[04/08, 21:52] Hubbey Frd Ameena Kn: [4:40AM, 7/15/2018] hubbeey: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*Sat/july/14/2018.*
*STORY*
*By*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Aindo k'afar yawo)._*
*_WRITTEEN & EDITING_*
*BY*
*_HABEEBA IDREES(Hubbeey)._*
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*_ALLAHUMMA LAASAHLA ILLAMAJA'ALTAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZ'NA IZA SHI'ITA SAHLAH._*
*💠SMASHER & HUBBEEY🌺 FANS GROUP 1&2.*
*WAN NAN PAGE 'DIN NA FARKO NAKUNE KUYI YADDA KUKE SO DASHI.*
*GARGA'DI*
*BAN YARDA WANI/WATA SU JUYAMIN WAN NAN LABARINBA TA KOWACCE SIGA, HAK'IK'A YIN HAKAN ZAISA IN 'DAUKI BABBAN MATAKI GA DUK WANDA YA AIKATA HAKAN.*
*IDAN KUNNE👂🏻👂🏻 YAJI..........*
*HAK'IK'A WAN NAN LABARIN BA K'IRK'IRARSA NAYI BA, HAKAN YAFARU DAGASKE KUMA ZANFARA RUBUTA WAN NAN LABARINE DA YARDAR WACCE ABIN YAFARU AKA*
*_PAGE1⃣_.*
Yarinya ce 'yar kimanin shekaru goma sha uku,
Gudu takeyi iya k'arfin a dai² lokacin da AUDU mak'ocinsu ke k'wala mata kira..
"Indoooo! Indoooo!!
Inaaaa aituni indo tasha kwanar dazata sadata da gidan sabuwar Amaryar da aka kawo kwanaki uku dasuka wuce..
Tsaki AUDU yayi yanacewa "kai jama'a wan nan yarinya indo akwai k'afar yawo duba yadda BAFFAN ta yake kiranta nima na mai² ta mata amma saida takai ga inda take son zuwa ALLAH yashirya...
Ko sallama babu indo ta tura kai cikin d'akin Amaryar, a jikin k'aramin gadon Amaryar ta jingina, itakuwa Amaryar ido kawai tazuba wa indo, ganin yadda Amaryar take kallonta ne yasa INDO ta matsa daga jikin gadon...
"Ke mene haka zakishigomin d'aki ko sallama babu?"
Washe baki INDO tayi tana faman dariya kamar bada ita Amaryar take maganba........
Daga bakin k'ofa taji sallama, aikuwa suna had'a ido da INDO ya d'aure fuska, gaban INDO ne yafad'i saboda arayuwar ta bata k'aunar taga mutum ya 'bata rai saboda ita, baiyi mata maganaba sai wata muguwar harara dayake watsa mata, sum sum sum takama hanya tayo waje bata tsaya ko inaba sai bakin k'aramar kasuwar dake cikin garinna su.....
Tun daga nesa suke mata dariyar yadda suka hango k'afarta ko takalmi babu, haushine yaka mata ranta A 'bace ta k'araso inda suke...
"Amina nagaya miki banason abinda kukeyi min amma kullum bakuji ko?"
kallon k'afar INDOn Amina takeyi ta kuma kwashewa da dariya.......
Sosai INDO taji haushi ganin zasu maida ita mahaukaciya ne yasa tayi saurin barin wajen......
Chaaaan gefe tasamu tazauna tana ta kallon sauran mutanen dake kai komo acikin kasuwar....
Kamar antsikara mata wani abu haka ta mik'e ta kyalla da gudu gida tanufa bata zarce ko inaba sai d'akin BAFFAN ta babu kowa ad'akin bincike tashiga yi duk inda tasan BAFFA yana ajiya saida ta duba amma sam bata samu abinda take nema ba.......
A tsakar gidansu ta tsaya tana tunanin ina zataje, jitayi an damk'e hannunta tabaya da sauri INDO ta juyo ganin wadda ta rik'eta d'in yasatayi shiruuu takasa cewa komai........
"INDO wato ke bazaki iya zaman cikin gidanku bako?"
"GOGGO naga sai na gama miki komai san nan nake fita"
INDO tabata amsa tana turo baki gaba.....
"Ehhh amma dai kinsan wan nan fita yawon da kikeyi yana 'batawa BAFFAN ki rai ko?"
A dai² lokacin ne BAFFA yashigo gidan, da sauri GOGGO tasaki hannun INDO......
K'afar indo kawai BAFFA yakalla ya girgiza kai da alamun damuwa sosai akan fuskarsa, baice komai ba yashige d'akin yabarsu anan, aikuwa tana ganin BAFFA yashiga d'aki da gudu INDO tayi waje........
jiyo muryar GOGGO yayi tana salati da sauri BAFFA yafito yana tambayarta mene yafaru?
Nan ta shaida masa cewar ai INDO ce tasake ficewa daga gidan,
'Daga kansa yayi sama kamar mai duba wani abu............
"Kai jama'a YA ALLAH kaine kabani AISHA ALLAH kaine zaka shirya min ita, YA ALLAH ka karemin ita aduk inda take"
GOGGO dake gefe ta amsa da "AMEEN"
Ta cikin wata k'atuwar gona tabiyo tafiyar ta take hankalinta kwance duk da duhun maghreb dayafara amma ko kad'an INDO batajin tsoro haka take taka k'afar wadda ko arzik'in takalmi bata samuba, itayi kamar ana binta abaya ahankali ta juya babu alamun tsoro atareda ita.....
AUDU tagani ya d'akko ice mai makon INDO tabashi hanya kawai saita juwa tacigaba fa tafiyarta....
"INDO kauce mana kina ganin kaya akaina ko tsoro bakiyi ga Almoru ta kawo kai"
Kamar bada ita yake maganaba haka taci gaba da tafiyarta san nan ta tage saurin da takeyi....,
Haushine yakama AUDU haka ya hak'ura ya kaucewa INDO yashiga cikin gonar mutane yana sauri² baifi taku biyar AUDU yayi ba ji kake yiiippp AUDU ya fad'i shida itacen da yad'akko.....
Da gudu INDO tak'araso inda AUDU yake kwance, a gabanshi ta tsuguna wata irin muguwar dariya INDO taleyiwa AUDU, shikuwa sai salati yake yi yana neman ataiaka masa....
"INDO nakarye wllh INDO nakarye"
Fad'a yake yana mai² tawa amma duk da haka INDO bata dena dariyar datakeyi ba......
Saida taji dai yayi shiru san nan itama ta dena dariyar.....
"ALLAH sarki AUDU sannu bara inkai maka itacen gida sai ingayawa INNA LAMI ka karye a gonar MALAM TANIMU"
Da kyar ta iya d'ora itacen akanta san nan ta d'auki hanyar gida......,
Tundaga jikin dangar gidan AUDU INDO tafara kwalawa INNA LAMI kira tareda sanar da ita cewar AUDU yafad'i yakaye, kamar daga sama INNA LAMIn take jiyo mufyar INDO d'in.....
A dai² k'oafar dazata shiga gidan AUDU ne taci karo da d'angidan AUDU agabansa ta saki itace saura kad'an yasauka akan k'afarsa....
"Ga itacen kunan kuma babanka yana chan kwance a gonar malam tanimu ya fad'i yakarye inkun gadama kuje ku d'akko shi"
Tana gama fad'ar haka ta juya takama hanyar gidansu.
*_FANS DAN ALLAH KUMIN AFUWA NARASHIN YIN TYPING EN NOVEL EN SAMEERA, JIYA DA YAU DABANYI BA AMMA INSHA ALLAHU GOBE ZANYI DA YARDAR ALLAH._*
*_Ur's Hubbeey._*
[4:41AM, 7/15/2018] HASSN ATK: Hmmm kingama wachanna
[4:41AM, 7/15/2018] hubbeey: Gobe zan gamashi
[4:43AM, 7/15/2018] HASSN ATK: Hmmm lallai km
[4:49AM, 7/15/2018] hubbeey: 😏😏😏😏
[4:50AM, 7/15/2018] hubbeey: *Falyaqul khairan auliyasmuut*🤫🤫
[4:52AM, 7/15/2018] MEINAH LTTL: 😂😂😂
[4:52AM, 7/15/2018] MEINAH LTTL: Bafa abinda nace
[4:52AM, 7/15/2018] MEINAH LTTL: Ba tsiya nafa ba
[04/08, 21:52] Hubbey Frd Ameena Kn: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*sun,july,15,2018.*
*_STORY_*
*BY*
*_AISHA MODIBO_*
*_(indo k'afar yawo)._*
*_WRITTEN_*
*BY*
*_HABEEBA IDREE(hubbeey)._*
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAASAHLAH ILLA MAJA'AL TAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZ'NAH IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*S.H.D.G NOVELS GROUP*
*S.H.D.G COMMENTS GROUP*
*S.H.D.G KITCHEN GROUP*
*MIJIN AURENA FANS GROUP*
*&*
*GAMU GA ALLAH FANS GROUP*
*DUK NAZO GAREKU*
*_WAN NAN PAGE 2 'DIN NAKUNE_*
*_KUMA KARKU MANTA DA SAKA INDO CIKIN ADDU'O'INKU._*
*_page2⃣._*
A k'ofar gida INDO tagamu da BAFFAN ta bashiri ta sunkuyar da kanta k'asa tabi ta gefensa ta shige cikin gida, Abakin murhu ta samu GOGGO tana kwashe dasauri INDO tafara d'aukan tuwon da GOGGO ta kwashe tana kaiwa cikin d'akin girkin su, itakam GOGGO da ido kawai tabita a zuciyarta kuwa tanayi mata addu'ar ALLAH YASHIRYE TA da wan nan yawon datakeyi, bayan tagama kaiwa tanufi bakin rijiyar su ruwa ta jawo tazubawa GOGGO a buta itama ta zuba tayi alwala.....
Tunda tashiga d'aki take jero sallolin dabatayiba wanda suka wuce ta tana chaaan wajen yawo, har GOGGO ta idar tayi addu'o'in ta amma INDO bata idarba.........
Bayan ta idarne tafara jero addu'oi afili takeyin addu'ar yadda duk wanda yake cikin d'akin zai iyajin abinda take fad'a cikin addu'ar.....
"YA ALLAH KASA INADA RABON ZUWA BIRNI KODA AK'AFANE, KUMA ALLAH KASA INNAJE BIRNI INSAMU MIJI MAI KU'DI WANDA ZAI BARNI INTAYAWO NA INA GANIN GARI"......
GOGGO kuwa dake gefe guda cikin d'akin tana jan charbi da sauri ta juyo saboda jin wanan Addu'a da INDO tayi, ba shiri GOGGO ta shafa addu'ar datakeyi ta fice daga d'akin GOGGO tana fita tanufi soro ta rufe k'ofar gidan da kuuba, abakin k'ofar soron sukayi karo da INDO zata fice wata harara GOGGO ta watsawa INDO ta wuce tabarta awajen...
'Dakin BAFFA GOGGO tashiga a zaune tasameshi sallama take tayi amma sam BAFFA baisan ma tanayi ba yayi nisa sosai cikin tunanin "yarsa INDO, harsaida GOGGO ta zauna kusa dashi ta kama hannusa tasauke daga kan kuncinsa wanda ya zabga tagumi dashi.
"haba MODIBO saunawa Zan gaya maka kadena yawan tunanin nan addu'a ya kamata muyi tayi mata bawai musaka damuwa aranmuba"
" kayya BINTA bakisan yadda nakeji ba wllh saboda yawan yawon da INDO takeyi, indama nake godewa Allah bata jawo min magana barta dai tashiga nan tashiga chaan amma hakan ko kad'an bashida wani amfani musamma ga ita mace, gaskiya BINTA bazan 'boye mikiba wan nan abu yana matuk'ar damuna wllh"
Ya k'arashe maganar yana kamo charbinsa...
"to yaya zamuyi MODIBO addu'a babu abinda ta bari ita zamuci gaba dayi mata har muga k'arshen lamarin"...
GOGGO tayi tunanin fad'awa BAFFA irin addu'ar dataji INDO nayi d'azu da ta idar da sallah, amma ganin yadda tasamu BAFFA ne yasata fasa gaya masa....
mik'a masa kuubar data rufe gidan dashi tayi...
"Gashi inzaka fita sallah Isha sai ka bud'e"
"Hmmm yanzu ma fita zatayi ko?"
BAFFA yatambaya fuskarsa cike da damuwa...
" a'a kawai dai na rufene, bara inkawo maka abincin ko?"
" a'a kibari saina dawo daga sallah tukunna"
Yana fad'ar haka GOGGO ta mik'e tabar d'akin.......
Alokacin da iyalan AUDU suka isa gonar malam tanimu sosai garin yayi duhu dan Alokacin ma anashirin yin sallar ISHA, akwance suka sameshi ga k'afarsa d'aya akarye, nan suka shiga tunanin yadda zasu d'aukeshi, halliru wanda qanin ga AUDU shine yaba shawarar akoma ad'akko kura sai asakashi aciki atafi gidan dori, aikuwa haka akayi halliru da Aminu d'angidan AUDU sune suka komo gidan dan d'aukar kurar dazau sako AUDU aciki, basu wani jima sosai ba suka dawo suka d'aukeshi suka sakashi aciki, haka sukayi ta turashi har suka shigo cikin garin, kai tsaye gidan. Sarkin 'Dori suka nufa dashi.....
Bayan BAFFA yadawo daga sallah isha ne ya rufe gidan tareda yin addu'a, d'akin GOGGO ya lek'a ya kirawo INDO cewar taje tasameshi a d'akinsa....
Saida tagama nuk'u-nuk'un ta kafin ta tashi ta tafi...,
Daga bakin k'ofar ta tsaya tace
"BAFFA gani"
" haba AISHA shigo daga ciki mana"
"Wllh BAFFA nasan fad'a zakayi min innashigo gara kawai intsaya daga nan idan naji ba fad'an bane sai in k'araso ciki"
Tayi maganar tana kunbura baki irin na shahararrun shagwa'ba'b'bun yara.....
Wani murmushin takaici BAFFA yayi san nan yace..
"Ba fad'a zan miki ba aikenki zanyi"
Aifa tanajin kalmar aike da sauri tashige cikin d'akin....
"yawwa ko kefa AISHA ta, amma kafin in aike ki bari in tambaye ki nasan bakyayin k'arya dan Allah AISHA ki fad'amin gaskiya kminji"
"To BAFFA na zangaya maka"
"yawwa AISHA jiya dana fita kinsan na jima bandawo ba ko?"
Bai jira ta amsaba yacigaba da maganar sa..
"To dan Allah wakika gani yashigomin d'aki?, da na dawo natarar anyimin bincike kuma ni nasan ba GOGGON ki bace, AISHA ko kinsan wanda yashigo min?"
Batare da wani jin tsoro ba INDO ta kalli BABBAFAN ta tafara magana..
"BAFFA wllh nice nan nashigo inaneman kud'ina dana baka ajiya zan sayo takalmi akasuwa kuma nayita dubawa baganiba na hak'ura, amma yanzu tunda ka tinamin saila d'akko min kud'ina ko?"
Dariya sosai BAFFA yayi
"Yanzu AISHA daman haka akeyi idan anbawa mutum ajiya sai naya nan azo ayi masa bincike? ashe tba banzaba BINTA tace tadena karban ajiyar ki kota meye, to nigashi tunjiyan banga kud'ina ba dana ajiye kinga kenan kin d'auki kud'in takalmin ki ko?"
Nanfa idanun INDO suka ciko da hawaye tashiga rantsuwa..
"Wllh BAFFA saidai inwani ne ya shigi ya d'aukar maka amma wllh Allah niban d'aukar maka kud'I ba"
"To shikenan naji yanzu koibari kinga gobe LARABA innaje kasuwar LARABAR ZANGO sai in sayo maki takalmin ko"?
" BAFFA nidai dakabani kud'in sai insayo da kaina"
"haba AISHA tunda nace zan sayo naki aikinsan zansayo maki ko?"
Itakam abun bai mata dad'i ba kawai ta hak'ura ne saboda tafiso taje kasuwar dakanta....
"BAFFA to kabani aiken mana intafi"
INDO ta tunawa BAFFAN maganar aiken dazai mata.....
"Kibarshi ma naga dare yayi da safe in Allah yakaimu saiki sayomin"
Bakinta tura gaba ta mik'e zata bar d'akin, da sauri BAFFA yakamo hannunta "AISHA fushi kikayi dani"?
Hannu tasaka ta rufe fuskarta saboda taji kunyar tambayar da ABBAFA yayi mata...
"A'a ba fushi nayiba"
"Yawwa AISHA ta jeki to ALLAH yayi miki albarka, ALLAH yashirya minke, inkije kice ina kiran GOGGON ki"
Da to ta amsa masa, harta kai bakin k'ofa ta juyo..
"Au BAFFA bangaya makaba wllh d'azu ina tafiya akusa da gonar malam tanimu saiga AUDU ya d'akko itace daga gonarsa wai a lallai sai ta inda nakebi shima zaibi nikiwa nak'I kaucewa, shine yabi ta cikin gonar aikuwa ya fad'i yaketa salati BAFFA ingaya maka harji nayi yanacewa wai yakarye, saboda zabar dayaji"
Ta k'ashe maganar tana dariyar ta alamun babu abinda yadameta.
Dasauri BAFFA ya mik'e yana fad'in "SUBHANALLAHI"
Amma shine AISHA baki gayamin ba sai yanzu da daddare?"
"To BAFFFA mai zakayi masa innagaya maka, tunda naje gudansa nafad'a aishikenan ko"
Tana fad'ar haka tayi tafiyarta, shikuwa BAFFA k'am yak'ame awajen.
*_Ur's Hubbeeey._*
[04/08, 21:53] Hubbey Frd Ameena Kn: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
©®.
*21/7/2018.*
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITTEN BY✍🏻_*
*_HABEEBA IDREES_*
*_(Hubbeey)._*
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAA SAHLAH ILLA MAJA'ALTAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZ'NA IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*_KARKU MANTA DAI INDO K'AFAR YAWO🚶🏻♀ZAI DINGA ZUWA MUKUNE ARANEKUN ASABAR DA LAHADI INSHA ALLAH._*
*SAK'ON INDO ZUWA GAREKU*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*DOMIN FITAR DA KAUSHIN K'AFA KO FASO:-*
*KISAMU RUWAN ZAFI KIZUBA A BAHO SAI ZUBA BAKING POWDER COKALI 2 SAIKI SAKA K'AFARKI ACIKI TASAMU KAMAR MINTI 15 SAN NAN KI FARA GOGE TA DA ABIN GOGE KAUSHI IDAN KIN GAMA SAIKI SHAFA MAN KA'DANYA.*
*_page 3⃣._*
Tunda gari ya waye BAFFA yagama shirinsa don zuwa duba AUDU a gidan sa, INDO ce ta tareshi a k'ofar soro bayan ta gaida shi.....
"BAFFA zaka fita baka bani kud'in takalmin ba"
"Haba AISHATU yanzu harkin manta yadda mukayi dake jiya, yanzu hakafa gidan AUDU zanje indubashi sai kuma inwuce kasuwa kuma ina shiga kasuwar takalmin zanfara saya miki kafin ink'ara rumfa ta karki damu insha Allahu yau zan sayo miki kinji"?
"To shikenan BAFFA Allah ya kiyaye hanya"
"Yawwa AISHATU maza jeki kirawo min GOGGOn ki"
Da gudu tanufi d'akin GOGGO amma koda tashiga tsalle tayi ta haye gado abinta ta kwanta bata sanarwa da GOGGOn sak'on BAFFAn ba, itakam GOGGO kawai kallon INDO takeyi tana jiran taji tasanar mata da sak'on BAFFA saboda duk tana jin yadda sukayi amma ta ji shiru, ganin bata da niyyar gaya matane kuma tasan BAFFAN yana chaan yana jiranta yasata mik'e ta je wajenshi......
"Ahh modibo harka fito?"
GOGGO ta tambayi BAFFA wanda ke tsaye yana jiranta..
"Ehhh na fito zanje gidan AUDU ne induba shi daga nan kuma sai inwuce kasuwa"
"Allah sarki bashida lafiya ne?"
"Ehh jiyane yadawo daga gona ya d'akko itace sai yafad'i yasamu karyewa a k'afa"
"subhanallahi Allah yabashi lafiya amma bansaniba"
"Ehh nima sai da daddare indo take gayamin da yake wai agabanta yafad'i ita tazo gidansa ma tafad'a, kema inkin gama abinda kike sai kuje da INDO kudubashi, to nizan tafi Ga INDO nan dan Allah Kici gaba da hak'uri da halayen ta Insha Allahu wata rana sai labari kinji?"
Tuni idon GOGGO ya ciko da hawaye lokuta da dama haka modibo yake cemata wataran sai labari amma itakam takasa ganin wan nan lokacin da za'ayi labarin saboda gashidai INDO kullum girma take kuma YAWON ta k'aruwa yakeyi....
Ganin tayi nisa cikin tunanintane yasa BAFFA yayi ficewar sa yabarta anan tsaye saboda inda sabo yasaba da halin GOGGO na tunanin, kamar yadda itama ta saba danasa halin, Kuma duk tunanin nasu akan INDO ne.......
A soro yasamu AUDU inda aka kwantar dashi, bayan sun gaisane BAFFFA yake tambayar AUDU yadda tsautsayin yasameshi, murmushi kawai AUDU yayi yace "abar maganar kawai Allah yakiyaye gaba kuma ALLAH yashirya mana zuri'a"
BAFFA kam yakasa gane wan nan kalma ta AUDU....
Amin kad'ai BAFFA ya iya furtawa san nan sukayi sallama akan zaije kasuwa amma inyadawo da yamma zai dawo yasake dubashi....
Malam AUDU mutum ne mai matuk'ar hak'uri, dan ko natar shi yak'i gayawa yadda akayi yafad'i har yasamu karaya, yaranshi kuwa duk sunyi iya tambayarsu amma furr yak'i gaya masu kawai sai yace "DAGA ALLAH NE" saboda yasan idan yagaya masu abin bazaiyi kyauba.........
Rana tayi jama'a duk suntafi kasuwa garin yayi shiruuuu, GOGGO ta shirya zata shiga gidan AUDU domin ta duba shi, A soro taci karo da INDO anan tasanar mata da cewar BAFFA yace suje su duba AUDU...
"Kije GOGGO gani nan yanzu zanbiyoki"
GOGGO kuwa bata amsa mataba haka ta fice tayi tafiyarta ita kad'ai, fitar GOGGO kedawuya
wani yaron mak'otansu yashigo an aikoshi wajen BAFFA...
"INDO BAFFAn ki yanan"?
Inji yaron da yashigo gidan wanda ko sallama baiyiba......
"Kai wanne irin gidahumine?, zaka shigo gida ko sallama babu, kuma mai zakayiwa BAFFA na da kake nemansa?"
INDO ta fad'a tana masifa tareda matsowa kusa da yaron kamar zata dakeshi, shikuwa sai jaaaa dabaya yakeyi saboda yasan halinta yanzu saitayi masa duuuka, cikin in'ina yaron yafara magana...
"Innnn innnnn daman innar muce tace idan BAFFAN ki zaije kasuwa ga kud'i yasayo mata gero kwano uku"
Ya fad'a yana mik'owa INDO kud'in, aikuwa da sauri ta karba...
"Kaje kace BAFFA yatafi kasuwa amma nizanje kasuwar anjima zan siyo mata, maza kayi sauri katafi gida kace zankawo mata innadawo"
Badan ransa yaso ba haka yaron yabata kud'in saboda innar shi ta.gargad'eshi da cewar in har BAFFA baya nan to yadawo mata da kud'inta, yaron yana fita INDO ta wanke fuskarta ta lafka mai a k'afarta tazari takalmin GOGGO ta nufi kasuwa..........
Tafiya ce mai tsayi tsakanin garin tsiiko da kasuwar larabar zango dake k'aramar hukumar ajingi cikin garin kano, amma hakan bai hana INDO mik'a k'afafunta tayi wan nan tafiyarba dan ganin taje wan nan BABBAR KASUWA dan cika burinta, duk da dai akwai masu tafiya a k'afarsu amma duk cikinsu Babu mai k'ank'anta kamar INDO, dan haka duk duk inda tabi kawai kallonta akeyi musamman takalmin dake k'afarta yafi komai jaan hankalin jama'a, itakam ko ajikin ta tafiyar ta take abinta lokaci² kuma tana duba kud'in da taci d'amara dasu a k'ugunta..........
Layi² takebi cikin kasuwar idan taga d'an garinsu saita yashe baki alamar taganeshi haka tayi taci gaba da kutsakai cikin kasuwar har Allah yakaita layin 'yan takalma duk takalman wajen na roba ne akwai silifas akwai sau ciki, babu magana kawai INDO ta fara iban takalmi nan fa tashiga gwada takalma tasaka wan nan ta cire wanchen, shikuwa mai takalmi ya zuba mata ido shi duk atunanin shi bata da hankali saboda sunsaba had'uwa da yara masu tabin hankali suna yawo a kasuwar, duk takalimin da INDO ta gwada baiyi mataba saita mayar ta ajiye shikuwa mai sayar da takalmin sai ya d'akko ya goge saboda duk wanda ta gwada saita shafa masa k'asa da maik'on mai wanda ta lafkowa k'afarta, hakadai tayi ta gwadawa harta samu wanda sukayi mata guda hud'u ta d'iba, biyu sau ciki(fillo toms) biyu kuma silipas nan tashiga k'ok'arin kunto kud'in da ta d'aure a k'ugunta gaba d'aya ta mik' masa kud'in bayan yaduba ne yaga tana da ragowar chanji ya bata chanjinta yasaka mata takalman aleda, anan tabaro takalmin GOGGO wanda tasako, ta d'auki d'aya daga cikin sabon da ta saya tasa ka ak'afar ta, daga wajen mai takalma INDO ba ta sake zuwa ko inaba saita nufi hanyar gida itakam buk'atar ta tagama biya burinta yacika..........
Sai bayan ta 'bace daga wajen san nan mai takalmin ya lura da ta bar takalmin datazo dashi ak'afarta sai ya d'iba ya ajiye mata wai kozata tuna ta dawo.........
Tunda GOGGO tadawo take neman INDO amma shiruu babu labarin inda ta tafi, abinda yafi Tsorata GOGGO shine tadda taga babu takalman ta dake k'ofar d'aki lallai hakan yanuna mata cewar INDO nisa tayi dan indai harba cikin gari INDO zata bariba babu abinda zaisa ta tasaka yakalmi a k'afarta, fatan GOGGO dai shine Allah yasa kar BAFFA yariga INDO dawowa saboda tasan lallai zaifita shiga damuwa......
Sai bayan da aka idar da sallah la'asar san nan INDO tashigo gidan su koda tashi bata samu kowaba, dan haka ta nufi d'akin BAFFA anan ta 'boye takalman da ta sayo san nan ta rufo masa d'akin tashiga gari....
Tuni GOGGO tashiga neman INDO gida-gida duk inda GOGGO taje sai ace INDO batazo ba harta gaji ga yamma tayi ko tuwo bata d'ora ba haka ta hak'ura ta dawo gida.
*_Ur's Hubbeey._*
[04/08, 21:53] Hubbey Frd Ameena Kn: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*22/7/2018.*
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITTEN BY_*
*_HABEEBA IDREES_*
*_(Hubbeey)._*
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAA SAHLAH ILLA MAJA'AL TAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZNA IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*KARKU MANTA*
*🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO🚶🏻♀ZAI DINGA ZUWA MAKUNE ARANEKUN ASABAR DA LAHADI INSHA ALLAH.*
*SAK'ON INDO GAREKU*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*DOMIN RAGE TUMBI CIKIN SATI BIYU:-*
*1-BAKING POWDER*
*2-KHAL TUFFA*
*3-RUWAN ZAFI*
*YADDA ZAKI HA'DA*
*KIFARA ZUBA RUWAN KHAL TUFFA MURFI 'DAYA A CUP SAIKI KAWO BAKING POWDER TEA SPOON KISHARE SAMAN DA 'DAN YATSANKI KODA BAKIN GOGONIN SAIKI RABASHI 1/⁴ SAIKI ZUBA 'DAYA CIKIN WAN NAN KHAL TUFFA EN ZAKIGA YAYI KUMFA TSAMIN KHAAL TUFFA EN YAFITA KENAN TA YADDA HAR MAI OLCER ZATA IYA SHA, SAIKI ZUBA RUWAN 'DUMIN KI CIKA CUP EN 'DUMIN YAZAMA DAI² YADDA ZAKI IYASHA KAMAR TEA KISHA DA SAFE KAFIN KICI KOMAI SAI KISHA DA RANA BAYAN KINGAMA CIN ABINCI SAI KUMA KISHA DA DADDARE KAFIN KI KWANTA.*
*INSHA ALLAHU ZAKIGA YADDA TUMBINKI ZAI KOMA.*
*_page4⃣._*
Gaba d'aya hankalin GOGGO baya jikinta kawai dai tanayin aikinne kamar mara lafiya,
hakan nan ta d'ora murhu biyu na tuwo daban na miya dantayi saurin gamawa kafin BAFFA yadawo, har aka fara kiran sallah maghreb INDO bata shigo gida ba anan hankalin GOGGO ga k'ara tashi, tunanin ta d'aya kar BAFFA yace tayi watsi da AMANAR da yabata, Tana cikin wan nan tunani ne yaro yayi sallama bayan GOGGO ta amsane yaron yafara sanarwa da GOGGO sak'on innarsa.....
"Wai inji INNA tace idan BAFFAn INDO yadawo daga kasuwar wai yabata sak'on"
Cikin rashin fahimta GOGGO ke kallon yaron "itakam wanne sak'o ne?" GOGGO ta tambayi kanta cikin zuciyarta jin shiru ba ansa ne yasa ta tuna cewar azuciyarta take maganar, shikuwa yaron jira yake tabashi yatafi... "kace BAFFAN bai dawo ba inyadawo zangaya masa, kace ina gaida INNA mai koko kaji?"
Yaron ya amsa da "to" san nan yayi ficearsa, nan GOGGO ta tashi tayo alwala ta shiga d'aki.......
Da gudunta ta nufi inda mai machine d'in yasauke saurayin duk inda cikakken d'angayu yake to wan nan saurayin yakai awancen lokacin, rataye yake da wata jaka wadda daga gani kasan kayan sawarsane aciki saikuma wata Bagco a hannunsa, tana k'arasawa wajen yana gama sallamar mai machine d'in, kallonsa kawai INDO takeyi da Alamun wan nan saurayin yayi matuk'ar burge ta....
"Ai daga gani daga wani garin yake gashinan ya banbanta da jama'ar garin nan lallai dole inbishi gidansu kodan yabani labarin inda yaje kuma yagaya min nawa ake zuwa ALLAH dai yasa mata ma suna zuwa karyace min mazane kawai suke zuwa"....
yayin da INDO tayi nisa cikin tunanin ta batasan lokacin da wan nan saurayin ya d'auki kayansa yayi gaba ba sai farkawa tayi kawai taga baya wajen, zazzare ido tashigayi ganin babu kowa sai d'ai² kun mutane dake k'ok'arin shiga massalaci domin yin sallah, wani irin tsaki INDO taja kafinta wuce ta nufi gidansu.............
Da sallama ta tura kai cikin gidan alokacin GOGGO ta idar da sallah tana ta addu'a, kamar daga sama tajiyo muryar INDO a tsakar gida godiya tasakeyi ga Allah saboda jiyo sallamar INDO datayi, cikin sand'a kamar wadda za'a kama haka INDO ta shiga d'akin GOGGO takalminta ne rik'e a hannu tana k'ok'arin bud'e fantekar GOGGO zata ajiye aciki, dafarko GOGGO batayi niyyar yi mata maganaba saida taga INDO nashirin ruguzo mata da jeren d'akin akanta san nan tacewa wa INDO takawo takalmin ta ajiye mata, ba musu kuwa INDO ta mik'awa GOGGO takalmi mamakine yakama GOGGO sanda ta kalli sabon takalmin da INDO ta mik'o mata....
"INDO yaushe BAFFAn ki ya sayo maki takalmi?"
Nan fa INDO ta yashewa GOGGO baki da farin cikinta take magana....
"Wllh GOGGO d'azune bayan kintafi duubo malam AUDU sai inna mai koko ta aiko da kud'i wai BAFFA ya sayo mata gero akasuwa saboda ta rainamin BAFFA shi zata aika kasuwa? nikuwa nayi maganinta na kar'ba kud'in na tafi kasuwar nasayo takalma daman BAFFA yace zai sayo min to kinsan halin mantuwar BAFFA shine kawai na kar'ba kud'in naje BABBAR KASUWA nasayo harguda hud'u".....
Jin ta ambaci BABBAR KASUWA ne yasa GOGGO saurin sakin takalmin ak'asa sai alokacin ta tuna da yaron inna mai koko da yazo d'azu "INDO BABBAR KASUWA fa kikace, kedawa kukaje?"
GOGGO take tambayar INDO
"Lallai ma GOGGO nid'in sai da wani zan iya zuwa BABBAR KASUWAR?"
"HAZBUNALLAHU WANI'IMAL WAKEEL kai jama'a anya kuwa INDO k'alau kike? To nawane kud'in inna mai kokon?"
"Oho mata ni iya lissafinnayi? Naji dai yaron yace kwano uku za'a sayo mata geron, nikuma danaje wajen mai takalmin saina bashi kud'in gaba d'aya sai yabani chanji"....
Nan tsahiga laluben inda ta d'aure chanjin amma batasamu ba....
"To GOGGO kingama nazubar da chanjin da mai takalmin yabani, daman ke zankawo wa kozaki sayi wani abun"
INDO tafad'a tana turo baki kamar zatayi kuka.
"Haba INDO kin kashe su dai kawai"
"a'a wllh GOGGO ban kashe su ba kinsan bana kashe kud'i"
Dan dole GOGGO tayi shiruu saboda tasan tabbas INDO bata kashe kud'i ko kad'an barta dai da shegen yawo ko yunwa bata ji inhar tana yawonta, k'arkashin gado GOGGO tazuba takalman san nan tafito waje ruwan wanka ta had'awa INDO mai d'umi takai mata bayi, san nan tadawo d'aki "INDO tashi ga ruwan wanka chaan na had'a maki daganan sai kiyo alwala kiyi sallah"
Ba musu INDO tacire kayanta ta tafi wanka....
Kamar yadda BAFFA yayiwa malam AUDU alk'awarin zai dawo yadubashi haka kuwa yana dawowa daga kasuwa ko gida baijeba yabawa almajiri kayansa yakai masa gida shikuwa BAFFA yanufi gidan Malam AUDU, BAFFA ya jima awajen malam AUDU har bayan sallah isha san nan BAFFA yanufi gidansa........
Alokacin da BAFFA yashigo gida INDO kam tajima dayin bacci, har k'ofar d'akin GOGGO yazo yana kiran AISHAn sa sai GOGGO ce tace masa "tayi bacci" sosai BAFFA yayi mamaki Anya kuwal lafiyar INDO k'alao zatayi bacci yanzu? Kai saidai in tayi yawo tagaji gaskiya, duk azuciyar sa yake maganar bayan ya koma d'akinsa...
Sallamar GOGGO ne ya katse masa tunanin sa, saida ya amsa mata san nan ta ajiye tray d'in abincin da ta kawo masa.....
"GOGGOn AISHA yau kam mai kikayiwa AISHAn ki tayi bacci haka dawuri?"
Fuskarsa d'auke da fara's ake tambayar GOGGO....
Itakam GOGGO tarasa amsar dazata bashi, ko kad'an GOGGO batason abinda zaisaKa BAFFA cikin damuwa Amma bayadda ta'iya yazama dole tasanar dashi kodan ya gaggauta biyan inna mai koko kud'inta saboda bayyada zatayi ta biya mai koko kud'in kilama har zancen yadawo kunnen BAFFAn batare da ta biya mai kokonba, dan haka kawai ta yanke shawarar gayawa BAFFA komai....
"Ina magana kinyi shiruuu kodai AISHAn bata da lafiya ne"
"Hmmmmm a'a lafiyarta k''alau gajiya ce kawai take damunta dan yau har BABBAR KASUWA taje"...
Da sauri BAFFA ya tashi zaune yana mai² ta maganar da GOGGO tafad'a.
"BABBAR KASUWA fa kikace maitaje yi?"
Anan GOGGO ta kwashe yadda komai yafaru ta gayawa BAFFA...
Hawayen data gani yana sauka daga kan fuskarsa shiyafi komai tayar mata da hankali, matsowa tayi kusa dashi tana share masa....
"Dan ALLAH MODIBO kadenayi nata kuka, kukan ka agareta bashine zai shiryar da itaba addu'a ce mafita kawai"
"Ko kad'an ba AISHA nakewa kuka ba ina tunanin wanne laifi nayiwa Allah ne da yabani AISHA mai k'afar yawo"
"subhanallahi MODIBO bantabajin wan nan mummunan maganar daga bakinka ba kaifa musulmine kuma mai tawakkali dan Allah karka sake fad'ar haka".
*_Ur's Hubbeey._*
[04/08, 21:53] Hubbey Frd Ameena Kn: 🚶♀ *INDO K'AFAR YAWO*🚶♀
*TRUE LIFE STORY*
28/7/2018.
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITEEN BY_*
*_HABEEBA IDREES(Hubbeey)._*
_________________________
*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
_tσ gєt αccєѕѕ σf σur nσvєl'ѕ víα thíѕ línk tσ jσín σur fαcєвσσk grσup._
_____________________
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAASAHLA ILLAH MAJA'AL TAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZNA IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*SAK'ON INDO ZUWA GAREKU
FAN'S*
*DOMIN MAGANCE NANKARWA (STRECTH MARKS).*
Da farko dai shi Nankarwa wasu tabbai ne layilayi da suke fitowa mace a jiki musamman wacce ke dauke da ciki zuwa haihuwa Wanda idan anyi maganin sa da wuri wato daga fitowar sa zasu iya bacewa gaba daya amma barin shi ya dade kan hana sa bacewa gaba daye sai dai zai dushe ya zama dan kadan kadan ake iya gani
suna fitowa ne a wurare kamar haka :-
Cikin mace daga kasa (mara)
Cinya
Saman mama
Mazauni
Saman hannu ta wuraren hammata
Da sauran su.
*ME KE KAWO NANKARWA ?*
Akwai abubuwa da dama da suke sa nankarwa kamar:-
1-daukan ciki zuwa haihuwa (wannan shine babban abinda ke kawo nankarwa)
2-ramewa tashi daya (ga mutum mai qiba)
3-yin qiba tashi guda (ga mutum mai rama)
4- gado daga mahaifiya
5-jinya na tsawon lokaci
6- damuwa mai yawa da makamantar su
*MATAKAN NANKARWA*
Yana da matakai guda uku gasunan kamar haka:-
1) farko fitowar sa zaki gansu sirara yana da pink kala sannan yakan yi kaikayi wannan matakin bashi da wahalar magani
2) zai zama ja ko ruwan bula sannan girman su zai karu yanzun kam babu kaikayi sai lokaci zuwa lokaci zai iya bacewa ki ya ragu ya danganta da yanayin jikin mutum
3) zai zama fari ko ruwan silva wannan kam yana da matukar wahalan magani sai an jure shima din sai dai ya ragu ba wai ya bace baki daya ba.
*PAGE 5.*
Tun sanda Malam *AUDU* yasamu karyewa *INDO* ko sau d'aya bataje ta/dubashi ba,kullum idan Malam *AUDU* ya tuna hakan yana 'bacin rai saidai kuma yanayi mata uzirin k'uruciya da shirme dasuke tare da ita........
Kamar kullum yanda tasaba ficewar ta yawonta babu ruwan ta da cewar dare ne ko safiya itakam duk sanda yawonta yatashi kawai kama hanyarta take yi sai dai idan *GOGGO* ce ta kulle mata k'ofa shine za'a samu lafiya, dayawa mutanen garin suna danganta cewar *INDO* tana da Aljanu sune suke sakata wan nan shegen yawon.........
Yauma tasamu sa'a *GOGGO* bata rufe k'ofar ba dan haka tasamu damar fellawa da gudu daga d'akin *GOGGO,* *GOGGO* tana kwala mata kira amma inaaa zakara yabawa *INDO* sa'a, *GOGGO* tsayawa tayi kawai tana kallon k'ofar soro ta inda *INDO* ta felle addu'a tashiga yi mata cikin ranta kafinnan takama aikinta.....
Tana fita tanufi k'aramar kasuwar dake cikin garin nasu,babu mutane sosai a kasuwar saboda safiya ce dayawan mutane basu firfito ba amma hakan bai hana *INDO* samun wani itacen bishiyaba tayi zamanta tana kallon d'ai² kun mutanen da wuce domin sayen abinda zasuci.........
Daga nesa ta hangoshi cikin shigarsa ta burgewa,daganin sa kasan ba rayuwar garin k'auyen yasaba ba, cikin fara'a tanufi inda yake ta washe fararen hak'oranta tafara gaidashi, shima yasaki fuska sosai ya amsa tareda yi mata 'yan tambayoyi ciki harda tambayar waye babanta acikin garin?...
Bayan yagama jero mata nasa tambayoyin itama tashiga tambayarsa.
"Amma kai ba d'an garin nan bane ko?"
Saida yayi wani irin murmushi san nan yabata amsa...
"Ehh nazo gidan k'anin Abbana ne"
Yabata amsa cikin kulawa
"Aidama tun ranar da na ganka ka sauka a mahin nasan kai ba a nan garin kake ba"
Dariya yayi sosai an nan ya tambayeta...
"To mene da mutanen garin dazakice banyi kama da mutanen garin ba?"
"Hmmmm zangaya maka amma sai mun sake had'uwa, zan tafi ni sai anjima"
Bata jira amsar dazai bata ba kawai *INDO* tayi gaba abinta......
Sai da akafara kiran Sallah Azahar san nan *INDO* tashigo gida alokacin *GOGGO* tagama aikin cikin gidan duka, Abinci *GOGGO* ta d'akko wa *INDO* ta mik'a mata amma abin mamaki sai *INDO* tace ita ta k'oshi bazata ciba, *GOGGO* kam har cikin ranta bataji dad'i ba gashi zuciyarta tana sak'a mata abubuwa kala² ita kam bataso taga *INDO* tak'i cin abinci ko kad'an bata jin dad'in hakan.
" *INDO* mai yasa bazakici abin cin ba?"
" *GOGGO* sai anjima zanci yanzu kam bana jin yunwa"
Badan ran *GOGGO* yasoba haka ta hak'ura ta k'yale *INDO*, fitowa tayi taje ta kulle k'ofar gidan ta 'boye makullin.
*TUNA BAYA*
*WANENE MALAM MODIBO?*
*MALAM ABUBAKAR MODIBO* shine cikakken sunan Mahaifin *MALAM MODIBO* baban *INDO* wato *MODIBO* na yanzu, *BABAN MODIBO* cikakken bafulatani ne kuma sun kasance fulanin tashine basu zama ako ina sai jeji tareda dabbobinsu dasuka had'ar da shanu tumaki zabi da kaji *MALAM ABUBAKAR* shine sarkin rugar garin kuma babban Malmi ne wanda mutanen rugar suna ganin girmansa sosai duk rugar da suka zauna dazarar mutane sun fara cika wajen sai sukuma su tashi suk'ara shiga jeji suda jama'ar su, sun zauna a garuruwa da dama har Allah yakawo su cikin garin kano k'aramar hukumar *AJINGI* ananma ba'a waje d'aya suka zauna ba dan ko kad'an basu son rayuwa cikin jama'a dan haka ne suke yawan tashe² daga wan nan jejin sukoma wanchen...
*MALAM ABUBAKAR* ya jima Allah bai bashi haihuwa ba dan saida sukayi shekaru 15, shida matarsa *SAFIYYA* basu ta'ba haihuwa ba,duk inda *MALAM ABUBAKAR* yaji maganar magani sai yaje yanemo musu ahaka har Allah yasa suka dace tasamu ciki murna sosai awajen *MALAM garnets* tareda jama'ar sa, bayan watanni 10 ne Allah yasauki *SAFIYYA* lafiya tahaifi yaronta namiji ansaha bikin al'adun fulani a wancen lokacin yayin rad'awa yaro suna, *MALAM ABUBAKAR* ya rad'awa jariri suna *ABUBAKAR* wato ya maida sunan sa akan yaron kenan saboda haka sai ake kiran yaron da *MODIBO.*
Shekarun *MODIBO* k'arami goma sha bakwai (17) Allah yayiwa maifiyarsa rasuwa, alokacin saura kwanaki kad'an a d'aura masa aure da *AMINA* mahaifiyar *INDO* kenan.
*SAFIYYA* tagamu da jalinta yayin da *MALAM MODIBO* mijinta yakawo wani k'ato sa wanda babban abokinshi yabashi kiwo shikuma yakawo cikin gidan ya had'ashi da saura shanun dayake kiwo agidansa, tun ranar da aka kawo wan nan *SA* d'in hankalin SAFIYYA yakasa kwanciya dashi saboda yana da matuk'ar fad'a kuma a lokuta da dama idan *MODIBO* k'aramin bayanan itace take basu abinci, kamar kullum yauma *MODIBO* K'arami yauma yatafi kasuwa hakanne yasa *SAFIYYA* kaiwa shanun abinci har cikin garken su, shigarta keda wuya wan nan bak'on *SAN* yayo kanta gadan² kafin ta ankara ya soka mata k'ahon sa a cikinta atake tafad'i sumammamiya tanan wajen har Allah yayi ikonsa ta amsa kiran mahaliccinta babu wanda ya ankara da abinda ke faruwa...
Saida aka kusa yin sallah maghreb sannan *MODIBO* k'arami yadawo daga kasuwa d'akin *INNAR* sa Yanufa amma ga mamakin sa sai yaga batanan wanda a dai² wan nan lokacin yasaba samunta cikin d'akinta tanajira ayi sallah maghreb, fito wa yayi yafara nemanta inda aka kewaye dabbobin nan ya nufa yana zuwa cikaro da *INNA* sa a kwance zuwa lokacin ma tuni tafara sandarewa, fad'awa yayi kanta yana kuka yana salati..
mak'ocin sune yajiyo ihun MODIBO K'arami cikin garken shanun da sauri shima yashiga yana zuwa yaganewa idon sa gawar *iNNA SAFIYYA* kwance ahankali ya janye MODIBO daga jikin *INNA*, saida yak'ara duba ta sosai yatabbatar da cewar rai yayi halinsa san nan yakoma yasanar da sauran jama'a.
*ALLAH YA JIK'AN INNA SAIYYA KAKAR INDO.*
*_Ur's Hubbeey._*
[04/08, 21:54] Hubbey Frd Ameena Kn: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*TRUE LIFE STORY*
*1/8/2018.*
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITEEN BY_*
*_HABEEBA IDREES(Hubbeey)._*
_________________________
*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
_tσ gєt αccєѕѕ σf σur nσvєl'ѕ víα thíѕ línk tσ jσín σur fαcєвσσk grσup._
_____________________
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAA SAHLAH ILLA MAJA'AL TAHU SAHLAH WA'ANTA TAJ'ALUL JAZNA IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*WAN NAN PAGE EN NA RANAR LAHADI NE WANDA NAYI BANSAMU DAMAR YIBA KUMA NA 'DAUKI ALK'AWARIN ZANYI MUKU KAFIN NA RANAR ASABAR.*
*ALHAMDULILLAH*
*NAJI DA'DI DA ALLAH YABANI IKON CIKA WAN NAN ALK'AWARIN.*
*MUCH LOVE MY FANS*
*_Page6⃣._*
Kwanan INNA SAFIYYA arba'in da biyar(45) da rasuwa aka d'aurawa MODIBO K'ARAMI aure da kyakkyawar matarsa ASM'AU wadda agarin suke kiranta da MA'U, ASMA'U tana da matuk'ar kyau ga gashi anyi matuk'ar artabu tsakanin masu neman aurenta cikin su kuwa MODIBO baban INDO shine yayi nasara dasamunta a matsayin matar aurensa, bayan SHA'DI da akasha ayayin neman auren wanda awancen lokacin kowa yashaida tsawon shekaru a rugar tasu ba'a tabayin SHA'DI da gwagwarmaya kanneman aure ba sai akan MA'U wadda kowa yashaida tabbas MA'U mai kyauce..........
Ansha shagalin biki irinna al'adun fulanin asali nawancen lokacin Amarya da ango kowa cikin tsananin farin ciki, A Al'adar garin bayan angama biki ba alokacin amarya zata tare ba, saita tasamu kamar wajen wata biyu agida koma fiye da haka, hakama bayan ankaita sai anyita artabu da ita kafin ta zauna agidan mijin dan kusan kullum sai ta gudo gida komai nisan garinsu haka zata gudo sai bayan wasu kwanaki sai amaida ita ahaka harta tasaba da gidan mijin san nan ta zauna.....
To hakanne yakasance akan MA'U maman INDO amma itakam nata haryayi yawa dan harsai da aka had'a mata da rok'on Allah san nan akasamu tazauna a gidan MODIBO, duk nisan da ke tsakanin garin da Akakaita hakan baya hana MA'U guduwa wuyarta MA'U tasamu 'yan kud'inta tofa zata biya ta hau motar garinsu..........
Hakama idan tasauka daga motar wata muguwar tafiyar ce kafin akai ga dajin da rugar su MA'U take................
Soyayya da shak'uwa mai tsananin sun samu wajen zama a zuk'atan MODIBO da MA'U kullum kafin MODIBO yatafi kasuwa sai ya tabbatar da yagama komai na aikin cikin gidan kafin yafita, haka suke rayuwarsu gwanin ban sha'awa duk dacewar suna k'auye ne amma hakan bai hanasu yin soyyayarsu yadda suke soba.....
Yau kimanin shekaru goma shabiyu (12) kenan da auren MA'U da MODIBO amma har wan nan lokacin MA'U ko 'batan wata bata tabayiba hakan kuwa yana matukar damun MODIBO......
Haka itama MA'U abin yana damunta amma saboda tsananin kunya haka take daurewa bata nuna masa gashi duk sa'anin aurenta duk suna da "ya"ya..............
Wata rana bayan MODIBO yadawo daga sallah maghreb ne suna hira shida MA'U cikin jin dad'iq kawai sai MA'U takawo wa MODIBO magana akan cewar tanaso yak'ara aure, wan nan magana tayi matuk'ar 'batawa MODIBO rai kuma saida yanuna mata afili saboda ko kula ta baiyiba haka ya saka takalmin sa ya bar gidan.....
Sai chaaaan bayan sallah isha yadawo, baiko nemi inda takeba ya nufi d'akinsa yayi kwanciyarsa...
itakam MA'U tarasa inda zata saka kanta dan ko kad'an bataso taga mijinta cikin 'bacin rai ballema ace ita ta haddasa masa, amma ita aganinta idan MODIBO yak'a aure ai zasu samu farin ciki idan amaryar ta haihu, dan haka ta tsaya akan cewar saitayi yadda tayi dan ganin yak'ara auren......
Juyi kawai MODIBO yakeyi yakasa bacci, ganin baccin ya gagareshi ne ya tashi yanufi d'akin MA'U, ga mamakinsa itama sai yasameta a zaune takasa baccin sai tunani takeyi, kusada ita yazauna.......
"Haba ASMA'U gaskiya banji dadin maganarki da kika yi minba d'azu, yanzu ASMA'U kina tunanin akan bamu samu haihuwaba zan k'ara aure?, sam hakan bazai yiwuba muyita hak'uri har mujira lokacin da Allah zai yanke mana dan Allah kicire damuwa daga ranki kinji?"
Tunda yafara magana MA'U batace komai ba kuma bata d'ago kanta ta kalleshi ba, hannunsa yasaka a fuskarta ya d'ago kanta, hawayen da yagani suna sauka daga idanunta sunyi matuk'ar tayar masa da hankali, da sauri ya jawota jikinshi cikin tashin hankali yake tambayarta MENE DALILIN HAWAYENTA? shiru tayi takasa bashi ansa, shima shiruuu yayi da tambayar ta haka yayita rarrashinta har bacci mai nauyi yayi gaba da ita, sai da ya tabbatar tayi nisa cikin barcin ta san nan yatashi, Alwala yayi yazo yafara jero sallolin nafila kamar yadda yasaba yi duk dare...........
Haka rayuwar MA'U da MODIBO tacigaba da tafiya kuma harzuwa wan nan lokacin MA'U tana kan bakarta kullun cikin rokon MODIBO take akan yak'ara aure amma fuurrrr yak'i Amincewa da buk'atar ta..........
Yau Laraba MODIBO yagama shirinshi tsaf dan tafiya kasuwa k'ofar d'akin MA'U yazo danyi mata sallama kallo d'aya yayi mata yaji gabansa yayi wani mummunan fad'uwa, anan yadafa k'ofa yanata ambaton sunayen Allah cikin ikon Allah kuwa atake yasamu sassaucin bugun zuciyar tasa, itakam MA'U kawai kallonsa take dan tasan abinda tagama shirya masa, Sallama yayi mata itakuma tayi masa fatan dawowa lafiya tareda addu'a, jikinsa babu kwari haka yafito yakama hanyar kasuwa......
Saida ta tabbatar dacewar tsawon lokacin da MODIBO yafita ya isa yakaishi kasuwa, san nan ta mik'e tashiga had'a kayanta bata d'auki wani lokaci ba tagama had'a kayanta a kanta ta d'ora faggon kayan wanda ta d'auresu a acikin wani tsohon d'ankwalin ta, mak'otan ta tashiga a soron gidan ta ajiye kayanta tashiga cikin gidan, sak'o ta bayar na kuubar data makulle gidan, cewar idan sunji motsin MODIBO shibashi, matar gidan taso ta tambayi MA'U inda zataje amma ganin yadda tale saurine yasa tafasa tambayar ta.........
Ta bayan gari MA'U ta d'auki hanya sai faman sauri takeyi, tafiya ce mai matuk'ar nisa kafin tasamu ta futo babban titin dake garin AJINGI cikin nasara tasamu mota kasancewar ranar kasuwar LARABAR ZANGO keci ba'ayin wahalar mota.
*_Ur's Hubbeey._*
[04/08, 21:54] Hubbey Frd Ameena Kn: *🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*TRUE LIFE STORY*
*4/8/2018.*
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITEEN BY_*
*_HABEEBA IDREES(Hubbeey)._*
_________________________
*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
_tσ gєt αccєѕѕ σf σur nσvєl'ѕ víα thíѕ línk tσ jσín σur fαcєвσσk grσup._
_____________________
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LAA SAHLAH ILLA MAJA'ALTAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZNAH IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*BRR ALEEYAH*
*NA*
*AUFANA*
*HAK'IK'A INA MAI MATUK'AR TAYAKI MURNAN KAMMALA WAN BAN SHAHARARREN NOVEL NAKI MAI 'DAUKE DA ILMANTARWA,FA'DAKARWA TAREDA NISHA'DANTARWA ALLAH YAK'ARA 'DAUKAKA DA BASEERA.*
*SAK'ON INDO ZUWA GAREKU FANS.*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*AMFANIN LALLE GA MATA*
Lalle dai da farko wani sinadari ne mai dauke da alfanu iri iri, kuma addini ya kwadaitar da mata su yi lalle akwai sirrika acikin sa.
Nafarko dai lalle Kariya ce daga sihiri, Kariya ce daga aljanu sannan kuma Kariya ce daga cututtuka da dama, yin lalle a kafa na zuqe cutar dake kafan sannan yana kula da dumin mace, bi ma ana yana kiyaye. ni imar mace ba tare da ya gushe ba, innace lalle wasu zasu dauka zanen henna nake nufi ko, to lalle dai na gargajiya wanda muka rabu da yinsa yanzu shi nake magana akai:
Ga kuma sadaqa ga duk mai infection ta tafasa lalle inyadan huce sai ki dinga zama a ciki na sati biyu, in Allah yayarda za ki warke.
: Saboda maganin da lalle keyi ma akan iya shan ruwan lalle cokali daya don wankin dattin ciki amma banda masu ciki, to yanzu dai zamu dauki bangare daya daga cikin amfanin lalle muyi magana akai, wato shine amfanin lalle da kuma yanda ake amfani da shi don gyaran Fata.
Lalle dai ba karamin tasiri yake dashi wajen gyara fata ba, domin shi natural toner ne ba bleaching yake ba amma yanasa haske mai kyau kuma yana goge dattin fata, in kina son gyara fuska tai kyalli, laushi da haske to ki kwaba lalle da ruwan Kwai amma banda kwaiduwar kwan ki kwaba ruwa ruwa amma ba sosai ba ki lizimci shafa shi kullum minti talatin kafin wanka, za ki sha mamaki in sha Allah:
Ga masu son hasken fata, ki kwaba lalle da ruwa, ki shafe a jikinki inya bushe ki dirje da man zaitun zakiga canji.
sannan gamai son kamshin fata
: Ki kwaba lalle da turaren ki mai kyau na ruwa wanda ake durawa ki zuba isasshen ruwa a bucket ki sa garin lalle ya jika yay já zir sai ki tsiyaye ruwan ki diga turaren ki mai kamshi ciki Bayan kinyi wankan sabulun ki sai ki dauraye jikinki dashi inkin lizimci haka to bake ba rabo da kamshin jiki in sha Allahu.
: Sannan ga gyaran duka jiki kuma zaki hada lalle da sabulun salo da Zuma kina wanka dasu duk zakiga canjin fata in sha Allah
Sannan ga Amare kuma
Kafin kiyi dilke na aurenki
: fata zatayi laushi, haske da kuma santsi.
Ki samu lalle mai kyau ki kwaba da turaren ki mai maiko, turaren gargajiya mai mai dinnan to ki jika kamar botiki ba ruwa ruwa sosai ba Kamar dai kunu, kullum sai ki shafe jikinki da hadin lallen nan duka jikin ki, sãi kizo ki saka turaren wuta a kasko ko burner ki rufu akai ki turara jikinki hayakin turaren nan ya shiga sosai sai ki fita kije kiyi wankan ki zakiga canji.
Daga karshe kuma ga masu fama da pimples, sai ki hada lemon tsami da lalle kwabi mai dan tauri amma ba sosai ba kina shafa wa a fuskaar ki, kuraje zasu mutu sannan tabo bazai zauna ba ga hasken fuska da laushi.
*_Page 7⃣._*
Kafin La'asar MA'U ta isa cikin rugar su bata zarce ko inaba sai cikin gidan iyayenta, INNAr MA'U tayi matuk'ar razana da ganin MA'U dan ita atunaninta MA'U gudowa tayi wanda tad'e batayiba, fuskar INNA ba yabo ba fallasa haka ta karbi MA'U, abinci da ruwa ta kawo mata san nan ta fara tambayar ta dalilin zuwanta, nan MA'U ta gayawa INNArta duk abinda yafaru bata 'boye komai ba, anan tasamu damar rok'onsu INNA akan su taimaka mata susaka baki acikin maganar AUREN dan itakam tana matuk'arson taga yaro/yarinya agidansu kodakuwa ba ita ta haifaba....
INNA dai shiruuu tayi tana ta tunani akan maganar MA'U takasa cewa komai..........
Sai dab da sallah maghreb MODIBO yak'araso cikin garin.......
Daga nesa yaron yagano MODIBO dan haka yakoma gida da gudu yana gayawa Umman sa cewar ga MODIBO chan yadawo, tashi tayi ta d'akko makullin da MA'U takawo ajiya tabawa yaron, da gudu yasake futowa yanufi MODIBO dake dab da k'ofar gidansa, "BABA MODIBO ga makullin gidan" cikin mamaki MODIBO ya kalli yaron yace
"waye yabaka yace ka kawo min"
"ai tunda safe ne MA'U takawo tace in UMMAna taji motsinka abaka"
Hannu yasa ya karbi makullin...
"To nagode maza ka tafi gida"
Da "to" yaron ya amsa san nan ya fellah da gudu abinsa....
Jikinsa a sanyaye yasa Makullin ya bud'e gidan san nan yashiga da sauran kayansa daya sayo a kasuwa,haka yayi alwala yanufi masallachi domin yin sallah maghreb.......
Bayan sallah maghreb ne BABAN MA'U ya shigo gida shima yayi mamakin ganin MA'U amma ko kad'an bai bayyana musu afiliba, bayan yagama cin abinci ne INNA ta shaida masa dalilin zuwan MA'U kamar yadda MA'U ta gaya mata....
"To kingadai kece mahaifiyar ta kuma ke kikasan halayen mata fiye da ni yanzu yaya kike ganin zamuyiwa MODIBO?"
BABAN Ma'u keyin maganar alokacin da INNA tagama gaya masa buk'atar MA'U.
"Hakane amma ina ganin kawai mukirawo MODIBO muyi magana dashi idan mukaji ta bakinsa sai kuma musan abinyi agaba, amma zamu nunawa MODIBO cewar yak'ara auren tunda dai ita tasakashi kaga komene yafaru ita tajawowa kanta ko?"
Inji INNAr MA'U kenan
"Shikenan in ALLAH yakaimu gobe da sassafe zan aika Akirawo MODIBO sai muyi maganar"
"to Allah yakaimu"
INNA ta amsa masa......
Washegari da sassafe saiga MODIBO ya sauka a babbar rugar tasu, kowa yayi mamakin ganinsa da wan nan farar safiyar babban abin mamakin wajen mutane shine tayaya MODIBO yasamu mota da wan nan safiyar?
Shikuwa tunda yasa kansa zai zo bai jira wata mota ba kawai hayar machine yad'akko tundaga garin dayake yakawoshi har cikin rugarsu......
kamar yadda MA'U ta zarce gudan iyayenta a jiya da sauka rugar, haka shima MODIBO kai tsaye gidan BAFFANsa yanufa.........
A k'asan bishiya ya hango BAFFANsa inda yasaba zama kullim domin kar'bar k'orafin al'ummar rugar kasancewarsa sarkin rugar garin kuma babban malami......
Tun daga nesa BAFFA yake k'arewa MODIBO kallo tareda gano damuwa k'arara akan fuskarsa, MODIBO yayi sa'a babu wasu mutane a majalissar mahaifinnasa dan haka yaji dad'in ganin BAFFANsa, bayan sun gaisane MODIBO yagayawa BAFFA abinda yagani jiya na rashin ganin MA'U agidan bayan yadawo daga kasuwa.....
Sai da BAFFA yayi shiruuu na d'an wani lokaci kafin yafara magana irintasu ta manya....
"Ehhh ni tunjiya labari ya isheni cewar anga MA'U tazo, amma saboda nasan bata zuwa ita kad'ai sai nayi tsammanin ko kana hanya kaima to amma sainaji shiruu bakaxoba harna tashi daga fada......."
Shiruuuuu BAFFA yasakeyi tsawon wani lokaci kamar mai wani tunani san nan yaci gaba.......
"To inaso kagayamin maikayi mata da har yasata tawo gida batare da kasani ba?"
Nanma yayi shiruuu yana jiran yaji daga bakin MODIBO....
"A gaskiya BAFFA nidai a jiya da shekaranjiya nikam bamu samu wani sa'bani da MA'U ba"....
Anan MODIBO yayi shiru
"A'a MODIBO basai a jiya da shekaranjiya ba koda acikin wan nan shekararne indai kasan kun samu wani sabani kagayamin, dan kasan su mata wani lokacin abu baya wucewa awajensu, kokuma dakayi wani laifin sai su tuno da wancen da wuce, dan haka yanzu katashi kashiga cikin gida abaka abinci ka karya san nan kayi tunani akai sai kazo mu k'ara maganar ko"
Bai musawa BAFFA ba haka yatashi zuciyarsa cike da tunani kala², a tsakar gida yasamu GOGGO wato matar mahaifinsa, hannu biyu ta karbeshi nan takawo masa abinci suka gaisa tareda tambayar sa iyali, sosai MODIBO yayi sa'ar matar mahaifi domin kuwa inbaka saniba zakayi tunanin GOGGO ce ta haifi MODIBO haka shima yanayi mata biyayya dai² iyawarsa.
*_Ur's Hubbeey._*
*🚶🏻♀INDO K'AFAR YAWO*🚶🏻♀
*TRUE LIFE STORY*
*11/8/2018.*
*_STORY BY_*
*_AISHA MODIBO_*
*_(Indo k'afar yawo)._*
*_WRITEEN BY_*
*_HABEEBA IDREES(Hubbeey)._*
_________________________
*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
_tσ gєt αccєѕѕ σf σur nσvєl'ѕ víα thíѕ línk tσ jσín σur fαcєвσσk grσup._
_____________________
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.*
*ALLAHUMMA LASAHLAH ILLA MAJA'AL TAHU SAHLAH, WA'ANTA TAJ'ALUL HAZNAH IZA SHI'ITA SAHLAH.*
*KAMAR YADDA KUKA SANI WAN NAN NOVEL NA INDO K'AFAR YAWO YANA ZUWA MUKUNE AKOWANNE RANEKUN ASABAR DA LAHADI NA KOWANNE SATI DAN HAKA AWAN NAN SATIN,*
*INA MAI FARIN CIKIN SANAR DA MASOYANA CEWAR GOBE LAHADI SHA BIYU GA WATA AUGUSTA,(AUGUST) SHINE RANAR HAIHUWA TA YAZAGAYO, (MY BIRTHDAY) WANI ABIN DA'DINMA HAR DAY 'DIN DAI² YAZO RANAR SUNDAY.*
*DAN HAKA BA LALLAI GOBE INSAMU YIN TYPING EN WAN NAN NOVEL BA, AMMA INHAR NAGA DA HALI ZANIYI INSHA ALLAH.*
*SAK'ON INDO ZUWA GAREKU FANS.*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*HANYOYIN DA ZAKI GYARA FATARKI CIKIN SAUK'I.*
Babu wata mace da ba ta so a ce fatarta tana sheki da yalki; babu kuma macen da take so a ce fatarta ba ta da kyau ko daukar hankali. Hakan ya sanya mata da yawa ke kashe makudan kudade wajen lura da fatar jikinsu ko ta fuska. Da yawa daga cikin mata kuma sun fada tasku sakamakon amfanin da mayukan da suke da sinadarai, wanda a maimakon kwalliya ta biya kudin sabulu sai su buge da da-na-sani. Wannan dalili ya sanya na taho miki da hanyoyin 6 da za ki bi wajen lura da fatarki ba tare da tararradin ko fatarki za ta gamu da wata matsala ba. Ga hanyoyin kamar haka:
1. Ki samu kukumba sai ki yayyanka ta, daga nan sai ki nika ta, sannan ki ajiye ta gefe guda. Hada ruwan Rose Water da ruwan lemon tsami ko jus din lemon tsami. Bayan nan sai ki hada su waje guda da kukumbar, sai gauraya sosai. Bayan kin yi haka sai ki shafa a fuskarki ko sauran fatar jikinki, sannan ki kwanta har zuwa wayewar gari. A lokacin da kika zo wankewa, sai ki samu ruwa mai dumi. Hakan zai kara wa fatarki lafiya da kuma sheki.
2. Hanya ta biyu ita ce, ki samu madarar shanu wacce ba a dafa ba, sai ki samu gishiri da kuma cokali biyu na ruwan lemon tsami ko ruwan jus din lemon tsami, sannan ki gauraya sosai. Bayan nan sai ki samu auduga ko tsumma mai tsabta sannan ki rika dongala kina gogawa a jikinki ko a fuskarki. Bayan nan, sai ki wanke jikinki ko fuskarki da ruwa mai dumi. Hakan zai cire miki dukkan dattin da ke makale a kofofin fatarki.
3. Hanya ta uku ita ce, ki gauraya ruwan Rose Water da kuma ruwan lemon tsami. Ki shafa a fuskarki ko jikinki. Yin hakan zai cire tabon da yake fata ko fuska, sannan yin hakan zai sanya fata ta yi laushi da danshi.
4. Ki samu lemon zaki sai ki yayyanka, daga nan sai ki markada. Bayan nan sai ki shafa a fuska ko a jikinki. Wannan zai sanya miki laushin fata.
5. Ki samu karas sai ki markada, daga nan sai ki shafa a fuskarki ko jikinki. Bayan awa biyu sai ki wanke da ruwa mai dumi. Yin hakan zai sanya jikinki ya rika haske da kuma daukar hankalin duk wanda ya kalle ki.
6. Ki samu kurkum sai ki daka, daga nan sai ki hada da dakakkiyar alkama, sannan ki hada da man zaitun. Daga nan sai ki shafa a fuskarki ko a jikinki. Bayan awa biyu ko uku sai ki wanke fuskarki ko jikinki da ruwa mai dumi. Hakan yana cire kwayoyin cutar da ke makale a kofofin fata.
Yadda Za Ki Yi Amfani Da Kurkum Wajen Gyara Fatarki
Kurkum na dauke da sinadarai da dama kamar su, bitamin B6 da bitamin C da sauransu. Kuma yana rike fata yadda ba za a sami rauni . Yawan amfani da hadin kurkum na sanya fata musamman ta fuska laushi da santsi da kuma haske. Don haka, ya kamata kada a manta da wannan kurkum idan an zo kwalliya. ta zama sakakkiya ba. Amfani da kurkum na sanya sabuwar fata fitowa da wuri a inda tsohuwar tAmina Abdullahi
•A sami garin kurkum da zuma cokali daya da ruwan lemon tsami kwatan kofi. A kwaba su sosai har sai sun yi laushi. Sannan a shafa a fatar fuska a bari ya jima na mintuna 15 sannan a wanke da ruwan dumi. Yin wannan hadin na hana kurajen fuska fesowa. Za a iya yin wannan hadin kamar sau daya ko biyu a sati domin samin ingantaccen sakamako.
•Amfani da kurkum na rage gautsin fuska. A kwaba kurkum da nono ko kindirmo. Sannan a wanke fuska kafin a shafa hadin a fuska. A jira na tsawon mintuna 10-15 kafin a wanke. Za a iya jarraba wannan hadin a kullum bayan an yi wanka.
•Idan ke mai yawan aiki a karkashin rana ce, ya kamata ki samu kurkum kadan da kindirmo mai yawa sai ki rika shafa wa a inda kunan rana ta bata fuska. kunan rana na sanya fuska ta zama kamar mai shafe-shafe don haka wannan hadin zai magance wadannan matsalolin.
•Ko kun san cewa kurkum na magance bakar fatar karkashin hammata? To! A sami zuma kamar cokali daya sai a hada da ruwan lemon tsami kamar cokula 3-4 sai a zuba garin kurkum kadan sannan a kwaba a shafa a karkashin hammata a bari ya jima na tsakwon mintuna 10-15 kamin a wanke.
*_page 8⃣._*
MODIBO Yana cikin cin abinci ne yake tuna abinda yafaru tsakaninsa da MA'U a sati d'aya daya wuce take ya ajiye abincin yafara tunanin ta yadda zai sanar da BAFFAN sa, HAJJO matar mahaifin MADOBI ta lura sarai da yadda MODIBO yashiga damuwa alokaci guda taga ya mik'e ya futa daga gidan.....
Sai Bayan sallah azahar san nan MODIBO suka samu zama da BAFFANsa, Tun kafin BAFFAN yafara magana tuni MODIBO yafara gaya masa yadda sukayi shida MA'U, shiruuuu BAFFAN yayi na d'an wani lokaci.......
"Yan MODIBO wan nan shine dalilin dayasa MA'U zatayo yaji akan kak'i k'ara aure?"
"Wllh nidai BAFFA iyakachin abinda nasani kenan, saida ko akirawo ta muji abinda zatace"
Kan MODIBO ak'asa yake Bawa BAFFAN sa amsae tambayarsa.....
"Ehhh gaskiya ne daman dole insa akirawo ta inzauna daku tare"
BAFFA ne kenyin maganan yana mai kallon MODIBO.....
Nan suka saka wata hirar, sai bayan sallah La'asar san nan BAFFA yasa aka kirawo MA'U, wan nan zaman shikuma acikin d'akin BAFFA akayishi.......
Kanta ak'asa takasa had'a ido da MODIBO ballantana BAFFA, tsawon wani lokaci babu wanda ya iya cewa komai, ganin shirunyayi yawane BAFFA yafara tambayar MA'U meke faruwa saida BAFFA ya maiamaita mata tambayar sau biyu, san nan tafara bashi amsa cikin tsananin jin kunya, ta kwashe yadda sukayi ita da MODIBO bata boye komaiba har zuwa tawo warta gida, yadda MODIBO yafad'awa BAFFA komai haka itama MA'U ta fad'a dan haka BAFFA yaji dad'in sosai babu wani bata lokaci ya yanke musu hukunci akan cewar dole MODIBO yayi aure kamar yadda MA'U take so......
MODIBO bayadda ya iya haka ya karbi maganan auren dan bazai ta'bayin musu da maganar mahaifinsaba, haka zaman yatashi MA'U tana cikin farin ciki, shikuwa MODIBO kawai yak'e yakeyi wan da hausawa suke cewa "yafi kuka ciwo".........
Washegari da wuri MA'U da MODIBO suka gama shirinsu tsaf na komawa garin su, HAJJO ta had'amusu kayan tsara ba, haka itama INNAR MA'U tayi musu tara ta arziki......
Da wuri suka sauka agarin su tunda suka tawo babu wanda yayiwa kowa magana haka har suka shiga gida itakam MA'U batada wata damuwa tunda burinta yacika dan haka kome MODIBO zaiyi babu ruwanta........
Da daddare bayan MODIBO yadawo daga sallah ne yasamu MA'U ad'akinta, alokacin ta idar da sallah tanata addu'a, saida yabari ta idar san nan tara mata magana....
"MA'U burinki ya cika mahaifina yace ink'a aure, amma sanin kankine banida wata mace da nikeso bayanke ko? Dan haka aiki yarage naki saikinemo wacce kike so ku zauna da ita nikam babu abinda yadameni inkinnemo zanyi aure kuma duk abinda yabiyo baya karkiyi kuka da ABUBAKAR MODIBO danke kika jawowa kanki, BAFFA yabani wata 2 inyi aure dan haka nikuma nabaki sati 2 kinemomin matar dazan aura"
Yana gama fad'ar haka baijira jin amsar dazata bashiba yayi ficewar sa daga d'akin, Nan MA'U tashiga funanin wadda zata nemowa MODIBO amatsayin AMARYAR sa........
Bayan kwana uku (3) MODIBO yatashi gina wasu sababbin d'akuna acikin babban gidansa, 'Dakuna yayi manya guda uku. Akayi masu rufin kwano, wanda a cikin garinsu MODIBO ne mutum na farko daya farayin rufin kwano alokacin ansha zuwa kallon gidan MODIBO saboda kyawun gidan, daga wan nan lokacin wasu suke kiran MODIBO da MAI DIGAN KWANO.
Wata yarinya BINTA mai kawo wa MA'U tallan kayan miya, itace MA'U ta fitarwa MODIBO amatsayin wadda zai aura, BINTA yarinya ce mai hankali ga nutsuwa kuma tanayin karatun boko da islamiyya saidai kuma su BINTA suna cikin tsananin talauci saboda hakanema duk wanda suka fito neman auren BINTA sai su fasa saboda yadda za'ayita d'aga auren saboda babu yadda za'ayi asaya mata kayan d'aki, dan haka MA'U take tsansnin tausayawa rayuwar BINTA da mahaifiyarta da k'annenta guda 2, wan da magaifinsu ya jima da rasuwa......
Har d'akin MODIBO MA'U tasameshi da maganar BINTA shikam Bashida wata amsa dazai bata dan tabbas yasan yadda su BINTA suke kuma yasan tarihin mahaifiyar BINTA kokad'an bata da hayaniya dan haka bai musawa MA'U ba..........
Cikin k'an k'anin lokaci BAFFAN MODIBO yaje yanemawa MODIBO auren BINTA, babu wani 'bata lokaci aka basu, aka saka biki wata d'aya, itakam BINTA ko kad'an abin bai mata dad'i ba dan ganinta taci amanar MA'U wadda kullum intakai mata tallah ko bazatayi amgani da abinba saita saya dankawai ta farantawa BINTA bayan kayan sawa da abinci datake bata takawo mahaifiyarta, dan haka ansha artabu kafin BINTA ta amince amma acewar ta saidai MODIBO yaraba musu gida dan bazata iya zama da MA'U amatsayin kishiya ba saboda yadda take tsananin ganin mutunci da k'imar MA'U.
*_Ur's Hubbeey.😘_*
0 Comments