DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
5-6
Megari nazaune akofar gida akarkashi wata katuwar bishiya shi da jamaarsa segani sukayi motoci nata jeruwa suna tsayawa akofar gidan shi kallan ikwan Allah suka tsaya yi can Kuma sukaga faffah da yafito awata motar gakuma nabil ga shatuwa du anfito dsu amotar anrukosu zuwa gaban megari ana Haka Sega umaru da iya Suma sun iso wajan
Salati umaru baban shatuwa yafara yace wlh nasani shatuwa ce iya kinganiko abin naki shatuwa yaci gaba har da tsokano gari guda Daman ana cewa muzo ana kiranmu akofar gidan megari nasan shatuwa tayi halin wlh badaniba yau iya sedai koke inzaki iya baruwana wlh
Megari yace iya Isa umaru kajira muji meke faruwa ko mu Nan bamusan meyafaruba ganinsu kawai mukayi
Baffah yace du ku kwantar da hankalinku bawani abin tashin hankali bane sosai alheri ne yakawomu dukanmu Nan yanzu megari Ina neman alfarma dakai da liman da mahaifin shatuwa umaru da Kuma wayannan dattawan garin namu da suke wajannan inaso mudan koma gefe Dan da bayanin da nazo dshi zan muku alheri ne insha Allahu Allah yasa ku goyi bayana Amma Banda iya tadan jiramu tukunna in mungama tantaunawa itama akirata afada Mata aji raayinta
Megari yace to alhamdulillah du kutashi muje wayanda yace yanaso suji mgnar
Haka du suka tashi zuwa wani daki dake soran megari du suka samu waje suka zauna
Baffah ne yafara mgn yai sallama yabude da addu'a yace wani abune yau yafaru tsakanin jikana da shatuwa agidan gonar Dana sani Nan yabasu labarin abinda yafaru tindaga farko har karshe Kuma Ni na hango wani Abu alheri ne inhar kungoyi bayana Dan shima jikan nawa irin shatuwa ne ko ma nace yafi shatuwa da mugun Hali Dan tawani wajan halinsu yazo Daya tawani wajan kuma sun banbanta ta halaye Dan Haka hadin da nakeso ayi zezo dedai kowa acikin susu biyun zasu gyara junansu insha Allahu Dan na hango alheri alamarin Ni malam usuman mahaifi ga alhaji sani Kaka ga nabil Ina neman alfarma agabanku malam umaru mahaifin shatuwa yabawa jikana auran yarshi shatuwa adau rashi yau anan kofar gidan megari saboda abinda yafaru tsakaninsu Dan sukara hankali gaba ga tawagar munan nazo da ita ta Yan daurin aure Ina bawa malam umaru hakuri Akan abinda jikana yaiwa yarshi shatuwa insha Allahu ba ze kumaba Kuma Ni malam usuman namaka alkawari agaban su megari nabil da mu damgin nabil zamu rike shatuwa tsakani da Allah har karshan rayuwarta
Megari yace to fa wannan mgn batamu bace takace umaru Dan Kaine mahaifin shatuwa mu shawara ce tamu aciki Kai muke jira umaru muji raayinka akai
Malam umaru yace to gaskiya Ni wannan hadin auran baze yuwoba ban yarda dashiba Dan kowa yasanni agarinnan bawani kudi gareni ba se rufin asiri Kai Kuma baffah kowa yasanka Kai da ahalinka masu kudine barinma danka sani yafi kowa kudi azuriarka Kuma kowa yasan jikanka nibil da irin halinshi in yashigo garinnan itama Kuma shatuwa kowa yasanta da ita da iya da irin halinsu gankiya Ina gudun abinda zeje yadawo kunfi karfinmu ta ko Ina faffah shima Kuma nabil yafi karfin shatuwa ta ko Ina Dan da ba akasar Nan yai karatuba akasar waje yai karatu shatuwa fa da ko makarantar Allo batayiba bare ta boko wannan hadin baze yuwuba da matsala babba in akayishi kagafa faffah tashin farko haduwarsu me yafaru bare Kuma aka hadasu gida daya suyi zaman aure tare Kuma basan junansu sukeba Kuma nawa shatuwa take Bata wani girmaba Ina da dogwan buri akan shatuwa in Allah yabani iko Ina da burin shatuwa tayi karatu me zurfi sosai Kuma inaso in gyara ta ta Dena wannan halin nata Kuma yanzu ya zaayi da iya da ko tinanin rabuwa da shatuwa batayi ba Dan da kauna me karfi tsakaninta da shatuwa bazama ta taba Yarda da maganar aurannanba Dan bazata yarda arabata da shatuwa ba se dai kukira iya kuji nata ko zata yarda
Baffah yace karka damu umaru mudai yardarka kawai mukeso da sa albarkarka amatsayinka na uba awajan shatuwa iya kuma Ni da megari munsan yanda zamuyi mu rarrasheta ta yarda da auran Kai dai in tashigo kayi shuru karkasa Baki amaganar
Yace to shikenan Bari naje na kirata tashigo taji meyake faruwa
Umaru fita yayi yakira iya tashigo megari da baffah sukai Mata bayani nanfa Tai tsalle tadire tace batasan zanceba Babu me rabata da shatuwa bare har ai Mata aure da wani Dan gayu Kuma yanda ya karya Mata jika shima nabil se ta karyashi da kanta tace Ni iya fadan yadawo hannuna Ina yake Dan kwal uban yaro Naga shatuwa du tafadamin abinda yafaru da yaran kanku kirani ku fadamin Daman jira nake kufito na kwashe ubansa da Mari nazata dashi aNan ashema babushi yau Babu me rabani da jikanka usuman wlh banki mu doku Ni da Shiba Dan senayi zaman Yan bori Akan kafarsa shima har se na karyashi Zan tashi ai Naga yaran me kirar aljanu da yakoma kala biyu gaba Daya kamar ba Dan hausawaba Kuma kubude kunnanku kuji shatuwa dai bazan taba yarda da wannan auranba bazaaje akashemin jikata abanzaba afa garin masu kudinnan da naji ana fada shi uban yaran yake abawa dansa shatuwa suje su su sayarmin da ita sukara wani kudin Akan kudin da suke dshi
Megari rarrashin iya yayi da dadin Baki Amma fur Taki yarda
Baffah yace haba kekuwa aishatu Kaka wajan shatuwa ia bakisan yanda nake san shatuwa ba tana burgeni yarinya me kirki ga ladabi ga biyaiya na yaba da irintarbiyar da kika bawa shatuwa Dan Haka naso muhada iri da ke Baki iya tawashe Jin anyabi jikarta tin daganan suka hango alamun nasara ki temaka ki yarda da wannan hadin auran Dan Allah Kuma Kinga yau mukeso ashige da ita gidan mijinta dake Abuja Kuma Ni da kene yankai amarya da ango ke zakije kiga inda akakai jikarki da kanki acan zatayi jinya agidan mijinta zakina zuwa kina ganinta akai akai kema kina tayani ganin irin zaman da zasuyi Kuma in kin yarda da auran har kujerar aikin hajji Zan biya Mana Ni da ke muje mu rokarmusu zaman lfy Kinga har uban nabil da mahaifiyarsa du kikai musu kakar abinda da dansu yaiwa shatuwa Kinga se su jamasa kunne ko
dakyar baffah yasha Kan iya ta yarda da auran tate adaura Allah yabada zaman lfy kowa na wajan yayi murna umaru shima hamdalah yayi shatuwa zatabar gabansu yahuta da ba da hakuri da rigimar iya megari yafi kowa murna yahuta da sharia kullin
Megari yace alhamdulillah iya mungode sosai da wannan alfarmar da kikai Mana yanzu muje nasa ayi shinfida kowa ya zauna agudanar da daurin auran itakuma amarya shatuwa ashigo da ita ciki me gyaran karayar Naga ya iso tin dazu yashigo ya dorata kafin agama daura auran muntura Akira mahaifiyar shatuwa itama tasawa yarta albarka Kan atafi da ita
Nan aka shigo da shatuwa me Dori yadorata tana ihu tana komai iyama na ihu har aka Gama Dora karayar hannunta
Akofar gida Kuma Ana gudanar da daurin auran shatuwa da nabil baffah ne waliyin nabil malam umaru shine waliyin shatuwa baffah hannu yasa a aljihun nabil yaciro damin kudi ya irgi dubu dari biyu yamikawa megari yace ga sadakin shatuwa kowa ya sheda megari yasa hannu yakarba yasa albarka yanunawa kowa baffah yamayarwa da nabil sauran kudinsa
nabil yakoma hoto bakinshi yamutu yakasa mgn gani yake mafarki yakeyi wani iri yakeji zuciyarsa nayi be zataba be nufaba seji yayi anacewa Allah ya yarda aure ya dauru tsakani nabil sani da shatuwa umaru jikar iya ikwan Allah Akan sadaki nera dubu dari biyu lakadan ba ajalanba
kafin nabil yagama mamaki se jiyayi abokansa Yan tsokana sun dagashi sama suna tayashi murna suna ta Masa dariyar mugunta da tsokana
Megari ne yashiga yafasawa iya angama daura auran tafito ita da amarya zasu tafi Abuja haka mahaifiyar shatuwa tana hawaye taiwa yarta nasiha du da tasan bawani dauka zatayiba Haka aka fito da amarya shatuwa aka sata amota tare da iya akatafi
Baffah ya dada bawa kawayan shatuwa hakuri Akan abinda yafaru tsakaninsu da nabil yakuma musu alkawarin zuwa ganin gidan shatuwa in komai yanutsa hakama yabawa suwaiba mahaifiyar shatuwa hakuri tayi hakuri itama zata tagano inda yarta take in ankwana biyu Haka faffah yakama hannun nabil yasashi amota tare da tawagarsa ta Yan fati suka dunguma zuwa Abuja raka ango da amarya
Hajiya Fatima da alhaji sani sunacan basusan meyake faruwaba faffah ne yakira Amina yayar nabil yace Tai maza tataho gidansu tajirasu komai dare sunanan tahuwa zebata wata Amana yakira Hajiya Fatima itama yace Mata tashirya gashinan tare da Baki abinnan da takira tafada Masa komai yakankama Dan Haka tashirya gasunan sauran bayani se yazo ya tambayeta sani dansa nagari tace eh yace to du sujirashi gasunan
Sedare suka Isa Abuja zokiga zare Ido wajan iya da shatuwa sunga birni ko Ina da hasken wutar nepa kamar ba dareba ga dankara dankaran gidaje agarin anazuwa gidan su nabil Nan kallo yakoma sama iya dada zare Ido take saboda ganin dankareran gidan Dan baffah Haka aka bude musu gate motocinsu suka shige wajan fitowa amota ansha fama da iya cewa tayi bazata fitoba ayanke Mata Kai abinda yadada Bata tsoro ganin sojoji da bindigogi ahannunsu tadada tsurewa Dakar Amina tazo ta lanlabata tashiga
Baffah godiya yayiwa tawagar abokan nabil sannan kowa yashige gidansu sukayi sallama da ango mijin amarya shatuwa
Baffah Kama hannu nabil yayi zuwa cikin gidan da sallama ya shiga afalo yasamu hajiya Fatima da alhaji sani da su iya waje yasamu yazauna ya zaunar da nabil kusa dshi baffah yafara mgn yai sallama yace to sani da Fatima kubude kunnanku kuji me nazo dashi musamman Kai sani Dan nasan daga gunka matsalar take Nan yaimusu bayanin abinda yafaru tindaga zuwan nabil ma,agai har daura auransa da akayi da shatuwa wannan da kuke gani me karaya ahannu itace amaryar tashi Kuma itace Wanda ya karya din itakuma wannan tsohuwar itace iya kakar shatuwa tazo taga inda jikarta zata zauna yanzu amarya zata zauna a bangaran nabil cakin gidannan Kuma adakin nabil har se tawarke sannan acikin gidajanka kabasu Daya sutare acan Dan Haka ga amananan ankawo muku ta Yar mutane kuji tsoran Allah kukula da ita kamar yanda zaku kula da danku nabil
MINISTER yace baffah meyasa kahada wannan auran kafasan nabil wlh baze taba yarda da wannan Yar kauyanba Kuma nasan nabil basanta zeyiba Kuma baffah na sanka Baka tambayi nabil ko yana san ta ko baya san ta kawai ka yanke hukunci ne ka aura Masa ita wlh daga ganin yarinyarnan Bata da kunya Kuma bazasu zauna lfyba ko ta ilimin nasan nabil yafita da komai kagan tafa yarinya kamar aljana se zarzare Ido take tin da suka shigo ko ita kakar tata Naga se wani huhura hanci take tana wani zarzarewa mutane Ido wlh in har akabar nabil da yarinyarnan ancuceshi Kai nabil kana santa ko baka Santa kafada kowa yaji Dan Allah baffah inyace bayaso kabarshi yasaketa kowa yahuta Dan wannan aljanar yarinyar ba ajinsa bace
Nabil yace daddy bakinciki ya hanani mgn tin daga lokacin da yake hada auran nakasa cewa komai Dan ganin komai nake kamar amafarki Ni abinda yafi konamin Rai wai a cikin aljihuna baffah yaciri kudi yabiya sadakin wannan mahaukaciyar yarinyar wlh daddy nakuma tsanar mace arayuwata Mata sun yimin abinda bazan taba mantawaba natsani yarinyarnan ranar da nafara ganinta na tabata ta zamemin Bala,I ta zamemin alakakai arayuwa Wai yau mace akakawo gidanmu azaman matata inba Wanda ya haifi ubanaba waye zemin Haka na barshi ban dau matakiba aduniyarnan bazan taba san taba Kai bama itaba du wata mace wlh na tsanesu illa uwata da Yan uwana Mata sune kawai ban tsana Suma sun Zama Dolene awajena daddy yau baffah ya kunyatani Wai Ni nabil nine baffah yasa aka dinga daukana agaban yarana da abokaina da wayannan mahaukatan yaran cancak kamar wani yaro anasawa amota ana ta rikeni Wai Kar na gudu Ni baffah yaiwa auran Dole dabaka ta da hankalinkaba baffah saboda Ni har abada bazanyi aureba Dan ko anyimin bani aka daura waba mommy da daddy ka daurawa aurannan ko Kuma kanka ka daurawa tin amazagai nakeso nai kuka ko naji Dadi azuciyata Amma nakasa Daddy zuciyata zata fashe in har aka barni da mace azaman matata faffah Zan hutar da Kai Zan saketa yanzu Ni nabal sani Zan
Kafin yakarasa iya tace wlh karma kafara baka Isa kamayar min da jika bazawaraba inaji Ina gani da ban yarda da auranba Amma yanzu na yarda da auran shatuwa da Kai Kuma wannan ikirarin da kayi na ka tsani du wata mace wlh kajawa kanka Zama daram Kai da shatuwa Dan Haka ka karya min jika bass kamar kasamu rake to karike wlh baka karya banzaba se nasa shatuwa tarama Kuma ko ban sataba nasan shatuwa Yar halakce Ni tagado zata rama Kuma wlh da Wasa ka tabamin jika se narama Mata itama Kuma kafin natafi Sena Mata nasiha akanka du abinda Kai Mata tarama Kar ta barka kana kiramin jika mahaukaciya kaifa me kala biyu Dan Allah jibeka ko gashin kanka abin kallone jibi wani wando Rabin duwawu du awaje ana ganin wandanka naciki jibi wasu uban sarkoki awuyanka sunfi kala biyar jibi yatsun hannunka zobunan da suke hannunka dubi shigar taka babu ta arziki da ubanka yake Kiran jikata Yar Kauye me kirar aljanu Kai kumafa me kirar me za a kiraka me kirar aljani ifiritu Zan kiraka ko dandaudu ko me tabin hankali da ubanka yake cewa jikata ba ta da ilimi indai irin ilimin kane wlh gara ta zauna Haka da Wanda na koya Mata jikata ba jahila bace Dan Ni Nan nice na ke koya Mata karatu har me kwanciyar tsakar daki du na koya Mata kai Kuma na dawo wajanka sani kake kowa wlh inkai Wasa Zan tsinkeka da Mari Dan Naga baka da mutunci tinda nashigo Naga kana harararmu kaganni Nan wlh shegen karfine da Ni bankiba daga Kai har Dan nake mu daku Dan jina ne ke dakaukau saboda karfi Kuma Nima nayi alkawarin senayi zaman Yan bori Akan kafar danka tinda ya karya min jika Kuma wlh ko yasaki jikata Bata sakuba Zama daram Dan Bazata koma mazagai ana kiranta da bazawara da kuke kiramin jika Yar Kauye kowa asalinsa Kauye Dan kwal ubanka daga Ina ubanka yake in ba da ga kauyenba anzo birni anyi kudin Alla ya Isa anci burudi da shayi da abin Yan gayu an manta da kauye usuman kajawa danka da jikanka kunne wlh Basu sanni bane labarina sukeji Zan gwada musu halina in suka kaini bango
Kafin baffah yai mgn MINISTER yace lanlai tsohuwar Nan daga ganinta Bata da mutunci Ni kike gayawa wannan mgnar lanlai in baaraba aura nabil da wannan yarinyar ba wlh kashemi Dana zakuyi ke da jikarki yanda kike San jikarki Haka Nima nake san Dana nabil Ni Kuma azamana na mahaifin nabil bangoyi auran nabil da jikarkiba Dole ya saketa Kuma Nima zanwa Dana nasiha in jikarki tamasa rashin kunya yarama Kar ya barta nama San Dana nabil shima Dan halakne ze Rama kakuma balballata Ni nasaka kaji nabil wlh wuya kadai se tasa jikarki ta gudu ji wani suna Wai shatuwa ko dadin ji Babu Dan Allah baffah karka Hana nabil sakin yarinyarnan wlh ke tsohuwa karki Kara kiran Dana Dan kwal uba nagaya Miki
Kafin kowa yayi mgn shatuwa tatakarkara takurma wani uban ihu se da nabil ya toshe kunnansa tace nashiga uku Ni yanzu ma nagane me ake nufi tin amazagai ban ganeba se yanzu har fadan da babarmu taimin Wai nabi mijina Ni du ban ganeba Ashe Wai aure akaimin iya kina Ina aka auramin wannan dandaudun Mata matamazan aka auramin iya Kika Bari haka tafaru Daman shi abbah ba Sona yakeba neman Kai yake Dani su megari ma Haka du basa Sona Wai ma Kuna nufin anan garin Zan zauna billahillazi ba Zan iyaba tinda muka shigo garin Banga gonakiba Kuma Ni bazan iya rayuwa Babu dawa da gonaki Babu kawayena Kai dandaudu wayacema Ina sanka Allah yakiyaye na auri rabi mutun rabi aljani yanda baka Sona Nima bana sanka yanda ka tsaneni Nima na tsaneka Kuma nadau alwashi se narama abinda kami wlh bazan taba hakuraba bakasan shatuwa jikar iya ikwan Allah ba
Nabil yace nashiga uku kaina zefashe Dan Allah baffah kakawo karshan rigimar Nan Dan Allah badan niba kaji tausayi na baffah karabani da mahaukayar Nan wlh na tsaneta ko ganinta banaso nayi karka min Haka Dan Allah baffah Kai mgn kayi shuru tin dazu
nabil yaje yarike wa baffah kafa
Baffah yace nabil wlh wlh wlh kaji na rantse har sau uku aure ya dauru Babu me Rabashi se Allah tinda shine komai yake hannunsa Amma wani Dan Adam wlh be Isa yaraba auranka da shatuwa ba Babu shi Kuma baayishiba Kai da ubanka kubude kunnanku kuji Ni Ni usuman mahaifin sani Kaka awajanka nabil in har ka kuskure ko da Wasa kasaki shatuwa wlh wlh wlh Sena tsinewa ubanka sani yabi duniya ya lalace Kuma bani bashi har abada kuma nacireshi acikin yarana gabadaya in kanasan ubanka kabar mgnar raba aure ko mgnar saki in Kuma bakasan ubanka gafili ga medoki ka saketa kaga aiki da cikawa Kai da ubanka me daurema gindi naji kana gigin ambatan saki wlh daga yanzu mgnar tafita bakinka gaba daya Kai da shatuwa mutu karaba Kai zaka binneta ko ita ta binneka kace katsani du wata mace ko to ga macenan ku zauna gida daya tare in kaso Dan Allah kamutu tana warkewa zaku bar gidannan Kai yanda kakeji da rashin mutunci hakama shatuwa takeji dshi ga tanan ku kashe junanku daga ita har Kai da kuke cewa ba kwasan juna aure dai ya dauru Babu batun rabuwa kuje Kai da ita ku koyi San junanku Kai sani shawara ta rage taka kace bakasan wannan auran ko to kaiwa danka fada yazauna da matarsa lfy ko kabi San danka ya saketa Ni Kuma mahaifinka na tsine maka
Gaba daya Kan MINISTER ya daure wani uban gumine yake ta ketomai ajiki du sanyin esin da ke falan Amma yajike da gumi se gogewa yake jiyayi gaba daya ya tsani shatuwa arayuwarshi da kakarta iya yanzu ya zeyi tinda har baffah Yana Kiran ze tsine Masa Akan wannan aljanar yarinyar Baki narawa yafara mgn yace Dan Allah baffah bekai hakaba Amma Ni da zakabi tatawa da kasa nabil yasa
Iya CE tataso tazo gaban MINISTER tace au baka sadudaba ko bakayi sanyiba du da dokar da ubanka yasa maka ko tu Bari kaga tinda kaki jin mgnar ubanka Ni Bari na fara wankeka da Mari tukunna
hannu tadaga zata mareshi kafin hannunta ya Kai fuskar MINISTER nabil yayi kukan kura yataso cikin fishi yarike hannun iya jikinshi se tsuma yake Dan masifa da bacin Rai da yake cin ransa yace ke tsohuwa ki nutsu kishiga taitayinki kafin na koya Miki hankali uban nawa Zaki Mara haba zance kike wlh Ina gani ki mararmin ubana Ina wajen Ashe ban haifuba ko da Wasa Kar ki Kuma gigin daga hannu da sunan mararmin uba kema inaga ban karyakin bane Dan Haka kikaki yin sanyi har kike cewa Zaki ramawa jikarki Nima se kin karyani ko ta Bari kiji somin tabi hannunta ya matse da karfi iya tasaki Kara Dan azaba Kuma ki jawa jikarki kunne tashiga hankalinta da Ni takuma iya bakinta in bahaba Zan canja Mata kamanni ke ko kunya bakijiba ubana na MINISTER kidaga hannu Zaki mareshi kin san waye shi a kasarnan Kinkuwa San me mukamin MINISTER na man fetir yake nufi koni DAN MINISTER kin Isa kisa hannu ki mareni bare ubana dada matsa hannun iya yayi takuwa da wata karar me karfi
Haba wa cikin fishi shatuwa tataso tararumi wata kwalbar fulawa da ke gefen TV zata kwadawa nabil tana jefuwa cikin zafin nama MINISTER yataso yatare Dan karya samu nabil seji akai kau agoshin MINISTER lokaci daya jini yaballe Yana zuba agishin sa ran nabil dada baci yayi jiyayi zuciyarshi zata fashe Daya hannunsa yasa yadafe kirjinsa jiyayi jiri na ibansa lokaci daya idansa yakada yayi jajir besan lokacin da yasaki hannun iyaba shima yafara neman abinda ze kwadawa shatuwa da besamuba idanshi yarufe yayi kan iya yabi ze daka azaman shatuwa ihu iya tafara tana neman dauki Dan nabil yayi Bali,in Bata tsoro dagudu Tai bayan kujerar da baffah yake azaune
tana cewa nashiga uku yau Naga ikwan Allah usuman Daman Haka jikanka yake ka hadashi aure da jikata ko dai shima Yana shaye shayennan na zamani da matasa keyi wannan wanna kalar aurene Kai nifa sirikarkace jikata kake aure usuman zefa lahantani kanaji kana gani in wannan zakin yai wasan kura Dani wlh ragargazani zeyi
Tsawa baffah ya dakawa nabil ya tsashi tsaye yace Kai karka yonan ko dawasa bare har kakuma tabata kaikuma sani kadan kagani ku bacemin dagani afalannan Kai da danka zamuyi Zama na musamman Ni da Kai sani kekuma shatuwa bakiga me kikaiwa sirikinkiba ko Baki San uban mijinki bane
Shatuwa tace Ni bashi nai niyar samuba wannan dandaudun nai niyar jifa shikuma yatare Masa na fasa Masa goshi ban saniba tsautsayine se hakuri Kai Kuma wlh Sena zubar maka da jini tukunna zakasan nice shatuwa
MINISTER hannun nabil yakama suka bar falan Yana tafe Yana masifa
Du wanna ruwan masifar da akeyi hajiya Fatima da Amina na wajan sun kasa mgn se Ido da dariya da mamaki
Baffah yace Amina jeki Basu wajan kwana Kan gobe bangaran nabil Zaki kaisu kimusu du abinda yadace ko abinci Basu ciba du kibasu suci in kin Gama dsu kizo nabaki Amana ke da mahaifiyarki kinji Yar albarka
Tace to baffah suka fice zuwa bangaran nabil
Hajiya Fatima tace baffah yau naci dariya Naga ikwan Allah
Baffah yace rabu da su Ina sane nahada aurannan insha Allahu shine silar shuryuwar nibil da sani Dan Allah kiga abin kunyar da sani da iya suka yi gaban yarannan memakwan suyi musu nasiha suhada kansu su zauna lfy Sema dada Bata abin sukayi kowa nawa nashi muguwar huduba Akan zaman auransu sani idansa yarufe San dansa yake du mgnar da tafito daga bakinshi fada yake Haka iya San jikarta itama yarufe Mata Ido du abinda yafito daga bakinta fada take Fatima ke da Amina ga amananan nabaku na shatuwa ku temaka ku gyarata ku wayar da ita asata amakaranta in tawaye itace zata gyara nabil Kuma itace zata cusawa nabil Santa azuciyarshi da San Du wata ya mace azuciyarshi takuma nuna Masa darajar mace da mutuncinta awajanshi da kansa ze sauka daga Kan akidarsa ta kin Mata yakuma so shatuwa ammafa se anyi Dan karamin yaki sosai agidan nabil Kuma fa se kunyi hakuri da halayan shatuwa Dan yarinyar bataji Kuma Bata da tsoro ko kadan Dan Haka na hadata da nabil zata iya da shi rashin tsorantane yasa na hadata da shi Dan Naga nabil na da wata baiwa kusan kowa tsoransa yake tin da Kika kirani awaya Kika fadamin halin da nabil ke ciki nake ta tinanin matar da Zan zaba Masa Kuma Sega wannan abin yafaru tsakanin sa da shatuwa da Kuma kalaman da naji yanayi Kan mace yasa na hada wannan auran Allah yasa kin fahinceni Fatima
Hajiya Fatima tace nagane baffah Kuma naji dadin hadinnan Allah yabamu ikwan rike amanar Yar mutane yanzu inda matsalar take awajan alhaji take Dan shima yadace yaba da gudun mawa wajan hada Kan shatuwa da nabil Amna se gashi shima bayasan auran saboda dansa bayaso kasanshi du abinda nabil keso shi yakeso in da nabil yace Yana Santa shima alhaji ze sota yagoyi bayan auran Amma yanzu tashin farko kaga me yafaru da idanka Ni nataba ganin wannan Bala,in ranar da aka kawo amarya akwashi wannan ruwan masifar haka memakwan ayi farin ciki se abin yakoma bacin Rai Allah ya kyauta
Baffah yace rabu da shi se gone zamu hadu da sani yanzu zanje na kwanta gobe in Allah ya kaimu zamu karasa yanda zaayi Dan gobe in komai yalafa zamu koma Ni da iya
Kai 馃ぃ馃ぃ Yan DAN MINISTER fans ku da kuke tashirin zuwa biki kunga yanda aka kwashe ranar da aka Kai amarya shatuwa to Ina Kuma ga ranar da ake Shan biki Ashe zakusha raban fada tsakanin iya da MINISTFR da shatuwa da Nabil馃ぃ se kunzo
su hasana lawan
da su maman munur
da su shafa Umar
da Aisha ummu Minal
da hajiya Rashida
maman Abdulhakim
Yar mulki
maman Haifa
Amina isima il
maman baby
ummu hasim
maman kairat zariya
maman yaseer
momin twins daweesu novel grp ayishat daweesu novel grp
Asha biki lfy nidai Ina daga gefe馃ぃ
Ngd sosai Yan DAN MINISTER fans grp da irin ruwan shirhin da kikaimin tin daga ranar da nafara DAN MINISTER zuwa yanzu
da sauran grp grp da sunayansu na manta godiya nake Allah yabar zumunci da du wayanda na manta sunansu Dan Allah kuyi hakuri ngd sosai Allah yabar so da kauna
Bana turawa ta PC Dan Allah kuyi hakuri
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈�
*'YAR KWALLIYA* 馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
7-8
Adaran aka Kira Dr yazo yaduba MINISTER yaimasa dinki nabil ma se da Dr ya dubashi har da su allura Dan ya samu bacci
Iya kwana tayi tana ta ruwan masifa Akan abinda nabil da babansa sukai musu hadub kuwa ta yanda shatuwa zata zauna da su tashata wajan iya gajiya shatuwa tayi da sauraran iya har bacci yakwasheta sannan itama iyan tasamu waje ta kwanta
Washegari da safe bayan anhada abin karyawa Amina tace mommy yazaayi wajan cin abincin safe kinsan dai inhar gabadaya za ahadu aci har da su daddy da su iya to wlh ba abinci zamuciba raban fada zamuci Dan Haka meye abinyi Ni wlh baffah nafijin tausayi shine me Shari,a jiya fa se da na Kai Masa maganin ciwan Kai yasha bayan yaci abinci Allah yabani tausayi to yanzunma in har aka hadasu waje Daya to tarihi zekuma maimaita kansa Dan Naga daga iya har daddy Babu me gudun abin kunya Akan aurannan Dan basa ganin mutuncin juna kowa nashi yakeso baa Kuma mgnar ango da amarya wayannan Kuma se Dua,i jiya dazan kwanta nasha dariya sosai Ni mantawa ma nayi da har awaya Zan daukeso du ranan da suka shirya na nuna musu abin kunyar da sukayi ranar auran shatuwa da Nabil Ni tin Ina mamaki har abin yakoma bani dariya yanzu mommy me kikece Amma Dan Allah abar baffah yagama huta gajiyar jiya in kin yarda kowa akai masa abin karyawarsa har inda yake jiya har wasu daga Yan iakin gidannan sunsan meyafaru jiya har kunyarsu nadinga ji su da abin kunya mu da Jin kunya Allah yakyauta
Hajiya Fatima tace eh Haka zaayi Amina kisa akaiwa iya da shatuwa nasu alhaji da nabil mu hadu muci tare baffah shima akaimai nashi gwara da mijinki yabarki Kika kwana da abin yamin yawa ai wannan Kuma Babu maganar muje mu kama waje ayi Dinner Dan abin kunya zasu barmana Kuma ba damuwarsu bace Da ni yanda na tsara abokan nabil da na shatuwa da mu kanmu iyaye du zamu hadu mu tayasu murna Amma yanzu fitinarsu bazata bariba ayi abin arzikiba daga iya da alhaji har amarya da angwan Dan Haka mun hakura ahadu ahidimar haihuwa in Allah yashryasu suka haihu mayi shagalin suna Allah yabasu zaman lfy
Amina ta amsa da ameeeen
Amina ce da kanta Tai sallama takaiwa su iya abin Kari tare da rakiyar Yar aikin gidan
Amina tace iya antashi lfy yagajiyar jiya ya kwanan kanwar tamu shatuwa Babu mgn ko du gajiyarce tana dariya ta karasa mgnar
Iya tace lfyklau yarnan ainaga ke da matar gidan Kuna da mutunci bakamar ebanbuncanba wannann hajiyar itace ta haifi rabi mutun rabi aljani kema Kuma yayar sace
Amina tace eh iya wannan itace mahaifiyar mu uwa Daya uba Daya muke da nabil
Iya tace Amma albasa batai halin ruwaba ammafa hajiya na hakuri da ubanku da wannan Dan kwal uban yaran
Dariya Amina tayi tace iya tamu Kuma kakarmu amarya awajan mijin shatuwa to iya ke da angwan naki haka zakuyi zaman auran ko dai kishi kike Dan jiya ya auro shatuwa ya Miki kishiya
Iya tace Allah yakiyaye ajikoki wannan yazama jikana yaran da tashin farko ya karyamin jika jiya Nima yakusa karyani Allah ne ya kwaceni yaro da shegen karfi se kace me kashin mindiriki
Me Amina zatayi inba dariyaba tace iya tamu Bari na barku ku ci abinci anjima zandawo muyi hira
Ficewa Amina tayi tana dariya tana mamakin rikicin tsufa irin na iya
Lokacin da Amina takoma taje tatarar har nabil da MINISTER sunfito sun fara karyawa
mommy tace mu har munfara mungaji da jiranki
Amina tace Hira muka tsaya yi da kawar nabil iya
Nabil da MINISTER wani kallo su kaiwa Amina Babu shiri taja bakinta Tai shuru
Kowa yayi shuru ana ta cin abinci Babu zato Babu tsammani se muryar iya akaji tashigo tana masifa hannunta dauke da kulolin da Amina takai musu na abin Kari tare da rakiyar shatuwa
Salati hajiya Fatima tafara tace shikenan Allah yai dare gari yawaye za afara Kuma ko karyawa ba mu gamaba bare ya tsirgamana iya ke dawa me yafaru yihakuri ki fadamin
Iya tace Ina suke ebanbunnan wajansu nazo nasan da sa hannunsu sune zasusa aimana wannan abincin azaman abincin safe ke dai nasan babu ruwanki kina da kirki ba kamar wayancan Marasa mutuncin ba yauwa Ashe gasucan takarasa gaban alhaji sani da nabil ta ajje musu kololin abincin agabansu ta karbi na hannu shatuwa shima ta ajje musu ga tsiyarku Nan kuhada kuyi taci ku hankalinku kwance sekai Loma Baki kuke tayi mukuma inmunso mumutu Ni da jikata Dan mugunta kunsan Koko da kosai da dumaman tuwo da yartsala da Masa mukafi sani da safe shine zakusa adafo Mana wannan abincin masu jankunnuwan nasara akawo Mana Dan yunwa takashemu takalli nabil Kai mekiran zakuna hararar me kake Mana tin da muka shigo dakai da wannan uban naka me katan ciki
Hajiya Fatima rokar alhaji sani da nabil take da Ido karsu kulata suyi shuru Amma Ina abanza
zuciya ta ebi nabil hannu yasa yakaiwa dining table duka se da wasu daga cikin glass cup din dake Kai suka fado kasa suka fashe idansa yarine yakoma Jah saboda bacinrai Daman Kuma da haushin su yakwana aransa shima Kuma tinanin in sun hadu irin hukuncin da ze dauka akansu yakeyi se Kuma Allah yakawo su taruwan sanyi
Yace ke tsohuwa wlh ya isheki haka cinfuskar da kike Mana Ni da ubana ya Isa Haka daga haduwarmu da ke zuwa jiya da yau kin kirani da kalar sunan banza yakai nawa ubanama Baki bariba Dan bala,i Kai se yanzu nagodewa Allah da nadage yarena na hausa be bar bakinaba du da zaman da nayi a America Kuma Allah yasa inasan yarena kome kafada min da yarena na hausa Zan gane Ashe da kin cuceni kamar nasan da wannan ranar narike yarena na hausa hannu binbiyu akasar da batamuba ga jikarki itama Babu kalar da sunan banzan da Bata kirani da shiba ita da kawayanta har da min Waka haduwata da ku akwana Daya tazamemin fitina wlh ke tsohuwa inhar kikai Wasa Kika Kuma kirana da wani sunan daba nawa wlh Sena gurza Miki Baki se na karasa cire wayannan jajayen hakwaran na gaban bakinki da suka rage Daman inajin haushin jikarki ta fasawa ubana goshi har da dinki Kuma se nadau fansa ko akanki ko Akan jikarki
Shatuwa Tai caraf ta anshe mgnar tace au Ashe Babu Dadi Ni da ka karyawa hannufa ai kome yafaru Kaine kaja ba waniba da baka Fara tsokana taba da du Haka Bata faruba gashi Ina ji Ina gani kabarni da jinya ai ko jiyan Ni ba shi nai niyar jefaba Kai nai niyar fasawa goshi yai maza yatarema Kuma wlh har yanzu ban hakuraba se narama Kuma ga tsiyar abincin kunnan Kuma Dole aje asamo Mana Wanda muka iya ci agarinmu
Nabil yace au har yanzu bakuyi sanyiba ko Dan ban gama nunamuku irin
Kalata bako
Plet da glasscup din Kan dining table din nabil yasa hannu yafara jifansu dshi suna tsalle suna kaucewa iya du tacika wajan da ihu da masifa shatuwa da taga abin bana Kare bane itama kome tasamu jifan nabil take dshi har abincin da yake gabansu ta dauka tana jifan nabil da shi lokaci Daya suka Bata ko Ina na wajan MINISTFR mutuwar zaune yayi yakasa motsi Yana kallan ikwan Allah Amina ita gefe ta koma tana kallansu anrasa me Basu hakuri hajiya Fatima tana boye abayan labulan wajan in taji anyi ihu se ta leko kanta daga taga ana niyar jifanta satai maza ta komar da kanta nabil kofin gaban MINISTER ya dauka da ruwan shayi ciki me zafi Yana tiriri garin ya watsawa shatuwa se awuyan iya wata mahaukaciyar Kara iya tasaki Dan azaba lokaci Daya du tabi ta gigice Dan zafi ai batasan lokacin da tashige karkashin dining table ta buyaba tana mai da numfashin wahala lokaci Daya wuyan iya yatashi abinka da tsufa ruwan shayin ya Kona Mata fata sosai ta gefan wuyanta
shatuwa ganin ruwan shayin da nabil ya watsawa iya da Kuma yanda iya take ta ihu yakuma konawa shatuwa Rai batasan lokacin da Tai tsanle ta finciko karfen labulan wajan gaba daya ta rikitosu sukayi kasa se ga hajiya Fatima abayan labule tana raba Ido tana ijiran ikwan Allah shatuwa Kan nabil tayi dagudu da karfen labulan ahannuta in takai Masa duka dshi se yai tsalle ya kauce Babu zato Babu tsammani garin shatuwa ta kwadawa nabil karfen se a gadan bayan MINISTER zafin karfenne yadawo da shi daga mutuwar zaunen da yayi tin dazu Dan azaba besan lokacin da shima yashige idan iya ta buyaba sun hadu susu biyu suna jinyar in da kowa aka illata shi Dan azaba bayansa rikewa yayi Dakar ma yakai kansa in da yabuya iya da MINISTFR Baki yamutu Babu me mgn
sunbar nabil da shatuwa na fafatawa fadan yakoma na manya nabil shima samu yayi yadauki karfen labulan daya yakan shatuwa da shi dagudu Yana kokarin kwada mata bakajin komai se karar karfe awajan Dan karfin Hali na shatuwa da hannu daya take wannan rigimar Kuma dudahaka shatuwa bakinta yaki mutuwa inbanda bakaken mgn Babu abin da yake fitowa daga bakinta tana gayawa nabil shikuma Yana dada tinzira ransa nadada baci gabadaya sunhada wani uban gumi Kai ace wani uban aikin wahala aka basu su keyi
Amina da taga suna niyar jiwa junansu ciwo kuma Babu Wanda yake da niyar hakura ya dena Dakar da dabara tasamu tafita wajan baffah ta gayomasa abinda ke faruwa da sanyin safiyar Nan da sauri baffah yabiyo bayan Amina tinkan yakaraso yakejin muryar shatuwa da Kuma karar karafuna natashi shikuma muskili Nabil baajin muryarsa akwai wata kofa tabaya Amina tacewa baffah sushiga tanan Dan asamu arike Daya daga ciki suna shiga Allah yabawa Amina sa,a tarike shatuwa tabaya shikuma baffah yasamu yarike nabil tabaya
Tsawa baffah yadaka musu ya wankawa nabil Mari yace kunutsu kushiga hankalinku meyake damunku haka ko kunsamu tabin hankaline bamu saniba daga jiya zuwa yau Kai nabil meyasa kake biyewa mace Kuma matarka Dan Allah jibi yanda dukanku kuke maida numfashi kamar wayanda sukayi aikin wahala Dan Allah kukalli barnar da kukayi awajannan gaba daya kun lalata komai nawajan har falo Baku bariba abincinma gabadaya kun zubar dshi saboda Bala,inku Ina sani da iya da fatima suke suka barku Kuna wannan danyan aikin
Hajiya Fatima ce tasamu tafito daga wajan buyar da tacanja tace baffah du munanan abinne yafi karfinmu in muka tsaya ciwo zasuji Mana abanza abarmu da jinya ai yanda suka haukace dinnan ran kowa yake abace acikinsu Babu me iya raba fadannan Daman se Kai baffah Suma masu daure musu gindin sunyi takansu sun kasa rabawa baremu Yan kallo baffah Ni banma San Ina suka buyaba tinda naji ihun iya dazu ban Kara jiba inaga sunsamu sunfice suna waje abin yafi karfinsu
Muyar iya sukaji ta karkashin daining table tana fitowa da rarrafe tace kun ganmu Nan Ni da Mara mutuncinnan muna jinyar jikinmu konani da ruwan zafi mekirar zakunannan rabi mutun rabi aljani yayi daban gudu na buyaba da salibeni zeyi kamar kaza aruwan zafi gabadaya ko ya aikani lahira Babu shiri mutun amurmurde kamar samudawan farko fuska amurtuke sekace me gadin gidan wuta idanshi Dan mugunta har wani Jah da Kore suke komawa Dan masifa usuman kahada shatuwa da Bala,i rashin sani yasa na yarda ankawo jikata inda zaa kasheta nashiga uku Ni Aisha anfasa aurena billahillazi usuman kadau mataki Dan bazan yarda inaji Ina gani acutarmin da jikaba Dan Allah kaga yanda gabadaya Rabin wuyana yasale da ruwan zafin da wancan damisan yawatso min ko tsufana beganiba Dan rashin imani har da cewa ze karasa ciremin hakwaran bakina nagaba da suka rege Kuma wlh ze iya fin hakama Dan Babu tausayi da digwan imani azuciyarshi zantafi da jikata in komai yalafa sunyi hankali shi da ubansa na dawo da ita wlh inaji Ina gani bazan bar jikata akashemin itaba
MINISTER ne yafito shima Yana rike baya yace Ni bance inaji Ina gani jikarki zata kashemin yaroba Nima ta gurguntani se ke baffah kagani da idanka tin da aka kawo fitinanniyar yarinyarnan take hakona jiya kaga me tai min yauma gashi ta barni da ciwan baya Dan Allah Dan annabi baffah ka temaka kacire dokar da kasa Mana Ni da nabil ya sauwake Mata sukama gabansu su koma in da suka fito har in da muke Dan masifa muna karyawa tsohuwar Nan tazo ta samemu tahau Mana masifa Wai su tuwo da Koko da kosai suka sani Dan kauyanci tin ajiya nabil yakuma fadamin bayasan yarinyarnan ko ganinta bayaso yayi ya tsaneta karfa murasa nabil baffah kadau mataki Dan Allah
Baffah yace du kanku kunemi waje ku zauna zamuyi mgn da ku kowa Zama yayi baffah yakalli nabil Kai nabil dakai Zan Fara Dan Kaine yanzu komai yake hannunka na shatuwa zaman nan dan kai da shatuwa akeyinshi yanzu Dan Allah azamanka na mijinta abinda ka kulata kukeyi yadace kaifa yanzu girma ya kamaka ko kana so ko baka so Dole kana hakuri Akan wani abin in matarka tamaka karfa kamanta ko Babu aure sama kake da ita ka girmeta bare Kuma yanzu da take akarkashin ikwanka Dan Allah ba girmanka bane karka Kara kulata ku Kara raba abin fada haka gaban mutane da safiyar Allah yanzu girmannan da kake da shi agaban yaranka da yan aikin gidannan yanzu du kazubar dshi a idansu dakai da ubanka dalilin wanna abin kunyar da kukayi jiya da yau kaga kuwa yanda maaikatan gidannan suka taru awaje suna sauraran abin kunyar da kukeyi Kuma saboda suna tsoro ko rabawa Babu Wanda yashigo yayi kabi zabin da nai maka nabil insha Allahu zakaga alheri komai daran dadewa kaji jikana nimafa ina sanka Ina kaunarka kamar yanda sani yake sanka San da nake makane yasa na zabama matar aure da kaina Dan Allah kana hakuri da ita karka Kuma kulata Kaine babba itama Zan Mata fada se mgnar iya kakar shatuwa cefa matarka itace Kuma ta raini matarka tin tana cikin tsumma har zuwa yanzu kaga kuwa dolene ka girmamata karka Kara kulata kome tai maka kaima kakace awajanka yanzu kaga ka kona Mata wuya saboda zafin Rai irin naka Dan Allah karage zafin Rai bashi da anfani arayuwa kaji nabil Allah yai maka albarka
Kekuma shatuwa nabil mijine awajanki dolene ki bashi girma Kuma kibishi sau da kafa aure yafi karfin Wasa Babu raini tsakanin miji da Mata daga yau se yau karna karajin wani abin yafaru na fada tsakaninku Dan Allah kuji tsoran Allah ku zauna lfy kiwa mijinki biyaiya aljannarki tana karkashin kafarsa se yadaga Zaki shiga karki Kara dagawa mijinki ko da muryane bare har takai ga niyar zaku illata juna da makami yanzu kema kin girma bakamar da bane da Baki da aure tinda kike kin taba ganin babarki suwaiba da umaru suna irin abinda kukeyi daga jiya zuwa yau ko Kai nabil tin da kake kataba ganin Fatima da sani suna fada to karna karaji kun yi ku zauna lfy ku Zama abin alfahari adangi da duniya gaba daya kodan yaran da zaku Haifa gaba inma mafarki like ki farka aure dai anriga an daura Babu rabuwa mutu karaba ke da shi inma zaku koyi San junanku to ku ku koya Dole muma wasu daga cikinmu dahaka muka so namu matan shatuwa dolene ki girmama iyayan nabil wannanfa da kike gani Kika fasawa Kai jiya yau Kuma Kika kwadamai karfe abaya uban mijinkinefa karki kuma gida dayafa zakuyi rayuwa kuke haka karna karajin bakin wani daga cikinku ku tashi ku tafi nagama daku Allah yaimuku albarka Allah yabaku zaman lfy yakade fitina Amina maida shatuwa dakinta
Kafin su tafi iya ta kalli nabil tace me mugun Hali kadaiji me Wanda ya haifi ubanka yace saura kaki ji Dan Allah jibi yanda yake ta huci kamar wani mayunwacin Zaki Tai maza ta toshe bakinta au yacefa in na Kara kiranshi da wani suna ze ciremin hakwaran gaba da suka rege na bakina Wai jiya wanama suna naji kakira ubanka dshi ko miss miss kome Kai Kuma naji kace Wai kana Dan miss miss ko me usuman Daman gwaunati mukamin da tabawa danka kenan mukamin Kiran maguna miss miss Kuma naji yakira fetir Daman du uban kudinnan da yatara da mukamin kiran miss miss ya tarasu Ashe magunama na da daraja akasar Nan ban saniba dakai na kirkine sani ai da inna komawa mazagai da nasa na tarama maguna dayawa in zan dawo ganin shatuwa na tahoma da su to baka da mutunci daga Kai har danka me shigar Mata
Me hajiya Fatima da Amina zasuyi inba dariyaba hajiya Fatima tace nabil tafi daki ka kwanta kaji ka huta rabu da iya Wasa take muku kema shatuwa jeki kwanta ki huta Kan akawo Miki abinda kike din
Bayan su nabil sun fita
Baffah yace iya na dawo gareki Dan Allah Dan annabi karki Kuma kula nabil kome yai Miki jikankine shi Kuma sirikinkine ki Dena kula sani kome yai Miki kizo ki fa da min shatuwa Kuma namiki alkawari nabil Babu abinda ze Mata ga Fatima za tana kula da shatuwa da Nabil yanzu anjima Ni da ke zamu koma mazagai Kayan dakin shatuwa anyafe du za ai Mata anan ki kwantar da hankalinki Kuma in an kwana biyu akai akai zamuna zuwa Ni da ke muna ganin yaran muga Kuma ya suke Zama kije dakin shatuwa ki shirya anji zamu tafi Allah ya kiyaye gaba
Iya tace habawa ai in ban ciba Babu wani bayani bana Kuma Jin ko wace mgn Ni fa afah bani abinda nafi wayo naci bazan iya cin Kayan da mugayannan suke ciba akawo min Koko da kosai ko tuwo ko Yar tsala da kunun tsamiya
Baffah yace karki da mu du NASA ai Miki kije zaa kawo Miki
Tace to yanzu naji zance shimafa wannan kaja Masa kunne Dan Naga har yanzu wani gani gani yake min Kuma Ni da naso mu Dan Kara kwanaki Dan wlh bazan iya rabuwa da shatuwa ba Kuma wlh Babu inda zani Ina nan Kuma ai nazata nice Zan Mata zaman daki
Tatashi ta fice tana sababi
Baffah yace sani kaban kunya wlh kabani mamaki sani da iliminka da hankalinka kake kula tsohuwar Nan Kuna Raba abin kunya gaban yaranku Kai sani bakaji kunyaba ko mukamin da kake dash na MINISTER baka dubi girmanshiba saboda San danka yarufema Ido ka daka ta tsohuwar nan kuka dinga Raba abin kunya gaban su nabil ita ai yadace Kai Mata uziri akwai tsufa na damunta da rashin ilimin Kai kumafa wlh kaiwa kanka fada kayi kokari ka hada Kan yarannan su zauna lfy Kar na karajin makamancin haka yasake faruwa
Yace to baffah kayi hakuri Amma gaskiya inajin tausayin nabil wlh
Baffah yace au du abinda nake fada be shigi kunnan kana ko
Katashi ka tafi kaima da mgnar da zamuyi da fatima
New writer's
Hakan Take
0 Comments