har gari ya waye"


Tanaji yafara tsotsar lips d'in cikin wani salo na mugunta


Bata da ikon hanasa dan bata da yadda zatayi, in Banda rad'ad'i babu abunda lips d'in kemata



Wani kalan yanayi taji tafara shiga, ahankali tunaninta yafata tsayawa taji kanta yanayimata waiwayi take wani kalan bacci me cike da wahala ya d'auketa.



B'angaren Umar ko kai-kawo yike tayi acikin d'akin


Ahankali yaji mararsa tayi wani k'arfi tare da fara ciwo


Ya kwanta a k'asan kafet hannunsa dafe da mararsa


Da k'yar bacci ya d'aukesa


***   ***   ***


Washegari,ana kiran assalatu tafarka, tabud'e idanuwanta dasukayi mata nawi tana kallon cikin d'akin


Babu kowa aciki,jitayi bakinta nayimata zugi ahankali k'wa-k'walwarta tafara tariyomata abunda yafaru


Ajiyar zuciya tasauke tatashi daga kwanciyar datake ta jingina da jikin gadon


Gani takeyi kamar mafarki take,amma kuma tasan ba mafarkin bane


Nannauyar ajiyar zuciya tasauke  tana tunanin yadda zata cigaba da rayuwa da aljani amatsayin mijinta bayan kuma ga nata mijin yanaso yarabata dashi


Mik'ewa tayi tashiga bayi tad'auro alwala,tagabatar da sallar Asuba


Sannan tafito falon lokacin gari yafara haske, bedroom d'insa ta nufa dan bataji fitowarsa sallah ba


Ta tura k'ofar d'akin tana sallama


Yana kwance k'asan kafet yatakure guri d'aya


A sanyaye ta k'arasa inda yike ta durk'sa tana kallonsa cike da tausayinsa


"Na k'osa muyi aurannan chuchu,inhuta da kwanciya nikad'ai,yazamana kullum ina manne dake ina shak'ar daddad'an k'amshinki"


Maganar umar tadawo mata



Sassanyar ajiyar zuciya tasauke tasa hannu a gefen fuskarsa tana shafawa ahankali


Ya bud'e idanunsa ya watsasu akanta dama ba baccin yikeyi ba ya farka tuntuni


Kallon juna sukayi sosai

Daga bisani ya sakarmata guntun murmushi


"Madam har kintashi?


Ta d'aga masa kai alamar eh tare da cewa


"Kaima yakamata katashi kayi sallah"


Ya yunk'ura ya mik'e zetashi,mararsa tayi wani mugun k'ullewa


Dasauri yakoma yazauna yana d'an runtse idonsa alamar ciwon na damunsa


Rauda tace

"Lafiya jaana?


Guntun numfashi ya sauke yana bata amsa

"Cikinane ke ciwo"


Cikin tausayawa tace

"Sannu,tunyaushe yafara ma?


"Cikin dare amma nasha magani nasan zebari nan bada jimawa ba"


Ta gyad'a kai tare da mik'ewa

"Allah yak'ara sauki bari inhad'ama ruwan wankan"


Bayin tashiga tahad'a mai tafito tace ta had'a


Saida yashiga sannan tafito da ga d'akin tashiga kicin


A gurguje ta had'a abun kari,tana cikin jerawa,yasauko


Ya zauna yanayimata sannu


Itama tazauna suna fuskantar juna tafara tsiyaya ruwan zafi a Kofi


Kallonta yikeyi anatse ya lura da lips d'inta dasukayi ja

Yace

"Chuchu meyasami lips d'inki?


Kallonsa tayi tana ajiye kofin


"Babu komai"


Ze kuma magana mararsa takuma k'ullewa


Dasauri ya dafa cikinsa,tasowa tayi dasauri ta dawo inda yike tana tambayar


"Jaana cikinne?


Ya d'aga mata kai kawai


Hankalinta yatashi

"Fad'amin inda maganin yike in d'auko maka"


Ya girgiza Kai

"Aa,d'auko min wayata kawai inkira doctor zainab nasan yanzu bata wuce asibiti ba sai ta biyo takawomin allura"


Tad'auko mai wayar tamik'amai har lokacin yana dafe cikinsa


Ya lalubo numban doctor zainab yadanna


Ringing  biyu  tad'auka tana fad'in ango kasha k'amshi


"Kinwuce asibiti ne?


Tace aa


"Yace kibiyo please banad'an jin dad'i"


Daga can b'angaren doctor zainab tace

"Subhanallah meke damunka?


Yafad'a mata

Tace

"To shikenan ganinan zuwa yanzu insha Allah"


Ya ajiye wayar Yana mik'ewa da gyar


"Bari naje nakwanta kafin tazo,kibiyoni da Lipton d'aki"


Ta jinjina kai cikin damuwa tana bin bayansa da kallo haryashige


Sannan tasauke ajiyar zuciya,ta had'a Lipton d'in tabishi da shi



Ya amsa yana kurb'a kad'an-kad'an


Hannunta yakama ganin yadda duk tashi ga damuwa


"Chuchu bafa wani abu bane,inayin alluran zedena dama nasaba irin ciwon kada kid'aga hankalinki please"


Hmmmmmm tasauke doguwar ajiyar zuciya


Knocking d'in k'ofar falon akafarayi taje tabud'e


Doctor zainab ce,suka gaisa sannan tayimata jagora zuwa d'akinsa.


Sama-sama ya amsa gaisuwar doctor zainab dan ciwon ya matsamasa


Doctor zainab ta fahimci abunda yike damunsa tsaf hakan yasa data mai allura zata wuce tacema Rauda tana son magana da ita


A falo suka zauna,Rauda zata had'amata tee tacemata tabarshi ta k'oshi tazauna suyi maganar kawai


Bayan sun zauna doctor zainab takalleta sosai tace


"Kinayin al'ada ne?


Rauda takalleta tana mamakin tambayar


Doctor zainab tayi murmushi tare dacewa

"Kiyi hak'uri inason infahimci wani abune"


Girgiza mata kai Rauda tayi 

"Aa banayi"


Doctor zainab ta jinjina Kai


"Amma meyasa kik'i yarda da mijinki?


Cikin rashin fahimta Rauda take kallonta


Doctor zainab tayi murmushi tana cigaba dacewa


"Nasani yawancin y'ammata idan akakawosu gidan auransu sukank'i yarda da angwayensu,badan komai ba sai dan tsoro


Kuma dama tsoro wajibine ga duk macen da takai budurcinta gidan mijinta


Amma yanzu kai ya waye andaina wannan k'in amincewar,kuma miyema abun gudu ga wanda yazama muharraminka?


Bakisan idan Sha'awa tayiwa namiji yawa tana iya halaka saba?


Wannan ciwon cikin dakikaga yanayi somin tab'i ne inhar bazaki yadda da mijinki ba


Tad'an dakata sannan tacigaba da cewa


"Dan allah ki ajiye wani tsoro da fargaba agefe ki bawa mijinki kulawa kinji?


Gyad'a mata kai kawai Rauda tayi tana nazarin maganganunta


Doctor zainab tamik'e tana d'aukar jakarta.


"Nizan wuce nasan yanzu yasamu bacci dan allurar tanasa bacci sai anjima"


Rauda tamik'e tayimata rakiya zuwa k'ofar falo sannan takoma d'akinsa


Ganin yasamu bacci yasa ta janyo mai k'ofar tadawo falo tana nazarin abunyi


Gabad'aya tarasa yadda zatayi,wayarta tad'auko tadanna numban aminiyarta Salma bugu d'aya salma ta d'auka tanacewa


"Amarya kinsha k'amshi,sai yau akatuna dani?anata ragargazar amarci?


Rauda tasauke ajiyar zuciya cikin damuwa tace

"Salma ina cikin matsala bansan ya zanyi ba"


Daga can b'angaren salma tace

"Subhanallah matsala kuma Rauda?


Rauda tafashe da kuka 

"Salma bansan yazanyi da rayuwata ba,inaganin na tsallake rijiya da baya ashe bansani ba cikin rijiyar nafad'a"


Cikin tashin hankali Salma tace


"Nashiga uku ni Salma,me yafaru Kuma?


Rauda takwashe komai tafad'a mata


Hak'ik'a Salma ta kad'u da jin labarin

Tama rasa abunda zatace


Zuwa can tasauke numfashi tare da cewa


"Kenan Aasim kwantan b'auna yayi,yayi kaman yarabu dake ashe azzalumin yananan......


Rauda tayi saurin katseta

"Aa Salma karki zagesa wallahi ayanzu yawuce duk inda kike tunani"


Salma tasauke doguwar ajiyar zuciya


"Hmmmmmm yanzu miye abunyi Rauda?danni wallahi kaina ya kulle"


Itama Rauda ajiyar zuciyar tasauke


"Ni yanzu damuwata d'aya cewa dayayi Umar ze mutu idan har ya kusanceni,gashi umar yana matuk'ar buk'atata, kifad'a min yadda zanyi please Salma,ke kad'aice wacce nike iya gayama damuwata"


Salma tasauke numfashi


"Ina ganin kaman yafad'a miki hakane dan ya tsorataki, Amma baze iya kashesa ba, Dan ina tunanin umar yafi k'arfinsa tunda har yabari kika auresa"


Ta girgiza Kai

"Bana tunanin hakan"


Salma tace

"To yakamata munemi wani malamin Rauda,zan k'ara yin tunani anjima inga yadda za'ayi amma kafinnan kinsan y'ar dabaran dazakiyima umar d'in dan ki rage masa feeling d'in"


"Shikenan saina jiki anjiman"


Rauda tafad'a tare da aje wayar


Tanaciga da lulawa cikin tunani


Sai k'arfe biyun rana yatashi tana zaune agefen sa


Tasha fa gefen fuskarsa tana cewa da tausassar muryarta


"Jaana,yajikin?cikin yadena ciwo?


Yayi murmushi yana bata amsa

"Yadena chuchu,saidai kukan yunwa dayikeyi"


Tamaida mai martanin murmushin

"To alhamdulillah,kawatsa ruwa bari ind'auko ma ferfesun kifin danayima"


Yagyad'a kai yana mik'ewa

"To madam"


Fitowa daga d'akin tayi tashiga kicin tabud'e kular data zuba ferfesun kifin tare da d'auko plate zata zuba?


Saidai me a memakon taga kifin saitaga manyan b'eraye kwance acikin kular da alamu sun dahu sosai sai uban turiri sukeyi"


Mamakine ya kamata kodayike ba abun mamaki bane dantasan zata iya ganin abunda yafi hakama ayanzu


Rufe kular tayi tad'auka ta wurgata dustbin


Ruwan indomie ta maida tana tsaye har indomin ta nuna tajuye a plate  


Tadawo d'akin lokacin yafito da wanka yana sallah


Tazauna tanajiran ya idar,yasallame sallar yana shafa addu'a


Sannan ya juyo yana dubanta


"Madam yadai?


"Dede"

Tafad'a tana ajiye plate d'in agabansa


   Yayi murmushi tare da kamo hannunta yazaunar da ita a k'asa inda yike zaune


"Ai tare zamu ci,dannasan kema baki ci abincin rana ba"


Bata mai musu ba sukaci indomin tare


Bayan sunkammala yace

"D'azu bayan fitarki zayyad ya kirani akan maganar danamai na malaminnan,yace ze turomin numban malamin inyaso sai muyi masa bayani"


Tagyad'a kai

"To allah yasa mudace"


Ya amsa da amin


Daddare suna zaune a falo wuraren misalin shabiyu nadare


Yakalleta yana cewa

"Madam tashi inrakaki kije kikwanta"


Marai-raice fuska tayi tana kallon sa

"Allah yau bazan iya kwana nikad'ai ba,jiya nikad'ai nasan abunda nagani"


Hmmmmm yasauke numfashi


"To yanzu yakike so ayi?.


"Mukwana tare,wannan tsarin naraba d'aki a sokeshi please"


Yayi guntun murmushi

"To shikenan tashi muje,a wani bedroom d'in zamu kwana?naki ko nawa?


"Naka"


Tafad'a

Yace

"Ok tashi muje"


Yakashe kayan kallon 


 Bedroom d'inta yafara rakata dan tasa kayan bacci tabud'e wardrobe d'in kayan baccin tana tunanin wanda zata sa


Umar ya d'auko wata maroon d'in riga yamik'o Mata


"Naga sai ruwan ido kikeyi kisa wannan"


Murmushi tayi ta amsa


Yakauda kansa yayinda takesa rigar dan bayaso yaga abunda zetada mai hankali


Takammala sa rigan tace

"Muje"


Suka rufe bedroom d'inta suka shiga nasa


Zama tayi bakin gadon tana duba addu'o in da salma taturomata


Shiko canza kayan yikeyi yana kallonta,wani irin feeling d'inta na taso Masa


Tun yana kauda abun aransa haryaji baze iya ba


Jingina yayi da bangon d'akin yana maida numfashi ahankal


Tad'ago tana kallonsa


"Lafiya jaana?


Ya girgiza kai batare dayace mata komai ba


Ajiye wayar tayi tataso,tana k'ara tambayar sa


"Jaana cikinne?


Yabud'e idanuwansa ahankali yana kallonta


Rigar tabi jikinta sosai


Jiyayi wani abu na fizgarsa da k'arfi


Besan sanda ya janyota yamannata da jikinsa ba yafara kissing d'inta ta ko Ina


"Jaana!


Be saurareta ba ya sureta ya ajiyeta kan gadon yana cigaba da kissing d'inta


"Jaana please kabari sai munje gun malamin tukunna banaso wani abu yasameka.....


Rufe mata bakin yayi da nasa,takasa k'arasa abunda zatace


Shasshafata yashiga yi ta ko Ina yana sauke wani numfashi a wahalce


Bakinta dake cikin nasa yasaki yamaidasa kan wuyanta  


Yanacigaba da kissing d'inta ta ko ina



 Wata irin iskace da guguwa ta turniki'e d'akin



Lokaci d'aya, hankalinta yatashi jin batajin motsin Umar,    tabud'e idanuwanta a firgice data rufe yayinda guguwar ta turnik'e d'akin


Aasim tagani tsaye idanuwansa sunyi jawur yana nuna wani abu da hannunsa


Dasauri takalli abunda yike nunawan, Umar ta hango can saman d'akin jijiyoyin wuyansa sun mummurd'e idanuwansa sun firfito waje


Ta zabura tamik'e jikinta yafara rawa

"Narok'eka kada ka kasheshi,dan girman allah"


Ko kallonta beyi ba,ta taso dasauri tana nufar inda yike


"Dan girman allah narok'eka........


Da razanannun idanunsa yayimata wani kallo


Wani irin haske yafito daga cikin idonsa


Wata iskace tad'auketa tahad'a  da bango wanda kanta yayi mugun buguwa


Durk'ushe wa tayi tana kuka tana cigaba da rok'onsa


"Wallahi bazan k'ara sab'a ma umarninka ba,duk abunda kace inyi zanyi amma dan allah kada karabasa da rayuwarsa


Kuma kallonta yayi idanuwansa nakuma rinewa


Yafara magana muryarsa nafita bibbiyu


"Kina ganin kamar bazan iya abunda nace ba ne ko,to yau zanbaki mamaki!!!!


"Wallahi bazan k'ara sab'a ma ka ba nayi alk'awari,kada ka kashesa dan allah"


Hannunsa yaja baya, umar yafad'o daga saman yazube a k'asa yana maida numfashi sama-sama dan ya wahala matuk'a


Dagudu tatashi ta isa gun Umar tana jijjigasa tana kiran sunansa


"Kisani ayanzu dama biyu zanbaki,ko kisa yasakeki ko kuma ki rasasa gabad'aya"


Yana gama fad'ar haka ya b'ace


Hankalinta yayi matuk'ar tashi jijjigasa kawai takeyi


"Jaana katashi karkata fi kabarni......


Yabud'e idanuwansa a wahalce yana kallonta


Ahankali yamaida idanunsa yarufe


Kuka takeyi sosai tana jijjigasa


"Ayanzu dama biyu tarage miki, ko kisa shi yasakeki kokuma kirasasa gaba d'aya"


Maganar Aasim tadawo mata


Hannunta tasa a k'irjinsa da sauri,jin yana numfashi yasa ta mik'e tad'auki wayarsa jikinta na rawa ta lalubo numban zayyad tadanna Kira


Zayyad naganin kiran yasan ba lafiya ba,ya d'auka Jin muryar Rauda yasa yace


"Lafiya Rauda?a darennan ina umar d'in?


Muryarta narawa tace


"Zayyad kazo kataimakeni Umar ze mutu"


Mik'ewa zayyad ya yi daga kujerar da yike na office dan ranar Yana asibiti duty d'in dare yikeyi


"What?meyasamesa


"Kazo yanzu dan Allah"


Kawai tafad'a tana ajiye wayar tana cigaba da kuka


Shima aje tashi wayar yayi yafito dasauri yashiga motarsa


Gudu yike yi sosai har ya kawo gidan,saidayayita horn sannan me gadi yabud'e dan shi baccinsa yikeyi besanma wainar da ake toyawa ba


A tsakar gidan yayi parking yafito dasauri yana bubbuga k'ofar falon


Tana rungume dashi tana kuka taji ana bubbuga k'ofar


Tasan zayyad ne ta tashi har lokacin jikinta narawa taje tabud'e k'ofar


Ganin yanayin datake ciki yasa zayyad tambayar ta dasauri


"Ina Umar d'in?


D'akinsa ta nunamai da hannu kawai dan tama kasa magana


Yashiga d'akin,ganin halin da umar ke ciki yatada mai hankali sosai


Ciccib'osa yayi yafito dashi tana tsaye gabad'aya ta firgice 


"Maza d'auko mayafinki muwuce asibiti"


Hijabin datake sallah dashi dake gefen kujera tad'auko tazura,yashimfid'eshi abayan motar


Yatada,zata shiga baya yace aa tashiga gaba dan ba inda zata zauna abayan


 Yafigi motar aguje yana kuma tambayarta


"Kifad'a min meyasamesa?


Bakinta narawa tace


"Aasim...Aasim....


Yakalleta da sauri dayike yasan duk abunda kefaruwa


"Aasim?


Ta jinjina mai kai


Yasauke numfashi yana cewa


"Shikenan idan munje asibiti koda za atambayeki ace meyasamesa kice accident yayi kinji?


Ta gyad'a mai kai kawai tanajin kanta kamar ze juye


Suna isa asibitin akabashi taimakon gaggawa


 Lokacin da doctor zayyad da nurses suka fito biyu saura


Ta taso daga durk'usan datayi tana kallon zayyad


Kafin ta tambayesa yace


"Kikwantar da hankalinki yadawo cikin hayyacinsa yanzu amma yasamu bacci kina iya shiga"


Tatura k'ofar d'akin tashiga


Zayyad yabita da kallon tausayawa


A kujerar da ke gaban gadon tazauna tana kallonsa


Lokaci d'aya harya fad'a,tana zaune tana kallonsa har asuba inbanda kuka ba abunda takeyi


Lokacin yafarka,ganinsa a asibiti yasa k'wa-k'walwarsa ta tariyo masa abunda yafaru


Cikin kuka taruko hannunsa tanacewa


”kayi hak'uri,duk sanadina kashiga wannan halin.....


Ya girgiza kai yana cewa


"Hak'urin mekike bani chuchu?


Kuka yacigaba dayi cikin tsananin damuwa


Ajiyar zuciya yasauke me nawi


Tare da sa hannu ya share mata hawayen da suke bin fuskarta


"Saiyanzu nafahimceki chuchu, saiyanzu na fahimci abundance yasa kika k'i yarda Dani, Amma inaso kisani babu abunda zesa inrabu dake

Inatare dake duk runtsi duk wuya"





Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 *_JINNUL_*

        *_AASHIQUE_*🌹



                 NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/




Dedicated to Little hajjo and my elder sister



🅿AGE📕 8⃣



_Wannan page d'in nakune masoya jinnul aashique,na sadaukar dashi gareku,saboda k'aunarku ga littafin,ina godiya ga yadda kuke son wannan labari allah yabar zumunci,sannan ina baku hak'uri akan dad'ewa danikeyi bana typing insha allahu zanyi k'ok'ori inga ina yin yadda yadace nagode._



*_GAISUWA ga Aishatu Babayo Jos,ina godiya da kulawarki gareni,ba irin su o'o ba @maman ummi,dan inbanda tsokana babu abunda ta iya ba😜 amma dai duk da haka kema ina gaisuwa_*



_ADDU'A Ga besty safiyya maina,allah yabaki lafiya yasa kaffarane_



Bissmillahir rahmanir rahim👏🏻


Ta girgiza Kai cikin kuka tace

"Yanzu inane keyimaka ciwo?


Ajiyar zuciya yasauke dan babu inda bayamasa ciwo ajikinsa amma dan kada yak'ara tada mata hankali yasa yace


"Chuchu nifa naji sauk'i yanzu,wuyanane kawai ked'an yimin zafi,kuma shima nasan zuwa anjima zedaina insha allahu"



Ta kwantar dakanta agaban gadon

"Jaana tunanina yafara raguwa,Ina tsoron watarana k'wak'walwata ta juye danjina nikeyi kamar na kusa haukacewa"


Numfashi yasauke me nawi zuciyarsa cike da tarin damuwa dan shima tunanin nasa ya tsaya yarasa ta inda ze b'ulloma al'amarin,ada yayi tunanin al'amarin mesauk'i ne amma daren jiya yatabbatar mai da al'amarin Aasim ba k'aramin babban al'amari  bane


Idanuwansa ya runtse yana furta ya rabb!


Ahankali

K'arfe takwas doctor zayyad yashigo d'akin yana sallama


Umar ne ya amsa mai,dan ita Rauda baccine yad'auketa me tattare da ciwon kai me tsanani


Zayyad yajanyo wata kujera yazauna yana duban umar


"Yajikinnaka?


"Dasauk'i"

Ya amsa mai


Zayyad yace

"Jiya cikin dare Rauda takirani tace inje kana cikin wani Hali dana tambayeta meke faruwa sai tace min Aasim,wai meke faruwane Umar?


Umar yasauke numfashi yana cewa


"Zayyad yanzu ba lokacin dazanyima bayani bane amma aikasan bana b'oyemaka komai"


Zayyad ya jinjina Kai

"Hakane,to yanzu inane kedamunka ajikinka?


"Wuyana,yanamin zafi da ciwo sosai kad'auko alluran....... yafad'a mai sunan alluran sannan yacigaba da cewa


"Kayimin,koze d'an lafamin"


Zayyad yamik'e yafice daga office d'in batare da yakuma cewa komai ba amma zahiri yana cikin damuwa da ganin halin da abokinsa keciki


Allurar yad'auko yamasa bayan yagama yace

"Ni zanje gida na dawo"


Umar yace

"To amma da na tashi Rauda ka ajiyeta itama inzaka dawo sai kabiya kad'aukota"


Zayyad yagyad'a kai yatsaya yana dubansu.


Hannunsa yasa Yana d'an bubbuga bayanta yana kiran sunanta


A d'an razane tafarka dan gabad'aya atsorace take


"Chuchu calm down nine"


Umar yafad'a,tasauke numfashi tana kallonsa


"Jikinne?


Ya girgiza Kai

"Aa ni naji sauk'i kitashi zayyad ze wuce ya ajeki agida inze dawo sai ya biya yad'auko ki"


Girgiza kai tayi ahankali


"Ni ba inda zanje,bazan barka kai kad'ai ba"


Hmmmmm chuchu kinmanta da night gawn ne ajikinki kiyi hak'uri kije kicanza kaya ai ba dad'ewa zaki yi ba"


Umar yafad'a,shuru tayi Tana nazari dan gani takeyi kamar idan tatafi wani abunne zekuma samunsa


Gefen fuskarta yashafa

"Tashi kinji nima kitaho min da kaya kala d'aya tunda nasan zuwa dare ko gobe dasafe zamukoma gidan gabad'aya"


Mik'ewa tayi badan ranta yasoba tana tafiya tana waigensa


Harta fice daga d'akin


Tunda suka shiga motar babu wanda yayi magana harsuka iso gidan


Sannan zayyad yace

"Nan da awa nawa zaki kammala abunda zakiyi"


"Minti talatin ma yayi yawa"


Zayyad yayi murmushi

"Kidai shirya atsanake nan da awa d'aya zandawo"


Tagyad'a mai kai kawai tare da ficewa daga motar yaja yawuce.


Tunda ta doshi k'ofar falon ta tsinci kanta da fad'uwar gaba



Tatsaya a bakin k'ofar tanajin kamar kartashiga amma babu yadda ta iya yazamarmata dole


Murd'a k'ofar tayi ahankali gabanta na fad'uwa


Saida tatsaya tana k'arema falon kallo kamar yaune tafara ganinsa sannan tashiga tamaida k'ofar tarufe


Ahankali tafara takawa zuwa step tafara hawa step d'in ahankali


Jitayi k'arar sawun tafiyar bibbiyu


Tad'an dakata da tafiyar tana kallon gefenta


Babu kowa azahiri amma tasan a bad'ini akwai wani awurin


K'arfin halin cigaba da tafiya tayi tashiga d'akinta  


Tana tunanin abunda zata farayi,tana tsoron yin wanka gashi Kuma yazama dole


Ahankali tacire hijabi da rigar dake jikinta  tashiga bayin 


Bata tsaya sa ruwan zafi ba,nasanyi ta tatara   cikin k'an k'anin lokaci tayi wankan daba ta da tabbacin tafita.


Ko mai bata tsaya shafawa ba ta sanya atamfa riga da skirt d'akinsa ta nufa dan d'auko masa kayan


Ta bud'e wardrobe tana tunanin kayan dazata d'auka


Shesshekar kuka tafaraji sama-sama


Tad'an dakata da abunda takeyi tana k'ara kasa kunne dan tabbatar da abunda taji


Sautin shesshekar kukanne yacigaba da k'aruwa kuma da dukkanin alamu daga bayi shesshekar yike futowa


Gabanta yacigaba da fad'uwa 

Kayan tad'auka da sauri tafita daga d'akin 


Ajiyar zuciya tasauke mai nawi tana hamdala da bataga abunda ke kukanba dan tabbata ba alkhairi bane


Saidai me kukan tak'ara ji anayi a falon dake k'asa


Fargaba da tsoro suka k'ara kamata, ahankali tafara saukowa daga step k'irjinta na dukan uku-uku 


Harta gama saukowa can gefe tahango wata tsohuwa kwance tana d'ago mata hannu tana cigaba da kukan


Wani irin lugude k'irjinta yacigaba dayi tana jin zuciyarta na rawa kamar zata fito waje saboda tsananin tsoro


Tama rasa inda zatayi dan dole saitabi gaban tsohuwar kafin tafita waje ita kuma ba abun takoma sama ba taga abinda yafi wanda takegani ayanzu


Sautin kukan tsohuwar nafita tsigar jikin Rauda na tashi 


Jikinta na rawa tafara tafiya tana nufar hanyar fita


Idanun tsohuwar akanta tana cigaba da kukan


Tazo saitinta da addu a abakinta tana shirin rugawa


Tsohuwar tatashi tazauna gashin kanta ya barbazu a ajikinta


Dukda akwai tazara atsakaninsu sosai amma hannu kawai tsohuwar tasa tajanyo wuyanta 


Tsananin tashin hankali da tsorata Rauda tashiga,hannunta tasa ta na k'ok'orin b'an-b'are na tsohuwar amma takasa


Dan gam ya manne da wuyanta 


Cikin wata kalar murya me tsoratarwa tsohuwar tace

"Babu inda zakije ki gujemana,duk inda kikaje muna tare dake"


Runtse ido Rauda tayi dan kallon fuskar tsohuwar na k'ara razanata 


Jin shuru yasa tabud'e idanuwan a tsorace saidai wayam bataga kowa ba babu tsohuwar


Abun mamaki kuma ganinta tayi a d'akin umar gaban wardrobe d'insa


Ita da har tad'auki kayan tafita falo ya akayi kuma taganta a d'aki


Jikinta narawa tabaro d'akin tana k'ara kallon inda taga tsohuwar


Amma babu kowa awurin


Ficewa tayi dasauri tamaida k'ofar tarufe sannan ta jingina da k'ofar tana maida numfashi


Ahaka zayyad yadawo yatadda ta


Tana ganinsa ta taso tashiga motar dan jinta takeyi kamar akan k'aya take


Kallon ta zayyad yayi sosai take yafahimci firgici atare da ita hakan yasa shi tambayarta yace


"Rauda lafiya naganki atsorace haka?


Ta jinjina mai kai 

"Lafiya"


Yagyad'a nashi kan yana cigaba da tuk'in


 Suna isa asibitin ko parking begama yiba tafito


Dan gani takeyi kaman wani abu ya samu umar.


Da hanzari ta ke tafiya har ta isa d'akin


Ganin sa jingine yasa tasauke ajiyar zuciya


Kallonta yayi ganin yadda tashigo a hargitse


"Lafiya madam?


K'arasawa tayi bakin gadon saikuma ta fashe da kuka


Hannunta yakama yazaunar da ita kusa dashi yace


"Mekuma yafaru chuchu?

Cikin kuka tace

"Bazan iya cigaba da zama agidannan ba,bazan iya ba......


Ya sauke numfashi me nawi,tare da fara rarrashinta


"To shikenan, kukan ya isa haka,ya isa"


Yafad'a yana d'an bubbuga bayanta


Saida tadena kukan,sannan ya k'ara tambayar ta


"Mekika gani yau Kuma?


Ta fad'a Masa,yayi ajiyar zuciya yana nazarin abunda tafad'a mai sannan yace


"Inaganin gobe idan allah yakaimu mutafi katsinan kawai gurin malamin da zayyad yace"


 Ta jinjina Kai kawai batare data k'ara cewa komai ba



Daddare tana zaune kusa dashi yafarayin bacci, itama gyan-gyad'i ne yafara d'aukanta


Taji ana k'wan-k'wasa k'ofar


Ta mik'e taje tabud'e

Doctor zayyad tagani,yace

"Yihakuri kinfara bacci natasheki ko?


Tayi d'an murmushi tace

"Aa babu komai"


Yagyad'a kai

"Dama akwai allurar daban masa bane saiyanzu na tuna shine nazo inmasa"


Tad'an kallesa tanacewa

"Ba d'azu kayimasa ba?


Ya d'aga kai alamar eh sannan yace

"Wannan watace daban"


Shuru tad'an yi daga bisani tabashi hanya tanacewa

"Gashi kuma yayi bacci  natashesa kenan?


Ya girgiza Kai

"Aa basai kintashesa ba,ai allurar bata baya bace ahannu za aimasa"


Tace to tare da zama tana kallon Umar d'in


Yakama hannun yana tsira mai allurar


Kallonsa tayi sosai ganin ko jijiya be nema ba amma yanayin allura

"Doctor dama ana allura ba a nemi jijiya ba?


Be bata amsa ba yacigaba da abunda yikeyi


Jin yayi mata shuru yasa takuma cewa

"Doctor magana nikeyi fa"


Still banza yayi da ita,cikin idanuwansa takalla taga k'wayar idonsa golden


Azabure tamik'e lokacin yagama allurar yazare yana wani mugun murmushi



Dede lokacin Umar yafarka


Jikin Rauda na rawa tace


"Allurar me kamasa zayyad...


Kasa k'arasawa tayi yayinda ya kauda fuskar zayyad dayayi amfani da ita fuskarsa ta bayyana


Subiyun duka suka zaro ido suna kallonsa


"A..asim"

Tafad'a cikin rawar murya


Yashafa gefensa da hannunsa saiga wata kujera tabayyana


Yazauna har lokacin da murmushin mugunta a fuskarsa


Zatai magana ya katseta tahanyar cewa


"Kafin kitambayeni bari ni na baki amsa,danna san tambayar ki bazata wuce"allurar mekamasa ba"


To allura ce wacce ruwan dake cikinta yike d'auke da abubuwa da dama,zanfad'a miki kad'an daga ciki


Dafarko dai tana d'auke da guba wacce bata kisa amma tana shiga cikin k'ashi da b'argo da kuma jijiyoyin mutum,ta rink'a rugurguza k'ashi tana tsittsinka jijiyoyi,abu nabiyu shine takan saka mutum ya cutar da kanshi yanaji yanagani batare da ya iya hana kansa ba,


Sannan tana d'auke da abubuwan dasuke canza halittar d'an adam"


Yad'an dakata sannan yacigaba dacewa 


"Wannan kyauta ce daga gareni,kuma kinsan makarin wannan guba??


Magani ko wani abu baze tab'a karyata ba face saki


Yafad'a yana maida kallonsa ga Umar sannan yacigaba


"Kaga saika zab'a,ko lafiyarka kokuma zama da matarka"


Umar yatashi daga kwanciyar dayayi daky'ar yana dubansa cikin dakewar zuciya yace


"Duk wad'annan abubuwan kanayine dan karabani da matata,to kasani inason matata fiye da yadda nike son kaina,kuma babu wata barazanarka da zata sani naji Tsoro


Sannan inaso kasani kalmar saki bazata tab'a fitowa daga bakina ba


Dariya Aasim yayi sosai sannan yace


"Banga laifinka ba dan kafad'i haka ayanzu,saboda allurata batadad'e da shiga jikinka ba,nabaka sati biyu kacal dakanka,dabakinka zaka furta "


Yamaida kallonsa kan Rauda

  

Yana cigaba da dariyan ya b'ace


Zubewa Rauda tayi tana fashewa da kuka



Umar yasauko ahankali ya durk'usa agabanta yanajin kukanta harcikin zuciyarsa


"Rauda kisani inasonki babu abunda zesani fargaba akanki,ko kad'an kalamansa basu dameni ba Dan nasan be isa yamin abunda allah be minba,ki kwantar da hankalinki babu abunda zesameni kinji?



Ta jinjina Kai kawai tanacigaba dayin kukan  tarasa wannan wace irin Jarabawa ce take bibiyarta takuma kasa rabuwa da ita


Ya d'aga ta suka kwanta akan gadon asibitin yana cigaba da kwantar mata da hankali


 Washegari, yafarka jikinsa da sauk'i,hakan yasa yace sukoma gida


Zayyad yad'auko su, yadawo dasu,suna shigowa motar anty kaltum nashigowa


Suka fito atare 


Suka gaisheta ta amsa had'i da cewa

"Kukan lafiya nike ta kiran wayoyinku basa shiga?


Umar ne yabata amsa

" Wayoyinne suka samu matsala amma lafiya Lau"


Kallonsa anty kaltum tayi ganin yadda yarame

"Meyasameka naga kafad'a?


Zayyad yace

"Habadai anty idonki ne amma babu ramar dayayi"


Jinjina kai tayi amma bata yarda ba dan tafi kowa sanin k'anin nata


Rauda ce takatsemata tunanin da datakeyi tahanyar cewa


"Anty kaltum mushiga daga ciki Mana"


Anty kaltum ta girgiza Kai


"Aa, office zani dama nabiyo ne inga lafiyarku tunda kuma kuna lafiya shikenan"


Tafad'a idanuwanta akan umar tana k'ara yin nazarinsa


Umar yace

"To sister gobe zamuzo amana girki medad'i"


Gyad'a mai kai kawai tayi tashiga motarta ta tada


Suka sauke numfashi lokaci d'aya


Zayyad yace

"Ni zan tafi daddare zanbiyo in k'ara duba jikinnaka mukuma k'ara tattaunawa akan zuwa katsinan"


Umar yagyad'a kai tare dacewa

"Shikenan sai anjiman"



Suka shiga falon bayan wucewar zayyad


Zama sukayi na y'an mintoci sannan Rauda tace


"Mezan had'a maka na karyawa"



"Kisa ruwan zafi kawai musha tea"


Tace to tare da shiga kicin


Shiko kwantawa yayi yanajin jikinsa nayimasa wani iri, ya lumshe idanunsa  cike da damuwa da fargaba


Ahaka ta gama had'a abun karin tasamesa,tadad'e tsaye akansa tana magana amma bejiba dan yalula cikin tunani


Saida ta tatab'asa sannan tad'anyi firgigit yana kallonta


"Lafiya?ko jikinne?


Tatambayesa

Yakakaro murmushi yana tashi daga kwanciyar dayayi


"Aa lafiya lau harkin kammala"


Tad'aga masa Kai alamar eh


Sunfara karyawan yana shan tea hannunsa rik'e da Kofi


Jikinsa yafara rawa,yanajin cikin naman jikinsa kamar ana huramai wuta


Aje kofin hannunta tayi dasauri tana dubansa tare da amsar kofin hannunsa


"Jaana,meke faruwa?


Kasa bata amsa yayi dan zafin cikin jikinsa dad'a k'aruwa yikeyi


Daky'ar ya iya furta

"D'auko min ruwan sanyi kizubamin ajikina"


Dasauri tamik'e tabud'e fridge tad'auko goran ruwan tafara shafamai ajiki


Amma kamar k'aramai zafin takeyi


Yadakatar da ita tahanyar cewa

'barshi haka ya isa"


Aje goran tayi hankalinta atashe


Jiyayi hannunsa yafara wani irin ciwo yarike hannun dasauri yana ambaton sunan Allah


Saida yakusan awa d'aya ahaka sannan hannun yalafa,amma still zafin jikin yananan





Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹  


             🧞‍♂🧞‍♂

                🧞‍♂

                  NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)🧕🏻✍✍✍✍✍✍✍



  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to Little hajjo and my elder sister Hafsat Aliyu


🅿AGE📕 9⃣



Ina bawa masoyana hak'uri abisa ga jimawa dani keyi ban yi posting ba,nima ba da son raina bane,bank'i ace kullum naturo muku ba amma uzururruka sunyi min yawa inafatan zaku amshi uzurina,kuma zanyi k'ok'ari insha allahu inga ina yin posting akan lokaci nagode da k'aunarku gareni da kuma jinnul aashique.



GAISUWA

Ga y'an uwana y'an Golden pen writters allah yak'ara mana dank'on zumunci


FATAN ALKHAIRI

Ga aminiyata AISHA  A IBRAHIM allah yazab'a miki abinda yafi alkhairi a rayuwarki Amin.


Wannan page d'in sadaukarwa ne gareka jarumi sadauki,AASIM na sadaukar dashi gareka ranka shi dad'e allah yak'ara girma👍🏻



Bissmillahir rahmanin rahim


Duk iya k'ok'orin da umar yayi,wajen ganin ya b'oye yadda yikeji ajikinsa dan gudun kada hankalinta ya tashi,kasawa yayi saboda tunda yike a duniya betab'a jin irin yadda yike ji ahalin yanzu ba,iya kuma karatunsa na likita da yayi betab'a karo da wannan irin ciwon da yikeji ajikinsa ba bare yasan wani magani ko allura ze ma kansa yaji sassauci.


Yasa ta k'ure AC d'in falon,takuma kawo mai fankar k'asa,badda wacce take sama tanata nata aikin


Amma a banza,a memakon yaji sanyi-sanyi sai ma yikejin zafin nakuma k'aruwa.



"Chuchu"

Ya kira sunanta ahankali ganin yadda tashiga damuwa sosai


Ta zare hannunta daga tagumin da tayi tana amsawa


"Na'am"


"Please karki d'aga hankalinki,naji ma jikin yafara lafamin"


Yafad'a cikin son kwantar mata da hankali


Ta sauke ajiyar zuciya hmmmmm

"Taya hankalina baze tashi ba,bayan ina ganin ka cikin wannan halin?


Jaana ina jin tsoro,jikina na bani wani babban al'amari yana shirin faruwa damu,bana so wani abu yasameka"


Tak'ara sa fad'a idanuwanta na ciccikowa da hawaye


Yayi murmushin k'arfin Hali Yana kama hannunta yace

"Banaso kina fad'in haka,babu abunda ze samemu da izinin Allah,kinji?


Ta d'aga mai kai kawai amma ita jikinta ya gama yin sanyi


"Yauwa chuchu na,mik'omin wayata inkira zayyad"


Yafad'a


Ta mik'amai wayar,yadanna numban zayyad bugu biyu ya d'auka


Yace mai yazo yaduba shi,ga abunda yikeji


Ba a jima ba kuwa zayyad yadawo gidan,gwaje-gwaje yayi masa amma bega komai ba


Cikin mamaki yadubi Umar


"A bayanin dakamin nayimaka gwaji akan abunda nike tunani yana damunka amma banga komai ba"


Hmmmmmm umar yasauke numfashi


"Dama banyi tunanin zaka komai d'in ba......


Sai kuma ya dakata yana duban Rauda dan ba ya so yayi maganar agabanta


"Madam had'a min ruwan wanka"


Ta mik'e ta hau sama,ya maida kallonsa kan zayyad Yana cigaba da cewa


"Zayyad,zafin dani keji a jikina yawuce yadda zan kwatanta maka,jini keyi kamar ana huramin wuta acikin jikina"


Zayyad yasauke numfashi yace

"Wai to meke faruwa haka?


Umar ya zayyana mishi abunda yafaru daren jiya a asibiti,da allurar da Aasim yayi masa


Zayyad zaro ido yayi zuciyarsa cike da tsoro


"Yayi shigata yayimaka allura?nashiga uku nikuma me yasakoni a al'amarinsa?


Umar shuru yayi yana kallon zayyad


Zayyad ya ciga ba da cewa

"Amma wannan al'mari akwai rud'ani da rikitar wa wallahi,kace ciwon maka ba na asibiti bane"


Umar ya yi ajiyar zuciya me nawi

"Hmmmmmm zayyad al'amarinnan yafara bani tsoro,duk inda kake tunanin Aasim wallahi ya wuce Nan,ina fargaban abun da ze iya faruwa gaba"


Zayyad ya jinjina kai cike da tsananin mamaki danshi tunda yike aduniya betab'a jin makamancin al'amari irin wannan ba Koda kuwa a littafi ballan tana a zahiri


"Gaskiya dole musan abunyi,inaga mushirya mutafi katsinan yanzu kawai"


Umar ya girgiza Kai yace

"Allah bazan iya tafiya me nisa ba,idan ka rok'esa baze yarda a turamai kud'i yazo ba?


Zayyad yad'an yi shuru yana tunani sannan yace


"Babban malami ne gaskiya,kuma koda yaushe gidan shi cike yike taf da jama'a bana tunanin ze iya barinsu yazo,amma bari na kirasa naji"


Yak'arasa fad'a yana zaro wayarsa a aljihu


Ya danna numban malamin bugu biyu ya d'auka suka gaisa,zayyad yasanar dashi buk'tarsu akan yazo tare da rok'onsa daya taimaka


Yace ba matsala gobe da safe ze taho 


Zayyad yayi mai godiya sannan ya kashe wayar yana kallon Umar yace


"Bari yaturo account numban sai inmai transfer"


Acan bedroom kuwa Rauda,


Ta gama had'a ruwan,zata fito kenan taji wani k'ara  





Ta waiga da sauri tana kallon cikin bayin,ruwan data had'a acikin kwamin wanka ne taga yana ta zakud'owa kamar dakwai wani abu aciki


Ta rufe idanuwanta da sauri jin tsigar jikinta na tashi bakinta na ambaton sunan Allah


"RAUDA!


Taji ankira sunanta da wata kalar murya me tsoratarwa


Tabud'e idanuwanta da sauri tana kallon cikin ruwan inda taji ankira sunannata


Wani mutumi tagani d'an k'arami shi ba wada ba shi ba yayan wada ba,d'an siriri,fatar jikinsa wata kala kamar gansa kuka,koriya shataf,idanuwansa wasu kala kamar na mage


Futowa yayi daga cikin ruwan yana tahowa inda take


Jikinta na rawa ta murd'a k'ofar bayin zata fita amma gam k'ofar ta rufe


Addu'o i tacigaba dayi dasauri tana jijjiga k'ofar


Ganin ya iso gab da ita yasa  tayi sarranda



Ta runtse idanuwanta kawai,jitayi an damk'i hannunta ta ware idanun tana k'wala ihu


"Bazamu tab'a rabuwa dake ba"


Taji yafad'a

Tare da kecewa da wata kalar dariya


Takuma k'wala ihun tare da zubewa a sume,


Umar nafalo, yajuyo ihunta, zayyad ya dubesa yana fad'in


"Kamar ihun Rauda ko?

Umar ya d'aga kai yana mik'ewa


"Bari Naduba Ina zuwa"


Yafad'a yana hayewa sama da sauri


A dur k'ushe yasameta,ya d'agata dasauri yana kiran sunanta


"Rauda!Rauda!


Amma shuru,d'aukota yayi ya yo falo da ita, zayyad na hangosa ya mik'e yanacewa


"Subhanallah me yasameta?


"Wallahi bansani ba"

Umar yafad'a yana shimfid'ar da ita a kan doguwar kujera


Yazauna gefenta yana d'an girgiza ta,yana cigaba da kiran sunanta


Zayyad da ke tsaye yad'auko ruwa agora ya mik'ama umar yana cewa

"Ina ganin suma tayi,yayyafa mata mugani"


Ya amsa ruwan ya yayyaffa Mata,ko minti biyu beyi da yayyafa mata ruwan ba,tafarfad'o tana sauke ajiyar zuciya me nawi


Lokaci d'aya ta bud'e idanuwanta ahankali harta gama bud'e su akansa


Ahankali k'wa-k'walwarta ta tariyo mata abunda tagani a bayi


Tashi tayi a zabure ta fad'a jikinsa tare da fashewa da kuka


"So sukeyi su kasheni,sunce bazasu tab'a rabuwa dani ba wayyoh allahna na shiga uku!


Umar yasauke numfashi zuciyarsa cike da tsananin damuwa,

Kasa cewa komai yayi,ya rungume ta kawai yana sauke numfashi ahankali


Zayyad yayi jugum Yana kallonsu gabad'aya tausayinsu yikeji,lokaci d'aya yanayinsu ya sauya daga farin ciki zuwa tashin hankali


Be bar gidan ba sai da aka kira sallar magriba


Suko suna falon har lokacin,ba maganar neman abinci dan babu me jin yunwa acikinsu


Zuwa can dai ya dubeta tana kwance akan k'afafunsa yayinda yike zaune kan doguwar kujera yace


"Mekike buk'atar kici insa me gadi ya siyo Miki?


Girgiza masa kai tayi tace


"Ni banajin yunwa"


"Nasan bakyaji ai,nima baji nike yi ba amma yazama dole munemi wani abu musa acikin mu dan zama da yunwar itama babbar matsalar ce"


Ta jinjina Kai

"Shikenan kasa yakawo koma miye"


Koda me gadin yasiyo kuwa,kad'an suka tsakura, suka gabatar da sallar magriba da issha,sannan suka kunna karatun qur'ani acikin a falon


A haka bacci ya d'auke Rauda,shiko umar ko kad'an be runtsa ba dan jikeyi kamar ana d'add'aure jijiyoyin jikinsa,ga zafin da yike ji Yana dad'a k'aruwa.


Sai wajen asuba Rauda ta farka,taga yadda ya had'a zufa


"Ba kayi bacci bane?


Ta tambayesa da damuwa a fuskarta


Ya girgiza Kai yana k'ok'orin b'oye yanayin da yikeji


"A a nayi Mana kiran sallar da akayi ne ya tasheni"



Hmmmmm tasauke numfashi


"To muje muyi alwala ko"


Suka mik'e atare,jiyayi k'afarsa ta rik'e tana mai zugi


Yad'an tsaya yana kallon k'afar,kallon Rauda tayi tace


"Lafiya?


Yad'an k'ak'aro murmushi

"K'afata ce ta rik'e ina ganin Dan na kwana a zaune ne shiyasa"


Cikin tausaya wa tace

"Meyasa baka tasheni ba to,dana kwanta akan k'afafunka?


Ya kuma yin murmushi

"Taya zan tasheki?zan iya kwana a tsaye ma inhar ke zakiyi baccin cikin kwan ciyar hankali"


Sonsa da k'aunarsa da kuma tausayinsa suka k'ara shiga cikin zuciyarta


Wasu siraran hawaye ne suka biyo kuncinta


Cikin damuwa yace

"Miye kuma na kuka chuchu"


Hannu tasa tashare hawayen tana cewa


"Tabbas samunka matsayin miji agareni,wani babban rabo ne daga ubangiji,na tabbata da bakai na aura ba da yanzu wanda na aura ya maidani gidanmu danna tabbata babu me iya zama dani da wannan lalurar atare Dani"


Tak'arasa fad'a wasu sabbin hawayen na gangarowa daga idanunta


Ajiyar zuciya yasauke tare da kama hannayenta yana kallon cikin idonta


"Rauda,allah yayi nine mijinki shiyasa ma ya k'addaro miki wannan al'amarin,dan Allah ki kwantar da hankalinki banaso inga damuwa a fuskarki,wallahi nikad'ai nasan yadda Nike Jin zuciyata idan naganki acikin damuwa"


Tayi murmushi still hawaye nabin fuskarta


"Zan rink'a b'oye wa dan kawai hankalin naka ya kwanta amma kasan damuwata bazata tab'a ciruwa ba face na rabu da matsalar dake tattare Dani"


Har lokacin hannayenta na rik'e cikin nasa

"Jikina nabani kinkusa rabuwa da wannan matsalar,ko ince munkusa rabuwa da ita,insha allahu muna gab da fita daga cikinta"


Ta gyad'a kai kawai dan ita tasan yanzu ma suka fara shiga cikin matsala


"To allah yasa"


Tafad'a,suka shiga cikin bedroom suka d'auro alwala


Shiya jasu sallar, Allah-allah yikeyi ya idar sabida zugin da k'afarsa keyi masa


A daddafe ya sallame sallar,ya mik'ar da k'afar yana mamakin zugin da k'afar ke masa


Jikinta yayi sanyi dan ta fahimci ba kwanan dayayi azaune bane yasa k'afar tasa haka,k'ila abunda ke shiga cikin jikinsa ne


"Jaana haryanzu k'afar bata dena ba ko?


K'ak'aro murmushi yayi yace


"Aa ta Dena,kawai dai na mik'ar da ita ne"


Ajiyar zuciya tayi tana girgiza Kai,batasan me yasa yike son b'oye mata halin da yike ciki ba


"Jaana dan allah kadena min irin haka, at least in kanajin abu kafad'a min ko kana da wacce tafi nine?


Nida bani da wanda yafika ai komai naji saina sanar dakai amma Kai......


Ya katseta

"Chuchu kinsani babu abunda zan b'oye Miki,k'afar ta Dena tund'azu"


Ta kauda kanta gefe gudun kada yaga hawayen da ke Shirin zubo Mata


"Chuchu"


Yakira sunanta,saida tashare hawayen sannan ta juyo tana amsawa


"Na'am"


"Zonan"


Yafad'a,ta taso tak'arso gabansa ta durk'usa


Janyota yayi ya rungume ta yana sauke wani numfashi me nawi


"Kizauna ajikina,ko zanji sanyi acikin zuciyata"


Yafad'a yanajin yanayin sa na k'ara canzawa,k'afa da zafin jikin nakuma addabarsa


Runtse idanuwanta tayi wasu sababbin hawayen na ambaliya a fuskarta


Yakuma matseta ajikinsa bakinsa na ambaton


"La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minaz zalumin"


Ta bud'e jik'akk'un idanunta tana kallon yadda ya runtse idonsa alamar yana jin rad'ad'i


Addu'o i tafara tofa Masa, idanuwanta na fitar da hawayen tausayi da tsantsar damuwa



K'arfe tara tayima zayyad a Tasha,Dan malam aminu ya sanar dashi sunkusa isowa


Ko minti goma beyi da zuwa ba,motarsu ta tsaya


Yafito cikin manyan kayansa da nad'in rawani akansa


Dattijone kamilalle me cike da natsuwa,ya mik'ama zayyad hannu sukai musa baha suka gaisa,sannan suka shiga motar zayyad d'in


Bayan zayyad yatada motar yace


"Malan sannu da hanya,gaskiya kun iso da wuri motar tayi gudu"


Malan yace

"Ai da wuri nafito ina idar da sallah danma motar tad'an tsaya mana amma da mun iso tund'azu"


Zayyad ya jinjina kai yana cewa

"Allah sarki,kayi hak'uri fa malan,muntasoka mu yakamata ace munzo da kanmu amma halin da abokinnawa ke ciki yasa nace bari dai kazo d'in"


Malan yayi d'an murmushi

"Babu komai"


Tunda suka iso get d'in gidan malan aminu ya fahimci akwai gagarumar matsala acikin gidan


Hakan yasa ya umarci zayyad da ya dakata da shiga cikin gidan


Sai da yayi addu'o I sosai sannan yace zayyad ya shiga


Zayyad ya shiga yayi parking,sannan suka fito zayyad yafara knocking d'in falon


Har lokacin suna rungume da juna, bakinta kuma bedena karanto addu'o in ba


K'wan-k'wasa k'ofar da zayyad yayine yasa suka bud'e idanuwansu atare


Dede lokacin wayar Umar tafara k'ara ganin numban zayyad yasa yace


"Ina ganin zayyad ne,mukoma falon"


Suka mik'e sukayo falon yana d'an ciccije bakinsa dan ciwon dad'a k'aruwa yikeyi


Kan kujera ya zauna,Rauda ta bud'e k'ofar


Ta gaishe da su tana kallon malan aminu Wanda shima ita yazuba ma ido


Ta basu hanya suka shiga sannan ta maida k'ofar tarufe,takoma kusa da Umar tazauna


Yayinda suma suka zauna suna gaisawa da Umar d'in


Malan aminu yatashi ya dafa kan umar yana nazartar abunda ke damunsa


Ya girgiza kai fuskarsa d'auke da damuwa yana duban Rauda sannan itama ya dafa nata kan


Janye hannunsa yayi dasauri yana kallonta fuskarsa d'auke da tsantsar mamaki


A fili yace

"Aasim bin ramzad?

Yasauke numfashi Yana kuma girgiza kai cike da tarin fargaba


"La haula wala k'uwwata illah billah"


Malan aminu yafurta yana komawa kan kujerar ya zauna


Gabad'aya sun zuba mai ido suna jiran suji abunda zece


Ya sauke numfashi yana kallonsu


"Zahiri kuna cikin babbar matsala,domin kuna tare da rauhanin da ba kowani malami bane ze iya ja dashi"


Yad'an numfasa sannan yacigaba dacewa


"Amma nayi mamaki,Aasim bin ramzad rauhanine,kuma a iya sanina rauhanai basa cutarwa,wani laifi kuka masa haka da ya tunzurasa yike azabtar daku?


Ya k'arasa maganar Yana kallonsu sosai


Ganin basu bashi amsa ba yasa yacigaba da cewa


"Tabbas akwai laifin dakuka masa mai girma wanda ya tunzurasa ya canza daga ainihinsa,kuma ni tabbas bazan iya ja dashi ba amma zan iya nemansa inji dalili inkuma jaraba rok'onsa ko ze iya hak'ura"


Har lokacin babu wanda yayi magana kallonsa kawai sukeyi,umar ne yakatse shurun ta hanyar cewa


"Malan dan Allah kataimaka kayi iya abunda zaka iya, wallahi muna cikin damuwar da bazamu iya kwatanta maka ba"


Malan aminu yagyad'a kai yaciro wani turare a aljihunsa ya fesa sannan yafara karanto addu'o I da basajin me yake fad'a illa bakinsa da suke gani yana motsawa


Ahankali d'akin yafara duhu,saiga shi ya bayyana  cikin ainihin suffarsa ta yarima


Malan aminu nagani,yazube a k'asa yana faman jera kirari


"Allah yataimaki yarima,me martaba d'an sarki,basarake me dubbannin dawakuna"


Fuskarnar tasa a tamke ya watsawa malan aminu razanannun idanunsa cikin b'acin rai yace


"Kai wanene,da har ka kai matsayin da zaka nemeni"


Bakin malan aminu na rawa yace

"Ka gafarceni ranka shidad'e,tuba nike allah ya huci zuciyarka"


Ya kad'a kai yana cewa


"Fad'i kiran me kakemini,meke tafe dakai,me Kuma yashigo dakai matsalar da babu ruwanka,shin kanaso rayuwarka ta salwanta ne?


Jikin malan aminu na kyar-kyarwa yace


"Tuba nike ranka shidad'e,amsa Kira na dakayi kad'ai ya isheni,bakuma nanemeka bane dan na Isa,illa Dan na rok'eka da ka sassauta ma wad'annan bayin allahn.....


Da wata kalar tsawa ya katsesa

"Kai!

Kashiga taitayinka,kakuma tuna da wanda kake magana,kai baka isa ka nemar musu afuwa ba,kuma hukuncine nariga da na yanke,mafita ta rage garesu"


Malan aminu bakinsa na rawa saboda kid'imar da yayi

 Yace


"Kagafarceni tuba nike allah ya huci zuciyarka"


Aasim ya kalli Rauda da umar yana yimusu wani kallo da shi kad'ai yasan ma anarsa


"Nafad'a kuma zansake fad'a muku,ko ku rabu da juna kokuma daga yanzu kicigaba da fuskantar barazana,kuma gubata akullum k'ara ratsaka zatayi wallahi sai ka gwammace mutuwarka da halin da zaka shiga


Ke Kuma....yanuna Rauda sannan yacigaba da cewa


"Yanzu ne zaki fahimci ko ni waye dakuma matsayin da nike dashi"


Yana gama fad'ar haka yab'a ce


Nan danan haske ya gauraye falon ya dawo yadda yike


Gabad'aya malan aminu ya jik'e sharkaf da zufa,shiko zayyad harda fitsari ya saki saboda tsananin tsorata


Malan aminu yasauke doguwar ajiyar zuciya yace


"Agaskiya bazan iya ba,ku gafarceni amma ya wuce k'arfin da kuke tunani,bazan iya ba dan allah karku sake nemana dan rayuwata zata iya shiga cikin hatsari"


Yak'arasa fad'a yana mik'ewa ze fita


Zayyad na kiransa amma be tsaya sauraronsa ba ya k'arasa ficewa daga falon dan gabad'aya ya firgita


Rauda ta runtse idanuwanta cikin tashin hankali maganganun malan aminu nayimata yawo acikin kunnuwanta


"Aasim bin ramzad rauhanine kuma rauhanai basa cutarwa tabbas kunyi masa laifin dakuka tunzurasa wanda yasa ya canza daga ainihinsa"


Wasu hawaye ne masu zafi suka cigaba da gangaro mata


Ahankali ta furta


"Tabbas ban kyauta ba maka ba,amma ban cancanci wannan hukuncin daga gareka ba"


Wanene Aasim? Menene had'insa da Rauda? Me suka masa da ya canza sa daga ainihinsa?


Muhad'u a page 🔟 dan jin yadda zata cigaba da kasancewa taku a kullum




Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹


              🧞‍♂🧞‍♂

                 🧞‍♂


                NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo) 🧕🏻


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


Dedicated to little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu



🅿AGE📕 🔟



_Wannan Page naki ne anty Nabeelt Allah nike rok'o ya baki lafiya, yasa kaffara ne ya kuma k'ara dank'on zumunci a tsakaninmu Amiiiin_


Maman ummi kema ina Allah yak'ara lafiya yasa kaffarane yakuma nuna mana auran ummi lafiya😅


Ban manta da ke ba safnah👩🏻‍🎤. Ina godiya da addu'o in ki gareni


_GAISUWA DA JINJINA_


*_Ga ya ommer allah yak'ara k'warin ido muna godiya da zak'ulo mana kura-kuran mu daka keyi, da kuma gyara dakake mana, bazamu iya biyanka ba ya Ommer wlh muna jin dad'in shugabancin ka sosai Allah ya bar mana kai da rai da lafiya mai anfani, ya kawo bata tagari kuje har katsina musha ringen-rigegen_*💃🏻💃🏻💃🏻



Bissmillahir rahmanin rahim✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



FARKON LABARI


Cikin katafariyar jami'ar dake cikin katsina


D'alubai ne sukayi dandazo a wani wuri da alama sakamon jarabawarsu da sukayi suke dubawa


Hayaniya da turereniya sunyi yawa a wurin,dan ko wani d'alubi burinsa yaga sakamakon sa



Tafiya Rauda Take yi cikin sauri har da gudu-gudu yayinda ta hango dandazon d'aluban


Gabanta na fad'uwa, k'irjinta na dukan uku-uku ta isa wurin


Ganin yadda maza da mata suka cakud'e yasa tasamu gefe ta tsaya,dan bazata iya shiga cikin maza ba


Saida taga d'aluban sun ragu,sannan ta k'arasa wurin gabanta na fad'uwa


Bata ma fara duba sunan ta daga sama ba,daga tsakiya tafara tanayin k'asa


K'irjinta yayi mugun bugawa yayinda taga abunda taci


Takasa d'auke hannun ta awurin   sakamakon sanyin da jikinta yayi


Wasu y'ammata masu ji da kansu dake gefenta suka fashe da dariya 


Cikin haibaci d'ayar me suna laurat wacce itace take fitowa da first class a department d'insu,takalli d'ayar me suna farida tace


"Farida waike wace irin k'wa-k'walwa kike da itane,ace kowani semester bakya iya fitowa da ko third class sai dai probation"


Farida taga ne nufin laurat sarai hakan yasa ta fashe da dariya tace


"Kannawa ne a toshe yike, kwata-kwata baya iya d'aukar komai,saboda dattin talauci da kuma miyar kuka sun toshesa"


Dariya suka sakeyi gabad'aya su biyun cikin nishad'i da annashuwa


Rauda tasan da ita suke,hakan yasa tabar gurin jikinta a sanyaye ba tare da ta tanka mu su ba


 Can baya taje tazauna k'asan wata bishiya, gabad'aya tarasa me ke mata dad'i dan ta tabbata idan tacigaba da kasancewa tanafitowa da wannan sakamakon to tabbas watarana koranta za ayi


Wasu hawaye ne masu zafi sukafara biyo kuncinta yayinda ta tuno mahaifinta dakuma yadda yike so tayi karatu


Shin ya zatayi?


Wata tattausar murya taji tayi mata sallama,tad'ago da idanuwanta da sukayi sharkaf tana kallon me yin sallamar


Wani kyakkyawan saurayi ne  tsaye cikin k'ananan kaya 


Kyawunsa yawuce yadda za a fasalta


Duk da damuwar datake ciki behana zuciyarta yaba kyawunsa ba 


Yakuma yin sallama a karo na biyu


Amma nanma kasa amsawa tayi dan ji tayi jikinta yayi mata wani iri tsigar jikinta tafara tashi


Murmushi saurayin yayi yana durk'usawa daga tsayen dayike,tazarar dake tsananin su bazata wuce kamu hud'u ba


Har lokacin da murmushi a fuskarsa


"Be kamata ace kink'i amsamin sallama ba,domin ko nasan ke musulma ce yakamata ace kin amsamin"


Cikin muryarta da ta fara dashewa tace


"Wa alaikumus Salam"


Murmushi ya kuma yi yana zaro farin handkerchief daga aljihunsa,ya mik'ama ta


"Kwata-kwata hawaye beyi kyau a wannan kyakkyawar fuskar ba,kamata yayi ace murmushi ne akanta ba hawaye ba"


Murmushin ko tayi dan taji dad'in abunda yafad'a


Amma still da hawayen a fuskarta


Yazauna dirshan a k'asan kamar yadda take a zaunen yana cewa

"Wa yacemiki ana had'a murmushi da kuka?ai sai kin share hawayen tukunna"


Mamakine ya kamata ganin yanayinsa da Kuma tsadaddun kayan dake jikinsa amma kuma ya zauna a k'asa


Handkerchief d'in ya sake mik'amata

"Amsa Mana na k'osa inga kingoge wannan hawayen"


Amsa tayi idanuwanta a kansa,tana tambayar zuciyarta, shi kuma wannan wanene?


"Baki sanni ba ko,nazo na cika ki da surutu,kiyi hak'uri nima surutu ba d'abi'ata bace kawai dai banaso naga mutum ya na cikin da muwa ne"



Tayi murmushin daya tsayamata iya baki tana share fuskarta


Bayan ta gama goge hawayen ta mik'a mai handkerchief d'in tana mamakin kafeta da idanu dayi


Be amsa ba kuma har lokacin bata ce mai komai ba


Ya rausayar da kai yana cewa


"Menene yasaki kuka haka,ko kin fad'i jarabawa ne?


Ajiyar zuciya ta sauke yanayin fuskarta ya k'ara nuna alamun damuwa


Amma kuma har lokacin batace uffan ba


Ya sauke numfashi Yana K'ara kallonta sannan yace


"Da dukkanin alamu bakyaso kifad'a min,to koma menene ba kuka yakamata kiyi ba,addu a yakamata kiyi,ki rok'i Allah da ya yayemiki


Abunda ke damunki kinji?


Dede lokacin k'awarta Salma ta iso wurin tana cewa


"Haba Rauda, tund'azu inata nemanki ashe kinanan.........


Takasa k'arasawa samakon lura da saurayin dake zaune dirshan gaban Raudan


Rauda tamik'e tace


"Inanan,kindubo result d'innaki?


Cikin daburcewa salma ta d'aga mata kai tana kallon saurayin wanda shima ya mik'e


Ganin yadda salmar ta saki baki tana kallon sa yasa Rauda ta galla mata harara tana matsowa kusa da ita


Cikin murya k'asa-k'asa tace

"Miye haka?


 Salma tad'an dai-daita natsuwarta tana maida kallonta ga Rauda


"Am....nace...dama...


Harara Rauda takuma galla mata ganin yadda duk tawani daburce daga ganin mutum


"Kikace me? Ta tambaya tana kafeta da idanu


Salma zata kuma magana ta katseta


"Kinga malama muje ko?


Tak'arasa fad'a tana nuna mata hanya


 "Amma dan Allah inaso ind'an yi magana dake,na y'an mintoci idan bazaki damu ba"


Saurayin yafad'a yana duban Rauda


Rauda ta girgiza Kai tace

"Kayi hak'uri bani da lokaci,inada abunda zanyi"


Bata jira jin me zece ba taja hannun salma suka wuce


Tunda suka bar wurin Rauda ke mita


"Wannan ai zubar da ajine,ki wani saki baki kina kallon mutum salon ya rainaki,inbanda shashanci miye zaki wani kafe mutum da ido kamar kinga wani sabon halitta "


Itadai salma bata tanka mata ba,harsaida suka koma d'akinsu


Rauda wurgar da k'aramar jakar dake hannunta tayi tafad'a kan k'aramin gadon k'asa tana lumshe idanuwanta dasuka k'an-k'ance saboda b'acin rai da kuma damuwar da take ciki


Salma ta zauna kan kujerar dake tsakar d'akin,


Tace

"K'awa waye wannan dana gani,a ina kika samosa?


Rauda ta tashi daga kwanciyar da tayi tana dafa kanta


"Wai meyasa kike tambaya akansa ne?miye damuwar ki da shine?


Kamata yayi kidamu da jarabawar Dana fad'i ba ki tsaya kina tambaya akan wani can da k'ila ma ba k'ara ganinsa zaki yi ba"


Salma ta sauke numfashi tana tasowa daga kan  kujerar tada wo gefen raudar ta zauna


Dafa kafad'ar ta tayi tace cikin kwantar da murya


"K'awata kema kinsani nafi kowa damuwa da damuwarki,kawai dai na tambaya waye shine ganin bantab'a ganinki tare da shi ba,amma kiyi hak'uri"


Rauda ta tasauke doguwar ajiyar zuciya


"Bansan ya zanyi da raina ba,kiduba fa kiga tunda jarabawar nan ta matso na dena bacci,kwana nikeyi ina karatu,amma abun haushi sai naje rubuta jarabawar sai inji namanta komai,


Haka b'angaren lissafi kwata-kwata bana ganewa, nasan nan gaba korata za'ayi"


Tak'arasa fad'a idanuwanta na ciccikowa da hawaye


Salma tasauke numfashi,tana girgiza mata Kai


"Dan Allah karkiyi kukannan,addu'a zamu cigaba da yi,sannan kuma kik'ara dagewa insha'allah za'a wuce wurin"


Gyad'a Kai kawai tayi takoma ta kwanta


Daddare tana zaune bacci yakasa d'aukar ta, tunanin sakamakon jarabawar ta kawai takeyi


Taja guntun tsaki tare da mik'ewa tasha ruwa sannan ta dawo zata kwanta


Handkerchief d'in da yabata d'azu ne tagani a k'asa,sai lokacin ta tuna be amsa ba


Ta durk'usa ta d'auka sannan takoma bakin gadonta,tana jin k'amshin dake fita ajikin handkerchief d'in sama-sama


Zaunawa tayi tana k'arema handkerchief d'in kallo,farine k'ar sai wani zanen fulawa golden a jiki,ta kara kusa da hancinta


Wani sassanyan k'amshi ne medad'i ya bugi hancinta


Ta lumshe ido zuciyarta na hasko mata kyakkyawar fuskarsa


"Waye shi?


Ta tambayi zuciyarta,Tana sake kallon handkerchief d'in


Ganin bata da amsa,yasa takwanta batajima da kwanciya ba bacci ya d'auketa


Washegari da sassafe ta shirya dan k'arfe tara take da lecture


Ko karyawa bata tsaya tayi ba,kasancewar tasan halin lecture ran bayi da kirki ko kad'an gashi yayi mugun samata ido 


Gabad'aya ajin yayi tsit, yayinda yashigo ya gabatar da bayani me tsawo sannan sannan ya rubuta wani word ajikin allo


Ya juyo yana kallon d'aluban yana duba wanda ze zak'ulo ya maka mai tambaya


Ba abunda k'irjin Rauda keyi face dukan uku-uku


Dan tasan zeyi wuya be kira sunanta ba


"Rauda"


Taji yakira sunanta,k'irjinta yayi wani mugun bugawa


Yakuma Kiran sunan

"Rauda"

Yana nunata da hannu 

Sannan yacigaba da cewa

"Tashi kifad'a min miye na rabuta"


Jikinta na rawa ta mik'e tana kallon allon,cikin rawar murya takaranta


"Radi..cals"


Lecturer mamman ya gyad'a kai

"Fad'amin miye ma'anar radicals?


Shuru tayi dan batasan miye ma'anarsa ba,bugun zuciyarta nadad'a k'aruwa


Tsawa ya daka Mata

"Ba tambayar ki nayi ba kikayimin shuru"


"Radicals is a........


Saikuma tayi shuru


Lecturer mamman ya dafa kansa na y'an mintuna sannan ya ware jajayen idanuwansa yana kallonta


"Yauma baki sani ba ko?duk wata tambayar da za'ayima d'an secondary idan akayimiki Baki sani ba,wai shin a wace makaranta kikayi karatu kafin kizo jami'a?


Shin lefin daga malamankine wad'anda suka koyar dake?kokuma daga k'wa-k'walwarki ne?


Yad'an numfasa tare da jan dogon tsaki sannan ya d'auke kallon sa daga kanta yamaida kan sauran d'aluban


"Waye ne ze fad'amana ma'anar radicals?


Cikin yauk'i da yanga laurat ta mik'e tafara bayani cikin wani salo na turanci me burgewa


Lecturer mamman ya jinjina kai cike da gamsuwa da bayanin da tayi


Yak'ara dacewa

"Haka akeson d'alubai masu hazak'a ba wanda kullum k'wa-k'walwarsu take a toshe ba"


Tunda Rauda tafito da ga ajin zuciyarta ke suya, gabad'aya taji rayuwar tafitan mata arai,


Gabad'aya d'aluban dake tsakar makarantar sauri  sukeyi saboda hadarin da yayi bak'ink'irin yanata cida alamar yana gab da fara ruwa


Banda Rauda datake tafiya kamar wacce k'wai ya fashemawa aciki 


Jitayi ta bangaji mutum,litattafan da ke hannunta suka zube a k'asa


Dasauri takallesa,saurayin jiya ne


Atare suka durk'usa dan kwashe litattafan


Cikin muryarsa me taushi yace


"Yauma allah ya k'ara had'amu"


Yafad'a yana tattara litattafan


"Kayi hak'uri bansan ya kayi na bangajeka ba"


Ya jinjina kai iska na kad'a  kwantaccen gashin kansa


"Babu damuwa,ina zaki je haka?ga hadari ya taso?


"Hostel zankoma"


Ya d'an kalleta yace

"Amma tsakanin hostel da nan aida d'an nisa natabbata kafin kikai ruwannan ya sakko......


Be k'arasa ba ruwa yafara saukowa da k'arfi 


Hannu tamik'a yabata litattafan,ya mik'o yana cewa


"Amma ki fake acan wurin........


Hannunta da nashine suka gogi juna,


Wani irin yarr taji ajikinta, dasauri takallesa suka had'a ido


Jitayi gabanta yafad'i ahankali taji kanta yad'an Sara


Ta d'auke idanuwanta akansa Tana mik'ewa da niyyar cigaba da tafiya zuwa hostel d'in


Jitayi ya ruk'o hannunta tajuyo da sauri tana kallonsa


"Tafiya cikin ruwannan ze iya haifar miki da zazzab'i ki fake ruwan ya tsaya dan Allah"


Yafad'a yana kallon cikin idanunta


Zame hannunta tayi ahankali idanuwansu na sark'e da juna,batamai musu ba suka k'arasa gurin barandar


Kan wani dankali ta zauna,shikuma ya tsaya Yana goge gashin kansa da  ruwa yafara jik'awa


Kallonsa takeyi sosai takasa d'auke idanuwanta akansa


Ya maida handkerchief d'in aljihu yana kallon yadda ruwan ke sauka da k'arfi


Daga bisani ya juya yana dubanta


"Dama ance mata ba sa tsoron ruwa, amma kuma hakan kuskure ne,saboda ze iya shafar lafiyar mutum"


Ya k'araso wurin dakalin ya zauna a gefe


Yana kallonta atsanake, yacigaba da cewa


"Yau kuma meyafaru naga damuwa a fuskarki, ko tun da muwar jiya ce?


Itama kallonnasa takeyi gani takeyi kamar ta sanshi,kamar ta tab'a ganinshi,to amma a ina?


"Wanene Kai?


Tambayar tafito daga bakinta batare da ta shirya yinta  ba


Yayi d'an murmushi


"Kinaso kisan ko ni waye? Yad'an dakata sannan yacigaba dacewa


"To ai ba damuwa bane,sunana Aasim ni sabon d'alubi ne"


"Aasim?

Ta mai-maita sunan tanaso ta tuna inda ta tab'a jinsa


Ya d'aga kai

"Eh Aasim,kinji sunan wani iri ko?


Ta  gyad'a Kai tana k'ara nanata sunan a zahiri

"Aasim?narasa a inda na tab'a jin sunannan,amma kai ba d'an k'asar nan bane ko?


Be bata amsa ba ya wurgo mata nasa tambayar

"Me kika gani?ban yi kama da y'an nigeria bane?


Ta d'aga kai alamar eh tace


"Kaima kasani ai"


Dariya yayi,wacce tabayyana fararen hak'oransa 


"To inni ba d'an Nigeria bane ya akayi nike jin hausa?


Tayi dan murmushi tana bashi amsa


"May be zama yakawoka, Nigerian ka koya"


Dariya ya Kuma yi

"To ni d'an Nigeria ne"


Tak'ara kallonsa 

"Amma iyayenka su ba y'an nigeria bane"


"Um to,yanzu dai abar maganar Nigeria ko wata k'asa,da y'an wata k'asa nayi miki Kama?


Tayi jim tana nazarin da wata k'asa zata dangan tashi 


"Ummm to nina rasa ma da wata k'asa zan dan gantaka,saudiyya ne ko india?ko da yikema farinka ba irin na indian bane"


"Tofa? to ko da y'an china nike kama ne?


Yafad'a cikin zolaya


Tayi murmushi gami da cewa

" Ni gani nikeyi kamar  muntab'a had'uwa kafin wannan lokacin"


"Nima haka nike gani,baki fad'amin naki sunan ba"


Yafad'a yana son kawda zacen da ta kawo


"Sunana Rauda"


"Suna medad'i, kamar yadda me sunan ta kasance"


Yafad'a fuskarsa na nuna tsantsar farinciki data rasa gan me ko farincikin menene


"Nagode"


Tafad'a tana maida kallonta ga ruwan da yafara rage k'arfi


Ya sauke numfashi,yace

"Zanso muk'ulla alak'a ta abota,ma'ana muzama kaman y'an uwa ni dake,tunda nafara ganinki naji na natsu dake,bansani ba ko zaki bani damar hakan"


Tayi guntun murmushi tana sauke numfashi


"Gaskiya aa,saboda nidakai bamu had'a hanya ba kwata-kwata"


Cikin rashin fahimta yace


"Bangane ba"


Ta kuma sauke numfashi a karo na biyu


"Ni ina alak'a ne da wad'anda suke Dede Dani,amma kai kafi k'arfina kayi hak'uri"


Ya jingina da bango har lokacin idanunsa na kanta


"Wannan ba magana bace,dani dake duk d'aya ne,kuma duk allah ne yayimu danhaka kada kisake fad'in haka"


Ta jinjina Kai

"Shikenan"


Tundaga wannan Rana alak'a me k'arfi tashiga tsakaninta dashi


Kodayaushe idan batada lecture suna  tare Yana koya mata karatu wanda take fahimta sosai


Ahankali k'wa-k'walwarta tafara bud'ewa yazamana duk wata tambayar da za'ayima ta a aji tana amsawa


Wanda hakan yafara ba wa mutane mamaki,ita kanta tana mamakin kanta,da ta karanta abu sau d'aya sai taji ya zauna mata


Kamar kullum tagama d'aukar darasi,tafito daga lecture room fuskarta d'auke da nishad'i  daga nesa ta hango motarsa,inda yayi mata horn


Tak'arasa suna ma juna murmushi,sallama ta mai ya amsa yana K'ara rage glass d'in motar


"Yau kindad'e"


Ta d'aga Kai tana murmushi

"Kasan jarabawa ta kusa,shiyasa"


Yace

"Hakane shigo to yau yawo zamuje"


Bata musa ba,ta zagaya ta bud'e marfin motar tashiga, Saida tazauna ya tada motar sannan tace


"Yawo Kuma? To ina zamuje?


Hankalinsa nakan tuk'in yabata amsa


"Yawo,kawai ko kuma akwai inda kikasani ki kaimu?


Ta girgiza Kai

"Aa ni bansan ko inafa,danni ko a kaduna ba yawo nike yi ba ballantana a garin da ba nawa ba"


Ya jinjina kai cikin gamsuwa

"Hakan yana da kyau ai,ba kimar mace bace ace tana yawo"


Gyara zamanta tayi tana kallonsa sosai


ya juyo suka had'a ido,tayi saurin lumshe nata tana cewa cikin wata kalar murya me sanyi


"Wai meyasa idan muka had'a ido sai inji tsigar jikina na tashi ne?


Tayi mai tambayar idanuwanta a lumshe


Guntun murmushi yayi,yana k'ara kallon ta


"Nima bansani ba, hala nawa idanun sunfi naki k'arfi ne shiyasa"


Ta bud'e idanun ta sauke su akansa,tana jin jikinta nayi mata wani iri


"Kace dai kai d'an baiwa ne kawai,dan komai naka ya  bam-banta dana sauran mutane"


"To kodai ni ba mutum bane?


Ya jeho mata tambayar


Tayi dariya tace


"Haba dai to ko da aljani nike tarayya bansani ba?


Itama tayi mai tata tambayar tana dariya


Ya d'aga kai tare da cewa


"Ze iya kasancewa,kinsan aljanu duk inda kike tunaninsu sun wuce Nan"


Dariyar ta kuma yi


"Eh lallai Kam,ai duk k'arfin aljani baze iya yin siffar mutum kaman naka ba,sufa ance ko sunyi suffar mutum to basa iya yin k'afar mutum saidai kaga kofato"


Idanunsa na kan titi yace


"Ashe?tofa


Ta jinjina kai


"Eh Mana,ai ta k'afafunsu ake gane su,kuma ance muryarsu ma basa iya yin ta mutane"


"Hu'um ashe basa samun cigaba kenan?


Yafad'a


Rauda ta d'aga hai had'i da cewa


"Kaga,mu bar maganar aljanun nan kar su jimu,dan wallahi ni tsoronsu nike ji,wai shin ma ina zaka kaini ne,naga kana ta luluk'awa?


Dariya yayi sosai harda rik'e ciki


"Rashin sani yafi dare duhu"


Ta kallesa cikin rashin fahimta

"Bangane ba?


Ya tsayar da dariyar yana cewa


"Nufina inda zankai ki,da kinsan inda zan kaiki da baki ce inata luluk'awa ba"


Ta gyad'a Kai 

"To ina zaka kaini?


"Gidan aljanu"


Yabata amsar a tak'aice yana guntse dariya


 Galala,tayi mai wani kallo


"Sai dai ka kaini gidan sarkinsu"


"Nan ma idan kinaso zan kaiki ai kwantar da hankalinki"


Y'ar dariya tayi tana cewa

"Kasan duk ina tsoronsu ina kuma sonsu?


Ya kalleta na y'an sakwanni sannan yamaida kallonsa kan titi


"Bangane ba aljanun kikeso?


Ta d'aga Kai 

"Eh bari kaji inbaka wani labari,akwai wata rana ina kwance bayan sallar magriba,d'akin babu haske sosai najuya zan gyara kwanciya sai naga jariri  akwance kusa Dani,amma banga fuskarsa ba,mace ne ko na miji bansani ba,nak'ara kallo a karo na biyu still nagani,amma kafin in k'yafta idona sai naga babu komai,


Washegari nike ba y'an gidanmu labari har Nike ce musu,da ace zankuma ganin jaririn dana d'auka  shine suka dinga min dariya wai inje ind'auka ma aljanu d'ansu zan gane kurena"



Aasim ya jinjina kai fuskarsa na nuna alamun mamaki da jin labarin


"Cap kuma da kikagani baki ji tsoro ba?ai ni innine bazan iya bacci ba?



"Lallai baccina nayi harda munshari"


 Dede lokacin suka isa bakin wani gida,yayi horn


Masu gadi suka bud'e get


Wani madai-dai cin gidane me kyan gaske wanda tsayawa fasalta shima b'ata lokacine


Gabad'aya jikinta yayi sanyi kallon gidan kawai takeyi gabanta na fad'uwa


Ya faka motar,agefe yana cewa


"Muje ko?


Kallonsa tayi 

"Ina ka kawoni?


"Idan muka shiga zaki gani"


Ta girgiza Kai

"Aa bazan shigaba kafad'a min inane Nan?


Yasauke ajiyar zuciya hmmmmmm

"kinsan dai bazan kawoki inda zan cutar dake ba ko?


Shuru tayi tana k'ara kallon gidan jinsa da tayi tsit da alamun babu kowa aciki


"To inane Nan?me yakawo ta yamata?


Ya katse mata tunanin


"Please muje kinga yamma nayi "


Ajiyar zuciya tasauke me nawi,yafito yabud'e mata k'ofar


Tafito,yayi gaba tana binsa abaya




Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹


           🧞‍♂🧞‍♂

              🧞‍♂


               NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)


✍✍✍✍✍✍✍

  *GOLDEL PEN WRITER'S ASSOCIATION*    

✍✍✍✍✍✍✍


❄_We are bearers of sooo golden a pen We write assidiously percieven no pain Sooo magical Our creative golden pen Be hold our words  A product of our pen  Savour our words, for it will cause you no pain_❄




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



Dedicated to little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu



🅿AGE📕 1⃣1⃣



Wannan Page d'in nakune jinnul aashique group,ina me k'ara baku hak'uri akan rashin typing d'in da banayi dawuri.


Gaisuwa da fatan alkhairi ga 

Safnah

Maman ummi

Maman khalifa

Maman Khadijaa


Allah yabar zumunci


11:06 🕐am.     TUE,APR 16 ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Bissmillahir rahmanin rahim


Ya murd'a k'ofar falo,yana cewa


"Ina y'an gidannan suke,kufito ga matata na kawo muku"


Yafad'a cikin d'aga murya yana k'arasa shiga cikin falon


Wata kyakkyawar budurwa ta taso daga cikin falon dasauri tana fad'in


"Dagaske?tare kuke?


Bata hanya yayi yanacewa


"Gatanan kuwa kina gani"


Budurwar da bazata wuce sa'ar Raudan ba ta k'an-k'anme Raudan cikin farinciki da jin dad'in ganinta


"Oyoyo sister"


Harararta Aasim yayi

"Kinga nazma,saketa daga zuwanta ko hutawa batayi ba zaki wani ruk'ur-k'usheta salan ki gajiyar min da ita"


Nazma ta zame daga jikin Raudan tana dariya


"Afuwan d'an uwa, sister mu shiga kizauna"


Tak'arasa fad'a tana jan hannun Raudan zuwa cikin falon


Itadai Rauda butun butumi tazama,dan takasa cewa komai kallonsu kawai takeyi,ga kuma tambayar dake zuciyarta


Jin Aasim yakirata da matarshi,shida ko maganar soyayya bata tab'a shiga tsakanin su ba,miye na kiranta da matarshi?


Nazma ta zaunar da ita akan kujera tana cewa


"Mekikeson infara kawo Miki?gasashhiyar kaza,ko gasasshen rago? Talo-talo ko kayan ciki?


Aasim yadafa kansa cikin damuwa da surutun nazma


"Kinga fad'ama ammi tafito su gaisa sannan kizo kiyi shirmen naki"


Dariya nazman tayi tana wucewa


Rauda da batace komai ba har lokacin,ganin nazman ta wuce yasa takalli Aasim da sauri tace


"Ina Nan?


Gyara zama yayi yana bata amsa


"Gidan mu Mana"


Tasauke numfashi dansai lokacin hankalinta ya kwanta


"Shine baka fad'amin ba tuntuni?


Yad'aga gira

"To ba gashi yanzu nafad'a Miki ba"


Harararsa tayi tana kallon kayan jikinta


"Ai sai ka fad'amin tun a makaranta nan zamuzo inje incanza Kaya Amma......


Shigowar wata farar mata ya sa tayi shuru


Da ka kalli fuskarta ka kalli ta Aasim zaka gane itace mahaifiyar shi


Matar tazauna akan kujera idanuwanta akan Rauda


Rauda tazame k'asa tana gaisheta


Matar ta amsa fuskarta a sake tana cewa


"Koma kizauna y'ata"



Takoma ta zauna tana duban Aasim daya tashi daga kujerar ya koma wacce mahaifiyar sa take yazauna yana kama hannunta


"Ammi,nayi missing d'inki sosai"


Ammi tayi murmushi tana shafa kansa


"Nima haka,kana lafiya dai ko?


Ya girgiza kai


"Aa ammi"


Nan da nan ko yana yinta yasauya zuwa damuwa tafara tattab'a jikinsa alamun tana so ta ji zafin jikinsa


"Me ke damunka,ina kema ka ciwo"


Yayi dariya yana kama hannunta yana matsawa


"Kwantar da hankalinki ammi,lafiya ta k'alau"


Ta sauke ajiyar zuciya


"Harkasa hankalina ya tashi,katabbata babu abunda ke damunka?


Ya gyad'a kai yana murmushi


Rauda ko Sha'awa suka bata,dan dukkanin alamu akwai soyayya da shak'uwa me k'arfi a tsakaninsu


Dede lokacin nazma tadawo falon d'auke da wani fankacecen tire


Wanda yike shak'e da takarcen kayan ciye-ciye dana lashe-lashe


Aasim yarik'e baki ganin yadda tad'auko tiren da k'yar


"Nazma duk wad'annan kayan ina zaki kaisu?


"Na antyna ne,ita na kawo mawa"


Dariya sukayi gabad'aya,ammi tace


"To kai mata sashensa,dannasan nan bazata iya sakewa ta ci ba"


Nazma tace to tana juyawa


 Ammi tace tana kallon Aasim


"Yaro tashi kakaita sashenka"


Wata yarinya da bazata wuce shekaru biyu da rabi ba,ta tashigo falon rik'e da k'atuwar y'ar baby


Tafad'a jikin Aasim cike da jin dad'in ganinsa


Shima cikin farinciki yad'agata yana juyi da ita


 Suna ta dariya,sannan ya rungume ta yanacewa


"Ina kika je banganki ba tunda nazo sai yanzu"


"Nade tallon wuwa"


Tafad'a da maganarta ta yara da bata gama iyawa ba



Ya dire ta a k'asa yana yimata nuni da Rauda dabata lura da ita ba


Aiko tana ganinta ta ruga aguje tayi wajenta


Rauda tad'auketa tana kallon yarinyar,farace k'ar kamar lantarki, kyakkyawa,ga gashi da aka kama mata da rimbom wanda yasauka har gadon bayanta


Lokaci d'aya taji yarinyar ta shiga ranta,


"Miye sunanki?


Rauda ta tambayeta tana kallonta


Cikin gwalantonta yarinyar tace


"Tatida"


"Tatida? Rauda ta nanata 


Ammi tayi dariya tare da cewa


"Shahida ta ke so tace"


Rauda ta gyad'a kai tana murmushi

"Shahida,shekaraki nawa?


Hannu shahida ta d'aga tana nuni da yatsunta guda uku


"Shekararki uku?


Rauda ta tambaya tana mamakin wayon yarinyarShahida ta d'aga Kai

Alamar eh


Ammi tace

"Kinga y'ata karki biye ma shirmen shahida,tashi kuje kisa wani abu acikinki"


Rauda tayi dariya,tana mik'ewa rik'e da shahidan a hannunta


Aasim yayi gaba tana binsa a baya,wani madai-dai cin falo suka shiga


Komai na falon kalar golden ne,kama daga kan kujeru,kafet,labulaye kai komai na d'akin kalar golden akayi ado dashi


Yayi Mata nuni da kujera


"Bissmillah,zauna"


Ta zauna hankalinta na kan shahida gabad'aya k'aunar yarinyar ya shiga zuciyarta


Ta rasa dalilin hakan


Ko dan tanason fararen yarane oho


Aasim ya matso da zagayayyen tebur d'in da nazma ta d'aura tiren akansa gabanta yana cewa


"Madam ajeta fa zakiyi kici abinci"


Tad'an kallesa gami da cewa

"Nifa banajin yunwa"


Komawa yayi kan kujera ya zauna yana dubanta


"Kedai kice ganin shahida ya k'osar dake,da alamu tashiga ranki ko?


Rauda ta jinjina kai tana murmushi


"Kabari kawai,dan Allah ina mamanta take? 


In tambayeta ta bani ita"


Ya rausayar dakai yace yana mik'ewa yad'auki shahida


"Bari inkaita gurin ammi,dan ba barinki zatayi kici abincin ba"


"Please Aasim kabarta,zanci Allah"


Be saurareta ba ya sab'a shahida a kafad'a ya yi hanyar fita


Shihada na d'aga mata hannu alamar bye bye


Ajiyar zuciya Rauda tasauke,azuciyarta tana addu'ar allah yabata irin shahida


Bayan yafice tamaida kallonta ga tiren dake gabanta,babu abunda babu akai,nama,nono,abinci ma kala-kala gashinan tarkace wasu ma bata tab'a ganin kalar su ba


Takuma sauke ajiyar zuciya tana tambayar zuciyarta,haryaushe daga zuwanta aka shirya mata wad'annan abubuwan?


Tunda a fahimtar da tayi basuma san da zatazo ba


Shigowar sa ne ya katse mata tunanin data fara,


"Wai haryanzu baki fara cin komai ba?


Ya tambaya yana zama a gefenta dayike kujerar da take kai three seeter  ce


Bata ce mai komai ba,ya d'auko wani juice ya tsiyaya mata kofi yana mik'a Mata


Numfashi ta sauke tana kiran sunansa

"Aasim!


Yad'ago suka had'a ido


Tayi k'ok'orin cigaba da kallon cikin idonsa

"Meyasa kace y'an gidan ku ga matarka ka kawo?idan suka d'auka dagaske muna soyayya fa?


Hmmmmm ya sauke guntun numfashi


"Meyasa kika tambayeni?ko laifine dan nafad'i hakan?


Ta d'aga kai alamar eh tana kurb'ar juice d'in da ya mik'omata


Sannan tace


"Kadube kanka da kyau,kaduba irin baiwar kyau da allah yayi maka,sannan ka kalli gidan ku


Tafad'a tana zagaye falon da idanuwanta sannan tacigaba da cewa


"Kai ba k'aramin mutum bane,tayaya zaka dangantani da matar ka,kadubeni da kyau,ni ba kyakkyawa bace kuma ni ba y'ar babban gida bace,shin baka tunanin zasuji badad'i ayayinda kafad'i hakan?


Tak'ara sa maganar tana kallonsa


"Ina sonki"


Taji yafad'a,tayi y'ar dariya

"Ni maganar gaskiya Nike maka, please ka aje maganar wasa"


"Ina sonki"

Ya kuma fad'a


Ta ajiye kofin tana tambayar sa

"Wai kasan mekake cewa kuwa?


Akaro na uku ya kuma mai-maita wa

"Ina sonki"


Ta kallesa sosai tana nanata abunda yace


"Kana Sona?


Zamewa yayi daga kan kujeran yana kama hannunta


"Ina sonki Rauda,ina k'aunarki kece farin cikina"


Sororo tayi tana kallonsa tana kuma mamakin sa


Ya cigaba da cewa

"Meyasa baki fahimci cewa ina sonki ba tuntuni?


Ya kamata ace kin fahimci inasonki ko ta irin kallon da nike miki"


Ta zame hannunta daga rik'on da yayi mata tace


"Dan allah kabar maganar Nan, kaima kasan ba abu me yuwuwa bane"


"Miyene baze yuwu ba Rauda?

 

Ya tambaya da alamar damuwa a fuskarsa


Tasauke ajiyar zuciya tare da cewa


"Wai tayaya ma soyayya zata yuwu a tsakanina da Kai?


Nida kai sam ba mu dace da juna ba"


Mik'ewa yayi yana kama hannunta


"Tashi muje,infad'a agaban ammi,kisan cewa da gaske nikeyi"


Fizge hannunta tayi da sauri


"K'afad'a agaban ammi?dan allah karufamin asiri,ni muje ma ka maidani makaranta"


Tafad'a cikin zaro ido


Ya koma ya zauna yana sauke numfashi


"Shikenan,amma ki yarda ina sonki dagaske,dan Allah"


Dawowar nazma falon yasa suka bar zancen



"Haba antyna, kamar baki ci komai bafa nike gani"


Nazma tafad'a yayinda tak'ara sa shigowa falon


Rauda ta yi murmushi tace


"A k'oshe nike shiyasa"


Nazma ta gyad'a kai cikin nuna rashin jindad'i


"Shikenan Amma zan tattara miki su kitafi dasu,kuma dan Allah karkice aa"


Rauda ta gyad'a kai har lokacin da ragowar murmushi a fuskarta


"To shikenan nagode"


Ta k'arasa fad'a tana mik'ewa

"Muje kamaidani banaso dare yamin awaje"


Tafad'a tana kallon Aasim


Bece k'ala ba ya mik'e yana d'aukar wayoyinsa ya zuba su a aljihu


Yayi gaba,yayinda suka jera ita da nazma


Babban falo suka dawo,inda ammi take


"Badai har zaki tafi ba?

Ammi ta tambaya yayinda taga fitowarsu


Rauda ta durk'usa cikin girmamawa tace


"Eh zantafi,banaso nayi dare ne"


Ammi ta jinjina Kai


"Eh kinada gaskiya,jirani to inazuwa"


Tafad'a tana mik'ewa


Batafi minti biyar ba tadawo rik'e da k'atuwar leda


Tamik'a ma Aasim tace


"Gashi kasa mata amota,y'ata sai yaushe zamu sake ganinki?


"Insha'allah idan na samu lokaci"


"To shikenan nagode kinji"


Sukai sallama,Rauda na dube-duben inda zata hango shahida


Sai da suka fito zasu shiga mota,sannan ta hangota 


"Shahida"


Ta kira sunanta,aiko tana jiyo kiran ta rugo a guje


Rauda tad'auketa tana cewa


"Ina ta nemanki muyi sallama ashe kina waje"


"Tafiya da tiyi?


Shahida ta tambaya tana kallonta


Rauda tad'aga kai alamar eh


Aiko Sai tayi narai-narai da ido zatayi kuka


Cikin d'an mamaki Rauda tace


"Shahida,baki so intafi ne?


Tad'aga kai alamar eh batason tatafi


Rauda tayi murmushi soyayyar yarinyar nak'ara shiga zuciyarta


"Karki damu zandawo nan bada jimawa ba"


Shahida ta girgiza Kai alamar bata yadda ba


"Nide kan titafi"


Rauda tayi shuru tana kallon ta sosai hakanan take jin zuciyarta wani iri,dan ita kanta bata son rabuwa da yarinyar


Aasim dake tsaye yana kallonsu ya mik'oma shahida hannu alamar tazo


"Shahida zo inkai ki gurin ammi kinji,nan da kwana biyu zanzo inkaiki gurinta kinji?


Ta mik'a mai nata hannun yad'auketa


Yace

"Yauwa Small habibty"


Wata kyakkyawar mata da bazata wuce shekara talatin ba tak'araso wurin


Suka gaisa da Rauda sannan ta amshi shahida a hannun Aasim ta juya


Basu dena kallon juna ba ita da shahida har saida matar ta sha kwanar falon


Rauda ta sauke ajiyar zuciya me nawi tana maida kallonta ga Aasim


"Wannan itace mamar shahida?


Aasim ya girgiza kai yace


"Aa me kula da itace"


"To ina mamarta take"


Be bata amsa ba ya zagaya ya bud'e motar ya shiga


Itama shiga tayi tana nanata tambayar ta


"Nace ina mamar shahidar fa?


Yatada motar yana cewa


"Meyasa kike tambaya akanta?


"Saboda kawai inaso inganta,dan ta iya haihuwa data haifo kyakkyawar yarinya irin haka,allah zuciyata ta kamu da son yarinyar"


Ya jinjina kai


"To nikuma fa?


Takallesa tace

"Kai kuma me?


"Zuciyarki bata kamu da sona ba?


Ta jingina da kujerar motar tana bashi amsa


"Dan Allah ka ajiye maganar wasa"


Ya jinjina kai yace.

"To shikenan tunda soyayya kin mai data wasa bari inyi miki ta gaske


Zaki aure ni?


"Miye?

Tatambaya tana d'an zaro ido


Yace

"To kince maganar soyayya wasace,aure kuma ai shi gaske ne ko?shine nace zaki aureni?


"Dan Allah ka rufamin asiri"


Tafad'a


Ya k'ara gudun motar yana cewa.

'kamarya in rufa miki asiri?


Ta gyara zama tana dubansa


"In aureka?cap ai tsoratani zaka rink'ayi idan dare yayi"



Yayi dariya har fararen hak'oransa suka bayyana


"Nidai nace ina sonki,kisoni ko karki soni wannan matsalar ki,danni soyayya dake ba gudu ba ja da baya"


Dariya ta kuma yi

"Allah Aasim bazan iya soyayya dakai ba,kafi k'arfina Allah"


Ya tab'e baki

"Nagaya miki wannan matsalar kice,amma ni inkinga na ja da baya to nadena numfashi ne Allah"


Dariya tayi tana girgiza kai batare da tak'ara cemai komai ba


Ana kiraye-kirayen sallar magriba suka koma makarantar


Bayan tafito, yafito mata da k'atuwar ledar da ammi tabata ya mik'ama ta


"Masoyiya gashi"


Harararsa tayi

"Wacece masoyiyar taka?


"Ke Mana,kodayike matata yakamata ince tunda baki san kalmar wasa"


Yafad'a cikin tsokana yana gimtse dariya


Itama dariyar tayi ta amshi ledar tana juyawa

"Nagode saida safe"


Murmushi kawai yayi,saida tad'an yi nisa sannan yace da k'arfi


"I love you habibty"


Wai gowa tayi dasauri tana kallon mutanen dake kai da komowa


Ze kuma magana tayi mai nuni da yayi hak'uri dan tasan ba k'aramin aikin d'alubai bane su taru suna kallonsu


Murmushi yayi yana kuma fad'a k'asa-k'asa yadda motsin bakinsa kawai ta hango


Ta maida mai martanin murmushin tana juyawa da sauri


Tana shiga d'akinsu ta tadda salma na ta patrol a d'akin da alamu hankalinta atashe yike


Rauda na ganin haka ta rungume ta tabaya tana fad'in


"K'awalliya romon jab'a,nasan duk rashin ganina ne yasa aketa patrol,to gani na dawo"


Salma ta galla mata harara tana k'wace jikinta


"Sakeni ni,kinsa hankalina yatashi yadda y'an kidnapping d'innan sukayi yawa gabana nata fad'uwa,ina fargaban ko su sukayi awon gaba dake.....



Dariya Rauda tayi sosai,ta zauna gefen gado tana kallon salmar


"To da ba sai ki saido gonar ki kibiya a sakoni ba"


Salma takuma galla mata harara tace


"Wace gona?ai nairata baza tayi ciwon kai ba"


Dariya Rauda takuma yi


"Amma ai idonki ze yi ko,dannasan idan kika dunga rusa kuka sai hawayenki sun k'are"


Tsaki salma taja, tabud'e tukunyar girkin da take yi batare da ta sake kula ta ba


Rauda ta taso daga gefen gadon ta dawo kusa da ita ta zauna


"Kinga k'awata,kiyi hak'uri,wallahi ina fitowa daga lectures  Aasim yajani wai muje yawo"


Salma tad'ago tana kallonta


"Yawo Kuma?kuma kika bishi,allah Rauda kiyi hankali da Aasim d'innan,dan wallahi y'ay'an masu kud'i ba kirki garesu ba"


Rauda ta girgiza kai had'i da cewa


"Aa shi ba haka yike ba,ba yadda kike tunani bane,gidan su yakaini,gidan iyayenshi kinga ma abunda mahaifiyar sa tabani"


Tak'arasa fad'a tana janyo ledar,tafito da kayan dake ciki


Atamfofi ne masu tsada guda uku,sai less da doguwar jallabiya,sannan turarruka da kayan kwalliya


Salma ta saki baki tana d'aga kayan


"Daga zuwa gaisheta shine ta baki wannan uban kayan"


Rauda ta jinjina kai tare da cewa


"Wallahi k'awa bakiga kirkin mutanen ba,yadda suke da kud'i da kyau,saiki rantse zasuyi wulak'anci 


Amma sam abunda suke dashi be rufe musu ido ba,baki ga yadda suka tarbeni ba,kuma ma kinsan me?


Salma ta girgiza kai

"Inafa na sani ai sai kin fad'a"


"Wai cewa yayi yana Sona"


Rauda tafad'a


Salma ta zaro ido tace


"Wa? Aasim d'in?


Rauda tad'aga mata kai alamar eh


"Babbar magana,to ke mekika ce Masa?


Rauda ta mik'e tace

"Me ko zance masa,ce masa nayi ni bazan iya soyayya dashi ba dan sam bamu dace da juna ba"


Salma ta jinjina kai gami dacewa


"Gaskiya Kam,amma kuma da baki cemai haka ba k'ila rabon jindad'i ne ke kiranmu"


Girgiza Kai Rauda tayi tana dariya tashige toilet dan d'auro alwala


Da daddare,tana kwance bacci yakasa d'aukar ta,hakanan take jin zuciyarta cikin farinciki mussaman idan ta tuno maganganun sa


Ta duba agogo k'arfe d'aya saura


Gyara kwanciyar ta tayi tana rufe ido da niyyar bacci


Saidai a memakon baccin yad'auketa, zuciyarta ce ta hasko mata kyakkyawar fuskarsa alokacin da yike dariya


Ta matse filon dake hannunta a k'irjinta, ahankali bakinta ya furta


"Please zuciya ta kada kifara son Aasim, Aasim yafi k'arfinki ta ko ina ba sa'an ki bane please"


Wayarta ce tayi k'ara alamar shigowar message


Tajanyo wayar ta bud'e


Ganin numban Aasim yasa tayi saurin bud'e wa k'irjinta na d'an bugawa


"Amincin Allah ya tabbata ga tauraruwa ma'abociyar haske da k'yal-k'yali, hak'ik'a a yau dana bayyana miki sirrin dana dad'e ina b'oyewa acikin zuciyata,


Naji kaman na sauke wani nawi da ya rataya a kaina,bazan iya kwatanta miki irin k'aunar da nikeyi miki ba 


Ina sonki habibty!


Murmushi tayi tana jin wani farinciki na ratsa zuciyarta ajiye wayar tayi tana lumshe idanuwanta


Wani bacci medad'i yad'auketa


Washegari bata da lectures,hakan yasa suka kwashi kayan su dayayi datti suka fara wanki



Suna cikin wankin kira yashigo wayarta,salma dake kusa da wayar tad'auka zata mik'o mata


"Aje ta mugama kawai"


Salma takalleta tace


"Aasim ne fa"


Rauda ta jinjina kai

"Nasani ai"


Salma ta ce


"Ya akayi kikasani bayan baki duba wayar ba?


Murmushi tayi tana bata amsa


"Saboda gabana yafad'i lokacin da kiran yashigo"


Salma ta rik'e baki


"Kai Rauda badai har kinfara sonshi ba?


Rauda ta girgiza kai


"Allah bawai yau kad'ai ba,tun farkon had'uwarmu,indai kiransa zeshigo wayata to sai naji gabana yafad'i


Haka ma ko ganinsa nayi"


Salma ta matse kayan dake hannunta tana cewa


"Kedai kice kinfara sonsa kawai"


Ganin bata yadda da abunda tace ba yasa tabar zancen


Bayan wata d'aya

Soyayya me k'arfi tashiga tsakaninta da Aasim tayadda inbata ji muryarsa ko ta gansa ba, bata jin dad'i sai taji gabad'aya ta rasa sukuni


Duk yadda tayi da karta sa soyayyar sa aranta kasawa tayi dan shi d'in na dabanne


Arana sai yakirata fin sau goma,kuma duk sanda yakira da irin zafafan kalaman da yike fad'a Mata masu matuk'ar rikita mata zuciya


Kamar kullum tana mak'ale da waya a kunnenta suna fira


Tace 

"Ni fa yunwa nike ji kuma yau batajin cin abinci wallahi"


Daga can b'angaren yace


"To mekike son ci habibty, fad'a min ko menene shi zan nemomiki shi"


Ta girgiza kai kamar yana ganinta


"Dambu nike son ci kuma babu inda zaka samo dambu"


"Ina zuwa"


Kawai yace ya kashe wayar


Bayan minti talatin sai gashi yakuma kira tana d'auka


Yace

"Kifito ina wajen hostel"


Tace to,tana ajiye wayar


Kasancewar ana sanyi a lokacin rigar sanyi kawai tad'aura akan doguwar rigar dake jikinta


Tafito,yana tsaye ya jingina da wata bishiya


Tayi mai sallama ya amsa yana sakar mata murmushi me cike da so da k'auna


Ya mik'o mata ledar dake hannunsa yana cewa.


"Amsa maza kije kici,banason kirink'a zama da yunwa"


Amsa tayi tana tambayar sa


"Menene aciki?


"Ba dambu kikace kinason ci ba? shine aciki"


Kallonsa tayi da d'an mamaki


"Habadai?


Ya jinjina kai


"To kiduba kigani Mana"


Tako bud'e ledar ta duba take away d'in da yike ciki


Dambunne kuwa yaji zogale,sai zuba k'amshin man k'uli yikeyi


Mamakine ya kamata


"A ina kasamo dambu a darennan?


Yayi murmushi

"Kedai ba cine naki ba?dan haka kije kici"


Ta girgiza kai tace


"Aa saikafad'amin inda kasamo shi,dan a iya sanina ba inda ake saida dambu anan kusa-kusa kai ko da ranane


Ballantana da daddare, please kafad'a min"




Hak'ik'a naji dad'in comments d'inku,ina kuma k'ara godiya a gareku yawan comments d'in ku shike k'ara k'arfafamin gwiwa Page 12 yana zuwa insha Allah,taku akullum




Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: 🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹


             🧞‍♂ 🧞‍♂

                🧞‍♂


                 NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)



Dedicated to Little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*




🅿AGE📕 1⃣2⃣


Wannan Page d'in nakine  mamana,allah ya k'ara miki lafiya yasa kaffarane, ina k'aunarki araina domin kin kasance uwa tagari me share min kuka na a kodayaushe.🥰


NA KASA MANTAWA DAKE😭

Dede da rana d'aya, kodayaushe cikin tuna ki nikeyi, hak'ik'a nayi babban rashi da na rasaki,y'ar uwata hajara aliyu allah Nike rok'o ya jik'anki da rahama,ya gafarta Miki,yasa aljannah ce makomarki Amin😭😭😭



8:57🕐am.     SUN,APR 21✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Bissmillahir rahmanin rahimYa sauke numfashi idanuwansa na kanta,yace


"Akwai wani sabon restaurant da aka bud'e babu kalar abincin gargajiyan da basa saidawa,kuma har dare suna kaiwa,anan na siyo"


Ta jinjina Kai


Ya cigaba da cewa

"Sannan dakike cewe a iya sanin ki babu inda ake saidawa a kusa -kusannan yawo kike yi? Keda sai kiyi sati ma wani zubin baki lek'a ko wajen makaranta ba"


Tayi dariya tana gyad'a Kai


"Hakane,to nagode allah ya k'ara bud'i "


Ya amsa da Amin


Taja iska alamar sanyi na ratsa jikinta sosai tana tana mammatse jikinta da yike rawa kad'an saboda sanyin dake kad'ata


"Wai shin kai baka jin sanyi ne?


Ya bata amsa

"Me kikagani?


Rauda tace

"Gani nayi bakasa rigan sanyi ba,kuma ko rawar sanyi bakayi"


Aasim yayi murmushi

"Kafinnazo nan inajin sanyi sosai,amma ina had'a ido dake,sai naji wani d'umi na ratsani, gabad'aya sai naji sanyin ya tafi"


Tayi dariya tana girgiza Kai

"Kai ko?


Shima dariyar yayi yana kwai-kwayar yadda take magana


"Ni me nayi?


Dariya takuma yi sosai tace


"Allah har fargaban ayi hutu nikeyi,saboda zanyi missing d'inka,da dariyar da kake sani,tunda nahad'u dakai ka kawarda duk wata damuwata kasanya ma zuciyata farin ciki ina godiya sosai"


Murmushi yayi me cike da abubuwa da yawa


"Kin can-canci komai habibty,zan iya yimiki komai,sannan zan iya yin komai akanki"


Itama murmushin takeyi


"Dagaske?zaka iya yin komai akaina?


Ya jinjina kai

"Dagaske habibty,zan iya bada rayuwata akanki"


Wata sassanyar ajiyar zuciya tasauke,tana jin wani farinciki na ratsa illahirin zuciyarta


Ta d'aga kai tana kallon saman bishiyar wacce iska ke kad'a ganyayyakinta,suna kad'awa ahankali


"Bansan meyasa kake sona ba,duk da nasan matsayina be kai ace ka soni ba"


Yad'an matso gab da ita suna kallon juna


Yace

"Nima kaina bansan meyasa ba,abu d'aya ne nasani na kuma yarda dashi,shine allah ne ya jarabceni da k'aunarki,habibty bazan iya rayuwa idan babu keba,kuma kada kiyi tunanin nafad'a mikine dan kawai soyayya


Wallahi dagaske nikeyi,ina k'aunar ki"


Ta kuma sauke ajiyar zuciya da yin shuru na y'an sakwanni sannan tace


"Nima ina sonka Aasim,kuma insha allahu zan rayu tare da Kai,dannasan zan rayu cikin farin ciki idan na kasance tare da Kai"


Aasim yayi murmushi da alamu maganar da ta fad'a tayi masa dad'i sosai


"Nagode habibty,bari nabarki kikoma ciki,tunda sanyin na damunki"


Ta gyad'a kai tace


"Shikenan nagode, Saida safe"


"To sai da safe"


Tafad'a tana juyawa,harta d'an yi nisa tajuyo 


Yana tsaye inda tabarsa yana kallonta


Tace

"Yadai da magana ne indawo?


Ya girgiza kai yace


"Aa,kawai inaso inga shigarki ne tukunna sai inwuce"


Ta gyad'a Kai tana murmushi 


Sannan taci gaba da tafiya


"Rauda!


Ya Kira sunanta,ta waigo tana kallonsa batare da ta amsa ba


"Ina sonki"


Yafad'a,takuma yin murmushi tare da juyawa dasauri,tashige ciki


Koda ta koma d'aki, murmushi be bar fuskarta ba,taci dambun sosai tasha Lipton sannan ta kwanta zuciyarta cike da tunaninsa


Washe gariDa wuri ta shirya zuwa lectures,tana tafiya tana tunanin meyasa be kirata ba yau,dan kullum da asuba sai ya kirata,shike tashin su sallah,


Haka ma idan gari yayi haske sai ya kirata yace ta tashi ta shirya


Ta ciro wayarta ta latsa numbansa taji a kashe


Ta maida wayar jaka taciga ba da tafiya 


Wunin ranar wayar sa bata shiga ba,data kira sai taji a kashe


Tashiga damuwa sosai,dan bata tab'a kiran wayarsa taji a kashe ba


Har ta koma hostel, tana k'ara trying d'in kiran


Amma still a kashe

Ta yada jakar ta a k'asa tana zubewa a kan katifa


Salma dake zaune ta kalleta tana cewa


"Yadai?duk gajiyar ce?


Ta d'aga kai alamar eh tare da cewa

"Da gajiyar da kuma damuwa"


Salma tace

"Damuwa Kuma? Tamece?


Ta sauke numfashi tana tashi tazauna


"Yau tun safe Nike kiran wayar Aasim a kashe,shine duk hankalina ya tashi wallahi,dan bantab'a kiransa naji irin haka ba"



Salma ta jinjina kai

"Gaskiya dole kishiga damuwa,to ko wayar tasa ta fad'i ne?


"Nima nayi tunanin hakan,amma kuma da fad'uwa wayar tayi,da yazo yafad'a min kuma da na gansa acikin makaranta,amma fa banga alamunsa ba,har inda yasaba tsayawa naje bangansa ba, shiyasa nike tunanin ba lafiya ba"


Salma ta jinjina kai

"Gaskiya, to amma kik'ara gwadawa anjima insha'allah zata shiga,k'ila abubuwane suka mai yawa ya kashe"


Rauda tayi shuru kawai dan ita zuciyarta tafi bata ba lafiya ba


Daren ranar batayi wani baccin kirki ba,washegari ma haka takira wayar yafi sau d'ari amma abu d'aya ake gaya mata,akashe


Hankalinta ya tashi sosai,ko abinci takasa ci,bata tab'a sanin tana k'aunar sa ba sai a lokacin


Ahaka aka kwashe kwana uku, lokacin tagama jigata da rashin sa


Hakan yasa bayan tafito daga lectures tayanke shawarar zuwa department d'insu ta tambaya


Suka ci karo da salma ita ma tafito daga nata lectures d'in


"Yadai Rauda ina zakije?


Salma ta tambaya,

"Zan lek'a b'angaren su Aasim ne intambaya nagaji da zama cikin rashin sanin wani Hali yike ciki"


Salma ta jinjina Kai

"To muje inrakaki nima abun nadamuna wallahi"


Suka jera suka tafi,da isarsu suka tadda d'alubai na zaune suyi group-group sunata fira da shewa da alamu sunfito daga lectures ne,wasu kuma suna ta bitar karatu


Wani matashi suka gani a zaune shikad'ai da handout a hannunsa


Suka k'arasa gurin suka mai sallama


Ya amsa fuskarsa a sake suka gaisa,sannan Rauda tace


"Dan allah ina tambayar Aasim ne,kwana biyu bana ganinsa bansani ba ko lafiya?


"Aasim?


Matashin ya tambaya, Rauda ta d'aga kai tana fad'in


"Eh "


Yace

"Gaskiya bangane shi ba saidai ku tambayi wancan shine yike da list sunayen gabad'aya kuma shi ze iya saninshi,amma ni ba lallai insanshi ba saboda muna da yawa"


Yak'arasa fad'a yanayimata nuni da wani


Rauda ta jinjina kai


"Hakane,nagode sai anjima"


Tafad'a sannan suka k'arasa gurin wanda ya nuna musu suka mai sallama


Sannan suka tambayeshi


Shima mai-maita sunan yayi

"Aasim, Aasim,anya anan department d'in kuwa?Ta d'aga kai

"Eh"


Yad'an yi shuru yana nazari sannan yace


"Gaskiya bangane shi ba,abokina ko kasan me suna irin haka haka?


Yak'arasa fad'a yana kallon wanda yike kusa da shi


Shima girgiza kai yayi alamar be sani ba


Wanda suka fara tambayar yace


"To gaskiya bamu san wani me suna haka ba,sai dai inba a department d'inmu yike ba"


Rauda ta girgiza kai tace


"Anan fa yace yike,yananan zaka ganshi wani fari dogo haka"


Ya ajiye numfashi yace

"Nafad'a miki bansanshi ba gaskiya"


Ta gyad'a kai cike da damuwa a cikin zuciyata


"Shikenan nagode,mutafi Salma"


Suka juyo jiki babu k'wari


Salma tace

"To ya akayi haka Rauda?ni al'amarinnan yafara d'aure min kai fa,ace a department d'insu babu wanda yasansa?


Rauda ta sauke numfashi me nawi batare da ta ce komai ba, Dan gabad'aya jikinta yayi sanyi


Wata mota ce tasha gabansu,cikin b'acin rai salma Tafara fad'a


"Wannan wani irin wulak'anci ne zaka wani.......


Kasa k'arsawa tayi yayinda ya sauke Glass d'in motar


Rauda ko kanta na k'asa ko kallon motar batayi ba dan damuwar dake zuciyarta nema takeyi tafi k'arfinta 


"Habibty...


Taji anfad'a, dasauri tad'ago kanta,suka had'a ido


Ya sakar mata lallausan murmushi 

"Habibty,bazaki amsa kiran nawa bane,duk fushi dani d'inne ya jawo haka?


A memakon tabashi amsa,sai kawai idanunta suka cicciko da k'walla 


Nan da nan hawaye yafara wanke mata fuska


Dasauri ya bud'e marfin motar,yafito yana fad'in


"Subhanallah,kuka habibty,me yake faruwa?


Ya tambaya hankalinsa a tashe


Ji tayi k'afafunta suna neman kasa d'aukarta,hakan yasa ta durk'usa tana cigaba da yin kukan


"Habibty please kiyi hak'uri,tashi kishiga  mota, banaso hankalin mutane ya dawo kanki"


Kasa mik'ewa tayi saida Salma ta kamata tukunna,sannan tashiga motar


Salma tawuce tabarsu,itako Rauda kifa kanta tayi agaban motar tana cigaba da yin kukan da ta rasa ko na menene


Ya sauke numfashi yana cewa


"Dan girman Allah habibty,ki wa girman allah kiyi shuru,wallahi kukanki sosamin zuciya yike yi"


D'agowa tayi tana kallonsa da jik'akk'un idanunta



"Inyi shuru fa kace?kasa nashiga tashin hankali da tsananin damuwa,ina fargaban ko ba lafiya kake ba,inata fargaban ko wani abune ya sameka,ashe lafiyar ka k'alau.....


"Please kiyi hak'uri nasan nayi kuskure, Amma ba wai da niyya nai hakan ba,tafiya ce takamani kuma cikin gaggawa......


"Okay idan tafiya takamaka baka iya sanar min kafin katafi?


Ta katseshi,ya girgiza kai yace


"Naso insanar dake kafin intafi amma saboda yadda tafiyar tazo min bansamu daman kiranki ba"


"To dakaje fa,meyasa baka kirani ba?


Ta kuma tambaya still idanuwanta na kansa


Ya bata amsa da yanayin damuwa a fuskarsa


"Habibty inda naje waya bata shiga shiyasa"


Jingina tayi da kujerar motar batare da ta k'ara cewa komai baYa matso kusa da ita yana cigaba da cewa


"Abunda natsana a duniya shine inga hawaye a fuskarki, narok'eki habibty, ki tsayar da hawayennan haka"



Banza tayi dashi,ya gyad'a kai yana cewa

"To shikenan cikin biyu yanzu dole za ayi d'aya

Ko ki tsayar da hawayennan,ko kuma ki juyo da fuskar yana zubowa ina lashewa"


Harara ta galla Masa,yayi dariya yana kama kunnuwansa 


"Please habibty I'm sorry"


Yadda ya lank'wasa muryar tasa taso tasata dariya


Ta share hawayen tana fuskantarsa,


"Dan Allah karka k'ara yimin irin haka,bakasan halin da na shigaba wallahi nikad'ai nasan tashin hankalin dana shiga"


Tafad'a cikin marai-raice fuska


Ya jinjina kai

"Shikenan, insha'allah bazan sake ba,kin hak'ura yanzu?


Ta d'aga kai alamar eh


Yayi murmushi

"Yauwa tawan Allah yabar minke,yanzu fad'amin ina kikeso muje,gurin shan ice cream,gurin cin tantabara ko gurin saida dambu?


Dariya tayi had'i da fad'in


"Sai dai gurin saida fate"


Shima dariyar yayi yana tada motar


Ita ko Rauda zuba mai fararen idanuwanta tayi tana sauke ajiyar zuciya



"Zahiri tana sonsa acikin zuciyarta, Wanda bata tab'a tunanin zata k'ara sa wani d'a namiji a cikin zuciyarta ba


Dan gabad'aya a rayuwarta ta tsani soyayya,takuma yi alk'awarin bazata sake yinta ba


Sai gashi Aasim ya canza mata tunani yasa ta k'ara komawa soyayya


Ajiyar zuciya ta sauke me nawi


Aasim ya juyo yad'an kalleta sannan yamaida kallonsa ga titi yace


"Yadai habibty,wannan ajiyar zuciya haka?


Ta kuma sauke wata a karo nabiyu sannan tace


"Aasim kasa na karya alk'awarin dana d'aukar ma kaina,na bazan sake yin soyayya ba,gashi yanzu zuciyata tagama amincewa dakai


Inada wata kalar zuciya da bata iya yin soyayya ba,idan harna fara son mutum to gabad'aya hankalina gushewa yikeyi


Dan allah kada kayi amfani da son danike maka,ka wahalar min da zuciyata,nasha wuya a baya banaso nasake mai-maita wa"


Ta k'arasa maganar idanuwanta na ciccikowa da hawaye


Da alamu jikinsa yayi sanyi da jin magan-ganunta


"Insha'allah habibty,bazan zama mesaki damuwa ba,abu d'aya nike so agareki...


Yad'an dakata, Rauda ko kallonsa takeyi


Yavcigaba da cewa


"Inaso kiyimin alk'awarin ko da nan gaba kin gano wani abu da baki san da shi ba a tare Dani,to kiyi min alk'awari bazaki rabu dani ba,ba kuma zaki dena sona ba, sannan kuma zaki gafarceni abisa b'oye mikin da nayi"


Kallonsa takeyi cikin rashin fahimta dan gabad'aya bata fahimci inda maganarsa ta dosa ba


"Bangane ba,dama kana b'oye min wani abu ne?to meyasa?kuma menene shi?


Yayi murmushin da ya tsaya masa iya labb'a kawai


"Lokaci na zuwa,da nasan dole zaki gane gaskiya,aduk lokacin dana tuna hakan sai inji hankalina ya tashi dan bansan wani hukunci zaki d'auka a lokacin ba"


Ta sauke guntun numfashi tace.

"To wai miye kake b'oyemin ne?


Sai kuma ta dakata alamar ta tuna wani abu, tacigaba da cewa


"Owo nafahimta,kana da aure ne ko?kana da mata shine ka b'oye kak'i fad'amin ko?


Ya murmushi yana girgiza kai


"Aa,wallahi bayan ke bani da wata Mata"


Tabud'e idanunta tana masa wani kallo


"Eyen,ni d'in ko?to yaushe na zama matarka?


Yad'an yi jim kaman ya naso ya tuna


"Eh to,kaman shekaru hud'u da suka wuce"


"Kai lokacin ma ko sanina kayi,duka-duka ko rabin shekara ma munyi da had'uwa ne?


Tafad'a tana k'walalomai ido


Yayi dariya yace


"Agurinki kenan amma ni agurina had'uwarmu tun bayan shekara ashirin ne?


Ta kuma bud'e idanuwanta sosai


"Kai, lokacin ma ko haihuwata anyi?ohhh na tuna anhaifeni lokacin kenan tun ina jaririya ko?


Ta tambayesa cikin yi galala da baki


Dariya yayi Yana paka motar a harabar gurin saida Ice cream


"Kinga habibty muje musiyo muyi mu koma,yanzu aka kirani akafad'a min muna da meeting"


Tace to,harzata bud'e motar kuma sai takoma tazauna


"Kace yanzu aka kiraka?da wace wayar to ince ga wayarnan a ajiye,kuma ni tunda nashigo motarnan banji ankirata ba?


Yayi k'ok'orin tsaida natsuwarsa guri d'aya yace


"D'azu nike son ince"


Gyad'a kai tayi tana tab'e baki


"Ook muje"


Basu wani b'ata lokaci ba,suna shiga tazab'i kalar ice cream d'in datake so suka fito


Bayan yatada motar sunfara tafiya tace


"Namanta ban tambayi shahida ba,tana lafiya? Ya ammi da nazma?


"Duk sunanan k'alau"

Yabata amsa a tak'aice


Gudu yayi sosai saboda meeting d'in da yace suna dashi


Yana ajiyeta ya juyaDa daddare bayan tayi shirin kwanciya,ta kira wayarsa,tagama ringing be d'auka ba


Tana ajiye wayar message na shigowa ta bud'e


"Habibty bamu gama meeting d'inba haryanzu,ki kwanta kiyi bacci ina sonki"


Murmushi tayi tare da rungume wayar a k'irjinta baccin da batayi kwana biyu ba kuwa yad'auketa


Bayan sati d'aya, hankalinta ya kwanta,dan suna tare soyayyar su nadad'a yin k'arfi


Ranar wata laraba,tashirya dan zuwa gurin saloon,dama sunyi dashi intaje shi zeje yad'aukota


Saboda yace yana da meeting a lokacin


Hakan yasa tafito bakin titi ta tari adai-daita sahu


Sun d'an yi nisa kad'an wata kyakkyawar budurwa ta tsaida a dai-daitan da Rauda ke ciki



Da sallama tashiga, Rauda ta amsa suka gaisa


Napep d'in tacigaba da tafiya


Budurwar da tashi ga napep d'in tace


"Rauda ko?


Da mamaki Rauda ta kalleta jin takira sunanta


"Eh itace"


Budurwar tayi murmushi

"Ni kuma saima"


Rauda tak'ara kallonta, bata tab'a ganinta ba,to a ina tasan ta?har tasan sunanta?


Saima ta katse mata tunanin da takeyi


"Kinyi mamakin kiran sunanki da nayi ko?


Rauda ta d'aga Kai

"Eh gaskiya danni bansanki ba,to ko makarantar mu kike?


Saima ta girgiza kai alamar aa


"Ba a makarantar ku nike ba malama Rauda"


Rauda ta jinjina Kai

"To ya akayi kikasan sunana?


Saima ta kuma yin murmushi,sunan ki ai sananne awurina,ke bama nikad'ai ba gabad'aya ahalina,babu wanda be sanki ba"


Mamaki yakuma kama Rauda


"Ahalinki? bangane ba"


Saima ta d'aga kai tace


"Eh,amma bawannan surutun ya kawoni ba,meyasa zuciyarki take saurin amincewa da mutane?


Baki san akwai wasu jinsi dazasu iya biyowa ta suffar mutane su cutar dake ba?


Cikin raahin fahimta Rauda ke kallonta amma takasa K'ara cewa komai


Dan ji tayi tsigar jikinta tafara tashi


Saima takuma yin murmushi,tana cigaba da cewa


"Ya kamata dai kirink'a ban-bance jinsin mutum da kuma na aljani,domin yana tare dake akodayaushe


Nabarki lafiya"


Tana gama fad'ar haka ta dire ko cewa me napep d'in ya tsaya batayi ba


Rauda tsoro ne yakamata, jikinta yayi sanyi sosai


Dede lokacin me napep d'in yatsaya a k'ofar shagon saloon d'in


Taciro kud'insa tabasa, dasauri tashiga shagon tazauna tana maida numfashi


Me saloon d'in me suna Amira tace


"Yadai customer?lafiya naganki wani iri?


Rauda ta girgiza Kai


"Aa bakomai"


Amma cikin zuciyarta mamaki da kuma al'ajabin saima ne,me take nufi da yakamata ta rink'a ban-bance jinsin mutum da na aljani?


Domin yana tare da ita a kodayaushe?


Maganar Amira ce ta katse mata tunanin data tafi


"Me za'amiki, retouching ko steaming?


"Steaming"


Tabata amsa a tak'aice


Har aka kammala mata bata dawo cikin natsuwarta ba,juyayin abunda yafaru kawai takeyi


Tana zaune ana taje mata kai, Aasim yayi sallama dayike yasan wurin ya tab'a kawota


Amira ce ta amsa tana bashi izinin shiga


Yashiga shagon da murmushi a fuskarsa yana kallon gashin kanta da yayi bak'i sid'ik yana ta shek'i


"Wow habibty kinga yadda gashin yayi kyau kuwa?


Amira tayi dariya tana fad'in


"Sai ka biyani da yawa"


Ya rausayar da Kai yace

"Baki da matsala, tunda kina gyara min matata"


Murmushi Rauda jeyi


"Ai nayi zaton bazaka zo ba"


Ya girgiza Kai yace


"Haba nina Isa?muna gama meeting d'in nan nayo direct"


Ta jinjina Kai tana janyo d'an kwalinta zata d'aura gaban makeken madubin da ke manne a bango


Gabanta ne yafad'i Ras, yayinda ta ga Aasim sanye da  wasu kaya irin na sarakai ta cikin madubin kuma yayi wani bau farinsa da kyansa ya ninka wanda tasani


Tayi gaggawar kallonsa a fili


Yana tsaye yana bawa amira kud'i sanye da k'anan Kaya


Ta murza idanuwanta dasauri tana ganin kaman gizo idanun ke mata


Takuma kallon madubin, still da kayan sarautar ta k'ara ganinsa


Maganar saima ce tadawo Mata, gabanta yayi wani mugun fad'uwa


Tayi saurin kauda kanta a madubin ganin madubin yafara yimata dishi-dishi


Kallonta yayi yace


"Yadai naganki a daburce meyafaru?


Ta girgiza kai dasauri batare da tace komai ba


Amira tace

"Nima dai yau tunda tashigo haka naganta"


Yakuma kallonta sosai 

"Habibty,lafiya?meke faruwa"


Kuma girgiza kai tayi alamar babu komai


Ya jinjina kai amma be yadda babu komai d'in ba


"Shikenan muje"


Yayi gaba yana yiwa amira sallama


Bin bayansa tayi da kallo gabanta na fad'uwa


Yad'an waigo yana dubanta ganin tana tsaye bata da niyyar tafiya


"Yadai,ko baki gama bane"


Ta girgiza kai tana d'aga k'afarta datayi mata nawi a tafito


Yabud'e mata motar tashiga,sannan ya shiga ya tada


Yana cewa

"Kifad'a min meke faruwa,ni nasan akwai wani abu hakanan dai bazan ganki a daburce ba"



Tayi k'arfin halin danne tarin fargaban da yike zuciyarta


"Aasim,intambaye ka zaka fad'amin gaskiya"


Ya kalleta


"Eh zanfad'a miki indai nasani"


Ta jinjina Kai tace


"Aasim kai mutum ne?


Ta jeho mai tambayar da be shirya jinta ba


"Eyeh,mene?mekika ce?


Yafad'a cikin sark'ewar murya


"Nace kai mutum ne?


Yayi shuru na y'an sakwanni sannan yace


"Me yasa kika yimin wannan tambayar?


Ta gyad'a kai fad'uwar gabanta na dad'a tsananta


"Akwai abunda nagani da nakasa fahimta, please k'afad'a min gaskiya kai mutum ne?


Ya sauke numfashi tare da cewa


"Eh ni mutum ne"


Girgiza kai tayi cikin rashin yadda


"Banyadda ba,idan kai mutum ne ya akayi siffarka,da kayan jikinka suka sauya acikin madubi?


Ya taka burki da sauri yana kallonta


"Suffata Kuma,ayaushe?saidai in gizo idanun ki suka Miki"


Ta gyad'a kai tana zage jakar ta ta ciro reza ta bud'e tare da    sawa akan yatsanta ta danna


Sai ga jini b'ul-b'ul,


"Miye haka habibty,yanka kanki kikayi fa?


Yafad'a dasauri,ta jinjina

" kai nasani ai,kai ma inaso ka yanki yatsanka,saboda in tabbatar da abunda nike zargi"


Girgiza kai yayi


"Habibty baki yadda dani bane?


"Ko na yarda dakai inaso inga jini a jikinka,idan har kasan abunda kafad'a min gaskiya ne to ka amsa kayi abunda nace"


Tafad'a cikin wani irin yanayi na tashin hankali


"Habibty..,.


Katseshi tayi ta hanyar kama hannunsa zata danna rezar


Yayi saurin rik'e hannunta da d'ayan hannunsa


Sai dai ina,kafin yayi wani yunk'uri ta yanke sa


A memakon taga jini,wani kalar abu taga yana fitowa kore shataf


Ja baya tayi dasauri, k'irjinta yayi wani mugun bugawa


Hannunta tasa akai,ta k'wala ihu


Yayi saurin matsowa yana fad'in


"Habibty narok'eki ki kwantar da hankalinki"


K'ok'arin bud'e motar tafarayi da sauri amma Gam,tak'i bud'ewa


Tafara jijjigata da k'arfi tana cigaba da yin ihu


Ya k'ara matsowa yana kiran sunanta


Ganin k'ofar bata da alamun bud'ewa yasa ta juyo tana kallonsa tare da had'e hannun ta guri d'aya cikin kuka da tsananin firgici tace


"Narok'eka kada ka cutar Dani,kayi hak'uri idan laifi nemaka"


Hannunta yakama zeyi magana,ta fizge hannun da sauri


"Kada katab'ani kayiwa Allah kabud'emin infita"


Ajiyar zuciya yasauke tare dacewa

"Kiyi hak'uri ki fahimceni,ki natsu dan Allah"


"Nidai kabud'emin infita,karabu dani kayi hak'uri,kar ka cutar Dani wallahi banyi ma komai ba......


Tsawa ya daka mata


"Nace ki natsu ko!!!!!!


Shurun ko tayi dan tsawar ta k'ara razana ta, kyar-kyarwa kawai takeyi kamar anciro ta da ga cikin k'an-k'ara


Aasim ya cigaba da cewa


"Inda zan cutar dake da tuni na cutar dake,kinsan adadin shekarun da nayi ina tare ke ne?


Da zan cutar dake da tuni ban cutar dake ba,ko kinga al'amarin cutarwa a tare Dani?


Yafad'a cikin yanayin damuwa


Sannan ya sassauta murya


"Kiyi hak'uri na d'aga miki murya,amma dan allah ki kwantar da hankalinki,


Tunda Kingane gaskiya ai dole zanyi miki bayani"


Ta jinjina Kai tana kallonsa,ayanzu tsoron yafara raguwa dan ko tafahimci ba cutar da ita d'in zeyi ba


Ya numfasa sannan yace

"Ayanzu babu abunda zan b'oye Miki,


Zanyi miki bayanin komai,kuma inaso ki saurareni da kunnen basira


Ki kuma fahimci bayanin da zanyi miki kinji?


Tad'aga kai alamar taji


Yacigaba da cewa


"Ni ba mutum bane,kuma ni ba aljani bane amma ni rauhani ne,


Kamar yadda kikasani sunana Aasim, Aasim bin ramzad,


Mahaifina shine sarki ramzad dake mulkar masarautar rauhanai


Kuma ni mijinki ne,inada aure dake tun shekaru hud'u da suka wuce,sannan har da y'a  a tsakanina dake"


Zaro ido tayi tana kallonsa


"Aure,harda y'a?kuma Dani?


Tafad'a cikin rawar murya da kuma mamaki


Ya jinjina Kai


"Eh Rauda,shahida da kika gani y'arki ce kece mahaifiyar ta"


Ta kuma zaro ido tana kallonsa


Yacigaba dacewa


"Zanyi miki bayanin ko ni waye,da kuma yadda akai na aure ki har kika haihu batare da kinsani ba"




🙎🏻

Typing dakwai wahala Allah, muhad'u a Page 13



Yarfillo.🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹


             🧞‍♂ 🧞‍♂

                🧞‍♂


                 NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)



Dedicated to Little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu



🅿AGE📕 1⃣2⃣


Wannan Page d'in nakine  mamana,allah ya k'ara miki lafiya yasa kaffarane, ina k'aunarki araina domin kin kasance uwa tagari me share min kuka na a kodayaushe.🥰


NA KASA MANTAWA DAKE😭

Dede da rana d'aya, kodayaushe cikin tuna ki nikeyi, hak'ik'a nayi babban rashi da na rasaki,y'ar uwata hajara aliyu allah Nike rok'o ya jik'anki da rahama,ya gafarta Miki,yasa aljannah ce makomarki Amin😭😭😭



8:57🕐am.     SUN,APR 21✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Bissmillahir rahmanin rahimYa sauke numfashi idanuwansa na kanta,yace


"Akwai wani sabon restaurant da aka bud'e babu kalar abincin gargajiyan da basa saidawa,kuma har dare suna kaiwa,anan na siyo"


Ta jinjina Kai


Ya cigaba da cewa

"Sannan dakike cewe a iya sanin ki babu inda ake saidawa a kusa -kusannan yawo kike yi? Keda sai kiyi sati ma wani zubin baki lek'a ko wajen makaranta ba"


Tayi dariya tana gyad'a Kai


"Hakane,to nagode allah ya k'ara bud'i "


Ya amsa da Amin


Taja iska alamar sanyi na ratsa jikinta sosai tana tana mammatse jikinta da yike rawa kad'an saboda sanyin dake kad'ata


"Wai shin kai baka jin sanyi ne?


Ya bata amsa

"Me kikagani?


Rauda tace

"Gani nayi bakasa rigan sanyi ba,kuma ko rawar sanyi bakayi"


Aasim yayi murmushi

"Kafinnazo nan inajin sanyi sosai,amma ina had'a ido dake,sai naji wani d'umi na ratsani, gabad'aya sai naji sanyin ya tafi"


Tayi dariya tana girgiza Kai

"Kai ko?


Shima dariyar yayi yana kwai-kwayar yadda take magana


"Ni me nayi?


Dariya takuma yi sosai tace


"Allah har fargaban ayi hutu nikeyi,saboda zanyi missing d'inka,da dariyar da kake sani,tunda nahad'u dakai ka kawarda duk wata damuwata kasanya ma zuciyata farin ciki ina godiya sosai"


Murmushi yayi me cike da abubuwa da yawa


"Kin can-canci komai habibty,zan iya yimiki komai,sannan zan iya yin komai akanki"


Itama murmushin takeyi


"Dagaske?zaka iya yin komai akaina?


Ya jinjina kai

"Dagaske habibty,zan iya bada rayuwata akanki"


Wata sassanyar ajiyar zuciya tasauke,tana jin wani farinciki na ratsa illahirin zuciyarta


Ta d'aga kai tana kallon saman bishiyar wacce iska ke kad'a ganyayyakinta,suna kad'awa ahankali


"Bansan meyasa kake sona ba,duk da nasan matsayina be kai ace ka soni ba"


Yad'an matso gab da ita suna kallon juna


Yace

"Nima kaina bansan meyasa ba,abu d'aya ne nasani na kuma yarda dashi,shine allah ne ya jarabceni da k'aunarki,habibty bazan iya rayuwa idan babu keba,kuma kada kiyi tunanin nafad'a mikine dan kawai soyayya


Wallahi dagaske nikeyi,ina k'aunar ki"


Ta kuma sauke ajiyar zuciya da yin shuru na y'an sakwanni sannan tace


"Nima ina sonka Aasim,kuma insha allahu zan rayu tare da Kai,dannasan zan rayu cikin farin ciki idan na kasance tare da Kai"


Aasim yayi murmushi da alamu maganar da ta fad'a tayi masa dad'i sosai


"Nagode habibty,bari nabarki kikoma ciki,tunda sanyin na damunki"


Ta gyad'a kai tace


"Shikenan nagode, Saida safe"


"To sai da safe"


Tafad'a tana juyawa,harta d'an yi nisa tajuyo 


Yana tsaye inda tabarsa yana kallonta


Tace

"Yadai da magana ne indawo?


Ya girgiza kai yace


"Aa,kawai inaso inga shigarki ne tukunna sai inwuce"


Ta gyad'a Kai tana murmushi 


Sannan taci gaba da tafiya


"Rauda!


Ya Kira sunanta,ta waigo tana kallonsa batare da ta amsa ba


"Ina sonki"


Yafad'a,takuma yin murmushi tare da juyawa dasauri,tashige ciki


Koda ta koma d'aki, murmushi be bar fuskarta ba,taci dambun sosai tasha Lipton sannan ta kwanta zuciyarta cike da tunaninsa


Washe gariDa wuri ta shirya zuwa lectures,tana tafiya tana tunanin meyasa be kirata ba yau,dan kullum da asuba sai ya kirata,shike tashin su sallah,


Haka ma idan gari yayi haske sai ya kirata yace ta tashi ta shirya


Ta ciro wayarta ta latsa numbansa taji a kashe


Ta maida wayar jaka taciga ba da tafiya 


Wunin ranar wayar sa bata shiga ba,data kira sai taji a kashe


Tashiga damuwa sosai,dan bata tab'a kiran wayarsa taji a kashe ba


Har ta koma hostel, tana k'ara trying d'in kiran


Amma still a kashe

Ta yada jakar ta a k'asa tana zubewa a kan katifa


Salma dake zaune ta kalleta tana cewa


"Yadai?duk gajiyar ce?


Ta d'aga kai alamar eh tare da cewa

"Da gajiyar da kuma damuwa"


Salma tace

"Damuwa Kuma? Tamece?


Ta sauke numfashi tana tashi tazauna


"Yau tun safe Nike kiran wayar Aasim a kashe,shine duk hankalina ya tashi wallahi,dan bantab'a kiransa naji irin haka ba"



Salma ta jinjina kai

"Gaskiya dole kishiga damuwa,to ko wayar tasa ta fad'i ne?


"Nima nayi tunanin hakan,amma kuma da fad'uwa wayar tayi,da yazo yafad'a min kuma da na gansa acikin makaranta,amma fa banga alamunsa ba,har inda yasaba tsayawa naje bangansa ba, shiyasa nike tunanin ba lafiya ba"


Salma ta jinjina kai

"Gaskiya, to amma kik'ara gwadawa anjima insha'allah zata shiga,k'ila abubuwane suka mai yawa ya kashe"


Rauda tayi shuru kawai dan ita zuciyarta tafi bata ba lafiya ba


Daren ranar batayi wani baccin kirki ba,washegari ma haka takira wayar yafi sau d'ari amma abu d'aya ake gaya mata,akashe


Hankalinta ya tashi sosai,ko abinci takasa ci,bata tab'a sanin tana k'aunar sa ba sai a lokacin


Ahaka aka kwashe kwana uku, lokacin tagama jigata da rashin sa


Hakan yasa bayan tafito daga lectures tayanke shawarar zuwa department d'insu ta tambaya


Suka ci karo da salma ita ma tafito daga nata lectures d'in


"Yadai Rauda ina zakije?


Salma ta tambaya,

"Zan lek'a b'angaren su Aasim ne intambaya nagaji da zama cikin rashin sanin wani Hali yike ciki"


Salma ta jinjina Kai

"To muje inrakaki nima abun nadamuna wallahi"


Suka jera suka tafi,da isarsu suka tadda d'alubai na zaune suyi group-group sunata fira da shewa da alamu sunfito daga lectures ne,wasu kuma suna ta bitar karatu


Wani matashi suka gani a zaune shikad'ai da handout a hannunsa


Suka k'arasa gurin suka mai sallama


Ya amsa fuskarsa a sake suka gaisa,sannan Rauda tace


"Dan allah ina tambayar Aasim ne,kwana biyu bana ganinsa bansani ba ko lafiya?


"Aasim?


Matashin ya tambaya, Rauda ta d'aga kai tana fad'in


"Eh "


Yace

"Gaskiya bangane shi ba saidai ku tambayi wancan shine yike da list sunayen gabad'aya kuma shi ze iya saninshi,amma ni ba lallai insanshi ba saboda muna da yawa"


Yak'arasa fad'a yanayimata nuni da wani


Rauda ta jinjina kai


"Hakane,nagode sai anjima"


Tafad'a sannan suka k'arasa gurin wanda ya nuna musu suka mai sallama


Sannan suka tambayeshi


Shima mai-maita sunan yayi

"Aasim, Aasim,anya anan department d'in kuwa?Ta d'aga kai

"Eh"


Yad'an yi shuru yana nazari sannan yace


"Gaskiya bangane shi ba,abokina ko kasan me suna irin haka haka?


Yak'arasa fad'a yana kallon wanda yike kusa da shi


Shima girgiza kai yayi alamar be sani ba


Wanda suka fara tambayar yace


"To gaskiya bamu san wani me suna haka ba,sai dai inba a department d'inmu yike ba"


Rauda ta girgiza kai tace


"Anan fa yace yike,yananan zaka ganshi wani fari dogo haka"


Ya ajiye numfashi yace

"Nafad'a miki bansanshi ba gaskiya"


Ta gyad'a kai cike da damuwa a cikin zuciyata


"Shikenan nagode,mutafi Salma"


Suka juyo jiki babu k'wari


Salma tace

"To ya akayi haka Rauda?ni al'amarinnan yafara d'aure min kai fa,ace a department d'insu babu wanda yasansa?


Rauda ta sauke numfashi me nawi batare da ta ce komai ba, Dan gabad'aya jikinta yayi sanyi


Wata mota ce tasha gabansu,cikin b'acin rai salma Tafara fad'a


"Wannan wani irin wulak'anci ne zaka wani.......


Kasa k'arsawa tayi yayinda ya sauke Glass d'in motar


Rauda ko kanta na k'asa ko kallon motar batayi ba dan damuwar dake zuciyarta nema takeyi tafi k'arfinta 


"Habibty...


Taji anfad'a, dasauri tad'ago kanta,suka had'a ido


Ya sakar mata lallausan murmushi 

"Habibty,bazaki amsa kiran nawa bane,duk fushi dani d'inne ya jawo haka?


A memakon tabashi amsa,sai kawai idanunta suka cicciko da k'walla 


Nan da nan hawaye yafara wanke mata fuska


Dasauri ya bud'e marfin motar,yafito yana fad'in


"Subhanallah,kuka habibty,me yake faruwa?


Ya tambaya hankalinsa a tashe


Ji tayi k'afafunta suna neman kasa d'aukarta,hakan yasa ta durk'usa tana cigaba da yin kukan


"Habibty please kiyi hak'uri,tashi kishiga  mota, banaso hankalin mutane ya dawo kanki"


Kasa mik'ewa tayi saida Salma ta kamata tukunna,sannan tashiga motar


Salma tawuce tabarsu,itako Rauda kifa kanta tayi agaban motar tana cigaba da yin kukan da ta rasa ko na menene


Ya sauke numfashi yana cewa


"Dan girman Allah habibty,ki wa girman allah kiyi shuru,wallahi kukanki sosamin zuciya yike yi"


D'agowa tayi tana kallonsa da jik'akk'un idanunta



"Inyi shuru fa kace?kasa nashiga tashin hankali da tsananin damuwa,ina fargaban ko ba lafiya kake ba,inata fargaban ko wani abune ya sameka,ashe lafiyar ka k'alau.....


"Please kiyi hak'uri nasan nayi kuskure, Amma ba wai da niyya nai hakan ba,tafiya ce takamani kuma cikin gaggawa......


"Okay idan tafiya takamaka baka iya sanar min kafin katafi?


Ta katseshi,ya girgiza kai yace


"Naso insanar dake kafin intafi amma saboda yadda tafiyar tazo min bansamu daman kiranki ba"


"To dakaje fa,meyasa baka kirani ba?


Ta kuma tambaya still idanuwanta na kansa


Ya bata amsa da yanayin damuwa a fuskarsa


"Habibty inda naje waya bata shiga shiyasa"


Jingina tayi da kujerar motar batare da ta k'ara cewa komai baYa matso kusa da ita yana cigaba da cewa


"Abunda natsana a duniya shine inga hawaye a fuskarki, narok'eki habibty, ki tsayar da hawayennan haka"



Banza tayi dashi,ya gyad'a kai yana cewa

"To shikenan cikin biyu yanzu dole za ayi d'aya

Ko ki tsayar da hawayennan,ko kuma ki juyo da fuskar yana zubowa ina lashewa"


Harara ta galla Masa,yayi dariya yana kama kunnuwansa 


"Please habibty I'm sorry"


Yadda ya lank'wasa muryar tasa taso tasata dariya


Ta share hawayen tana fuskantarsa,


"Dan Allah karka k'ara yimin irin haka,bakasan halin da na shigaba wallahi nikad'ai nasan tashin hankalin dana shiga"


Tafad'a cikin marai-raice fuska


Ya jinjina kai

"Shikenan, insha'allah bazan sake ba,kin hak'ura yanzu?


Ta d'aga kai alamar eh


Yayi murmushi

"Yauwa tawan Allah yabar minke,yanzu fad'amin ina kikeso muje,gurin shan ice cream,gurin cin tantabara ko gurin saida dambu?


Dariya tayi had'i da fad'in


"Sai dai gurin saida fate"


Shima dariyar yayi yana tada motar


Ita ko Rauda zuba mai fararen idanuwanta tayi tana sauke ajiyar zuciya



"Zahiri tana sonsa acikin zuciyarta, Wanda bata tab'a tunanin zata k'ara sa wani d'a namiji a cikin zuciyarta ba


Dan gabad'aya a rayuwarta ta tsani soyayya,takuma yi alk'awarin bazata sake yinta ba


Sai gashi Aasim ya canza mata tunani yasa ta k'ara komawa soyayya


Ajiyar zuciya ta sauke me nawi


Aasim ya juyo yad'an kalleta sannan yamaida kallonsa ga titi yace


"Yadai habibty,wannan ajiyar zuciya haka?


Ta kuma sauke wata a karo nabiyu sannan tace


"Aasim kasa na karya alk'awarin dana d'aukar ma kaina,na bazan sake yin soyayya ba,gashi yanzu zuciyata tagama amincewa dakai


Inada wata kalar zuciya da bata iya yin soyayya ba,idan harna fara son mutum to gabad'aya hankalina gushewa yikeyi


Dan allah kada kayi amfani da son danike maka,ka wahalar min da zuciyata,nasha wuya a baya banaso nasake mai-maita wa"


Ta k'arasa maganar idanuwanta na ciccikowa da hawaye


Da alamu jikinsa yayi sanyi da jin magan-ganunta


"Insha'allah habibty,bazan zama mesaki damuwa ba,abu d'aya nike so agareki...


Yad'an dakata, Rauda ko kallonsa takeyi


Yavcigaba da cewa


"Inaso kiyimin alk'awarin ko da nan gaba kin gano wani abu da baki san da shi ba a tare Dani,to kiyi min alk'awari bazaki rabu dani ba,ba kuma zaki dena sona ba, sannan kuma zaki gafarceni abisa b'oye mikin da nayi"


Kallonsa takeyi cikin rashin fahimta dan gabad'aya bata fahimci inda maganarsa ta dosa ba


"Bangane ba,dama kana b'oye min wani abu ne?to meyasa?kuma menene shi?


Yayi murmushin da ya tsaya masa iya labb'a kawai


"Lokaci na zuwa,da nasan dole zaki gane gaskiya,aduk lokacin dana tuna hakan sai inji hankalina ya tashi dan bansan wani hukunci zaki d'auka a lokacin ba"


Ta sauke guntun numfashi tace.

"To wai miye kake b'oyemin ne?


Sai kuma ta dakata alamar ta tuna wani abu, tacigaba da cewa


"Owo nafahimta,kana da aure ne ko?kana da mata shine ka b'oye kak'i fad'amin ko?


Ya murmushi yana girgiza kai


"Aa,wallahi bayan ke bani da wata Mata"


Tabud'e idanunta tana masa wani kallo


"Eyen,ni d'in ko?to yaushe na zama matarka?


Yad'an yi jim kaman ya naso ya tuna


"Eh to,kaman shekaru hud'u da suka wuce"


"Kai lokacin ma ko sanina kayi,duka-duka ko rabin shekara ma munyi da had'uwa ne?


Tafad'a tana k'walalomai ido


Yayi dariya yace


"Agurinki kenan amma ni agurina had'uwarmu tun bayan shekara ashirin ne?


Ta kuma bud'e idanuwanta sosai


"Kai, lokacin ma ko haihuwata anyi?ohhh na tuna anhaifeni lokacin kenan tun ina jaririya ko?


Ta tambayesa cikin yi galala da baki


Dariya yayi Yana paka motar a harabar gurin saida Ice cream


"Kinga habibty muje musiyo muyi mu koma,yanzu aka kirani akafad'a min muna da meeting"


Tace to,harzata bud'e motar kuma sai takoma tazauna


"Kace yanzu aka kiraka?da wace wayar to ince ga wayarnan a ajiye,kuma ni tunda nashigo motarnan banji ankirata ba?


Yayi k'ok'orin tsaida natsuwarsa guri d'aya yace


"D'azu nike son ince"


Gyad'a kai tayi tana tab'e baki


"Ook muje"


Basu wani b'ata lokaci ba,suna shiga tazab'i kalar ice cream d'in datake so suka fito


Bayan yatada motar sunfara tafiya tace


"Namanta ban tambayi shahida ba,tana lafiya? Ya ammi da nazma?


"Duk sunanan k'alau"

Yabata amsa a tak'aice


Gudu yayi sosai saboda meeting d'in da yace suna dashi


Yana ajiyeta ya juyaDa daddare bayan tayi shirin kwanciya,ta kira wayarsa,tagama ringing be d'auka ba


Tana ajiye wayar message na shigowa ta bud'e


"Habibty bamu gama meeting d'inba haryanzu,ki kwanta kiyi bacci ina sonki"


Murmushi tayi tare da rungume wayar a k'irjinta baccin da batayi kwana biyu ba kuwa yad'auketa


Bayan sati d'aya, hankalinta ya kwanta,dan suna tare soyayyar su nadad'a yin k'arfi


Ranar wata laraba,tashirya dan zuwa gurin saloon,dama sunyi dashi intaje shi zeje yad'aukota


Saboda yace yana da meeting a lokacin


Hakan yasa tafito bakin titi ta tari adai-daita sahu


Sun d'an yi nisa kad'an wata kyakkyawar budurwa ta tsaida a dai-daitan da Rauda ke ciki



Da sallama tashiga, Rauda ta amsa suka gaisa


Napep d'in tacigaba da tafiya


Budurwar da tashi ga napep d'in tace


"Rauda ko?


Da mamaki Rauda ta kalleta jin takira sunanta


"Eh itace"


Budurwar tayi murmushi

"Ni kuma saima"


Rauda tak'ara kallonta, bata tab'a ganinta ba,to a ina tasan ta?har tasan sunanta?


Saima ta katse mata tunanin da takeyi


"Kinyi mamakin kiran sunanki da nayi ko?


Rauda ta d'aga Kai

"Eh gaskiya danni bansanki ba,to ko makarantar mu kike?


Saima ta girgiza kai alamar aa


"Ba a makarantar ku nike ba malama Rauda"


Rauda ta jinjina Kai

"To ya akayi kikasan sunana?


Saima ta kuma yin murmushi,sunan ki ai sananne awurina,ke bama nikad'ai ba gabad'aya ahalina,babu wanda be sanki ba"


Mamaki yakuma kama Rauda


"Ahalinki? bangane ba"


Saima ta d'aga kai tace


"Eh,amma bawannan surutun ya kawoni ba,meyasa zuciyarki take saurin amincewa da mutane?


Baki san akwai wasu jinsi dazasu iya biyowa ta suffar mutane su cutar dake ba?


Cikin raahin fahimta Rauda ke kallonta amma takasa K'ara cewa komai


Dan ji tayi tsigar jikinta tafara tashi


Saima takuma yin murmushi,tana cigaba da cewa


"Ya kamata dai kirink'a ban-bance jinsin mutum da kuma na aljani,domin yana tare dake akodayaushe


Nabarki lafiya"


Tana gama fad'ar haka ta dire ko cewa me napep d'in ya tsaya batayi ba


Rauda tsoro ne yakamata, jikinta yayi sanyi sosai


Dede lokacin me napep d'in yatsaya a k'ofar shagon saloon d'in


Taciro kud'insa tabasa, dasauri tashiga shagon tazauna tana maida numfashi


Me saloon d'in me suna Amira tace


"Yadai customer?lafiya naganki wani iri?


Rauda ta girgiza Kai


"Aa bakomai"


Amma cikin zuciyarta mamaki da kuma al'ajabin saima ne,me take nufi da yakamata ta rink'a ban-bance jinsin mutum da na aljani?


Domin yana tare da ita a kodayaushe?


Maganar Amira ce ta katse mata tunanin data tafi


"Me za'amiki, retouching ko steaming?


"Steaming"


Tabata amsa a tak'aice


Har aka kammala mata bata dawo cikin natsuwarta ba,juyayin abunda yafaru kawai takeyi


Tana zaune ana taje mata kai, Aasim yayi sallama dayike yasan wurin ya tab'a kawota


Amira ce ta amsa tana bashi izinin shiga


Yashiga shagon da murmushi a fuskarsa yana kallon gashin kanta da yayi bak'i sid'ik yana ta shek'i


"Wow habibty kinga yadda gashin yayi kyau kuwa?


Amira tayi dariya tana fad'in


"Sai ka biyani da yawa"


Ya rausayar da Kai yace

"Baki da matsala, tunda kina gyara min matata"


Murmushi Rauda jeyi


"Ai nayi zaton bazaka zo ba"


Ya girgiza Kai yace


"Haba nina Isa?muna gama meeting d'in nan nayo direct"


Ta jinjina Kai tana janyo d'an kwalinta zata d'aura gaban makeken madubin da ke manne a bango


Gabanta ne yafad'i Ras, yayinda ta ga Aasim sanye da  wasu kaya irin na sarakai ta cikin madubin kuma yayi wani bau farinsa da kyansa ya ninka wanda tasani


Tayi gaggawar kallonsa a fili


Yana tsaye yana bawa amira kud'i sanye da k'anan Kaya


Ta murza idanuwanta dasauri tana ganin kaman gizo idanun ke mata


Takuma kallon madubin, still da kayan sarautar ta k'ara ganinsa


Maganar saima ce tadawo Mata, gabanta yayi wani mugun fad'uwa


Tayi saurin kauda kanta a madubin ganin madubin yafara yimata dishi-dishi


Kallonta yayi yace


"Yadai naganki a daburce meyafaru?


Ta girgiza kai dasauri batare da tace komai ba


Amira tace

"Nima dai yau tunda tashigo haka naganta"


Yakuma kallonta sosai 

"Habibty,lafiya?meke faruwa"


Kuma girgiza kai tayi alamar babu komai


Ya jinjina kai amma be yadda babu komai d'in ba


"Shikenan muje"


Yayi gaba yana yiwa amira sallama


Bin bayansa tayi da kallo gabanta na fad'uwa


Yad'an waigo yana dubanta ganin tana tsaye bata da niyyar tafiya


"Yadai,ko baki gama bane"


Ta girgiza kai tana d'aga k'afarta datayi mata nawi a tafito


Yabud'e mata motar tashiga,sannan ya shiga ya tada


Yana cewa

"Kifad'a min meke faruwa,ni nasan akwai wani abu hakanan dai bazan ganki a daburce ba"



Tayi k'arfin halin danne tarin fargaban da yike zuciyarta


"Aasim,intambaye ka zaka fad'amin gaskiya"


Ya kalleta


"Eh zanfad'a miki indai nasani"


Ta jinjina Kai tace


"Aasim kai mutum ne?


Ta jeho mai tambayar da be shirya jinta ba


"Eyeh,mene?mekika ce?


Yafad'a cikin sark'ewar murya


"Nace kai mutum ne?


Yayi shuru na y'an sakwanni sannan yace


"Me yasa kika yimin wannan tambayar?


Ta gyad'a kai fad'uwar gabanta na dad'a tsananta


"Akwai abunda nagani da nakasa fahimta, please k'afad'a min gaskiya kai mutum ne?


Ya sauke numfashi tare da cewa


"Eh ni mutum ne"


Girgiza kai tayi cikin rashin yadda


"Banyadda ba,idan kai mutum ne ya akayi siffarka,da kayan jikinka suka sauya acikin madubi?


Ya taka burki da sauri yana kallonta


"Suffata Kuma,ayaushe?saidai in gizo idanun ki suka Miki"


Ta gyad'a kai tana zage jakar ta ta ciro reza ta bud'e tare da    sawa akan yatsanta ta danna


Sai ga jini b'ul-b'ul,


"Miye haka habibty,yanka kanki kikayi fa?


Yafad'a dasauri,ta jinjina

" kai nasani ai,kai ma inaso ka yanki yatsanka,saboda in tabbatar da abunda nike zargi"


Girgiza kai yayi


"Habibty baki yadda dani bane?


"Ko na yarda dakai inaso inga jini a jikinka,idan har kasan abunda kafad'a min gaskiya ne to ka amsa kayi abunda nace"


Tafad'a cikin wani irin yanayi na tashin hankali


"Habibty..,.


Katseshi tayi ta hanyar kama hannunsa zata danna rezar


Yayi saurin rik'e hannunta da d'ayan hannunsa


Sai dai ina,kafin yayi wani yunk'uri ta yanke sa


A memakon taga jini,wani kalar abu taga yana fitowa kore shataf


Ja baya tayi dasauri, k'irjinta yayi wani mugun bugawa


Hannunta tasa akai,ta k'wala ihu


Yayi saurin matsowa yana fad'in


"Habibty narok'eki ki kwantar da hankalinki"


K'ok'arin bud'e motar tafarayi da sauri amma Gam,tak'i bud'ewa


Tafara jijjigata da k'arfi tana cigaba da yin ihu


Ya k'ara matsowa yana kiran sunanta


Ganin k'ofar bata da alamun bud'ewa yasa ta juyo tana kallonsa tare da had'e hannun ta guri d'aya cikin kuka da tsananin firgici tace


"Narok'eka kada ka cutar Dani,kayi hak'uri idan laifi nemaka"


Hannunta yakama zeyi magana,ta fizge hannun da sauri


"Kada katab'ani kayiwa Allah kabud'emin infita"


Ajiyar zuciya yasauke tare dacewa

"Kiyi hak'uri ki fahimceni,ki natsu dan Allah"


"Nidai kabud'emin infita,karabu dani kayi hak'uri,kar ka cutar Dani wallahi banyi ma komai ba......


Tsawa ya daka mata


"Nace ki natsu ko!!!!!!


Shurun ko tayi dan tsawar ta k'ara razana ta, kyar-kyarwa kawai takeyi kamar anciro ta da ga cikin k'an-k'ara


Aasim ya cigaba da cewa


"Inda zan cutar dake da tuni na cutar dake,kinsan adadin shekarun da nayi ina tare ke ne?


Da zan cutar dake da tuni ban cutar dake ba,ko kinga al'amarin cutarwa a tare Dani?


Yafad'a cikin yanayin damuwa


Sannan ya sassauta murya


"Kiyi hak'uri na d'aga miki murya,amma dan allah ki kwantar da hankalinki,


Tunda Kingane gaskiya ai dole zanyi miki bayani"


Ta jinjina Kai tana kallonsa,ayanzu tsoron yafara raguwa dan ko tafahimci ba cutar da ita d'in zeyi ba


Ya numfasa sannan yace

"Ayanzu babu abunda zan b'oye Miki,


Zanyi miki bayanin komai,kuma inaso ki saurareni da kunnen basira


Ki kuma fahimci bayanin da zanyi miki kinji?


Tad'aga kai alamar taji


Yacigaba da cewa


"Ni ba mutum bane,kuma ni ba aljani bane amma ni rauhani ne,


Kamar yadda kikasani sunana Aasim, Aasim bin ramzad,


Mahaifina shine sarki ramzad dake mulkar masarautar rauhanai


Kuma ni mijinki ne,inada aure dake tun shekaru hud'u da suka wuce,sannan har da y'a  a tsakanina dake"


Zaro ido tayi tana kallonsa


"Aure,harda y'a?kuma Dani?


Tafad'a cikin rawar murya da kuma mamaki


Ya jinjina Kai


"Eh Rauda,shahida da kika gani y'arki ce kece mahaifiyar ta"


Ta kuma zaro ido tana kallonsa


Yacigaba dacewa


"Zanyi miki bayanin ko ni waye,da kuma yadda akai na aure ki har kika haihu batare da kinsani ba"




🙎🏻

Typing dakwai wahala Allah, muhad'u a Page 13



Yarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* 




🌹 JINNUL

         AASHIQUE🌹


               🧞‍♂ 🧞‍♂

                  🧞‍♂


                NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)🧕🏻


Dedicated to Little hajjo and my elder sister Hafsat aliyu



🅿AGE📕 1⃣3⃣


Wannan Page d'innaki ne besty hajiyayye, Allah ya kaimu December musha biki,mu rak'ashe mu kwaso shoki😁😁



Fatan alkhairi ga golden pen writters gabad'aya,ina jinjina muku da kuma fatan Allah yak'ara mana basira.



3:28🕒pm.

WED,APR 24✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Bissmillahir rahmanin rahim👏🏻


Ya gyara zamansa sosai yana sauke nannauyar ajiyar zuciya


"Duk da banso ace zansanar  dake a wannan lokacin ba,amma ya zamar min dole,


Amma ina rok'onki da kisa ma zuciyarki natsuwa, kicire duk wani tsoro dake cikinta


Nasan tsoro wajibine amma kisani bazan tab'a cutar dake ba


Rauda ina k'aunar ki  kuma inaso kituna da alk'awarin dakika min rannan,akan ko kingane wani abu da baki sani ba atare Dani,


Zaki cigaba da Sona,bakuma zaki rabu dani ba


wallahi ina yimiki so me tsanani bazan iya rayuwa idan babu ke ba,dan allah ki fahimceni ki kuma amshi uzurina"


Yafad'a cikin wani irin yanayi wanda yak'ara sa jikinta yayi sanyi


Ganin abun takeyi kamar a mafarki,ga jikinta yayi wani mugun mutuwa


Daky'ar take iya motsa jikinta, hak'ik'a zuciyarta na cike da tarin tsoro amma maganganun sa sun d'an rage tsoron


Kallonsa kawai takeyi takasa gasgata al'amarin,wai Aasim ba mutum bane,kenan shine JINNUL AASHIQUE d'in da malamai ke fad'a Mata,yana hana ta aure.


"Rauda!


Aasim ya kira sunanta,ta kallesa kawai amma takasa amsawa


"Kinyi alk'awari zaki fahimceni?


Tad'aga kai alamar eh


Yasauke ajiyar zuciya yana cewa


"Nagode"


Yad'an yi shuru sannan ya cigaba da cewa


"Sunana Aasim,d'a agurin sarki Ramzad, mahaifina shike mulkar masarautar rauhanai. 


Yana da mata biyu,da yara biyu


Ni ne nafarko kuma nikad'ai ne agurin mahaifiyata,sai k'anina yarima samran wanda yakasance d'a agurin kishiyar mahaifiyata.


Mahaifina na sona sosai dan yana fifitani a kan yarima sarman agaban kowa, Wanda hakan ke bak'anta ran sarauniya jalila(kishiyar mahaifiyarsa)


Masarautar mu babban masarauta ce dake can wata duniya,muna rayuwa kamar yadda ku mutane kukeyi 


Kuma muna saukowa zuwa wannan duniyar duk k'arshen sati sau d'aya domin muga abunda yike tafiya


Mukuma shak'ata,mahifina yana da zafi sosai dan idan yayi magana d'aya to baya canza ta


Amma kuma duk yadda yakai ga zafi,idan narok'e sa akan abu yana yi yakuma hak'ura


Hakan yasa ko samran da mahaifiyar sa idan suna so suyi wani abun sai sunbiyo ta hanyata.


Muntaso cikin rayuwar jindad'i bamu tab'a neman wani abu mun rasa baMuna da k'arfin iko da kuma k'arfin mulki,tayadda ake tsoron mu a ko'ina,duk wani aljani fargaban ya had'u damu yikeyi 


Akwai wata rana munsauko wannan duniyar,nida fada wa na,muna tafiya cikin nishad'i da kwanciyar hankali


Kwatsam sai muka fara jin k'amshin salbaan, salbaan wani abune da ake haihuwar rauhanai dashi kuma kowani rauhani da kalar nasa salvaan d'in


Amma abun mamaki sai naji k'amshin shi a duniyar mutane,na lula cikin tunanin ya akayi haka?meke faruwa?


Maganar d'aya daga cikin fadawa nane ya katsemin tunanin dana tafi inda yace


"Ranka shidad'e kajiyo k'amshin salvaan da muke ji kuwa?


Na d'aga kai alamar eh ina cewa


"Naji,amma ya akayi  haka?tunda muke zuwa wannan duniyar bantab'a jin irin haka ba sai yau"


Ba faden me suna iliyas,wanda shine babba kuma shugaba agaba d'aya fada wana yace


"Ranka shidad'e idan kabani dama zanje naduba inda k'amshin ke futowa"



Nad'aga mai kai kawai,alamar nabashi


Cikin mintoci k'alilan sai gashi yadawo,yace


"Ranka shidad'e haihuwa ce akayi,kuma k'amshin daga jikin jaririyar yike fitowa,ina ganin kaman a jikinta salbaan d'in yake"


"Jaririya?kuma bil'adama ce?


Natambayesa da mamaki


Ya jinjina kai

"Eh ranka shidad'e"


Gyad'a kaina nayi ina cewa


"Muje inda jaririyar take"


Ko da naje naganki,natabbatar dake mutum ce kuma dakwai salbaan a jikinki,nayi mamaki sosai dan bantab'a ganin irin haka ba


Nayi miki addu'o i nakuma sa wata rauhaniya da tadinga kula dake da kuma al'amuranki"


Daganan naciga ba da harkokina batare da wani tunani akanki ba


Daganan kuma nayi tafiya nisa wacce bandawo ba sai da nayi shekaru goma Sha biyar


Bayan dawowa na,nazo wannan duniyar domin naga abubuwan da suka canza bayan tafiya ta


Munzo wucewa ta wuraren gidanku sai k'amshin salbaa nanki  ya bugi hancina


Alokacin ne na tuna dake,dan gabad'aya na manta,natura ma rauniyar danasa ta rink'a kula dake sak'on ina son ganinta


Sai gata ta bayyana,ananne take bani labari akanki,da yadda kikai rayuwa tsawon shekaru goma sha biyar.


Sannan tak'ara da cewa,ayanzu baki da lafiya


Hakan yasa nace mata ina son inganki


Tayi min inso harzuwa d'akin dakike kwance


Koda naganki sai naji gabana na fad'uwa


Nayimata umarnin data fita,sannan nazauna gefen gadon ina k'are miki kallo


Hak'ik'a kin kasance kyakkyawa,na kama hannunki nayi miki addu'a


Sannan natafi,sai dai ko da natafi, zuciyata bata dena tunanin ki ba


Wanda narasa dalilin hakan,wani dare ina kwance d'akina naji babu abunda nike so illa naganki


Hakan yasa naciro wani madubi narik'e a hannuna tare da ambaton sunanki


Bayyanar da kikayi acikin madubin itace mafarin komai,domin babu kaya ajikinki da alamu wanka kikeyi


Nayi saurin kauda madubin domin a k'a'idar mu bama kallon mutane a wannan yanayin


Sai dai zuciya ta ta d'arsu da k'aunarki, 


Nakuma sa tsoro me tsanani akanki,tayadda ko aljanun bayi bazasu iya kallonki a wancan yanayin ba


Alokacin dakika cika shekaru sha shida, alokacin nagama afkawa cikin kogin k'aunarki


Ban b'oye wa ammi komai ba,nasanar da ita dakuma auranki da nikeso inyi


Ammi tayi k'ok'orin fahimtar dani akan yaza'ayi ina jinsin rauhan in auri bil'adama?


Na nuna mata cewa nidai ina k'aunar ki kuma inason in aureki idan har tanason farincikina to ta amince min


Tace min to yazanyi da gimbiya saima y'ar k'anin mahaifina wacce tun muna yara take Sona?


Na sanar da ita cewa,ban tab'a son saima ba,ni ke nikeso kuma dake kad'ai zan iya zaman aure


Tunda taga na nace,ta tabbatar da ina yimiki so me tsanani,amma mahaifina fa?tasan inya sani bazetab'a yarda ba


Hakan yasa tace in aureki a sirrance,ta yadda masarauta bazasu sani ba


Na ko yi hakan,dan inbaki manta ba akwai wata rana dakikayi mafarkin wasu fararen mutane sunzo d'aura auranki


To alokacinne aka d'aura aure na dake,na kuma dunga rayuwar aure dake batare da kinsani ba


Wanda zuciya ta ta K'ara zafafa a k'aunar ki,tayadda bana iyayin kwana biyu banzo naganki ba.


Amma babu wanda yasani a masarautar illa fadawana


Alokacin manema suka fara b'ullo Miki,naso nad'auki mataki domin ina tsananin kishinki sai ammi ta hanani tanuna min ba dai-dai bane


Nadaure muka cigaba da rayuwa ahakan,


Alokacin da kikai sha bakwai,alokacinne me martaba yagano auren dake tsakanina dake


Wanda yashiga b'acin ran da duk wani wanda yike cikin masarautar sai da hankalinsa ya tashi


Ya umarci da a hukuntani ni da ke


Nadurk'usa ina kuka ina rok'onsa


Dana ga yak'i,sai na sanar dashi abunda yasa jikinsa yayi sanyi


"Abi,nasan nayi kuskure Amma kagafarceni,idan zakayi hukunci ka hukuntani nikad'ai domin,ita bata san ma ina tare da ita ba,sannan ayanzu tana d'auke da cikina"


Be k'ara cemin komai ba,yasa aka hukuntani abisa laifin b'oye masa danayi


Amma kuma be zartar da hukunci atsakanina dake ba wanda bansan abunda yasa sa yin hakan ba.


Haka lokaci ya cigaba da tafiya,har zuwa lokacin da kika haifi shahida


Duk da me martaba baya son auren,kuma be amince da shi ba,yayi matuk'ar farin ciki domin wannan karonne karo nafarko da aka sami jika a masarautar


Nayi farin ciki sosai haka ma ammi,ke gabad'aya masarautar sunyi farin ciki da haihuwar shahida


Hakan yasa taga gata,da riritawa,kuma tana tare da me martaba a kodayaushe domin yana sonta sosai


Maganar hana auranki kuma,ina kishinki bazan tab'a barin wani d'a namiji ya rab'e ki ba,duk ko ranar da hakan ta kasance to sai dai ranar da numfashina ze tsaya


Rauda  wannan shine ainihin gaskiyar dake tsakanina dake,


Dan allah ki amince mucigaba da rayuwa ahakan,babu abunda bazan iyayimiki ba indai zesaki farinci kuma inaso yazama sirri atsakaninmu..........



Ahankali tabud'e idanuwanta da sukayi mata nawi,dan tunda yayi nisa a labarinsa taji kanta kaman and'aura mata dutse


Sai dai a memakon ta ganta acikin motarsa kuma kusa dashi


Sai taganta kwance kan gadonta,ga salma gefenta tana ta sharar bacci


Mamakine ya kamata,ita da take cikin motarsa ya akayi taganta a d'akinsu?


Ta tashi dak'yar ta jingina da jikin gadon,to kodai mafarki tayi?


Ta tambayi kanta tana k'ara yin mamaki,agogo ta kalla k'arfe Sha d'aya nadare


Tabbas mafarki tayi dan alokacin dasuna magana dashi ko magriba ba tayi ba yanzu kuma shad'aya na dare


Ajiyar zuciya tasauke me nawi tana godiya ga allah da ya sa mafarkine ba zahiri ba


Ta janyo wayarta dake gefe ta danna numbansa bugu d'aya yad'auka yana ambaton sunanta


"Habibty.....


Bata amsa ba illa "allah nagode maka"


Datace,daga can b'angaren yace


"Meya faru ake godiya ga allah"


Takuma sauke ajiyar zuciya tare da cewa


"Wani mugun mafarki nayi Wai...........


"Wai ni ba mutum bane ko?kuma inada aure dake harda y'a ko?


Ya katseta


Sororo tayi da wayar a kunnenta, yacigaba dacewa


"Ba mafarki kikayi ba habibty zahirine,ganin halin dakika shigane yasa na maidaki d'aki"


Muryarta na rawa ta kira sunansa


"Aasim! Dan Allah kacemin mafarki nikeyi,taya zaka kasance ba jinsin mutum ba,wallahi ina sonka,idan wasa kakeyi kadena..........



"Hmmmmmmmm habibty,dan Allah kikwantar da hankalinki,ayanzu babu wani abun da ya rage baki sani ba.......


Yafad'a,cikin tashin hankali ta katseshi


"Kak'yaleni haka,kada ka haukatani.....


Ze kuma magana ta maka wayar a k'asa tana fad'in


"Kak'yaleni nace!!!!


Sai kuma ta fashe da Kuka,tana sa hannunta akai


"Wayyoh allah na na shiga uku!!!!!


Kukan da takeyi ne ya tada Salma,


Tafarka a gigice tana tambayar waye ya mutu?


K'an-k'ameta Rauda tayi tana cigaba da yin kukan


Hankalin salma ya tashi


"Me yafaru Rauda?fad'amin me yafaru?

Waye ya mutu?


"Salma,inaso inje gida,inason inga mamana,bazan iya cigaba da zama a makarantar nan ba"


Rauda tafad'a cikin kuka


Salma tace


"Wani abune yasamu maman?


Rauda ta girgiza Kai

"Nidai inason inganta,muje kisani a motar kaduna dan Allah"


Salma tace

"Kinsan k'arfe nawane yanzu da zaki doshi kaduna??


Sannan keda zaki fara jarabawa jibi mezasa kitafi?



Kuma fashewa tayi da wani sabon kukan


"Wayyoh allah na, Salma k'wa-k'walwata zata juye,nashiga uku"


Salma hankalinta yak'ara tashi dan bata tab'a ganinta cikin wannan yanayin ba


"Nace kifad'a min meyafaru,meya sameki? 


D'agowa Rauda tayi tana kalle-kalle a tsorace


"Ba mutum bane,ze iya zuwa Nan,kar ya cutar Dani,salma ki taimakeni,wallahi tsoro nikeji"


Tak'arasa fad'a tana k'ara shigewa jikin Salman


Maganganun da tafad'a yasa salma tunanin kotayi gamo da aljanune?


Hakan yasa tafara tottofa mata addu'o i,tanayi mata fifita


Aiko bata dad'e ba bacci me nawi yad'auketa


Salma tayi jugum tana kallon ta,da kuma tunanin abunda yasameta.


Washegari,bata farka ba sai wajen k'arfe tara na safe


Salma tadad'e da gama abun Kari,tana zaune gefenta tana jiran farka warta


Ganin tabud'e ido yasa tace


"Sannu Rauda kintashi?


Tad'aga mata Kai tana tashi ta zauna


"Yajikinnaki?


Salma ta kuma tambayar ta,


"Dasauk'i"


Rauda tabata amsa,salma tamik'e tana cewa


"Bari nakai miki ruwan wanka,inkinyi sai ki karya"


Bata ce mata komai ba tabi bayanta da kallo,sannan ta mai da idanuwanta kan wayar ta da salma ta had'a mata wacce ta ragar-gaje sakamakon bugata datayi a k'asa jiya


Bayan tayi wankan Salma tahad'a mata tea sannan tace


"Ki kwanta ki huta,zanje cikin makaranta indawo"


Gyad'a mata kai kawai Rauda tayi,tana bin bayanta da kallo harta fice


Sannan tasauke numfashi,tana tunanin abunda yafaru jiya


Takasa gasgata al'amarin,ta lumshe idanuwanta zuciyarta cike da tarin damuwa


"Habibty"


Taji muryarsa a cikin kunnuwanta


Tabud'e idanuwanta da sauri,agefenta ta gansa zaune


Ta danne tarin tsoron da ya taso mata tana kallonsa 


Zeyi magana ta katse shi


"Dakata banason jin komai daga bakinka,mekayi kenan?kana ganin kayi dai-dai?kasan bak'in cikin da zuciya ta shiga alokacin da aka fasa aurena har sau biyu?


Naji alokacin kamar bak'in ciki ze kasheni,haka b'angaren samarina da mutum yafara zuwa sai ya dena ashe kaine kake hanasu, kenan ahaka kakeso ink'ara ci rayuwa ta batare da nayi aure ba ko?


Ya girgiza kai


"Ina tare dake,duk abunda d'an adam zeyi miki zan iya yimiki ninkin baninkin shi,amma tabbas maganar aure ki cireta a zuciyarki"


Ta gyad'a kai tana nuna masa hanyar fita


"Ka k'yaleni dan Allah,katashi katafi"


Yayi guntun murmushi

"Zan k'yaleki ayanzu har zuwa lokacin da zaki huce,amma ina tare dake har zuwa k'arshen rayuwata"


Yana gama fad'ar haka ya b'ace


Dafa kanta tayi dayike Sara mata tana ambaton sunan allah


Bayan sati biyu,bata k'ara ganinsa ba,bata kuma k'ara jin d'uriyarsa ba 


Har suka kammala jaraba wa, suka fara Shirin tafiya gida


Tana cikin had'a kayanta taga wata farar takadda


Wani rubutu tagani me kyau kamar anyi shi da ruwan zinari


Tafara karantawa


"Amincin Allah yatabbata agareki,yake abar alfaharina,nasan nayi kuskure Amma kisani k'aunar ki ce tasani yin hakan kigafarceni dan Allah"


Tasan takaddar Aasim ce,ta ninketa tana sauke ajiyar zuciya sannan tacigaba da had'a kayan


Tare suka fito da Salma,dan yayan salman dake gombe yazo zed'auketa


Kowacce janye da akwatinta,


Suka gaisa da shi, sannan sukayi sallama,ita kuma Rauda tafito bakin titi tana jiran adai-deta sahu wacce zata Kai ta Tasha


Wata rantsattsiyar mota ce ta faka agabanta,tad'ago ta kalli wanda ke cikin motar


Aasim ne,yasha wasu maroon d'in jeans da T-shirt


Ya Salam, tafad'a afili dan yayi kyau nafitar hankali, azuciyarta tace dama ashe wannan kyan da walaki,dan yayi yawa


"Habibty Bismillah"


Girgiza kai tayi dasauri azuciyarta tana fad'in ba zan shiga ba


Sai dai kafin ta k'yafta ido,tuni taganta zaune acikin motar


Kallonsa tayi ad'an tsorace


Yayi dariya yana fad'in


"Wai ni naga ikon Allah,mata tana gudun mijinta"


Ta murd'a k'ofar zata fita,taji Gam


Ya kuma yin dariya

"Dama kin zauna dan ba bud'uwa zatayi ba"


Ajiyar zuciya tasauke tana jingina da kujerar motar,ko minti biyu cikakku ba ayi ba taga motar ta tsaya acikin wani gida me shegen kyau


Kallonsa tayi da mamaki sosai a fuskarta


"Inane nan kuma kakawoni?


"Gidanki Mana"


Yabata amsa a tak'aice


"Nida zantafi gida ya za'ayi kakawoni Nan?


Ya rausayar dakai yana cewa


"Nasani ai,awa uku kawai zamuyi"


Ta girgiza Kai


"Nariga nakira mama nafad'a mata nataho,idan taga nadad'e fa?nide kabarni intafi"


Yasauke guntun numfashi had'i da cewa


"Kinsan nisan dake tsakanin nan da katsina?


Ta girgiza kai,


Yacigaba da cewa

"Idan a mota zakije tafiyar awa arba'in da hud'uce,dan haka ki kwantar da hankalinki acikin minti d'aya zan iya kaiki har cikin gidanku"


Shuru tayi tana mamakinsa, yabud'e motar yafito,ya bud'e Mata


"Muje madam"


Kamar bazata fito ba,sai kuma tafito tana k'are ma gidan kallo,wanda yasha ado da furanni masu shegen kyau


Yayi gaba tana binsa abaya


Wani falo suka shiga,shima fad'an  kyawunsa b'ata lokaci ne


Yayi mata nuni da kujera


"Zauna"


A d'erere ta zauna ta kallon kayan alatun da aka zuba ma falon


Maganar shi ce ta katseta


"Me zan kawo Miki?dannasan bawani karin kirki kikayi ba"


Girgiza mai kai tayi alamar babu komai


Shima ya girgiza nasa kan


"Nan fa d'aya,bazeyuwu kizauna da yunwa ba"


Yak'arasa fad'a yana janyo wani k'aramin tebur ya ajiye aganta tare da ambaton,tea,aarish


Sai gasu sun bayyana akan tebur d'in


"Oya Bismillah"


Mamakine ya k'ara kamata, kallon teburin kawai takeyi


Ya tashi daga kujerar da ya zauna,yadawo kusa da ita yana cewa


"Please mamakin ya isa haka,kici ko kuma yanzunnan kijisu a cikinki"


Kallonsa tayi amma ta kasa cewa komai


Yagyad'a kai gami da cewa


"Shikenan"


Abun al'ajabi gani tayi wayam,babu komai akan tiren sannan taji cikinta yayi dam


K'ara kallonsa tayi a hanzarce


Ya d'aga mata gira


"Na hutar dakene habibty"


Tasauke dogon numfashi tana fatan in mafarki takeyi ta farka hakanan



Durk'usa wa yayi agabanta yana ambaton sunanta


"Rauda!!!


Kallonsa kawai takeyi amma takasa amsawa


"Dan allah ki yafemin,nasan nayi kuskure kuma ban kyauta miki ba,amma ki gafarceni wallahi ina k'aunar ki,son da nikeyi miki ne yasa na aikata duk abunda nayi


Bakisan yadda naji ba,dakike jin wani iri akaina,zan iya yimiki komai dan insaki farinciki, nayi miki alk'awari amma inaso ki yafemin, bazan iya zama cikin kwanciyar hankali ba muddin kina fushi Dani"


Maganganun sa sun sa jikinta yayi sanyi,cikin sanyin jiki tace


"Na yafema,amma kaima kayi min alk'awarin bazaka cutar dani ba"


Yayi murmushin Jin dad'i yana kama hannunta


"Nayi miki alk'awari habibty,babu cutarwa a tsakanina dake,amma kicire tsoron da kike ji akaina wallahi da zan cutar dake da tuni nayi hakan kisani ke b'arin jikina ce, idan har zan iya cutar dake to zan iya cutar da kaina"


Hmmmmmmmm tasauke doguwar ajiyar zuciya 


"Shikenan"


Mik'ewa yayi,yana dubanta


"Mik'e habibty"


Ta mik'e kamar yadda  ya umarceta


Rungume ta yayi sosai ajikinsa yana maida numfashi


"Nasan dama zaki fahimceni,abu d'aya nikeso kiyimin,shine kiyarda ina k'aunarki"


Ji tayi gabad'aya tsoronsa da takeji ya yaye,ta Lumshe idanuwanta tana jin wani abu na ratsa zuciyarta


"Aasim!


Ta kira sunansa da murya k'asa-k'asa


Ya amsa

"Na'am habibty"


Sai kuma tayi shuru


Yad'ago ta ahankali yana kallon kyakkyawar fuskarta


Itama shid'in take kallo


"Habibty, kifad'a min duk abunda kikeso zanyi miki shi da izinin Allah"


Tayi murmushi tare da cewa


"Shikenan nagode"


Ya gyad'a kai yace


"Babu y'ar godiya,muje kizagaya gidan kigani komai natsara shine dan idan kika gani ya burgeki"


Tagyad'a kai tare da cewa


"To muje"


Kama hannunta yayi suka fara zagaye gidan,sannan suka dawo bedroom


Shima antsara shi komai na d'akin kalar pink,sannan ya bud'e mata toilet d'in dake ciki


Shima bayin abun burgewa


"Komai yayi Miki?


Ya tambaya yana kallonta


Jinjina kai tayi tare da cewa


"Yayi,amma nida ba zama zanyi aciki ba,meyasa......


Ya tsunsa biyu ya d'aura a lips d'inta


"Wayace Miki,aduk sanda kikaga dama zakizo,kuma nima aduk sanda naga dama zankawoki"


Tayi ajiyar zuciya kawai batare da ta k'ara cewa komai ba


Hannunsa yasa yana shafa dokin wuyanta ahankali yakai kan zip d'in doguwar rigar dake jikinta


Ta kallesa tace


"Yadai?


Guntun murmushi yayi tare da fad'in


"Dede, yakamata kiyi wanka ai ko?


Ta girgiza kai aa


Shima ya girgiza Kan

"Nikuma nace eh"


Kafin ta k'ara magana sai ganinta tayi cikin kwamin wanka shak'e da ruwa yasha wasu k'ana-nun fulawowi jajaye wanda suka lullub'e saman ruwan


Ta shafa jikinta dasauri taji wayam babu kaya


Kallonsa tayi har lokacin yana tsaye bakin bayin


Yad'aga mata rigar ta dake hannunsa

Yana cewa


"Gatanan kwantar da hankalinki"


Saurin kare jikinta tayi da hannayenta tana dun'k'ule wa guri d'aya


"Dan Allah kabani kayana"



Girgiza kai yayi gami da cewa


"Sai fa kinyi wanka,zanbaki"


"Please kabani"


Yakuma girgiza kai


"Allah bazan baki ba sai kinyi wankan,idan kuma bazakiyi ba to taso ki amsa"


Yafad'a yana mik'o mata kayan


Girgiza kai tayi


"Naji zanyi,amma ka ajiye min kayan kuma kafita ka kulle k'ofar"


Ya jinjina kai yana cewa


"Shikenan,kuma wankan tsakani da allah zakiyi ba kwara ruwa ba"


Ta jinjina kai


"Naji"


Ajiye kayan yayi akan abun wanke hannu,yafita ya kullo mata k'ofar


Numfashi tasauke, tana kallon cikin ruwan,sannan tayi wankan a gurguje


Tafito daga cikin kwamin zata d'auki,samtsin tiles ya kwasheta zata fad'i


Ji tayi an ruk'ota,a tsorace ta juya dan tasan yafita abayin


Sai dai me shid'in tagani yana mata murmushi


"Baka fita ba?


Ta tambayesa da mamaki


Ya jinjina kai


"Eh dawowa nayi"


"To ya akayi banga dawowar ka ba"


Dariya yayi tare da cewa


"Mutum ne inze shiga wuri sai ansani amma mu sai munga dama za'asani"


"Kenan agabanka nayi wankan?


Ta K'ara tambayar sa cikin yin sororo da baki


Dariya ya kuma yi yana fad'in


"Wad'ancan kayan a canzasu ne?


Baya tayi dasauri dan tama manta bata maida kayan jikinta ba


Dariya yakuma yi sosai,yana bud'e k'ofar bayin ya fice


Tazura kayan tare da fitowa tana cewa


"Allah munyi fad'a,ni muje ka kaini gida"


Ya janyo ta tafad'a jikinsa


Suka kalli juna sosai


"Habibty I'm sorry bazan sake ba,amma miye laifina danna kalli matata??


Sauke numfashi tayi 

"Nidai muje kakaini"


Yasauke ajiyar zuciya


"Kingaji daganina ko?


Ta girgiza kai tace


"Bahaka bane"


"Aa kifad'a min gaskiya,yanzu danni ba mutum bane kin rage son dakikeyi min ko?


Ta kuma girgiza kai


"Inaso inje gida ne,amma bawai da wani abu araina"


Gyad'a kai kawai yayi amma yanayin fuskarsa yanuna Babu dad'i


"Amma yanzu innakai ki,za'a ga kin kai dawuri, kibari nan da minti arba'in sai inkai ki"


Tasauke numfashi tace


"Shikenan"




Sis nabila ina missing d'inki Allah ubangiji yabaki lafiya yasa kaffarene




Y'arfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



🌹 JINNUL

          AASHIQUE🌹



                🧞‍♂ 🧞‍♂

                    🧞‍♂


                   NA

HARIRA ALIYU (y'arfillo)🧕🏻



Dedicated to Little hajjo and my elder sister Hafsat Aliyu



🅿AGE📕 1⃣5⃣


Wannan page d'in nakune y'an golden forum,na sadaukar dashi gareku kuyi yadda kukeso da shi🧡🧡



8:00🕒 Am

FRI,MAY 3



Bissmillahir rahmanin rahim👏🏻👏🏻👏🏻



Mama bata k'ara tambayar ta ba,dan tafi kowa sanin matsalar y'arta


Addu'a taci gaba da tofa Mata,bata bari ba harsai da tadawo cikin natsuwata


Lokacin ana kiraye-kirayen sallar asuba


"Kina yin wasa da azkar ko Rauda?


Mama tafad'a tana kallonta


Rauda ta girgiza kai alamar aa


Mama ta cigaba da cewa


"Aa kina wasa dashi banace miki duk sanda zakiyi bacci kiyi alwala ba, sannan kitofa ma jikinki addu'o i?yaushe rabon da kiyi hakan?


Rauda ta yi shuru tana tunani,dan ita rabonta da tayi alwala ko azkar d'in bacci har ta manta


Mama ta girgiza kai cikin damuwa


"Karatun al'qur ani ma kin rabu da yi ko?


Shuru Rauda tayi nanma mik'ewa mama tayi tafice daga d'akin dan d'auro alwala


Rauda ta jingina da jikin gado kanta nawani irin sarawa, gabad'aya yanzu tunanin ta nema yikeyi ya tsaya jitayi kamar ba ita ba


B'angaren Aasim,atsaye ya tadda ammi jikin wata k'atuwar bishiyar da ke cikin sahara


Wacce take gefen shiga masarautar


Kallo d'aya yamata yagano tashin hankali da tsananin damuwa a tare da ita


Kama hannunsa tayi suka zauna suna kallon juna


"Ammi,wai meke faruwa ne naga sak'on me martaba"


Ammi ta sauke numfashi tana bashi amsa


"Akan tarayyarka da Rauda ne,kasan tun bayan haihuwar shahida be kuma cewa komai ba,to jiya abu saima yaje fada


Yike cewa abunda kakeyi sam be dace ba,saboda da wanine yike aikata hakan da tuni an d'auki mataki akansa


Amma saboda kai d'an sarki ne,sai azuba maka ido ak'i cemaka uffan


Shine sarki yaturama sak'on Kira,kafin na turama nawa sak'on sai da naje na sami me martaban akan wani mataki yike shirin d'auka


Shine yace bega laifin abu saima ba,dan  tabbas ba adalci bane,kana d'an da ya haifa kana aikata laifuka wanda kaine jigon masarautar,kuma ya zamar maka dole ka rabu da ita,domin auran jinsin d'an adam baya daga cikin tsarin masarauta"


Numfashi Aasim ya sauke,ya na kad'a kai


"Inbanda munafurci meya ruwan abu saima da rayuwata,nafahimcesa tunda nak'i auran y'arsa na nuna banason ta yashiga bak'in ciki Dani"


Ammi tadafasa cikin damuwa tare da cewa


"Nidai duk wannan bashi bane,abunda nikeso da Kai dan Allah ka amince ka rabu da ita, banaso ka bijirewa umarnin da mahaifinka ze baka,nayi maka alk'awarin tara maka kyawawan mata a jinsinka kazab'i wacce tafi maka........


Katseta yayi ta hanyar girgiza kai


"Bazan iya ba ammi,wallahi bazan iya ba,bazan iya rabuwa da ita ba"



Ammi tayi shuru tana kallonsa,durk'usawa yayi agabanta yana kama hannayenta


"Ammi kitaimaki rayuwata dan Allah,ammi bazan iya rayuwa inba tare da ita ba,idan da abunda zaki iya yi kiyi dan Allah"


Yafad'a cikin tsananin damuwa


Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon cikin idonsa


"Aasim babu abunda zan iyayi,kasani kai kad'ai gareni bayan kai banida wani d'a aduniya, narok'eka kada ka fusata mahaifinka dan nasan ze iya d'aukar ko wani hukunci akanka,bar ganin yana sonka amma yafi son kimarsa da darajarsa fiye dakai kuma zeyi komai ne abisa adalci"


Aasim ze kuma magana ta had'e mai hannunta guri d'aya


"Kaga dai nice na haifeka amma narok'eka daka bi umarnin da ze baka,banaso wani abu ya sameka kai kad'ai nike dashi aduniya"


Ta k'arasa fad'a hawayen daya cika idanuwanta na gangarowa


Runtse idanuwansa yayi yana cize leb'ansa 


Ammi ta mik'e tana kallonsa tare da cewa


"Zan wuce,gobe katabbata dakazo a lokacin da ya baka"


Jingina yayi da jikin bishiyar wasu zafafan hawaye na gangaro Masa 


Ya bud'e idanuwansa yana kallon sararin samaniya


"Bazan iya rabuwa da ita ba,ya allah kataimakeni"


Yafad'a cikin damuwa da rashin sanin abunyi


Ita ko Rauda kasa komawa ta kwanta tayi,tunda tayi sallar asuba tana kan darduman 


Gabad'aya jinta takeyi cikin damuwa,da kuma tsananin fargaba


Har mama ta kammala abun kari ta dawo d'akin bata tashi daga kan darduman ba


"Wai ke lafiyan ki k'alau kuwa? kintashi bazaki je kigaida baban ku ba"


Mik'ewa tayi jikinta babu k'wari,ta ninke dar duman tana yin hanyar waje


Mama ta dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta


"Rauda"


Rauda ta juyo tana amsawa

"Na'am"


"Meke damunki?


Mama ta tambaya tana tsare ta ido


Girgiza mata kai Rauda tayi


"Babu komai,banjin dad'ine kawai kai na ke ciwo"


Mama ta gyad'a kai had'i da cewa


"Shikenan jeki gaishe sa kidawo kisha magani"


Jinjina kai tayi tare da ficewa


Da sallama ta shiga d'akin Abba


Ya amsa,ta tsugunna tana gaishesa


Amsawa yayi yana kallon ta a tsanake


"Raudatu baki da lafiya ne?


Ta k'ak'aro murmushi tana cewa


"Aa baba,kaina ne ked'an min ciwo,shima kuma ba sosai ba"


Ya kad'a kai yace


"To tashi kije ki karya kisha magani,idan bedena ba anjima idan nadawo kasuwa sai inkaiki chemist"


"To"


Tace tare da mik'ewa tafito daga d'akin


Kan gadon mama tadawo takwanta

Tana jin maganar sa a cikin zuciyarta


"Habibty,anjima da daddare zamu tafi"


Shuru tayi tana lumshe idanuwanta,mama tadawo d'akin hannunta rik'e da kofin tea da paracetamol


Ta amsa tasha,tasha maganin sannan ta koma ta kwanta


Ranar mama ce da girkiDan haka bata zauna ba,tana ta ayyuka, Rauda tayi k'ok'orin fitowa ta tayata amma tace aa taje takwanta tunda bata jin dad'i


Wunin ranar haka Rauda tayi shi sukuku


Da yamma, tana bayi zatayi wanka ta tasa ruwan agaba tana kallo 


Wani haske tagani ya b'ullo cikin bayin,sai ga Aasim ya bayyanaKallo d'aya suka ma juna suka gano damuwar da kowanensu yike ciki


Kauda kanta tayi daga kansa, gabanta na fad'uwa


Shiko wani kalar abune ya k'ara sukar sa,Wanda yasan tsan-tsar k'aunar tane


Tayaya ze iya rabuwa da wannan kyakkyawar halittan?


Yasan akwai kyawawan mata a duniya amma bega tamkar ta ba, tabbas baze iya rabuwa da ita ba 


Gab da ita ya tsaya,dan tana jingine ne da bangon bayin


"Rauda"


Ya kira sunanta,ta juyo da kanta tana kallonsa ba tare da ta amsa ba


Shima shuru yayi suka kalli juna na y'an wasu sakwanni sannan yace


"Meyasa kika tada hankalinki?ba wani abun tsoro zaki gani ba idan munje,zaki ga kowane a suffar mutane kamar yadda kike ganina,kuma sannan ina tare dake,babu wani abun da zesa meki"


Juyawa tayi da niyyar fita daga bayin


Yasa hannu ya dafe bangon ya tare mata hanyar


"Rauda ki yarda dani, wallahi bazan cutar da ke ba"


Kallonsa tayi da idanuwanta da suka fara cikowa da hawaye


"Aasim,dan allah ka rabu Dani, kabarni inji da abunda yike damuna please"


Tak'ara sa fad'a tana tana juyawa da sauri ta d'ayan gefen


Jitayi ya rungumo ta tabaya,tayi saurin runtse idonta danji tayi illahirin jikinta ya amsa


Nannauyan numfashi yasauke yana sak'alo kansa ta gefen wuyanta


"Rauda,ina sonki,nasan kema kina sona dan allah kada kik'ara ambaton in rabu da ke"


Juyowa tayi dasauri,still Tana rungume a jikinsa,suna fuskantar juna


"To in ina sonka fa?yazanyi, zanciga ba da rayuwa dakai ne ahaka?


Meyasa kakasance a wani jinsi meyasa?


Tak'arasa fad'a tana fashewa da kuka


"Aasim ina sonka,dan girman allah idan mafarki nikeyi cewa kai ba mutum bane ka tasheni,nayi alk'awarin bazan sake yin baccin ba bare inkuma yin makamancin irinsa"


Tausayinta had'i da k'aunarta suka sake mamaye mai zuciya


K'ara rungumeta yayi yana runtse idanuwansa,cikin tsananin damuwa


Sai da suka kwashi minti biyar ahaka,sannan ya d'agota yana kallon kyakkyawar fuskarta data jik'e sharkaf da hawaye


"Rauda,nayi alk'awarin zan rayu dake ako wani irin yanayi, zanyi miki komai kamar yadda jinsin ki zeyi Miki,dan allah ki kwantar da hankalinki kinji?


Ta bud'e jik'akk'un idanunta tana kallonsa kawai batare da ta ka'ra cewa wani abu ba


Hannunsa yasa yana share mata hawayen


"Kinsan abunda natsana shine ganin hawayenki,shine abunda ke tada min da hankali,kibar yimin asarar su please"



Ya d'an numfasa sannan yacigaba da cewa 


"Kinsan ya fuskarki take komawa idan kina kuka?


Ta tsaresa da kyawawan idanuwanta tana kallon yadda yike ya mutsa fuskarsa alamar haka tata fuskar take komawa idan tana kuka


Murmushi tayi,duk da batayi niyyar yi ba


Ya dafa kafad'unta yace


"Yauwa kokefa, Baki ga kinfi kyau ba"


Ya k'arasa fad'a yana sauke ajiyar zuciya


"Bari inbarki kiyi wankan,anjima dai kar ki manta"


Gyad'a masa kai kawai tayi,yayi murmushi tare da manna mata kiss a goshi


Ta sauke doguwar ajiyar zuciya bayan b'ace warsa sannan tayi wankan a sanyaye


Da daddare,misalin k'arfe goma,mama tagama Shirin ta tana mik'ewa


"Kisamin sakata a k'ofa,kada kibar min k'ofa ta kwana a bud'e sannan kiyi addu'a kafin ki kwanta"


"To"

Rauda tace,mama ta fice daga d'akin tana janyo mata k'ofa


Rauda tamik'e ta sa sakata a k'ofar falon sannan ta dawo ta zauna tana d'aukar wayarta dake k'ara


Numban Salma tagani,ta d'auka tana sallama


Daga can b'angaren salma tace


"Mara kirki,tunda baki kira kinji ya na sauka ba nina kiraki"


Rauda ta yi murmushi


"K'awa kina Raina,ya kike"


"Habibty"


Taji an fad'a abayan ta,ta waiga Aasim tagani


Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa salma


"Bari zankira ki ina zuwa"


Ta katse wayar tana kallon sa


"Muna iya tafiya?


Yatambaya,ta jinjina masa Kai alamar eh


A cikin y'an sakwanni taganta acikin sahara,babu gida gaba babu gida baya


Kallonsa tayi k'irjinta na dukan uku-uku 


Amma takasa yin magana


"Abun hawa na hanyar zuwa yad'auke mu"


Begama rufe baki ba saiga wasu dokuna guda biyu,d'aure da wata kujera ta zaman mutum biyu da rumfa a samanta


Saurin rik'esa tayi,dan girman dokunan ya wuce misali,wani irin tsoro yafara d'arsuwa acikin zuciyarta


Aasim ya lura da hakan,ya yi mata murmushi cikin k'arfafa mata gwiwa


"Habibty kada kiji tsoro kinji?muje"


Yak'arasa fad'a yana kama hannunta,babu yadda ta iya suka shiga suka zauna,dokunan suka juya inda suka fito a guje


Rauda ko mamakine da aljabi ya dabai-bayeta


Gabad'aya gurin Sahara ne,amma kuma ga wasu bishiyoyi masu shegen kyau dasukayi ma wurin ado


Daga nesa ta hango wani katafaren gari wanda katanga ta za gayesa 


Jitayi tsigar jikinta ta tashi yarrr


Ta yi saurin runtse ido tana ambaton sunan allah


Kallonta Aasim yayi ganin yanayin data fara shiga


Yasa ya kama hannunta ya damk'e cikin nasa


Ahankali taji tsigar jikin ta dena tashi,suka kalli juna yayi mata murmushin k'arfin Hali dan gabad'aya hankalinsa a tashe yike


A k'ofar garin dokunan suka tsaya,wacce take a kulle


K'ofar tana da fad'in gaske,tsayawar dokunan keda wuya k'ofar tabud'e


Wasu zabga-zabgan mutane Rauda tagani masu matuk'ar girma sanye da bak'ak'en kaya da wasu manyan takobi ahannayensu


Idanuwannasu jawur kamar gauta,tayi saurin rufe idanuwanta k'irjinta nawani mugun bugawa


Maganar su ce tasa tabud'e idon dasauri jin muryoyinsu a kausheshe


Gabad'ayan su zubewa sukayi a k'asa suna fad'in


"Barka da isowa,yarima,allah shi baka nasara"


Ya d'aga masu hannu yanayi musu magana da wani yare


Nan da nan suka basu hanya,dokunan suka cigaba da tafiya


Rauda sakin baki tayi tana kallon cikin masarautar,da tsayawa fasalta ta b'ata lokacine 


Ga mutane kala-kala iri-iri kuma duk inda suka gifta sai sun zube suna kwasar gaisuwa


Kallonsa tayi taga kayan jikinsa sun sauya zuwa kayan sarauta,idanuwansa ma k'wayar ciki sun tashi daga bak'in dasuke sun koma wani kala 


Shima d'in tsoro yabata,ta k'an-k'anme jikinta tana ambaton sunan allah


Cikin sauri yace


"Rauda,yazamarmin dole inkoma yadda nikene,ki kwantar da hankalinki dan allah,"


Bata sauraresa ba tacigaba da karantasu addu'o i, jikinta na kakkarwa



Bata yadda tak'ara bud'e idanuwanta ba harsaida taji dokunan sun tsaya


Tabud'e idanuwanta a tsorace tana kallon inda suke


Wani k'ayataccen wurine me shegen kyau daga can gabansa kuma wata k'atuwar fada ce


Inda take hango wasu sanye da fararen kaya zazzaune


Ta kuma runtse idanuwanta tana fad'in


"Aasim,kataimakeni kamayar dani"


Hannunta yakama yana karanto wasu abubuwa da batasan ko menene ba


Take taji tsoron da takeji yatafi,sai abunda ba a za rasa ba


Takuma bud'e idanuwan ahankali tana watsasu akansa


"Habibty babu abunda zesameki,mutafi fada,kuma idan munje duk abunda kiga nayi kiyi irinsa kinji?


Gyad'a masa kai tayi tana bin bayansa


Har k'ofar fada, gabad'aya wad'anda ke zazzaune rusuna masa sukayi suna kwasar gaisuwa


Banda wani me kama da larabawa da ya hakimce a kan wata kujerar zinari


Aasim ya rusuna agabansa,itama Raudan ta rusuna kamar yadda taga yayi


Aasim yace


"Allah ya taimaki me martaba"


Sarki Ramzad ya kad'a kai batare da ya amsa ba


Mik'ewa Aasim yayi suka d'anyo baya sannan ya zauna,itama ta zauna kamar yadda yayi


"Yarinya!


Sarki Ramzad yafad'a yana kallon Rauda


Ta kallesa batare da ta amsa ba, gabanta na fad'uwa


"Shin kinsan waye Aasim?


Ya tambaya still idanuwansa na kanta


Nan ma shuru tayi,dan bata da bakin magana


Sarki Ramzad ya cigaba da cewa


"Aasim d'ane,kuma magaji a wannan masarauta,sannan kuma rauhani"


Ya d'an numfasa kad'an,sannan ya cigaba da cewa


"Amma duk da sanin hakan,kika amince zaki cigaba da rayuwa da shi?


 Nayi miki uzuri,awancan lokacin domin ko kina cikin rashin sani,amma ayanzu zan yanke hukunci a bisa saninki"


Ya maida kallonsa kan Aasim yana ambaton sunan sa,


Aasim yad'ago da kansa k'irjinsa na bugawa


"Ina buk'atar ka furta kalmar saki,ayanzunnan sannan kayi alk'awarin rabuwa da ita,taje ta auri jinsinta"


Cikin kad'uwa da jin kalaman mahaifinsa ya zube,cikin tashin hankali yace


"Kayi min afuwa,abi bazan iya furta kalmar saki a gareta ba"


Sarki Ramzad ya had'e fuska ya kuma mai-maita abunda yace


Nan d'inma  kuma zubewar yayi


"Abi kataimaki rayuwata, wallahi ita kad'ai nikeso bazan iya rayuwa idan babu ita ba"


Sarki Ramzad ya kad'a kai yace


"Amma kasan a dokar masarautar mu babu auran jinsin bil'adama ko?


Aasim ya jinjina kai


"Nasani abi,amma kayimin rai kabarni naciga ba da rayuwa tare da ita"


Sarki Ramzad ya girgiza kai


"Abune da baze tab'a yuwuwa ba kana d'an dana haifa inbarka ka sab'awa shari'ar masarauta,dan haka ka furta saki agareta"



Ammi dake gefe ta taso cikin tashin hankali ta wanka masa mari


"Baka da hankali ne Aasim?da mahaifinka kake jayayya?


Sarki Ramzad ya d'aga mata hannu


"Ya Isa,ki k'yaleshi zanga iya kafiyarsa dakuma taurin kansa"


Komawa tayi inda take,tanayi ma Aasim wani kallo me cike da bada umarnin ya aikata abunda akace Masa


"Na baka minti biyar,ka aiwatar da abunda nace"


Sarki Ramzad yafad'a cike da k'asaita 


Aasim ji yayi kamar kansa ze juye saboda tsananin tashin hankali


Gabad'aya fadar tayi tsit,kowa maganar Aasim yike jira


Ahaka har minti biyar d'in tayi


Sarki Ramzad ya sauke numfashi tare da cewa


"Bazaka bi umarnina ba kenan?


Aasim jan gwiwowinsa yayi zuwa gabansa ya fashe da kuka


"Abi, kagafarceni bazan iya rabuwa da ita ba"


Runtse ido sarki Ramzad yayi,cike da tsananin takaici


Yabud'e su ya watsa su akansa


"Aasim akan bil'adama kake jayayya Dani?


Aasim ya kuma fashewa da kuka


"Ni me biyayya ne agareka abi,amma ina rok'onka da ka yimin agaji"


Sarki Ramzad ya jinjina kai yana kallon me fad'an hukunci


"Miye hukuncin duk wanda ya karya dokar masarauta?kuma akace ya bari ya yak'i bari"


Me fad'an hukunci yayi shuru,yana tunanin abunda zece ganin d'an sarki ne dakansa


Sarki Ramzad ya katse mai tunani ta hanyar cewa



"Kada kayi la'akari da wai d'anane,kafad'i hukuncin da ya rataya akanshi"


Me fad'an hukunci yasauke numfashi tare da cewa


"Za'a koresa daga masarautar gabad'aya"


Sarki Ramzad ya jinjina kai yana kallon Aasim yace


"Kaji hukuncin da ya rataya akan duk wanda ya aikata laifi irinnaka,dan haka sai ka zab'a cikin biyu,


Ko kasaketa karabu da ita,ko kuma ka bar masarautar gabad'aya"


"Abi ni d'anka ne,kaji tausayina........


Sarki Ramzad ya katsesa


"Tunda ni amatsayina na mahaifinka ban isa inbaka umarni kabi ba,yazamar min dole ind'auki hukunci akanka,dan haka fad'i ina jiranka,wane kazab'a"


Yak'arasa fad'a cikin d'aga murya

"abi,kayi hak'uri ka gafarceni........



"Nace kazab'a d'aya ko?


Sarki Ramzad ya katsesa a fusace


Kallon Rauda yayi wacce gabad'aya itama hankalinta ya gama ta shi


Ya maida kallonsa ga me martaba da yike cewa


"Zan irga uku,idan har na irga uku baka  saketa ka rabu da ita ba,to tabbas zaka bar min masarauta"


"D'aya.....


Biyu........


Cikin tashin hankali Aasim yace


"Abi dan girman allah.........


Sarki Ramzad ya d'an dakata yana jiran jin abunda zece


Amma kuma sai yayi shuru,yana cize leb'ansa da k'arfi tare da runtse idanuwansa


"Uku"


Me martaba yafad'a,ammi ta taso da sauri tana jijjiga Aasim


"Aasim,kadawo hayyacinka,takan mace,macen ma bil'adama zaka zab'i rabuwa da ahalin ka,maza ka rok'i gafarar mahaifinka ka aiwatar da abunda yace"


Tafad'a a zafafe cikin kid'ima


Bud'e idanuwan sa Aasim yayi yana zuba su akanta


"Ammi kigafarceni,bazan iya rabuwa da ita ba..."


Yafad'a cikin zafin zuciya


Ammi baya tafara ja tana girgiza kai


"Aa,aa, Aasim kada kayi min haka"


Abu saima ne ya mik'e shima cikin tashin hankali dan betab'a zaton Aasim ze zab'i barin masarautar akan Rauda ba,ga saima can tana kukan inda babu shi bazata iya rayuwa ba,kuma shi yayi hakanne dan sama ma y'arshi farin ciki dan yasan idan Aasim yarabu da Rauda dole ze auri saima



"Yarima kasan hukuncin duk wanda ya zab'i barin masarauta kuwa? Dole fa sai ka bi ta tauran


(Tauran wani wurine zagayayye,da yike da k'unci da zafi, Wanda duk bayan minti biyu yike fitar da wani k'ara me kama da sautin tsawa,wanda duk wanda yike ciki sai hucin k'arannan ya tsattsaga jikinsa)


Abu saima ya cigaba da cewa


"Wanda sanin kankane sai rauhan yatsaya acikin tauran har sai ya tsallake k'arar tauran guda arba'in da tara,shin kamanta da azabar dake cikin tauran ne?


Aasim yayi masa wani kallo me cike da tsana dan inba da din munafuncinsa ba da yanzu wannan abubuwan basu faru ba


"Nasani,kuma na amince ko da hakan zeyi sanadiyyar rasa rayuwata ne"


Gabad'aya fadar zaro ido sukayi cike da al'ajabi


Rauda da jikinta ya gama mutuwa hawaye suka gama wanke mata fuska saboda tsananin tausayin Aasim,shin wani irin so yike mata da ze zab'i rabuwa da ahalinsa saboda ita?


Cikin kuka ta matsa kusa dashi tana fad'in


"Aa Aasim,kada ka bijirewa umarnin iyayenka akaina"


Girgiza kai yayi yana kallonta da idanuwansa da suka rine


"Rauda ina k'aunar ki,zan iya hak'ura da komai inhar zan rayu dake"


Sarki Ramzad da jikinsa yagama yin sanyi duk da b'acin ran dayike ciki kukan d'annasa na tab'a masa zuciya


"Na baka daganan zuwa gobe,kaje kanatsu kayanke wa kanka abunda yafi maka,wannan ne adalci na k'arshe da zan maka


Idan har ka amince da rabuwa da ita,to kazab'i ko y'ar sarkin wace k'asa ce zan aura ma ita


Idan kuma har kakai goben kana kan bakanka na k'in rabuwa da ita to tabbas zaka bar min masarauta


Sannan kuma zaka tsallake tauran ninki biyu, d'aya na barin masarauta d'aya kuma na jayayya dani"



Bubbuga k'ofar da akayine ya sa Rauda ta tashi,akan gadon mama ta ganta


Tana jiyo muryar maman tana cewa


"Kitashi kiyi sallah"


Dafa kanta tayi da yike sarawa kamar ze rabe biyu tana girgiza shi


"Aasim,kada kayi haka dan Allah"




Y'arfillo.



[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*     

       *AASHIQUE*🌹 



               🧞‍♂ 🧞‍♂

                  🧞‍♂

   

                NA

HARIRA ALIYU _(y'arfillo)_🧕🏻




_Dedicated to little hajjo and my elder sister Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 1⃣6⃣


Ina yima ɗaukancin masoyana barka da sallah, dafatan anyi sallah lafiya, wannan Page na baku shi amatsayin barka da sallah, sannan ina me baku haƙuri akan jina shuru da kuka yi bani da lafiya ne ina buƙatar addu'arku


_7:32_🕒 PM

FRI, JUN 7


_Bissmillahir rahmanin rahim_



"Aasim kada kayi haka,kada kayi haka dan Allah"


Tafad'a cikin tsananin damuwa


Bubbuga k'ofar mama ta kuma yi akaro na biyu


Cikin rashin k'warin jiki ta mik'e jiri na d'ibarta,ga kanta da yayi mata mugun nawi tana jin kamar an d'aura mata gingimemen dutse


Ta zare sakatar falon tana jingina da bango da sauri,dan ji tayi tana neman fad'uwa



Mama ta kalleta sosai tace

"Haryanzu kan bedena ciwon bane?


D'aga mata kai kawai tayi batare da tayi magana ba


Mama tasauke numfashi cikin damuwa tace


"Sannu,ina ganin idan gari yayi haske kawai zamu je k'aramin asibiti adubaki, k'ilan harda typhoid,kidaure kiyi sallan"



To Rauda tace tafito ta d'au buta tayi alwala,tana rawar sanyi


Lokaci d'aya zazzab'i me zafi ya rufeta,


A gaggauce tayi sallar saboda sanyin datake ji sosai,tana idar da sallar ta koma kan gado ta lullub'e



B'angaren Aasim kuwa,tunda taron fada ya tashi,yashige d'akinsa tare da kullewa dan gabad'aya baya son a damesa


Yana jiyo muryar ammi daga bakin k'ofar tana fad'in ya bud'e


Amma yak'i saboda baya son yaga tashin hankalin dake tare da ita,harta gaji ta wuce


Ya na zaune a k'asa kawai, cikin tsananin tashin hankali


K'wan-k'wasa k'ofar aka kuma yi,yaja gajeren tsaki tare da   kifa kansa 


Daga can  k'ofar d'akin muryar mus'ab yaji Wanda ya kasance babban amininsa


Hannunsa ya d'aga yayi nuni  da k'ofar, tabud'e


Mus'ab ya shiga d'akin Yana fad'in

"Wai meke damunka ne Aasim? Ace tun daren jiya ka kulle kanka a d'aki kakuma sawa d'akin takunkumi tayadda bawanda ze iya shigowa"


Aasim numfashi ya sauke yana d'auke kansa da ga kan mus'ab


"Kawai banaso a dameni ne,ina buk'atar natsuwa ne"


Mus'ab ya jinjina kai yace

"Hakan yayi kyau,inafatan a natsuwar da kasamu ka canza abunda ke zuciyarka,


Dan nasan jiya kana cikin rud'ani ne,shiyasa kak'i yin abunda me martaba ya umarce ka"


Aasim Ya  sauke gauron numfashi tare da lumshe idanuwansa wad'anda suka kad'a sukayi ja


Mus'ab ya gyara tsugunnuwar da yayi yana k'ara fuskantar Aasim d'in


"Kayi shuru,ba kace komai ba,ko haryanzu kana kan bakannaka?


Ya bud'e idanuwansa yana d'aura su akan mus'ab


"Mus'ab,bazan iya rabuwa da ita ba,bazan iya ba"


Yafad'a cikin wani irin yanayi


Zaro ido mus'ab yayi yana kallonsa cike da mamaki


"Mekake nufi Aasim?kana nufin kazab'i rabuwa da ahalinka,takan bil'adama?


Yad'an numfasa sannan ya cigaba da cewa


"Ni wallahi banga abunda kagani agurin waccan bil'adamar ba,da yasa gabad'aya ka rikita tunaninka,


Dan allah kadawo cikin hankalinka,akwai kyawawan mata aduniya,ga kuma saima..........


Katsesa yayi ta hanyar d'aga masa hannu


"Dan allah kada ka k'ara b'ata min Rai,ni ita nike so kuma ita na zab'a zanyi rayuwa da ita,abunda nagani da ya rikita min tunani akanta kuma


Wannan ba damuwar ka bane,idan zaka bani shawara a matsayinka na aboki na kabani,idan kuma maganganun banza kazo kafad'a min ga hanya"



Ya k'arasa fad'a yana nuna mai hanyar fita


Mus'ab ya sauke ajiyar zuciya cike da juyayin al'amarin abokinnasa


"Aasim nikake fad'a ma haka?


Aasim ya d'aga kai yace


"To mekake so ince maka? A matsayinka na aminina kamata yayi kabani shawarar yadda zanyi insamu mafita amma kazo kana fad'a min abunda kasan ze k'ara min b'acin ran danike ciki"


Mus'ab yakuma sauke numfashi yana kad'a kai


"Shikenan,allah ya baka hak'uri"


Yafad'a yana mik'e wa ze fita


Sannan yace

"Bazan takuraka ba,akan fasa abunda kayi niyya,amma ina me baka shawara da kada ka bijirewa umarnin mahaifinka,katuna da haihuwar ka da yayi,da kuma rainonka har izuwa girmanka ko ba komai yaci wannan arzik'in "


Yana gama fad'ar haka ya fice


Doguwar ajiyar zuciya Aasim ya sauke tare da jinginar da kanshi


Tabbas yasan abunda yike shirin yi ba dai-dai bane,to amma ya zeyi? Ya zeyi da muradin zuciyarshi?


Ya runtse idanuwansa yana hango kyakkyawar fuskarta 


"Bazan iya rayuwa babu keba *Rauda*"


Yafad'a tare da furzar da wata iska me zafi


Mik'ewa yayi yana fad'in


"Nasan zaka fahimceni abi,idan nak'ara yimaka bayanin yadda nike jinta a cikin zuciyata"


B'acewa yayi,be bayyana a ko ina ba sai abakin falon sarki inda yike hutawa



Kallo d'aya yayima kuyangin dake tsattsaye bakin k'ofar ya kauda kai tare da cewa


"Ku isar da zuwa na"


D'aya da ga cikinsu wacce take daf da k'ofar tace


"Yarima Aasim na buk'atar iso ranka shi dad'e"


Tafad'a cikin d'aga murya


Daga ciki aka basu izinin su bud'e k'ofar


Suka bud'e suna rusunawa


Gabanshi na fad'uwa ya shiga k'asaitaccen falon da akayi masa ado da zinarai kala-kala


Sarki Ramzad na zaune kan wata kujera me d'an fad'i ya jingina idanuwansa a lumshe


Shigowar Aasim d'inne yasa ya bud'e idanuwansa yana zubasu akansa


Cikin ladabi Aasim ya rusuna yana fad'in


"Barka me martaba,ina fatan kana cikin k'oshin lafiya"


Sarki Ramzad ya ce


"Lafiya,Ina fatan kaima haka?


Aasim yace


"Nima ina lafiya"


Sarki Ramzad ya gyad'a kai yana kauda kansa daga kallonsa


"Me ke tafe dakai?


Aasim ya d'an yi shuru sannan yace


"Inason magana dakai ne"


Jinjina kai sarki Ramzad yayi yana yima wazirin sa nuni da hannu alamar yafita ya basu guri



Cikin girmamawa wazirin ya rusuna tare da b'acewa


Sarki Ramzad ya maida hankalinsa kan Aasim yana cewa


"To ina jinka,fad'amin abunda kayanke ko sai munje fada tukunna?


Aasim ya sauke numfashi yana mik'e wa ya k'arasa gaban sa


Ya durk'usa tare da d'aura kansa a kan k'afafuwan mahaifinsa


Wasu hawaye masu zafi suka shiga gangarowa daga idanuwansa


Sarki Ramzad ya sauke numfashi tare dasa hannunsa yadafa bayan sa


Tabbas babu abunda yi keso sama da Aasim, yana matuƙar jinsa acikin zuciyarsa


Kuma babu abunda yafiso irin yaga Aasim cikin farin ciki


Amma dole ne ya dakatar dashi


Cikin kwantar da hankali yace


"Aasim, ka sani bawai na hanaka abunda kake so bane, dan jin daɗina


A'a, saboda adalci ne, domin babu wani rauhani daya isa yayi haka a ƙyalesa, Kaga ko bekamata na ƙyaleka ba dan kana ɗan dana haifa


Kasani da zarar akace babu ni, to kaine mai mulkin wannan masarautar


Ya kamata ka fahimce ni, nayi maka alƙawarin ko ƴar gidan wacece idan Kaga tayi maka zan auramaka in har a jinsin ka ce


Amma baze yuwu in barka ka cigaba da rayuwa da bil adama ba bazeyu ba"


Aasim ya ɗago kansa cikin muryarsa da ta dishe yace


"Abi,dan Allah kabarni nayi rayuwa tare da ita,ita kaɗai nike so banajin zan iya rayuwa da wata mace a duniya in ba ita ba........


" dakata!


Sarki ramzad ya katse sa, sannan ya cigaba da cewa


"nabika ta faɗa bakaji ba, na bika ta lallami nanma bakaji ba


To kasani bazan takura ka ba, tunda har ban isa dakai ba, nan da awa ɗaya zamu je fada, duk abunda kayanke kafaɗa acan"


Aasim ze kuma magana ya dakatar dashi ta hanyar ɗaga masa hannu


"bana son na kuma jin komai daga gareka, tashi ka bani wuri"


"Abi.....


Be ƙarasa ba, sarki ramzad yasa hannu ya ɓatar dashi



Ƙarfe takwas suka isa ƙaramin asibitin gwamnatin, sun tadda mutane da yawa akan Layin ganin likita


Hakan yasa suka zauna suna jiran layi yazo kansu


Kallo ɗaya zakama Rauda, kagano ramar da tayi acikin kwana ɗaya kacal


Kallon jama'ar dake wurin kawai take yi amma zahiri hankalinta baya gurin



Damuwarta ta kuma ƙaruwa yayin da taga har zuwa lokacin bata ji wani alamun Aasim ba,


Me ya faru dashi, bayan dawowarta? Shin ya amince ya rabu da itanne ko yaya?


Tambayar da tayi ma kanta kenan wacce bata da amsar ta


Maganar sa ce ta dawo mata


_"Rauda ina ƙaunarki, zan iya haƙura da komai inhar zan rayu dake"_



"baze amince ya rabu dani ba nasani"


Tafaɗa a fili batare da tasan maganar ta fito filin ba


Mama dake zaune kusa da ita ta kalleta cikin rashin fahimta tace


"mene?


Kallon maman tayi itama cikin rashin fahimtar


" waye baze amince ya rabu dake ba?


Mama ta jefo mata Tambayar tana kafeta da ido


Daburcewa Rauda tayi, dan ita bata san maganar da tayi a zuciya ta fito fili ba, ta rasa me zata ce


Numfashi mama ta sauke tana kaɗa kai, lokacin layi yazo kansu tamiƙe tayi gaba batare da ta kuma cewa komai ba


Rauda tabi bayan ta, gwajin farko da likita yayi ya gano BP ɗinta yayi ƙasa sosai


Kallon ta yayi yana cewa


"meke damunki? Da BP ɗinki yayi ƙasa haka?



Shuru Rauda tayi, likitan ya cigaba da cewa


" BP ɗinki yayi ƙasa sosai, shi yasa kike jin ciwon kai da kuma jiri, zan rubuta miki magunguna Asiya kisha, sannan kidena barin kina shiga cikin tunani Allah ya ƙara lafiya"


Mama ta amshi takaddar maganin suka, fito kowanne zuciyarsa babu daɗi


Napep suka hau ta kawo su gida suna gab da tsayawa taji maganar Aasim


_"kisameni a bayi yanzu"_



ko tsayawa bata bari mai nepep ɗin ya gama yi ba ta diro


Cikin faɗa mama tace


"wani irin ganganci ne wannan? miye kikema sauri da ba zaki tsaya yagama tsayawa ba?


Cikin sauri Rauda tace


" bayi nikeso na shiga"


guntun tsaki mama ta ja,tana zage Jakarta zata ba mai Napep ɗin kuɗi


itako Rauda ta ƙagara tagansa,juyawa tayi da sauri ta shige cikin gidan


Ko buta bata tsaya ɗauka ba ta shiga bayin



 A tsaye tagansa,rufe ƙofar bayin tayi da sauri tare da ƙarasawa inda yike


"Aasim, kana lafiya? Me ya faru na jika shuru? Ince dai ba wani abu a kayi maka ba?


Ta jero mai tambayoyin cikin zaƙuwa da son jin abunda ta tambaye sa


Be bata amsa ba, illa rungumeta da yayi,yana sauke wata nannauyar ajiyar zuciya


Ita ɗinma ajiyar zuciyar ta sauke, tana jin sonsa na bin duk wani sassa na jikin ta 


"kabani amsa mana Aasim"


Ɗagota yayi ya zuba ma fuskar ta ido amma kuma har lokacin beyi magana ba


Kawai yana hango yadda za ace yayi rayuwa babu ita ne


Girgiza kai yayi yana ƙara rungumeta sosai


"baze yuwu ba, baze yuwu ba"


Yafaɗa cikin tsananin damuwa


"miye baze yuwu ba, kayi min magana yadda zan fahimta dan Allah"


Kuma Ɗagota yayi yasa hannayensa duka biyu ya tallabo fuskarta yace


"Rauda inaso kiyimin alƙawarin cewa ba zaki taɓa rabuwa dani ba,har ƙarshen rayuwarki"


Kallon sa ta keyi sosai,


"Aasim kasani ai, bazan iya rabuwa dakai ba"


Girgiza kai yayi, yace


"nasani a yanzu, amma bansan meze iya faruwa nan gaba ba, shi yasa nikeso kiɗaukar min alƙawari da kanki da kuma bakinki"


Kaɗa kai tayi tare da cewa


"shi kenan nayi alƙawari bazan taɓa rabuwa da kai ba"


Gauron numfashi ya sauke yana gyaɗa kai


"nagode, wannan alƙawarin da kika ɗauka a yanzu ya kuma ƙarfafamin gwiwa,zanje in sanar dasu abunda na yanke"


"amma Aasim, bekamata.......


Katseta yayi


" kinga Rauda kada kice komai,na san watarana zamu dai-daita dasu, amma ke bazan iya jurar rashinki dai-dai da rana ɗaya ba"


Be jira jin mezata ce ya ɓace


Ajiyar zuciya ta sauke me nawi, tare da fitowa daga bayin, ɗaki ta shiga ta zauna akan gado

Maganar daya faɗa ce kawai take yi mata yawo a kunne


_"kinga Rauda kada kice komai nasan wata rana zamu dai-daita dasu amma ke bazan iya jurar rashinki dai dai da rana ɗaya ba"_


Sauke ajiyar zuciya tayi, ta janyo filo ta ɗaura kanta


Meyasa ze zaɓi rabuwa da ahalinsa saboda ita? Me yasa?


Tayi wa kanta tambayar


Lumshe idanuwan ta tayi, tana fatan ace har yanzu Mafarki take yi


Dan har lokacin ta kasa gasgata abunda ke faruwa


Ɓangaren Aasim kuwa, lokacin da ya koma masarauta saura ƴan mintoci a tafi fada


Yana zaune a ɗakinsa ya zuba tagumi, fulawar saƙo ta shigo ɗakin


Hannu yasa ya damƙe, saƙon ammi ne tana son ganin sa


Kamar baze je ba, sai kuma yaga rashin dacewar Hakan



Miƙewa yayi ya bayyana a ƙofar sashenta


"ku isar da zuwa na"


Yace ma kuyangin dake bakin ƙofar


Tun kan su kai gayin magana aka basu izinin buɗewa


Shiga yayi da sallama yana rusunawa


Ammi tayi ma jakadiyarta nuni data fita sannan ta dawo da kallon ta kansa


"Aasim ni kake wulaƙantawa ko? Ace tun jiya nikeson yin magana da kai amma ka sawa Ɓangaren ka takun kumi ko?


Ƙasa yayi da kansa

" kiyi haƙuri ammi, ba nayi Hakan danna ɓata miki bane, nayi ne dan nasamu natsuwa"


Ta jinjina kai tace


"yayi kyau, saura minti biyar taron fada, me ka yanke a zaɓin da aka baka?


Shuru yayi yana nazarin abunda zece


" tambayar ka nikeyi kayi min shuru"


Cikin fargaba yace


"ammi ki gafarceni, amma banajin zan iya haƙura da duka zaɓi biyu"


Kaɗa kai tayi cike da ɓacin rai da kuma tashin hankali


"kadai ce kawai ka zaɓe ta a kanmu, ka fifita bil adama akan iyayenka


Wai shin Aasim lafiyar ka ƙalau kuwa? Ko ko taɓin hankali ne yasa meka?


Taɗan numfasa sannan ta cigaba da cewa


" shin kana tunanin bil adama zata sama ma dauwamamman farin ciki ne?


Kayi babban kuskure Aasim, ko da yike laifi na ne da na goyama baya tun farko


Amma ina so ka sani nadama da danasani zasu biyo bayan ka inhar kazaɓi rayuwa da ita sannan........


Ƙarar sanar wa data Kaɗa ita ta dakatar da ita


Numfashi ta sauke tana ɗauke idanuwan ta a kansa


"lokaci yayi, zaɓi ya rage gareka, abu na ƙarshe da nike so  kasani shine. Idan har kazaɓi rayuwa da ita to kada ka ƙara zuwa inda nike,kaje inayi maka fatan alheri"


Tana gama faɗar haka ta ɓace daga gurin


Aasim numfashi ya sauke  Yana Miƙewa cike da tsananin ruɗani tabbas ya san ze aikata babban kuskure amma yana da yaƙinin iyayen sa ba zasu iya jurar rashin sa ba, nan da wani ɗan lokaci zasu nemesa kuma ma ya san da wuya Abi ya zartar da hukuncin kora a kansa ƙilan yafaɗi Hakan ne dan ya tsorata sa ya rabu da rauda


Ɓacewa yayi ya bayyana a fada, kamar kullum fadar cike take da manyan rauhanai


Suna zazzaune, Aasim na bayyana suka rusuna suna gaishe sa


Saida Aasim ɗin ya zauna a kujerar sa sannan suka ɗago


Shuru ya biyo baya na wasu mintoci, sannan sarki ramzad yayi gyaran murya


Hakan yasa fadar yin tsit


"Aasim, kafaɗa ma fada abunda ka yanke, shin ka haƙura zaka rabu da itanne? Ko ko kana kan bakanka na rayuwa da ita?


Aasim yayi shuru cike da tsananin fargaba


Sarki ramzad ya kuma mai-maita tambayar sa sannan ya ƙara da cewa


" bana buƙatar jin shurun ka, rayuwa da mu kazaɓa ko rayuwa da ita?


Aasim saukowa yayi daga kan kujerar ya durƙursa


" Abi ka gafarceni, har yanzu nakasa yanke komai, bana jin zan iya Haƙura da duka zaɓi ɓiyun da ka bani"


Sarki ramzad ya jinjina kai yace


"kenan har yanzu kana kan bakanka na ƙin rabuwa da ita?


Aasim ya ƙara dur ƙurshewa


" Abi dan Allah, kayi haƙuri kabarni na cigaba da rayuwa da ita, nayi maka alƙawari bazan sake aikata kuskure ba.......



Ɗaga mai hannu sarki ramzad yayi cike da ƙunar zuciya


" ya isa, ka riga da ka bani amsar tambaya ta, dan haka kada ka ƙara cewa komai"


Aasim ya runtse idanuwan sa yana ambaton sunan Allah


Sarki ramzad ya maida kallon sa ga rauhanan da suka yi jugum jugum saboda mamakin kafiyar da Aasim yayi


Yace

"tunda abunda ya zaɓa kenan, to bazan fasa hukuncin dana yanke ba, dan haka aje a shirya tauran zuwa jibi za a zartar da hukuncin"


Ɗaya daga cikin manyan fadawanne ya durƙusa cike da tashin hankali yace


"mai martaba, Aasim ɗan kane, be kamata ayi masa hukuncin kora ba, a sassauta masa ranka shidaɗe"


Shima wani ba faden zubewar yayi yana faɗin


"a sassauta masa ranka shidaɗe, a canza masa wannan hukuncin"


Sarki ramzad ya girgiza kai


"babu ruwan ku da matsayinsa, na riga da na yanke hukunci kuma wannan hukuncin shine adalci dan haka bana so na ƙara jin wani daga cikin ku ya furta komai, aje a shirya tauran kamar yadda na bada umarni"



Gabaɗaya jikin Aasim ya gama mutuwa, amma ya kasa ƙara furta komai


Hawaye kawai yikeyi, a haka aka watse daga fadar cike da juyayin al'amarin


Tunda Aasim ya koma Ɓangaren sa ya kwanta, yana ta tunanin bijire ma mahaifinsa da yayi


Tabbas yayi kuskure kuma be kyauta ma kansa ba


Buɗe ƙofar ɗakin aka yi aka shigo


Ya ɗago yana duban me shigowan, shaida ce


Ya tashi ya zauna yana kamo hannunta


"shahida, lafiya na ganki wani iri? Baki da lafiya ne?


Cikin gwaran cinta tace


" ba kai bane,kake ta yin kuka ɗazu"





ƴarfillo.

[7/12, 10:50 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*  

          *AASHIQUE🌹*


              🧞‍♂ 🧞‍♂

                  🧞‍♂


                 NA

HARIRA ALIYU _(y'arfillo)_ 🧕🏻




Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE 📕 1⃣7⃣  


  Wannan Page nakane......... Ina alfahari da kai a ko da yaushe


_9:15_🕒 PM

SAT, JUN 8



_Bissmillahir rahmaninr Rahim_


Murmushin ƙarfin hali yayi yana ɗaukan ta ya ɗaura ta ajikinsa


"dan kinga ina kuka, shi ya sa kika yi wani iri? Ba kyaso kiga ina kuka ne?


Shahida ta ɗaga kai alamar eh


Murmushi ya kuma yi yana tallabo kyakkyawar fuskarta


"shi kenan farin ciki na, daga yau bazan sake yin kuka ba, kinsan Abi ɗinki na sonki da yawa baya so ya ganki cikin damuwa"


Shahida tayi murmushi tana kwanta wa a jikin sa


"abbi,ina ammi na?


Aasim yayi shuru, yana kallon ta


Shahida ta ɗago kanta tana kallon sa tare da nanata tambayar da tayi


Yayi ƙoƙorin kauda damuwar dake fuskar sa yace


" kinaso kiganta ne?


Shahida ta ɗaga kai da sauri


Ya rungume ta ajikinsa yana sauke numfashi


" shi kenan, ki ƙara haƙuri kinji? Zaki ganta har sai kin gaji, yanzu faɗamin me kikaci yau?


Haka ya dinga lallaɓata har tayi barci, sannan ya kwantar da ita


Ya tsura mata ido yana jin tausayinta, kullum bata da maganar da ta wuce ina amminta?


Gashi da wuya ta rayu da ita yadda take so numfashi ya sauke tare da nuni da hannun sa


Wani ƙaton madubi ya bayyana, ya sake yin nuni da hannun sa


Sai ga Rauda ta bayyana a ciki, har lokacin tana kwance akan gado tana rawar sanyi


Ta duƙunƙune da bargo


"Rauda!


Ya kira sunan ta, ta buɗe idanuwan ta a hankali tana duba inda ta jiyo muryarsa amma bata ga kowa ba


Ya sauke ajiyar zuciya yana jin ƙaunarta na ƙara ratsasa


Hannu yasa ta cikin madubin ya ɗaura a wuyan ta yaji zafi rau


Ita ko zabura tayi dan bata ga kowa ba ta kuma ji antaɓata


Guntun murmushi yayi tare da faɗin


"matsoraci ya, nine"


Ta ƙara duba kan gadon bata ganshi ba, a hankali tace


"to kana ina? Ya aka yi bana ganin ka?


" ina masarauta, nima banajin daɗine bazan iya zuwa ba, kinsan duk abunda kikeji ajikinki inaji ajikina,ga kuma damuwar da nike ci"


Ta maida idanuwan ta ta Lumshe tare da cewa


"da gaske kana jin yadda nikeji a yanzu?


Ya ɗaga kai kamar tana ganin sa


" sosai habibty,zafin jikin ki yayi yawa,kinsha magani?


Ta ɗaga kai alamar eh


Ya jinjina kai

"sannu Allah ya baki lafiya,nan da ƙan-ƙanin lokaci zakiji sauƙi in sha Allahu"


"yanzu me kake yi? Ina so in ganka"


Ya gyara zamansa yana dai-dai ta saitin madubin


"to shi kenan rufe idanuwan ki ki natsu sosai"


Ta rufe kamar yadda yace, amma ba ta ganshi ba har zata buɗe, sai taga duhun dake cikin idanuwan ta ya fara yayewa


Ahankali Ahankali har duhun ya yaye gaba ɗaya ya bayyana


Guntun numfashi ta sauke tana cewa a zuciyar ta


"wannan kyawun naka dama ai sai jinsin aljanu"


"habibty"


Ya kira ta,ta amsa na'am


"kinyi mafarki ɗazu ko?


Ta ɗaga kai alamar eh


Ya jinjina kai


" to ba mafarki bane, abunda ya faru a fada ne kika gani"


Jikinta yayi sanyi

"amma Aasim Meyasa zaka yi haka, Hakan ba dede bane, Meyasa bazaka bi umarnin su ka rabu dani ba?


Ya sauke nannauyan numfashi, tare da dafa ƙirjinsa


" ba zaki gane yadda nike jinki a nan ɗina ba, wallahi Rauda bansan dalilin da yasa nike miki irin wannan son me zafi ba, jini keyi kamar idan na rasa ki zan iya rasa rayuwa ta, nima ba da son raina na bijire wa umarnin su ba, amma nasan ba zamu jima ba zamu dai-daita dasu"


Ajiyar zuciya ta sauke tana jinjina girman ƙaunar da yike mata


"amma ya maganar tsallake tauran da Naji anyi magana?


Ya sauke gauron numfashi yace


"zan tsallake jibi"


Jikinta ya ƙara yin sanyi


"Aasim dan Allah inda hanyar da zaka bi kabi, bana so kasha wahala"


Yayi murmushi yana sa hannu ta cikin madubin ya kama hannun ta tare da matsewa cikin nasa


"kar ki damu habibty, tabbas nasan tsallake tauran akwai wahala kuma nima hankalina na tashi idan na tuna azabar dake ciki


Amma kuma hankalina ya kan kwanta idan na tuna cewa zan samu ƴancin yin rayuwa dake bayan wannan wahalar, fatana dai kiriƙe min alƙawarin da kika ɗaukar min"


Haƙiƙa ta ƙara jin ya shiga zuciyar ta to me ma zesa ta karya alƙawarin data ɗaukar mai?


Ta tambayi zuciyar ta tana ganin babu, Guntun murmushi yayi tare da katse mata gajeren tunanin da ta tafi


"ki tuna ke mutum ce, kuma halin mutanen yanzu sai Allah, zasu ɗaukar ma alƙawari amma daga baya su nuna su basu ma san da maganar wani alƙawari ba, amma dai ke na yarda dake na kuma san ba zaki taɓa juyamin baya ba"



Hmmmm Ta sauke ajiyar zuciya kawai batare da ce komai ba


Murmushi ya kuma yi yanayi mata nuni da gefen sa


"baki ga wacce take kusa dani bane?


Sai lokacin ta lura da Shahida dake kwance gefen sa


Ta ƙura ma yarinyar ido tana jin ƙaunar ta acikin zuciyarta


" na tashe tane? Dan ɗazu ta gama tambaya ta ina amminta"


Girgiza kai Rauda tayi alamar a'a tana cigaba da kallon ta


"Meyasa?


Ya tambaya


"saboda kanta ze iya yin ciwo idan ka tashe ta"


Dariya yayi yana duban Shahida dake ta baccinta


"wa yace miki muma rauhanai irin ku ne mutane ragwaye,babu abunda kanta zeyi"


Ta gyaɗa kai tace


"shi kenan tashe ta"


Ya durƙuso sai tin fuskarta yana shafa fuskarta da ambaton sunan ta


Sai ko tabuɗe idon

"Shahida tashi ga amminki"


Tashi zaune Shahida tayi da sauri tana rarraba idanu


Yayi murmushi tare da nuna mata madubin


Haka suka cigaba da fira har saida barci ya fara ɗaukar Rauda sannan ya kaudar da madubin


Yana jin kamar bashi da wata damuwa, dan firar da yayi da ita yasa hankalinsa ya ɗan kwanta


Miƙewa yayi ya isa sashen ammi, sai dai kuyangin ƙin buɗe masa ƙofa suka yi dan sunce tace bata buƙatar ganawa da kowa


*Ranar tsallake tauran*


Duk wani masoyin Aasim da ke cikin masarauta hankalinsa a tashe yike, musamman ammi da gaba ɗaya ta fita hayyacinta


Haka Shima sarki ramzad dauriya kawai yikeyi yana nuna kamar abun Be dame shi ba, amma zahiri ƙasan zuciyarsa cike take da tashin hankali


Ammi kasa haƙuri tayi saura minti goma sha biyar ta shiga Ɓangaren sarki ramzad


Umarni ta bawa waziri da ya fita sannan ta ƙarasa gaban sa ta durƙusa


Cikin tashin hankali da tsananin damuwa ta fara magana


"na roƙeka ka janye wannan hukuncin akan ɗana, shi kaɗai gareni"


Sarki ramzad yayi mata wani kallo yace


"in janye hukunci fa kika ce? Kema kinsan abunda baze taɓa yuwu wa  ba kenan,akwai sauran minti sha biyar, kina iya zuwa kisa ɗanki ya bi abunda nace mai, dan shine kika isa dashi.


Amma ni baki isa kisani in canza abunda na yanke ba


Yadda bawa zeyi laifi in hukunta sa, haka zan hukunta abunda na haifa dan haka babu maganar janyewa"


Kuka ta fashe dashi

"amma kasan bayan Aasim bani da wani ɗa a duniya ko?


Gyara zama yayi cike da ƙaguwa da kukannata dan tashin hankalin da yike ciki kaɗai ya ishesa


"kinga Samira,bana buƙatar jin wannan kukan naki, ki tashi ki ɓace min da gani"


Miƙewa tayi cike da ɓacin rai


"na fahimci ni kaɗai nike son Aasim, kai wahalar da ze shiga ko ajikinka, to shi kenan zan tafi amma ka sani duk abunda ya sami ɗana da kai zanyi kuka"


Shima miƙewar yayi a fusace


"ki dakata min da waɗannan kalaman naki, duk ba laifinki bane da Ace tun farko baki basa goyon baya ba da munkawo wannan matakin?


Juya wa ammi tayi ta fice tana kuka bata zame a ko ina ba sai Ɓangaren Aasim


Yana tsaye jikin bango, ya Lumshe idanuwan sa da suka kaɗa sosai


Jin kukan ta yasa ya buɗe su da sauri


Ganin halin da ta shiga ya ƙara ɗaga mai hankali


Durƙushewa tayi a wurin tana cigaba dayin kukan


Ya ƙarasa gaban ta da sauri ze ɗaga ta


Dakatar dashi tayi ta hanyar ɗaga masa hannu


Ya durƙusa yana tambayar ta


"ammi me yafaru?


" idan kai baka son rayuwar ka ni ina so, ka duba wahalar da za kasha idan ka shiga tauran"


Ammi tafaɗa


Aasim ya sauke numfashi yana kama hannun ta


"ammi indai tsallake tauran ne,ki kwantar da hankalinki zan tsallake lafiya insha Allahu Babu abunda ze same ni"


Ta kallesa da jiƙaƙƙun idanunta


"Aasim......


Katseta yayi ta hanyar cewa


" ammi dan Allah kada ki ƙara cewa komai, ammi Rauda itace farin ciki na na kuma son kina son duk wani abu da ze faranta min


Kinsan kema bazan taɓa yin nisa dake ba, dan haka ki kwantar da hankalinki dan Allah, kada ki karya min gwiwa"


Miƙewa tayi tana jinjina kai


"shi kenan, tunda abunda ka zaɓa kenan, Allah ya baka sa'a"


Tana gama faɗar haka ta ɓace


Ajiyar zuciya Aasim ya sauke cike da tausayin mahaifiyar tasa


Sai dai baya jin ze fasa abunda yayi niyya


*filin tauran*


Wurin ya cika sosai da rauhanai, Aasim na tsaye daga gefe inda babban ba fade yike


"Yarima Aasim, shin da gaske ka amince da barin masarauta ta hanyar tsalle ke tauran??


Me faɗar hukunci ya tambaya


Aasim ya ɗaga kai

" na amince "


" ka tabbata?


Me faɗan hukunci ya kuma tambaya


Aasim ya jinjina kai

"na tabbata"


Sarki ramzad ya runtse idanuwan sa cike da tsananin takaici


Babban ba fade yayi nuni da tauran take ƙofarta ta buɗe


Kai tsaye Aasim ya dumfareta


Yana kallon yadda haya ƙin hucinta ke fita


Runtse idanuwan sa yayi yayin da ya isa ƙofar, ya ɗan tsaya ya karanto wasu abubuwa sannan ya kutsa kai


Yana shiga ƙofar ta rufe


Nan da nan garin yayi duhu, iska ta fara kaɗawa da ƙarfi


Wani baƙin hayaƙi ne ya dunƙule yayi tsawo baka iya ganin ƙarshensa a saman tauran ɗin


Wasu kibiyoyi masu haske suna shiga cikin hayaƙin


Zuwa can hayaƙin ya fitar da wata ƙara me razanar wa wanda ta sauka a jikin Aasim


Faɗuwa yayi a ƙasa saboda tsananin azaba,gashi ba a so a kwanta dan danne mutum take yi


Yun ƙurawa yayi ya tashi da ƙyar yana duban jikinsa daya fara huhhujewa


Haka ƙarar ta dinga sauka a jikinsa har sau arba'in da tara


Iya jigatuwa Aasim ya jigatu


Gaba ɗaya jikinsa ya huhhuje,lokacin da ƙofar ta buɗe faɗowa yayi


Mus'ab ne ya ruga da gudu ya taro sa yana Kiran sunansa cikin kaɗuwa da halin da ya shiga


Aasim be kuma sanin inda kansa yike ba, har saida yayi kwana biyu


Sannan ya farfaɗo, lokacin da ya farfaɗo mus'ab ya gani a kusa dashi


Mus'ab na ganin ya buɗe ido ya matso kusa dashi sosai yana faɗin


"sannu Aasim ka tashi? Yaya jikinnaka?


Aasim ya kaɗa mai kai kawai ba tare da yace komai ba


"sannu, ga magani ammi ta aiko maka, tace da ka farka kasha ze taimaka gurin komawar jikin ka dai-dai"


"Allah sarki ammi"

Aasim ya faɗa a cikin zuciyar sa, yunƙurawa yayi ze tashi


Mus'ab ya dakatar dashi


"kada ka tashi, baka ga halin da kake ciki bane?


Aasim ya girgiza kai


" mus'ab barni na tashi, taimaka min dai in jingina"


Mus'ab ya jinjina kai tare da tallafa masa ya jinginan


"amma ya kake ji yanzu? Da kwai wani guri da yike ma ciwo?


Mus'ab ya kuma tambayansa


Aasim yayi murmushin ƙarfin hali yana sake girgiza mai kai


" a'a abokina, ka kwantar da hankalinka babu inda ke min ciwo"


Ya faɗa da muryarsa da ta dashe sosai


Mus'ab ya jinjina kai,yana miƙa mai maganin da ke cikin wani kofin silver


"gashi kasha, me kake buƙatar kaci?


Jar abarba ko koriyarta?


Aasim ya girgiza kai yana kai kofin bakin sa


Sai da ya sha rabin maganin sannan ya ajiye yana kallon yana yin garin


" yau kwana nawa anan?


"kwanan ka biyu da yini"

Mus'ab ya bashi amsa


Ya ɗan zaro ido


"kwana biyu??


" eh kwana biyu me ya faru?


Mus'ab ya tambaya yana kafesa da ido


Cikin ƴar damuwa Aasim yace


"Rauda mana, Nasan tana cikin damuwa da jina shuru da tayi"


Mus'ab ya kauda kansa da ga kan Aasim yana mamakin irin ƙaunar da yike wa wannan bil'adamar


"to Meyasa zata damu, bayan ta juya ma tunani, ta san yanzu ka zama nata ita kaɗai"


Yana yin fuskar sa ya sauya


"Kaga mus'ab bana so kana faɗan magan ganu marasa daɗi a kanta"


Mus'ab yace


"to maida wuƙar angon bil'adama"


Guntun tsaki Aasim ya ja tare da yin nuni da hannun sa madubi ya bayyana


Ya kuma nuna sa da hannu, sai ga Rauda zaune ta zuba uban tagumi


Kallon mus'ab yayi yace


"ka nemomin ko ma miye ina jin yunwa"


Mus'ab yayi murmushi tare da faɗin


"kadai ce kana son ganawa da tauraruwar mata"


Ya faɗa yana Miƙewa


Aasim banza yayi dashi, sai da ya fice sannan yaja gajeren tsaki


Tare da fuskantar madubin sosai


" *habibty!*


Ya kira ta, ta ɗago kai da sauri tana kalle-kalle


" Aasim kana inane, me ya faru da kai najika shuru?


Ta tambaya a ƙagare


"ina nan lafiya habibty, ki kwantar da hankalinki"


Hmmmm ta sauke nannauyar ajiyar zuciya


"inaso inganka yanzu please"


Ya kalli jikinsa yadda ya huhhuje tare da sauke numfashi


"habibty kiyi haƙuri baza ki iya ganina ba"


"amma Meyasa? Ka san damuwar da na shiga kuwa? A sanadin na Dena jinka, na Dena ganin ka"


Ya kuma sauke numfashi yace


"da gaske habibty?


Ɗaga kai tayi da sauri


" da gaske Mana, nidai Ina son inganka yanzu dan allah"


"habibty bana so kiganni a yana yin da nike ciki ne, kiyi haƙuri a kwana biyu tukunna"


Ya faɗa


Ta jingina da kujerar da take kai tana sauke ajiyar zuciya


"ni ko a yaya kake Ina son ganin ka ahaka"


Yayi Guntun murmushi tare da cewa


"to bazan iya zuwa ba, sai dai in janyo ki ta cikin inda nike kallon ki, amma kafinnan ina mama?


" Mama bata nan"


Ya jinjina kai


"shi kenan"


Cikin minti biyu ta ganta a ɗakinsa


Sai dai yana yin data gansa ya yi mugun ɗaga mata hankali ta tsorata sosai


Gaba ɗaya tsigar jikin ta tashi take yi


Cikin kiɗima ta ja da baya tana kallon sa


A tsorace


"A...a..sim"


Ta Kira sunansa cikin rawar murya


Miƙewa yayi daƙyar ya ƙara sa inda take, dan har lokacin yana jin jiki


"kingani ba, shiyasa banso kika ganni ba"


Ya faɗa yayin da ya isa gabanta


Kallon sa kawai take yi cike da al'ajabi


"me yasa Meka haka? Ya aka yi kakoma haka?


Yayi murmushin ƙarfin hali yace


" tauran, ko kin manta?


Idanuwan ta ne suka cicciko da hawaye


"Aasim, saboda ni ka koma haka?


Ta faɗa hawayen da suka ciko idanuwan ta suna gangarowa


Murmushi ya kuma yi


"dan Allah kada kiyi kukannan, kinsan dai abunda bana so na gani a fuskar ki kenan ko?


Ji tayi zuciyar ta ta karye, Bata damu da yanayin data gansa ba ta rungume sa


Cikin shesshekar kuka tace


" duk a sanadina Aasim? Yanzu ahaka zaka cigaba da zama kenan?


Ajiyar zuciya ya sauke me nawi yana jin guguwar ƙaunarta na daɗa lulluɓesa


Ɗago ta yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta


"a'a habibty, nan da wani ɗan lokaci zan koma yadda nike, ki kwantar da hankalinki kinji?


Mai da kanta tayi kan ƙirjinsa tana cigaba da yin kukan


Ya Lumshe idanuwan sa yana jin kukan ta har cikin ransa


"ki yi shuru hakanan dan Allah, ko kinaso Nima in fara ne?


Girgiza kai tayi tana share fuskarta





Ƴarfillo.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE*


                  🧞‍♂🧞‍♂

                     🧞‍♂


                     NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 1⃣8⃣


_wannan Page nakune ƴan golden forum, haƙiƙa bana gajiya da yabonku domin kun can-canta Allah nike roƙo ya ƙara mana basira da fasaha ya kuma ƙara mana danƙon zumunci a wannan gida na mu me albarka amin_


_8:52_🕒 AM

SUN, JUN 9


_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Ya kuma yin murmushi ya na kama hannun ta zuwa bakin gadon suka zauna suna fuskantar juna


"to shi kenan ya isa haka,Nasha faɗa miki cewa idan kina kuka bakya yin kyau amma kinƙi yarda"


Ƙarasa goge ragowan hawayen tayi tana zuba masa fararen idanuwan ta


"ni dama bani da kyau, ko banyi kuka ba"


Ya ɗan fito da idanuwan sa waje tare da faɗin


"inji wa ya faɗa miki? Ai ke idan akwai abunda ya wuce kyakkyawa dashi ya kamata a kira ki, domin kyawun ki na daban ne"


Murmushi tayi tana girgiza kai


"zan iya yadda da Hakan amma a gurinka, dan nasan son da kake min ze iya sawa Kaga kyau na fiye da kima, amma ni nasan ni ba kyakkyawa bace"


Ya kama hannun ta yana matsewa cikin nasa


"da gaske habibty kina da kyau, bawai idona rufe wa yayi ba"


Ta kaɗa kai tace


"to shi kenan Naji, amma ya kake ji ajikinka nasan ko ina yima ciwo yike yi ko?


Ta Ƙarasa faɗa idanuwan ta na kuma yin rau-rau da ƙwalla


" ya ilah, habibty baki ji abunda nace miki ba ko? Kina so raina ya ɓaci ko?


Girgiza kai


Yace

"oook idan bakya so raina ya ɓaci ki maida hawayen nan kada ki bari su zubo"


Tayi ƙoƙorin maida hawayen amma ina kafin tayi wani yunƙuri su biyo kumatun ta


Hannayen sa yasa ya tare hawayen suka ɗiga akai


"bazan taɓa bari hawayenki su zuba a ƙasa ba, indai ina tare da ke Rauda, dan Allah ki bari"


Kwantawa tayi a jikinsa tana haɗiye wani ƙullutun damuwa da ya dunƙule mata maƙogoro


"ka barni inyi kukan dan Allah,in banyi ba ina jinsa yana dunƙule min a ƙirji"


Hmmmm ya sauke numfashi tare da cewa


"to wai kukan me kike yi ne? Faɗa min,indai kukan halin da nike ciki ne kibari, nan da wasu kwanaki zaki ga na koma dai-dai"


Dai de lokacin mus'ab ya shigo ɗakin ɗauke da tiren abinci


Ganin su a tare ya sa ya shigo da sallama


Aasim ne ya amsa yana tambayar har ya dawo?


Be bashi amsa ba illa ajiye tiren da yayi ya fice


Cike da takaicin ganin ta da yayi, dan shi gaba ɗaya haushinta yike ji


Dama ya san ze ganta Aida da ainihin suffarsa ze shiga ɗakin dan ya razana ta


Ƙwafa yayi tare da ɓacewa


Ita ko Rauda bayan fitar mus'ab ɗago wa tayi tana duban Aasim dan a kallon da mus'ab ya yi mata ta hango tsanarta ƙarara a tare dashi


"wanene wannan da ya shigo?


"abokina ne"


Ya bata amsa


Ta ɗanyi shuru sannan tace

"amma nayi masa wani laifi ne?


Girgiza kai yayi yana murmushi


" kinga ƙyalesa akwai abunda ya ɓata masa rai ne kawai"


Jinjina kai tayi tana duban tiren da ya ajiye


Wasu kalar abinci ta gani da bata san dasu ba a duniya


Abu ɗaya ta fahimta a tiren itace arbaba, kuma abarbar ma ja


Mamaki ne ya kamata dan ita a sanin ta abarba ba ja bace


Ganin yadda take kallon tiren yasa yace


"yadai, me kike mamaki ne?


"dama akwai abarba Jane?


" eh akwai amma anan duniyar mu"


Ta jinjina kai tana duban madubin


Mama ta gani ta dawo


Zaro ido tayi cikin fargaba


"mama ta dawo"


Ya kalli madubin yace


"to yanzu yaza ayi? Ta ina kike so in maida ki?


A gaggauce tace


" bayi, sai in yi kamar daga bayi nike"


Duba bayin yayi yaga akwai mutum a ciki


"da akwai mutum a bayin"


Dafa kai tayi cikin damuwa


"maidani uwar ɗaka kawai tunda tana falo"


Jinjina kai yayi ya maida ta yana cigaba da kallon madubin


Ita ko tana ganin ta a ɗaki ta miƙe ta yo falo


Ganin ta ba ƙaramin faɗar mama da gaba yayi ba


"ke ta ina kika ɓullo?


Rauda tayi saurin ɓoye fargaban da take ciki tace


" daga uwar ɗaka mana mama"


Mama mamakine ya bayyana a fuskarta


"bangane daga uwar ɗaka ba, ba yanzu na shiga na ajiye hijabi ba, ya aka yi ban ganki ba?


Tayi mata tambayar tana kafeta da idanu


Gaban Rauda ya cigaba da faɗuwa


"baki dai lura bane, ina kan gado,"


Ta faɗa cikin dake wa


Mama ta jinjina kai tace


"to gaskiya zanje adubamin hawan jinana ƙila ya hau da yawa da ni banga kowa ba a ɗaki wallahi"


Ajiyar zuciya Rauda ta sauke ganin mama ta yarda


Ƙarasowa kan kujera tayi ta zauna kusa da maman tana dariya


"mama Bawani hawan jini fa, tsufa ne kawai da kika fara"


Mama tace


"gidan ku, dudu nawa nike? Bari kiga kiyi aure kibani wuri yadda zan koma yarinya shataf, dan gayu zan dinga ci"


Dariya Rauda tayi sosai


"Haba ainasan babu wani gayu da zaki rinƙayi, ni da baba ze ji shawara ta ma da ya ƙaro muku ƴar budurwa"


Mama kai mata duka tayi


Ta goce tana cigaba da yin dariyar


Bayan sati biyu,hankalin Rauda ya kwanta sosai bata da wata damuwa musamman data ga Aasim ya warware ya koma yadda yike


Uwa uba ga soyayyar da suke yi me zafi, wacce tasa ko da yaushe bata rabo da tunanin sa


Kamar ko wani dare bayan mama tayi bacci


Rauda na zaune a falo tana guga


Maganar sa taji


"habibty ina son ganin ki"


Ɗan ɗagowa tayi tace


"kabari in gama guga please....


Kafin ta Ƙarasa maganar taji wata iska me daɗi ta lulluɓeta tana janta


Lumshe ido tayi tana faɗin


"oh Aasim kasan fa Bama samun wuta sosai yanzu waze Ƙarasa min gugar"


Jin iskar ta lafa yasa ta buɗe idon, a kwance tagansa gefen gado


Kanne mata ido ɗaya yayi yana faɗin


"ba dai guga bace? To juya kigani"


Juyawan ko tayi tana duban madubin


Abun mamaki ion ɗin da kansa taga yana yin gugan


Ta zaro ido cike da mamaki


Dariya yayi yana janyo ta ta faɗa jikin sa


"miye na wani zare idanu, abunda yafi haka ma zaki gani, zaki wani ce in bari ki gama guga, kinsan yadda na matsu in ganki kuwa?


Ta marai-raice fuska tace


" to ni yanzu me zan maka?


Murgina wa yayi da ita, ya zama itace a kwancen


"me ma zaki min kike tambaya na?


" to ni bacci nike son nayi"


Ta faɗa a shagwaɓe


Yadda tayi maganar ya ƙara rikita sa


Ya tsa yasa yana zagaye gefen fuskarta


"bacci? To kiyi mana aiban hanaki ba"


Ji tayi wani abu ya fara taso mata ta Lumshe idanuwan ta daga kallon sa da take yi


Shiko sun kuyowa yayi daf da fuskarta yana kallon ɗan ƙaramin bakin ta


Yatsan sa ya dawo dashi yana zagaye tausasan lips ɗinta wanda Hakan ke ƙara sa tana shiga wani yanayi


Kissing ɗinta ya fara Ahankali yana bin duk wani sassan jikin ta


Gaba ɗaya jin ta take yi a wata duniya da bazata iya fasalta irin ta ba


Haka ya cigaba da sarrafa ta bata masan sanda ta shiga duniyar bacci ba



Shi ko Hakan ya bashi damar aiwata muradin zuciyar sa


Sai wuraren ƙarfe uku ta farka, yana kwance kusa da ita ya zuba mata ido


"habibty!


Ya faɗa cikin shauƙin ƙaunarta


Ɗago da kanta tayi tana kallon sa ba tare da ta amsa ba


"habibty ina sonki ina ƙaunar ki"


Murmushi tayi idanuwan su na cigaba da sarƙewa da juna


"Nima Ina son ka Aasim"


Ya rungume ta tsam a jikinsa


"ki faɗi,duk abunda kike so, nayi miki alƙawarin zanyi miki shi a take batare da ɓata loka ci ba"


Murmushi ta kuma yi


"babu"


Ya ɗago ta yana kuma kallon fuskarta


"mu cigaba da rayuwa a haka dan Allah habibty"


Gyaɗa mai kai tayi


"shi kenan"


Washegari


Bayan ta fito daga wanka tana zaune tana shafa


Bayan tagama ta ɗauko doguwar riga ta saka tana zage zip ɗin


Ji tayi zip ɗin ya kuma zagewa, ta kuma zagewa still ya kuma


Juya wa tayi dan tasan shine


Aiko shi ɗin ta gani ya harɗe hannayesa yana murmushi


Ta maida mai martanin murmushin tana cewa


"nifa bana son tsokana"


Ya matso gab da ita yana mai-maita abunda tafaɗa


"nifa bana son tsokana"


Dariya tayi dan yadda yayi maganar shi a dole ya kwai-kwaye ta


"ka ganka ko? To me ya faru na ganka da rana haka"


Wani zobe yaciro yana nuna mata


"wallahi kin gansa nan, nazo wucewa ta wata kasuwa nagansa naga ze yi miki kyau a hannun ki shine na siyo miki"


Murmushi tayi tana duba siririn zoben zinarin


"wow gaskiya yayi kyau kamar kasan kuwa ina son siririn zobe"


Ya kama yatsanta yana zura mata zoben


"yaza'ai bazan san abunda matata take so ba?


Har lokacin da ragowar murmushi a fuskar ta


"na gode, abban Shahida"


"shhhhh"


Yayi yana ɗaura Yatsan sa akan bakin ta


"kar in ƙara jin kalmar godiya abakinki, dan babu ita a tsakanin mu"


Sallamar da aka yi a falon ce tasa ya sumbace ta a goshi


"kije kunyi baƙuwa,sai mun haɗu anjima"


Gyaɗa kai tayi tana murmushi


Ya ɓace ƙara zage zip ɗin tayi ta fito falon


Anty ummi ce


"zama tayi kan kujera cike da nisha ɗi tana duban Anty ummin


"kune da rana haka?


Anty ummi kallon ta tayi tace


" eh me ya faru a gidan ne?


Cikin rashin fahimta Rauda tace


"bangane ba"


"gani nayi kina ta farin ciki"


Anty ummi ta faɗa


Dariya Rauda tayi tana girgiza kai


"to babu abunda ya faru kinsan wata ran zakiji ki cikin annashuwa"


Anty ummi ta jinjina kai tana kallon zoben hannun ta


"wannan zoben fa, kamar zinari, ina kika samoshi?


Rauda ta girgiza kai tace


" a'a ba zinari bane, ɓarawon zinari ne, a makarantar mu wata take saida wa dubu ɗaya to tunda na siya ma ban taɓa sawa ba sai yau"


Anty ummi ta jinjina kai


"aiko kamar zinari wallahi,zan baki kuɗi idan kun koma

Kisiyomin, ina mama?


" ta shiga gidan maman murja anyi haihuwa"


Anty ummi ta miƙe


"dama hanif zanɗauko a makaranta nace bari in biyo, kince zakizo har yanzu baki zo ba"


Rauda ta miƙe itama tana yafa ɗan kwalin ta dan ta rakata


"kinsan banji daɗi ba kwana biyu amma zan zo jibi in Allah ya kai mu"


Anty ummi tace

"shi kenan in maman ta dawo ki gaishe ta"


Washe gari suna zaune a tsakar gida gabaɗayan su suna gyara masarar da baba ya kawo


Suna cikin gyaran aisha ta shigo yarinyar umma da ƙaramin akwati a hannun ta idanuwan nan nata sun yi jawur da alamu kuka taci


Tana shigowa umma tace


"me zan gani Aisha, yau ma ya jin kikayo"


Aisha ta tsugunna tana fashewa da kuka


"umma ni wallahi na gaji,Ace kullum nasiru sai yayi waya da ƴammata"


Umma maka ta kai mata cike da harzuƙa


"ubanki kenan, nace ubanki kenan Aisha, dan yayi waya da ƴammata shine abun yaji?


Mazan yanzu ba haƙuri ake yi da su ba, ina farin ciki hankalina ya kwanta na gama aurar da ku shine kike kike so ki tattago naki auran?


Ga wasu nan auran ma ya gagare su suna neman mazan ruwa a jallo basu samu ba"


Inna ta jinjina kai tace


"ƙwarai kuwa jummai, a zamaninnan in ka samu ka aurar da ƴaƴanka ai ka gama hajji da ummara"


Umma tace


"faɗa mata dai, wata ma sau biyu ana fasa auran ta kuma babu wanda ya ƙara shinshinar ta, sai ke da Allah ya tarfa ma garin ki nono ya rufa miki asiri kikayi auran zaki rinƙayin yaji


Maza tashi ki ɓace min da gani in ba kinaso in rufe ki da duka ba, sakarya kawai"


Mama Miƙewa tayi ta shige ɗaki dan tasan da ita suke yada haibaicin


Rauda ma Miƙewa tayi tabi bayan maman


A zaune tasa meta ta zuba uban ta gumi


Ta zauna gefen ta tace


"mama dan Allah kada abunda suka faɗa ya ɓata miki rai"


Mama ta sauke ajiyar zuciya tana jingina da kujerar


"dole ya dameni Rauda, kullum fatana Allah ya kawo miki miji kiyi aure amma har yanzu shuru, yanzu ankai matakin da babu me sallama wa yace yana kiranki


Addu'a nike, maganin nike nemar miki amma shuru"


Ta Ƙarasa maganar cike da tsananin damuwa


Jikin Rauda yayi sanyi sosai, tausayin mama take ji, anya wannan rayuwar da tekeyi a ɓoye da Aasim tayi wa kanta da mama adalci kuwa?


Ya zamar mata dole ta yi masa magana dan ta samu mafita


Dan tasan yana da hannu wajen ɗaukewar mane manta


Guntun numfashi ta sauke

Tace


"komai lokaci ne mama, kuma komai yayi farko yana da ƙarshe ki kwantar da hankalinki ai da banyi auran ba ba a zaune nike ba, karatu nikeyi"


Mama ta girgiza kai

"aure ai mutuncin ƴa mace ne, hankali na zefi kwanciya idan Naga kinyi auran kina cigaba da karatun"


Rauda tayi shuru kawai tana ƙara yin nazari


Allah Allah take yi dare yayi


A gaggauce tagama ayyukan da zata taya mama dan ranar itace da girki


Ƙarfe goma mama tayi mata sallama taja mata ƙofar da yike hadari ya taso sosai


Tana fita Aasim na bayyana a ɗakin


Cikin sauri Rauda tace


"yauwa dama yanzu nike shirin kiranka"


Kama hannun ta yayi yana ƙoƙarin janyo ta jikinsa


Ta dakatar dashi


"a'a Aasim, magana nike so muyi dan Allah"


Ganin yana yin fuskarta yasa ya gane da gaske take yi


Hakan yasa ya zauna a kan kujera itama ta zauna


"maganar me kike so muyi habibty?


Ta gyara zaman ta tana fuskantar sa


" ina so muyi wata muhimmi yar magana, kuma dan Allah inaso ka fahimce ni, ka kuma yarda da abunda zan faɗa ma"


Ya kaɗa kai

"to insha Allah ina jinki"


Ta sauke numfashi sannan ta fara cewa


"a gaskiya babu abunda nike so sama da kwanciyar hankalin mama, kuma hankalin ta baze kwanta ba har sai taga nayi aure sannan...........


Katseta yayi

" sannan me? Faɗamin kawai me kike so kice"


Ta kuma sauke numfashi a karo na biyu


"ina so kadena korar min mane mana kabar su su cigaba da zuwa....


" sannan me?


Ya tambaya cikin tsare gida da ɗaure fuska


"sannan kabarni inyi aure........


" dakata dakata Rauda, kin san me kike cewa kuwa?



Ya faɗa cikin ɓacin rai


Jinjina kai tayi tace


"na sani Aasim, kuma kai ma ka san baze yuwu  In cigaba da zama a haka ba, idan ni nasan ina tare da kai ai mutane basu sani ba.......


"kinga kima dakatar da waɗannan shirmamman maganganun naki"


Yafa ɗa yana kauda kansa


"magan ganun nawa ne shirme?


Ya jinjina kai yace


"eh shirmammu ne mana, ina so ki sani bazan taɓa barin wani ɗa namiji ya raɓeki ba, dan haka ki ma cire maganar aure a rayuwarki duk wani abun da ɗan adam zeyi miki nayi alƙawarin zanyi miki ninkin shi"


Kallon sa kawai take yi yadda ya tamke fuska kamar be taɓa dariya ba


Durƙusawa tayi a gaban sa idanuwan ta suka cicciko


"Aasim dan Allah na   roƙeka,Hakan shine kwanciyar hankalin mama, ka riga da ka san a yanzu babu wanda nike so sama da kai, kuma bawai ina nufin kabar ni in yi aure dan inyi nisa da kai bane, a'a...


"kinga Rauda idan kinji abunda nafaɗamiki to, idan kuma baki ji ba bari in sake nanata miki


Bazan taɓa barin wani ɗa namiji ya raɓeki ba"


Runtse idanuwan ta tayi wasu siraran hawaye na gangarowa


"kenan haka kake so incigaba da rayuwa?


Ɓacewa yayi ransa a ɓace batare da ya ƙara ce mata komai ba


Ita ko Rauda fashewa tayi da kuka cike da tsananin damuwa


Haka ta kwana bata runtsa ba


Sai da suka yi kwana biyu be kuma zuwa inda take ba,bata damu ba dan haushin sa take ji sosai dan ta fahimci ba zasu daidaita dashi ba dan baze yuwu ta cigaba da rayuwa mutane suna yada Mata habai ci ba


Rana na ukun tana tsaye a ɗaki tana ninke kayan da ta kwaso akan igiya


Ɗagowar da zata yi suka haɗa ido


Maida kanta tayi kamar Bata gansa ba cigaba dayin abunda take yi


Hakan ya sosa masa rai amma sai ya danne ya ƙara so tare da rungume ta ta baya


"habibty fushi kike yi dani?


Janye jikin ta tayi tana kallon sa


" dan Allah ka rabu dani,ka ƙyaleni"


Ta faɗa cikin dakiya


Ajiyar zuciya ya sauke yana matsowa gab da ita


"shi kenan Naji nayi miki laifi, amma kiyi haƙuri"



"nayi"

Tafaɗa tana cigaba da ninke kayan


Cikin damuwa yace

"miye haka Rauda,? Nine fa?


Ta ɗaga ta watsa mai fararen idanuwan ta


"to inkaine sai mene Aasim? Me kake so ince maka? Tunda ka kasa fahimtata"


Ya girgiza kai yace


"ba haka bane, dan Allah ki saurareni, ranar ma raina ne ya ɓaci, kinsan ina ƙaunar ki, kishin ki da sonki ne suka hanani fahimtar ki a ranar"


Ta ajiye kayan tana faɗin


"shi kenan ina sauraron ka"


"amma ai ba atsaye zamuyi maganar ba ko?


Ta zauna bakin gado batare da ta sake magana ba


Ajiyar zuciya ya sauke yana zauna wa a kusa da ita


"to dan Allah ki saki ranki kinji? Ba na son ganin ki a yana yin ɓacin rai"


Ta sassauta ɗaurin da tayi ma fuskarta tana duban sa kawai


Gauron numfashi ya sauke yana kama hannun ta


"kinsan irin son da nike miki ba zaki taɓa neman wani abu agurina ban miki ba, amma gaskiya kamar yadda na faɗa miki bazan iya barin wani ɗa namiji ya raɓeki ba sai dai ina da wata mafita guda ɗaya"


Ta kallesa sosai


"mafita? To wace kalar mafita? Faɗi inji"


Ya gyara zama yana kuma fuskantar ta


"kinga ƙarfin da nike dashi idan na bayyana ga mutane da yawa ba zasu iya ganina ba


Ƙarfin da nike dashi mutum biyar ne zasu iya ganina,


To akwai wani kogo da ake zuwa a ƙasar Iraq inda wani tsohon rauhani yike


Idan rauhan yayi training awurinsa na tsawon watanni ƙarfin sa ze ƙaru ta yadda ze iya bayyana a bainar mutane da yawa


Kinga idan nayi sai inbayyana a gidan ku a matsayin mutum in kuma auranki kinga shi kenan baki da wata damuwa"


Kallon sa tayi da mamaki


"da gaske ana yin Hakan?


Ya jin jina kai


" da gaske, dan haka ina ganin jibi zantafi"


Jinjina kai tayi da sauri dan dama burinta be wuce ta rayu dashi ba, kuma tunda ga hanyar da babu wanda ze gane ai shi kenan


"dama ka san da wannan hanyar shine bakayi ba tun tuni?


" yanzu ai zanyi dole na"


Ya faɗa


Kama ɗayan hannun sa tayi cike farin ciki


"dan Allah ka tafi yanzu, wallahi ina son ka da kai kaɗai nike so nayi rayuwa a yanzu"


Murmushi yayi


"kwantar da hankalinki, jibi in Allah ya kai mu zan tafi,sai dai innata fi babu wata hanya da zata sa damu har sai na gama watannin da zanyi"


Kaɗa kai tayi tace

"to miye abun damuwa? In ka dawo ba shi kenan ba"


Ya jinjina kai


"shi kenan, yanzu hankalinki ya kwanta ko?


Ta ɗaga kai tana murmushi


Bayan kwana biyu suna tsaye suna sallama dan ranar ze tafi


" habibty dan Allah ki kula da kanki,na ajiye miki kuɗi a cikin akwatinki duk abunda zaki buƙata kiyi dasu,inda zan shiga bani da damar koda ganin ki ta madubi dan haka ki kula min da kanki"


Jinjina kai tayi tana ɗan murmushi


"baka da matsala, zan kiyaye insha Allah, kaima ka kula da kanka sosai"


Ya sumbace ta a goshi


"shi kenan ni zan wuce"


"Allah ya kiyaye hanya ta faɗa"


Ya ɓace, zama tayi zuciyar ta cike da kewarsa da ƙaunar ta


Bayan sati ɗaya lokacin komawarta makaranta yayi


Dan haka ta gama shirin ta tsaf, motar rana zata bi


Mama nasiha ta mata sosai akan ta cigaba da tsare mutuncin ta


Baba da kanshi ya kai ta tasha


Sai da yaga motar su ta tashi sannan ya tafi


Ita ko Rauda kallon gefen hanya take tayi zuciyar ta cike da tunanin Aasim


Ƙarfe biyar ta sauka a bakin makaranta


Inda Salma ke tsaye tana jiran ta dan ta riga ta dawowa


Tana ganin ta suka rungume juna cike da kewar juna, salmar ce ta ɗauki akwatinta tana tambayar ya hanya


"lafiya lau"


Ta bata amsa suna tsallakawa


Wata rantsattsiyar mota ce ta shanyo kwana a guje


Salma ta Ƙarasa tsallakawa da gudu yayin da takalmin Rauda ya turguɗe


Kafin tayi wani yunƙuri tuni motar ta bugeta


Faɗuwa tayi tana ambaton sunan Allah tare da tashi da sauri tana kallon motar


Ganin motar ta tsaya yasa ta duba ƙafarta inda take jin zafi da alamu anan ne taji ciwon


Wanda yike tuƙa motar ya fito hankalinsa a tashe


Fari ne tas, dogo kyakkyawan gaske


Da hanzari ya isa gabanta


Ganin ta durƙusa tana duba ƙafarta yasa shima ya durƙusa yana faɗin


"sannu baiwar Allah, kinji ciwo haka? Tashi mu tafi asibiti wallahi bada niyya ta na buge ki ba, saurin da nike yi ne"


Ƙirjinta ne ya fara bugawa yayin da taji tausassar muryarsa


"dan Allah tashi inkaiki asibiti, kinga jini na zuba a ƙafarki"


Gabanta ne ya sake faɗuwa,ƙarfin hali ɗagowa tayi ta kallesa suka haɗa ido


Atare gabansu yayi mummunan faɗuwa


Kallon-kallo kawai suke yi


Shine ya katse ɗauke wutar da suka yi ta hanyar kiran sunan ta


*"Rauda"*


Ƙirjinta ne yaci gaba da bugawa, zuciyar ta ta fara harbawa da sauri


Ganin wanda bata taɓa sa ran zata gansa a duniya ba


Har zata amsa sai magan-ganunsa na baya suka dawo mata


_"kada ki ƙara kirana ko nemana, kisa a ranki cewa baki taɓa sanina ba a duniya, ki gogeni daga rayuwarki"_


Nan da nan ɓacin ran shekarun da suka wuce ya dawo mata sabo fil


Miƙewa tayi tana jin raɗaɗin dake ƙafarta ya tafi sakamakon tuno wa da maganar sa da tayi


shi ko jikinsa na rawa ya kuma kiran sunan ta


"Rauda ba zaki amsa min ba?


Wani kallo tamasa tare da haɗe fuskarta


"ba sunana Rauda ba"


Tana gama faɗar haka tayi gaba


Yayi saurin shan gabanta


"Haba Rauda, nasan kece ki tsaya inkai ki asibiti"


Ranta ya soma ɓaci


"nace maka ni ba sunana Rauda ba, ka tafi ka ƙyaleni"





Ƴarfillo.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*

          *AASHIQUE🌹*


                 🧞‍♂🧞‍♂

                    🧞‍♂

                    NA

HARIRA ALIYU _(y'arfillo)_ 🧕🏻



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 1⃣9⃣


_Wannan Page nakune masoya ƴarfillo, haƙiƙa ina jin daɗin yadda kuke yaba labarina a koda yaushe, nayi kuma matuƙar mamakin yadda labarina ya samu karɓuwa a gurinku, babu abunda zance muku face godiya Allah ya bar zumunci_


*_Aishatu babayo_*

_ina jinjina miki a koda yaushe,ina kuma godiya da kulawar ki gareni_


*_fatan alkhairi_*


_ga babbar aminiyata da babu kamar ta, *Aisha a Ibrahim* marubuci yar hilwana_



_11:34_🕒AM

TUE,JUN 11


_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Ze kuma yin magana ta dakatar dashi ta hanyar ɗaga masa hannu


"malan ka bani hanya in wuce? Taimakon kai ni asibiti ne bana so ko ana yima mutum dole ne?


Mama kine ya kama sa sosai kallon ta kawai yike yi


" wai shin Rauda ko baki gane ni bane? Umar ne fa"


"Umar?


Ta mai-maita sunan tana kaɗa kai


"Kaga Malan ni bansan ka ba"


Kafin ya kuma wata magana tuni ta ratse ta gefen sa ta wuce


Binta yayi da kallo yana tambayar kansa to wai ko ba ita bace ne? Ko gizo idanuwan sa suke masa


Binta Salma tayi da sauri tana kiran sunan ta


"Rauda kinfaji ciwo sosai, ya kamata ki tsaya muje asibiti a dubaki"


Rauda ko waigo wa bata yi ba taci gaba da tafiya


Kira ta da Rauda da Salma tayi ya tabbatar mishi da itace


Har ze bisu cikin makaranta


Wayar sa ta fara ƙara


Ya zaro ta daga aljihu, ganin me kiran yasa yayi saurin ɗagawa tare da karawa a kunnen sa


"doctor Umar mutanen nanfa suna cikin wani hali suna gab da rasa rayukansu dan Allah ka hanzarta"


Be ce komai ba ya kashe wayar yana ƙara kallon get ɗin makarantar ganin sun shige yasa ya koma motar sa


Tare da tada wa ya jata a guje


Amma gaba ɗaya hankalinsa ya rabu biyu


Ita ko Rauda ba ta tsaya ba har sai da ta isa ɗakin su tana shiga ta wurgar da ƙaramar jakar dake hannun ta tare da zubewa a ƙasa tana mai da numfashi sama-sama


Gaba ɗaya ganin sa ya hautsina mata hankali gami da daburta zuciyar ta


Salma ce ta shigo ɗakin ganin halin da take ciki yasa tace


"Rauda kita shi mutafi asibiti"


Rauda ta girgiza kai alamar a'a


Salma ta durƙusa tana duba ƙafar Raudan da har lokacin take zubar da jini


"bangane a'a ba, kina ganin yadda jini ke zuba, ga kuma numfashin da kike yi sama-sama"


Rauda ta kuma girgiza kai a karo na biyu


"nace miki baza ni ba, ki ƙyaleni dan Allah"

Salma ta kaɗa kai tana miƙewa


"aiko bazan ƙyale ki ba, tunda ba zaki tashi mutafi asibitin ba bari na kira sadiya ƴar medicine tazo ta dubaki"


Rauda jingina tayi da bango tana ƙara sauke numfashi


Ƙarfe shida da kwata ya isa Abuja


A harabar tamfatsetsen asibitin yayi parking


A gaggauce ya shiga office ɗinsa ya sanya kayan aiki


Tare da fitowa inda sauran likitocin suke


Basu ɓata lokaci ba suka emergency room inda Majin yatan suke



Basu suka fito ba sai. Sai Ƙarfe tara


Office ɗinsa ya koma ya yi wanka sannan ya zauna akan kujera tare da miƙar da ƙafafunsa ya jingina su da zagayayyen tebur ɗin dake gabansa


Jingina yayi da kujerar zuciyarsa na hango masa fuskarta


Maganar ta ce kawai take yi masa yawo a kunne


_"Kaga Malan ni ban san ka ba"_


Ya Lumshe idanuwan sa yana tambayar zuciyar sa


"anya kuwa Raudar da ya sani ce kuwa?


Dan ya tabbata inda itace bazata yi masa haka ba


Zuciyar sa ta kuma hasko Masa ita a lokacin da ta ɗago fareren idanuwan ta ta kallesa


Mamaki haɗe da fargaba da kuma tashin hankali ya gani a cikin idanuwan ta


To idan ba ita bace me yasa zata yi masa wannan kallon?


Ya kuma tambayar kansa


Numfashi ya sauke yana Miƙewa tare da ɗaukar makullin motar sa


"ko ma dai yaya ne gobe zankoma katsinan in tabbatar"


Ya faɗa yana ficewa daga cikin office ɗin


Washegari


Rauda na zaune riƙe da plate ɗin abinci tana jujjuya cokalin dake hannun ta


Dan gaba ɗaya ba ta jin cin abincin hakanan take tsintar kanta da faɗuwar gaba a duk sanda ta tuna sa


_"kada ki ƙara kirana ko nemana, kisa a ranki cewa baki taɓa sanina ba a duniya, ki goge ni daga rayuwarki"_


Maganar sa ta kuma yi mata yawo a kunne


Aje plate ɗin tayi tana jijjiga kanta


"meyasa Nike yin tunaninsa? Meyasa?


Ta faɗa cikin yana yin damuwa


Salma kallon ta tayi sosai tace


"Rauda, wai me ke damunki ne wai?


Ta kuma sauke numfashi a karo na biyu tana kallon salma da idanuwan ta da suka canza launi


"babu komai"


Salma ta girgiza kai tace


"a'a da akwai komi fa, tun jiya yana yinki ya canza, wai shin ma waye ne wannan na jiyan da ya bugeki"


 ta zame daga gefen gadon tana Lumshe ido


"waye kuwa Salma, a gabanki fa na fara ganin sa"


"to amma Meyasa tunda kika gansa yana yin ki ya canza?


Ada nayi tunanin ciwon da kika jini, sai da Naga ana wanke miki ciwon naga ko a jikin ki hankalinki da tunanin ki ma basa gurin gabaɗaya


Hakan ya tabbatar min da ba ciwon da kika ji bane"


Ta buɗe idanuwan ta da suka kaɗa suka yi ja saboda ɓacin ran da ta shiga sakamakon zafafan magan ganunsa da suka kasa dena yi mata yawo a kunne


"Salma dan Allah bana son Magana a halin yanzu"


Salma ta tana kaɗa tace 


"shikenan"


Wunin ranar haka Rauda tayi shi cikin rashin wal-wala


Shi ma Umar haka ta kasance gareshi ko abincin kirki ya kasa ci Allah Allah yike gari ya waye ya tafi Katsina


Washegari da wuri ya tashi ya shirya ya ɗauki jakar sa wacce ya sa kaya kala biyu a ciki ya fito falo


A kan dining ya tadda Anty kaltum tana haɗa abun kari


Ya gaishe ta ta amsa tana kallon jakar hannun sa


"yadai na ganka da jaka"


Ya gyara ratayar da yayi wa jakar yana cewa


"tafiya zanyi zuwa Katsina"


"Katsina kuma? Ince shekaran jiya ka dawo daga katsinar? Me zaka je kayi kuma?


Ta tambaya tana kallon sa


" wani abu ne ze kaini, amma bazan wuce kwana biyu ba zan dawo insha allah"


Sanin sa baya son yawan tambaya yasa ta jinjina kai


"shikenan Allah ya tsare"


"amin"

 Ya faɗa tare da juyawa ya nufi hanyar fita


Har ya kusa kaiwa ƙofa ta dakatar dashi ta hanyar cewa


"to bazaka tsaya ka karya ba?


Ya girgiza kai yana cigaba da tafiya


" no Anty bana jin yunwa"


Bata ƙara cemai komai ba ta bisa da kallo


A harabar gidan ya buɗe haɗaɗɗiyar motar sa ya shiga ya tada


Me gadi ya buɗe masa get yana gaishe sa


Ɗaga masa hannu kawai yayi ya figi motar a guje


Ɓangaren Rauda kuwa ta samu ɗan sassauci dan har ta shirya dan zuwa duba sakamakon jarabawar su da ya fito a ranar


Tare da Salma suka fito suna tafiya suna fira jefi-jefi har suka isa wurin


Kamar yadda wurin ya saba da cika maƙil da ɗalubai a duk sanda sakamakon ya fito


Haka yauma, dan ko wani ɗalubi burinsa yaga abunda yaci


Rauda tsayawa tayi daga baya kaɗan tana na zartar yana yin wurin yayin da Salma ta kutsa cikin ɗaluban


Rauda na tsaye har Salma ta dubo nata ta fito tana mai da numfashi


Ganin Raudar a tsaye a inda ta barta yasa tace


"ha'a baki duba ba?


Rauda ta ɗaga kai

" kema kinsan bazan iya shiga cikin dandazo nan ba, ya kiga na ki?



Salma tace

"ba laifi, bari na dubo miki"


Ta faɗa tana juyawa ta koma cikin dandazon


Daga ƙasa ta fara duba na Rauda kamar ko da yaushe


Sai dai ba ta gani ba, Hakan yasa taɗaga kai sama tana dubawa


Numban jarabawar Rauda ta fara gani a farko ta ɗan ware idanu tana sake dubawa


Numban raudan ce kuwa, wani irin farin ciki ne ya lulluɓeta ta daka tsalle tana ihun murna


Tare da fitowa daga cikin dandazon


Tana ƙan-ƙame Rauda cikin tsananin farin ciki


Rauda riƙe ta tayi da sauri jin tana niyyar faɗuwa


"miye haka, Salma kada ki kadani mana"


Rauda ta ɗago tace.

"ƙawa result ɗinki first class, da first class Kika fito"


Rauda zaro ido tayi cikin mamaki


"first class? Bana son zolaya Salma please faɗamin me ki kagani"


Salma tace


"wallahi Rauda first class"


Rauda ta girgiza kai tana faɗin


"banyadda ba, bari in duba da kaina"


Ta Ƙarasa faɗa tana kutsawa


Tayi matuƙar mamaki ganin first class ɗin kuwa


Wani irin farin ciki ne ya mamaye mata zuciya


Fitowa tayi fuskarta ɗauke da tsantsar farin ciki, dan har wasu siraran hawaye ne suka biyo kuncin ta


Salma ta riƙe mata hannu tana dariyar jin daɗi


"yanzu kin yarda ƙawa?


Rauda ta jinjina kai kawai dan ta ma kasa magana


Salma ta cigaba da cewa


" kinga zauna a wurin bishiyar can ki jirani inje in haɗo mana drinks dan munana farin cikin mu"


Tana gama faɗa ta juya a guje ta nufi wurin da ake sai da drinks


Rauda ta Ƙarasa gurin bishiyar ta zauna Aasim ne ya faɗo mata


Tare da maganar da ya faɗa mata a rana ta farko da ya fara koya mata karatu


_"Rauda ina tabbatar miki da cewa zaki iya, kuma jarabawa me zuwa da first class Zaki fito Abu ɗaya nike so dake ki mai da hankali akan abunda zan rinƙa koya miki"_


Guntun murmushi tayi tana furta sunan sa a hankali 


"Aasim nayi rashin ka sosai,zan so ace kana tare dani ayau nasan sai ka fini farin ciki"


Dai-dai lokacin Umar ya shigo cikin makarantar wuri ya samu yayi parking yana kallon ɗaluban da ke kai da komowa


"ta ina zan fara neman ta?


Ya tambayi kansa yana sauke ajiyar zuciya


 wayar sa ya ɗauka  tare da buɗe marfin motar


Tunda ya zuro da ƙafafunsa ƴammatan dake zaune suna tattauna wa akan saka makon jarabawar su suke kallon sa


Sai da yaɗan ɗauki wasu sakwanni yana nazarin wurin dan ta cikin glass ɗin motar yana hango yadda ƴammatan suka zuba masa ido suna jiran suga fitowarsa


Guntun tsaki ya ja dan shi a rayuwar sa ya tsani kallo


Ya Ƙarasa fitowa da jikinsa tare da dafa marfin motar


"wow"


Wasu daga cikin ƴammatan suka faɗa ya yinda wasu daga cikin su suka saki baki suna kallon sa


Haɗe fuskar sa yayi sosai yayi kamar be san da wasu a wurin ba


Hange-hangen inda ze hango ta kawai yike yi amma bega ko alamar ta ba


Ya ja Guntun tsaki

"to wai ta ina zan fara ne manta ne?


Ya faɗa a fili yana ci gaba da hange hangen


Wata daga cikin ƴammatan ta taso ta ƙaraso inda yike tana yauƙi wai dan ko zata ja hankalin sa


Ko kallon ta beyi ba, bare yasan ma wace kala ce


"yallaɓai akwai wanda kake ne mana?


Ta faɗa cikin karya murya


Kallon ta yayi a fusace yace


" idan da akwai wanda nike nema miye ya shafe ki? Miye ya ruwan ki? Ko akwai abunda ya dameki dani ne"


Ya faɗa cikin ɓacin rai


Tsaye kawai budurwar tayi dan gaba ɗaya kunya ta gama lulluɓeta ganin yadda ya yarfa ta cikin jama'a


Zuciyarsa ce ta ɗan lallashe


"fushi ba naka bane, kai da kake so ka nemo ta, kuma ai dole sai da tambaya zaka gano inda take"


Numfashi ya sauke ya juya sosai yana fuskantar budurwar tare da zare glass ɗin idanun sa


"I'm sorry, I'm sorry na ɗaga miki murya"


Ya ɗan numfasa yana ci gaba da cewa


"ina neman wata ne me suna Rauda"


Ƙarfin hali budurwar tayi dan ganin kyawawan idanuwan sa sun ƙara rikita ta


A ɗan daburce tace


"a wani department take?


Girgiza kai yayi yace


"no bansan department ɗinta ba"


Budurwar tace


"masu suna Rauda suna da yawa a makarantar nan, gano ta batare da sanin department ɗinta ba, zeyi wuya gaskiya amma miye sunan mahaifin ta?


Kuma ya kamannin ta suke? Dan akwai wata dana sani a department ɗin mu"


Gyara tsayuwar sa yayi yana so ya tuna sunan mahaifin ta


_"Cikakken suna na shine Rauda isma'il"_


Ƙwaƙwalwarsa ta tariyo masa maganar ta


"yauwa sunan ta Rauda isma'il,bata da jiki,kyakkyawa ce me fararen idanu"


Ya faɗa cikin sauri


Girgiza kai budurwar tayi


"gaskiya ba ita bace dan wannan sunan ta Rauda mannir kuma ita tana da jiki"


"ook bayan ita fa? Baki san wata ba?


Ya tambaya a ƙagarance


ɗaga kai tayi alamar eh


Ajiyar zuciya ya sauke yana kaɗa kai


" shikenan nagode "


Juya wa budurwar tayi da sauri tabar wurin


Shiko jingina da motar yayi cikin da muwa


Haka yayi ta tambayar mutane amma duk wanda ya tambaya sai yace be san ta ba


Rauda na zaune taji gaban ta na faɗuwa


Kamar ance ta waiga ta hango sa yana tambayar wasu


Gabanta ne yayi wani mugun faɗuwa


Tayi saurin ɗauke kanta tana dafa ƙirjinta dake bugawa da sauri


Shi ko Umar juyawa yayi da niyyar komawa mota dan ya fara gajiya


Karaf suka ci karo da Salma


Wani irin farin ciki ne ya lulluɓesa


Cikin jin daɗin ganin ta yace


"yauwa alhamdulillah Allah na gode maka"


Rauda tayi saurin Miƙewa tana girgiza ma salma kai


Dayike ita take fuskantar inda take yayin da Umar ya juya mata baya


Salma ta kalli Rauda ta dan bata gane abunda take nufi ba amma sai ta mai da kallon ta ga Umar tana cewa


"bawan Allah lafiya?


" dan Allah ki nuna min inda Rauda take, ina son in yi magana da ita ne please "


Ƙara kallon Rauda tayi har lokacin girgiza mata kai take yi


"OK  ɗan jirani bari in kai saƙon nan indawo"


Gyaɗa kai yayi yana bin bayan ta da kallo


Karaf suka haɗa ido da Rauda da ke shirin barin wurin


Cikin sauri ya Ƙarasa gurin bishiyar yana yi mata sallama dan kafin Salma ta Ƙarasa tuni ya riga ta Ƙarasa wa


Tattaro dauriyar ta tayi duk da faɗuwar da gaban ta keyi ta dake


Tare da yin banza da shi


"Rauda ko ba komai kya amsa min sallama aiko?


Ɗagowa tayi ta watsa masa wani kallo me cike da ma'anoni da yawa


"ok wa alaikumussalam"


Ya yi murmushi yana cewa


"nafi awa ɗaya ina neman ki, duk wanda na tambaya sai su ce basu sanki ba....


"nemana kuma? Akan me kake nema na? Lafiya?


Ta tambaya tana kafe sa da ido


Ya sauke numfashi yana gyara tsayuwar sa


" kinga Rauda dan Allah kiyi haƙuri, ki tsaya ki saurare ni ki sauko daga fushinnan please"


Itama ta gyara tsayuwar tata tana fuskantar sa sosai


"nifa bawan Allah bangane abunda kake nufi ba wani fushi?


Duka-duka inace yau ne haɗuwar mu ta biyu


Ta ɗan daka ta sannan ta kaɗa kai tana ci gaba da cewa


" ohh na tuna wai na bugeni da kayi? Ai babu komai nasan tsau tsayi ne, sai anjima"


Ta Ƙarasa faɗa tana niyyar wuce sa


Tare ta yayi da sauri  ta hanyar shan Gabanta


"wai me kike yi ne haka ne? Me yasa kike nuna kamar baki sanni ba?


Ta harɗe hannayen ta a ƙirjinta tana ƙara kallon sa


"da alamu dai kayi ma kuwa ne, dan ni Banta taɓa ganin ka ba face ranar da ka bugeni"


Mamaki ne ya ƙara ka masa


Ya zuba mata ido kawai


zuciyarsa na cigaba da harbawa, wata kalar sabuwar ƙaunar tace ta fara bi masa jinin jikinsa


"Rauda nasan nayi kuskure a baya amma dan Allah kada kiyi min irin wannan hukuncin na nuna baki sanni ba..........


" daka ta bawan Allah, na gaya maka bansan ka, ban san ka ba, kaje Kane mi Raudar da ka sani dan Allah ka ƙyaleni"


Tana gama faɗar haka tabar wurin dan ji tayi zuciyar ta ta fara karye wa


Jingina da bishiyar yayi yana bin ta da kallo kawai


Numban zayyad ya kira babban amininsa bugu ɗaya ya ɗauka


"zayyad kana ina ne?


Daga can Ɓangaren zayyad yace


" gani zanje Katsina, mama ta aikeni kai kana ina ne?


Ya sauke ajiyar zuciya yace


"Nima Ina katsinan"


"kana Katsina? Yaushe kaje baka faɗa min ba"


Numfashi ya kuma sauke wa yace


"zayyad ina cikin damuwa ka hanzarta kazo dan Allah"


Zayyad yace


"ook ok ganinan zuwa, amma ka kwantar da hankalinka dan Allah, a Ina zan same ka?


Sunan hotel ɗin da ya sauka ya faɗa mishi, sannan ya kashe wayar ya koma motar sa


Tunda ta koma ɗaki take kuka wanda bata san taka mai-mai na menene ba, tana yi ne kawai dan ta samu sassauci a cikin zuciyar ta wacce take yi mata suya


Salma kallon ta kawai take yi tana mamakin irin wannan al'amari


Ƙarfe biyar zayyad ya isa hotel ɗin Numban ɗakin ya tambaya a ka nuna masa


Ya ƙwan-ƙwansa ƙofar


Umar na kwance kan gado ya Lumshe idanuwan sa jin ana ƙwan-ƙwansa ƙofar yasa ya miƙe


Ji yayi kansa ya sara, ya dafa kan yana cigaba da tafiya ya buɗe ƙofar


Zayyad kallon sa yayi sosai ganin yana yin sa ya tabbatar mai da yana cikin damuwan


Zama suka yi kan kujerar dake ɗakin zayyad na tambayar sa


"wai me yake faruwa ne umar? Me ke damunka?


Kwashe komai umar yayi ya faɗa masa


Zayyad yayi murmushi yana cewa


"to miye na damuwa anan? ince Rauda ce yarinyar da baka so Meyasa zaka dami kanka dan kawai tace bata sanka ba?


Umar ya sauke doguwar ajiyar zuciya yace


" zayyad bazaka gane ba, wallahi a yanzu zuciya ta ta kamu da tsananin ƙaunar ta, tun ranar dana haɗu da ita Naji naka sa sukuni"


Zayyad ya kuma yin murmushi


"aini wallahi Rauda tayi min dai-dai da ta nuna bata ma taɓa sanin ka ba


Yarin yar nan tasha wulaƙanci a wurin ka, dan kawai Kaga Tana mutuwar sonka kai ta wulaƙantata  ni kaina ta sha kirana tana kuka akan abubuwan da kake mata


Har ta gaji, sai yanzu ne zaka zo kace wai kana son ta?


Ni wallahi dama nasan wannan ce damuwar taka dan ban tada hankali na nayi ta gudu akan hanya ba"


Hannun sa umar ya kama ya na marai-raice fuska


"zayyad tabbas nasan nayi kuskure a baya amma yanzu wallahi ina son ta, ka taimake ni muje tare da kai ka bata ha ƙuri nasan tana ganin girman ka" 



Ƴarfillo.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*

         *AASHIQUE🌹*


                  🧞‍♂ 🧞‍♂

                     🧞‍♂

                   NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣0⃣


_Wannan Page na sa daukar da shi ga kan kaina,nawa ne ni kaɗai🤥_



*_fatan alkhairi_*

_Gareka yayana Abdullahi ɗan Fulani nagode da kulawar ka gareni da Allah ya ƙara dan ƙon zumunci a tsakanin mu_


*_Gaisuwa da fatan alkhairi_*

_Ga ansholly group ina muku fatan alkhairi musamman *meenah wayer* ina ganin yadda kike tambayar littafina a koda yaushe ina godiya sosai, *Hadiza tunau* ina jinjina miki Allah ya ƙara basira a cigaba da suburbuɗo mana me cetona😍_


_Ban manta da ku ba *matan ƙwarai* group kuma Allah ya bar zumunci_



_12:00_🕒AM

Wed, JUN 19


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Zayyad ya zame hannun sa yana faɗin


"wa? rufamin asiri inje inbata haƙuri ta saurare ka ka kuma wulaƙan tata? Ai wallahi babu ruwana"


Umar ya kuma marai-raice fuska


"Zayyad wallahi ina son ta,ka taimaka muje dan Allah wallahi tun safe ba abunda nasa ma cikina.....


Kallon sa Zayyad yike yi galala


"wai duk saboda Raudar ka kasa cin abinci?


Umar ya Gyaɗa kai


Murmushi Zayyad ya kuma yi yace


"to Naji zan yi tunani kafin goben, dan nasan ka nasan wannan shegen miskilancin halin naka"


Umar be ƙara cewa komai ba, har Zayyad ya tashi ya je ya siyo abinci ya ajiye ledar a gaban sa


"ka tashi muci abinci"


Umar girgiza kai yayi


"kaci kawai ni bana jin yunwa"


Dariya Zayyad yayi sosai


"ka san Allah Umar bana wani jin tausayin ka, wallahi dariya ma kake bani,dubi yadda ka wani marai-raice akan yarinyar da ka furta da bakinka baka son ta, baka ra'ayinta"


Dariya ya cigaba da yi ya zauna kan kujerar yana cigaba da cewa


"wallahi Rauda kinyi dai-dai Allah ya sa ma gobe ko mun je ta kuma nuna bata san ka ba"


Umar ta gumi ya zuba yana kallon Zayyad


"yanzu Zayyad dan kaganni cikin damuwa shine kake wannan dariyar har kana faɗin baka jin tausayi na?


Anya kai aminin kirki ne kuwa?


Zayyad ya kuma darawa


"to me kake so ince?


OK yi haƙuri, gaskiya kabani tausayi sosai jima nike yi kamar inyi ma kuka"


Ya faɗa cikin tsokana


Umar Miƙewa yayi yana jan tsaki ya bar mai ɗakin


Wurin da aka tana da dan shaƙatawa a hotel ɗin can ya nufa


Ya zauna ya tsurawa swimming pool ɗin dake wurin ido


Gaba ɗaya zuciyar sa ta cun kushe da tunanin ta



Salma ga jiya da jin kukan tayi tace


"wai ni Rauda na kasa gane miki wallahi, kin zauna kina ta kuka daga ganin mutumi,


Na tambaye ki waye shi kince baki san shi ba yakike so inyi da raina ne?  Wallahi kukan nan naki ɗaga min hankali yike yi"


Rauda tayi ƙoƙorin tsai da kukan ta amma ta kasa dan da ta tuno sa sai taji wani dunƙulen abu ya to kare mata ƙirji


Kukanne kaɗai yike sa ta samu sassauci


"Salma kiyi haƙuri, baki san abunda nike ji bane, nayi alƙawarin zan faɗa miki amma ba a yanzu ba, dan yanzu ina buƙatar natsuwa ne"


Salma ta sauke ajiyar zuciya tace


"shikenan ubangiji ya yaye miki, amma ki rage sa kanki cikin wannan muguwar damuwar"


Kaɗa Mata kai kawai tayi alamar taji, amma Saman zuciyar ta ji take yi kamar an ɗaura mata wani abu me nawi


Tambayar kanta kawai take yi wacce ta rasa bawa kanta amsa


"me yasa dan nagansa hankalina ze tashi haka? Shin ko har yanzu ƙaunar sa bata fita acikin zuciya ta bane?


Girgiza kai tayi da sauri tana sa hannu ta bubbuga kanta


Dan gani take yi kamar ƙwa-ƙwalwarta na so ta bijiro mata da abunda ya wuce


"Rauda ki natsu, kin riga da kin cire sa aranki,tsayin lokaci,ki cigaba da man tawa da shi kamar yadda ya umarce ki a baya


Kada ki manta da alƙawarin da kika ɗaukar ma kanki na ko zaki mutu baza ki ƙara ne mansa ba"


Ta faɗa a fili, sannan ta share fuskar ta Tana ƙoƙarin sai-sai ta natsuwar ta


Tausayin ta Salma taji sosai, dan sai lokacin ta gane abunda take nufi


*Kogon iraq*

(bari mu wai-wayi Aasim)


Zaune yike cikin ƙan-ƙara tsananin sanyi na shiga jikinsa


Wani hayaƙin sanyi ne ke fita a duk yayin da ya buɗe bakin sa


Sunfi su arba'in a wurin


Kallo ɗaya zaka ma sauran rauhanan ka gano tsantsar gajiya da damuwa a tare da su


Domin suna matuƙar shan wuya a training ɗin


Banda Aasim da shi sam babu wannan alamar gajiyar a tare da shi


Abul simnan shine shugaban wurin


Tsohone tukuf fari sol me dogon gemu, dan gemun sa har jan ƙasa yike yi


Yana zaune kan kujerar sa ya na karantar yana yin rauhanan


Turawa yayi aka kira masa Aasim


Aasim ya durƙusa yana gaishe sa


Amsawa Abul simnan yayi yana ƙara karantar yana yin sa


"yaro wani abu ne ya tsaya min a rai ya sa na kira ka, gani nayi gaba ɗaya rauhanan da suke training sun nuna gajiya warsu da ƙosawar su


Amma kai Kwata-kwata banga Hakan a tare da kai ba, dan wani zubin ma hango ka nike yi kana murmushi"


Murmushi Aasim yayi yana cewa


"tabbas abunda kafaɗa gaskiya ne, Sam ajikina bana jin gajiya wa,ƙosawa ta ɗaya ce ingama inje inyi abunda nazo domin sa"


Jinjina kai Abul simnan yayi


"tabbas ba ƙaramar ƙauna kake yi wa bil'adamar can ba, tunda har ka iya rabuwa da ahalinka da matsayin ka na ɗan babban sarki, ka kuma zo kana shan wahala dan kawai ka cigaba da rayuwa da ita


Amma kana ganin ba kayi kuskure ba kuwa? Da ka bata yarda ɗari bisa ɗari?


Murmushi Aasim ya kuma yi yana girgiza kai


"ko kaɗan banjin nayi kuskure, domin yadda nike son ta, haka ita ma take sona"


Abu simnan yayi ɗan murmushi


"to shikenan Allah yasa Hakan, amma nasan halin mutane lokaci ɗaya zasu nuna son abu lokaci ɗaya kuma zasu nuna ba sa so, ina yi maka fatan nasara a rayuwar ka"


Miƙewa yayi ya koma cikin ƙan-ƙarar yana jujjuya maganar abu simnan


Maganar tace ta faɗo masa


_"Aasim ina son ka dan Allah mu cigaba da rayuwa a haka"_


Murmushi yayi yana faɗin


"nasan ba zaki taɓa juya min baya ba Rauda, ina tsananin rashin ki Allah yasa kina kula min da kanki"


Ya faɗa cikin tsananin begen ta


***     ***    ***


Da sassafe Umar ya tashi ya shirya cikin manyan kaya, wani ya din malesia ne me silɓi kalar navy blue


Yayi kyau sosai ya taje sumar sa tare da fesa turare


Ya ɗauko hula ya saka yana maƙala tsadaddan agogo a hannunsa


_"Jaana idan kasa manyan kaya kana yin kyau, ganin ka nike yi kamar ango"_


Maganar ta tabaya ta dawo masa


Murmushi yayi yana kallon kansa a madubi


Inda ya bayyana na ainihinsa na halfcas


"na sane dan na burge ki Rauda Allah yasa ki saurare ni yau"


Ya faɗa yana komawa bakin gadon yana tashin Zayyad dake ta sharar baccin sa


Zayyad buɗe ido yayi yana miƙa


"wai miye ne ka takuramin ka hanani inyi bacci ne?


Umar yace


" ka ta shi mana mu tafi makarantar su Rauda"


Kallon agogo Zayyad yayi ƙarfe bakwai saura


"me zamuje muyi da  sassafe haka? Kabari gari ya waye sosai mana"


Umar ya ce


"ai dama ba yanzu zamu tafi ba, kata shi dai ka shirya dan nasan wannan daɗewar da kake yi a wanka kamar me canza fata"


Zayyad Miƙewa yayi yana faɗin


"Allah ka cika ta kura umar, sai kaje ka haɗo mana abin kari ai kafin in fito"


Umar zama yayi yana duba agogon hannun sa


_Umar dan Kaga ina son ka shiya sa kake wulaƙan Tani ko? Ka sani cewa bani na ɗaura wa kaina ba, Allah ne ya ɗaura min"_


Maganar ta tabaya ta kuma yi masa yawo a kunne


Dafa kansa yayi cikin damuwa yana jin haushin kansa


"Meyasa nayi mata haka ne? Me yasa?


Ya faɗa cikin jin ta kai cin abunda yayi mata


Dogon tsaki yaja

Cike da Nadama


Ƙarfe goma da rabi ta fito daga lecture


Dai dai lokacin Umar suka yi parking


Suka fito suka tsaya jikin motar


Tun daga nesa suka hango juna wanda sai da ƙirjinsu ya amsa su duka biyun


Kamar ta juya ta koma sai kuma wata zuciyar tace ta cigaba da tafiya kawai


Tunda ga nesa yike kallon ta,tafiya take yi a natse kamar tana jin tsoron taka ƙasa


Komai nata daban ne, wani numfashi ya sauke tare da ajiyar zuciya


Domin be taɓa sanin haka Allah yayi mata kyau ba


Zayyad ko burgesa tayi ganin yadda ta ɗauke kanta kamar Bata gansu ba


Ta kuma haɗe fuskarta, har ta iso inda suke tana niyyar wucewa


Zayyad ne ya tare ta yana yi mata sallama


Ta amsa, tana neman ya bata hanya


"Rauda dan Allah ki tsaya ki saurare mu, mun san munyi kuskure amma kiyi wa girman Allah da soyayyar da kike yi wa annabi Muhammadu(s.a.w)"


"sallallahu alaihi was salam"


Ta faɗa tare da tsayawa


"to bawan Allah ina jin ka na tsaya ne ba dan niyya ba sai dan kira fiyayyen halitta da kayi"


Zayyad ya jinjina kai yace


"nagode sosai, amma me ze hana muɗan sami wuri mu zauna, saboda mu tattauna abunda ya kawo mu a tsana ke?


Girgiza kai tayi tace


" a'a nan ma ya isa,ina jinka"


Zayyad yace


"ok to shikenan,dama akan maganar Umar ne, ya ce min kin ƙi kula sa kina ce mai baki san shi ba, Rauda nasan Umar me laifi ne a wurin ki amma dan Allah kiyi haƙuri....


Dafa kanta tayi cikin damuwa tana kallon Umar da ya zuba mata ido


" oh Allah na,bawan Allah wai ba kaji abunda nafaɗa ma jiya bane? Nace ma ban san ka ba"


Ta mai da kallon ta ga Zayyad tana cewa


"bawan Allah idan baya jin hausa sosai ne kafaɗa masa yadda ze Fahimta bansan sa ba"


Zayyad yayi murmushi


"Rauda nasan zafin zuciya ne yasa kike faɗan haka, yanzu Nima zaki ce baki sanni ba?


Ta ɗaga kai


" eh kaima ban san ka ba, ina ga dai me kama da ni kuka sani amma bani bace gaskiya"


Ta juya gurin Umar tana ci gaba da cewa


"amma ita wacce kuka sanin miye cikakken sunan ta?


Gaba ɗaya kan shi ya ɗaure ganin irin kallon da take masa


" Rauda isma'il"


Ya faɗa cikin rashin sanin abun yi


"gashi sunan mu yazo ɗaya, amma shin ka taɓa haɗuwa da ita ne a baya?


Ya girgiza kai alamar a'a


Ta gyara tsayuwarta tana cigaba da kallon sa


" to a ina ka Santa kenan? Tunda baka taɓa haɗuwa da ita ba?


Cikin damuwa yace


"Rauda sau nawa zan baki haƙuri ne? Idan ma haƙurin da na baki beyi miki bari indurƙusa in baki amma kidena nuna min bake bace please"


Ya Ƙarasa faɗa yana niyyar durƙusawar


Dakatar dashi tayi da sauri


"ni bance ka dur ƙusa min ba, kadai bani amsar abunda na tambaye ka"


Gauron numfashi ya sauke yana kaɗa kai


"shikenan a waya na Santa"


"Ashe?


Ta tambaya tana buɗe idanuwan ta sosai


" kenan hotuna ta tura maka, ta kuma faɗa maka sunan ta Rauda isma'il


Shin baka tunanin tayi amfani da hotunan da ba nata ba, ta kuma yi maka ƙaryar suna?


Cikin tsananin damuwa da ƙosawa da yadda take masa yace


" idan tayi min ƙaryar suna da kuma hotuna ai bazata aro fuskar ki tasa ba, kinga Rauda kidena wani kwana-kwana ke ce domin har video call mun sha yi dake"


Taɓe baki tayi tace


"to ni dai ban san ka ba, nafaɗa kuma zan sake faɗa, dan Allah kada ka sake biyo ni inda nike, kaje ka nemi wacce ka sani amma bani Raudan ba  Dan ni ko me kama da kai ban sani ba bare kuma kai"


Haƙiƙa maganganun ta sunyi masa ciwo amma sai ya danne


Zayyad yace


"Rauda ko Allah muna yi masa laifi ya yafe mana bare tsakanin mu ƴan adam........


Bata jira jin me ze gama cewa ba tayi gaba


Umar ze bita zayyad ya dakatar dashi


"Umar shiga mota mu tafi ko kabita bazata saurare ka ba, kuma Kaga hankalin mutane ya fara dawowa kanmu"


Be ce komai ba ya buɗe motar ya shiga, zayyad ya mara masa baya yana tada motar


Lumshe idanuwan sa yayi kawai yana jin kansa na sa rawa


"zayyad kafaɗamin yadda zanyi in shawo kanta, wallahi ina jin zuciya ta tana min nawi, ina sonta zayyad"


Zayyad ya ɗan kallesa sannan ya maida kallon sa ga titi


Tabbas a yanzu ya yadda Umar da gaske yi ke yi yana sonta, ganin duk irin zafin sa amma yana niyyar durƙusa mata


Amma Sam shi bega laifin ta ba, dan Umar ya cancan ci hukuncin da ya wuce haka ma a wurin ta


Guntun numfashi ya sauke yace


"kai ma Umar ka san ba ka kyauta mata ba,abunda da yawa maza ba su gane ba shine


A memakon su nuna kulawar su ga matan da suka nuna suna sonsu


Sai su yi amfani da wannan damar su dinga wulaƙanta  mace, bayan sun mance cewa ita mace kunya gareta


Amma ta danne wannan kunyar ta nuna tana sonsu,


Wace magana ce ban gaya maka ba a wancan lokacin Umar?


Har roƙonka nayi akan ka sassauta jan ajin da kake mata


A gabana sai ta yi maka kira fin ashirin

Amma ka ɗauka ne kake ganin asara, kuma idan ka ɗaukan ma a daƙile kake yi mata magana


Idan taji baka da lafiya nikaina sai tamin kira fin goma tana tambayar ya jikin ka


Amma kai sau nawa tana faɗa ma tana gadon asibiti amma ka iya kira ko sau ɗaya ne kace mata ya jiki ba kayi


Umar maganar gaskiya ka wulaƙanta tata, dole ma tayi ma haka wallahi"


Umar ya runtse idon sa zuciyar sa cike da takaicin kansa


"zayyad dan Allah ka dena tuna min abunda ya wuce nasan ni me kuskure ne ka faɗa min yadda zanyi kawai"


Zayyad ya sauke ajiyar zuciya sannan yace


"ka cigaba da zuwa kana bata haƙuri insha Allah zata sauko"


Rauda na shiga ɗaki tafaɗa kan katifa tana maida numfashi dan zahiri ba ƙaramar dauriya tayi ba


Gaba ɗaya hankalin ta ya tashi,haƙiƙa ƙaunar sa ne ma take yi ta dawo mata


Ta rasa irin sa,ba ƙaramar wahala tasha ba wajen ya kice sa a zuciyar ta


Amma gashi yazo yana so ya burki ta mata lissafi


Tabbas ta san yadda taso Umar, babu wani mahaluki a duniya da za taso kamar yadda ta sosa


Tasha yin kuka,kasa barci akan ƙaunar sa kai har rashin lafiya


Wasu siraran hawaye ne suka biyo kuncin ta yayin da ta tuno wahalar da tasha a kan ƙaunar sa


"me yasa Umar? Me yasa kamin haka? Me yasa baka zo a sanda nike buƙatar ka ba sai bayan na cire ka a zuciyata?


Ta faɗa a fili tana share hawayen dake biyo kwarmin idanun ta


Dafa ƙirjinta tayi tana jingina da filo


"dan Allah zuciya ta kada ki dawo min da ƙaunar shi,ki ci gaba da manta wa da shi"


Ta faɗa cikin karyewar zuciya


Bayan sati ɗaya


Umar ya fita hayyacin sa sosai dan babu ranar da baze je makarantar su Rauda ba


Amma still nuna take yi bata Sansa ba, wani zubin ma ko saurarar sa bata tsaya wa yi


Ya Rame sosai, dan ko abincin kirki baya iya ci


Zayyad tun baya jin tausayin sa har ya fara bashi tausayi


Kamar kullum yana tsaye inda ya saba tsayawa


Ta fito zata je ɗaukar darasi


Daga nesa ta hango sa ya jingina da jikin mota


Gaban ta ne ya faɗi yayin da taga yadda ya Rame acikin ƴan kwana ki


Dauriya tayi ta cigaba da tafiya har tazo wuce wa ta inda yike


"Rauda!


Ya kira sunan ta cikin wani irin yana yi


Yadda ya kira sunan tan yasa taji jikin ta yayi sanyi


Ji tayi bazata iya wuce sa ba


Ta tsaya kawai batare da ta juya inda yike ba


Zagayo wa yayi Gabanta ya zuba mata kyawawan idanuwan sa


" Rauda ya kamata ki tausaya min, ki sassauta min haka, wallahi ko barci bana iya yi,Rauda ina ƙaunar ki a yanzu fiye da yadda kike tunani........


Ɗaga masa hannu tayi idanuwan ta na ciccikowa da hawaye


"na roƙeka ka fita da ga rayuwa ta kadena zuwa inda nike, dan Allah"


Umar ya kaɗa idanuwan sa da suka yi ja


Tare da cize lips ɗinsa


"ina sonki Rauda bazan iya rayuwa babu ke ba, dan girman Allah ki yafemin abunda nayi miki"


Ya Ƙarasa faɗa ya na durƙusawa bisa gwiwowin sa Be damu da jama'ar dake kallon sa ba


Ji tayi kuka na so ya ci ƙarfin ta,da sauri tabar wurin tana dafa ƙirjinta da yike yi mata suya


Can ƙarshen aji ta zauna ta kifa kanta tana kuka


Salma ta dafa ta dan a idon ta komai ya faru


"Rauda dan Allah ki sassauta masa haka, wallahi ya galabaita kuma kema fa har yanzu kina son sa"


Rauda ta ɗago jiƙaƙƙun idanun ta tana kallon salma


"Salma ya zanyi da raina? Ki faɗamin ji nikeyi kamar zuciya ta zata fashe"


Salma sauke numfashi tace


"haƙuri zaki yi ki yafe masa, tunda ya amsa yayi kuskure"


_kada ki ƙara kirana ko nemana kisa aranki cewa baki taɓa sanina ba ki gogeni daga rayuwar ki_


Girgiza kai tayi da sauri yayin da zafafan kalaman sa suka sake yi mata yawo a kunne


"bazan iya ba Salma, bazan iya ba idan nayi haka ban kyauta wa kaina ba, shi da bakin sa yace in goge sa daga rayuwa ta, nayi kuma abunda yace Meyasa yanzu ze dawo gareni Meyasa?


Ta Ƙarasa faɗa tana fashewa da kuka


Salma ta sauke numfashi tana cewa


" shikenan ya isa haka kukan, kinga lecturer ya shigo"


Share hawayen ta tayi tana kallon lecturen da ya fara darasi


Gaba ɗaya babu abunda take fahimta,dan kanta ya cushe


Tunda ya koma mota yike jin zuciyar sa na ƙuna tuƙi kawai yike yi batare da yana kallon hanya sosai ba


Gaba ɗaya ya rikice, jijiyoyin kansa sunyi burɗum-burɗum


Sakamakon tsananin ciwo da kansa keyi,


Ya zeyi mata ta fahimci ƙaunar da yike mata?


Ya zeyi ya goge laifin sa a gareta?


Tambayoyin da yayi ma kansa kenan wanda ya rasa amsar su


Runtse ido yayi cike da tsananin damuwa


Ƙarar horn yaji daf dashi


Ya buɗe idanuwan sa da sauri wata ƙatuwar mota ya gani gab da shi


Ya juya sitiyari da sauri dan ya kauce mata


Sai dai duk da haka Be tsira ba dan wata ƙatuwar bishiya ya daka


Ya yin da motar ta dawo baya ta daki jikin waccan motar


Ta kuma yo gaba ta tuntsura


***    ***   ****


Tsattsaye suke sunyi layi gaban wani kogo


Wanda yike fitar da turi ri acikin sa


Abul simnan ne tsaye a gaban su inda yike yi musu jawabi


"kamar yadda muka gama da horon ƙan-ƙara yanzu zamu shiga kogon marzaj


Kogone dake ɗauke da tsumi wanda dashi ne zan haɗa muku bayyana acikin jama'a


Sai dai kusani kafin kuje inda tsumin yike akwai wasu baƙaƙen ifiritai wanda suke da sarauniyar su guda


Sanin kanku ne kamar yadda muke da ƙarfi haka suma ifiritai suke da shi


Dan haka sai kun dage dan idan ba kuyi da gaske ba, za ku iya rasa rayukan ku


Dan haka sai kun kula da kyau, kun kuma dage


Da zarar kun isa wurin wannan tsumin kuyi gaggawar ɗiba sannan kuyi gaggawar fitowa


Amsawa suka yi da to


Wasu daga ciki farga ba ne maƙil acikin ransu, yayin da shi Aasim Sam baya jin wata fargaba


Dan Abul simnan na shiga shi ya fara mara mai baya


Tafiya suka yi sosai har sai da suka kusa gab da wurin


Sannan Abul simnan ya tsaya yace


"anan zan dakata inbarku ina yi muku fatan nasara, sannan kusani shan wannan tsumi agareku bawai bayyana acikin jama'a kaɗai ze muku ba


Harda ƙarfi me tsanani da ze ƙara muku"


Jin Hakan yasa suka ƙara himma tare da yin gaba


Aasim ne a gaba, tafiya suka ƙara yi me nisa sannan suka isa ƙofar wurin


Sai da suka tsaya sukai nazarin wurin sannan suka doshi ƙofar


Wasu manyan ifiritai ne suka bayyana wanda girman su ya wuce na misali sanye da wasu baƙaƙen kaya da manyan wuƙaƙe


Suka zaga ye su


Nan da nan suka kaure da faɗa


Sunyi kusan awa ɗaya suna gabzawa yayin da su Aasim suka jigata sosai


Dan har sunfara sarewa


Tunawa da Rauda da yayi da irin ƙaunar da yike mata yasa yaji wani sabon ƙarfi yazo mishi


Nan da nan ya miƙe daga zubewar da yayi ya shiga tsakiyar su yana kai musu sara ta ko ina 


***   ****   ****


Suna tashi daga lecture Takoma ɗaki ta kwanta


Wani kalan zazzaɓi me zafi ne ya rufe ta


Ga kanta da yike sarawa kamar ze rabe biyu sakamakon kukan da taci


Wani bacci me cike da damuwa ne ya ɗauke ta


Bata farka ba sai bayan kiran sallar asuba


Har lokacin ciwon kan Be sauka ba


Ta ɗauro alwala ta gaba tar da sallah sannan ta ɗaga hannu tana kai kukan ta ga ubangiji


Ƙarfe bakwai takwas ta gama shiryawa


Tana ɗaukar jakarta


Salma tace


"ba zaki tsaya ki karya ba?


Girgiza kai tayi tace


"banajin cin komai"


Tana gama faɗa ta sa takalmi ta wuce


Tunda ga nesa take kallon inda yike tsayawa duk safiya amma bata ga motar sa ba


Wani iri taji a zuciyar ta


Kenan ya gaji ya haƙura?

Daga can gefe ta hango Zayyad


Yanayin data gansa ya sa ta faɗuwar gaba dan hankalinsa a tashe yike


Yana ganin ta ya ƙaraso yana cewa


"tun ɗazu nike jiran fitowar ki, har da zan juya"


Bata kula sa ba ta cigaba da tafiya


Zayyad ya bi bayan ta da kallo yana faɗin


"Rauda kitsa ya ki saurareni Umar ne ya yi accident jiya a hanyar sa ta koma wa daga wurin ki"


Ƙirjinta ne yayi wani mugun bugawa ta juyo a razane tana duban Zayyad


"ac.. cident!! "


Ta faɗa cikin rawar murya


Zayyad ya jinjina kai idanuwan sa na ci kowa da ƙwalla.


"Rauda Umar ya na cikin wani ma wuya cin hali bani da tabbacin ze rayu ko baze rayu ba"


Ji tayi ƙafafunta sunfara rawa sun gaza ɗaukar ta


Tayi saurin dafa ƙarfen dake wurin tana faɗin


"innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku!!!




Ƴarfillo.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: *🌹JINNUL*

         *AASHIQUE🌹*


                  🧞‍♂ 🧞‍♂

                     🧞‍♂

                   NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣1⃣



_Wannan Page naki ne *safnah* kiyi yadda kike so dashi_ 



~_Ina da wata buƙata kutayani da addu'a Allah ya biya min,ya cika min burina please_~


_8:50_🕒PM 

THU, JUN 20


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


"Zayyad me ya sami Umar? Ka faɗamin wani hali yake ciki?


Tayi mai tambayar cikin rawar murya da tsananin tashin hankali


Zayyad yace


"baki ji me nace bane? Accident yayi kuma duk kece sanadi, dan da kin saurare sa da Be shiga damuwar da ze fita hayya cin sa ba"


"inna lillahi wa inna ilaihi raji'un, ka kai ni asibitin da yike ka kaini in gansa dan Allah"


Ta faɗa tana runtse idanuwan ta da suka cicciko da hawaye masu zafin gaske


Be ƙara cewa komai ba ya buɗe mota ya shiga


Binsa tayi ta shiga jikin ta na tsuma zuciyar ta cike da tarin fargaba


Ya tada motar ya fige ta aguje


Idanuwan sa sun kaɗa sunyi ja


"duk mutumin da yayi maka laifi ya dawo yace ka yafe masa ai Be kamata kaƙi kula sa ba


Sanin kanki ne Umar ɗin da kika sani da, ba shi bane yanzu


Wani irin roƙo ne be yi miki ba? Wani irin haƙuri ne be baki ba? Amma duk kika nuna baki san yanayi ba?


Dafa kanta kawai tayi da yike cigaba da sarawa batare da ta ƙara tanka masa ba


Suna isa asibitin suka fito yayi gaba tana Binsa


Ƙofar emergency room ya murɗa ze buɗe


Wata nurse ta ƙara so wurin da sauri tana faɗin


"baiwar Allah kijira a fito dashi daga emergency room tukunna"


Zayyad ya kalli nurse ɗin yace


"baki ga tare dani take bane?


Sun kuyar da kai nurse ɗin tayi


"sorry doctor Naga doka ce ba a shi.....


Be jira jin me zata Ƙarasa cewa ba ya buɗe Ƙofar ya shige


Gabanta na faɗuwa ta kutsa kanta ciki


Kwance ta hango    Jikinsa duk bandeji, jikin ta na rawa ta Ƙarasa gaban gadon zuciyar ta na wani irin rawa


"Umar!


Ta Kira sunan sa,ko motsi Be yi ba ballantana ya amsa mata, idanuwan sa na rufe ruf


Zuba masa ido tayi, gani take yi kamar baya numfashi


Cikin tashin hankali da kiɗima ta fara jijjigasa tana faɗin


"Umar ka tashi, ka tashi dan Allah, Naji na haƙura"


Har lokacin ko motsi beyi ba


Kuka ta fashe da shi tana cigaba da jijjigasa


"na roƙeka katashi, kada ka tafi ka barni Umar"


Maganar ta ya fara ji tana ratsa kunnuwan sa


Ji yike yi kamar mafarki yike yi


"katashi Umar, dan Allah katashi wallahi na haƙura"


Ta kuma faɗa


Buɗe idanuwan sa yayi da suka yi masa nawi


Dishi-dishi ya fara ganin ta


Kafin ya ganta sosai,ita ko ganin ya buɗe idon yasa ta sauke wani nannauyan numfashi


"Rauda"


Ya kira sunan ahankali


Kasa amsawa tayi kallon sa kawai take yi


"Rauda ina son ki, dan Allah ki ce min kin haƙura da abunda nayi miki, ki amsa kin yafe mini"


Zuciyar ta tsinke,janyo kujera tayi ta zauna jin jiri-jiri ya fara ɗiban ta


Ze kuma magana ta katse shi


"Umar,na haƙura ya riga da ya wuce"


Ya Lumshe idanunsa yana faɗin


"nagode"


Hannu tasa ta share fuskar ta da tayi sharkaf da hawaye


Sannan ta ƙara matsawa kusa dashi


Tana kiran sunan sa


Kuma buɗe idanuwan sa yayi ya zuba su a kanta


"kayi haƙuri da jefa ka damuwa da nayi...


Girgiza kai yayi a hankali


"a'a Rauda, sam kada ki bani haƙuri na cancan ci fiye da abunda ma kikai min"


Ya faɗa da rauninniyar muryarsa


Kaɗa kai tayi tana kuma share fuskarta gaba ɗaya jikin ta ya mutu.


Miƙewa tayi tace


"zanta fi,anjima zan dawo"


Ta Ƙarasa faɗa tana niyyar juyawa


Ruƙo hannun ta yayi,ta juyo suka zuba ma juna ido


"kar ki tafi Rauda dan Allah,ina buƙatar ganinki a kusa dani"


Ta sauke ajiyar zuciya tace

"kayi haƙuri Nima bana jin daɗi ne, anjima zan dawo"


Ya girgiza kai

"a'a ki tsaya Zayyad ya duba ki, ki tsaya tare dani please"


Hannun ta ta zame tana girgiza kan itama


"a'a akwai wacce zata duba ni"


Bata jira jin me ze ƙara cewa ba tayi gaba,tana tafiya jiri na kwasar ta


Zayyad ya tashi da sauri ya tare ƙofar


"bafa ze yuwu ki tafi cikin wannan halin ba, tunda dai har kinzo asibiti muje induba ki"


Zatai magana Zayyad ya dakatar da ita


"kada ki ce zaki yi musu Rauda, dan Allah"


Numfashi ta sauke tana kaɗa kai dan ta ƙagara ta zauna ji take yi kamar zata faɗi


Zayyad ya dubi Umar ya ce


"bari muje na duba ta yanzu zan dawo"


Umar binsu da ido yayi kawai

Suka fita, wani office suka shiga ya nuna mata kujera ta zauna


"dame-dame kike ji yana damunki?


" ciwon kai, sai jiri da kuma ƙirji"


Ya jinjina kai, sannan yayi mata gwaje-gwaje


Nurses ya kira yace suzo su sa mata drip,da kuma allurai


Dole ta haƙura suka sa mata dan tana buƙata ita ma


Ta Kira Salma ta faɗa mata,ba'a fi minti ashirin ba Salma ta zo asibitin


Da daddare,tana zaune kan gadon asibitin ta tsura ma drip ɗin ido, gani take yi baya sauri dan kaɗan-kaɗan yike ɗiga, Allah Allah take yi ya ƙare su tafi


Zayyad ya shigo ɗakin yana yi mata ya jiki


Amsawa tayi da "dasauƙi"


Sannan ta ce

"kaɗan ƙara gudun ruwan bana so dare yayi sosai ba mu tafi ba"


Zayyad yace

"ai bayan wannan ma akwai wasu,dole tafiyar ki sai ta kai gobe da yamma saboda da alamu kinyi ta ciwon a tsattsaye"


Salma tace

"gaskiya gwara kitsaya ki samu sauƙi Ƙawa,kiyi haƙuri zuwa goben"


"Hakan ya kamata,Shima Umar yanzu muka dawo dashi ɗakin dake jikin wannan"


Bata ƙara cewa komai ba ta kwanta,


Bata daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗauke ta


Ƙarfe ɗaya na dare ta farka,a gigice


Sakamakon mafarkin da tayi wai Umar ya rasu


Lokacin Salma ta daɗe da yin bacci,zare abun ruwan tayi ta sauko ta fito


Babu kowa a harabar wurin ta windon ɗakin da yike ta hango sa


Murɗa ƙofar ɗakin tayi ta shiga ta Ƙarasa gaban gadon


Gabanta na faɗuwa ta dafa ƙirjinsa jin yana numfashi yasa ta sauke doguwar ajiyar zuciya tare zauna wa a kujerar dake gaban gadon


Ta tsura mai ido,kyakkyawar fuskar nan nasa tayi fayau, sai dogon hanci


"Umar!


Ta Kira sunan,da alamu bacci yike yi dan be amsa ba


Ta cigaba da kallon sa zuciyar ta na saƙo mata abubuwa da yawa


Tabbas ta san har yanzu tana ƙaunar sa, dan sonsa da banne acikin zuciyarta


Shine wanda ta fara so, kuma shi kaɗai ne wanda tayi ma so me tsanani


Gashi lokacin ta daɗe tana fatan zuwan sa na ranar da Umar ze ƙauna ce ta yazo, amma sai dai kash


Aasim,ya riga da ya danne komai, dan Shima tana sonsa amma bazata taɓa haɗa son da take yima Umar da wanda take yi masa ba


Umar ƙaunar sa daga Allah ne, dan shine ya jarabce ta


Hawaye masu ɗumi suka shiga gangaro mata


"Meyasa sai yanzu Umar? Me yasa kabari lokacin Dana daɗe ina jira ya wuce?


Meyasa?


Ta jingina bayan ta da kujerar tana runtse idanunta wasu sababbin hawayen na gangarowa


"kai ne burina, kai ne zaɓi na, kai ne wanda nayi fatan rayuwa dashi a matsayin miji na har abada, amma kabari lokaci ya wuce dan bazan iya janye alƙawarin da nayi wa Aasim ba, bazan iya ba!


Kuka me ƙarfi ne yaci ƙarfin ta, ta kifa kanta jikin gadon tana kuka me tsuma zuciya


Umar duk abunda ta faɗa yana ji, da fari farin ciki ne da jin daɗi ya mamaye zuciyar sa amma Aasim da ta ambata yasa jikin sa yayi sanyi


Waye shi? Wani irin alƙawari ta ɗaukar masa da take faɗin bazata iya karyawa ba?


Yayi wa kansa tambayoyin,da bayi da amsar su


Ita ko Rauda Miƙewa tayi ta koma, ɗakin da take


Ta kwanta,har lokacin ƙaunar sa ce ke kuma bin jinin ta


Ta dafa sai tin zuciyar ta da take yi mata nawi tace


"dan Allah kada ki bari ƙaunar Umar ta kuma tasiri a zuciyar ki, Aasim shine wanda ya cancan ce ki, shi ne ya sadaukar da rayuwar sa da komai nasa akan ki, Umar ko shine ya wulaƙanta ki a lokacin da kike neman kulawar sa"


***   ****  ****

Sunɗauki awanni suna gabzawa da manyan ifiritan, yayin da wasu daga cikin rauhanan sun ji ciwo sosai suka kuma sare


Aasim ne kaɗai har lokacin yike fafatawa dasu,duk da Shima ya galabaitan


Sarauniyar ifiritai tana zaune kan kujerar ta tana kallon abunda yike faruwa


Sai da tagama kallo tsaf, sannan ta cewa ifiritan su dakata


Dakatawar suka yi kuwa, yayin da Aasim da sauran suka tsaya suna mai da numfashi


Gurin yayi tsit,Sarauniyar da har lokacin idanuwan ta na kan Aasim tace


"nadaɗe banga jarumi irin ka ba,sannan kuma na daɗe banga sakarai irin ka ba wanda yike sadaukar da rayuwar shi dan kawai ya rayu da bil'adama wannan babban kuskure ne"


Aasim Shima da tun da ta fara maganar yike kallon ta yace


"a gareni Sam ba kuskure bane,kuma a shirye nike da inshiga kasadar da tafi wannan in har yin Hakan ze ƙara min kusanci da ita"


Murmushi Sarauniyar tayi yayin da tagama duba madubin tsafin ta


"tabbas kayi kuskure me girma da ka amince da bil'adama,sannan kuma zaka yi da na sani domin kuwa duk wannan wahalhalun da kake sha zasu tashi a banza"


Ta ɗan numfasa sannan ta cigaba da cewa


"kun aikata laifi dan kawai ku sami bayyana acikin mutane kuka shigo mana kogo kuka karya mana doka,amma duk da Hakan jarumtar da ka nuna zata sa inyi abunda bantaɓa yi ba


Wato inbada gudunmuwa wajen karya dokar da kakannina suka kafa, tabbas wannan tsumi dokace bama bari a ɗiba amma kuje na baku dama ku ɗiba iya wanda ze muku"


Wazirin ta ne ya zube yace

"ranki shi daɗe maƙiyanmu ne fa ko kin manta gabar dake tsakanin mu dasu ne?


Ta girgiza kai tace

" ban manta ba zundaj,amma kada ku ƙara taɓa su ku bar su su ɗiba"


Aasim murmushin jin daɗi yayi tare da rusunawa


"godiya muke sarauniya, Allah ya ƙara girma, haƙiƙa kina da taushin zuciya me cike da tausayi ubangiji ya shiga cikin lamarinki"


Jinjina kai kawai tayi tana nuna musu hanya


Suka wuce zuwa inda tsumin yike, tun da suka isa wurin Aasim ke murmushi


Ya shafa hannun sa wani ƙoƙo me Marfi ya bayyana yasa ya ɗiba


"Rauda yanzu zamu rayu ni dake cikin kwanciyar hankali batare da wata damuwa aranki ba"


Ya faɗa yana rufe ƙoƙon


Sai da suka gama ɗiba sannan suka juyo suka yi ma sarauniyar godiya


Har sun juya zasu wuce ta dakatar da su ta hanyar kiran Aasim


Waigowa yayi yana kallon ta batare da ya amsa ba


"aduk lokacin da danasani ya riske ka,ka kuma yi niyyar ɗaukar fansa kada ka manta wajen neman agajina"


Yayi murmushi yana jinjina kai


"nagode sosai amma nasan babu danasani a rayuwa ta"


Murmushi kawai tayi ta ɓace


Shiko futowa suka yi zuciyar sa nayi masa wani iri


Meyasa ake yi masa zancen yayi kuskure, shi dai yasan Rauda bazata juya mai baya ba, to shi ko wani danasani zeyi?


***   ***  ****


Washegari da sassafe Salma ta koma makaranta dan akwai test ɗin da zata yi


Rauda na kwance ita kaɗai, Umar kasa haƙuri yayi ya taso ya shigo ɗakin


Ta yunƙura tana kallon sa ganin yadda ya shigo yana bin bango


"lafiya ka fito kai da kake kwance?


Zaunawa yayi yana mai da numfashi


"nakasa haƙuri ne Rauda, inaso in ganki shiyasa"


Kallon sa tayi sosai, sannan tace


"amma ai da ka aiko an kirani"


"kema baki da lafiyar ai"


Ya faɗa, ta girgiza kai


"amma ai ban kai ka jin jiki ba ko?


Ya jinjina kai


"ya jikinna ki? Yanzu dame-dame kike ji yana damunki?


"naji sauƙi babu abunda ke damu na yanzu,ya naka jikin?


" Nima Naji sauƙi alhamdulillah, me kike so a kawo miki ki karya?


Ya tambaya


Dai-dai lokacin Zayyad ya shigo ɗakin ganin Umar yasa yayi sororo yace


"kai kuma fa? me ya fito da kai?


Umar yace


"bansani ba, me Kaga inayi?


Zayyad ya Ƙarasa shigowa yana faɗin


"kana fama da kanka shi ne kake ƙoƙarin yin jinya?


Ya Ƙarasa faɗa yana ajiye abun kari


Rauda tace

"dan Allah kabarni in tafi yanzu tunda Naji sauƙi abar ragowar alluran haka"


Ta faɗa tana duban Zayyad


Zayyad ɗan murmushi yayi yace


"ki kwantar da hankalinki anjima kaɗan zaki wuce"


Bata ƙara cewa komai ba,ta ɗauki wayar ta da ke ƙara


"hello Salma kintaho ne?


Daga can Ɓangaren Salma tace


" wallahi Rauda na taho babu hanya, baki ga yadda matasa suke ta zanga-zanga ba da Manyan makamai "


Rauda tace

" subhanallah zanga-zanga kuma? Na mene?


"Nima bansani ba amma nasan baze wuce na siyasa ba, bari in koma dan Naga faɗa yana so ya kaure a wurin"


Rauda ajiye wayar tayi cikin damuwa


Da yamma tana tsaye tana kallon tvn dake manne jikin bango


Yadda faɗan ya kaure ake nunawa, ga sojoji nan ta ko ina


Nurse ce ta shigo


Rauda tace

"wai yanzu ko kaɗan babu hanyar da mutum ze bi ya koma inda yike"


Nurse ɗin tace


"wallahi babu, dan muma tun rana aikin mu ya ƙare amma waɗanda zasu amshemu basu zoba ga kuma Waɗan da aka ji ma ciwo ana ta kawo su"


Babu yadda Rauda ta iya dole ta ƙara kwana a asibitin


Washegari hanya ta buɗe ta koma


Bayan sati ɗaya Umar yaji sauƙi sai ɗan abunda ba'a rasa ba, yayin da garin hankali ya kasa kwanciya


Dan kullum cikin ƙone-ƙone suke da hayaniya


Hakan yasa dole makaranta ta bada hutun gaggawa dan abun harya fara shafan ɗalubai


Ba yadda Umar beyi ba akan Tabari su taho tare amma taƙi


Dan bata son suna kasancewa tare a yanzu so take yi ta nisance sa ko dan ta hani zuciyar ta



Bayan  kwana uku da dawowarta,suna zaune tsakar gida ita da mama suna girkin dare


Wayar ta ce ke ta ƙara kuma taƙi ɗagawa dan numban Umar ne


Wani kiran ne ya kuma shigowa mama ta kalli wayar tace


"wai waye ne yike ta kiran ki ba zaki ɗaga ba?


Ta ɗauki wayar ta kashe tana ba mama amsa


"kamfanin mtn ne"


Dai-dai lokacin baba ya shigo, suka mai sannu da zuwa


Ya amsa yana duban Rauda


"kije kina da baƙo a waje"


"baƙo?


Ta tambaya a zuciyar ta amma a fili shuru tayi tana mamakin wani baƙo ne zezo wurin ta


Katse mata tunani baba yayi


"ko baki ji ba, nace kina da baƙo a waje"


Amsawa tayi da to, yayin da baba ya wuce


Mama tace

"baƙo kuma? Wanene?


Rauda tace

" Nima bansani ba mama, dan bamuyi da wani zezo ba, amma bari naje nagani "


Ta Ƙarasa faɗa tana Miƙewa


Dogon hijabi ta zura ta fito ƙofar gida


Ko da mamakin ta, Umar ta gani tsaye ya sha wata maroon ɗin Shadda


Tsaye tayi jikin ƙofa tana kallon sa yayi kyau sosai


Ƙarasa fitowa tayi tana mamakin yadda akai ya san gidan su


Shiko murmushi ya saki yana amsa gaisuwar da ta masa


Ganin har lokacin da mamaki a fuskar sa yasa yace


"ki dena mamaki dan kinganni a ƙofar a gidan ku, nabi kwatancan da kikamin ne na shekarun da suka wuce"


Gyara tsayuwarta tayi tana yi masa wani irin Kanno masu fassarori da yawa


Ta danne zuciyar ta tare da ɗan ɗaure fuskarta


"to ka kyauta, amma me ya kawo ka gidan mu? Kuma Ƙarasa wanda zaka aika ya kirani sai mahaifi na?


Murmushi ya kuma yi yace


"adoka ta musulunci idan zaka nemi yarinya ai sai ka fara tambayar izinin iyayen ta, kuma na tambayi baba ya bani izini innemeki"


Gajeren murmushi tayi wanda ya tsaya mata iya baki kawai wanda ya rasa gane ma'anar sa


"izinin nemana fa kace Umar? To wai ma in tambaye ka, wani neman da ga ciki?


Cikin rashin fahimta yace


"wani nemane kuwa banda na aure?


Murmushin ta kuma yi tana ɗan kaɗa kai


" Umar ke nan, akan mene zaka nemi izinin aurena batare da ka nemi soyayya ta ba?


Yana yin fuskar sa ya sauya zuwa damuwa


"Rauda, ina ce waɗannan abubuwan sun wuce, nasan fa kina sona har yanzu Meyasa zaki ta maida hannun agogo baya....


Katsesa tayi


"har yanzu ina son ka? A yaushe na faɗa ma haka?


"ki faɗa sau biyu, da rana ta farko da kika je asibiti, da kuma rana ta biyu da kika shigo ɗakin da daddare


Duk abunda kika faɗa inaji"


"yayi kyau da kaji Hakan, amma ka sani faɗin ina son ka bashi zesa na saurare ka har na kuma yin wata soyayyar da kai ba, Umar dan Allah ka nisanci rayuwa ta ka gogeni daga rayuwar ka na roƙeka kamar yadda ka roƙeni a baya"


Ta faɗa cikin damuwa zuciyar ta na harbawa


Idanuwan sa suka kaɗa


"Rauda wallahi ina ƙaunar ki,idan kika amince min a gobe zan iya turo iyayena ayi maganar aure dan ki tabbatar da da gaske nike, wallahi a yanzu banajin zan iya rayuwa babu ke kuma nasan kema kanki a yanzu kin fahimci Hakan"


"babu abunda na fahimta, kaje kanemi wata, dan yanzu ina da wanda nike so dan Allah karka ƙara zuwa inda nike"


Ze kuma yin magana ta shigo gida da sauri


Ɗaki ta shiga ta zauna kan kujera tare da kifa kanta wasu hawaye masu ciwo suna biyo kuncin ta


Mama ta shigo ɗakin dan taga wucewar ta


Zama tayi tana tambayar lafiya?


Share hawayen tayi tana faɗin babu komai


Mama ta girgiza kai tace

"bangane ba komai ba, hakanan zaki shigo kina kuka dan jin daɗi?


Waye ne wanda ya zo?


Wasu hawayen ne suka kuma gangarowa


" Umar ne"


Mama ta ce

"wani Umar?


Umar da kika sani na da, wanda ba mu taɓa haɗuwa ba


Mama ta ɗan buɗe ido da mamaki tace


"wannan na wayar me kama da Larabawa? To ya aka yi kuka haɗu har yazo nan ba kundena waya ba tun tuni?


Kwashe komai tayi ta faɗa mata


Mama tayi murmushi


" to miye abun damuwa har da kuka? Ince Umar shine wanda kike so,ban manta ba fa duk mazajen da kika tsaida da Allah beyi auran ba kin tsaida su ne kawai dan baki samesa ba, Nasha ganin ki kina kuka kuma nasan duk a kansa ne, to tunda yanzu Allah ya kawo sa ba sai ki ma Allah godiya ƙila shine alkhairin kuma mijin shiyasa duk Waɗan can da akasa ranar da su aka fasa kuma yanzu kin tabbata da gaske yike yi?


Rauda ta numfasa tace


"cewa yayi wai a gobe ze iya turo iyayen sa dan intabbatar da gaske yike yi"


Wani irin farin ciki ne ya lulluɓe zuciyar mama


"to ba shikenan ba, ai kin rama abunda ya miki kuma ya gane kuskurensa kawai ki kula sa ki kuma amince dan nasan maƙiya sai sun kusan mutuwa saboda baƙin ciki"


Kallon mama kawai take yi yadda lokaci ɗaya ta shiga farin ciki tabbas mama tayi gaskiya ƙila shine alkhairin shiyasa aka fasa da waɗancan amma Aasim fa?


Gabanta ne ya faɗi yayin da ta tuno sa





~ƴarfillo~.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*

         *AASHIQUE🌹*


                  🧞‍♂ 🧞‍♂

                     🧞‍♂

                   NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣1⃣



_Wannan Page naki ne *safnah* kiyi yadda kike so dashi_ 



~_Ina da wata buƙata kutayani da addu'a Allah ya biya min,ya cika min burina please_~


_8:50_🕒PM 

THU, JUN 20


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


"Zayyad me ya sami Umar? Ka faɗamin wani hali yake ciki?


Tayi mai tambayar cikin rawar murya da tsananin tashin hankali


Zayyad yace


"baki ji me nace bane? Accident yayi kuma duk kece sanadi, dan da kin saurare sa da Be shiga damuwar da ze fita hayya cin sa ba"


"inna lillahi wa inna ilaihi raji'un, ka kai ni asibitin da yike ka kaini in gansa dan Allah"


Ta faɗa tana runtse idanuwan ta da suka cicciko da hawaye masu zafin gaske


Be ƙara cewa komai ba ya buɗe mota ya shiga


Binsa tayi ta shiga jikin ta na tsuma zuciyar ta cike da tarin fargaba


Ya tada motar ya fige ta aguje


Idanuwan sa sun kaɗa sunyi ja


"duk mutumin da yayi maka laifi ya dawo yace ka yafe masa ai Be kamata kaƙi kula sa ba


Sanin kanki ne Umar ɗin da kika sani da, ba shi bane yanzu


Wani irin roƙo ne be yi miki ba? Wani irin haƙuri ne be baki ba? Amma duk kika nuna baki san yanayi ba?


Dafa kanta kawai tayi da yike cigaba da sarawa batare da ta ƙara tanka masa ba


Suna isa asibitin suka fito yayi gaba tana Binsa


Ƙofar emergency room ya murɗa ze buɗe


Wata nurse ta ƙara so wurin da sauri tana faɗin


"baiwar Allah kijira a fito dashi daga emergency room tukunna"


Zayyad ya kalli nurse ɗin yace


"baki ga tare dani take bane?


Sun kuyar da kai nurse ɗin tayi


"sorry doctor Naga doka ce ba a shi.....


Be jira jin me zata Ƙarasa cewa ba ya buɗe Ƙofar ya shige


Gabanta na faɗuwa ta kutsa kanta ciki


Kwance ta hango    Jikinsa duk bandeji, jikin ta na rawa ta Ƙarasa gaban gadon zuciyar ta na wani irin rawa


"Umar!


Ta Kira sunan sa,ko motsi Be yi ba ballantana ya amsa mata, idanuwan sa na rufe ruf


Zuba masa ido tayi, gani take yi kamar baya numfashi


Cikin tashin hankali da kiɗima ta fara jijjigasa tana faɗin


"Umar ka tashi, ka tashi dan Allah, Naji na haƙura"


Har lokacin ko motsi beyi ba


Kuka ta fashe da shi tana cigaba da jijjigasa


"na roƙeka katashi, kada ka tafi ka barni Umar"


Maganar ta ya fara ji tana ratsa kunnuwan sa


Ji yike yi kamar mafarki yike yi


"katashi Umar, dan Allah katashi wallahi na haƙura"


Ta kuma faɗa


Buɗe idanuwan sa yayi da suka yi masa nawi


Dishi-dishi ya fara ganin ta


Kafin ya ganta sosai,ita ko ganin ya buɗe idon yasa ta sauke wani nannauyan numfashi


"Rauda"


Ya kira sunan ahankali


Kasa amsawa tayi kallon sa kawai take yi


"Rauda ina son ki, dan Allah ki ce min kin haƙura da abunda nayi miki, ki amsa kin yafe mini"


Zuciyar ta tsinke,janyo kujera tayi ta zauna jin jiri-jiri ya fara ɗiban ta


Ze kuma magana ta katse shi


"Umar,na haƙura ya riga da ya wuce"


Ya Lumshe idanunsa yana faɗin


"nagode"


Hannu tasa ta share fuskar ta da tayi sharkaf da hawaye


Sannan ta ƙara matsawa kusa dashi


Tana kiran sunan sa


Kuma buɗe idanuwan sa yayi ya zuba su a kanta


"kayi haƙuri da jefa ka damuwa da nayi...


Girgiza kai yayi a hankali


"a'a Rauda, sam kada ki bani haƙuri na cancan ci fiye da abunda ma kikai min"


Ya faɗa da rauninniyar muryarsa


Kaɗa kai tayi tana kuma share fuskarta gaba ɗaya jikin ta ya mutu.


Miƙewa tayi tace


"zanta fi,anjima zan dawo"


Ta Ƙarasa faɗa tana niyyar juyawa


Ruƙo hannun ta yayi,ta juyo suka zuba ma juna ido


"kar ki tafi Rauda dan Allah,ina buƙatar ganinki a kusa dani"


Ta sauke ajiyar zuciya tace

"kayi haƙuri Nima bana jin daɗi ne, anjima zan dawo"


Ya girgiza kai

"a'a ki tsaya Zayyad ya duba ki, ki tsaya tare dani please"


Hannun ta ta zame tana girgiza kan itama


"a'a akwai wacce zata duba ni"


Bata jira jin me ze ƙara cewa ba tayi gaba,tana tafiya jiri na kwasar ta


Zayyad ya tashi da sauri ya tare ƙofar


"bafa ze yuwu ki tafi cikin wannan halin ba, tunda dai har kinzo asibiti muje induba ki"


Zatai magana Zayyad ya dakatar da ita


"kada ki ce zaki yi musu Rauda, dan Allah"


Numfashi ta sauke tana kaɗa kai dan ta ƙagara ta zauna ji take yi kamar zata faɗi


Zayyad ya dubi Umar ya ce


"bari muje na duba ta yanzu zan dawo"


Umar binsu da ido yayi kawai

Suka fita, wani office suka shiga ya nuna mata kujera ta zauna


"dame-dame kike ji yana damunki?


" ciwon kai, sai jiri da kuma ƙirji"


Ya jinjina kai, sannan yayi mata gwaje-gwaje


Nurses ya kira yace suzo su sa mata drip,da kuma allurai


Dole ta haƙura suka sa mata dan tana buƙata ita ma


Ta Kira Salma ta faɗa mata,ba'a fi minti ashirin ba Salma ta zo asibitin


Da daddare,tana zaune kan gadon asibitin ta tsura ma drip ɗin ido, gani take yi baya sauri dan kaɗan-kaɗan yike ɗiga, Allah Allah take yi ya ƙare su tafi


Zayyad ya shigo ɗakin yana yi mata ya jiki


Amsawa tayi da "dasauƙi"


Sannan ta ce

"kaɗan ƙara gudun ruwan bana so dare yayi sosai ba mu tafi ba"


Zayyad yace

"ai bayan wannan ma akwai wasu,dole tafiyar ki sai ta kai gobe da yamma saboda da alamu kinyi ta ciwon a tsattsaye"


Salma tace

"gaskiya gwara kitsaya ki samu sauƙi Ƙawa,kiyi haƙuri zuwa goben"


"Hakan ya kamata,Shima Umar yanzu muka dawo dashi ɗakin dake jikin wannan"


Bata ƙara cewa komai ba ta kwanta,


Bata daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗauke ta


Ƙarfe ɗaya na dare ta farka,a gigice


Sakamakon mafarkin da tayi wai Umar ya rasu


Lokacin Salma ta daɗe da yin bacci,zare abun ruwan tayi ta sauko ta fito


Babu kowa a harabar wurin ta windon ɗakin da yike ta hango sa


Murɗa ƙofar ɗakin tayi ta shiga ta Ƙarasa gaban gadon


Gabanta na faɗuwa ta dafa ƙirjinsa jin yana numfashi yasa ta sauke doguwar ajiyar zuciya tare zauna wa a kujerar dake gaban gadon


Ta tsura mai ido,kyakkyawar fuskar nan nasa tayi fayau, sai dogon hanci


"Umar!


Ta Kira sunan,da alamu bacci yike yi dan be amsa ba


Ta cigaba da kallon sa zuciyar ta na saƙo mata abubuwa da yawa


Tabbas ta san har yanzu tana ƙaunar sa, dan sonsa da banne acikin zuciyarta


Shine wanda ta fara so, kuma shi kaɗai ne wanda tayi ma so me tsanani


Gashi lokacin ta daɗe tana fatan zuwan sa na ranar da Umar ze ƙauna ce ta yazo, amma sai dai kash


Aasim,ya riga da ya danne komai, dan Shima tana sonsa amma bazata taɓa haɗa son da take yima Umar da wanda take yi masa ba


Umar ƙaunar sa daga Allah ne, dan shine ya jarabce ta


Hawaye masu ɗumi suka shiga gangaro mata


"Meyasa sai yanzu Umar? Me yasa kabari lokacin Dana daɗe ina jira ya wuce?


Meyasa?


Ta jingina bayan ta da kujerar tana runtse idanunta wasu sababbin hawayen na gangarowa


"kai ne burina, kai ne zaɓi na, kai ne wanda nayi fatan rayuwa dashi a matsayin miji na har abada, amma kabari lokaci ya wuce dan bazan iya janye alƙawarin da nayi wa Aasim ba, bazan iya ba!


Kuka me ƙarfi ne yaci ƙarfin ta, ta kifa kanta jikin gadon tana kuka me tsuma zuciya


Umar duk abunda ta faɗa yana ji, da fari farin ciki ne da jin daɗi ya mamaye zuciyar sa amma Aasim da ta ambata yasa jikin sa yayi sanyi


Waye shi? Wani irin alƙawari ta ɗaukar masa da take faɗin bazata iya karyawa ba?


Yayi wa kansa tambayoyin,da bayi da amsar su


Ita ko Rauda Miƙewa tayi ta koma, ɗakin da take


Ta kwanta,har lokacin ƙaunar sa ce ke kuma bin jinin ta


Ta dafa sai tin zuciyar ta da take yi mata nawi tace


"dan Allah kada ki bari ƙaunar Umar ta kuma tasiri a zuciyar ki, Aasim shine wanda ya cancan ce ki, shi ne ya sadaukar da rayuwar sa da komai nasa akan ki, Umar ko shine ya wulaƙanta ki a lokacin da kike neman kulawar sa"


***   ****  ****

Sunɗauki awanni suna gabzawa da manyan ifiritan, yayin da wasu daga cikin rauhanan sun ji ciwo sosai suka kuma sare


Aasim ne kaɗai har lokacin yike fafatawa dasu,duk da Shima ya galabaitan


Sarauniyar ifiritai tana zaune kan kujerar ta tana kallon abunda yike faruwa


Sai da tagama kallo tsaf, sannan ta cewa ifiritan su dakata


Dakatawar suka yi kuwa, yayin da Aasim da sauran suka tsaya suna mai da numfashi


Gurin yayi tsit,Sarauniyar da har lokacin idanuwan ta na kan Aasim tace


"nadaɗe banga jarumi irin ka ba,sannan kuma na daɗe banga sakarai irin ka ba wanda yike sadaukar da rayuwar shi dan kawai ya rayu da bil'adama wannan babban kuskure ne"


Aasim Shima da tun da ta fara maganar yike kallon ta yace


"a gareni Sam ba kuskure bane,kuma a shirye nike da inshiga kasadar da tafi wannan in har yin Hakan ze ƙara min kusanci da ita"


Murmushi Sarauniyar tayi yayin da tagama duba madubin tsafin ta


"tabbas kayi kuskure me girma da ka amince da bil'adama,sannan kuma zaka yi da na sani domin kuwa duk wannan wahalhalun da kake sha zasu tashi a banza"


Ta ɗan numfasa sannan ta cigaba da cewa


"kun aikata laifi dan kawai ku sami bayyana acikin mutane kuka shigo mana kogo kuka karya mana doka,amma duk da Hakan jarumtar da ka nuna zata sa inyi abunda bantaɓa yi ba


Wato inbada gudunmuwa wajen karya dokar da kakannina suka kafa, tabbas wannan tsumi dokace bama bari a ɗiba amma kuje na baku dama ku ɗiba iya wanda ze muku"


Wazirin ta ne ya zube yace

"ranki shi daɗe maƙiyanmu ne fa ko kin manta gabar dake tsakanin mu dasu ne?


Ta girgiza kai tace

" ban manta ba zundaj,amma kada ku ƙara taɓa su ku bar su su ɗiba"


Aasim murmushin jin daɗi yayi tare da rusunawa


"godiya muke sarauniya, Allah ya ƙara girma, haƙiƙa kina da taushin zuciya me cike da tausayi ubangiji ya shiga cikin lamarinki"


Jinjina kai kawai tayi tana nuna musu hanya


Suka wuce zuwa inda tsumin yike, tun da suka isa wurin Aasim ke murmushi


Ya shafa hannun sa wani ƙoƙo me Marfi ya bayyana yasa ya ɗiba


"Rauda yanzu zamu rayu ni dake cikin kwanciyar hankali batare da wata damuwa aranki ba"


Ya faɗa yana rufe ƙoƙon


Sai da suka gama ɗiba sannan suka juyo suka yi ma sarauniyar godiya


Har sun juya zasu wuce ta dakatar da su ta hanyar kiran Aasim


Waigowa yayi yana kallon ta batare da ya amsa ba


"aduk lokacin da danasani ya riske ka,ka kuma yi niyyar ɗaukar fansa kada ka manta wajen neman agajina"


Yayi murmushi yana jinjina kai


"nagode sosai amma nasan babu danasani a rayuwa ta"


Murmushi kawai tayi ta ɓace


Shiko futowa suka yi zuciyar sa nayi masa wani iri


Meyasa ake yi masa zancen yayi kuskure, shi dai yasan Rauda bazata juya mai baya ba, to shi ko wani danasani zeyi?


***   ***  ****


Washegari da sassafe Salma ta koma makaranta dan akwai test ɗin da zata yi


Rauda na kwance ita kaɗai, Umar kasa haƙuri yayi ya taso ya shigo ɗakin


Ta yunƙura tana kallon sa ganin yadda ya shigo yana bin bango


"lafiya ka fito kai da kake kwance?


Zaunawa yayi yana mai da numfashi


"nakasa haƙuri ne Rauda, inaso in ganki shiyasa"


Kallon sa tayi sosai, sannan tace


"amma ai da ka aiko an kirani"


"kema baki da lafiyar ai"


Ya faɗa, ta girgiza kai


"amma ai ban kai ka jin jiki ba ko?


Ya jinjina kai


"ya jikinna ki? Yanzu dame-dame kike ji yana damunki?


"naji sauƙi babu abunda ke damu na yanzu,ya naka jikin?


" Nima Naji sauƙi alhamdulillah, me kike so a kawo miki ki karya?


Ya tambaya


Dai-dai lokacin Zayyad ya shigo ɗakin ganin Umar yasa yayi sororo yace


"kai kuma fa? me ya fito da kai?


Umar yace


"bansani ba, me Kaga inayi?


Zayyad ya Ƙarasa shigowa yana faɗin


"kana fama da kanka shi ne kake ƙoƙarin yin jinya?


Ya Ƙarasa faɗa yana ajiye abun kari


Rauda tace

"dan Allah kabarni in tafi yanzu tunda Naji sauƙi abar ragowar alluran haka"


Ta faɗa tana duban Zayyad


Zayyad ɗan murmushi yayi yace


"ki kwantar da hankalinki anjima kaɗan zaki wuce"


Bata ƙara cewa komai ba,ta ɗauki wayar ta da ke ƙara


"hello Salma kintaho ne?


Daga can Ɓangaren Salma tace


" wallahi Rauda na taho babu hanya, baki ga yadda matasa suke ta zanga-zanga ba da Manyan makamai "


Rauda tace

" subhanallah zanga-zanga kuma? Na mene?


"Nima bansani ba amma nasan baze wuce na siyasa ba, bari in koma dan Naga faɗa yana so ya kaure a wurin"


Rauda ajiye wayar tayi cikin damuwa


Da yamma tana tsaye tana kallon tvn dake manne jikin bango


Yadda faɗan ya kaure ake nunawa, ga sojoji nan ta ko ina


Nurse ce ta shigo


Rauda tace

"wai yanzu ko kaɗan babu hanyar da mutum ze bi ya koma inda yike"


Nurse ɗin tace


"wallahi babu, dan muma tun rana aikin mu ya ƙare amma waɗanda zasu amshemu basu zoba ga kuma Waɗan da aka ji ma ciwo ana ta kawo su"


Babu yadda Rauda ta iya dole ta ƙara kwana a asibitin


Washegari hanya ta buɗe ta koma


Bayan sati ɗaya Umar yaji sauƙi sai ɗan abunda ba'a rasa ba, yayin da garin hankali ya kasa kwanciya


Dan kullum cikin ƙone-ƙone suke da hayaniya


Hakan yasa dole makaranta ta bada hutun gaggawa dan abun harya fara shafan ɗalubai


Ba yadda Umar beyi ba akan Tabari su taho tare amma taƙi


Dan bata son suna kasancewa tare a yanzu so take yi ta nisance sa ko dan ta hani zuciyar ta



Bayan  kwana uku da dawowarta,suna zaune tsakar gida ita da mama suna girkin dare


Wayar ta ce ke ta ƙara kuma taƙi ɗagawa dan numban Umar ne


Wani kiran ne ya kuma shigowa mama ta kalli wayar tace


"wai waye ne yike ta kiran ki ba zaki ɗaga ba?


Ta ɗauki wayar ta kashe tana ba mama amsa


"kamfanin mtn ne"


Dai-dai lokacin baba ya shigo, suka mai sannu da zuwa


Ya amsa yana duban Rauda


"kije kina da baƙo a waje"


"baƙo?


Ta tambaya a zuciyar ta amma a fili shuru tayi tana mamakin wani baƙo ne zezo wurin ta


Katse mata tunani baba yayi


"ko baki ji ba, nace kina da baƙo a waje"


Amsawa tayi da to, yayin da baba ya wuce


Mama tace

"baƙo kuma? Wanene?


Rauda tace

" Nima bansani ba mama, dan bamuyi da wani zezo ba, amma bari naje nagani "


Ta Ƙarasa faɗa tana Miƙewa


Dogon hijabi ta zura ta fito ƙofar gida


Ko da mamakin ta, Umar ta gani tsaye ya sha wata maroon ɗin Shadda


Tsaye tayi jikin ƙofa tana kallon sa yayi kyau sosai


Ƙarasa fitowa tayi tana mamakin yadda akai ya san gidan su


Shiko murmushi ya saki yana amsa gaisuwar da ta masa


Ganin har lokacin da mamaki a fuskar sa yasa yace


"ki dena mamaki dan kinganni a ƙofar a gidan ku, nabi kwatancan da kikamin ne na shekarun da suka wuce"


Gyara tsayuwarta tayi tana yi masa wani irin Kanno masu fassarori da yawa


Ta danne zuciyar ta tare da ɗan ɗaure fuskarta


"to ka kyauta, amma me ya kawo ka gidan mu? Kuma Ƙarasa wanda zaka aika ya kirani sai mahaifi na?


Murmushi ya kuma yi yace


"adoka ta musulunci idan zaka nemi yarinya ai sai ka fara tambayar izinin iyayen ta, kuma na tambayi baba ya bani izini innemeki"


Gajeren murmushi tayi wanda ya tsaya mata iya baki kawai wanda ya rasa gane ma'anar sa


"izinin nemana fa kace Umar? To wai ma in tambaye ka, wani neman da ga ciki?


Cikin rashin fahimta yace


"wani nemane kuwa banda na aure?


Murmushin ta kuma yi tana ɗan kaɗa kai


" Umar ke nan, akan mene zaka nemi izinin aurena batare da ka nemi soyayya ta ba?


Yana yin fuskar sa ya sauya zuwa damuwa


"Rauda, ina ce waɗannan abubuwan sun wuce, nasan fa kina sona har yanzu Meyasa zaki ta maida hannun agogo baya....


Katsesa tayi


"har yanzu ina son ka? A yaushe na faɗa ma haka?


"ki faɗa sau biyu, da rana ta farko da kika je asibiti, da kuma rana ta biyu da kika shigo ɗakin da daddare


Duk abunda kika faɗa inaji"


"yayi kyau da kaji Hakan, amma ka sani faɗin ina son ka bashi zesa na saurare ka har na kuma yin wata soyayyar da kai ba, Umar dan Allah ka nisanci rayuwa ta ka gogeni daga rayuwar ka na roƙeka kamar yadda ka roƙeni a baya"


Ta faɗa cikin damuwa zuciyar ta na harbawa


Idanuwan sa suka kaɗa


"Rauda wallahi ina ƙaunar ki,idan kika amince min a gobe zan iya turo iyayena ayi maganar aure dan ki tabbatar da da gaske nike, wallahi a yanzu banajin zan iya rayuwa babu ke kuma nasan kema kanki a yanzu kin fahimci Hakan"


"babu abunda na fahimta, kaje kanemi wata, dan yanzu ina da wanda nike so dan Allah karka ƙara zuwa inda nike"


Ze kuma yin magana ta shigo gida da sauri


Ɗaki ta shiga ta zauna kan kujera tare da kifa kanta wasu hawaye masu ciwo suna biyo kuncin ta


Mama ta shigo ɗakin dan taga wucewar ta


Zama tayi tana tambayar lafiya?


Share hawayen tayi tana faɗin babu komai


Mama ta girgiza kai tace

"bangane ba komai ba, hakanan zaki shigo kina kuka dan jin daɗi?


Waye ne wanda ya zo?


Wasu hawayen ne suka kuma gangarowa


" Umar ne"


Mama ta ce

"wani Umar?


Umar da kika sani na da, wanda ba mu taɓa haɗuwa ba


Mama ta ɗan buɗe ido da mamaki tace


"wannan na wayar me kama da Larabawa? To ya aka yi kuka haɗu har yazo nan ba kundena waya ba tun tuni?


Kwashe komai tayi ta faɗa mata


Mama tayi murmushi


" to miye abun damuwa har da kuka? Ince Umar shine wanda kike so,ban manta ba fa duk mazajen da kika tsaida da Allah beyi auran ba kin tsaida su ne kawai dan baki samesa ba, Nasha ganin ki kina kuka kuma nasan duk a kansa ne, to tunda yanzu Allah ya kawo sa ba sai ki ma Allah godiya ƙila shine alkhairin kuma mijin shiyasa duk Waɗan can da akasa ranar da su aka fasa kuma yanzu kin tabbata da gaske yike yi?


Rauda ta numfasa tace


"cewa yayi wai a gobe ze iya turo iyayen sa dan intabbatar da gaske yike yi"


Wani irin farin ciki ne ya lulluɓe zuciyar mama


"to ba shikenan ba, ai kin rama abunda ya miki kuma ya gane kuskurensa kawai ki kula sa ki kuma amince dan nasan maƙiya sai sun kusan mutuwa saboda baƙin ciki"


Kallon mama kawai take yi yadda lokaci ɗaya ta shiga farin ciki tabbas mama tayi gaskiya ƙila shine alkhairin shiyasa aka fasa da waɗancan amma Aasim fa?


Gabanta ne ya faɗi yayin da ta tuno sa





~ƴarfillo~.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: *🌹JINNUL*

          *AASHIQUE🌹*

                    🧞‍♂🧞‍♂

                       🧞‍♂

                        NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*


🅿AGE 📕 2⃣2⃣


_Wannan Page nakane *ASLAM* _haƙiƙa ka kasance ɗan albarka wanda aduk sanda na tuna nike jin sanyi ko da ko ina cikin damuwa ne, ina son ka sosai yarona Allah ya albarkaci rayuwar ka_

*(nasan bestie zata ce yaro ko zuwa duniya beyi ba kin damemu da aslam aslam, to ki kwantar da hankalin ki duk da ban riga na haife sa ba amma ƙaunar sa na zuciya ta)*


_Ako da yaushe bana gajiya da yi muku fatan alkhairi masoyana Allah ya bar zumunci_


*_Sannan ina me baku haƙuri sakamakon daɗewa da nike yi banyi typing ba saboda ƙarancin lokaci, na yanke shawarar ringa yi akai-akai amma sai dai zaku rinƙa gani ba yawa nagode_*


_8:32_🕒AM

WED,JUL 3


_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Haka ya cigaba da kasancewa Umar kullum sai yazo gidan su Rauda, gaba ɗaya ya ajiye aikin sa dan ya tattaro ya dawo Kaduna kuma yayi ɗamarar baze koma Abuja ba har sai ya shawo kanta


Kamar kullum yana tsaye jikin motar sa yana jiran yaga wuce war yaro ya aika ya kira ta dan yayi ta kiran wayar a kashe


Be kai ga samun yaron ba sai gata ta fito zata amso candle


Sam bata lura da shi ba dan wurin yayi duhu babu haske


Cikin sauri take tafiya aiko tayi tintiɓe da wani dutse


Ƴar ƙara ta saki tana duƙawa da sauri


Shiko Umar ji yayi kamar shi yayi tuntuɓen ƙarasowa yayi da sauri  


"subhanallah sannu, baki ji ciwo ba?


Yayi mata tambayar, ɗago wa tayi dan sai lokacin ta lura dashi


Duk da duhun dake wurin be hana ta ganin kyakkyawar fuskar sa ba ma'abociyar haske da kwarjini


Ya tsugunna yana haska fitilar wayar sa


Ganin jini a ɗan yatsan ta yasa yaji wani yarrr


Handkerchief ɗin sa ya zaro da sauri yana ƙoƙarin goge mata


Miƙewa tayi idanuwan ta a kansa


Amma takasa ce mai komai dan duk sanda ta gansa jikin ta mutuwa yike yi


Shima ya miƙe yana faɗin

"muje chemist a duba ki"


Girgiza kai tayi cikin muryanta da tayi ƙasa tace


"a'a ai ba wani ciwo bane babba da sai anje chemist"


Yayi shuru yana kallon ta yana jin ƙaunar ta na wani irin fizgar sa


Ganin yayi shuru yasa ta gyara takalmin ta tana ƙoƙarin wucewa


"Rauda!


Ya kira ta da wani irin salo wanda saida tsigar jikin ta tashi


Tsayawa tayi tare da zuba masa fararen idanunta masu ƙara masa ƙaunar ta


Guntun numfashi ya sauke yace


" Rauda Allah ma da halicce mu muna yi Masa laifi mun roƙesa gafara ya kuma yafe mana, ballan tana imu-imu ƴan Adam


Kisani ko Abaya wallahi ina sonki, amma bansan me ya hanani zuwa wurin ki ba, wani zubin sai na ɗauki waya zan kira ki sai inji nakasa, kuma ko wulaƙancin da nayi miki Abaya ba da son raina bane


Da kin kirani zanji babu wacce nike jin haushi a duniya sai ke shiyasa nike gaya miki magan ganu marasa daɗi


Amma wallahi da na kashe, zanji nayi nadama abun kuma ze yi ta damuna


Kiyi haƙuri ki amince dani dan Allah"


Ya Ƙarasa faɗa muryar sa na raunanewa


Maganar Aasim ce ta faɗo mata


_"Kisani ƙaunar da nike miki bazata taɓa bari inbar wani ya raɓeki ba,ke tawa ce ni kaɗai"_


To Kodai yana da hannu wajen hana Umar zuwa a wancan lokacin?


Tayi wa kanta tambayar


Ji tayi kanta yayi mata nawi, ta Lumshe idon ta tana ambaton sunan Allah


Tafi minti biyu a haka daga bisani ta buɗe su ta kuma ɗaura su a kanta


Ya Rame sosai,kallo ɗaya zaka masa ka gano baya cikin kwanciyar hankali


Tausayin sa gami da ƙaunar sa suka sake mamaye zuciyar ta


Ajiyar zuciya ta sauke tace


"shikenan zanyi tunani,amma ka rage tada hankalin ka"


Murmushi yayi yana jin zuciyar sa cikin farin ciki


"hankalina baze taɓa kwantawa ba har sai kin amince dani,na kuma gode, sannan zuwa yaushe ne zaki gama tunanin?


"nan da sati ɗaya"


Ta faɗa


Ya jinjina kai


"Allah ya kai mu Allah kuma yasa kiyi tunanin da zanji alkhairi"


Bata ƙara cewa komai ba, ta juya zata koma gida dan bazata iya Ƙarasa wa shagon ba



"dan Allah zan kiraki anjima ki ɗauka"


Shige wa tayi tana tunanin yadda zata ɓullowa al'amarin


Dole tana buƙatar wanda ze bata shawara amma wa zata gaya mawa sirrinta?


Anty ummi zuciyar ta tabata amsa


Ita ce ƴar uwar ta, wacce zasu kashe su rufe batare da wani ya sani ba


Washegari da wuri ta shirya ta tafi gidan Anty ummi


Da sallama ta shiga gidan, mijin ta ne ya amsa yana yaye labulen falon dan ya gama shiri ze tafi kasuwa


Ganin ta yasa ya faɗaɗa fuskar sa


"auta kece da safiya haka?


Murmushi tayi tana faɗin


" ina kwana?


"Lafiya lau ya bata amsa yana bata hanya"


Shiga tayi ta zauna kan kujera tana kallon Anty ummi dake sanyawa hanif jakar makaranta


"yaro na yakake?


Ta faɗa yayin da take maida kallon ta ga hanif


"lafiya Anty kin kawo min sweet?


Tayi murmushi tana girgiza kai


" a'a my hanif ina sauri ne shiyasa amma zan kawo maka next time kaji?


Gyaɗa kai yayi yana bin baban sa


Anty ummi tace


"ya mama? Ince dai lafiya dannasan bakya fita da sassafe haka"


Rauda tace


"lafiya lau"


Anty ummi ta janyo flask tana niyyar zuba ruwan zafi


Dakatar da ita Rauda tayi


"kinga inni zaki zuba mawa karma ki zuba dan bana jin yunwa, magana nazo muyi"


Anty ummi ta kalle ta sosai


"magana kuma?


Rauda ta jinjina kai

" eh"


Anty ummi ta ajiye kofin tana cewa


"to inajinki nasan baze wuce kuɗi kike so ba"


Rauda ta sauke numfashi


"a'a Sam ba maganar kuɗi bace, ina cikin damuwa ne kawai na kuma rasa yadda zanyi"


Jin kalmar damuwa yasa Anty ummi ta gyara zama tare da tattara hankalin ta guri ɗaya


"damuwa kuma Rauda? Faɗa min me ke faruwa"


Ita ta gyara zaman ta tace


"zan faɗa miki amma inaso ki natsu sosai ki fahimce ni"


Anty ummi ta jinjina kai alamar taji


Rauda bata ɓoye mata komai ba tun daga ranar da ta fara ganin Aasim har zuwa tafiyar sa


Wani irin kallo Anty ummi take yi mata na wacce ta fara taɓuwa


Rauda ta numfasa tare da ƙarawa da cewa


"ki dena min kallon wacce ta fara taɓuwa Anty ummi, wallahi da gaske ne, kiyarda da abunda na faɗa miki"


Anty ummi ta sauke doguwar ajiyar zuciya


"bawai banyadda da abunda kika faɗa bane, a'a na yarda dan jinnul aashique mun san kina dashi amma tabbas baki da hankali


Dan Inba marar hankali ba babu wacce zata yi abunda kika yi, ace kiyar da kirinƙa rayuwa da jinnu har ki amsa mai zaki rayu dashi har abada kuma ki ɓoye mana"


Rauda gwauron numfashi ta sauke tace


"nidai Anty ummi kiga ya min yadda zanyi bagashi yanzu na faɗa miki ba, ki gaya min ya zanyi da Umar,ina tsananin ƙaunar sa har yanzu amma idan natuna wulaƙancin da Yamin Abaya sai inji duk ya fita a raina"


"ke yanzu har ma kya ga laifin Umar,ai wallahi kidena ganin laifin sa dan bayi da laifi kwata-kwata bayin kansa bane"


Anty ummi ta faɗa zuciyar ta cike da jimami


Rauda tace

"to yanzu yakike ganin zanyi?


Numfasawa Anty ummi tayi tare da nisawa tsayin mintoci


Daga bisani tace


"aganina tunda shi Aasim ɗin bada mugunta yazo miki ba ki kula Umar ɗin kucigaba da soyayya


Idan ya dawo sai ki basa haƙuri kice ya bar ki auri Umar, shi kuma ya cigaba da rayuwa dake a ɓoye, ina ganin Hakan itace hanya me sauƙi tunda Shima yana sonki"


Rauda ta Lumshe idanuwan ta da suka kaɗa saboda damuwa tace


"da wuya ya yadda, dan yana sona fiye da yadda kike tunani"


Numfashi Anty ummi ta kuma sauke wa


"dolen shi ma ya yarda dan babu inda aka ce aljan da mutum suyi rayuwa, kina ganin Gorin da ake yi miki akan rashin aurannan dan haka kada ki bari Umar ya kubce miki


Idan ma be yadda ta sauƙi ba ai sai aje gurin malamai ya rabu dake ta tsiya


Rauda ta girgiza kai

"Anty ummi ba zaki gane ba, Aasim ba kamar wanda kike tunani bane, kuma wallahi inajin tausayin sa a kaina fa......


Katseta Anty ummi tayi


" kinga Rauda kiyi abunda nace miki"


Ta kaɗa kai kawai amma ita ta san akwai babbar ƙura a gaba


Koda ta dawo gida haka ta wuni babu sukuni


Da daddare tana zaune abun duniya ya haɗu ya cunkushe mata kai


Tabbas dole tabi shawarar Anty ummi


Wayar ta ta ɗauko ta danna numban Umar


Kiran Nashiga ya katse, sai ga nashi ya shigo




~ƴarfillo~.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*🌹JINNUL*

          *AASHIQUE🌹*

                    🧞‍♂🧞‍♂

                       🧞‍♂


                       NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣3⃣


_Wannan Page ɗin nakine *khadija* marubuci yar ~*ashe kece*~_


_Tare da *khadija hydar* young novelist_


_Na sadaukar dashi gare ku kuyi yadda kuke so dashi_


_12:15_ AM

SUN,JUL 7


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Tsura ma wayar ido tayi tana kallon numban sa ta fito ɓaro-ɓaro


Sai da ta kusan tsinkewa sannan ta ɗaga,tare da karawa a kunnen ta


Sassanyar Sallamar sa ce ta karaɗe kunnen ta


Ta Lumshe ido a zuciyar ta tana faɗin


"komai nasa na daban ne"


Sai da yayi sallama sau uku sannan ta amsa


"ya kike? Ina fatan kina cikin ƙoshin lafiya?


Shuru tayi batare da ta bashi amsa ba


"chuchu!


Ya faɗa,jikin ta ne ya ƙara yin sanyi


Dan ko Abaya idan ya kira ta da chuchu wani iri take ji


"bakya jina ne chuchu?


Ajiyar zuciya ta sauke tace


"Umar ka tabbata da gaske kake yi yanzu kana sona,kuma zaka aurani?


Daga can Ɓangaren Umar tashi yayi daga kwancen da yike yana bata amsa


"na tabbata mana chuchu,wallahi a shirye nike da in aure ki koda kuwa anan da sati ɗaya ne"


Hmmmmmmm ta kuma sauke ajiyar zuciya


"shikenan idan da gaske kake yi inaso inga alama idan kuma bada gaske kake yi ba dan Allah kada ka kuma cutar da zuciya ta"


Wani irin farin ciki ne ya mamaye zuciyar sa


"da gaske chuchu? Yanzu komai ya wuce a wurin ki?


Ɗan murmushi tayi tace


" ya wuce amma dan Allah Jaana......


Sai kuma ta kasa Ƙarasa wa dan bata san sanda sunan Jaana ya fito daga bakin ta ba


Shiko Umar wani farin cikine ya ƙara lulluɓesa


"dan Allah me Rauda? Ki faɗi kome kike so wallahi zanyi miki shi a yanzu Ba tare da na ɓata lokaci ba"


Yanayin yadda yayi maganar ya tabbatar mata da ya shiga farin ciki


"dan Allah kada ka kuma cutar da zuciya ta, idan ka kuma yi min abunda kayi Abaya ina tabbatar maka da zan iya rasa raina......


Katseta yayi da sauri


"ba sai kin roƙe ni ba Rauda a yanzu bani da wacce nike so sama dake acikin zuciya ta,kuma ina me tabbatar miki da ba zaki sameni me kuma sanya ki damuwa ba, a yanzu buri na inga nasa ki farin ciki"


Wasu guntayen hawaye ne suka biyo kuncin ta wanda ta rasa na menene su


Na farin ciki ne? Ko kuma na tarin tunanin da ya cunkushe mata ƙwaƙwalwa


"Umar kasan Kaine wanda nike so kai ne zaɓin zuciya ta, me yasa kayi min abunda kayi Abaya me yasa?


Ta faɗa muryarta na raunanewa


Umar ya sauke dogon numfashi yace


"dan Allah ki dena tuna baya Rauda, na tabbata a yanzu son da nike miki ya ninka wanda kike min sau dubu"


Share hawayen tayi tace


"shikenan zan kwanta sai da safe"


"shikenan chuchu kiyi bacci me daɗi ina sonki"


Ya faɗa da murmushi a fuskar sa


Ajiye wayar tayi zuciyar ta na tambayar ta


"anya kin kyauta wa kanki kuwa Rauda? Ki tuna Aasim da ya bar ahalinsa matsayin sa da komai nasa akan ki, shin kina ganin kinyi masa dai-dai? Ya tafi yana fafutukar yadda ze rayu dake amma ke zaki ci amanar sa?


Ta karkaɗa kanta da sauri wasu sabbin hawayen na ciko idanuwan ta


"ban kyauta ba, ban kyautawa Aasim ba"


Ta faɗa cikin damuwa


"to idan baki amince kin auri jinsin ki ba, haka zaki ƙare rayuwar da jinsin da ba naki ba? Kuma Umar shine wanda kike so"


Wani sashe na zuciyar ta ya faɗa,


"idan Aasim ya samo abunda yaje nema fa, na bayyana acikin jama'a, baki da hujjar da zaki ce ya barki kiyi aure tunda dai Shima ze iya rayuwa dake a matsayin mutum batare da kowa ya sani ba"


Kanta ne ya Sara dan gaba ɗaya tunanin ta ya burki ce


Kwantawa tayi a kujerar da take zaune tana faɗin


"ya Allah ka taimake ni, bansan yadda zanyi Ba"


A haka bacci ɓarawo ya sace ta


Shiko Umar suna gama waya alwala ya ɗauro ya gabatar da nafiloli sannan ya ɗaga hannayen sa yana godiya ga ubangiji,yana kuma roƙon Allah da ya kaɗe duk wani sharri da ze sa ya ƙuntata mata


***   ****   *****


Zaune suke cikin Sahara suna tattauna yadda suka yi gwaji akan bayyana cikin jama'a


Wani daga cikin rauhanan yace


"ni fa a suffar mace na bayyana, na yi shigar kaya masu kyau na bayyana a wata kasuwa


Idan Kaga yadda mazen bil'adama suke kallo na kai kace haɗiye ni zasu yi


Ina jin wani yana cewa

"wannan kyakkyawar budurwar sai kace ƴammatan aljanna"


Be san garjejen ƙaton rauhani bane"


Suka fashe da dariya wani yana cewa


"amma kai ko ka iya iskanci wallahi, ni a suffar almajiri na bayyana a wurin wani cin a binci kuma a suffar yaro


Wata mata da ta ganni sai da ta kusan yin kuka


Wai ji ɗan ƙaramin yaro amma yana neman abunda zeci bata san ƙila tun kan a haifi iyayen ta nike duniya ba"


Dariya suka kuma sawa cike da nishaɗi


Aasim ko na zaune ya jingina da dutse yana kallon su


Jefi-jefi ya kan yi murmushi idan suka faɗi abun dariya


"Aasim kai kowa yana bada labari amma ka zauna kayi shuru, lafiya dai ko?


Ɗaya daga cikin rauhanan ya tambaya


Suka maida hankalin su kansa suna jiran jin me zece


" babu komai"


Ya faɗa


Rauhanin dake fuskantar sa yace


"a'a akwai komai mana, nasan baze wuce tunanin bil'damar ka kake yi ba, to ka kwantar da hankalinka mana saura wata ɗaya fa mu koma, musha biki"


"aikuwa dan mune nan abokan ango"


Wani Rauhanin ya faɗa, wani kuma yace


"Nikuma nine zan zama waliyyi"


Dariya suka kuma sawa


Jazmi da tunda suka haɗu da Aasim suka zama abokai yace


"abokina a wace ƙasa zaka ci amarcinne? Dan nasan yadda ka zaƙu muna komawa zaka yi mata maganar aure"


Har lokacin dariya suke yi


Aasim Miƙewa yayi yana murmushi


"ni kunbi kun cika min kunne da surutu bari in baku wuri"


Jazmi dariya yayi yace


"afuwan fa mun manta da yarima ne a wurin, wanda baya son haya niya"


Be kuma saurarar su ba ya wuce  can nesa dasu kaɗan ya zauna


Yana kallon yadda iska ke kaɗa saharan


Gaba ɗaya akwanakinnan tunanin ta ya hana sa sukuni, yayi tsananin rashin ta


Ya Lumshe ido yana hango kyakkyawar fuskar ta


"habibty ina tsananin rashin ki,nasan kema kina can kina tunani na, ke ce rayuwa ta habibty"


Ya faɗa cikin tsananin begenta


Motsi yaji a kusa dashi


Ya buɗe idonsa yana kallon inda yike jin motsin


Wata maciji ya ce,me kyau jikin ta fari sol


Hannu ya miƙa mata yace


"kyakkyawar maciji ya, zo inganki"


Macijiyar ta tsura mai ido amma ta kasa matsawa daga inda take


Ƙara kallon ta yayi, sai lokacin ya lura ciwon dake jikin ta


Cikin tausaya wa,ya ɗauko ta yana duba ciwon sosai taji


"ohhh sannu,ashe rauni kikaji, bari in sami ki magani kinji?


Abul simnan ya ƙara so wurin ya zauna


" Aasim ina ka samo maciji ya kuma?


Aasim yayi murmushi yana sama ta maganin


"anan na ganta,taji rauni"


Abul simnan ya jinjina kai yace


"ka kyauta da ka taimaka mata"


Har lokacin da ragowar murmushi a fuskar sa idanuwan sa kuma na kan Macijiyar


"na sa miki magani kinji, kiyi haƙuri zaki samu lafiya"


Ya Ƙarasa faɗa yana ajiye ta a ƙasa


Ta wuce


Ya maida kallon sa ga Abul simnan da yike kallon sa


"kana da kyakkyawar zuciya Aasim"


Aasim ya kuma murmushi


"kullum haka kake cewa Abul simnan"


Abul simnan ya jinjina kai


"da gaske nikeyi kana da kyakkyawar zuciya shiyasa nike tausaya maka"


Aasim ya maida kallon sa ga saharar dake kaɗawa


"kai ma kana da kyakkyawar zuciya,ina kuma godiya da yabo na da kake yi a koda yaushe"


**** ***** ******


Da safe, tana zaune tana tsakurar abun kari dan Sam bata jin cin komai


Wayar tace ta fara ƙara, ta ɗauka ta dubawa Umar ne


Ɗauka tayi tare da karawa a kunnen ta


Tana sallama


Daga can Ɓangaren Umar ya amsa yana faɗin


"barka da safiya chuchu,ina fatan kin tashi lafiya"


"lafiya lau"


Ta bashi amsa


Ya jinjina kai yace


"masha Allah Naji daɗi da Naji Hakan, tun ɗazu naso in kira ki sai nayi tunanin baki tashi ba"


Tayi ɗan murmushi dan jin muryar sa damuwar da ta cunkushe zuciyar ta ta rage


_~Ƴarfillo~_.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: *🌹JINNUL*

          *AASHIQUE🌹*

                    🧞‍♂ 🧞‍♂

                       🧞‍♂

                      

                        NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


✍✍✍✍✍✍✍

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*

✍✍✍✍✍✍✍



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*


Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣4⃣


_Wannan Page nakine *maman isqah* kin kasance me dogon sharhi a duk lokacin da nayi posting ina matuƙar jin daɗin Hakan Allah ya bar zumunci_


*_Fatan alkhairi_*

_Ga *princess mazadu* ina miƙa gaisuwa_



_9:48_🕒 AM

MON, JUL 8


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


"yau na tashi cikin farin ciki sakamakon wani kyakkyawan mafarki da nayi"


Umar ya faɗa


Rauda tace

"mafarki? Mafarkin me?


Daga can Ɓangaren Umar gyara zama yayi yana ɗan jingina da kujerar da yike zaune


"mafarki nayi munyi aure,kin haifa min kyawawan yara ƴan uku, masu kama da ke"


"ƴan uku fa? Amma a mafarkin naka na mutu ko?


Dariya Umar yayi yace


"dan kin haifi ƴan uku kuma sai ki mutu?


Ras na ganki kina ta yi musu wasa"


Wani murmushin ta kuma yi


"a'a nikam bazan iya haifar ƴan uku ba"


"zaki iya mana chuchu, ke fa jaruma ce"


Ta girgiza kai kamar yana ganin ta


"Allah bazan iya ba"


Jin tana amsa mai faran-faran yasa yaji ya ƙara shiga cikin nishaɗi


"inma ba zaki iya ba, ranar haihuwar sai mu raba in haifi biyu ki haifi ɗaya"


Dariya tayi tace


"to shikenan Allah ya nuna mana lokacin"


Amin ya faɗa haɗi da cewa


"wa yaga Umar na naƙuda, ai inaga duk faɗin garin Abuja sai sun taru"


Dariya ta kuma yi sosai, Shima ya taya ta


Yana cigaba da cewa

"Allah da gaske"


Rausayar da kanta tayi tace


"kawai dan kana rago"


"ke haihuwa fa, cap ai kudai mata sai dai mu muku fatan shiga aljannah amma zahiri kuna mugun ƙoƙari"


Ajiyar zuciya ta sauke, dan tunda ta fara jin muryar sa taji natsuwa na saukar mata


Tabbas ƙaunar sa daga allah ce


Katse mata gajeren tunanin da tafi yayi ta hanyar kiran sunan ta


"Rauda!


Ta kuma sauke ajiyar zuciya gami da amsawa


" na'am "


"kin karya?

Ya tambaya


" ina kan karyawan"


"ook to kigama sai in kuma kira, ko inzo yanzu ne?


Ta ajiye kofin tea ɗin da ya gama hucewa tace


" yanzu kuma? Safiya ce fa


Umar yace

"na sani kawai ina buƙatar inganki ne"


Murmushi tayi tace

"a'a kadai bari sai da yamma, ko da daddare"


Yace

"to shikenan Allah ya kai mu ki kula min da kanki"


"nagode"

Ta faɗa tana ajiye wayar


Ranar wuni tayi cikin farin ciki dan firar da suka yi ce kawai take mata yawo a kunne


Ya kira ta yafi sau biyar


Sai dai data tuna Aasim sai taji Gabanta ya faɗi


Tunda ga wannan ranar wata soyayya me ƙarfi ta ƙara shiga tsakanin su


Koda yaushe suna manne a waya dan ya koma Abuja


Amma duk weekend sai yazo Kaduna ya ganta


Mama ba ƙaramin farin ciki ta shiga ba


Ganin yadda su umma suke nuna hassadar su ƙarara


Dan duk wanda yaga Umar sai yayi mamaki ga kuɗi ka ga kyau ga kwarjini, duka Allah ya haɗa masa


Yau Asabar, tun ƙarfe huɗu Umar ya taso kuma tunda ya taso suke waya


Fira suke yi sosai me cike da annashuwa


Mama ta fito daga uwaɗɗaka tana faɗin


"wai ni Rauda yau wayar nan ba zata ƙare bane? Muna da aiki fa ga yamma nayi"


Murmushi Rauda tayi tana yin ƙasa da muryar ta tace


"mama na min magana, bari zan kira ka"


Tana gama faɗa ta kashe wayar tana duban mama dake ta zuba murmushin jin daɗi


"mama me za'a dafa ne?


Mama tace

"soyayya da mai da yaji"


Rauda tayi dariya tana faɗin


"kai mama"


Mama ma dariyar tayi tace

"eh mana, ace waya anfi ƙarfin awa ana yin ta"


Ƙasa Rauda tayi da kanta cike da jin kunya tana tura mai saƙo


_zamu ɗaura girki yanzu,Allah ya tsare hanya ya kawo ka lafiya_


Batafi minti biyu da turawa ba nashi saƙon ya shigo


_amin chuchu, ki kula min da kanki, ki kuma sa girkin dani zanci, ina sonki_


Murmushin jin daɗi tayi bayan ta gama karantawa a zuciyar ta tana faɗin


"na yarda da ake cewa addu'a bata faɗuwa ƙasa, kuma duk daren daɗewa Allah ze amsa ka"


Ta faɗa tana tuna lokacin da take tashi dare tayi ta addu'ar Allah ya ɗaura wa Umar son ta


Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tana sake hamdala ga ubangiji


Miƙewa tayi ta fita tsakar gida suka fara aiki da mama


Da daddare, tun da ta idar da sallar issha take tsantsara kwalliya


Ta kwashi minti 30 tana shiryawa, sai da ta gama sannan ta ɗauko doguwar riga ta sanya


Tana kallon kanta a madubi

Dan tunda take bata taɓa kwalliya irin ta ranar ba


Kiran Umar ne ya shigo ta ɗaga


"madam ina waje"


Ya faɗa


To tace tare da ajiye wayar ta ɗauko gyale ta yafa tare da fesa turare emergency


Cikin natsuwa ta fito yana tsaye yana waya cikin ƙana nan kaya


Yayi kyau sosai, yana wayar yana murmushi yana kuma shafa kwataccen sajen sa wanda ya zagaye farar fuskar sa


Ƙarasa wa tayi tana zuba masa kyawawan idanuwan ta wanda suka narke da ƙaunar sa


Sai da ya gama wayar, sannan ya fuskance ta yana kallon fararen idanunta fuskar sa ɗauke da murmushi


"wow chuchu wannan irin kyau haka?


Ta maida mai da martanin murmushin


"kazo lafiya, ya hanya?


" lafiya lau,boo boo kinsan Allah kinyi kyau kamar wata balarabiya, ji nike yi kamar in sace ki"


Dariya tayi, tace


"to kasace mana, ai dama ta kace"


Ya jingina da jikin motar yana Lumshe shanyayyun idanun sa da suka jiƙe da tsananin ƙaunar ta


"chuchu Allah kintafi da tunanina ji nike fa kamar zan faɗi"


Ta kuma yin dariya tana janyo baccin dake kusa da ita


"zauna to dan in ka faɗi bazan iya ɗaga ka ba"


Yayi lallausan murmushi yace


"chuchu, gaskiya ki gaya ma baba zanturo magabatana ayi maganar aure"


Ta zauna gefen bencin tana kallon sa


"habadai Badai yanzu ba"


Ya ɗan ware idanun sa


"ba yanzu ba to sai yaushe? Kinsan Allah bazan iya ƙara wata uku ba tare da na mallake ki ba"


Itama ware nata idanun tayi tace


"wata uku fa? Karatu na fa?


" sai ayi transfer ki koma ta Abuja, amma Allah bazan iya ƙara wani lokaci me tsawo ba tare dake ba"


Farin ciki ne ya mamaye zuciyar ta


"Jaana kadai bari,gaba tukunna"


Ya zauna gefen bencin idanuwan sa na kanta


"Allah bazan iya ba, ba zaki gane yadda nike jinki a raina bane, ki taimaka kiga ya ma baba kafin in koma na turo plz"


"shikenan kabari zanyi shawara da mama tukunna"


Ya jinjina kai


"shikenan"


Be bar gurin ta ba, sai tara da rabi kamar kar su rabu


Ko da ya koma gida sai da suka raba dare suna waya


*** **** ****

Tunda ya tashi yike jin kanshi cikin farin ciki da tsananin ɗoki dan gobe ne abul simnan ze sallami kowa


Gaba ɗaya ya ƙagara goben tayi jefi-jefi ya kan duba lokaci gani yike kamar lokacin baya gudu


Jazmi ya dafa sa ganin ya kasa zaune ya kasa tsaye yace


"abokina ka sa ranka a inuwa,nasan ka ƙagara ka ganta wallahi ni har mamaki nike yi"


Aasim yayi murmushi yana sauke ajiyar zuciya


"banga laifin ka ba, dan kayi mamaki ni kaina abun ɗaure min kai yike yi,dan bazan iya kwatanta adadin ƙaunar da nike mata ba"


Jazmi ya jinjina kai

"to Allah dai ya shige mana gaba"


Amin amsa ya faɗa


****   ****  ****


Washe gari Rauda na zaune gaban Abba, dan tun a daren jiya ta gaya ma mama abunda Umar yace ita kuma mama ta faɗa masa


Sai da ya gama karyawa sannan ya maida hankalin sa akanta


"maman ki ta faɗa min abunda Yaron yace, gaskiya na yaba da hankalin sa da kuma tarbiyyar sa, kuma nasa ya yanki amadu dake Abuja yayi min bincike a kansa bayi da wata matsala


Dan haka kice masa ya turo su jibi


Amsawa tayi da to, sannan ta fito


Tana fitowa ta danna kiran sa


Bugu biyu ya ɗauka

Suka gaisa sannan ta faɗa masa abunda baba yace


Tsallen farin ciki yayi haɗi da sujada ga ubangiji


"ai ni dama gobe yace wallahi,amma Allah ya kai mu jibin ki tambaye sa da wani lokaci zasu zo?


" to zan faɗa ma mama, idan ta tambaye sa sai in faɗamaka"


"shikenan amarya"


Tayi dariya tace

"amarya kuma?


Umar yace

" eh mana, dan zan faɗa ma uncle ɗina yace nan da wata uku suke so"


Murmushi tayi tana jin zuciyar ta fes


****  **** *****


Tunda ya fara haɗa kayan sa ya lura da abul simnan na kallon sa


Sai da ya gama tsaf sannan ya zo gaban sa


Cikin ladabi ya ɗan risina yace


"to ni na gama shiryawa zan tafi"


Abul simnan ya sauke numfashi cike da tausayin sa


"to Aasim ina maka fatan alkhairi, amma kada ka manta da neman taimako na aduk sanda ka shiga tsaka me wuya"


Aasim da har lokacin da murmushi a fuskar sa yace


"ina godiya, kuma ai zan ringa ziyartar ka,insha Allahu"


Jinjina kai abul simnan yayi


"shikenan Allah ya tsare ya kaika lafiya"


Aasim ya fito daga kogon yana tunanin ta hanyar da zebi


Jazmi ya ƙara so wurin yana cewa


"badai har ka shirya ba?


" na shirya tafiya zanyi"


"Nima na gama shiryawa mu haɗa hanya, amma dan Allah ina neman wata alfarma a wurin ka"


Aasim ya kallesa yace


"alfarma kuma jazmi? Wace irin alfarma"


Jazmi yace

"inaso mu biya ta masarautar mu, nasan mahaifiyata zata ji daɗi idan ta ganka,saboda sunan ka ya karaɗe duniya na ɗan babban sarki, kuma masarautar mu zata ƙara matar ba da suna idan kaje"


Aasim yayi murmushi yana Gyaɗa kai


"shikenan muje, amma fa muna zuwa zan wuce dan bazan daɗe ba"


"nayar da mu tafi"


Ɓacewa suka yi atare suka nausa sararin samaniya


Tun kafin su isa, jazmi ya tura saƙo masarautar su na ga sunan zuwa


Jin harda Aasim yasa aka fara gagarumin shirye-shirye


Suna isowa gaba ɗaya ƴan masarautar suka zube


Suna kwasar gaisuwa


Amsawa Aasim ya dinga yi cikin sakin fuska


Har suka isa gaban mahafiyar jazmi


Tayi farin ciki sosai


Nan da nan aka cika gaban sa da kayan ciye-ciye dana lashe-lashe


Gefe kuma kyawawan kuyangi ne ke rawa cikin salon ƙwarewa da ɗaukar hankali


Kallon su kawai Aasim yike yi amma kwata-kwata hankalin sa baya kansu in banda ƙosawa babu abunda ya cika zuciyar sa


Allah-Allah yike yi yaje yaga abar ƙaunar sa



*~Ƴarfillo~*.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: *🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                     🧞‍♂🧞‍♂

                        🧞‍♂


                         NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*


Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE 📕 2⃣5⃣


_Wannan Page nakine *sister ummi*, ladar zuwa katsina_🥰


_11:59_🕒 PM

MON, JUL 8



_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Duk ƙoƙarin da Aasim yayi ganin ya tafi a ranar gagara yayi


Domin magiyar duniya babu wacce jazmi da mahaifiyar sa basu masa ba akan ya kwana


Dole ya haƙura badan ransa ya so ba


washe gari

Ƙarfe bakwai tayi wa waliyyan Umar a gidan su Rauda, baba da ƙanin sa da kuma abokin sa malan shitu sun amshe su hannu bibbiyu


anan take suka bada kuɗin gaisuwa suna tambayar nawa aka yanke sadaki?


Dan su atake suke so agama yin komai


baba haƙuri ya basu akan ze neme su nan da wani ɗan lokaci amma dan ba Umar Rauda anbashi


Tun bayan tafiyar su Rauda da Umar suke maƙale a waya,wata kalar soyayya ce me zafi take ƙara shiga tsakanin su


kuma a ranar Umar ya koma Abuja


Ƙarfe biyar Aasim ya iso,kai tsaye gidan su Rauda ya isa


Yana bin ƙamshin jikin ta wanda yasa dashi da ita har uwaɗɗakan da take


Tana tsaye tana ninke kaya


Zubawa bayanna ta ido yayi yana jin kamar ya fizgota jikin sa


Ita ko tsayuwar mutum taji a bayan ta,kuma bata jiyo tafiya ba, Hakan ya sa gaban ta yaɗan fara faɗuwa


Juyo wa tayi a hankali,wani mummunan faɗuwa Gabanta yayi zuciyar ta na wani irin kaɗawa


Kallon-kallo suka shiga yi kamar lokacin suka fara ganin juna


Ya buɗe hannayen sa alamar ta shiga yana yi mata lallausan murmushi


Tsaye tayi tana kallon sa ta kasa ko ƙwaƙƙwaran motsi,in banda fargaba da tunanin abunda ze faru babu abunda ya cika zuciyar ta


Shiko mamaki ne ka masa, ganin ita da zata yi farin ciki da murnar dawowar shi,shine zata tsaya tana kallon sa kamar ma bata so dawowar nasa ba


"habibty!


Ya kira ta, mamaki na fara bayyana a fuskar sa


"Rauda kidawo natsuwar ki kar ya fahimta tun yanzu"


Zuciyar ta ta sanar da ita


Ƙaƙaro murmushi tayi tare da Ƙarasa wa ta rungume sa


Ajiyar zuciya ya sauke yace


"habibty duk ɗoki da murnan da nike yi akan naganki ashe ke bakyayin Hakan, nayi zaton zaki yi farin ciki da ganina amma sai Naga saɓanin Hakan, ki faɗa min me ke faruwa, ko kin canza min matsayi a zuciyar ki ne?


Ɗagowa tayi da sauri tana girgiza kai ganin yana so ya fahimta


"ko ɗaya kada kayi tunanin Hakan, matsayin ka yana nan babu abunda ya sauya, kawai dai gani nike kamar mafarki nike yi dan tun bayan tafiyar ka nike ta mafarkin gaka ka dawo sai na saki jiki ina jin daɗi kawai sai na farka, shi yasa Kaga Hakan"


Murmushi yayi tare da matse ta a jikin sa cikin tsananin ƙaunar ta yace


"to yanzu ba mafarki bane, zahiri ne nayi rashinki sosai habibty"


Ita ma murmushin tayi cikin fargaba tace


"ka dawo lafiya? Ina fatan kasamo abunda kaje nema?


Ta tambayesa tana fatan yace be samo ba dan ta samu hujjar kare kanta


"na samo habibty,yanzu baki da wata  matsala ko nan da gobe kika ce na fito na bayyana a gidan ku zan bayyana"


Zahiri ba taso jin Hakan ba,amma sai tayi murmushi tace


"masha Allah alhamdulillah, Naji daɗi sosai, isowar ka kenan yanzu?


Ya jinjina kai alamar eh


" to shikenan yanzu kaje ka huta, anjima sai ka dawo dannasan mama tana gab da shigowa"


"a'a anjima kam sai dai Nazo mu tafi, dan wallahi ina buƙatar ki sosai"


Ya faɗa, Gyaɗa kai tayi tace


"Allah dai ya kai mu anjiman, ka huta lafiya"


Kiss ya manna mata a goshi sannan ya ɓace


Jaɓar, ta zauna tana faɗin

"na shiga uku, yanzu ni ya zanyi?


Tabbas nasan ze wargaza al'amarina da Umar,da zarar ya gane


Ta runtse idon ta cike da tashin hankali


" a'a bazan bari Hakan ta kasance ba,dole na nemi mafita nasan yadda zan ɓullo ma al'amarin tun kafin Aasim ya gane"


Miƙewa tayi ta zura hijabi kai tsaye gidan Anty ummi taje ta gaya mata


Itama hankalin ta ya tashi amma sai ta danne tace


"kisa Allah aranki babu abunda ze faru insha Allahu,ze ya fahimce ki da yardar Allah"


Girgiza kai Rauda tayi dan ta san Aasim baze taɓa yarda ba


"Anty ummi nasan baze yarda ba, damuwa ta mani kada yayi ma Umar wani abu, ina sonsa sosai bana so wani abu ya same sa"


Ta Ƙarasa faɗa muryar ta na raunanewa


Anty ummi ta sauke dogon numfashi


"insha Allahu ze yarda, yanzu dai ki masa maganar anjiman tun kafin ya fahimta da kansa,idan ya yadda to, idan kuma be yadda ba sai mu san yadda zamu ɓullowa al'amarin"


Miƙewa Rauda tayi tana kaɗa kai bata ƙara cewa komai ba tafi to tana tafiya tana harharɗewa


Wayar ta ta fara ƙara alamar kira na shigowa


Ko bata duba ba ta san Umar ne, dan taken kiransa daban tasa masa


Ta ɗauka ta kara a kunnen ta


Tattausar muryarsa ce ta karaɗe kunnuwanta


"chuchu, yau kin manta da mijin ki ko?


Nannauyan numfashi ta sauke tace


" a'a ba haka bane, na kira ka da rana wayar bata shiga ba, da yammannan kuma bana cikin natsuwa ne shiya sa"


"subhanallah me ya faru?


Ya tambaya da sauri


Ta kuma sauke numfashi tace


"Umar kasan dai ina son ka ko?


" na sani chuchu"


Ta kuma numfasawa sannan ta cigaba da cewa


"bazan iya rayuwa babu kai ba, ina fargaban ka kuma nisan tata"


Daga can Ɓangaren Umar gyara zama yayi a office ɗinsa


"chuchu taya za'ayi na nisance ki? Kema kinsan bazan iya ba, a yanzu babu wani abun da ze rabani dake sai dai mutuwa"


"akwai Umar, akwai, ni nasani"


Ta faɗa cikin tsananin damuwa


Ya zare farin glass ɗin dake manne I donsa yace


"Rauda, wai meke faruwa ne? Ki faɗamin dan Allah, dan wallahi hankalina ya fara tashi"


Ta share hawayen da suka fara biyo kuncin ta


"wannan ba maganar waya bace, kabari zan faɗa ma amma kafinnan inaso kamin wata alfarma guda ɗaya"


"alfarma? Wace kalar alfarma kinsan kin wuce da matsayin alfarma a gurina kifaɗamin kawai ko menene zan miki shi"


"zan kashe wayata na tsawon kwana uku,kuma bana so inkaji shuru kace zaka kira wayar mama ko wata wayar da zaka sameni, sannan kada kayi yunƙurin zuwa har sai na neme ka da kaina"


"what? Kinsan me kika ce kuwa Rauda? Inyi kwana uku batare da Naji muryar ki ba?  Kema kinsan bazan iya ba"


Ya faɗa


Ta jingina da bangon waje dan ta iso gida


"kayi haƙuri, Nima ba da son raina bane,akwai matsalar da nike so inga yadda zata kasance ne tukunna"


Umar ya miƙe jin zufa ta fara karyo masa


"Rauda kifaɗamin abunda ke faruwa, kinsan ba ƙaramin aiki na bane nabaro Abuja yanzu ko?


"a'a, dan Allah kayi haƙuri,zan kashe wayar yanzu kuma dan Allah kayi abunda nace ma please Jaana"


Ze kuma yin magana ta katse kiran tare da kashe wayar gaba ɗaya


Wani kalan nawi taji ƙirjinta ya mata ta shiga gida lokacin mama ta dawo


"ina kika je?


Mama ta tambaya


" gidan Anty ummi"


Rauda ta bata amsa tana zama kan kujera


Mama ta kalle ta tace


"lafiya na ganki wani iri?


Tayi ƙoƙarin danne damuwar ta tace


" babu komai, ƙirjina ne ke ɗan min ciwo"


Da daddare, saida mama ta ta tafi ɗakin baba sannan taji iska na ɗiban ta


Kafin ƙyaftawa da Bismillah ta ganta a ɗakin sa


Yana kwance Saman lallausan gadon sa


Kyakkyawan murmushi ya mata yana miƙa mata hannun sa


Kallon sa take yi kamar taga wani sabon halitta ta kasa Ƙarasa wa


Ya miƙe ya ƙara so inda take ya sa hannu ya shafa gefe n fuskar ta


"habibty miye ne haka, baki san yadda na ƙosa dake bane?


Ya Ƙarasa faɗa yana janta jikinsa


Har lokacin ta kasa cewa komai

Wata kalar runguma ya yi mata da tasa duk jikin ta ya amsa


" Aasim!


Ta Kira sunan sa, ya sassauta rungumar da yayi mata tare da ɗago kyakkyawar fuskarta ya zuba mata ido


Yanajin ƙaunar ta na ratsa duk kan gaɓɓan sa


cikin fargaba tace

" inaso muyi wata magana da kai kuma dan Allah ka Fahim ci abunda zan faɗa maka"


Girgiza kai yayi yace

"a'a yanzu ba lokacin da zamuyi magana bane, wata na nawa bana tare dake?


Shuru tayi tana kallon sa kawai, sun kuyo da fuskar sa yayi yana ƙoƙarin haɗa bakin sa da nata


Tayi saurin kauda kanta tana faɗin


"please ka tsaya"


Ya ƙura mata ido yana ganin yadda take maida numfashi


"habibty, wai bakya jin tausayi na ne?


Tayi shuru dan bata san me zata masa ba


Kuma matse ta yayi yana shasshafa ta gaba ɗaya ya rikice


Ya ɗauke ta cak, ya aje ta kan gadon


Zata miƙe yayi saurin danne hannayen ta dana sa, yana kissing ɗin wuyanta


Ƙoƙarin tashi take yi amma ta kasa, dan ji tayi kamar an ɗaɗɗaure ta




*~Ƴarfillo~*.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*



*🌹JINNUL*

          *AASHIQUE🌹*

                    🧞‍♂🧞‍♂

                       🧞‍♂


                        NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _Hafsat Aliyu_



🅿AGE📕 2⃣6⃣



_Wannan Page nakine *oum deedad*, nakine ke kaɗai kiyi yadda kikeso dashi_


_11:22_🕒 AM

TUE, JUL 9



_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Kiciniya kawai take yi na ƙoƙarin ƙwace kanta


Hakan yasa ya dakata daga abunda yike yi ya tsura ma fuskar ta ido cike da mamakin sabon al'amarin da ta zo masa dashi


Dan yasan ada duk abunda ze mata bata yunƙurin hana sa


Yafi minti uku yana kallon ta da karantar yana yin ta, daga bisani ya ɗaga ta ya bar ɗakin


Tayi lamo akan gadon,zuciyar ta cike da tarin fargaba


"Rauda be kamata ki canza masa lokaci ɗaya ba, idan Hakan ya ɓata masa rai fa? Har ya gano kina ganin ze tsaya ya saurare ki?


Zuciyarta ta tunatar da ita


Tashi tayi da sauri ta dira daga kan gadon,ta fito falo


Kishingiɗe ta hango sa kan kujera ya Lumshe idanuwan sa


Ta riƙe ƙofar tana kallon sa kawai dan tama rasa yadda zata yi


Haƙuri zata je ta basa kome? Dan zahiri ba taso ya ƙara wata mu'amala da ita


Dan ta san aduk sanda wani abu ya shiga tsakanin su ƙara ƙaunar ta yike yi


Tana tsaye tana saƙe-saƙe taji ya kira sunan ta kuma har lokacin idanuwan sa na rufe


"Rauda! Zo nan"


Ta saki hannun ƙofar amma ta kasa Ƙarasa wa cikin falon


"nace kizo ko? Bawani abu zan yi miki ba ai tunda bakya so"


Ya faɗa still idanuwan sa na rufe


Jin ya haƙura da abunda yike niyyar yi yasa ta ƙara so gaban kujerar ta durƙusa


Tashi yayi daga kishingiɗar da yayi yana kama hannun ta na dama gami da  shafa tafin hannun


Sai ga wani ganye ya fito, mamaki ne ya kamata ganin yadda ganye ya fito a hannun ta


Ta cigaba da kallon sa kawai cike da al'ajabi


Aasim ko zuba ma ganyen ido yayi wanda yasa mata a hannu tun ranar da ze tafi, wanda ze ɗaukar masa duk abunda ya faru bayan tafiyar sa ba tare da rauda ta sani ba


Shafa ganyen yayi sai ga tsakiyar ganyen ya zama kamar TV take ya fara nuna masa


Ita dai Rauda taga yana kallon ganyen amma bata san me yike gani ba dan yana zaune ne akan kujeran yayin da take tsugunne a gaban sa


Cikin ƙanƙanin lokaci ya gama ganin duk abunda ya faru


Hankalin sa ya tashi sosai take idanuwan sa suka sauya kala zuwa ja kamar garwashin wuta


Nan da nan jikinsa ya fara fitar da wani turiri wanda yasa taja baya da sauri cike da tsoro


Ɗago turararrun idanuwan sa yayi ya watsa su a kanta tare da Miƙewa cike da tsananin ɓacin rai da tashin hankalin abunda ya rikita ƙwaƙwalwarsa


"ni zaki ci amana Rauda ni!!


Ya faɗa yana nuna kansa


Ja da baya ta fara yi cike da tsananin razana dan ya zamar mata kamar wani namijin zaki


Shiko tana ja da baya yana cigaba da taka wa zuwa inda take


"nace ni zaki ci amana? Ina can ina shan baƙar wahala da saida rayuwa ta akanki, ashe ke kina nan kina cin amana ta?


Dede lokacin ta kai jikin bango babu kuma inda zata ƙara matsawa


Damƙo gashin kanta yayi wanda yasa ta saki wata ƙara saboda tsananin zafin da taji


Ya matso da fuskar ta dede tasa dan tana jin yadda yike fitar da wani huci me zafin gaske


"kiyi magana!!


Ya faɗa cikin tsawa wanda saida fitulun ɗakin wasu suka tarwatse


Babu inda baya kyarma a jikin ta cikin tashin hankali da tsananin tsorata tace


" ka.....yi...ha..ƙuri"


Cigaba da kallon ta yayi still hannun sa na damƙe da gashin ta amma ya kasa ƙara furta komai in banda suya babu abunda zuciyar sa ke masa


Jin yayi shuru yasa ta buɗe idanuwan ta Ahankali


Aiko suna haɗa ido ta maida su ta rufe gam


Dan yanzu ma babu ƙwayar idon kwata-kwata, ƙara rinewa kawai suke yi


"ashe shiyasa baki yi farin cikin dawowa na ba,ashe shiyasa kika ƙi amince wa da buƙata ta saboda kin canzani a zuciyar ki"


Aasim ya faɗa cike da tsananin takaici


Kaɗa kansa yayi yana cigaba da cewa


"bazan taɓa amince wa da wannan butulcin ba, bazan taɓa amincewa ba!!!!


Ya faɗa cikin ƙaraji tare da wurgar da ita gefe


"zanje inga uban da ya tsaya masa,zan ɗanɗana masa kuɗar da bake kaɗai ba duk wata mace idan tagansa bazata yi marmarin ƙara kallon sa ba"


Ya faɗa yana juyawa a fusace


Yunƙura wa tayi da sauri tariƙo ƙafafuwan sa ta baya


"naroƙeƙa kada ka cutar da shi,duk abunda kace inyi zanyi amma kada kataɓa lafiyar sa"


Fincike ƙafafuwan sa yayi da ƙarfin gaske ya kuma yin gaba


Ta sake kamo ƙafafun cikin tsananin tashin hankali


"wallahi zan rabu dashi amma kada ka cutar dashi dan Allah"


Juyowa yayi tare da sukuyowa yana yi mata wani kallo me cike da razanarwa


"na baki nan da kwana uku, ki yanke duk wata alaƙar dake tsakanin ki dashi idan kuma kika ƙi........


Ya dakata da maganar yana yi mata gargaɗi da ya tsansa wanda saboda tsananin tashin hankalin da ya shiga yike rawa


"wallahi zaki yi mamakina, dan ke tawa ce ni kaɗai babu wani mahalukin da ya isa ya raɓeki, babu shi!!!!


Ya Ƙarasa faɗa yana ɓatar da ita


Bata ganta a ko ina ba sai, a uwaɗɗakan mama


Fashewa tayi da kuka me ciwo tana kifa kanta akan fulo


Kuka take yi sosai kamar ranta ze fita


Ji tayi an dafata, ta ɗago da sauri

Wata farar dattijuwa ta gani zaune kusa da ita


Rauda taja baya da sauri wani sabon tsoron na kuma kamata


"kada kiji tsorana Rauda, ni baiwar Allah ce me tsananin tsoron sa, bazan cutar dake ba"


Rauda ta takure da bangon gadon har lokacin illahirin jikin ta rawa yike yi


"wacece ke? Me ya kawo ki wurina?


Dattijuwar tayi murmushi tace


"sunana ummu Salma,kuma ni aljana ce, abunda ya kawoni gurin ki kuma nazo in taimake ki ne"


Rauda tayi shuru daga bisani tana ce


"taimako?


Ummu Salma ta jinjina kai


"na daɗe ina bibiyar rayuwarki, babu abunda bansani ba akan ki, tabbas rayuwar ki tana cike da sarƙaƙiya da ruɗani,shiyasa nazo na taimaka miki


Duk da ni aljana ce bani da ƙarfin da zan iya karawa da rauhani, rauhanin ma kuma Aasim bin ramzad wanda ya kasance ɗan sarkin rauhanai me ƙarfin gaske, nasan bani da ƙarfin da zan iya karawa dashi amma ina da ɗan taimakon da zan iya baki da kuma shawarwari waɗanda zasu amfane ki"


Cikin sauri Rauda ta girgiza mata kai


"a'a nagode da taimakon ki amma bana so wani abu ya same ki tunda kinyi niyyar taimakona, Aasim yana da wani madubi da yike ganina dashi yanzu nasan yana ganki ya na kuma jin duk abunda kike faɗa kiyi gaggawar barinnan dan Allah"


Ummu Salma tayi murmushi tana ciro wani ƙaramin turare


"kafinnazo nan saida nayi amfani da wannan turaren,a halin yanzu Aasim baya ganin mu


Kuma wannan turaren shi nazo na baki, saboda nasan a duk sanda yanzu Aasim ya ganki da Umar ze iyayi masa komai


Kuma ya kamata ki haɗu da Umar ki yi masa cikakken bayani, domin ya zauna da shiri da kuma addu'o i


Sannan kusan mafitar da zaku ne ma,a duk sanda zaki haɗu da Umar Kisha fa wannan turaren Aasim baze ganku ba, kuma inaso kuyi duk abunda zakuyi cikin gaggawa, sannan kijuye turaren a man shafawanki da zarar zaki haɗu da Umar ki shafa"


Ta Ƙarasa faɗa tana miƙa ma ta turaren


Amsa Rauda tayi tana kallon turaren


Yayin da ummu Salma ta cigaba da cewa


"ni zan tafi, kiyi ƙoƙari ki haɗu da Umar a gobe tunda kinga kwana uku kaɗai Aasim ya baki, sannan ki shafa idan zaki kira Umar ɗin, duk yadda kuka yi gobe zan dawo inji, na barki lafiya"


Rauda tayi shuru bayan ummu Salma ta ɓace tana juya turaren a hannun ta


****  ****  ****


Tun bayan da suka yi waya yike kiran wayar ta yike jin a kashe


Ya shiga damuwa sosai,dan ko bacci ya kasa yi kuma har lokacin kuma trying ɗin wayar yike yi amma still ba ta shiga


Aje wayar yayi a gefe yana janyo fulo ya tada kansa


Maganar ta ce kawai ke yi masa yawo a kunne


_Bazan iya rayuwa babu kai ba, ina fargaban ka kuma nisan tata_


Ajiyar zuciya ya sauke, ya rasa ta yadda ze gane abunda take nufi, gashi tace kada yake sai ta ne mesa, to me ke faruwa??


Miƙewa yayi ya ɗauro alwala, ya dinga nafiloli dan bayajin ze iya yin barci



*~Ƴarfillo~*.

[7/12, 10:51 AM] Harira Aliyu Mrbcy: *🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*



*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*


Dedicated to _little hajjo and my elder sister Hafsat Aliyu_


🅿AGE📕 2⃣7⃣


_Wannan Page nakine *Aysha Abubakar* Allah ya bar zumunci_


*_Gaisuwa da jinjina ga umar ɗalha  muna godiya da ƙoƙarin da kake yi a forum kai da sis nabila allah ya bar zumunci_*


_8:09_🕒 PM

WED, JUL 10


_Bissmillahir rahmaninr Rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Ya daɗe a tsaye yana za gaye ɗakin,jefi-jefi ya kan zauna ya zuba tagumi 


Me yasa Rauda zata masa haka?

Meyasa take Umar wannan zazzafar ƙaunan?


Ya sani tun bayanzu ba tana tsananin ƙaunar Umar shiyasa ya sa ido sosai akan Umar


Me Umar yike dashi da yike ɗaukar hankalin ta? Ya zo mata asuffa me kyau dan yana tunanin kyan da Umar yike dashi shine yasa ta ke sonsa


Amma sai gashi duk ƙoƙarin da yayi ganin karsu haɗu bayan tafiyar sa sun haɗu, abunda dai yike gudu shiya faru


Furzar da wata iska yayi me zafi yana faɗin


"Rauda ke ta wace ni kaɗai, ba zaki yi rayuwa da wani ba"


Ya Ƙarasa faɗa yana jingina da kujerar


**** **** ****


Washe gari,Anty ummi tazo Rauda ta sanar da ita duk abunda ya faru


Ba ƙaramar kiɗima tayi ba tace


"yanzu maza ki shafa turaren ki kira sa, dan abun bana zama bane karya je ya cutar da ɗan mutane"


Rauda ta ɗauko turaren ta shafa sannan ta lalubo wayar ta, ta danna kiransa


Lokacin Umar yana zaune a office wata patient tana mai bayanin abunda ke damunta


Sam hankalin sa baya wurin, dan bejin abunda take cewa Sam


Zayyad da ke zaune ɗayan Ɓangaren Shima yana sauraren bayanin da patient ɗin dake zaune gaban sa take masa


Ya lura da yanayin Umar Sam hankalin sa baya wurin da alamama ya Lula cikin tunani ne


Ɗan buga tebur ɗin dake gaban sa yayi wanda ya dawo dashi daga duniyar da ya tafi


"yadai doctor lafiya kuwa?


Umar ya sauke ajiyar zuciya yana faɗin

" babu komai"


Dede lokacin kiran Rauda ya shigo wayar sa


_chuchu_


Ya gani ɓaro-ɓaro a screen ɗin wayar


Ya miƙe da sauri yana ɗaukar wayar


"Zayyad ka duba wannan patient ɗin please ina zuwa"


Be jira jin me Zayyad zece ba, ya fice yana ɗaukar wayar


"Rauda yanzu fisabilillahi abunda kika yi kin kyau ta kenan? Kin sa hankalina ya tashi wallahi ko bacci ban iya yi ba"


Rauda ta sauke ajiyar zuciya


"kayi haƙuri,yanzu kana ina ne?


" ina asibiti"

Ya bata amsa


"ina son ganin ka ne da gaggawa ya za'ayi kenan?


" zan taho Kadunan, amma kafinnan faɗamin meke faruwa ne?


Ta gyara zamanta tana cewa


"kabari sai kazo, na gaya ma ba maganar waya bace"


Numfashi Umar ya sauke cike da damuwa


"shikenan zantaho yanzu, amma bazan iya driving ba zansa Zayyad ya kaini train station na biyo train kawai"


"to Allah ya kawo ka lafiya"


Ta faɗa tare da aje wayar


Anty ummi tace

"amma kina ganin idan kika faɗa masa yaji kina da aljani baze ce ya haƙura ba?


Rauda ta sauke numfashi tace


" to ya zanyi Anty ummi, ya zama dole infaɗa masa, idan yaji ze haƙura ba shikenan ba,haka Allah ya ƙaddaromin"


Ta ƙarasa faɗa idanuwan ta na cikowa da hawaye


Umar cikin sauri ya koma office, ko zama beyi ba ya fara tarkata takaddun dake gaban sa


"Zayyad tashi ka kaini train station please"


Cikin mamaki Zayyad yace


"train station kuma? Me zaka yi a can, kai da kake da patients ɗin da suke jiranka a waje?


Umar ya rataya jakar laptop ɗinsa yana duban Zayyad


" zanje Kaduna ne, kuma banajin zan iya driving shiyasa zanbi train"


"Kaduna?


Zayyad ya faɗa da mamaki sannan ya cigaba da cewa


" wai ba shekaran jiya ka dawo daga kadunan ba, me kuma zaka je kayi?


"bangane me kuma zanje inyi ba, kasan dai hakanan bazan tsiri tafiya ba, batare da dalili ba"


Zayyad ya ce

"Umar nifa kwata-kwata bangane maka ba, dan nasan ada sai kayi shekara ko watanni batare da kaje Kaduna ba


Amma tunda kafara son Rauda shikenan kamai da Kaduna kamar nan da wuse


Wai kana cikin hayyacin ka kuwa?


Umar ya Harare sa cike da ƙosawa


" to ba sai ka kaini asibitin mahaukata a duba ni ba, Kaga malan in zaka kaini ka kaini, in kuma bazaka kaini ba nafita na tari taxi drop"


Zayyad ya girgiza kai yace


"a'a muje inkai ka,ƙila takai sunan ka gurin malamai ne shiyasa duk kabi ka susuce"


Gaba yayi batare da ya ƙara kula Zayyad ba


Ƙarfe biyu ya iso Kaduna,da yike tsakanin tashar jirgin da gidan su Rauda Bawani nisa sosai yasa ya ɗauki keke napep ya kawo sa har ƙofar gidan


Ta zura hijabi, fuskar nan tata tayi fayau ga idanuwan ta da suka ƙanƙance saboda kukan da tasha


Tana fitowa suka haɗa ido, gaban sa ne yafaɗi dan yana kallon ta ya gano tsantsar damuwa atare da ita


Be amsa gaisuwar da take masa ba yace


"chuchu faɗamin abunda ke faruwa"


"ya kamata mu zauna tukunna, mu shiga ɗakin waje"


Be ƙara cewa komai ba suka shiga ɗakin da ba komai a ciki sai kujeru guda biyu da kafet


Ta Nuna masa kujera ya zauna sannan ta juya zata fita


"ina kuma zakiji je?


Ya tambaya


" zan kawo ma ruwa ne"


Ya girgiza kai

"a'a dan Allah ki zauna muyi magana, dan ganin ki a damuwa ya ƙara ɗaga min hankali"


Ta zauna a kujerar dake kallon tasa,yayin da shi ya zuba mata ido yana sauraran abunda zatace


Ta rasa ta inda zata fara faɗamai Gabanta ne kawai ke faɗuwa


"ke fa nike saurare Rauda"


Cikin damuwa tace


"bansan ta inda zanfara faɗama bane Umar, ina tsoron yadda zaka fahimci abun, da kuma hukuncin da zaka yanke idan na faɗama"


Ya gyara zaman sa sosai yana kallon ta


"ki faɗamin ko menene Rauda,zan fahimce ki insha Allahu"


Daurewa tayi ta faɗa mai labarin Aasim da kuma halin da take ciki a halin yanzu


Doguwar ajiyar zuciya Umar yayi yana zame hannayen sa daga kan haɓarsa


"wallahi na zata wani babban al'amari ne, da nasan wannan maganar ce ma da ban tada hankali na ba, duk ɗauka ta baba ne yace ya fasa bani ke"


Kallon sa tayi da mamaki a fuskarta tace


"yanzu wannan ba babban al'amari bane Umar?


Ya ɗaga gira sama yana faɗin


" yeah Rauda, ba tun yau ba na daɗe da fahimtar kina da jinnul aashique,kuma ni babu abunda zesa na janye daga neman aranki


Ki faɗa masa cewa neman ki yanzu nafara, alaƙa dake kuma yanzu nasa gaba"


Sororo tayi tana kallon sa


Ya taso daga inda yike ya tsugunna a gaban ta tare da kamo hannun ta


"kinga Rauda, ki kwantar da hankalinki babu abunda ze faru,ni da zaki min wata alfarma ma dakin amince munyi aurannan nan da wata ɗaya"


Zame hannun ta tayi tana jingina bayan ta da jikin kujerar dan ta san Be san waye Aasim bane shiyasa yike faɗar haka


"ba zaka gane ba Umar, ba zaka gane ba"


Ya gyara tsugunnuwar da yayi yace


"menene bazan gane ba Rauda?


Ta Lumshe idonta siriran hawaye na gangaro mata


" Aasim ba kamar aljanun da ka sani bane, yana da matuƙar ƙarfi,kuma ze iya yin komai akanmu"


"duk ƙarfin sa Allah ya fisa rauda, domin Allah shiya halicce mu ya kuma halicce shi, ubangiji shike da iko akan duk kanmu, dan haka babu abunda ya isa ya mana wanda Allah be yi mana ba, akwai wani babban malami da na sani zan faɗa masa nasan ze iya ɗaukar mataki a kansa


Amma kicire fargaban cewa ze raba mu, dan wallahi babu wanda isa ya raba ni dake sai Allah"


Kallon sa kawai take yi amma ta kasa ƙara furta komai


Yayi mata murmushin ƙarfafa gwiwa


"ki yarda dani babu abunda ze faru da izinin Allah, abu ɗaya nike so dake kidage da addu'a


Sannan ki kasance koda yaushe kina cikin alwala da kinji alamar sa kiyi addu'a


Kuma kada ki ƙara tanka masa, duk abunda ze ce miki kiyi banza dashi ya kasance bakin ki ba abunda yike faɗi face ambaton Allah"


Gyaɗa masa kai kawai tayi, yayin da ya miƙe yana faɗin


"yanzu zanje gida inyi wanka sai intafi zaria dan acan malamin yike,dama da mota nazo da daganan na wuce, amma kinga sai naje gida na ɗauki mota"


Ta sauke numfashi tana kallon sa ƙaunar sa na ƙara ƙaruwa acikin zuciyarta,tabbas shi na dabanne dan tabbata da wani ne yaji wannan labarin da yace ya haƙura amma shi ko ɗar beji ba


Katse mata Guntun tunanin da tafi yayi ta hanyar tafa hannun sa


"chuchu Banaso kina wannan tunanin, ki kwantar da hankalinki please"


Ta jinjina kai tare da cewa


"amma shekaran jiya ka koma, kuma yau na saka ka dawo, ka bar zuwa zarian sai gobe kada ka gaji da yawa"


Ya girgiza kai yace


"ai zama be ganni ba Rauda,anjimannan zan tafi"


"Allah ya kiyaye hanya, ya kaika lafiya"


Ta faɗa

Ya amsa da amin yana yin gaba


"Umar!


Ta Kira sunansa ya waigo yana zuba mata kyawawan idanuwan sa


"nagode da ƙaunar gareni"


Murmushi yayi tare da cewa


"kinga karki ƙaramin irin wannan godiyar muje ki rakani"




*~Ƴarfillo~*


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo and my elder sister Hafsat Aliyu_


🅿AGE📕 2⃣8⃣



_wannan page nakine *shahida* ina alfahari dake a koda yaushe_


*TA AZIYYA*

_ga y'ar uwarmu princess mazadu allah ya jik'an yaya ya gafarta mishi yasa aljannah ce makomarsa amin_



_7:38_🕒 PM

SUN,JUL 21


_Bismillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



sai da ya watsa ruwa ya sauya kaya sannan ya fito  hannun sa rik'e da makullin mota


hasina ce ta biyo sa dasauri tana fad'in 


"ya umar inzo inrakaka?


girgiza kai yayi yana cigaba da tafiya


"na hutar dake,nasan rakiyar bata tsakani da allah bace dan asaimiki waya ne"


dariya hasina tayi tace


"kai ya umar amma dai kasan ina raka ka ai ko ba maganar waya ko?


ya jinjina kai


"nadai hutar dake kibari anjima in na dawo sai muje in sai miki"


"owo yaya nagane gurin anty rauda zakaje ko?


juyowa yayi yana kallonta dan tana so ta isheshi da surutu


"kinsan bana son yawan magana ko?allah idan kika ban haushi zan fasa siyan wayar"


dariya hasina tayi tana girgiza kai


"aa yi hak'uri yayana,d'an tsaya ma muyi selfie"


ta fad'a tana k'ok'arin kunna cameran wayanta


umar wucewa yayi ya shiga mota batare da ya k'ara saurararta ba


ana kiran sallar magriba ya isa zaria


ya faka motar  a k'ofar gidan malan shitu 


tare da fitowa lokacin har sun tada sallah shi da almajiran sa


gorar ruwa ya d'auko a motar ya yi alwala ya k'arasa inda suke sallar 


sai da suka idar sannan malan shitu ya tashi dasauri yana d'aukar darduman da yike kai yace


"alhaji umar kaine da yamman nan tashi kan tabar man nan in shimfid'ama darduma"


umar yayi murmushi yace


"aa malan barni kan tabarman"


"aa dan allah tashi alhaji umar tabarma ba wurin zaman ka bane,bare wannan tabarman da ta yayyage"


umar ya kuma yin murmushi yace


"haba malan nida wataran cikin k'asa ma za a turbud'ani miye abun damuwa dan nazauna kan wannan tabarman?


malan shitu ya jinjina kai yace


"shiyasa a kullum kake burgeni alhaji umar sam baka da girman kai irinna masu kud'i ba ka nuna k'yamarka ga talakawa sam"


har lokacin da murmushi a fuskar umar


"bamu gaisa ba malan,ina wuni ya d'alubai"


malan ya amsa da lafiya lau 


ya hanya,hala hanya ce ta biyo da kai?


umar ya girgiza kai yace


"aa malan wata y'ar matsala ce ta tasoni wallahi"


malan shitu yace

"subhanallah to allah ya warware mana,tashi mushiga d'aki to"


umar ya mik'e yabi bayan malan suka shiga madai-daicin d'akin 


bayan sun zauna malan shitu yace


"ina jinka alhaji meke faruwa"


umar ya sauke numfashi yace


"wallahi malan akan  yarinyar da nike nema ne"


ya koro masa bayani dallah-dallah


malan shitu ya sauke numfashi bayan ya gama sauraren bayanin umar



"gaskiya wannan al'amari akwai rikitarwa amma bari muyi isikhara mu gani"


umar ya gyad'a kai yana duban sa kawai


malan shitu ya d'auko carbi yafara ja zuwa can ya nisa yace


"gaskiya alhaji umar da zakaji shawarata da ka hak'ura da wannan yarinyar saboda akwai sark'ak'iya sosai acikin al'amarinnan"


umar ya sauke ajiyar zuciya


"malan bazan iya hak'ura da ita ba,dan ina sonta fiye da yadda kake tunani idan da mafita da kuma yadda za'ayi ayi kawai"


malan ya gyad'a kai yana kuma d'aukar carbin sannan yace


"dan mafita za asamu mafita da izinin allah amma fa za a sha gwagwarmaya sosai"


umar ya gyara zama yana k'ara fuskantar malan shitu


"malan ashirye nike da in fuskanci duk wata gwagwarmaya indai akanta ne,dan haka karkaji komai indai akaina ne,kai dai kayi duk abunda kaga ya dace dan allah ga wannan ayi duk sadakokin da za'ayi"


ya k'arasa fad'a zaro bandir d'in kud'i ya aje a gabansa


malan shitu ya jinjina kai yace


"insha allah zamuyi abunda zamu iya amma kaima fa sai kadage da addu'a sosai,musamman inzaka kwanta allah ya shige mana gaba"


"amin"


umar ya fad'a yana mik'ewa yace


"to ni zan wuce malan saboda kar dare yayi"


malan ma ya mik'e yace


"shikenan alhaji umar allah ya kiyaye hanya duk abunda ake ciki zankira ka in sanar dakai insha allah"


bayan kwana uku,bata k'ara jin d'uriyar Aasim ba hakan yasa taji tad'an rage fargaba dan umar be koma abuja ba kullum sai yazo ya kwantar mata da hankali


yauma suna tare ya d'auko wata leda ya bud'e wacce malan shitu ya aiko mai dashi


ya d'auko wasu turaruka da wani mai a wata kwalba ya mik'o mata yana fad'in 


"d'azu malan shitu ya aiko dasu yace kifara amfani dasu a yau........


dagatawa yayi yana kallon yadda ta toshe hanci dan yana bud'e ledar taji wani mugun wari ya bugi hancin ta


"miye haka kuma?


ya tambaya idanuwansa akanta


"dan allah ka rufe ledar wallahi wari"


ya kalli ledar dan shi sam beji wani wari ba


"wari kuma?


ta d'aga kai tana k'ara toshe hancin dan ji take warin na kuma k'aruwa


"allah wari ka rufe kar inyi amai please"


ya sauke ajiyar zuciya har lokacin idanuwan sa na kanta


"chuchu baki son hankalin mu ya kwanta ko?


cikin rashin fahimta tace 


"kamarya jaana"


ya jinjina kai yace


"eh mana,kinsani muna cikin matsala amma kuma na kawo magani kina toshe hanci"


ta jingina da kujerar motar 


bata re da ta k'ara cewa komai ba


"ki amsa maganin kisha fa sa yanzu a gabana"


 d'an zaro ido tayi tana kallon sa 


"inshafa fa kace"


ya d'aga kai


"eh ko bazaki shafa bane?


ta girgiza kai ahankali tare da cewa


"bawai bazan  shafa bane,amma warin maganin yayi yawa"


ya gyara zamansa sosai yana fuskantar ta


"Rauda nasan bazaki ji dad'in amfani da magungunan nanba sam,amma ya zama dole ki daure ki duba damuwar da nike ciki dan allah "


ta sauke numfashi tare da zame hannayenta da toshe hancin dasu


ta amsa


murmushi umar yayi yace


"yauwa matar kirki nasan dama bazaki yimin musu ba"


dauriya kawai take yi dan warin maganin nema yike yi ya hautsina ta


"ya zanyi amfani da shi?


"kinga wannan idan zaki kwanta zaki shafa,wannan kuma da rana sai wannan hayak'i ne.........


ya d'an dakata ganin yadda take mashau-mashau da idanu


"lafiya chuchu?


ya tambaya,ta bud'e idanuwanta da suka fara yi mata nawi saboda sarawar da kanta ya fara yi mata


"kaina ke min ciwo"


cikin tausayawa yace


"sannu ze dena kinji,kiyi hak'uri dama malan yace dole zakiji haka"


kad'a kai kawai tayi tana bud'e turaren ta shafa a goshinta kamar yadda yace


wani kalan nawi taji goshin ya mata kamar an d'aura mata dutse


lumshe idanuwanta tayi tana ambaton sunan sa


"umar!


ta kira sunan cikin wani irin yanayi


gabad'aya tausayinta ya kamasa,


ya amsa yana jin kamar yadawo da ciwon da take ji jikin sa


"jikina na bani kamar wahalar da kanmu kawai zamuyi baza.......


katse ta yayi

"kada ki k'ara fad'in haka,insha allahu zamu yi nasara"


gyad'a kai kawai tayi amma ita zuciyar ta ta karaya


"please rauda kiyimin alk'awarin duk rashin dad'in maganinnan zaki daure kiyi"


ta k'ak'aro murmushin k'arfin hali tana jinjina kai


"zanyi insha allah"


b'angaren Aasim kuwa yana zaune yana kallon su ta madubi


guntun murmushi yayi yana shafa sumar kansa had'i da kallon ummu salma wacce ya d'aure da wasu mugayen  igiyoyi 


"tabbas kin tafka kuskure da kikai tunanin wani k'aramin alhakin turaren ki zeyi tasiri akaina,kin manta waye Aasim ne amma zan tunatar dake yanzu"


cikin tashin hankali da rud'ani ummu salma tace


"ka gafarceni ranka shidad'e kayi min afuwa nasan nayi kuskure ka yafeni dan allah"


hannunsa ya sa yayi nuni da ita sai ga wani haske ya fito ya caki k'irjinta


tasaki wata razananniyar k'arar azaba


ya mik'e yana kallonta da razanannun idanunsa 


"zaki kasance a haka har tsawon kwana bakwai,kinga gobe bazaki sake tunanin shiga gona ta ba"


yana gama fad'ar haka ya b'ace


gurin rauda ya nufa kai tsaye lokacin ta shiga gida dan umar aranar yike so ya koma abuja


tana zaune tana k'ok'orin shafa turarukan da maganin taji tsayuwar sa agabanta


d'ago kanta tayi da sauri suka had'a ido


gabanta ne yafara fad'uwa ganin kallon da yike mata 


"habibty intayaki shafawa ne?


ya tambaya yana yimata wani shu'umin murmushi


runtse idanuwanta tayi dasauri tana karanto duk wasu addu'o i da suka zo bakinta


zaunawa yayi kusa da ita yana amsar turaren hannunta yana juyawa


"kinyi shuru ko baki so intayaki ne?ba rabuwa kikeso kiyi dani ba ince wannan.shine maganin da akace miki ze rabaki dani?


har lokacin addu a kawai take karantowa kamar yadda umar yace tarink'a yi aduk sanda yazo


murmushi ya kuma yi yana rausayar da kai


"ohh na tuna saurayinki yace kidena tankamin ko?



*~y'arfillo~*


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 2⃣9⃣



_2:28_🕒 PM

MON,JUL 22


_Bissmillahir rahmaninr rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


"wato da nabaki lokaci ki yanke duk alak'ar dake tsakaninku shine kike neman ma rabuwa dani ko?


wallahi kinbani mamaki bantab'a tunanin haka daga gareki ba,na d'auki amana.da yardata na baki amma a k'arshe ni zaki watsa wa wa k'asa a ido"


hmmmm ya k'arasa fad'a yana sauke numfashi sannan ya cigaba  da cewa


"Rauda kisani bazan tab'a rabuwa dake ba,kuma bazan tab'a bari wani namiji ya rab'eki ba,kada ma ki wahalar da kanki wajen yin maganin da ze wahalar dake domin banga maganin da zeyi shamaki atsakanina dake ba,


sannan kisani kina d'auke da cikina a tare dake dan haka kibi ahankali wajen yin amfani da wasu magungunan da zasu iya cutar min da yaro ina fatan kingane?


bud'e idanuwanta tayi sosai tana kallon sa 


yayinda ya mik'e ya durk'uso saitinta gami da sa hannu akan cikinta ya shafa


"ki kulamin da yarona sosai"


be jira jin me zatace ba ya b'ace


"nashiga uku!


ta fad'a tana duban cikin,wasu hawayen tashin hankali suka fara biyo kuncinta


kwantawa tayi zuciyarta cike da tsananin damuwa


washegari umar na zaune a office bayan yagama duba iya adadin patient d'in da yace ze duba


kulle office d'in dan yana buk'atar ya huta sakamakon rashin baccin da bayayi kwana biyu dan duk dare tashi yike yi yay ta kai kukansa ga ubangiji akan wannan matsalar


wani sak'o ne ya shigo wayar sa ya bud'e yana dubawa


tsaki yaja ganin wasu kalar shirmen rubutu da besan ko na menene ba 


d'agowa yayi ze aje wayar karaf idonshi yayi gamo da Aasim wanda ke zaune a kujerar dake gaban tasa


kallonsa umar yayi da mamaki dan shi sam beji shigowar mutum ba hasali ma k'ofar office d'in a rufe take to ta ina ya shigo?


yayi wa kansa tambayar


Aasim yayi murmushi tare da mik'amai hannu yana mai sallama


umar ya amsa kawai batare da ya mik'a masa nasa hannun ba


Aasim ya janye hannunsa yana cewa


"kayi hak'uri nashigo ma office batare da  izinin ka ba"


umar ya gyad'a kai yace 


"ok meke tafe dakai?


Aasim ya gyara zama 


"kamata yayi kafara tambayar waye ni,kafin ka tambayi  abunda nazo dashi"


umar ya jinjina kai 


"to inajinka waye kai?


"sunana Aasim mijin wacce kake neman aure"


umar ya kallesa da sauri mamaki k'arara a fuskar sa,amma ko kad'an beji wani tsoro ba


hasalima d'an murmushi yayi  


Aasim ya cigaba da cewa 


"nazone inyi maka gargad'i cikin lalama,ka rabu da matata  dan zan iyayin komai akanta"


umar ya sauke ajiyar zuciya yace


"naji dad'in zuwanka da kuma yadda kazomin cikin salama,hakan ya tabbatar min da kana da sauk'in kai


amma ina so kasani bazan iya rabuwa da rauda ba domin inason ta fiye da yadda kake tunani"


Aasim yayi murmushin takaici 


"ba damuwa ta bane  yawan son  da kake mata,dannasan babu wanda zeso rauda fiye dani aduniya,inaso karabu da ita ayau ba sai gobe ba"


umar ya sauke numfashi yana girgiza kai


"bazan tab'a rabuwa da ita ba,domin itace zab'ina"


Aasim ya kad'a kai yace


"shikenan ni zan rabaka da ita dole,kashirya ma shiga tashin hankali kasa aranka cewa daga yau kun k'ulla abota da damuwa"


umar ya kad'a kai


"indai akanta ne,nashirya taryan komai"


Aasim ya mik'e yana jinjina


"shikenan mu zuba ni dakai"


numfashi me nawi umar ya sauke bayan b'acewar Aasim


yasa handkerchif ya share gumin da yafara tsattsafo masa  tabbas wannan abun bana zama bane


zaro wayarsa yayi ya kira malan shitu ya sanar dashi


daga can b'angaren malan shitu yace


"gaskiya al'amarinnan me girma ne,amma ina ganin zanje gurin wani kakana gobe dan yana da lak'anin da yafi nawa inyaso sai muji abunda zece shi"


umar yace


"shikenan malan dan allah ka k'ok'arta"


sukayi sallama ya ajiye wayar


haka suka cigaba da gwagwarmaya,har na tsawon wata d'aya amma babu canji


inbanda wahala ma babu abunda rauda kesha,dan arana sai tayi suma fin biyar


babu wanda besan matsalar da ake ciki ba a gidan


rauda ta rame sosai,dan ita kad'ai tasan azabar da take sha dan Aasim yace muddin bata rabu da umar ba to bazata samu sassauci ba


b'angaren umar ma kullum cikin kawo masa farmaki akeyi,amma da yike jarumi ne shi kuma yana tsaye da addu'o i shiyasa shi nashi ya zo dasauk'i


duk inda sukaji wani malami sai sunje amma a banza,dan babu abunda yike canzawa


ga lokacin biki k'ara matsowa yike yi


gabad'aya sun fita hayyacinsu babu wanda be rame ba


wahalar da rauda ke sha tafi komai d'aga ma umar hankali


ranar wata alhamis umar yazo,kai tsaye yayi sallama yashigo falon mama dan yanzu ba maganar fita waje


da ta tashi zata fita zata zube,hakan yasa dole inyazo yike shigowa ciki


mama ta kawo mai ruwa sannan suka fara gaisawa


ya k'ara da tambayar me jiki


mama ta amsa da 

"da dauk'i,d'azu dama nike niyyar nace a kira ka,wata k'anwar babansu tace akwai wani malami acan k'auyen yola kuma yanayin irin wannan aikin ana dacewa"


umar yace

"to mama ai babu matsala,yaushe kike ganin ya kamata atafi"


"zuwa lahadi"


umar ya sauke numfashi yace


"mama lahadi beyi nisa ba,me ze hana atafi asabar?


mama ta kallesa da tausayawa tace


"amma saidai kabari muje ko,kai ka huta dan.zirga-zirgan da kakeyi tayi yawa"


umar ya girgiza kai


"aa mama tare zamu tafi,babu damuwa ai"


mama ta sauke ajiyar zuciya tace


"shikenan,allah ya kaimu asabar d'in


bari na mata magana tafito"


ta k'arasa fad'a tana mik'ewa tashiga uwadd'aka


rauda na kwance kan gado ta dunk'un k'une da bargo


mama tace


"zaki iya fitowa falon?


Rauda ta girgiza kai

"bazan iya ba,gaba d'aya jikina nuk'urk'usa yike yi"


mama ta sauke numfashi,ta d'auko darduma ta shimfid'a mai a gefe sannan ta dawo falon tace


"shigo daga cikine,wai bazata iya fitowa ba"


amsawa yayi da to,ya mik'e cikin ladabi ya shiga uwadd'akan yana sallama


amsawa tayi da muryarta da tayi k'asa-k'asa 


ya zauna yana kallonta


zuciyarsa cike da tsananin damuwar halin da take ciki


"sannu chuchu ya jikin?


"da sauk'i"


ta amsa tana duban yadda shima ya rame 


ji tayi idanuwanta sun cicciko da hawaye tayi k'ok'arin shanye su amma takasa sai da zubo


shiko umar hankalinsa ne ya k'ara tashi


"chuchu me yafaru?ina ne ke miki ciwo kuma?


girgiza kai tayi ahankali tare da cewa


"ina tausayin ka ne umar,saboda ni ka rasa sukuni,karasa kwanciyar hankali"


umar ya sauke ajiyar zuciya yace


"ni banason ganin hawaye a fuskarki yana k'ara tada min da hankali,dan allah kibari"


hannu tasa ta share hawayen tanajin zuciyarta wani iri


mama ta shigo da kwanan abinci ta ajiye tana fad'in


"tun safe nike fama da ita tak'i cin komai,k'ila kai idan ka tursasata zata ci"


tana gama fad'a ta fice


"me yasa kika k'i cin abinci?


ya tambaya idanuwansa akanta


"banajin cin komai ne shiyasa"


ya bud'e kwanon yace


"to tashi kici yanzu bazeyuwu ki zauna da yunwa ba"




*~y'arfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣0⃣


_wannan page na kune *fans*,hak'ik'a sharhin ku na burgeni kuma yana k'ara k'arfafamin gwiwa,kuna burgeni irin sosai d'innan_


_5:13_🕒 PM

MON,JUL 22


_Bissmillahir rahamanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


daurewa tayi ta tashi ta zauna ya mik'a mata plate d'in abincin


dan bazata iya yi mai musu bane kawai yasa ta amsa tafara ci amma zahiri ji take kamar tana cin magani


kad'an taci ta ajiye plate d'in tare da komawa ta kwanta tana kuma jan bargon


ji yike yi kamar ya janyota jikinsa amma babu hali


hak'ik'a ayanzu k'aunar ta ta zame masa wani sashe na jikinsa


be bar gidan ba sai goma saura,


b'angaren Aasim ma gabad'aya baya cikin natsuwar sa,kullum fata yike rauda tace ta fasa auran umar dan shima bada son ransa yike mata abunda yike mata ba


yana yi ne kawai dan ta janye a kan k'udurinta amma gashi har lokacin bata da alamar janyewa


a gaban gadon da take kwance ya bayyana lokacin har tayi bacci


ya zaune gefen gadon tare da tsura ma kyakkyawar fuskarta ido


wani irin tausayinta ne ya k'ara dabai baye zuciyar sa


a hanakali ya furta


"me yasa Rauda? me yasa zaki zab'i kiyi ta wahala?


ina sonki,ina k'aunar ki bazan iya jurar ganin ki cikin wannan halin ba,ba zan iya ba habibty"


ya k'arasa fad'a cikin yana yin damuwa


kwantawa yayi kusa da ita ya rungumeta ta baya tare da sauke wani numfashi me nawi


tabbas rauda itace farin cikin rayuwar sa,taya ze bari wani ya rab'e ta


lumshe idanuwansa yayi wad'anda suka rine saboda tsananin damuwar da yike ciki


"please Rauda kada ki gujeni,bazan iya rayuwa idan babu ke ba,ki.kasance tare dani dan allah"


ya k'arasa fad'a yana k'ara matse ta a jikinsa


washegari umar ya shirya komai na tafiya yola  driver ya samu wanda ze kaisu ya dawo dasu


ranar asabar dawuri suka tafi dan tara dai-dai suka fita


tafiyar awa hud'u sukayi suka isa yola,wani restaurant suka fara tsayawa


kafin su shiga k'auyen,mama da goggo hanne ne suka fara yin gaba


umar da rauda suna biye dasu


ahankali-ahankali take tafiya dan jikinta babu k'wari 


umar kallonta kawai yike yi da tausayawa 


mama can gefe suka zauna aka kawo musu abinci yayinda umar da rauda ma suka zauna  daga can gefe


duka su biyun tsakurar abincin suke yi dan sam basa jin wata yunwa


ta ajiye cokalin tace

"jaana nifa na k'oshi"


shima aje nasa cokalin yayi yana fad'in


"wallahi nima haka,abincin ma babu dad'i ko na nemo mana abu me ruwa ne?


ta jinjina kai

"amma kafinnan inaso ind'an shiga bayi"


wata ma'ai kaciyar wurin ya kira yace ta nuna mata bayin shi kuma ya tafi inda ake saida drinks


Rauda ta tura k'ofar bayin ta shiga cikin y'an mintoci tagama abunda zatayi 


alwala tayi ta maida hijabinta sannan ta murd'a k'ofar 


saidai ta jita gam,ta kuma murd'awa amma taji k'ofar a gark'ame


jijjiga k'ofar tafarayi amma shuru


tsoro ne ya fara kamata yayinda taga bayin ya fara duhu


ta k'ara jijjiga k'ofar

tana fad'in 

"azo a bud'e!


amma da alamun babu wani a kusa da bayin


motsi taji a bayanta ta waiga da sauri amma bata iya ganin komai dan bayin yayi duhu dund'um


baki ta bud'e zata kurma ihu


taji anrufe mata bakin


hankalinta ya k'ara tashi,k'ok'ari take ta b'anb'are hannun da ya toshe mata bakin amma takasa


wani irin juyewa kanta yafara yi,zubewa tayi awurin a sume


umar tunda ya dawo wurin yike duba agogon wayar sa,ganin anfara kiran sallar magriba gashi har lokacin bata fito ba


goggo hanne ce ta kalli mama tace

"k'auyen nan fa da nisa,ga duhu nayi "


mama tace

"bari naje bayin nace mata tayi sauri,nima bana son tafiyar dare wallahi"


mama ta mik'e tana tambayar wata ma'aikaciyar wurin


"dan allah ina bayin ku yike?"


nuni tayi mata da hanyar bayin,mama ta k'arasa wurin bayuka uku ne,biyu a bud'e alamar babu kowa aciki


sai d'ayan da yike a rufe,k'wank'wasa k'ofar mama tayi tana fad'in


"wai Rauda me kike yi a bayine haka tund'azu "


shuru taji,ta d'an saurara ko zata ji motsin ruwa amma bataji ba


hakan yasa ta murd'a k'ofar


babu kowa a cikin bayin,ta dawo baya kad'an tana nazarin ko akwai wani bayin awurin amma da alamu bayukan kenan


ta dawo wurin ma'aikatan wurin tana tambayar su


"dan allah kuna da wasu bayuka ne bayan wa'ancan?


d'aya daga cikin su ne ta girgiza mata kai


"aa wani abune"


mama tace


"yarinya ce tace zata zaga tund'azu to munji ta shuru shine nai tunanin ko banan ta shiga ba,dan na duba bayukan banganta aciki ba"


"to saidai in wani wurin tayi,danni dakaina na rakata har k'ofar bayin amma muje wurin bayin nagani"


d'ayar tafad'a,komawa ko sukayi sai dai babu alamunta,hankalin mama yafara tashi


da sassarfa ta dawo cikin wurin inda umar yike tace


"kaga fitowar rauda kuwa?


umar ya girgiza kai

"aa "


"to ina tashiga?na duba bayukan wurin gabad'aya bata ciki"


"bata ciki?to ko.sallah taje tayi?


umar ya tambaya da d'anmamaki


mama tace

"to ai da tanan dai zata wuce tunda naga wurin sallar nasu a waje yike"


umar ya sauke numfashi yace


"bari naduba waje to ku k'ara duba cikin ko da tafito bamu lura bane"


babu inda ba a duba ba awurin ba alamar Rauda ba hankalin su mama kad'ai ba har na ma'aikatan.wurin sai da ya tashi


lungu da sak'on wurin babu inda ba a duba ba


A hankali tafara bud'e idanuwanta,harta bud'esu gabad'aya slip d'akin tafara kallo daga bisani ta saukar dasu k'asa


kan wani k'asaitaccen gado ta ganta,mamakine ya kamata ita da take bayi ya akai taganta a kan gado


ahankali k'wak'walwarta ta tariyo mata abunda ya faru


tashi tayi da sauri tana kalle-kalle  babu kowa acikin d'akin 


wata k'ofa tagani,ta diro daga kan gadon dasauri ta nufi k'ofar


Aasim ta hango tsaye yana jera abinci kala-kala akan wani had'add'en dining table


"barka da tashi habibty"


ya fad'a da murmushi a fuskarsa


kallonsa kawai take yi amma takasa furta komai,ya k'arasa inda take ya tsaya gab da ita had'i da d'aura hannun sa akan wuyanta


"zazzab'in jikinki ya sauka ko? nasan kina jin yunwa me kikeso kifara ci"


ture hannun sa tayi tana kallonsa da idanuwanta da suka fara ciccikowa


"ina ne nan ka kawoni?


"ina ne?tambaya kike yi?to gidana ne gidanki kuma inda zakiyi rayuwa ta har abada"


hawayen da suka cika idonta suka fara gangarowa


"me kake nufi Aasim,me kake nufi da kawo ni nan?


"kinga muje kici abinci,sannan kimin tambayoyin"


yafad'a yana kama hannunta tare da yin gaba


fizge hannun tayi tana durk'ushewa k'asa tare da had'e hannayenta wuri d'aya


"narok'eka ka maidani inda ka d'auko ni,kabar ni nayi rayuwa da wanda nike so" 


murmushin takaici yayi yana cigaba da tafiya ya zauna kan wata kujera yana kallonta kawai


ita ko kuka ta cigaba dayi tana cigaba da magiya


"umar shine zab'ina kataimakeni ka rabu dani,kaje kasamu jinsinka dan allah" 


tasowa yayi ya dawo gabanta ya durk'usa yana kallonta da idanuwansa da suka fara rinewa


"Rauda!"


ya kira sunanta,kallonsa kawai takeyi amma ta kasa amsawa


"agabana kike fad'amin wani ne zab'inki ko?kuma inrabu dake ko?


ya kad'a kai yana cigaba da cewa


"to kisani wallahi tallahi babu abunda zesa inrabu dake,rayuwa dake yanzu nafara"


kuma fashewa tayi da kuka tana fad'in


"nidai kamaidani inda ka d'auko ni"


ya mik'e yana yi mata wani mugun kallo


tare da yimata nuni da k'ofar fita


"ga hanya nan ban hanaki tafiya ba ai"


yana gama fad'a ya juya ya bar wurin


kuka takeyi sosai dan tasan umar da mama suna can hankalinsu a tashe


mik'ewa tayi ta nufi k'ofar da ya nuna mata,ta murd'a  dajine sosai me dogayen bishiyoyi 




*~y'arfillo.~*


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣1⃣


_wannan page nakine *karima keffi*,ina godiya da k'aunarki gareni allah ya bar zumunci_💛💛


_3:07_🕒 PM

THU,AUG 1



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


dajine sosai me dogayen bishiyoyi inbanda kukan tsintsaye babu abunda take iya juyowa


zamewa tayi awurin wasu sababbin hawaye na kuma ambaliya a fuskarta


umar ko na can hankalinsa inyayi dubu ya tashi har jami'an tsaro aka kira aka had'u dasu aka cigaba da nemanta amma shuru


goggo hanne ta kira malamin da zasu je wajen sa ta sanar dashi


yace su ma dena bawa kansu wahala dan ba mutum ne ya d'auke ta ba suk'arasa k'auyen kawai


tafi k'arfin awa biyu durk'ushe awurin gabad'aya k'wa-k'walwarta nema takeyi ta dena aiki,ganinta takeyi wani iri takasa gasgata cewa rayuwar da take yi da gaskene


ta sauke doguwar ajiyar zuciya tana kallon sararin samaniya da taurari sukamasa ado


a hankali ta furta

"ya allah ka taimakeni kafitar dani daga wannan rayuwar"


ta k'arasa fad'a wasu siraran.hawaye na biyo kwarmin idanuwan ta


Aasim yana tsaye yana kallonta gabad'aya jin zuciyar sa yike yi babu dad'i sam baya so ya ganta cikin damuwa


bayyana yayi a gabanta ya durk'usa tare da zuba mata kyawawan idanunsa


 itama zuba masa nata idanun tayi da suka jik'e da hawaye


"Rauda wai shin bazaki fahimci k'aunar da nike miki bane?


ya fad'a da damuwa sosai a fuskar sa


"ina k'aunarki kece farin ciki na,dan allah ki rayu dani ni kad'ai nayi miki alk'awari zansaki farin cikin da babu wata mahalukiya da zata fiki jin dad'i a duniya"


ya d'an numfasa yana zaunawa dirshan a gabanta


"miye umar yike dashi wanda bana dashi?ki fad'amin kisani ayanzu babu siffar bazan iya yi ba,zan iya yin komai domin insaki farin ciki..........


katse shi tayi ta hanyar d'aga masa hannu


"idan har kana sona,kuma son da kakemini na gaskiya ne to ka ky'aleni in auri jinsina,naji na amince muciga ba da rayuwa a sirrance amma kabarni na auri umar "


"inbari inga kina rayuwa da wani a matsayin miji? bazan iya ba"


ya fad'a yana girgiza kai sannan ya cigaba da cewa


"kinsan zafin da nike ji a duk sanda naga umar tare dake? kisani zan iya mutuwa a duk ranar da wani mahakuli ya kusance ki,dan haka ki ajiye maganar aure arayuwar ki dan bazan tab'a amincewa ba"


jinjina kai tayi cikin tsananin damuwa,tasa hannu ta share fuskarta tana fad'in


"shikenan Aasim nasan bani da ikon saka ko hanaka,kayi duk abunda kayi niyya kada kabari wani ya rab'eni


amma kasani gangar jikina ce kad'ai zaka cigaba da rayuwa da ita dan zuciyata tana ga umar,ayanzu shine mallakinta.......


runtse idanuwansa yayi dasauri dan jin maganarta yayi kamar wani mashi ya cake sa


ya bud'e su a wahalce yana d'aurasu akan kyakkyawar fuskarta


hannunsa yasa ya janyo ta da k'arfi tare da matseta gam a jikinsa


"duk abunda zaki ce sai dai kice,amma bazan tab'a lamuncewa da wani ya rab'eki ba"


ta janye jikinta kad'a kai


"shikenan,kayi yadda kake so dani,nasan allah yana tare dani kuma nasan wata rana zeyi min maganin komai"


ze kuma janyo ta ta d'aga masa hannu


"kada ka k'ara tab'ani"


ajiyar zuciya ya sauke me nawi tare da mik'ewa ya bar wurin


***   * ***     ***

bayan kwana biyu,addu a malan isa yasa almajiran sa suka duk'ufa yi,tare da saukar al qur ani


shima be zauna ba,ya duk'ufa sosai  haka umar ma da ko abinci ba iya ci


cikin ikon allah aikin da malan isa ya farayi ya fara nasara


ranar ma suna zaune,gaban malan isa wani k'ok'o ne me ruwa aciki


addu'o yike karantowa sosai,cikin ikon allah saiga Rauda ta bayyana aciki lokacin tana zaune ta d'aura kanta bisa gwiwowinta 


aka ci sa a ko,Aasim bayanan


kallonta kawai su mama sukeyi da mamaki k'arara a fuskarsu ganin irin had'add'en.wurin da take me kama da aljannar duniya


malan isa ya sauke numfashi yace


"tabbas inda take ba k'aramin wuri bane,kuma ba k'aramin nisa yike dashi ba,nasan ayanzu idan ni na kirata zataji tsoro saboda bata san muryata ba,dan.haka kai umar matso kusa da k'waryar ka kira sunanta da k'arfi"


umar ya matso jikinsa har rawa yike yi ya kwad'a mata kira


"Rauda!!


d'ago kanta tayi da sauri jin ankirata da kuma muryar umar,sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana maida kanta dan tasan ba dai-dai kunnenta yajiba


malan isa yace 

"ka kuma kiranta kagayamata kaine"


umar ya kuma kiranta a karo na biyo


d'agowa ta kuma yi,da mamaki a fuskarta 


"Rauda kina jina,nine umar"


mik'ewa tayi a zabure,tana kalle-kalle


"umar! kana ina ne?"


malan isa ya matso gab da k'waryar yace


"bazaki iya ganinsa ba amma mu muna ganinki,muna so muyi komai cikin gaggawa kafin Aasim ya dawo dan.haka ki natsu kiji abunda zan.fad'amiki"


jinjina kai tayi dasauri


"fad'i inaji"


malan isa ya sauke numfashi yace


"a yanzu rafanan da nike dasu bazasu iya shigowa inda kike ba,dan haka dole kifito daga cikin wannan gidan kiyi tafiya zuwa inda wata bishiya take"


kad'a kai tayi,tana yin hanyar waje kai tsaye


ta murd'a k'ofar ta bud'e,kallon dajin tayi gabanta na fad'uwa


malan isa yace


"dole ki hanzarta fa,dan ze iya dawowa a kowani irin lokaci"


ta gyad'a kai tana diro k'afarta d'aya k'asa


d'aga k'afar tayi dasauri jin ta taka wasu k'ayoyi masu zafin gaske tare da sakin wata y'ar k'ara


cikin tashin hankali umar yace


"me yafaru chuchu"


"bazan iya tafiya awurinnan ba,gaba d'aya wurin k'ayoyine"


malan isa yace

"ki daure dan wannan ita kad'aice damar da muke da ita,idan har ta kufce to ni gaskiya babu wani abun da zan iyayi kuma"


takawar tafara yi tana runtse idanuwanta saboda tsananin azabar datake ji a tafun k'afafun nata


ko rabin wurin bishiyar bata kaiba ta tsaya tana girgiza kai hawaye masu zafi na biyo kumatunta


"bazan iya cigaba da tafiya ba,bazan iya ba"


cikin tsananin tausayinta umar yace


"Rauda ki daure dan allah,kinji malan yace wannan ce kad'ai damar da muke da ita"


jinjina kai tayi wasu hawayen na ambaliya a fuskarta,ta cigaba da tafiyan


kafin takai gurin bishiyar ta galabaita dan tana kaiwa ta zube


malan isa yace


"yauwa alhamdulillah bari natura su yanzu"


wani turare ya d'auko ya d'iga acikin k'waryar  


saiga wani hayak'i ya fara fita


umar ganin ya dena ganinta cikin k'waryar yasa hankalin sa ya k'ara tashi


"ya naga nadena ganintame ya faru kuma"


murmushi malan isa yayi yana masa nuni can bayansa


umar ya kalli wurin da sauri,Rauda ya hango kwance


tashi yayi ya k'arasa wurin sauri yana kiran sunanta


mamako hannu ta d'aga tana yima allah godiya


Rauda ta bud'e idanuwan ta da suka k'ank'ance saboda tsananin wahalar da ta sha ta d'aurasu akan umar


"sannu Rauda,ya kike jin jikinnaki....


malan isa ne ya katseshi 


"malan umar bamu.da lokaci dan na tabbata Aasim na iya zuwa ayanzu,dan haka dole mu shirya cikin gaggawa"


umar ya jinjina kai


malan ya mik'a ma mama wani ruwan rubutu yace


"bata tasha yanzu"


mama ta tallabota ta bata tatasha,aiko tana sha taji cikinta yafara wani irin hautsinewa 


Aasim yana tsaye cikin katafariyar kasuwar su,tunani yike me ze siya ya kaimata wanda ze sa ta farin ciki


wani rauhani ne ya k'arasa inda yike ya rusuna cikin girmamawa yace


"ranka shidad'e me kake da buk'ata"


Aasim ya sauke numfashi yace


"ina kan nazari ne tukunna"


ya k'arasa fad'a idanuwansa na sauka akan wasu sari had'e da wasu gwala gwalai masu masifar kyau


"yauwa ina buk'atar wa'ancan"


rauhanin ya mik'e ya d'auko ya mik'amai cikin girmamawa


b'acewa yayi,ya bayyana a falonsa inda ya barta


mamakine ya kamasa ganin be ganta a falon ba,ya lumshe idanuwansa


yana ganin abunda yafaru,bud'esu yayi dasauri 


yana furzar da wata iska me zafi




*~y'arfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣2⃣


_wannan page nakine *fatima batula*,na sadaukar dashi gareki kiyi yadda kike so dashi_


_*gaisuwa da fatan alkhairi*_

_*ga duka marubutan mu na golden pen,hak'ik'a ina jinjina muku da kuma alfahari daku a koda yaushe*_


_12:04_🕒 PM

FRI,AUG 2



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



cikin tsananin b'acin rai da tashin hankali ya bayyana a gidan malan isa


kai tsaye ya danna kai ze shiga d'akin da suke amma wani turari me zafin gaske yasa yayo baya da sauri


kallon d'akin yafara yi da wani irin mugun wari ke fitowa daga cikinsa


ya kutsa kai cikin d'akin yana runtse idanunsa dan ji yayi wani zafi ya ratsasa kamar wuta


gabad'ayan su addu'a suke karantowa,banda Rauda da tayi lamo jikin mama tana jin k'wak'walwar ta kamar zata juye


akanta Aasim ya sauke idanun sa da suka kad'a sukayi ja


cikin zafin nama ya finciko ta yana kallon cikin idanunta


"meyasa zaki min haka,meyasa!


nafad'amiki cewa da akwai d'ana a jikin ki,meyasa zaki biye musu kisha wannan bak'in rubutun?


ya tambaya cikin fusata,ta kasa bashi amsa inbanda lumshewa babu abunda idanuwanta suke yi


maida idanunsa yayi kan malan isa da har lokacin yike ta kwararo addu'o


"narantse da allah idan har kayi sanadiyyar rasa d'ana sai ka d'an-d'ani kud'arka"


malan isa yayi ma Rauda nuni da hannu,alamar tayi abunda yasata


da k'yar ta iya bud'e bakinta ta feshe Aasim da turaren data guntsa


baya yayi dasauri yana sakin wata k'ara 


ita ko inbanda rawa babu abunda jikinta yike yi


wasu kalar sark'ok'i ne suka bayyana suka d'add'auresa 


wani kalar kallo yike mata me cike da mamaki


"Habibty,dake za a had'a baki amin haka?


zuciyar tace tafara karyewa ta durk'ushe awurin tana fashewa da kuka


malan isa ya sauke numfashi dan sai lokacin hankalinsa ya kwanta da yaga yayi nasarar kama sa


"duk zaune,ku kuma natsu,ina fatan yanzu zaka tsaya muyi magana ta fahimta"


ya k'arasa fad'a yana kallon Aasim


Aasim kallon Rauda kawai yike yi,yana jin zuciyarsa nayi masa wani irin rawa


"meyasa ka takura ma rayuwarta,me ta maka da ka addabi rayuwarta?


Aasim be bashi amsa ba,dan sam hankalinsa ma baya wurinsa


malan isa ya cigaba da cewa


"ina so ka rabu da ita,ka nisanci rayuwarta"


wani mugun kallo Aasim ya masa tare da cewa


"kada ma ka b'ata bakinka gurin fad'in inrabu da ita dan bazan tab'a rabuwa da ita ba har abada"


malan isa yace

"akan mene bazaka rabu da ita ba,bayan.kasan kasancewar ka tare da ita cutarwa ne a gareta?


"saboda itace farin cikina,matata kuma uwar y'ay'ana"


ya fad'a yana wurga masa wata muguwar harara


malan isa ya jinjina kai

"amma kasan aure be halatta a tsakaninku ba,akan mene bazakaje gurin jinsinka ba?


Aasim yace


"wannan ba damuwar ka bace,ita nagani na zab'a da kuma ita kad'ai zanyi rayuwa"


numfashi malan isa ya sauke yace


"to ina had'aka da allah,da ka furta ka rabu da ita ka kuma yi alk'awarin bazaka sake rab'arta ba"


Aasim ya girgiza kai yana ware idanunsa sosai


"kasani bazan tab'a rabuwa da ita ba"


malan isa ya kuma jinjina kai


"shikenan idan ba zaka rabu da ita dan allah ba,zamu rabaka da ita da ikonsa insha allahu"


ya k'arasa fad'a yana d'auko wata k'warya da ya cikata da rubutu da ruwan addu'a 


ya d'iba ya watsa masa


wani irin k'ara Aasim yayi cikin gigita ya kallesa da mamakin wani irin abu ya sa acikin k'waryar da har yayi tasiri ajikinsa


malan isa ya kuma d'iban ruwan ya kuma watsa masa


wata k'ara ya k'ara saki yana runtse idanunsa cikin azaba


"yanzu zaka rabu da ita ko bazaka rabu da ita ba?


Aasim ya bud'e idanunsa da suka fara k'ank'ancewa yace


"kada kayi tunanin zaka tab'a jin kalamar rabuwa da ita a bakina,kasani duk abunda zakayi sai dai kayi"


malan isa ya jinjina kai yana kuma d'ina ya k'ara watsa masa,ze kuma watsa mai


Rauda tayi saurin dakatar dashi ta hanyar rik'e k'afafun sa


"dan allah kar ka kuma watsa masa,ka k'yalesa haka"


tafad'a cikin tsananin tashin hankali tausayin sa


Aasim yayi murmushin takaici


"kisani wannan zafin da nike ji be kai zafin da nike ji acikin zuciya ta ba,na cewa kinzab'i rabuwa dani,ki barshi ya cigaba da aikinsa"


kafin ta kuma magana,malan isa ya cigaba da watsa masa


kuka Rauda keyi sosai kamar ranta ze fita


yasha matuk'ar wahala gabad'aya jikinsa ya wani irin kwakkwailewa kamar an watsa masa ruwan zafi


saida ruwan addu'ar ya k'are gabad'aya sannan malan isa ya koma ya zauna yana mamakin kafiya irin na Aasim


"wannan wahalar bata isheka bane da kakasa amincewa da abunda nasaka?


Aasim ya d'ago kansa yace


"kasani da zan rasa raina ne,bazan tab'a rabuwa da Rauda ba"


tsananin tausayin sa ne ya k'ara dabai-baye zuciyar ta


a durk'ushe ta k'arasa gabansa idanuwan ta na tsiyayar da hawaye


ya kalleta yana murmushin takaici


"kinyi farin ciki ko habibty?haka dama kike so ko,da kinsan bazakiyi rayuwa dani ba da baki amince min ba tuntuni,ki kasa na k'ara shiga duniyar k'aunarki amma yanzu zaki juya min baya ko?


tabbas mahaifina yayi gaskiya da yace nayi babban kuskure da na baki yardata,amma ina so kisani bazan tab'a rabuwa dake ba duk da kin butulce min domin kece zab'in zuciyata"


zuciyar ta k'ara karyewa cikin raunanniyar murya tace


"kayi hak'uri Aasim,bada son raina bane amma umar shine farincikina kayi hak'uri kabarni na rayu dashi amatsayin mijina,ka amsa ka rabu dani bazan iya jurar ganin ka cikin wannan halin ba"


murmushin takaici yayi yana kad'a kai


"nasan bazaki tab'a ganewa ba,bazaki tab'a gane irin k'aunar da nike miki ba,dan da ace kinsan ko da rabin.k'aunar danike miki ne dake kanki baki zab'i ki rabu dani ba,amma babu komai"


kuma fashewa tayi da kuka,tana jin zuciyar ta na yima ta wani irin ciwo


malan isa ya taso hannunsa rik'e da wata kwalba yace


"idan har baka amince ka rabu da ita ba,zan saka.cikin kwalbar nan ka k'arake rayuwar ka acikin ta,dan haka gaggauta yin abun da nace"


Aasim ya kuma murmushi har lokacin idanuwan sa na kanta


"ta tafi da komai nawa,soyayyar ahalina,matsayina da kuma muk'ami na sannan kuma da soyayyata,bazan tab'a yin abunda kake so ba,amma idan har ita tana kan bakanta na son rabuwa dani to kayi duk abunda kayi niyya"


malan isa ya gyad'a kai yana k'ok'arin bud'e kwalbar


girgiza kai Rauda tafara yi 


"Aasim aa,dan allah "


yayi mata kallon takaici yace

"bazan tab'a yarda ina gani.wani ya rab'eki ba,idan har hakan yana ganin shine dai-dai kuma maslaha yayi"


zata kuma magana malan isa ya kalli mama yace


"kufita da ita"


mama ta kama hannun ta,k'wace hannun tayi tana k'ara sawa gabansa


cikin kuka tace

"Aasim banace ka rabu dani bane gabad'aya kabarni kawai nai aure shine buk'atata narok'eka.......


malan isa ya katse ta yana cewa mama


"nace kufita da ita ko"


tana turjewa mama da goggo hanne suna janta ahaka suka fita da ita


k'ok'orin.komawa d'akin take yi amma sun hanata,gabad'aya k'wak'walwarta ta hautsine,ahankali tafara ganin duhu a idanunta


daga nan bata k'ara sanin inda kanta yike ba


sai dai farkawa tayi ta ganta a gadon Asibiti


ahankali tagama bud'e idanunta ta sauke su akan umar da ke zaune kan kujerar dake gaban gadon


cikin farin ciki ya mik'e yana fad'in


"chuchu kin farka sannu"


d'aga mai kai,ya tsiyayo ruwa a kofi yana mik'a mata


yunk'urawa tayi ta tashi,tana jin jikinta yayi mata sakayau kamar  ancire.mata wani abu me nawi


"me ya kawoni asibiti kuma?


ta tambaya tana amsar kofin ruwan,umar yayi murmushi yana fad'in


"rashin lafiya mana,amma ya jikin naki me ke miki ciwo?


ta girgiza kai dan ji take kamar tafara wata sabuwar rayuwa,gaba d'aya jikinta babu inda ke mata ciwo 

"ba ko ina,yaushe aka kawoni.asibiti"


"yau kwanan ki uku"


ta d'an ware ido da mamaki


"kwana uku?


umar ya d'aga kai


"eh kina ta bacci ba,ni da harkin fara bani tsoro ma"


d'an murmushi tayi 


"habadai kayi zaton bazan farka bane.......


kasa k'arasawa tayi sakamakon tunawa da Aasim da tayi


kallon ta umar yayi sosai ganin yadda ta tsaya cak tana k'walalo idanu


"me ya faru?


ya tambaya yana kafeta da ido


"Aasim,ya aka.k'are dashi?


ta tambaya zuciyar ta narawa


umar ya sauke ajiyar zuciya yace


"wannan kima manta da zancen sa anriga da an rufe babinsa"


ji tayi zuciyarta tayi mata wani iri,gaba d'aya saitaji babu dad'i 


ganin zata shiga wani tunani na daban yasa yace


"kinga chuchu me kike so kici,dannasan kintashi da yunwa"




hmmmmmm ina da exam,plz kutayani da addu'a allah ya bani sa'a



*~y'arfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣7⃣



_Wannan page nakine *ummu sayyid* ina godiya da ƙaunarki ga jinnul aasshique_



_11:38_🕒 PM

WED, OCT 23



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


*Daga Cikin Ayyukan Alheri Da Kyawawan Halaye*


*Jabir bn Abdullahi, Allah ya yarda da shi, ya ce; Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Idan duhun dare ya gabato – ko kuma almuru ta yi – to ku hana 'ya'yanku fita, domin shaidanu suna bazuwa a wannan lokacin. Idan sa'a ta gota a cikin dare, to sai ku bar su. Ku rufe kofofi, kuma ku ambaci sunan Allah (yayin da kuke rufewa), domin Shaidan ba ya bude kofa rufaffiya. Ku zuge bakin salkunan ruwanku, kuma ku ambaci sunan Allah (yayin da kuke zugewa), kuma ku rufe kwanukan abincinku, ku ambaci sunan Allah (yayin da kuke rufewa); ko da ku dora wani abu ne a kan kwanukan. Kuma ku kashe fitilinku na a-ci-balbal.*


*Allah ya yi tsira da Aminci da albarka ga Annabinmu Muhammadu, da alayensa da Sahabbansa baki daya.*





Shin wai meke damunka ne Umar? Kana cikin hayyacin ka kuwa?


Ɗaga mata kai yayi yace

"nadai faɗa miki kada ki sake ki taɓani"


Ajiyar zuciya ta sauke me nauyi tare da miƙewa ta juya zata fita har ta kai bakin ƙofa ya kira sunan ta dan yadda yaga yanayin ta ya sauya Sam sai yaji beji daɗi ba


"Rauda!


Dakatawa tayi batare da ta juya ba


" kiyi haƙuri kinji?


Hmmmm ta sauke guntun numfashi tana cigaba da tafiya


"Rauda!


Ya kira sunan ta a karo na biyu


Juyowa tayi tana jingina da jikin ƙofar ta zuba mai ido kawai batare da ta amsa ba


Umar ya yunƙura ya tashi da ƙyar ya koma kan gadon har lokacin idanuwansa na kanta


" Rauda ina so ki ɗaukar min alƙawari tare da yin rantsuwar cewa ba zaki taɓa aikata abunda Aasim ya saki ba"


Sai lokacin ta gane dalilin da yasa yaƙi yadda ta taɓasa


Tsananin tausayin sa ne ya ƙara kanannaɗe zuciyar ta


Take hawaye suka ciko idanuwanta


"ina sonki Rauda, kisani idan kika aikata abunda ya saki yayi nasara wallahi ba tausayin rayuwa ta kika yi ba, ki sani zan kasance acikin farin ciki idan har zan cigaba da rayuwa da ke,ki taimaki zuciyata da ƙaunar da nike miki ki bar mu mu cigaba da rayuwa a haka "


Ya ƙarasa faɗa muryar sa na ƙara raunanewa



Komawa cikin ɗakin tayi ta zauna nesa kaɗan dashi


" shikenan ka kwantar da hankalin ka babu abunda zanyi Insha Allah "


" kinyi alƙawari?


Ya tambaya yana kafeta da ido


Ɗaga masa kai kawai tayi, amma a zuciyar ta bata fasa abunda tayi niyya ba


Hannu ya miƙo mata yana murmushin ƙarfin hali


Matsawa tayi ta kwantar da kanta a jikin sa


Gauron numfashi ya sauke yana lumshe idanuwansa a hankali


"kece kwanciyar hankali na Rauda ina sonki"


Ya faɗa a sanyaye


Aasim yana tsaye yana kallon su ta cikin madubin sa, wani irin baƙin ciki da kishi ne suka dunƙule suka tarun masa a wuri ɗaya


Wai Raudan sace kwance jikin wani yana faɗa mata kalaman soyayya, da ransa da lafiyar sa


Zagaye ɗakin ya fara yi yana furzar da wata iska me zafi dan shi kaɗai ya san yadda yike ji a ransa


Baze yuwu ba, baze yuwu in zuba muku ido ba na baki kwana biyu kacal wallahi idan baki aiwatar da abunda nace ba zakiga abunda zanyi


Ya faɗa a zafafe


Rauda taji maganar da yayi, gabanta ne ya faɗi


Aasim ya cigaba da cewa

"ki tashi daga jikin sa inba haka ba yanzu na illa ta shi"


Ta shi tayi da sauri ta ɗan ja baya kaɗan tana zazzare ido


Kallon ta umar yayi yace


"lafiya chuchu?


Girgiza kai tayi tace

" babu komai "


Ya gyaɗa kai ba tare da ya ƙara cewa komai ba


Aasim numfashi ya sauke me nawi dan sai lokacin ya ɗanji raɗaɗin da yike ji aransa ya ragu


Fulawar saƙo ce ta sauka a hannun sa ya buɗe ta


Saƙon ammi ne cewa tana son ganin sa ya same ta a iyakar shiga masarauta


Bayyana yayi a wurin, tana tsaye jikin bishiyar da suka saba haɗuwa a wurin, dan bayi da ikon shiga masarauta tun bayan tsalle ke tauran da yayi


Kallon sa ammi take yi cike da tsananin damuwa a fuskar ta ganin yadda ya lalace duk akan bil'adama


Cikin girmamawa ya gaishe ta, bata amsa mai ba illa zuba mai ido da tayi


Zuwa can ta kira sunan sa


"Aasim!


" na'am ammi"


Ya amsa yayin da yike ɗagowa yana duban ta


"yanzu kana ganin rayuwar da zaɓarma kanka ta dace da kai kenan?


Ta tambaya tana yi masa wani irin kallo


Ƙaƙaro murmushi Aasim yayi yace


" ammi nafaɗamiki kidena damuwa a kaina ina cikin farin ciki...


"ƙarya kake yi Aasim, dubi yadda ka lalace ka sauya kamar ba yarima ɗan babban sarki ba,da gatan ka da komai Aasim ka zauna kana wahala akan mace macen ma bil'adama wacce tayi maka butulci"


Ta ɗan tsaya sannan ta cigaba da cewa


"me yasa bazaka cire ta a ranka ba? Ga mata nan bila adadin a duniya Aasim zaka samu wacce tafi ta ka dawo masarauta ka nemi gafarar mahaifin ka ka dawo cikin gatan ka inda ake tarai-rayar ka Sam bana jin daɗin yadda nike ganin ka a haka"


Murmushin takaici yayi dan ya san ammi bazata taɓa ganewa ba, da zata gane son da yike ma Rauda da Sam bazata rinƙa faɗin maganganu haka ba shi kansa besan dalilin da yasa yike mata so me tsanani ba ya kuma kasa haƙura da ita


Guntun numfashi ya sauke har lokacin kansa na ƙasa


Ganin bayi da niyyar magana yasa ta girgiza kai cikin damuwa


"shikenan tunda har yau bani da matsayin da zance kayi abu kayi, nagode"


Matsowa yayi kusa da ita ya kamo hannun ta suka zauna still hannun ta na riƙe cikin nasa


Sam ya kasa danne hawayen da suka ciko kwarmin idanunsa


Cikin muryar sa me taushi yace


"ki gafarceni ammi,nasan ni me laifi ne tunda har na bijire wa umarnin ku, amma kimin uzuri dan Allah ammi, ammi nikaɗai nasan yadda nike ji acikin raina bazan iya rabuwa da ita ba"



Ammi tausayin sa ne ya ƙara ka mata dan tasan duk abunda zesa sa kuka ba ƙaramin abu bane


Nisawa tayi tana ajiye Gauron numfashi


"shikenan Aasim, Allah ya kawo ma mafita amma ka rage sanya ranka cikin damuwa kaji?


Gyaɗa mata kai yayi ba tare da yace komai ba


Magana tayi wa jakadiyar ta dake can gefe sai gata ta bayyana hannun ta ɗauke da shahida



Shahida na ganin sa ta faɗa jikin sa a guje cike da tsananin farin ciki


Aasim ya ɗagota cike da jin daɗin ganin ta dan tunda ya bar masarauta rabon shi da ya sake ganin ta dan sarki ramzad ya hana a fita da ita ko ina


"shahida na!


Ya faɗa yana kallon ta, cikin murna ta ƙara shige wa cikin jikin sa


Ammi dake kallon su cikin tausayawa tace


" kullum maganar ta baya wuce ina abban ta, amma me martaba ya hana fita da ita ko nanda can yau ma dan yayi tafiya ne Shine na samu na ɗauko ta"


Aasim yayi murmushi dan ganin ƴar tasa yasa yaji sanyi


"yaushe ze dawo ammi?



" kwana uku zeyi"


Ta bashi amsa


Aasim yace

"ammi to dan Allah Kibari in tafi da ita inyaso jibi da sassafe sai in maido da ita"


Ammi ta ɗan yi shuru tana nazari


"dan Allah ammi"


Ya faɗa cikin marai-raicewar murya


"shikenan kutafi"



Ƙarfe sha biyu saura ya dawo gida, kan kujera ya zaunar da ita ya cika mata gabanta da kayan tanɗe-tanɗe


Sai da ya tabbatar ta ƙoshi sannan ya tasa a gaba tana ta yi masa surutu 


Dariya yike yi sosai, harda riƙe ciki abunda rabon shi da yayi har ya manta 


Shahida yarinya ce me wayau da basira, sai da suka kwanta zasu yi barci sannan tace 


"Abi ina ammina? 


Danne abunda yaji a zuciyar sa yayi da ya tuna inda take ya ƙaƙaro murmushi yace 


" kina son ki ganta ne? 


Ɗaga mai kai tayi, ya ɗago yace 


"to gobe zan kaiki wurin ta kinji, yanzu ki kwanta kiyi barci kinji? 


Murmushin jin daɗi tayi, ta kwanta a Jikinsa bata daɗe ba barci ya ɗauke ta 


Sai da ya tabbatar da baccin nata yayi nisa sannan ya kwantar da ita ya tsura ma fuskar ta ido yana jin ƙaunar ta a cikin ƙoƙon ransa  


Madubin sa ya saita zuwa wurin Rauda 


Tana kwance tana bacci fuskar nan tata tayi fayau kamar wacce ta yi watanni tana ciwo


A hankali yasa hannu ya shafi gefen fuskar ta cikin kalar wani yana yi na shauƙin ta, da yanzu suna tare suna soyayya amma wannan banzan ya ruguza masa tsarin sa 


Lumshe idanuwan sa yayi yana ƙissima abubuwa da yawa a cikin ransa


Ɗan murmush yayi yabuɗe idanun yana kuma ɗaura su a kanta 


"Rauda ke tawa ce nikaɗai" 


Ya faɗa cikin wata kalar murya 




*~Ƴarfillo.~*



*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



*Addu'ar Sallar Istihara (Neman Zabin Allah Idan Mutum Zai AikaTa Wani Abu).*




*Jabir Ibn Abdullah, Allah ya yarda da shi da mahaifinsa, ya ce; Manzon Allah (SAW), tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana koya mana yin istihara (neman zabin Allah) a Cikin dukkan al'amura kamar yadda yake koya mana sura daga Cikin Alkur'ani, yakan ce, "Idan dayanku ya yi niyyar yin wani al'amari to ya yi sallah raka'a biyu ba ta farilla ba, sannan ya ce;*


اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْألُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيم، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلا أَقْدِر، وَتَعْلَمُ وَلا أَعْلَم، وَأَنْتَ عَلاّمُ الغُيوبِ، اللّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ- وَيُسَمِّي حَاجَتَهُ - خَيْرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، عَاجِلِهِ وَأَجِلِهِ فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ شَرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ وَاصْرِفْنِي عَنْهُ وَاقْدُرْ لِي الْخَيْرَ  حَيْثُ كَانَ ثُمَّ أَرْضِنِي بِهِ.



*Allahumma innee astakheeruka bi'ilmik, wa-astaqdiruka biqudratik, wa-as-aluka min fadlikal-'azeem, fa-innaka taqdiru wala aqdir, wata'lamu wala a'lam ,wa-anta 'allamul ghuyoob, allahumma in kunta ta'lamu anna hazal-amr (say your need) khayrun lee fee deenee wama'ashee wa'akibati amree fakqurhu lee, wayassirhu lee, thumma barik lee feeh, wa-in kunta ta'lamu anna hazal-amr sharrun lee fee deenee wama'ashee wa'aqibati amree fasrifhu 'annee wasrifnee 'anh, waqdur liyal-khayra haythu kan, thumma ardinee bihi.*


*Ya Allah! Ina neman zabinka domin iliminka, kuma ina neman Ka ba ni iko domin Ikonka, kuma ina rokonka daga falalarka Mai girma; domin Kai ne mai iko ni kuwa ba ni iko, kuma Kai ne Masani, ni kuwa ban sani ba, kuma Kai ne masanin abubuwan fake. Ya Allah! Idan ka san cewa wannan al'amari sai ya ambaci bukata tasa alheri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata, da kuma karshen al'amarina a wata rayuwar; da magaggaucin ala'marina da majinkircinsa Ka kaddara mini shi, kuma Ka saukake mini shi, sannan Ka albarkance ni a cikin sa. Kuma idan Ka san wannan al'amari sharri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata da karshen al'amarina a wata ruwayar; da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa – Ka kawar da shi daga gare ni, kuma Ka  kawar da ni daga gare shi, kuma Ka kaddara mini alherin a duk inda yake, kuma Ka sanya ni in yarda da shi".*


*Duk wanda ya nemi zabin mahalicci, kuma ya yi shawara da talikai muminai, kuma ya yi azama a Cikin lamarinsa, to ba zai yi nadama ba, domin Allah madaukakin sarki Ya ce;*


(وَشَاوِرْهُمْ فِي اْلأَمْرِ فَإِذَا عَزَمْتَ فَتَوَكَّلْ عَلَى اللهِ)



*(Washawirhum Fiyl Amri Fa'iza Azamta Fatawakkal Alallahi).*


*"Kuma ka shawarce su cikin lamarinka, idan kuma ka kuduri aniya, to ka dogara ga Allah".*




Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣8⃣


_wannan page nakine *jamila Aliyu* masoyiyar Aasim, Aasim yana yinki irin sosai ɗinnan_



_10:23_🕒PM

Sun, Oct 27


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


_(mu yawaita karatun al qur'ani,mu maida al a marin mu ga ubangiji dan shi ze yi mana maganin komai, Allah ya tsarkake zuciyar mu ya biya mana buƙatun mu amin)_



Tun cikin dare umar ya farka sakamakon wani azazzaben ciwon ciki da ya farkar dashi


Zamowa ƙasa yayi yana riƙe cikin, cikin tsananin wahala


Sai da yayi ta karanto addu'a sannan yaji cikin ya lafa masa, gumi ne kawai ke ta keto masa duk da ac ɗin da yike ƙure kuwa


_"ya Allah ka kawo min agaji, ka fitar dani daga cikin wannan ƙangin"_


Ya faɗa a hankali,komawa yayi kan gadon ya tsura ma fuskar ta ido,ko kaɗan baya jin a ransa cewa ze iya rabuwa da ita, ko da kuwa wannan ciwon zeyi ajalin sa ne


Shin wace irin ƙauna ce yike mata, Meyasa yike jinta a cikin jinin jikin sa?


Tabbas ita ɗin ta dabance,haka yayi ta saƙe-saƙe


Washegari jikinsa ya kuma tsanani sosai dan magana ma da ƙyar yike iya yi


Tana tsaye a gefen gadon tana kallon sa, gabaɗaya ya fita hayyacin sa zayyad ne zaune gefen sa yana goge masa jikin sa da towel


Fita tayi daga ɗakin jin kuka na neman ƙwace mata, ɗakin ta ta shiga ta zauna takifa kanta akan gwiwarta wasu hawaye masu ciwo suna gangaro mata


Motsi taji a gefen ta, ta ɗago kanta a hankali,shahida tagani a gefen ta


Zuba mata ido tayi taka sa ce mata komai


"ammi"


Shahida ta faɗa cikin murmushi, Rauda tayi ƙoƙarin ƙaƙaro nata murmushin tana faɗin


"shahida, kece? Waya kawo ki?


"abbi"


Ta bata amsa a taƙaice,kallon ta Rauda ta cigaba da yi tana mamakin irin kyan yarinyar


Shahida ta kwantar da kanta kan cinyar ta tana faɗin


"kullum-kullum sai na cema Ammi babba takawoni inganki sai taƙi, Ammi ina son ganin ki kullum kice ma abi ya barni anan kinji?


Ɗan murmushi Rauda tayi tare da ɗagota tace


" kina son ki zauna tare dani shahida?


Shahida ta ɗaga kai


"shikenan Kibari nan gaba zan sa a dawo min dake nan kinji?


Cikin murna da jin daɗi Shahida tace

" to ammina"


Rungume ta Rauda tayi tana ɗan shafa bayan ta


"ina babanki?


"yana can gida yace ina gama ganin ki ze zo ya ɗaukeni"


Rauda ta gyaɗa kai


Sai bayan awa ɗaya sannan Aasim ya bayyana a cikin ɗakin 


Kallo ɗaya yayi ma Rauda ya ɗauke kansa yana duban Shahida 


"tuffah zo mu tafi ko? 


Maƙale kafaɗa tayi 

" nidai anan zan zauna"


"tuffah bakya so na kawo ki gobene? Taso mu tafi kinji? 


Shahida ta marairaice fuska tana duban Rauda 


"ki tashi ku tafi kinji, baki ji yace ze kawo ki gobe ba" 


Rauda ta faɗa, Shahida ta mayar da kallon ta ga Aasim tace 


"to abi kace ammi ta tashi mu tafi tare" 


Durƙusawa Aasim yayi ya kama hannun ta yana murmushin takaici 


"Shahida na anmin ki bazata bimu ba, bata son rayuwa damu kiyi haƙuri kinji" 


Shahida zata kuma magana ya girgiza mata kai 


"kada ki ƙara cewa komai" 


Ya ƙarasa faɗa yana miƙewa tare da ɗaukar ta


Juyawa yayi zetafi batare da ya ƙara duban inda Rauda take ba 


"ina son yin magana da kai" 


Ta faɗa idanuwanta a kansa 


Tsayawa yayi batare da ya juya ba


"inajin ki" 


Ajiyar zuciya ta sauke tare da miƙewa ta zagayo gabansa 


Kallon cikin ido su kayi ma juna, daga bisani ta zame nata idanun 


"gobe ne zan aiwatar da abunda kace saboda na zaɓi lafiyar sa akan zamana dashi" 


Ta ɗan numfasa tana ɗago idanuwanta ta kuma ɗaura su akan sa


"zan rabu dashi kamar yadda ka umar ta, amma inaso kasani bazan cigaba da yin tarayya da kai ba, zan yi rayuwa ta ni kaɗai" 


Be bata amsa ba sai da yaɓattar da Shahida zuwa can gida dan baya so yayi magana a gaban ta 


Sannan ya matso gab da ita yana kallon ta da idanuwansa da suka fara canza launi 


"ni kike faɗa mawa ba zaki cigaba da yin tarayya dani ba? 


Ki tuna cewa kinyi alƙawarin yin rayuwa dani har abada, dan haka baki isa ki janye wannan alƙawarin ba ki shirya ma cigaba da rayuwa dani har zuwa tsufanki" 


Be jira yaji abunda zata ƙara cewa ba ya ɓace 


Dafa kanta tayi da yike mugun sarawa,ta lalubo layin anty ummi ta sanar mata halin da ake ciki da kuma abunda zata yi


Cikin kuka take mata magana, ta ƙara da cewa 


"kije gida ki sanar ma su mama dan zuwa nan da kwana uku zan taho" 


Anty ummi cikin damuwa tace 


"amma Rauda aganina karki aikata wannan abun,ki ƙara jira aƙara gwada na wasu malamai" 


Girgiza kai Rauda tayi tace 


"dan baki ga halin da yike ciki bane anty, yaufa ko magana baya iya yi, haka Allah ya so kawai" 


Katse wayar tayi tana cigaba da yin kuka


Anty kaltum da ta daɗe tsaye a bakin ƙofa ta sauke numfashi tana ƙarasa shigowa cikin ɗakin 


Zaunawa tayi gefen ta tace 


"Rauda dan Allah ki kwantar da hankalin ki,ki dena kukannan haka dan ba maganin da ze yi miki" 


Cikin shesshekar kuka tace 


"shi kaɗai yike ragemin raɗaɗin da nike ji anty" 


Anty kaltum ta kuma sauke numfashi a karo na biyu 


"bana so kina sawa ranki damuwa,ina da yaƙinin komai ze wuce ya zama tarihi Insha Allahu" 


Kaɗa kai kawai Rauda tayi,suka yi shuru naɗan lokaci sannan anty kaltum tace 


"nida zayyad mun gama shirya komai, gobe idan Allah ya kai mu sai kiyi abunda yace ɗin, amma duk da haka ba zamu zauna ba dan ma yadda jikinna sa yayi tsanani ne da ba zaki yi abunda yace ba,amma nan da sati ɗaya zantafi Sudan wata ƙawata ta cemin akwai wani malami ƙwararre acan,zanje gurin sa"


Rauda ta jinjina kai kawai dan a yanzu itama maganar wahala take yi mata 


Yana zaune ƙasan wata bishiya yana kallon shahida dake ta tsalle-tsallenta dan ita ta matsa sai ya fito da ita 


Gabaɗaya ya Lula cikin tunani maganar ta ce kawai take yi masa yawo a kunne



_"zan rabu dashi kamar yadda ka umar ta, amma inaso kasani bazan cigaba da yin tarayya da kai ba, zan yi rayuwa ta ni kaɗai"_


Ajiyar zuciya ya sauke,tare da miƙewa ya kama hannun shahida


"tuffah mu tafi gida ko, kinga anfara kiran sallah"


Shahida ta ajiye sandar da take wasa da ita suka fara tafiya, sun zo wuce wa ta wani gida wata yarinya ta watso ruwan zafi sai a ƙafar shahida


Ƙara shida ta saki, Aasim yayi saurin durƙusawa yana duba ƙafar


Ita ko wacce ta watso ruwan ko a jikinta harkokin ta ma ta cigaba da yi dan ita bata san akwai wasu bayin Allah a wurin ba


Mahaifiyar ta dake zaune nesa kaɗan da ita tace


"wai bana hanaki zubar da ruwan zafi ƙasa bane?


Aasim numfashi ya sauke ya ɗauki shahida ya wuce


Kan kujera ya zaunar da ita yana sa mata ruwan sanyi a ƙafa


Sai da taci kukan ta sosai yana lallashin ta sannan tayi shuru


Zuwa can tace


" abi Meyasa baka yi mata magana ba, ƙonani fa tayi kuma naji zafi"


Murmushi Aasim yayi yana kama hannun ta yace


"shahida na,ki sani mu halitta ne da Muke rayuwa a ɓoye dole ne sai mun sa haƙuri a zuciyar mu, kinga ita bata san mun zo wuce wa ta wurin ba tunda bata ganin mu,kiyi haƙuri kinji?


_(mu kiyayi watsar da ruwan zafi a ƙasa,domin muna iya watsawa a kansu kuma idan ba aci sa'a ba aka watsa ma marasa haƙuri sai kuga sun shafi lafiyar mutum,mu kiyaye dan Allah)_


Shahida ta jinjina kai


"yauwa yarinyar kirki Allah yayi miki albarka"


Ya faɗa yana janyo ta jikin sa


Washe gari,Rauda na zaune gefen sa, shi ko yana kwance kamar matacce


Share guntun hawayen da ya zubo mata tayi ta shafa hannun ta sai ga ƙaramar wuƙar ta fito


Kamar anfaɗa masa ya buɗe idanuwansa ya tsura mata ido


"Rauda na faɗa miki, bazan yafe miki ba idan har kika aikata hakan"


Umar ya faɗa da ƙyar


"ka gafarce ni umar,ka gafarce ni........


Ta faɗa tana caka mai wuƙar


Runtse idanuwansa yayi jin wani sabon raɗaɗi a ƙirjin sa ahanakali yaji tunanin sa ya fara gushewa


Ita ko kuka ta fashe da shi,daidai lokacin su anty kaltum suka shigo


 Minti arba'in ya kwashe a sume,abun har ya fara basu tsoro ganin har lokacin ko alamar motsi baya yi


Sai da ya kwashe awa ɗaya a haka sannan ya sauke numfashi tare da yin miƙa yana karanto addu'ar farkawa daga barci


_alhamdulillahil lazi ah yana, ba'a dama a matana wa ilaihin nushur_


Ya ƙarasa faɗa yana buɗe idanuwansa gaba ɗaya


Ɗai-ɗaiya ya fara kallon su, dan shi ji yayi kamar daga barci ya tashi


Ganin yadda suka mai ƙuri-ƙuri da ido ya sa ya tashi zaune yana kuma ƙare musu kallo


Ɓangaren Aasim kuwa jiya yi zuciyar sa tayi fes,ajiyar zuciya ya sauke me nawi yana kishin giɗa a kujera




*~ƴarfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



*Daga Addu'o'in neman tsayar da ruwan sama*


اَللَّهُمَّ حَوالَيْنَا وَلاَ عَلَيْنَا، اَللَّهُمَّ عَلَى اْلآكَامِ وَالظِّرَابِ، وَبُطُونِ اْلأَوْدِيَةَ، وَمَنَابِتِ الشَّجَرِ.



*Allahumma hawalayna wala 'alayna, allahumma 'alal-akami wazzirab, wabutoonil-awdiyah, wamanabitish-shajar.*


*Ya Allah! Ka sanya shi ya zuba a kewayenmu ba a kanmu ba. ya Allah! Ka sanya shi a kan jigayi da duwatsu, da cikin rafuka, da wajen saiwoyin itatuwa.*




Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 3⃣9⃣



_Wannan page nakune masoya na masu haƙuri da daɗewa da nike yi amma still suna biye dani ina roƙon Allah da ya bar mu tare ya kuma ƙara danƙon zumunci a tsakanin mu_


_9:34_🕒 AM

Sun, Nov 3



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Sai da yayi wanka ya sauya kaya zuwa blue jeans da farar t-shirt sannan ya sauko ƙasa


A kan dining ya same su, anty kaltum da mijinta, hajiya,da kuma zayyad


Ya zauna yana faɗin

"wai hajiya yaushe kika zo ƙasar ne? Sam ni na kasa fahimta ga yana yin gidannan duk ya Sauya kamar bashi ba"


Kasa bashi amsa suka yi dan basu san me zasu ce mishi ba


Amsar plate ɗin da anty kaltum ta miƙo mai yayi, har ɗiba a cokali ze kai bakin sa idanuwansa suka sauka kan zayyad,a iya sanin sa da zayyad baya ƙaunar gashi a fuska amma gashi duk ya bar sake da gemu


Aje cokalin yayi da mamaki sosai a fuskar sa


"zayyad yau Kaine da saje? Shekaran jiya fa da muka rabu babu komai a fuskar ka"


Zayyad ya ɗan daburce yana tunanin amsar da ze basa


Tsura musu ido umar yayi tabbas akwai abunda suke ɓoye masa cikin yanayin damuwa yace


"wai dan Allah me yike faruwa ne? me kuke ɓoye min?


Alh sadik(mijin anty kaltum) shine dabara ta faɗo masa yace


"umar dole fa zaka sauye-sauye da yawa,domin yau shekarunka biyar kenan kana barci sai yau Allah yasa ka farka"


Zaro ido umar yayi yana kallon Alh sadik, daga bisani kuma ya kece da dariya


Ido kawai suka zuba masa, sai da yayi dariyar sa me isar sa sannan yace


"wani irin bacci ne kuma na shekara biyar?dan Allah baban Salim ka ajiye wasannan a gefe ku faɗamin me yike faruwa?


Hajiya tace

" da gaske ne abunda ya faɗa ma,Allah ya jarabce ka da lalura kuma dai tunda ya yaye maka banason yawan tambayoyi"


Shuru umar yayi yana kallon hajiya, dan Sam be yarda da maganar su ba,amma ganin yanayin da suka shiga yasa yace


"shikenan hajiya, kice inji tsoron ƙara kwantawa barci kada insake yin na shekara goma"


Ya ƙarasa faɗa yana guntse dariya


 Zayyad ya miƙe yana faɗin

"ni ina ganin zan wuce"


Umar shima ya miƙe yace

"bari mu fita tare,inga gari dan nasan abubuwa sun caccanza shekaru biyar ba wasa bane"


Ya faɗa cikin tsokana da dariya


Anty kaltum ta girgiza kai tace

"bafa inda zaka je umar dan baka gama warware wa ba kabari ka ƙarasa jin sauƙi tukunna"


Be saurare ta ba yayi gaba yana ɗan jijjiga jikin sa


"anty ni wallahi ƙalau nike,sai na dawo"


A tsakar gida ma, motocin da ya sani basu ya gani ba har ze yi magana sai kuma ya fasa yana faɗin


"komai ya canza, hajiya tace banda yawan tambaya, zayyad wacece motar ka a ciki?


Ya ƙarasa faɗa yana kallon zayyad


" banzo da mota ba"

Zayyad ya bashi amsa


 "Ok mu shiga waccan Naga kamar da makulli a ciki"


Shiga suka yi ya tada motar,tunda suka hau titi babu wanda yayi magana, jefi-jefi dai umar kan kalli zayyad ya tun tsire da dariya


Abun ya fara ba zayyad haushi cikin ƙufula yace


"wai mahaukaci na zamar ma ne?


Umar ya kuma yin dariya har da buga sitiyari


" no abokina sajennan ne naga yayi ma kyau sosai, sai yasa ka zama kamar wani ustaz wallahi"


Tsaki zayyad yayi yana maida kallon sa gefe


Umar ya kuma dariya


"yi haƙuri abokina, faɗamin yanzu ina zamuje?


"ka ajeni a gida inyaso duk inda zaka je sai kaje"


"ai baka isa ba wallahi, tare muka saba fita kuma dolenka yanzu ma mu je da kai"


Sanin halin sa da zayyad yayi yasa marai-raice fuska yace


"please umar wallahi kaina ciwo yike yi"


Umar gyaɗa kai yayi yana canza hanya zuwa hanyar gidan su


A ƙofar gida ya ajesa sannan ya dinga zagaye gari bashi ya koma gida ba sai sha ɗaya da rabi


Lokacin duk sun kwanta,Rauda na tsaye a kitchen tana tsiyaya ruwan zafi a kofi dan sai lokacin taji tana jin yunwa


Bayan ta gama haɗa tea ta fito zata koma ɗaki


Dai-dai lokacin shi kuma umar ya shigo be kula da ita ba dan babu haske sosai a ɗakin suka ci karo


Kofin hannun ta ya faɗi ƙasa tean ya zube,ɗan ja baya tayi da sauri gudun kar ya fallatsan mata a ƙafa


Ido umar ya zuba mata,yana so ya tuna a inda ya Santa


Duk da babu wadataccen haske falon ne hana ta ganin kyakkyawar fuskar sa kasancewar sa fari sosai


Hannu ya kai ya kunna glop ɗin falon, still idanuwansa na kanta


Ji tayi kamar kar ta ɗauke nata idanun dan gani tayi yayi mata wani irin kyau


Jin hawaye na neman cika mata ido ya sa tayi saurin sadda kanta ƙasa


A hankali ya fara taka wa zuwa inda take sai da ya rage be fi taku ɗaya tsakanin su ba sannan ya tsaya


Ɗago kanta tayi, karaf idanuwan su suka sarƙe da juna


Yarrr yaji wani abu ya tsarga a jikin sa,yayi saurin lumshe idanuwan sa zuciyar sa ta fara bugawa a hankali 


Ganin haka yasa tayi saurin hayewa sama, buɗe idanuwansa yayi yana bin bayan ta da kallo 


Har ta shige sannan ya sauke idanuwan sa tare da zama kan kujera 


Wacece ita?Meyasa yaji zuciyar sa na bugawa a sanda ya kalli cikin idanuwan ta? 


Ya jero ma kansa tambayoyin da ya bayi da amsar su 


Miƙewa yayi jikin sa babu ƙwari, wani ɗaki anty kaltum take? Dole yaje ya tambaye ta 


Sama ya hau ya buɗe ɗakin farko,hajiya ya gani kwance tana ta munshari


Ya maida mata ƙofar ya rufe a hankali sannan ya wuto ze dawo ƙasa 


Shesshekar kuka ya fara ji a hankali a ɗakin da ke kusa da wanda hajiya take 


Murɗa ƙofar yayi a hankali tare da turawa 


Gefen gado ya hango ta ta kifa kanta tana kuka


Runtse ido yayi dan jin kukan nata yayi har cikin ƙoƙon ransa


Murɗa ƙofar da taji anyi ne yasa ta ɗago kanta 


Tayi ƙoƙarin mai da ragowar kukan tare da share fuskar ta da sauri 


A jiyar zuciya ya sauke 

"wani ɗaki anty kaltum take? 


" tana ɗakin ƙasa"


Ta bashi amsa,juyawa yayi ya maida mata ƙofar ya rufe


Sai da ya ƙwanƙwasa ƙofar sannan ta buɗe dan ta rufe 


Ganin sa yasa taɗan yi mamaki 


"umar baka kwanta ba? Ba dai jikin bane ba ko? 


Girgiza kai yayi yace 


" a'a lafiya ta ƙalau, inaso muyi magana ne"


Bashi hanya tayi ya shige sannan ta bi bayan sa, a gefen gado suka zauna 


"inajin ka" 


Sai da ya sauke numfashi sannan yace 

"anty wacece wannan dana gani? 


Ta san Rauda yike nufi kuma dama ta tanaji amsar da zata bashi dan ta san dole ze tambaya 


"ƴar'uwar baban Salim ce,ya ɗauko ta ta dawo wurina da zama"


"amma meyasa Naga tana kuka, akwai wani abu dake damun tane?




Manage plz banda caji


*~ƴarfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 4⃣0⃣



_wannan Page nakine fretu muna godiya da yabawa ma rubuta golden pen da kike yi muma muna yinki kuma muna tare dake irin sosai ɗinnan_



_10:19_🕒 AM

Thu, Nov 7



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Addu'a Yayin Da Aka ga Tumu,


اَللَّهُمَّ بَارِكْ لَنَا فِي ثَمَرِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي مَدِينَتِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي صَاعِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي مُدِّنَا.

Allahumma barik lana fee thamarina, wabarik lana fee madeenatina, wabarik lana fee sa'ina wabarik lana fee muddina.

Ya Allah! Ka albarka ce mu a cikin kayan gonarmu, ka albarkan ce mu a garinmu, Ka alabarkance mu a kwanon awonmu, Ka albarkan ce mu a mudun awonmu.




Washe gari

Tana tsaye saman bene ta tsakar gida,ta dafa jikin zagayayyen ƙarfen da yayi ma wurin gajeruwar katanga,wasu tsuntsaye biyu ta tsura ma ido da suke ta shawagi a jikin bishiyar gidan


Jikin ta ne ya bata ana kallon ta, ta sauko da kallon ta ƙasa 


Umar ta gani tsaye ya harɗe hannayen sa a ƙirji ya zuba mata dara-daran idanuwansa 


Tsawon minti biyu suna kallon juna daga bisani ta janye nata idanun ta maida su gurin bishiyar 


Numfashi umar ya ajiye sannan ya fara taka matakalar a hankali, duk da tana jin sawun hawowar sa besa ta kuma juyawa ba 


Har sai da ya ƙarasa hawowar, kamar yadda tayi shima haka yayi dafa ƙarfen yayi da hannayen sa duka biyu 


"barka da yammaci" 


Umar ya faɗa yana ƙoƙarin saisaita idanuwansa a kanta


"yauwa barka" 


Ta amsa mai a taƙaice


Yayi ɗan shuru yana tunanin abunda ze ce mata,ita ko gaban tane ya fara faɗuwa dan gani take kamar yana gab da dawowa cikin tunanin sa


"anty ta cemin gobe zaki koma garin ku ko?


Ya tambaya


Ɗaga masa kai kawai tayi alamar eh batare da tayi magana ba


Ya sauke guntun numfashi tare da faɗin


"shin bakya jin daɗin zama damu ne?


Shuru bata amsa mai ba,ya lumshe idanuwansa na ƴan sakwanni sannan ya sake buɗesu ya kuma ɗaura su akan ta


"bansan me yasa nike jin zuciya ta na bugawa ba a duk sanda na ganki,dan Allah kada kiyi nisa dani"


Yana yin yadda ya ƙarasa maganar ya sa jikinta ya ƙara yin sanyi 


Tabbas ƙaunar da yike mata ba kaɗan bace,tunda har yanzu ya kasa dena jinta a cikin ransa duk da tuggun da Aasim yayi a tsakanin su 


Take idanuwanta suka ciko da hawaye,matso wa yayi gab da ita yana ci gaba da cewa 


"ki ci gaba da zama a nan please" 


Sai lokacin ta ɗago ta zuba mai idanuwanta wanda suke cike taf da hawaye 


A hankali hawayen suka fara gangarowa daga kurmin idanun ta 


Juyawa tayi tabar wurin da sauri dan bazata iya jurar tsayawa a wurin ba


Ɗakin ta ta faɗa tana fashewa da kuka me ciwo,ya zamar mata dole tayi gaggawar barin gidan dan inbahaka ba ta san al'amarin yana gab da kuma jagulewa


Kayan ta ta fara haɗawa a akwati,tana haɗawa tana kuka 


A haka anty kaltum ta shigo ta same ta, gabaɗaya tausayin ta ya gama cika zuciyar anty kaltum 


Nasiha tayi mata sosai da kuma cewa ta kwantar da hankalin ta dan sauran kwanaki tafiyar ta Sudan 


Cikin dare,Rauda ta kasa runtsawa ko kaɗan,tana zaune kan darduma bayan ta idar da nafiloli 


Hakanan taji tana son taga umar,har ta miƙe wani sashi na zuciyar ta ya haneta 


"yanzu idan kika tafi kinsan ranar da zaki ƙara ganin sa? 


Wata zuciyar ta tambaye ta,jikinta ba kuzari ta kalli agogon ɗakin 


Ƙarfe biyu na dare, tasan yanzu yayi barci hakan yasa ta fito daga ɗakin ta, ta murɗa ƙofar bedroom ɗinsa a hankali 


Kwance ta hango sa yana bacci,ta maida ƙofar ta rufe sannan ta taka a hankali zuwa bakin gadon


Durƙusawa tayi sai tin fuskar sa ta tsura mai ido


Tunda take a duniya bata taɓa ganin me kyan umar ba, yana da wani irin sihirtaccen kyau me cike da haiba


"karki tafi please ki zauna tare dani"

Ya faɗa cikin barci da alamu mafarki yike yi


Ɗan murmushi tayi me cike da damuwa tare da kama hannun sa a hankali cikin murya ƙasa-ƙasa tace


"zantafi ne ba dan inaso ba jaana,zan barka a zahiri amma kasani zuciya ta na gare ka gangar jikina ce kaɗai zata yi nisa da kai..


Ta numfasa tana kai bakin ta dai-dai goshin sa ta sumbata


Hawaye ne masu ɗumi suka fara gangaro mata


Tayi saurin kauda fuskar ta daga tasa tare da miƙewa tabar ɗakin 


Asubar fari tayi wa su anty da hajiya sallama dan bata so umar ya dawo masallaci ya same ta


Dama driver na jiran ta, ta shiga motar tana hawaye


Basu ɓata lokaci ba driver yaja suka wuce


Suna tafe tana tunanin yadda rayuwar ta zata cigaba da kasancewa


A haka bacci ɓarawo ya sace ta tunda dama bata runtsa ba ko kaɗan


Sanda ta farka mamaki ne ya kamata ganin ita da tasan tana cikin mota suna tafiya amma ta ganta kwance kan wani ƙayataccen gado


Yunƙurawa tayi ta zauna tana ƙare ma ɗakin kallo, babu shakka gidan Aasim ne


Ta dafa kanta cikin damuwa,dan tasan su mama zasu shiga tashin hankali tunda sun san ta taho


A haka Aasim ya shigo fuskar sa ɗauke da walwala da nishaɗi


"habibty sannu kin farka"


Bata bashi amsa ba illa zuba mai ido da tayi,ya ƙara so ya zauna yana sakar mata lallausan murmushi


Kallon sa ta cigaba da tayi, cikin tsananin damuwa tace


"Meyasa kake yimin haka ne, duk abunda kace inyi nayi me yasa ba zaka barni in samu natsuwa ba tukun?


Aasim ya sauke ajiyar zuciya yace


"duk natsuwar da kika samu ta kusan shekara bata isheki ba, wata kuma kike buƙata?


Kinga habibty a yanzu bazan iya jurar rashin ki ko da na misƙala zarratun ba,bazan kuma yarda nayi sakacin da nayi a baya ba"


Guntun numfashi ta sauke me cike da takaici


"me kake nufi kenan,ka rabani da mijina iyayena suma rabani da su zaka yi?


Ya ɗan kauda kansa da ga kallon ta garin irin kallon da take masa


" bance Hakan ba"


Ta sauke gauron numfashi tana saukowa daga gadon ta durƙusa a gaban sa


"dan girman Allah ka mai dani nasan mama tana can hankalin ta ya tashi in ya so daga baya duk yadda kake so sai inmaka"


Ta ƙarasa faɗa idanuwanta na ci kowa da hawaye


Numfashi ya sauke tare da ɗago kyakkyawar fuskarta


"habibty ki kwantar da hankalin ki,ki kalli can"


Yayi mata nuni da madubin sa,mama ta gani dasu anty ummi,tsakiyar su kuma wata Rauda ce tunda dai ita gata anan


Mamaki sosai ya bayyana a fuskar ta,ta mai kallon rashin fahimta tare da cewa


"waccan kuma wacece?


" wata rauhaniya ce nasa tayi shigar ki, zata ci gaba da zama tare dasu mama a madadin ki har zuwa wani  lokaci dan gaskiya bazan yadda in kuma rasa ki ba"


Kallon sa kawai ta cigaba da tayi, ya sauko shima ƙasan yana janyo ta jikin sa


"habibty nayi rashi da kewar ki sosai, dan Allah ki rayu dani ni kaɗai"


Janye jikin ta tayi tana ɗaga mai hannu


"ina buƙatar natsuwa kabarni da Allah"


Ajiyar zuciya ya sauke tare da miƙewa  ya fice daga ɗakin


Ita ko jingina tayi da gadon wasu siraran hawaye na biyo kuncin ta


Be kuma dawowa ɗakin ba falo ya koma ya kwanta kan kujera


Iyaka dai ya tura mata tire shaƙe da abinci,bata kula abincin ba sai bayan wasu awanni da taji cikin ta na neman agaji sannan ta tsakuri kaɗan


Sai dare ya dawo ɗakin, Rauda na tsaye jikin window ta zuba ma dogayen bishiyoyin dake dokar dajin ido


A bayan ta ya tsaya,bata wai ga ta kallesa ba,hannu yasa ya fara zage zip ɗin rigar ta ta baya


Tayi saurin waigowa a ɗan tsorace,murmushin nan nasa ƙasaitacce yayi yasa hannu ya saƙalo ta taba ya tare da manna ta da jikin sa


"miye ne na wannan tsoron, bafa wani abu zan miki ba wanka ne"


Ta riƙe zip ɗin tana girgiza mai kai


"ka bari zanyi da kaina"


Ya matso da fuskar ta gab da tata dan karan hancin su ma yana gogan juna


"da raina da lafiya ta inbar matata tayi wanka da kanta?ki sani a yanzu zan nuna miki tsantsar soyayyar da tafi tada ta yadda zaki yadda cewa zan iya yin abunda ze ninka wanda ɗan adam ze miki"


Zata kuma magana ya ɗaura yatsun sa biyu kan ƙaramin bakin ta


"shhhhhh kar ki ce komai"


Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana kallon idanuwansa wanda kalar ƙwayar ciki take caccanzawa


Ya ci gaba da zage zip ɗin har ya kai ƙarshe sannan ya zame rigar


Runtse idanuwanta tayi da sauri, yayin da ya cigaba da kallon ta yana tambayar kansa


"ta yaya ze yadda ya rasa Rauda, ina!!!!


Bata ankara ba taji ya ɗauke ta cak,sai da ya tsundu mata a ruwa sannan ta buɗe idanun ta


Ruwane me ɗumi wanda saman sa yike mamaye da pink ɗin fulawowi


"kabarni nace zan yi da kaina"


Bece mata komai ba yaci gaba da abunda yike yi, da kansa yayi mata wankan ya naɗo ta da tawul sannan ya zaunar da ita a gaban madubi


Yana sunkuyo da kansa dai-dai wuyan ta


Ta cikin madubin suke kallon juna,gaba ɗaya idanuwansa sun narke da tsananin ƙaunar ta


"Rauda wallahi ina sonki"


Ya faɗa cikin wata murya me cike da shauƙin ta


Wani mai ya ɗauko ya shafe ta da shi sannan ya shafa gefen gadon sai ga wata rigar bacci me kyau ta bayyana sai da ya zura mata rigar sannan ya zame tawul ɗin


Ya kama hannun ta ya miƙar da ita tare da rungume ta sosai a jikin sa


Tabbas yayi kewar farin cikin rayuwar sa


Itako gabaɗaya jikin ta ya mutu,lumshe idanuwanta tayi kawai


Sai da suka kwashi minti biyar a haka sannan ya ɗago ta,ya na sunyo da fuskar sa zuwa bakin ta


Ta gane abunda yike shirin yi a kasalance tace


"hakan ba daidai bane kasan..........


Yayi saurin haɗa bakin su guri ɗaya dan baya so ta ƙarasa abunda zata faɗa


Minti uku baya ta janye jikin ta da ƙyar tana sa mai kuka


Bakin gadon ya zauna yana zuba mata ido cike da yanayi na galabai ta


Be lallasheta ba sai da tayi kukan ta me isar ta sannan ya kamo hannun ta ya zaunar da ita kusa dashi yana fuskantar ta


"habibty tunda bakya so bazan yi miki komai ba, ki dena kuka kinji?


Ya ƙarasa faɗa yana share mata hawayen fuskarta


" kwanta kiyi barci bazan yi miki abunda ranki ba ya so ba"


Kwantawar ko tayi,tana ɗan rawar sanyi wani lallausan bargo me taushi yasa ya lulluɓe ta




*~ƴarfillo~*.



*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



*Addu'a Idan Mutum Ya yi fushi.*



أَعُوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ.    


*A'oothu billahi minash-shaytanir-rajeem.*


*Ina neman tsarin Allah daga shaidan tsinanne.*




Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 4⃣1⃣



*_wannan Page ɗin nakine JAMILA ALIYU dake sa group ɗin ku masu ƙaunar jinnul aashique ina yin ku irin sosai ɗinnan_*



_7:45_🕒 AM

Wed, Nov 13



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Bayan sati ɗaya

Umar ya jigata ƙwarai tun bayan tafiyar ta yike jin kamar ya rasa wani sashi na jikin sa ya rasa meke faruwa da ake ɓoye masa


Dan yanzu ma anty kaltum ta tilasta masa komawa gidan ta wai har sai ya ƙarasa samun lafiya


Ya rasa gane abunda ke faruwa kuma wanda ya tambaya baya samun gamsasshiyar amsa


Yana zaune cikin mota gaban wani shagon turaruka yana jiran mutanen da suka cika shagon su ɗan ragu sannan ya shiga


Gabaɗaya ya shiga cikin rikitaccen tunani dan ranar da ta shiga ɗakin sa idanuwansa biyu ba barci yike yi ba


"zantafi ne ba dan inaso ba jaana,zan barka a zahiri amma kasani zuciya ta na gare ka gangar jikina ce kaɗai zata yi nisa da kai..


Ya rasa gane abunda take nufi a cikin maganar ta,ya dafa kansa da yike jin yana ɗan sa rawa kaɗan 


Da ƙyar ya iya fitowa ya shiga shagon yana tsaye yana duba turaren da yike son siya yaji ance 


"Doctor umar dama talaka na ganin ku? 


Umar ya juya inda yaji maganar yana kallon mutumin,tsayin sakwan uku yana so ya tuna a inda ya san mutumin 


Be kai ga gama tunani ba mutumin ya ƙara so yana miƙamai hannu 


Bayan sunyi musabaha mutumin yace 


"doctor mutanen Allah,ya gida ya iyali? Ko ince amarya kayi haƙuri sanda aka yi auren ka bana ƙasar kuma naso na kira ka nayi maka Allah ya sanya alkhairi ashe numban ka na cikin Layina da ya ɓata" 


Umar yayi sororo ya na kallon sa dan Sam be fahimci abunda mutumin ke faɗa ba


"nasan yanzu ƙila amarya ta haihu ko? Samin numban ka dan Allah zanzo har gida na ga amarya" 


Mutumin ya ƙarasa faɗa yana miƙa mai faskekiyar wayar sa 


Sa mai numban kawai yayi batare da ya ƙarasa sa numban ba ya fice daga shagon motar sa ya faɗa ya kifa kan sa akan sitiyari 


"to yaushe yayi aure be sani ba? Kuma wacece wacce ya aura? 


Yayi ma kansa tambayoyin a jere,


"zantafi ne ba dan inaso ba jaana,zan barka a zahiri amma kasani zuciya ta na gare ka gangar jikina ce kaɗai zata yi nisa da kai..


Maganar ta ta kuma yi masa yawo a kunne,tabbas idan ya kasance yayi aure to itace matar sa


Ya girgiza kai cikin dagulewar tunani, dole ne ya san abunda ake ɓoye sa


Tada motar yayi ya nufi gidan sa kai tsaye


A tsakar gida yayi parking ya zaro makullin gidan ya buɗe falon


Ya daɗe tsaye yana kallon cikin falon kamar yau ne karo na farko da ya fara ganin sa


Daga bisani ya shiga ya zauna akan kujera


Nan ma ya daɗe ƙwaƙwalwarsa naso ta tuno masa wani abu amma sai yaji kan sa ya cushe


Bedroom ɗin sa ya shiga ya zauna gefen gado idanuwansa suka sauka kan laptop ɗin sa


Jikin sa ba ƙwari ya miƙe ya ɗauko laptop ɗin dan ya san baze rasa wani abu da ze taimaka masa wajen gano abun da yike so ya gano ba


A can Kaduna kuwa gidan su mama mamaki da ban al'ajabi ne yike ta kama su


Dan tun bayan zuwan Rauda ta bogi suke shiga jimami, dan da farko kishiyoyin mama habaici da gori suka fara yima mama da faɗan maganganu masu ciwo


Farha wacce itace Aasim ya turo a madadin Rauda rauhaniya ce Mara haƙuri hakan yasa duk ranar da wani yayi ma mama habaici ko ita ɗin kanta to idan dare fa yayi mutum ya dinga tsala ihu kenan


Dan abubuwan tsoro take tura masa,tun basu Fahim ta ba har suka fara fahimta


Hakan yasa suka shiga ɗari-ɗari da ita,ga aiki dan idan ta soma aiki Sam bata gajiya


Abun yayi ta bawa mamaki sanin Rauda da tayi sam bata son aiki, aiki kaɗan zata yi tace ta gaji amma yanzu har so take ma ace ga aiki


Mama tasha jinin jikin ta sosai dan taga canje-canje da yawa wanda yasa ta fara zargin anya ba canza mata ƴar ta aka yi ba?


Amma dai tayi shuru tana cigaba da zubawa sarautar Allah ido


Ɓangaren Rauda kuwa a yanzu duk wani tsoro ya fita daga ranta dan zuciyar ta ta ƙeƙeshe wuni take da kwana tunanin umar


Wani zubin idan Aasim ya fita ta kan je wurin madubin sa ta ambaci sunan umar tayi ta kallon sa


Yana yin data ga yana shiga na damuwa da kuma tunani shine abun da ya ƙara sanya ta cikin damuwa


Ta rasa inda zata sa kanta,kamar kullum tana tsaye jikin bishiyar gidan tana kallon da jin


Taga Aasim ya bayyana a gaban ta dan tun safe ya fita


Kallon sa tayi yana yi mata murmushi


"habibty"


Duƙar da kanta tayi ƙasa batare da ta amsa ba


Ya matso gab da ita yace


"baza kimin sannu da zuwa ba ko?


Nan ma bata amsa ba


Ya sauke ajiyar zuciya yana fito da kayayyakin da ya siyo mata


Manyan sarƙoƙin lu'u-lu'u ne da awarwaron su


Dan a yanzu duk abunda ze sa ta farin ciki ƙoƙari yike yi yayi mata


" kinga habibty nasan zasu yi miki kyau shine na siyo miki duba kigani"


Kallo ɗaya tayi musu ta ɗauke kanta, gaba ɗaya sai yaji yadda tayi masa babu daɗi


Zama yayi a ƙasan bishiyar yana jin wani iri


Sun jima a haka daga bisani ya juyo yana kallon ta


Zaunar da ita yayi tare da kama hannayen ta cikin damuwa yace


"na rasa yadda zan yi miki Rauda,dan Allah ki faɗamin me kike so sam bana son ganin ki a irin wannan yanayin"


Hawayen da suka maƙale a idanuwanta suka gangaro a hankali


"ya Salaam,kinsani na tsani Naga kukan ki ko?


Cikin muryar ta da tayi san yi tace


"to ya kake so inyi Aasim?duk wani roƙo da ya dace in maka nayi amma ka kasa tausaya min,babu yadda zanyi zan cigaba da rayuwa da kai kamar yadda kake so amma kasani bazan taɓa ci gaba da farin ciki ba"


Ya lumshe idanuwansa da suka canza launi


Ya daɗe a haka yana tunani sannan ya buɗe su ya ɗaura su a kanta


Har lokacin kuka take yi mara sauti


"kin kasance komai na rayuwa ta,na kuma baki dukkanin amanar kaina ban taɓa tunanin zaki juya min baya ba Rauda sai gashi ni kike gudu ni kike kuka dan ina tare da ke"


Ya ɗan dakata yana jin wani dunƙulen baƙin ciki na taso masa


"tunda kin zaɓi rayuwa da umar a kaina zan barki ki cigaba da rayuwa da shi amma da sharaɗi guda ɗaya"


Tayi saurin kallon sa yayin da ya cigaba da cewa


"kamar yadda na sadaukar da rayuwa ta dan in rayu dake na tsalle ke tauran to shima ze tsallake"


Wani irin kallo ta ci gaba da yi masa dan tasan ba abu bane da ze taɓa yuwuwa ba,shi rauhani ma ya ya ƙare da ya tsallake bare mutum


"amma kasan dai hakan baze yuwu ba,taya ya yana ɗan adam ze tsallake tauran ya kuma rayu?


Aasim ya sauke numfashi yace


"bazan taɓa manta wahalar da na sha a lokacin dana tsallake ba,kuma na amince dan in rayu dake a yanzu kuma da kike son rabuwa dani to wannan shine abunda ze sa in haƙura da ke, nayi alƙawari idan har ya tsallake zan rabu dake har abada zan bar ku ku cigaba da rayuwar ku cikin kwanciyar hankali"


Zata yi magana ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu


"bana son na kuma jin komai daga wurin ki wannan shine alfarmar da zan iya yi miki,tun da kinzaɓi rabuwa dani" 



Umar yana zaune ya tsura ma hoton da ke cikin laptop ɗin ido hoton sa ne da ita sun saƙale juna suna murmushi 


A hankali ƙwaƙwalwar sa ta fara tariyo masa komai 


Ya dafa kansa da sauri jin yayi wani mugun sarawa kamar an buga mai guduma


Jikin sa ne ya fara rawa ya runtse idanuwansa cikin tashin hankali 


"kina ina Rauda?me yasa zaki yi nisa dani? 


Karaf abunda ya faɗa a kunnen Aasim, mamaki ne ya kama Aasim ganin yadda cikin ƙanƙanin lokaci umar ya dawo cikin tunanin sa 


Cikin hanzari ya ɓace daga wurin da yike ya bayyana a ɗakin da umar yike 


Kallon tsana suka ma juna lokaci ɗaya yayin da umar ya miƙe cikin dakewar zuciya yace 


"ina mata ta?ina ka kai min ita? 


Aasim yayi murmushin takaici yace 


"matar ka ko matata?kayi nasarar dawowa cikin tunanin ka amma kasani ba zaka taɓa nasara a kaina ba" 


"ban damu akan yin nasara ko rashin ta akan ka ba,damuwa ta akan matata ne ka gaya min tana ina dan nasan tana tare da kai" 


Aasim ya kuma yin murmushi yace 


"haka ne matata tana tare dani sai dai kash zuciyar ta na tare da kai,kasani ban taɓa tsanar wani ɗan adam kamar yadda na tsanake ba Kaine wanda ka ruguza min farin cikina,idan naso zan kuma mantar da kai ko kai waye zan iya zautar da ƙwaƙwalwar ka amma bazan yi hakan ba kasan me yasa? 


Ya ɗan dakata yana furzar da wata iska me zafi,sannan ya cigaba 


"saboda bana son na cigaba da ganin damuwa a fuskar farin cikina,nazo ne na baka zaɓi idan har kana son Rauda ka na kuma son ka ci gaba da rayuwa da ita to zaka tsallake tauran ni kuma nayi alƙawari idan har ka tsallake to zan bar maka ita har abada" 


Umar ya rausayar da kai yace 


"idan har tsallake tauran ɗin ze sa kabar min matata ka kuma nisan ce ta  na amince zan tsallake" 


Aasim yayi wani mugun murmushi yana jinjina kai 


"tsallake tauran ba abu bane me sauƙi, na baka kwana biyu kaje kayi tunani a kai" 


Kafin umar ya kuma yin magana tuni ya ɓace 




*~ƴarfillo~*.


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Addu'ar Kin shu'umci


اَللَّهُمَّ لاَ طَيْرَ إِلاَّ طَيْرُكَ، وَلاَ خَيْرَ إِلاَّ خَيْرُكَ، وَلاَ إِلَهَ غَيْرُكَ.

Allahumma la tayra illa tayruk, wala khayra illa khayruk, wala ilaha ghayruk.


Ya Allah! Babu shu'umci sai abin da Ka halitta, kuma babu alheri sai alherinka, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba Kai ba.



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 4⃣2⃣



_Wannan page nakune masoya na masu haƙuri dani Allah ya bar ƙauna😄_



_gaisuwa ga *Fatima batula* ina taya ki murnan kammala littafin ki wanda ya faɗakar damu sosai Allah ya baki lada ya ƙara basira da fasaha_



_8:26_🕒 PM

Thu, Nov 28



_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Bayan kwana biyu umar yana tsaye jikin window ya ji motsi a bayan sa


Ya waigo a hankali Aasim ya gani


"kwanaki biyun da na baka sun cika shin ka gama shawarar?


Aasim ya tambaya yana zuba masa razana nun idanun sa


Umar ya jinjina kai yace


"shawara tun a lokacin na yanke ta na amince"


Aasim yayi murmushi yana jinjina kai


"da kyau amma Naga baka nemi shawarar iyayen ka ba,kuma dole akan idon su zaka tsallake tauran"


Umar yayi murmushi da ya tsaya masa iya laɓe kawai


"wannan ba damuwar ka bace zan tsallake ko da amince warsu ko bada amince warsu ba tunda Naga kaima lokacin daka tsallake bada amincewar naka iyayen ba dan da kabi shawarar su da hakan duk be kasance ba"


Aasim ya kaɗa kai cikin yanayi na ɓacin rai


"shikenan kafaɗa ma shaƙiƙan ka nan da kwana uku zaka tsallake tauran


Ka kuma yi sallama da duk wanda ya kamata dan walau ka rayu walau a kasin haka na barka lafiya"


Umar ya zauna shuru bayan ɓacewar Aasim gabaɗaya tunanin sa ya tsaya sai dai baya jin ze fasa abunda yayi niyya dan ko da ya rasa ransa yasan Rauda zata gane cewa yana yi mata so na haƙiƙa


Miƙewa yayi ya nufi gidan anty kaltum


A falo ya tadda ta ita da hajiya


Bayan ya gaishe su ya zauna shuru


Anty kaltum ta dawo kujerar da yike ta zauna tana tambayar sa


"ya dai umar na ganka wani iri ko jikin ne?


Ya girgiza mata kai a hankali


" to menene? Banason ina ganin ka a haka kasan bana son ganin ka cikin damuwa ko?


Ya kalle ta da idanuwansa da suka canza launi yace


"anty jarabawar da Allah ya ɗauro min kenan dole kiganni a haka, anty na dawo cikin tunani na meyasa kika ba Rauda goyon baya ta aikata min haka Meyasa?


Kefa ƴar uwata ce kuma auran ta da rayuwa da ita shine farin cikina shin bakya son farin cikin ɗan uwan ki ne?


Jikin anty kaltum yayi sanyi hajiya ko zuba mai ido tayi kawai cike da al'ajabi


"Sam ba haka bane umar.......


Ya dakatar da ita ta hanyar cewa


"na fahimci komai ba sai kinyi min bayani ba, yanzu abu ɗaya nike so a gare ku ina so ku bani goyon baya koda kuwa zan rasa raina ne"


Kallon sa kawai suka cigaba da yi yayin da ya zayyane musu abunda Aasim yace game da tsallake tauran


Shuru suka yi dan sun rasa abun da zasu ce


Durƙusawa yayi gaban hajiya idanuwansa na zubar da hawaye


"hajiya dan Allah ki bani goyon baya Rauda ita ce farin cikina dan Allah hajiya"


Hajiya itama hawayen ta fara yi


"tabbas soyayyar ka a gareta daga Allah ce,akwai wata hikima da ubangiji ya ɓoye a tsakanin ku na baka goyon baya umar ubangiji Allah ya baka sa'a Insha Allah zaka tsallake lafiya kaci gaba da rayuwa da matar ka"


Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana hamdala a zuciyar sa dan beyi tunanin zasu amince mai ta sauƙi ba


Hannun ta ya kama yana ɗan murmushi


"nagode hajiya"


Rauda kuwa tana zaune ta Lula cikin tunani bata ma san Aasim ya dawo ɗakin ba sai da taji gyaran murya


A hankali ta zare tagumin da tayi tana kallon sa da lunshasshun idanun ta wanda suka yi luhu-luhu saboda kukan da taci


Kallon juna suka yi na ƴan sakwanni daga bisani ta ɗauke idanuwan ta a kansa ta maida su ƙasa


Shi ko kallon ta yaci gaba da yi yana jin wani irin yana yi na daban


Ya sauke numfashi me nawi yana matso wa kusa da ita a hankali


_"Rauda"_


Ya kira sunan cikin yana yi na damuwa


Ta ɗago ta kuma kallon sa, gabaɗaya ya koma yana yin tausayi ya canza kamar ba shi ba


Kuma sauke idanun ta tayi dan ba zata iya jurar ci gaba da kallon sa ba


"shin ko da sau ɗaya ne ni ba zaki tausaya min ba?


Ya faɗa yana ruƙo hannun ta sannan ya cigaba da cewa


"Sam ni bakya tunanin halin da zan shiga a yayin da zan rabu dake?me yasa ki ka kasa yimin adalci ne?


Ki tuna abubuwan da na rasa a sanadin ki


A da bana komai sai abunda bayi da fadawa suka min,Sam bansan wani abu wahala ba a rayuwa babu gatan da bana samu


Amma a sanadin ki,ki duba wahalar da nasha Rauda na rasa muƙami na na yarima narasa soyayyar iyaye na duk dai akanki


Amma ke.......


Be ƙarasa ba ta faɗa jikin sa tana fashewa da wani kuka me tsuma zuciya


Dan gabaɗaya tausayin sa ya cika mata zuciya


Ya runtse idanuwansa dan yana jin kukan ta har cikin ƙoƙon ransa


Sun kwashi minti biyar a haka ya kasa lallashin ta dan jikin sa yayi sanyi ƙalau


Ɗago kanta tayi tana kallon sa cikin kuka take faɗin


"na sani banma adalci ba Aasim tabbas na cika me son zuciya amma yadda rayuwar mu tazo dole mu amshe ta a haka


Baze yuwu mu cigaba da rayuwa.......


Dakatar da ita yayi ta hanyar ɗaga mata hannu


Yana murmushin takaici


"ya isa haka Rauda,nasan dama bani da kalaman da zan sa ki fahimta babu damuwa har a bada ni me ƙaunar ki ne zan rabu dake a jibi idan har umar ya tsallake tauran kar ki damu"


Ya faɗa cike da takaici


Zata kuma magana ya miƙe ya bar mata ɗakin


Kifa kanta tayi kan gwiwar ta wani sabon kuka na ƙwace mata


Shin ya za tayi da ranta ne,anya idan ta rabu da Aasim tayi ma kanta adalci kuwa?


Rayuwar da suka yi da shi ce tayi ta dawo mata da irin yadda ya nuna mata tsantsar ƙauna


_"habibty nace ba ina sonki"_


Kalaman da yike faɗa kullum idan zasu yi sallama a makaranta


_"Rauda ina sonki zan iya haƙura da komai nawa in har zan rayu dake"_


Zuciyar ta ta cigaba da hasko mata fuskar sa yana murmushi cike da nishaɗi


"tabbas ban maka adalci ba ka cancanci na rayu da kai har a bada amma umar fa?


Ta tambaya a fili tana juya idanun ta cikin yanayi na fara fitar gayyaci


Duk wahalar ya sha ta gubar nan besa yaji ƙaunar ta ta ragu a ransa ba ta san inda wani ne da idan ana saki ɗari yayi mata dan ya samu lafiya


Amma shi ko kaɗan be nuna gajiyawar sa ba illa ma ƙarfafa mata gwiwa da kwantar mata da hankali


_"chuchu ina tsananin ƙaunar ki ba zan taɓa iya rabuwa dake ba,na amince na cigaba da rayuwa a haka in har zan ci gaba da kasancewa tare dake"_


"ya Allah"


Ta faɗa cikin tsananin tashin hankali dan jin kanta take yi kamar zeyi bindiga


Daren ranar bata yi barci ba kamar yadda Aasim da umar ma ko kaɗan basu runtsa ba



Washegari tana zaune bayan ta idar da sallah taga tiren abinci ya shigo shaƙe da kayan kari


Shafa cikin ta tayi da ya laƙume dan rabon da taci abinci har ta manta


Bata bi ta kan abincin ba ta miƙe ta fito


A tsaye tagan sa yana shirin fita


Tayi sauran tarar sa tana faɗin


"ina son Magana da kai"


Be kalle ta ba ya ci gaba da abunda yike yi


"faɗi inaji"


Ya faɗa a taƙaice


Tayi shuru tana tunanin yadda zata mai maganar


Ɗagowa yayi ya kalle ta


"ke nike saurare"


Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce


"dan Allah kabani dama ina so inyi magana da umar"


Ya ɗan yi shuru yana cigaba da kallon ta kamar ba ze sake yin magana ba sai kuma yace


"shikenan na baki minti goma"


Yana gama faɗar haka ya ɓace


Zura ma wurin da ya ɓace ido tayi tana tunanin to ina zata fita daga dajin


Bata kai ga gama tunanin ba ta ganta a bedroom ɗin umar


Babu kowa a ciki sai iskar fanka dake ta kaɗawa


Numfashi ta sauke tana faɗin


Ƙiri-ƙiri a maida mutum aljanin ƙarfi da yaji


Umar ya turo ƙofar dan dawowar sa daga masallaci kenan


Da kyakkyawar fuskar ta yayi karo


Ƙarasa shiga ɗakin yayi da sauri


Ya nufe ta da nufin rungume ta sai kuma ya fasa dan be san wani abun Aasim yace ta kuma yi ba


Ɗan murmushi tayi dan ta fahimce sa


"Jaana guduna kake yi ne?


Ajiyar zuciya ya sauke tare da ƙarasa wa gaban ta


Ya kasa magana illa tsura mata ido da yayi


Gabaɗaya gani yayi ta rame masa


Wani irin tausayi da son ta ne ya kuma dabaibaye sa


Besan sanda ya rungume ta sosai a ƙirjin sa ba


Wasu siraran hawaye ne suka biyo kuncin ta wanda bata san na menene ba


Na kewarsa ne ko kuma na ƙaunar sa


Sun kwashi minti uku a haka tunawa da minti goma Aasim ya bata yasa tayi saurin janye jikin ta


Tana faɗin


"minti goma kaɗai ya bani zauna muyi magana"


Ta ƙarasa faɗa tana jan hannun sa zuwa gefen gadon


Bayan sun zauna tace


"Jaana dan Allah ka janye maganar tsallake tauran da ba abune da zaka iya ba, mu ci gaba da addu'a kawai.......


Girgiza kai yayi yace


"Rauda kisa aranki kamar na tsallake ne dan bazan fasa ba"


Cikin damuwa take kallon sa


"shi kanshi rauhani fa jikin sa huhhujewa yayi ina ga kai mutum? Idan har ba so kakeyi in rasa ka ba dan Allah ka fasa"


Ta ƙarasa faɗa idanuwan ta na ci kowa


Yayi ɗan murmushi ya na dafa kafaɗun ta


"yace idan har na tsallake ze rabu dake ze barki kiyi rayuwa cikin kwanciyar hankali dan haka koda na mutu bani da faɗuwa tunda zaki cigaba da rayuwa babu takurawar sa"


Ta kasa ƙara magana


Umar ya cigaba da cewa


"ki kwantar da hankalin ki chuchu abu ɗaya nike so dake idan Allah ya sa na rasa rayuwa ta kada kisa ranki a ƙunci kiyi rayuwa cikin farin ciki....


Toshe mai baki tayi da sauri tare da faɗawa jikin sa


" umar dan Allah ka janye  na tabbata idan babu kai nima bazan iya ci gaba da rayuwa ba"


Ya kuma yin murmushi wanda yike tattare da ɗumbin damuwa


"chuchu a baya kin taɓa kuka a sanadina kin faɗi cewa ke kaɗai ke sona ni bana sonki


Nasan idan har na tsallake zaki yarda da cewa son da nike miki ya ninka wanda kike min"


Tayi saurin girgiza kai


"nasan kana sona umar dan Allah..........


Bata ƙarasa ba tagan ta akan kujerar falon Aasim


Kuka ta cigaba da yi dan tabbatar da baze shiga tauran ya fito da ran sa ba


Shiko umar zuba tagumi yayi,bayan ɓacewar ta


Ɓangaren Aasim kuwa can wurin tauran ya je


Mus'ab ya tarar a wurin hannun sa riƙe da wani haske me tartsatsi yana ta nuni ga tauran


Ya yin idan tartsatsin ya dake cikin ta take ƙara fitar da wani hayaƙi me zafin gaske


Aasim yayi saurin dakatar dashi


"Mus'ab me kake yi haka? Ƙarama tauran zafi fa kake yi"


Mus'ab ya jinjina kai


"eh mana yarima saboda ina so wannan bil'adaman ya gane yayi babban kuskure


Aasim ya girgiza kai yace


"shifa mutum ne taya kake tunani idan ya shiga ze kasance?


Mus'ab yayi ma Aasim wani irin kallo


" wai kai har ma tausayin sa kake ji?


Aasim yayi ɗan murmushi tare da zaunawa a kan kujera yana kallon yadda hucin tauran ke fita


Mus'ab ya kuma faɗin


"tambayar ka nike yi Aasim, mutumin da ya jagula ma rayuwar ka shine kake tausayi?


Aini wallahi so nike ko ɓurɓushin naman sa kar a gani"


Aasim ya kuma yin murmushi a karo na biyu sannan ya maida kallon sa ga babban abokin nasa


"Mus'ab ka sanyaya ranka kaji? Nasan kafini jin zafi amma inaso ka dawo da natsuwar ka mubi komai a hankali"


Mus'ab ya furzar da wata iska me zafi yace


"ni banga abun bi a hankali ba anan"


Wani irin ƙamshi me daɗi ne ya zagaye wurin


Aasim ya ɗago kansa da sauri dan yasan mahaifin sa ne kaɗai ke amfani da kalar turaren


Ga mamakin sa kuwa sarki ramzad ya gani cikin shigar sa ta ƙasaita


Mus'ab yayi saurin rusunawa cikin girmamawa yayin da Aasim ya cigaba da kallon mahaifin sa cike da tsananin kewar sa dan ya manta rabon da yayi tozali da shi


Sarki ramzad ya ƙara so wurin fuskar sa ɗauke da guntun murmushi


 Mus'ab yayi gaggawar barin wurin ya rage daga Aasim sai me martaba


"Kaga yadda halin bil'adama yike koh? Aasim naji daɗi ƙwarai da suka koya maka hankali


Na zo ne na kuma baka zaɓi idan gobe bil'adaman nan ya tsallake tauran to fa kasani ba ka isa ka karya alƙawarin da kayi na rabuwa da matar sa ba, dan haka ka ka kiyaye"


Yana kaiwa nan ya bar wurin


Aasim shuru yayi zuciyar sa na yi masa wani iri kallon tauran ya kuma yi sai kuma yaɗan yi murmushi dan yana da yaƙinin sai dai gawar umar ta fita badai da ransa ba




*~ƴarfillo~*


*🌹JINNUL*

           *AASHIQUE🌹*

                      🧞‍♂🧞‍♂

                         🧞‍♂


                          NA

HARIRA ALIYU _(ƴarfillo)_🧕🏻


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*





*~We are bearer's of so golden pen🖊~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*


*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



Dedicated to _little hajjo_ and my elder sister _hafsat aliyu_


🅿AGE📕 4⃣3⃣




Wannan page nakine nabiha kiyi yadda kike so dashi.




*Addu'ar Da Mutum Zai Fada Idan Wani Al'amari Ya zo Masa na Farin Ciki ko na Bakin Ciki*


الْحَمْدُ للهِ الَّذِي بِنِعْمَتِهِ تَتِمُّ الصَّالِحَاتِ .

Alhamdu lillahil-lazee bini’imatihi tatimmus-salihat.


Godiya ta tabbata ga Allah wanda saboda ni'imarsa ce kyawawan ayyuka suke cika.

اَلْحَمْدُ ِللهِ عَلَى كُلِّ حَالٍ.

Alhamdu lillahi ala kulli halin


Godiya ta tabbata ga Allah a cikin kowane hali.





_2:02_🕒 PM

Mon,Dec 16


_Bissmillahir rahmanin rahim_✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻



Kiran sallar assalatu yayi dai-dai da bugawar ƙirjin ta.


Tashi tayi da sauri ƙirjin ta na ci gaba da bugawa.


"yau ne, umar bazai iya ba".


Abunda zuciyar ta ta tunatar da ita kenan.


Tashi tayi ta fito falo bata ga Aasim ba. ta duba ɗakin sa nan ma baya nan.


Zamewa tayi ta zauna a ƙasa tana dafa kanta cikin tsantsar damuwa.


Ta lumshe idanuwan ta, zuciyar ta na hasko mata tauran.


Tabbas ta san yau zata rasa Umar, rashi na har abada.


Wasu siraran hawaye masu zafi suka biyo kwarmin idanun ta.


"kin manta da cewa Allah ya na nan kuma shi ke maganin komai? Addu'a tafi ƙarfin komai".


Wani sashe na zuciyar ta ya tunatar da ita.


Miƙewa tayi da sauri ta ɗauro alwala, bayan ta idar da sallah ta ɗaga hannayen ta sama.


Cikin kuka take faɗin;


"Ya Allah, Kaine sarkin da ka halicci sarakuna, kai ke da iko a kan dukkan halittun ka, ya ubangiji ka duba lamarinmu ka taimaki Umar ka kare sa daga sharrin tauran da sharrin duk wani halitta, ka taimake sa ya ubangiji"


Ta ƙarasa faɗa, zuciyar ta na ƙara raunane wa.


Aasim yana tsaye yana kallon ta, jin jikin sa yike yi wani iri.


Ƙarfe sha ɗaya dai-dai manyan rauhanai abokanan Aasim suka hallara a wajen tauran.


Anty kaltum, hajiya, da kuma zayyad, suma suna zaune a falo suka ga wata iska ta zagaye su kan kace kwabo suka gansu a wata kalar duniya.


Sun tsorata sosai ganin yadda tauran ke fitar da wani tartsatsi.


Addu'a kawai suke karantawa dan sun rikice.


Can kaduna ma, mama ce zaune da anty Ummi suna tattauna wa ƙasa-ƙasa akan Rauda ta bogi, dan gaba ɗaya basu yarda da ita ba.


Suna cikin tattauna war Farha ta fito ta zauna tana kallon su.


Da ɗan murmushi a fuskar ta tace;


"kuna yin tantama a kaina koh?".


Basu bata amsa ba illa kallon ta da suka ci gaba da yi.


Ta kuma yin murmushi tana ci gaba da cewa;


"To a yau tantamar ku zata ƙare insha'allah, kamar yadda kuke zargi hakane ni ba Rauda bace".


Ta ƙarasa faɗa tana shafa fuskar ta sai ga fuskar Rauda ta ɓace, ainihin fuskar ta ta bayyana.


Anty damƙe hannun mama tayi cike da tsananin tsorata.


Mama ko bata yi mamaki ba dan dama tayi tunanin hakan.


"ina ƴata ina kuka kaimin ita?!".


Mama ta tambaya, zuciyar ta a dake.


Farha tayi murmushi tace;


" ƴarki tana duniyar aljanu a yanzu haka, ana can ana shirye-shirye dan yau ne mijin ta yace zai tsallake tauran, dan haka kuma yanzu zan tafi daku dan dole ayi komai a kan idon ku".


Basu kai ga yin magana ba suka gansu a wani kalan wuri.


Babu inda baya rawa a jikin anty ummi dan har fitsari sai da tayi.


Banda mama da zuciyar ta take a dake.


Kallon kallo suka wa juna da su anty Kaltum amma babu wanda ya iya ma wani magana a cikin su.


Umar da tun cikin dare yake kan darduma har lokacin yana kai.


Ya ɗaga hannaye sa yana ta kai kukan sa ga ubangiji.


Motsin Aasim da yaji a ɗakin yasa ya shafa addu'ar tare da waigowa a hankali.


Yana tsaye ya harɗa hannuwan sa a ƙirji.


Ɗan murmushi Umar ya sakar masa tare da cewa, cikin dakiyar zuciya;


"muna iya tafiya yanzu koh?",


Aasim gyaɗa masa kai kawai yayi ba tare da yace komai ba.


Cikin sakwanni suka isa, tabbas hankalin Umar ya tashi da yaga yadda tauran take.


Amma tunawa da yayi Allah yana tare da shi yasa yaji tashin hankalin ya ɗan ragu.


Anty kaltum na ganin umar ta ƙara so gurin sa da sauri ta riƙe sa


Cikin tashin hankali da tsananin tsorata tace


"umar dan girman Allah ka haƙura da yarin yar nan kadu ba inda zaka shiga fa"


Umar ya sake kallon tauran sannan ya mai da kallon sa ga anty kaltum


Cikin ƙoƙarin kwantar mata da hankali yace


"Anty na riƙe Allah na kuma san insha'allah ze bani nasara ki ci gaba da yi min addu'a kinji?


Kuka kawai ta fashe zata kuma magana Rauda ta riga ta dan isowar ta wurin kenan


Ita ma a gigice take gabaɗaya ta daburce


"umar ka kalli inda kake son shiga fa? Na roƙe ka ka janye


Umar ya dafa kafaɗun ta yana yi mata guntun murmushi


"Rauda ba zan taɓa janye wa ba koda ko hakan ze yi sanadiyyar rasa raina ne, bare ma insha'allah zan tsallake lafiya ki kwantar da hankalin ki kinji?


Ganin bayi da niyyar fahimtar ta yasa ta juya gurin Aasim cikin tashin hankali take yi masa magiya


"Aasim ka ɗaukeni mu tafi can wata duniya inda ma baza a ƙara ganina ba na amince zan ci gaba da rayuwa da kai amma kar ka barsa ya shiga tauran dan Allah ka taimake ni idan na rasa sa bansan ya zanyi da rayuwa ta ba"



Aasim da fuskar sa ba annuri idanuwan nan nasa sunyi jawur ba wata alamar ƙwaya aciki dan dama duk sanda ransa ya ɓaci haka idanuwansa ke komawa


Zuba mata idanun yayi masu firgita duk wanda aka kalla dasu


"ni ba rai bane kenen da na tsallake a baya? Tsallakewa ya zama dole tunda ya gani da idonsa kuma be janye da kansa ba idan har ya shiga ya tsallake ya fito kuma da ransa to da ga yau na barki har a bada!!!


Ya ƙarasa faɗa cikin ƙaraji


Mus'ab dake tsaye yace yana duba umar


Yayin da tauran tayi wani baƙin hayaƙi a Samanta cikin ta kuma wasu siraran wuƙaƙe ne masu kafin gaske wanda iska take ta kaɗa su da ƙarfin gaske ta yadda duk wani abu da ya shiga ciki zasu yayyanke jikin sa



"tauran tana yi maka marhaba dan a yanzu ta shirya tsaf da tarbanka"


Mus'ab ya ƙara sa faɗa yana yi masa nuni da ita fuskar sa ɗauke da wani mugun murmushi


Umar jinjina kai yayi yana  kuma kallon tauran a hankali ya juya ze fara tafiya


Rauda ta ƙanƙame sa tana kuka tana faɗin


"umar kar kaje dan Allah mutuwa zaka yi"


Aasim ne ya fizgo a fusace


Ya yin da umar ya ci gaba da tafiya


A gigice ta kuma rugowa sai kafin ta ƙarasa inda umar Aasim yayi nuni da hannun sa wani kalar abu me kama da glass ya zagaye wurin gabaɗaya


Jita yi taci karo da abu gashi taku befi biyu ba tsakanin ta da umar amma wannan abun da Aasim yasa yayi shamaki a tsakanin su


Cikin kuka take bubbugawa tana kiran umar


A hankali ya juyo yana kallon ta


Tsananin tausayin ta ya ƙara za gaye zuciyar sa ya ɗauki tsayin biyu yana kallon ta daga bisani ya juya ya ci gaba da tafiya



Sai da ya karanta adduo i sosai sannan ya fara taka mata kalar wani kalan huci me zafi yaji yana dososa


Addu'ar dake bakin sa ya cigaba da karantawa har ya isa ƙofar tauran



Gaban sa ne ya fara faɗuwa yayin da yaga yadda wa'annan wuƙoƙin suke kaɗawa da ƙarfi



Jiyayi kamar ana fizgar sa yayi ƙarfin halin zura ƙafar sa ciki


Sai dai me? Jiyayi wani raɗaɗi ya mamaye sa yayi saurin kallon inda ya taka


Wasu mugayen allurai ne a caccake gabaɗaya kuma haka ƙasan wurin yike


Yayi shahada ya ƙarasa shiga yana ci gaba da ambaton sunan Allah


Cikin sakwanni wuƙaƙennan suka yo kansa ya runtse idanuwansa da sauri dan baya so yaga sanda zasu iso jikin nasa


Sai dai a me makon yaji yanka sai yaji ƙarar wuƙaƙen


Yayi saurin buɗe idon sa abun mamaki duk wuƙar da zo jikin sa sai ta lauye


Take sai ga wuƙaƙe birjik sun zube a ƙasa


"Allahu Akbar!!".


Ya faɗa, take wata izza me ƙarfi tazo masa ya ci gaba da tafiya duk da raɗaɗin da yake ji a ƙafafun sa.


Cikin mintuna biyu ya fara ganin duhu yayin da saman tauran ya ƙara baƙinƙirin.


Murmushi Aasim yayi dan yasan ƙarar farko da tauran zata yi zata halaka sa.


Daram!!



Wata kalar ƙara me razanar wa ta fita.


Sai da aka kwashi minti biyu sannan haske ya fara gauraye cikin tauran ɗin ta yadda suke iya hango cikin ta.


Umar suka hango kwance a ƙasa jini na malala a jikin sa.


Cikin farin ciki Mus'ab ya kalli Rauda yace;



"kingani ko, ƙara ɗaya ta tauran ji yadda ta mayar dashi, nasan a yanzu kuma sai dai wani Umar ɗin ba dai wannan ba".



Ya ƙarasa faɗa yana fashewa da dariya.


Su anty Kaltum kuka suke yi kamar ransu zai fita, yayin da Rauda ta zama kamar wata butumbutumi dan ko motsin kirki ta kasa yi, hawaye ne kawai ke bin fuskar ta.


Cikin hukuncin Allah Umar ya farfaɗo daga gajeruwar Suman da yayi.


Da sunan Allah ya farfaɗo a bakin sa.


Ya yunƙura  ya tashi cikin juriya ya cigaba da tafiya.


Mamaki ne ya kama rauhanan dake wurin, suka saki baki suna kallon sa.


 Rauda da sai lokacin ta samu damar magana ta kalli Mus'ab tace;


"Miye naka na sakin baki kuma? kana mamaki da ikon Allah ne??".


Mus'ab yayi ɗan murmushi tare da cewa;


"Me kike ma sauri? Duka-duka ƙarar tauran ɗaya ce fa amma ji yadda ta maida shi, ƙarar ta guda arba'in da takwas ta rage, ki ci gaba da zuba ido".


Dai-dai lokacin duhu ya ƙara mamaye tauran alamar ƙara na biyu na zuwa.


Jikin Rauda ya ƙara yin sanyi, zamewa tayi a wurin idanuwanta na ci gaba da zubar da hawaye.


Bayan minti talatin wanda yayi dai-dai da ƙarar tauran sau ashirin.


Umar ne kwance a ƙasa ya galabaita iya galabaituwa, amma duk da haka da ragowar ƙarfin sa sakamakon ƙarfin addu'ar da yake yi, kuma har lokacin ko wuƙa ɗaya ta kasa yankar sa.


Aasim yana tsaye yana kallon Rauda da taci kuka har ta gode Allah.


Tauran zata kuma sakin wata ƙarar yayi nuni da hannu ya dakatar da ita.


Mus'ab ya kallesa cikin sauri yace;


"me kayi haka yarima? Dakatar da ita fa kayi?".


Aasim ya jinjina kai kawai.


Mus'ab zai kuma magana ya dakatar dashi ta hanyar faɗin;


"sanin kanka ne ba wani mahaluki me rai da zai shiga cikin Tauran da wannan zafi da aka ƙara mata face ya mutu, ni kaina da nike jinsin rauhan sai da me martaba ya sanyaya ta sannan na iya tsallakewa, amma shi ka duba har yanzu ba alamar karaya a tare dashi, har yanzu babu wuƙar da tayi nasarar yankar sa bare ta illata sa, tabbas nayi kuskure da na manta cewa addu'a ma karin mumuni ce, idan har nace zan bar sa ya cigaba zanyi babban kuskure domin ko kamar na ja da hukuncin Allah ne".



Rauda ta kallesa da sauri jin abunda yace.


Shima kallon nata yayi idanuwansa na cikowa da hawaye.


A hankali ya rusuna inda take yana kallon ta cikin ido.


"kamar yadda na miki alƙawari yau zan barki, bazan ƙara bibiyar rayuwar ku ke da mijin ki ba, domin duk wanda ya sadaukar da rayuwar sa akanka ba ƙaramar ƙauna yake maka ba, abu ɗaya nike so ki sani ki kuma sa a ranki, ina sonki, kuma zan ci gaba da son ki har zuwa ranar da zanyi numfashi na na ƙarshe....",


Ya ƙara sa maganar cikin wani irin yanayi, tare da miƙewa ya juya da sauri.



Washegari Rauda ce zaune gaban gadon asibiti, Inda umar ke kwance, tana zaune kawai ta rasa meke mata daɗi.


A hankali Umar ya buɗe idanun sa.


Cikin rashin kuzari ta matso da kujerar da take zaune a kai gaban gadon, tare da ɗaura hannun ta saman nasa.


"ka farfaɗo?".


Tambayar da ta mai kenan tana kallon kyakkyawar fuskar sa.


Guntun murmushi ya sakar mata.


"na farfaɗo chuchu, alhamdulillahi mu gode ma Allah".


Siraran hawaye ne suka biyo kwarmin idanun ta.


Ta kwantar da kanta jikin gadon saitin fuskar sa ta yadda suke kallon juna ido cikin ido.


"yanzu kin yarda cewa ina miki so me tsanani chuchu?".


Ɗaga mai kai tayi tare da fara magana cikin sanyin murya.


" na yarda Umar, bansan kuma da me zan saka maka irin ƙaunar da ka nuna min ba".


Murmushi ya kuma yi tare da shafa gefen fuskar ta.


"Idan baki sani ba ni zan faɗa miki, yanzu tunda hankalin mu ya kwanta sai ki fara shirin biyana bashin da na daɗe ina binki".



Cikin rashin fahimta tace;


"bashi fa?".


Ya ɗaga kai.


"Eh ko baki san ina binki bashi ba?".



Ta ɗaga kai alamar eh.


Ya ɗan yi shuru yana tsura ma kyakkyawar fuskar ta ido.


"faɗamin bashin miye?".


"lallai ma yarinyar nan, wato da gaske baki sani ba, to bashin angoncewa na ko kin manta?".


Murmushi tayi cikin jin kunya.


"kana gadon asibiti kake wani maganar angoncewa, ai kabari ka samu lafiya ko?".


Shima murmushin yayi.


"Eh wai dama ina faɗa miki ne saboda ki shirya dan zaki gwaguru yarinya kamar ba gobe".


Ƴar dariya tayi har fararen haƙoranta  suka bayyana.


"zan gwaguru sai kace wata goruba?".



"yaushe rabon da inga dariyar ki?har na manta?".


Ya faɗa idanuwansa na kanta.


"kana son ka rinƙa ganin dariya ta ne?".


Ya jinjina kai.


"sosai ma kuwa, dan idan kika yi tana ƙara miki kyau kuma tana sani farin ciki".


Tayi murmushi tace;


"shikenan Jaana, bari in kira zayyad ya duba ka ko?".


Ta ƙarasa faɗa tana miƙewa. Hannun ta ya janyo ta faɗo jikin sa.


  Da sauri ta yunƙura zata tashi dan gudun kada ƙarin ruwan dake jikin sa ya goce, ya dakatar da ita ta hanyar faɗin;


"Please ki tsaya Ina son inji ɗuminki ne".


 Ta ɗan ƙwalalo ido tare da faɗin;

"A asibiti kake fa, kuma ka duba yana yin da kake ciki".



"Dan a asibiti nike sai me? Ai ɗumin ki nace ko?".


   Ta ɗan girgiza kai, dai-dai lokacin da Zayyad ya turo ƙofa.


Tashi tayi da sauri tana matsawa.


Zayyad yayi murmushi.


"A lallai abokina sauki ya samu, ashe ka farfaɗo har ka fara soyewa! Allah ya taimake ka da yanzu kana lahira".


dariya suka yi gaba ɗaya.



Bayan sati biyu

Umar ya samu sauƙi sosai dan har sun dawo gida


Tunda ga bakin get Rauda ta saki baki tana kallon gidan,dan a canza mai feti bata ƙara shiga mamaki ba saida suka shiga falon


An canza komai na gidan, ta maida kallon ta ga umar fuskar ta cike da mamaki


"Jaana Naga gidannan ya canza, Anya ba ɓatan hanya muka yi ba?


Yayi murmushi yana matso wa kusa da ita sosai, kyawawan idanuwan sa ya zuba Mata


Cikin murya me taushi yace


"gidan ki ne chuchu Bawani ɓatan hanya,nine nasa aka canza komai"


Ta sauke ajiyar zuciya tace


"amma gani nayi kayan gidan nan sababbi ne ba abunda suka yi"


Umar ya ɗaga kai yace


"nasani chuchu, rayuwar da mukayi a gidannan rayuwa ce me cike d firgici da tashin hankali, shiyasa na sa aka canza komai saboda banason muna ganin duk abunda ze rinƙa tuna mana da waccan rayuwar, na kuma sa anyi saukar alqur'ani me girma saboda kariya"


Murmushin jindaɗi tayi,tana kallon fuskar sa


"nayi farin ciki sosai,nagode"


Ya girgiza kai

"A'a fa ba anan ya kamata ki nuna farin cikin ki ba?


Har lokacin da ragowar murmushi a fuskar ta


" to a ina ya kamata in nuna ranka shidaɗe?


Surar ta yayi, yayi mata ɗaukar jarirai


"bari in kai ki, kigani"


Sama ya fara hawa ya nufi bedroom


Dariya ta fara yi tana zullo da ƙafafun ta


"nagane wayo kake so kamin, to banyar da ba ka sauke ni"


Shima dariyar yike yi cike da nishaɗi, ya tura ƙofar bedroom ɗin tare da kwantar da ita a kan gadon


Tayi saurin yunƙurawa zata tashi,ya hana ta hanyar yi mata rufa d faffaɗan ƙirjin sa


Kallon cikin ido suka fara yi ma juna,saboda shauƙin soyayya har basa ƙyaftawa


Sunyi minti uku a haka daga bisani ta mirgina,ya koma ƙasa ita kuma ta koma sama


Sunkoyo da fuskar ta tayi daidai tasa,yayin da karan hancin su yike gogan juna


"in faɗa ma wani abu??


Tayi tambayar cikin maƙoshi


Da ido ya bata amsar alamar eh


"ina sonka fiye da yadda kake sona"


Ya ɗan zaro ido yace


"kambu, wallahi banyar da ba,nafiki"


Tayi dariya har farare haƙoran ta suka bayyana


"to shikenan bari dare yayi zamu gani"


Ta faɗa cikin tsokana


Matseta yayi a jiginsa yace


"eyyeh wato har zumuɗin dare yayi kike? Ai ba sai da daddare ake yi ba bari ma kigani....


Ya ƙarasa faɗa yana yunƙurawa


Tashi tayi da gudu ta fice daga ɗakin tana dariya


Washegari da safe

Tana kwance Jikinsa tayi luf


Yana shafa Suman kanta da ta baje a bayan ta


_"chuchu"_


Ya kira sunan ta, ta buɗe idanuwanta da suka yi mata nawi, batare da ta amsa ba ta kalle sa kawai


Lallausan murmushi ya sakar mata


"Allah yayi maki albarka ya saka miki da gidan aljanna, kinsani farin cikin da ban taɓa shiga irin sa a rayuwa ta ba nagode"


Ta maida mai martanin murmushin tana jin ta cikin wata kalar sabuwar rayuwa me cike da natsuwa


Maida idanuwan ta tayi ta rufe dan sam bata jin ƙarfi


Da kanshi yayi mata wanka ya haɗa musu abun kari, be yarda taci da kanta ba a baki ya dinga bata bayan sun gama suka dawo cikin falon


Shagwaɓe masa tayi sosai ita ta gaji bacci take so ta sake yi


Ya zauna akan doguwar kujera sannan ta kwanta tayi matashi da cinyar sa


Lallaɓata ya dinga yi kamar ƙwai


Bayan wata biyu


Basu da wata matsala soyayyar su kawai suke sha,umar ya koma bakin aikin sa


Ranar wata Laraba yana zaune gefen gado yayin da take sanya kaya dan fitowar ta daga wanka kenan


Kallon ta yike tayi,ta ɗan tsaya hannun ta riƙe da riga tana kallon sa tace


"wai Jaana baka gajiya da kallona ne?


Murmushi yayi yana miƙewa idanuwansa akan ƙirjin ta


"kem kinsan har abada bazan taɓa gajiya da kallon ki ba"


Baya ta ɗan fara ja tana faɗin


"Jaana dan Allah kayi haƙuri ka bari muje siyan ice cream ɗinnan MU dawo"


Dariya yayi yana girgiza kai


"raguwa kawai, ba wani abu zanyi miki ba ni, gani nayi duk kin canza anya ba ciki ne dake ba kuwa?


Ta ɗan waro ido


"ciki?


Ta faɗa, umar ya jinjina kai


"eh haka nike zargi dan duk kin sauya amma bari mu bincika mu gani"


Gwaji na farko ko da yayi ya gano ciki ne


Farin ciki a gurin sa baya misaltuwa ɗaga ta yayi yayita juyi da ita


Har sai da ta fara ganin jiri


"Jaana ka saukeni dan Allah jiri nike gani"


Ajeta yayi a gefen gado ya durƙusa gaban gadon yana zuba ma kyakkyawar fuskar ta ido


"chuchu me kike so, me kike buƙatar kiga kin mallaka da ze saki farin ciki kifaɗamin zanyi miki shi yanzu"


Rauda tayi murmushi tana rusuno da fuskar ta kusa da tasa


"burina ɗaya ne a rayuwa inga na mallake ka,na riga da na samu Allah ya bani kai a matsayin miji bani da wani buri bayan wannan kasance wa dakai shine farin cikina"



Umar ya lumshe idanuwansa saboda daɗin kalaman ta da suka ratsa masa zuciya


"nagode Rauda, yanzu bari inje in siyo miki ice cream ɗin ki kwanta ki huta bayan shi kina buƙatar asiyo wani abu ne?


Girgiza masa kai tayi alamar A'a


Ya miƙe yana manna mata kiss a goshi


"sai na dawo"


Jinjina mai kai tayi, sai da ya kai bakin ƙofa sannan ta kira sa


Tsayawa yayi tare da juyowa


"ya aka yi madam?


Rauda tayi murmushi tace


" ka kula min da kanka sosai"


Shima murmushin yayi yace

"angama Ranki shidaɗe"



Bayan fitar sa, sujada tayi ga ubangiji na nuna godiyar ta garesa


Shafa cikin kawai take yi tana ayyano abunda zata haifa


Tunda ga wannan lokaci umar ya ƙara ƙaimi gurin nuna mata tsantsar kulawa.


 Bayan wata tara


Cikin ta ya tsufa sosai dan da ƙyar take iya tafiya


Ranar ya shirya ze tafi aiki yaga yanayin ta sai a hankali ya fasa


Ashe ko haihuwa zata yi


Abunka ga likita da kanshi ya karɓi haihuwar abarsa


Tasha wuya sosai, shi ko ya shiga damuwa ya ƙara tausayawa mata


Cikin hukuncin Allah ta haifo kyakkyawan yaro namiji


Sai da ya tabbatar ta dawo cikin hayyacinta sannan ya sanar da anty kaltum


Ba afi minti goma ba sai gata ta ƙara so


Cikin farin ciki take faɗin


"ah Lallai sannu wato dan kana likita shine ba zaka sanar damu tun tana na ƙuda bako?


Dariya umar yayi yana miƙa mata jaririn


"ga ɗanki nan sai ki shirya sa, ki barmini mata ta zan kintsa abata da kaina"


Anty kaltum ta amshi Yaron tana faɗin


"masha Allah sannu da ƙoƙari da Rauda"


Rauda dai ba bakin magana dan anji yadda mata keji



Da kansa ya kira anty ummi da mama ya faɗa musu


Sunyi murna sosai anty ummi tace tana nan tahowa Washegari



Da daddare Rauda na zaune kan gado ta tsura ma jaririn ta ido


Ji take ƙaunar sa na ratsa zuciyar ta ba abunda ya bari na mahaifin sa, har ma yaso yafi sa kyau


Bata san umar ya shigo ba sai da ya ɗan zungure ta


Ta ɗago ta kalle sa


Murmushi yayi tare da zaunawa


"sannu Maman baby, babyn ake ta kallo haka?


Ta maida mai martanin murmushin tace


" ina kallon kamannin ka daya kwaso ne ba abunda ya ɗauko nawa"


Ƴar dariya yayi me bayyana tsananin farin cikin da yike ciki


"Haba dai wannan ƙaramin bakin ai irin naki ne"


Ta maida kallon ta ga Yaron tana faɗin


"Bawani nan,kadai yimin wayo bari Allah ya kaimu next time idan nasamu ciki bazan sake kallon ka ba har sai na haihu, dan ina ganin kallon ka da na dinga yi ne yasa"


Dariya yayi sosai


"tofah to Allah ya kaimu,wani suna kike ganin ya dace mu saka masa?


Tayi ɗan shuru tana nazari  


"ni ina ganin Musaka masa Aasim"


Rauda tayi saurin kallon umar jin abunda yace


"Aasim fa kace?


Umar ya jinjina kai

" eh, miƙo sa ma inmasa huɗuba"


Rauda ta girgiza kai tace


"A'a Jaana kadai duba wani sunan....


Murmushi umar yayi tare da faɗin


" Aasim be cancanci Musaka sunan sa bane?


Shuru tayi tana cigaba da kallon sa


Umar ya cigaba da cewa


"Aasim masoyin ki ne na haƙiƙa wanda a yanzu ya sadaukar da soyayyar sa dan dai ki kasance cikin farin ciki,kisani da ace yana yana da mugun hali da tuni ya halaka ni, ya sha matuƙar wahala akan ki,ya sadaukar da abubuwa da yawa duk dai akan ƙaunar ki,bantaɓa jin tsanar sa a raina koda sau ɗaya ba saboda duk me sonki masoyi na ne,dan haka babu sunan da ya dace musa sai nasa"


Rauda ta kasa magana dan gabaɗaya jikin ta yayi sanyi


Lokaci ɗaya soyayyar ta da Aasim ta dawo mata


Umar ya ɗauki jaririn yayi Masa huɗuba sannan ya maida mata shi kan cinyar ta


"Allah ya Raya Aasim, bari inje in watsa ruwa"


Har lokacin ta kasa cewa komai


Ya ɗan tsaya yana kallon ta


"wai miye kika wani sauya, Haba madam smile mana"


Ajiyar zuciya ta sauke kawai


Dariya yayi yana ficewa daga ɗakin


Shimfiɗar da yaron tayi, ta kwanta tare rufe idanun ta


_"zan barki kamar yadda nayi alƙawari bazan sake bibiyar rayuwar ki, amma kisani bazan taɓa dena sonki ba har ƙarshen rayuwa ta"_



Kalaman shi na ƙarshe suka dawo mata


_haba habibty, kiyi murmushi mana idan kiƙa ƙi yifa zanyi kuka_


_Ina son ki fiye da yadda nike son kaina Rauda_


_Na amince na rasa komai inhar zan rayu dake_


Kalaman sa suka yi ta yi mata yawo a kunne


Ta shi tayi ta zauna, tana jin babu daɗi


Yanzu ko wani hali yike ciki oho, ya datse duk wata hanya da zata sa dashi da ita, yanzu shikenan ba zata ƙara ganin sa ba har abada?


Tayi wa kanta tambayar, sake rungume jaririn tayi tana jin wata sabuwar ƙaunar sa sakamakon sunan da aka sa masa


_matsayin ka a raina baze taɓa canza wa ba Aasim Allah yasa kana cikin farin ciki_


Ta faɗa cikin zuciyar ta


Ranar suna dangi sun taru sosai anci ansha anyi wadaƙa da kuɗi


Jariri ko ya samu kyaututtuka


Bayan wata huɗu Aasim ƙarami yayi wayau sosai dan har ya fara zama



Yaro ne me farin jini kowa sonsa yike yi


Yarima shine sunan da Rauda take kiran shi dashi


Ranar suna zaune  tana ma yarima wasa yana ta dariya


Umar kallon su yike yi cikin farin ciki da nishaɗi


  Miƙewa tayi ta ɗaura ma umar yarima aji kinsa


"Kaga idan na biye wa wannan yaron bazan je inyi wanka ba"


Umar ya ɗaga shi sama yana faɗin


"daɗin ta ga ubanshi a kusa bari na cigaba da ma wasan kaji ɗan albarka"


Dariya tayi ta haye sama, ta faɗa toilet tayi wanka


Shirin shadda pink tayi, tayi kyau sosai tana cikin ɗaura ɗan kwali ta lura da mutum a ɗakin


A ɗan tsorace ta ɗago, umar ta gani tsaye ya zuba mata idanun sa hannayen sa harɗe a ƙirji


"kai Jaana kabani tsoro wlhi yaushe ka shigo ban sani ba"


Ƙasaitaccen murmushi yayi yace


"ya za ai kisan na shigo hankalin ki ya tafi gurin kwalliya"


Ta sauke ajiyar zuciya


“hmmm to ai dan kai nike yi koh"


Jinjina kai kawai yayi, ya ware mata hannayen sa


“zo inji ɗumin ki plz“


Aje ɗan kwalin tayi ta shige ƙirjin sa


Ajiyar zuciya ya sauke me nawi tare da rungume ta sosai


murmushi tayi tana faɗin


"wannan irin ajiyar zuciya haka? Sai kace ka shekara batare dani ba, banfa fi minti ashirin da baroka ba"



"ba zaki gane ba,yanzu dai baki da wata matsala koh?


Ta jinjina kai


"bani da wata matsala mijina,nagode da kulawarka gare ni ina sonka"



Murmushi yayi tare da faɗin


"Nima ina sonki habibty"


Lumshe idanuwan ta tayi cikin farin ciki


"kasan wani abu.......


Kasa ƙarasa wa tayi, tare da saurin buɗe idanun ta


Idan batai kuskure ba habibty taji yace


"me kafaɗa yanzu? Mai maita"


Ta faɗa tana kallon cikin idanun sa,tabbas ze iya canza komai amma baze taɓa iya canza idanun sa ba



"Aasim......


Ta faɗa cikin rawar murya 



"na'am habibty"


Ya amsa yana shafa fuskar sa kamannin sa suka bayyana


Baya taja da sauri tana faɗin


"innalillahi wa inna ilaihi raji'un"


Yana yin fuskar sa ta canza zuwa damuwa


"sai kace kinga sheɗani Rauda?


Zubewa tayi a kan gwiwowin ta nan da nan idanuwan ta suka ciko da hawaye


" Aasim alƙawari fa ka ɗauka Meyasa ka karya? Dan Allah kada ka cutar min da mijina kada ka cutar min da ɗana........


Shhhh


Ya faɗa yayin da ya durƙusa gabanta


"ba wannan ya kawoni ba Rauda, tsakanina da mijin ki sai dai kariya ba dai cutar wa ba,ɗanki kuma ɗana ne bazan taɓa bari wani abu ya samesa ba, ki kwantar da hankalin ki dan Allah"


Kallon sa tayi da mamaki sosai tana tantamar abunda ya faɗa


"wallahi da gaske nike yi Rauda kiyarda dani"


Numfashi ta sauke tana jinjina kai


"shikenan me ya kawo ka gareni?


" zamu iya zama muyi magana?


Ya faɗa yana tsare ta da idanun sa


Gyaɗa kai tayi, bayan sun zauna yace


"Yanzu ba da bane Rauda, Bawani cutarwa da ze ƙara shiga tsakanin mu, tun ranar da umar ya shiga tauran na tabbatar da yana miki so me tsanani bazan ƙara yunƙurin raba shi dake ba,a shekara ɗaya da rabin da nayi ba tare dake ba na shiga tsananin ɗimuwa na koma rayuwa a ƙasan ruwa da ƙyar na yarda na koma masarauta


Rayuwa bata min daɗi Sam, bana shiga cikin ƴan uwana sai dai na kulle kaina a ɗaki


Ganin halin da na shiga me martaba ya auro min wata ƴar sarki


Amma bantaɓa jinta a raina koda sau ɗaya ba, Rauda bazan iya rayuwa babu ke ba kinkasance wani sashe na rayuwa ta


Ki amince kiciga da rayuwa dani nayi miki alƙawarin babu abunda ze faru da izinin Allah"


Rauda ta sauke ajiyar zuciya tace


"wace kalar rayuwa kenan Aasim amma dai ba irin wacce muka yi a baya ba koh?


"nidai ki amince min inrinƙa zuwa ina ganin ki, ko hakan ma ya isheni"


Kaɗa kai tayi tana ɗan murmushi dan sai lokacin hankalin ta ya kwanta


"nagode sosai habibty"


Da daddare suna kwance ita da Umar yana shafa gashin kanta ta kira sunan sa


Ya amsa, tace ɗazu fa Aasim yazo"


Umar yayi murmushi

"nasani ai,zan shigo ɗakin naji maganar ku"


Ta kalle sa da mamaki


"amma shine ranka be ɓaci ba?


"kan me raina ze ɓaci chuchu? Yariga ya zubar da makaman sa yanzu ya zama ɗan uwa agurina"


Ajiyar zuciya Rauda ta sauke ta jinjina kai kawai


Rayuwa ta canza,Maganar rikici ya ƙare


dan anriga anzama ɗaya, Aasim da umar sun koma kamar abokai musamman Aasim ya kan ɗauke su zuwa duniyar su


Rauda Sam bata da wata matsala dan bata aikin komai Aasim ya ajiye rauhanai mata masu yi mata,umar arziƙi ya ƙara haɓaka dan ya gina ƙaton asibiti na sa na kansa


Sukan haɗu su biyar, Aasim, umar, Rauda shahida da kuma da kuma Aasim ƙarami


Ayi ta nishaɗi su suna hira shahida na wasa da yarima


Ranar ma hakan ta kasance 



Suna zaune a falo,yarima yayi bacci yayin da umar suke ta wasa da shahida


Aasim kallon Rauda yike tayi, ta cikin zuciyar sa ya aika mata da magana


"ina son ki Rauda"


Murmushi tayi tana kallon su gaba ɗaya wani farin ciki na ratsa zuciyar ta.



Alhamdulillahi anan na kawo ƙarshen wannan labari na jinnul aashique


Babban abunda nike so na isar shine,rayuwa ta kan zo ma mutum a yadda ubangiji ya tsara masa


Labarin jinnul aashique kashi talatin cikin ɗari 30/100 ya faru da gaske a zahiri


Dan Aasim akwai shi a zahiri yayi soyayya da wata budurwa wacce kuma saurayin ta shine umar


Amma sauran labarin na tsara shi ne dan na faɗakar na nishaɗantar


Aduk halittun da ubangiji yayi babu halitta me kyau kamar ta bil'adama


Shiyasa aljanu suke bibiyar mu,ya kamata mu kula sosai musamman ƴammata dan sunfi samun irin wannan matsalar


Murinƙa azkar, yayin shiga bayi, lokacin kwanciya da sauran su


Dan ba kowani aljani bane yike jin tsoron Allah akwai mugaye akwai kuma na kirki


Jinnul aashique shine matsalar da yawancin ƴammata suke fama da ita, zaka ga yarinya da saurayi yazo indai maganar aure ne sai ka ga ya dena zuwa ko kuma ita taji bata son kowa


Irin wannan matsalar tana da wuyar sha'ani,sai mun kula sosai mun dage da addu'a.


Allah ubangiji ya ƙara karemu da zuri'ar mu baki ɗaya.


Mu haɗu a sabon littafi na, me suna *_ZAFEERAH_* da kuma ɗayan me suna *_JIDDAH_*


Taku a kullum *_ƴarfillo_*.



Post a Comment

0 Comments