DAN MINISTER hausa novels2

 DAN MINISTER* 馃拝馃拕

           馃馃





Written by *Husba'ahfama* 



 *IG officiall_husba'ahfama* 

Facebook *Real Husba'ahfama* 


Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama* 











 Alhamdulillah Alah kulli halin














                      3-4









Nabil da yashiga dakin mahaifinshi kwanciya yayi yarufe Ido tinani yake akan nacin da Mata sukeyi akansa na suna Sansa afili yace bana sanku kukuma Kuna Sona meyasa kukemin haka bazanyi aureba bani da lokacinku rufe Ido yayi yafara bacci lokaci daya ciwan mararshi yatashi tin Yana daurewa yanaso yayi bacci har abin yagagara juyi kawai yake tayi lokaci daya yahada gumi duda sanyin esin da ke dakin 


Ana Haka alhaji sani yashigo dakin Yana ganin halin da Dan nasa yake ciki lokaci daya yarude yakarasa wajanshi labil baka da lfyne meyake damunka 



Saboda azabar ciwan da yakeji ko mgn yakasa hannu yasa Yana nunawa baban nashi mararsa 


Dasauri alhaji sani yadau waya yakira Dr dake duba iyalinshi ya,fadamasa yai maza yazo dansa ba lfy cikin kankanin lokaci Dr yazo yafara dubashi yaimasa abinda yadace lokaci daya bacci menauyi yakwasheshi


Dr yace yallabai da matsalafa in har Baku dauki matakiba akan nabil Nan gaba kadan ze iya rasa kwayoyin haihuwarsa gabadaya saboda wannan temakwan da ake bashi zedena aiki Dan yanzu magani baya Masa aiki se allura itama nangaba kadan zata Dena aiki ajikinshi saboda Yana da karfin shaawa me zafi agaggauta yimasa aure Dan asamu mafita Kar abin ya illata lfyarshi Dan har aiki abin ze iya sawa aimasa nangaba 


Numfashi alhaji sani yaja yace to Dr ngd insha allahu zaaimasa aidolema aimasa Dan kullin burina Naga gudan jinin nabil aduniya 


Sallama sukayi da Dr  yatafi


 alhaji sani dakin matarsa hajiya Fatima yatafi

Yakarasa wajanta yazauna cikin damuwa yafara fada Mata abinda Dr yace akan dansu nabil


Hajiya Fatima tace anzo wajan alhaji aini tintini naso aiwa nabil aure ko zedena wasu abubuwan da yakeyi Amma nasan ban Isa nace wani Abu akan nabil ba kayarda danhaka nai shuru da bakina Kuma da matsala nabil yatsani Mata bayasan Mata tin abin baya da muna yanzu abin nashi yafara bani tsoro gani nake kamar nabil na da aljanu kyama sosai yake nunawa Mata Nima Dan uwarsace babu yanda zeyi Dani muke zaune inuwa Daya dshi Yan uwanshi matama dandai Babu yanda Suma zeyi dasu yake hurda dasu ko hanya bayaso yahada da mace bare Kuma ai maganar aure dazu dazunnan yaiwa Yar mutane duka har targade yaji Mata Dan taganshi yashigo tarude tarasa inda zatabi ya hukuntata Kuma wace macace zata iya Zama da nabil inba Wanda batasan ciwan kantaba irinshi kokuma ta aureshi Dan kudinshi Amma inhar mace me hankalice da tinani wlh bazata auri nabil ba komai kudinku Kai dshi


Alhaji sani yace kefa matsalata dke Kenan indai akan nabil ne alheri baya fita abakinki ai nafiki sanin raayin nabil Kuma da Babu wannan matsalar tashi da tataso da bazan Masa aureba har se ranar da yasoyi Dan kansa bare harnazo wajanki neman shawara Kuma yanzu zanbawa Dana shawara akai Kuma zedauka ko bayasan mace zan bashi shawara ya auri kowace macace inde zatamai maganin matsalarsa tashi yayi yafice cikin fishi


Hajiya Fatima tace Allah yaganar dku Kai da danka alhaji daga Kai harshi kunyi nisa zankira baffah na fadamasa halin da ake ciki nasan Kai bazaka fada masaba 




Shatuwace takwashi zugarta sukayi dawa cikin gonakin mutane du gonar da sukaga tamusu Haka zatasa sushiga suyi musu barna sannan subar wajan du sanda tarayo Mata gonakin mutanene wajan wasanta ita da zugar kawayen ta gonar wani me mangwaro da goba  suka shiga magwaran yanuna sosai sukai Masa barna sosai Kuma sukaki barin gonar suna tawasa aciki har me gonar yazo ya samesu yaga barnar da sukai Masa ransa yayi mugun baci sosai Kara dogo yadauka yahau dukan du Wanda yasamu Dakar suka,samu suka gudu du yasansu yagane fuskokinsu rainshi abace yatafi wajan megari yakaimai Karar abinda su shatuwa sukai Masa 


Megari sawa yayi akakira iyayan yaran da su kansu  su shatuwa har da iya seda tazo cewa tayi se tazo taga me zaayiwa jikarta


Gaba dayansu sunzo sun amsa Kiran megari Nan magari yasa me gona yafadi barnan da su shatuwa sukai Masa 


Budar bakin iya tace to yanzu malam me kakeso aimaka wayace karka zagaye gonarka kai Mata kofa yanda Babu Wanda ze iya shiga lefinkane da kayi da yarannan bazasu shigarma gonaba har simaka barna yarannan kwatakwata nawa suke yaran da basugama hankaliba Dan abin kunya kakwaso jiki kakawo kararsu wajan megari yanzu Dan Allah bakaji kunyaba tsofai tsofai dakai


Megona yace ke tsohuwar banza kishiga hankalinki Daman Ina da labarinki inkinwa mutane sunbarki saboda tsufanki Ni inkinmin ba barinki zanyiba kwatakwata shekara nawa Kika bani da zanji tsoran yimiki mgn har naraga maki saboda girmanki ke ko tsoran Allah bakyaji zomuje kiga barnar da jikarki tasa akaimin agona Kuma wlh da nazone akan ajamusu kunne karsu kuma Amma wlh yamzu se anbiyani tinda Babu mutunci gobema kukara barin su suje gonar mutane suyi musu barna


Megari yace Wai ba afada kukeba kuke wannan abinba Karna karajin bakin wani anan iya gaskiya bakya kyautawa haba iya meyasa kike Haka tsufa haukane du abinda kikewa mutane in ankawo Miki Karar shatuwa nasani mutane nazuwa su fadamin ninake Basu hakuri saboda zaman mutuncin da kukayi da iyayanmu nake barinki Amma wlh Daba hakaba da matakin da zan dauka akanki ke da iyalinki da se kinyi mamaki sosai yanzu tinda kingoyi bayan jikarki shikenan zaayiwa mangwaransa da goba kudi  ki biyashi ke da iyayan yaran da taja sukaje sukayi barnar Kuma du sanda suka Kuma harku iyayansu se mundau mataki akanku suma Kuma yaran bazamu barsu sutafi hakaba se nasa anmusu bulala yanda Nangaba bazasu kumaba


Kafin megari yagama yanke kudin da su iya zasu biya Sega wasu masu gonar Suma sunkawo karar su shatuwa Haka megari yahada yasa iyayan yaran da na  shatuwa suka biya kudadan barnar da sukayiwa masu gonakin megari yasa dogarinsa yaiwa su shatuwa bulala sosai ihu shatuwa take kurmawa haka iya ma take kurma ihu daga anzubawa shatuwa bulala Haka iya zata takarkara tazuba nata ihun  du sukabi suka cika wajan da ihu


 shidai umaru mahaifin shatuwa takaici yahanashi mgn ga takaicin uban kudin da akasu suka biya gana shatuwa da na iya tinanin irin hukuncin da zeyiwa shatuwa in sun koma gida yakeyi 



Nabil be farka daga bacciba se wajan magariba Yana tashi yafito bega kowaba bangaransu yashige yaje yai wanka yafito Yana zaune afalo alhaji sani yashigo shi da hajiya Fatima  suka zauna kusa dshi 


Alhaji sani yace nabil yajikin naka 


Yace da sauki daddy


Nan alhaji sani yafadawa nabil abinda Dr yafada Akan cutarsa yaku Gaya Masa shawar da suka yanke nayi Masa sure


Dariya nabil yayi sosai sannan yahade Rai yafara mgn yace daddy kafasan matsalata da raayina natsanar du wata yarinya mace Ni Babu wani aure da zanyi wlh Dan Zan iya lahanta Yar mutane abanza wlh Dan ko gida daya Bata Isa mu zauna tareba Ni fa daddy bani da raayin aure bazan yiba mezanyi da mace nasan daddy wannan ba raayin kabane raayin mommy ne da wannan tsohon faffah Yama gangara kowa yahuta yaki mutun se shegen taurin Rai yaki mutuwa wlh du sanda tsohonnan yamutu Babu kukan da zanyi Kuma in har aka dauramin aurannan da kowace yarinyace sedai faffah yazauna da ita ko mommy ko Kai daddy Danni bani kuka aurawaba Bari kuga yauma Ni ba agidannan Zan kwanaba a otal Zan kwana muna da cashiya da bazaniba Amma saboda kun batamin Rai Dole nabar muku gidan Wai yau meyake faruwa da nine ake tabatamin Rai gobe America Zan tafi nahuta da nanjeria gabadaya Dan nasan wannan tsohun zeyi kirana naje Kuma bazaniba Nan da sati biyu ma muna da fatin da zamu agidan gonarka na mazagai 


tashi yayi yaje  yashirya yai ficewarsa ko sallama bewa iyayan nashiba yai ficewarsa yabarsu zaune afalo 


Hajiya Fatima tace kunfi kusa alhamdulillah tinda har mahaifinka be bariba bare Kai kaga tafiyata ai bani da tacewa akan Dan gwal tashi tayi tabar alhaji sani Tai tafiyarta abinda zemata anfani


Alhaji sani kanshine yadau caji Yana ta tinanin yanda ze yiwa nabil aure saboda bayaso yarasashi afili yace nabil kayi hakuri banaso narasaka Dan Zan shiga wani Hali kilama Nima nabika Dan bazan jure rashin ganin,kaba nabil yanzu menene abinyi ita Fatima Ina zuwa wajanta zatahau gayamin bakar mgn tahau yiwa mutane waazi Zan ta rarrashinka nabil har seka yarda da mgnar aurannan


Yau nabil yadawo daga America satinsa biyu Acan shi da abokansa beso dawowaba saboda fatin da zasuyi na murnar ranar haihuwarsa a gidan gona na mazagai zaayi Dan Haka yadawo shi yace anan yake so yayi shagalin murnar ranar haihuwarsa saboda San gidan gonar da yakeyi kwansa biyu da dawowa aka hada shagalin 


yau akeyin  taran yagaiyaci manyamanyan abokansa du zasuzo bakaramin kudi akakashe awannan taran murnar haihuwar tasaba  fadama Bata bakine du wannan abinba akeyi hajiya Fatima da malam usuman kakan nabil du Basu saniba taro yayi taro kowa yazo shikadai kawai ake jira motocinsane suka jero Akan layi sababbi dal alhaji sani ne ya canjamai su motocin masu dankaran kudi daga kasar waje aka kawosu shigarsama tawannan ranar daban take Haka motocinnan suka shigo garin mazagai dagudu suna badawa mutane kura kowa se kaucewa yake lokacin shatuwa da zugar kawayanta sunfito zasu Wasa sukazo zasu shige tagabansu motocin saura kadan su buge  shatuwa akwai wani ruwa dake tare ahanya takai motocin sukabi tacikin ruwan gabadaya wannan ruwa yabatawa shatuwa jiki motar har tana gogarta shatuwa seda tafadi kasa ta kurje abin yayi mugun batawa shatuwa Rai motar da nabil yake ciki ita tafi ballatsawa shatuwa ruwa ko su tsaya suka shigesu warsu dagudu


Abin yamugun konawa shatuwa Rai tace Kan uba wayannan suwaye yau senaga ko suwaye musamman wannan motar da tafi kowacce  Kyau aciki wlh bazan yardaba Sena Rama yau zasuga mezan musu


Kawayan nata sukace Kai jikan faffah usuman ne wlh karki yarda sekin Rama muje murakaki muma zamu tayaki


Dagudu sukabi motocin har motocin suka shiga gidan gonar  ahankali su shatuwa suka faki idan mutane suka shiga gidan gonar Suma Babu Wanda yakula dasu 


nabil aka budewa kofa yafito habawa Nan guri yadau shewa anamasa oyoyo su shatuwa Baki suka saki suna kallan ikwan Allah namiji suka gani da wata shiga Wanda Basu santaba harda su sarka yahade Rai sewani Shan kamshi yake 


Me shatuwa zatayi inba dariyaba sauran kawayantama dariya suka fara nabil jiyayi kamar anamasa dariya juyawa yayi bega kowaba cigaba yayi da tafiya wajan da aka tanadar Masa Dan zama


Anfara gudanar da shagali du su shatuwa nagani wajan tayoyin motar da nabil yafito ciki shatuwa taje dakanta tanemi kusa ta fanfasa duka hudun bayan tagama  Kai tsaye wajan nabil tadosa tabayanshi taje da ruwan kwata dauke ahannunta acikin wani gwangwani tabayanshi Tatsaya 


tace Kai Dan daudu rabi aljani rabi namiji rabi Dan daudu juyo kaganni nicenan shatuwa masifa tsokana  jikar iya  ikwan Allah kowa yaci tuwo Dani Miya yasha


Nabil cikin mamaki dajin maganar shatuwa yajuyo ai shatuwa batayi watawataba tajuyemai ruwan kwatarnan akansan da jikinshi


Tace baamin ban ramaba da yau banrama abinda kaminba dako bacci bazan iyayiba saboda takaici gababa in kazo garinran in kaganni kakara watsamin ruwa ka bugeni nafadi su jinmai kuyi Masa Wakar danace zamuyi masa


Nan suka faramasa Waka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji Dan daudu matamaza meshgar mahaukata kowa yatabomu semun Rama katabo shatuwa jikar iya ikwan Allah 


Dan mamaki da takaici wata Kara nabil yasa yaikansu dagudu zedaka kallone yakoma kansu kowa na mamakin meya hadasu Kuma yaakai yaran suka shigo wajan  dakyar Nabil yakama shatuwa sukuma yaransa suka Kama kawayan shatuwa kida nabil yasa aka kashe 


Nabil yace yau Wana irin hukunci zan muku yau me zan muku nahuce ni kuka batawa ranar haihuwata ke Yar kyauye mezubin mahaukata nikika yiwa haka da ruwan kwata Kika batawa jikina kusake Wakar da naji kunayi min


Shuru kawayan shatuwa sukayi suka kasa mgn saboda yanda nabil ya tsoratasu dukansu jikinsu rawa yake Dan sun tsorata dashi sosai 


Shatuwa tace au Wai tsoransa kuke Amma kun bani kunya wannanne zebaku tsoro Toni Bari naimaka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji nandaudu matamaza kowa yatabamu se munrama

 nice shatuwa 


Kafin takarasa  nabil yadauketa da wani mahaukacin Mari Dan bakin cikin abinda Tai Masa yarasa wana kalar hukunci zemata hannu yasa yashake Mata wuya  menai muku meyasa Mata kuke Bina kintaba ganina a Ina Kika sanni sekin fadamin meyasa Mata du inda naje se sunbini se Kuma sun batamin Raina kifadamin Kona sumar da ke meyasa Kika batamin ranar haihuwata kinsan dogwan burin da nadauka Akan wannan ranar kinsan daga Ina nadawo Dan wannan ranar inajin  kwatar da aka zubamin nasan wlh Babu meyimin haka se mace Ni bana shiga harkarku Mata Amma ku se kun shiga tawa meyasa kifadamin 


Shatuwa takasa mgn Dan azaba se Ido da take zarewa Dan azaba sakinta yayi  yakama hannunta na dama yamurde se da hannun yaikara ya tambatar yakarya hannun shatuwa sannan yasaki hannunta


 wani mahaukacin Kara shatuwa tasaki Dan azaba tace mugu maye ze kasheni Daman matamaza dandaudu nada karfi haka kasheni zakayi da kakemin wannan tambayar Ni Ina nasani ni kasan mekamin dabaka tsokaneniba da bazan biyoka naramaba ka karyamin hannu wlh Nima Sena karya naka ko Nan gabane ta karasa mgnar tana mai da numfashi Dan azaba


 Kuma Dan taurin Kai irin na shatuwa bakinta yaki mutuwa rashin kuya take tamasa shikuma Yana dada tinzira zuciyarshi na dada baci kowa Ido yazuba musu anrasa me Basu hakuri saboda tsoran nabil da bakar zuciyarshi Dan in ransa yabaci abin bakyau baa iya rarrashinsa 


Nabil yakalli yaransa yace mekuke jira da wayannan mahaukatan kudakarmin su harse sun jigata kekuma bakinki yaki mutuwa ko to Bari kiga mezansa aimiki yanzu waiyau Ni nabil nine nataba mace haka da hannuna Amma yarinyarnan kin cuceni kingama Dani natsaneki kece mace tafarko da nafara tabawa da hannuna Kuma insha allahu kece takarshe Sena barmiki tarihi yau kamar yanda Kika barmin  ya kalli yaransa kubarsu Haka ai sunyi sanyi ku je ku kwasomin buhunhuna acan dakin kukawomin kuga me zanmusu



Ana kawo buhunhunan  yace kubude kufara samin wannan marakunyar da na karya ku kullemin ita kusata abutdin mota ku rufeta ita  kadai sauranma du ku zirasu abuhu kusasu abut dasu zamu tafi ni nasan inda zamu kaisu


Andaga shatuwa kenan zaasata abuhu kakansa malam usuman yashigo gurin yaga danyan aikin da jikansa yasa yaransa sunayi cikin tashin hankali yadaka musu tsawa 


Yace ku kisankai zakuyi nashiga uku nabil ze jamin mgn zaman garinnan zefi karfina adalilinka rainawa zaku kashe da banzoba mekuke Shirin aikatawa Haka nabil abin naka yakai Haka tinda labari yazomin kashigo garin katara mutane awajannan hankalina yaki kwanciya nace Bari nazo nagani wace tsiyar kake aikatawa Dan nasan halinka Dole sekayi abin fada me wayannan yaran sukai maka har wajan susu ashirin yanzu da ban zoba duka kashesu zakuyi ko Yaya nidai nasan indai akasa mutun abuhu baze shaki iska sosaiba nabil kafadamin mezakai da yarannan ko kafara satar mutane bamu saniba


Nabil yace shikenan hanaruwa gudu kazo komai yakuma baci faffah me yakawoka Nan Wana munafikinne yaje yafada ma meyasa daddy ya sai gidan gona anan yanzu Dan Allah faffah me yakawoka wajannan kokazo kunyatani acikin abokaina wlh faffah Ina raga maka Dan Kai Kaka nane Babu yanda zanyi dakai kasan me sukai min yau kasan wace ranace awajena Kai basanin mahimmanci ranar kayiba bazaka ganeba ko na fadama nifa kasan dokata na tsani Mata banasan Mata meyasa zasu zo su yimin haka Ni Babu abinda zanyi dasu Kano Zan kaisu nayardasu acan  Nan yafadawa faffah abinda su shatuwa sukai Masa 


Faffah yace nabil meyasa baka da hakuri meyasa kake wulakanta mutane du wannan halayan naka Babu meshi akaf iyalina sekai a Ina kasamo wannan mugun halin kayi kuskuran kula yarinyarnan bakasan itama wacece itaba yanda kake fitinanne itama haka take fitinanniya agarinnan  da datayi maka Haka da baka kulataba kazo kafada min  ko ka kaiwa iyayanta Kara ko megari Amma yanzu kaga abinda zuciya ta ebeka kayi ka karya musu yarinya kawayanta kasa anmusu mugun duka yanzu da ban zoba Ina zaka dasu kukama masu bin nashi manyan banza se abinda yace muku kuyi kukeyi saboda Kuna karkashinsa ana biyanku kudi acikinku kusan dukanku kun girmeshi Amma anrasa mebashi shawara tagari Dan Kuna tsoransa kace bansan ko yau wace ranace awajankaba nikuwa nasan ko waje ranace yau awajanka ba bikin murnar haihuwarka kakeba yau to nazo tayaka murna nakuma karama biki Daya akan Wanda kakeyi yau Zan karama wani farinciki yanda nasan bazaka taba mantawa da ranarba yanzu da ka karyata me kake nufi kana nufin ka karya banza  baka isaba nabil baka karya banzaba kasan karya yarinyarnan me kahadawa kanka ranar auranka ka hadawa kanka wlh yanda ka karyata Kaine mijinta baka karya banzaba yau ka karyataka yau zaka aureta Zan daura maka aure da ita kaga taro biyu kenan Ni nakarama biki Daya Kar Wanda yatafi anan du kubiyomu zuwa gidan megari Dan halartar daurin auran nabil  azamanku na abokansa muna gaiyatarku daurin auran nabil sani DAN MINISTER kuzo mutafi 


Faffah kanlan mazan da yazo dasu yayi yace Kai kaje ka kiramin umaru baban shatuwa da Kuma iya kakarta suzo gidan megari cikin gaggawa ana nemansu Kai Kuma kaje kataho min da me gyaran karaya zuwa gidan megari 


 Yan uwan alhaji sani ne wayannan mutanan majiya karfi faffah sasu yayi suka daukarmai nabil cak suka samaishi amota akasa shatuwa itama amota da zugar kawayanta suka ja zuwa gidan megari du abokan nabil da sukazo fatin nashi suka bi bayansu zuwa gidan megari Dan ganewa idansu wannan auran mamakin da zaa daurawa nabil shi


Post a Comment

0 Comments