BAFULLATANA hausa novels cmplt

 


COMPILED BY

ESHAAT SMILER 

HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS

WASAPP 08066360176 FOR MORE


?🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 1*



Ina me farawa   da sunan Allah subahanahu wa  ti'allah  Wanda shine zemin jagoranci rubuta wannan littafi nawa,  INA me roqon Allah daya  bani ikon gamawa lfy,,

Wannan lbariine da ya faru da gaske ba wai qagaggen labari bane, cikin ikon Allah zan  fara  kuma in gama da ikon sa.! 


                       ***


Tafiya suke  cikin daji tare da shanunsu  wata matashiyar yarinya CE wadda bazata wuce  shekaru goma  sha hudu ba she kuma dattijon dake  kusa da ita  da alama dai mahaifin ta be, cike da damuwa yarinyar ta daga  manta ta kalli mahaifin NATA cika da kulawa tace   wllh Baba nagaji kawai ka tafi  idan na huta  zan tawo cike da damuwa ta ware maganar

Cike da kulawa mahaifin nata  me kallonta sannan yace to rabe, amma fa ki kula sosai  a nitse ta amsa da to baba,  yana kaiwa nan ya juya  ya nufi hanyar  gida, yana tafiya  Rabe ta nufi wata bishiya dake gefanta ta zauna dan ta huta  a nitse ta core takalmin robar dake  wafarta tana  cirewa ta shin gida, bata  jima da kwantawa ba bacci ya dauke ta sabda gajiyar data yi mata yawa kallo daya Zak ayi mata ka fahimci tana  jin dadin baccin da take

A hankali iska me dadi ta fara kadawa can kuma se  aka fara iska me qarfi wadda itace ta zama sillar  farkawar rabe  daga  bacci a hankali ta daga  idonta zama  aiko da sauri  ta mike tafara  kada shanun tana  fadin  su kama hanyar  gida  cikin harshen fulatanci Yayi maganar aiko se  shanun suka fara tafiya kamar  yana tace  musu  suna cikin tafiya aka fara ruwa kamr wasa can kuma se ruwan ya balle  kamar  da bakin qwarya aiko ruwan nan haka yayiwa Rave dukan tsiya amma itako ko a jikinta wai an tsikari kakkausa inji 'yana magana lol

 Cike da annashuwa take tafiya tana  tsalle tana  kuma shiga  cikin ruwan da ya taru a kan hanya aiko jikin ta yay jajir  da jar qasa   haka tai tayi  har  seda ruwan ya dauke sannan ta kama hanyar  gida basu jima ba suka iso gida seda ta fara kai shanun cikin garken  su sannan ta qarasa inda  bukkokin su suke  da gudun ta ta qarasa bakin  qofar da zata sada  ta da dakin  matar babanta da sallama ta shiga  tare da fadin  inna na dawo cike da bacin  rai tare da tarin tsana take kallonta, cike da masifa ta fara CE mata ki fita  ki bani guri shegiyar yarinya me baqin jinin tsiya har yanzu kinqi auruwa sabida baqin jininki uwarki ma a tsiyace ta qare  kuma kema a haka zaki qare muddin ina  numfashi,

Tunda ta fara maganar  Rabe me kallonta cike da rashin fahimta dan ita  harga Allah bata  fahimci  abinda innah Laure  take nufi ba Sam  kullum tana  gaya mata haka  amma Sam abin baya damun ta amma kuma meyasa take yawan gaya mata haka?  Kuma meyasa take yawan tunani akan magar innar a yan  kawanakin nan?

Cike da mugunta inna Laure ta dauki kwanon dake  gabanta ta jefi Rabe dashi a gishi aiko nan da nan mini ya fara fita  a goshin ta a gigice ta juya ta nemi  hangar fita daga bukkar dan Neman agaji sabida gigita da tsoron jini da Rabe keda shine yasa ta nufi hanyar garken shanunsu  aiko se sukayi kacibus da mahaifin ta  wato malam moddibo,

Cike da tashin hankali take firta innanillahi'wainnah'ilaihirraji'un

[8:47PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 2*


Cike da tashin hankali ya nufeta tare da kama goshinta  da sauri  ya kama hannunta suka nufi dakinsa dan yasa mata maganin daze tsayar da zubar jinin, cikin ikon Allah kuwa jinin ya tsaya,, amma sedai goshin ya kumbura sosai kuma Yayi jajzir kasancewarta fara, a hankali ta shiga  sauke  numfashi sabida zafin da gurin ke  mata cikin sanyi murya  baba ya fara magana Lamar haka

Rabi'atu kiyi haquri da rayuwa kamar  yanda nake gaya miki  kullum kuma dik abin da ze dinga hadaki da Laure ki dinga kauce mashi  sbda bata  da burin daya wuce ta illatamin ke, kuma sanin  kanki  be bani da kowa yanzu seke tunda na rasa mahaifiyarki na rasa wani bangare na rayuwata  shikuma dan uwana tuna kina jaririya aka nemashi aka rasa seda ga baya  aka samu gawarsa  a bakin  hanya, run daga lokacin muka dena bin titi da dabbobin mu, tunda na rasa iyaye na ban qara samun farin ciki ba seda na auri mahaifiyarki, amma itama daga baya  Allah ya karbe ta, ta rasu  ta barmin ke  tun kina shan nono  a haka kina fara girma  ina  kula dake

Bayan rasuwar mahaifiyarki da shekara 2  malm iro yazomin da shawarar na qara aure sabida ki samu rayuwa me in ganci, cike da damuwa  na kalleshi nace mai yanzu iro wace macce zan aura wadda zata Iya kulamin da Rabe?? 

Har ga Allah bana  so ta rayu da ciwon maraici cike da kulawa malm iro ke kallon sa har ya gama mgana,,

Can kuma se Yayi murmushi yace zan baka  qanwata Laure ka aura nasan zata riqeta da gaskia, badan  zuciyata ta ameence ba na yarda nace zan aure ta 

Da malam iro ya fahimci zuciyata bata  gama amincewa da mganar auren ba se ya sake murmushi a karo na biyu yace indai ka amince ka aureta nikuma nayi maka alqawarin zan zama me koyar da ita  ilimin addini  cike murmushi ya qare maganar,

Batare da tinanin komai ba na amince zan auri Laure. Ashe abinda ban sani ba shine sanadin tarwatsewar rayuwar gidana da farin  cikina na auto ba ya qare maganar tare da matsananci kuka😭😭

A nitse Rabe ta rarrafo kusa da mahaifin nata ta rugumeshi tana  kuka tare da share mai hawaye da tafin hanunta   seda moddibo Yayi kukan me isarsa sannan Yayi shiru, cike da kulawa yace  kinci abinci ko?  Da sauri  ta daga masa  kanta  alamar  ae  kuma a zahirin gaskia bata ci ba the ae  ne  kawai dan hankali n mahaifin nata  ya kwanta

Moddibo yay murmushi yace to maza tashi ki tafi  daukar karatu maza jeki kuma banda tasayawa wasa kinji Allah ya albarkaci rayuwar ki Rabe na  

Ta amsa da amin sannan ta tashi ta nufi makarantar allon  malm iro inda  take daukar karatu

Dik da cewa su fulanin daji ne  amma hakan baya  hanasu karatun addini dik cikin sa' oin  Rabe babu wacce batayi aure ba se ita  da ruqatu sune kawai suka rage a yaran da basuyi aure ba 

Rabe kyakkyawar yarinya ce  kallo daya zakai mata ka fahimci hakn  tana  da many an idanu tare da gashin gira me yawa  hancinta dogo ne  sosai kamar na mahaifin ta sannan ya a da dan fadi kadan  labbanta ma daidaita ne kuma suna da dan tudu kadan   tanada yalwataccen gashin kai ma'ana yana da tsayi sosai, Rabe doguwa ce  amma ba sosai ba  kallo daya zakayi mata ka fahimci tana  da kyau  da diri irin na fulanin asali, Rabe miskilace ta ajin qarshe magana ma ba damunta tayi  ba balle  ma tayi  ta sedai hakan baya hanata  Haida muta ne   rabe yarinya be ma'abociya fara'a da son karatu hakan ne  yasa malm iron ke qaunarta  sosai

Sbda tana  gane  karatu sosai  koda wasa  bata  sakewa samarin rugar tasu wannan ne yasa suke cewa tana da girman kai , amma a zahiri sam ba haka bane, a nitse ta qarasa makarantar ba Wanda yazo se ita  kadai  tan zuwa ta ajiye allon ta ta dauki tsintsiya ta share gurin sannan ta shimfida tabarman kabar tahau ta zauna ta fara bitan karatunta dan a ranar zata wanke allon ta 

Tana cikin karatun ne  ruqatu ta qara so da sallamar ta amma rabe bata  tsayaba seda takai  aya sannan ta daga kai da murmushi ta ansa mata sallamar

Ruqatu tayi dariya tace   sannu sarkin hadda shine ko ki biyo min ko?? To ai gashi nazo  nima kuma nasan dan ki rigani wanke allo ne  yasa kika  tawo kika barni ko to ai na gane wayon naki

(cikin harshen fulatanci suke  maganar nayi haka be dan me karatu ya fahimci gundarin labarin sbda idan nayi ammafani da harshen fulatanci ba lallai wani ya fahimci abinda nake labarin yake nufi ba)

Rabe tayi dariya yace  ruqatu kenan   keada zakiyi aure kwanan nan ai kin ma kusa ki dena zuwa makarantar

Ruqatu ta hade  rai tace  to ai se munyi sauka zanyi  kuma yau saura sati biyu mu sauke  da ikon Allah  murmushi Rabe tayi sannan tace to Allah ya nuns mana sati biyun

[8:47PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page -3*


Da haka suka rufe  hirar tasu saka makon qara so wan  malm iro gurin cike da girmamawa suka gadashi ya amsa tare da sakin fuska yace dasu  qawayen juna  sukai murmushi suka sunkuyar dakai,,

Ruqatu aka fara biyawa kallonta sannan aka biyawa Rabe nata, suna kammalawa sukayi sallama da mlm suka kana hanyar  gidajensu a hanyar komawar su ne  sukai kacibus da  Aliko Wanda ze auri ruqatu, cike da fara'a suka gaisa da Rabe  ita kuwa ruqatu se boye  fiska take a bayan Rabe wai ita  kunya lol

Basu jima a tsaye ba Rabe tayimai  sallama ta nufi gida cike da tinanin me zata tarar  ta bata  dawo gida ba se yamma liqis kasancewar suna da nisa da makarantar,  cike da fargaba ta qarasa dakin da take kwana ta kwanta tare da sauke ajiyar zuciya, 

A hankali ta firta alhamdulillah, dan har ga Allah batason haduwa da inna Laure dan tasan haduwarsu ba alkairi bane, tana  cikin wannan tinanin  ne taji kamar an taba mata qofa da sauri ta mike tsaye dan a tariga ta gama tsorata  a, a zatonta innah Laure ce , da sallama ya shigo dakin  tana ganinsa ta tafi da gudu ta  rungume shi se kuma ta fashe da kuka   sosai kukan ta ke taba zuciyarsa  be hanata ba sda  tayi me isarta  sannan modibo  ya share mata hawaye yace da ita  kiyi haquri Rabe nasan tsoron Laure ne yake damun ki amma kiyi haquri wata rana se labari kinji ? Da sauri  ta daga kanta  alamar ae  a hankali ya kama kafadunta ya zaunar da ita  a bakin  katifar ciyawar dake dakin yace daga yau nayi miki  alqawarin bazaki  sake kukan rashin  uwa ba kinji ? Yana kaiwa nan a zancen sa yay hanyar fita  da sauri ta dago tace  baba kayin aure ko zan dena ganin innah Laure!

Cike da mamaki moddibo ya juyo yana kallon Rabe😳  aure kikace Rabe? Ba tare da tinanin komaiba  ta daga kai alamar ae

Jikin sa a mace ya tako inda  take ya dafata cike da kulawa yace dagaske kike kina son aure? Ba tare da fargaba ko shakkaba tace  ae baba Ina so, harga Allah bata San me ake  nufi da aure ba kawai ta fada ne dan ta samu sauqi a zuciyata

Mobabah   yay murmushi yace shike  nan zan kawo miki  miji har gida kinji?

Da sauri ta washe baki cike da yarinta tace  to babah yaushe zaka  kawo shi?? Abin ma seya  bawa moddibo dariya😃  itama murmushin tayi

A hankali ya kama kumatunta yace nan da 'yana kawanaki kadan  zan kawo miki  shi yana kaiwa nan yay hanyar fita  ya tafi masallaci, itama tashi tayi taje  tayi alwala tayi sallah sannan ta tashi ta nufi dakin babanta, tana shiga  ta sameshi a zaune yana Hada magunguna, dayake yana bada magani  irin na Gargajiya  dik rugar su shi ake  kira idan rashin lafiya ya samu wani cikin ikon Allah kuwa ana dacewa da maganin sa,

Da sallama  ta shiga  ta zauna,,,, tayi shiru bata ce  komai ba  ta hakan ne ya  fahimci yunwa take ji  be ce  mata komaiba ya dakko kwanon dake gefansa ya mika mata da sauri ta karba  furace da nono   nana da nan ta kafa  kai tafara sha  yanda take shan furar ne abin ya bawa  moddibo mamaki a nan zuciyar sa ta fara zargin anya kuwa Rabe taci  abinci yau kuwa???

[8:48PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 4*


Tabbas ze Iya daukar komai amma fa banda horon  yunwa  a fisace ya tashi ya nufi bukkar Laure ko sallama be mata ba ya hauta da bala'i kan cewa ze jure  komai da zatai mai amma fa Sam  be yarda da horon  yunwa ba

Tunda ya fara masifar Laure ke kallonsa  cike da mamaki sabida tunda take da moddibo be taba daga mata murya ba balle yay mata fada, Ashe haka moddibo yake??  Tabbas ta yarda ransa ya bacci sosai  shiyasa bata CE masa  komai ba tunda ya fara  fadan, idan tace  zatayi magana to tabbas komai ze Iya faruwa Wanda kuma ba lallai yay mata dadi ba

Yana gama zazzaga mata yay gaba ya barta da fargabar halinsa

Yana futa dakinsa ya nufa  da sallama ya shiga  dakin inda  ya bar Rabe anan ya sameta  da fara'arta tace  sannu da zuwa yay mata murmushi ya shafa kanta,  sun jima tana yi masa  shirmen hira har ya gaji yace taje tayi bacci,, ayko fir  taki  tafiya wai seya rakata, haka kuwa akayi har dakin ta  moddibo ya kaita seda ta fara bacci sannan ya tofa mata adduah sannan yay waje 

Wshe  gari da zanyi safiya  Rabe ta fito cikin shirinta na tafiya kiwo, sanye take da kaya irin nasu  na fulanin asali,qarta  kuwa sanye take cikin wani rufaffen takalmi na roba, 

Dakin moddibo ta nifa  da sallama sannan ta shiga  a zaune ta sameshi yana Karin kumallo, da fara'a ya dubi Rabe yace qara so kusa dani mana  mamana? Cike da fara'a ta qarasa jikn Baban nata  cike da soyayya ta fada jikin sa 

Tare sukayi Karin kumallon dashi bayan sun gama ne suka fito tare a waje  sukaci karo da Laure. Aiko seta hde rai kamar taga  mutuwar ta 

A dan tsorace rabe ta gaisheta, seda ta faki idon  moddibo sannan ta wtsawa rabe wani kallo aiko da sauri Rabe ta koma  bayan moddibo ta qanqameshi  bece komai ba ya kama hannunta suka fice daga Gidan 

Suna fita  garke suka nufa  dan su fita  kiwo

A nitse ta kallo moddibo tace  baba yau ni kadai zani  kiwo na  kaga se mu raba shanun biyu kai kayi hanyar gabas nikuma nabi yamma  idan muka dawo se a ga nawaye sukafi qoshi ko?

Cike da kulawa yace mata to muje sena raba mana ko,  da sauri take binsa cike da zumudi zata kiwo ita  kadai

Basu dai lokaci  ba ya raba shanun gida biyu ya Tisa  nasa  yay gaba  itama tayi gaba  seda yay mata kashedin ta kula da kanta  sosai kuma kada tabi ta hanyar da bata da kyau ma'ana  banda bin titi  sbda ya tsani bin titi tunda ya rasa qaninsa  zakariya😭

Tafiya take cike da kwanciyar hankali daganin ta kasan tana cikin farin ciki da walwala haka sukaita yawo a cikin dajin   seda suka dau lokaci  me tsayi  sannan Rabe ta lura lokacin zuwa makarantar ta Yayi 

 Dole ta kora shanun suka kama hanyar gida, koda ta dawo seta fahimci babanta be dawo ba, kuma kullum shine yake rigata dawowa daga kiwo to meyasa yau be dawo da wuri  ba??

Bangaren moddibo kuwa yana hanyar dawo wansa  daga kiwo ne  se ya hangi kamar mutum a kwance da Yayi zaton ko hutawa yake amma dya qaraso seyaga sabanin tinanin sa

Yaro ne matashi sanye yake da wata  tsaleliyar shadda light blue an masa  dinkin jamfa kansa  babu hula kansa  wani qaton Sara  ne hakama qirjin sa da kuma bayan sa

Jikinsa dik jini ne  a jiki dik da saran dake jikin sa hakan baze hanaka fahimtar yana da kyau ba cikin sauri moddibo  ya qarasa kusa dashi ya dago shi a nan ne ya fahimci yana numfashi, sabida tsabar riki cewa ma  ya rasa ta India ze fara bashi taimako,, (likitan Gargajiya kenan  lol)

Can dabara ta fado masa  ayko da qar  moddibo ya Iya dagashi ya Dora a bayan saniya daya ya daure  shi a jikinta ta yanda baze fadi ba suka nufo  hanyar gida

Sun jima sannan suka qara so gida ,,, a qofar gida suka hadu da Rabe dan tunda ta dawo taqi shiga  Gidan ta tsaya jiran moddibo

Da sauri moddibo yace ta shiga  da shanun cikin garke , ba tare da ta kula da mutumin dake bayan saniyar ba tayi gaba da qar  moddibo ya kwanto shi daga jinkin saniyar Yayi hanyar dakinsa dashi, suna shiga ya kwantar dashi  akan tabar marsa  ya mike ya dakko boronsa dayake sa magani   ya ajiye ya sake dakko wata qarya  ya ajiye qaho ne a cikin qwaryan da kuma aska  take moddibo ya yage  rigar dake jikin matashin subahanallah abinda ya firta Neman sabida yanda yaga jini ya taru a gefan qirjinsa na dama  da alama seda aka dake shi sannan aka sareshi

A nitse ya dauki askar ya daidaici gurin da bakin jinin ya taru sannan ya yanka gurin nan da nan wani bakin jini ya fara fita   a hankali ya shiga  goge mai seda ya gama gaba daya sannan ya shiga  samai magana a jikin raunukan bayan ya gama sa masa maganin ne ya fito yana kwadama Laure kira, jiki na rawa ta qaraso  tace gani mlm 

Yace maza ki kawo min ruwan zafi   jiki na rawa  ta tashi ta hada wuta ta Dora ruwan zafin

[8:48PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 5*


Ta dan dauki lokaci  kamin ta kawo ruwan zafin sabida sha'anin itace se'a hankali, dakyar ta samu wutar ta kama ba'a jimaba ruwan ya tafasa 

Qwarya  ta daukko ta juye masa  ruwan a ciki  ta nufi dakinsa dan ta kaimai ruwan. Sallama tayi  sannan yay mata izinin shigowa ta shiga

 Ya karbi ruwan sannan ya dakko wani farin  saki yasa a cikin ruwan sannan  ya dakko wani garin  magani  ya zuba a cikin ruwan  ita  dai Laure banda kallon moddibo ba abinda takeyi  bakinta fal  tambayoyi amma ta rasa ta inda  zata fara yimai Tambayar. Suna cikin haka ne Rabe ta shigo dakin da sallama  da fara'arta take kallon moddibo tace  bab wannan shine mijin daka  samo min din

Cike da damuwa ta qarasa maganar sabida se a lokacin ta lura da raunin dake jikinsa  moddibo be damu da ya bata amsa ba sabda shi gaba daya hankalinsa yana kan wannan matashin

Kamar zatayi  kuka  tace  baba amma wannan baqo ne ko?  Ciwo yaji ? A lokaci daya rabe ta dinga jefo masa  tambayoyi

Ba zato Laure ma ta jefo tata tambayar  mlm a ina  ka samo wannan yaron? Kai yanzu baka jin tsoron daukko shi ya zame mana masifa nan gaba?

Moddibo ya dube  ta cike da murmushi yace haba  Laure shin kin taba ganin inda  taimako ya zama masifa? Tayi shiru batace komaiba, daya ga bata da niyar magana seya  cigaba da maganarsa tin daga Hauwarsa da yaron har zuwa dakko shi da Yayi be boye  musu komai ba

Nan da nan idon Rabe ya fara zubda hawaye dama  su Rabe da arahan hawaye lol

Ita ko Laure ko a jikinta balle ma tausaya masa , dataga abin ya isheta ma seta fice daga dakin tana ta bambami wai moddibo ze ja  musu bala'i

Shidai  be kulata ba sema cigaba da gogewa matashin jiki da ruwan maganin daya hada  yakeyi

Cikin muryar kuka  Rabe tace  baba,  ya dago yana kallon ta sedai bece komai ba a hankali tace  dame  zan Iya taimakon ka?

Moddibo Yayi murmushi yace so nake kullum ki dinga yi masa  adduar samun  lfy kinji? Ta daga kai alamar gamsuwa moddibo ya share mata hawaye da hannunsa sannan yace ta tashi ta wuce daki ba musu ta mike ta tafi  dakin kamar yanda yace mata

Ranar dai Rabe bata samu zuwa makarantar allo  ba

A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah  yau  matshinnan ya cika sati biyu a gidansu Rabe amma ba abinda yake  motsi a jikinsa sedai kawai alamar numfashi, tun suna sa ran tashinsa har suka fara cire ran farkawar sa nan kusa

Yanzu Rabe CE take kula dashi  itace ke zuba masa  kunu a baki da ludayi tin baya shiga  bakin har yazo ya fara shiga  kadan  kadan  

Kallo daya zakayiwa matashin ka fahimci ya rame  sosai akan ranar da moddibo ya kawoshi Gidan ,   tun  ranar da aka kawoshi gdan Laure bata qara leqowa dakin ba dan acewar ta idan masifar ta zo ta afkawa moddibo da Rabe,  hmmm su Laure akwai bakar zuciya lol

Wasa wsa  Rabe ta shafe  kwanaki bata zuwa makaranta ko kiwo bata zuwa, amma Sam  hakan baya damunta  sabda tsa a ranta  taimakon mutum yana daya daga cikin dabi'u masu kyau

Mlm iro yazo yafi  a qirga kan ta dawo makarantar ayi suka da ita  amma fir taki  yarda ta koma  dan a ganin ta idan ta fita  ko qofar gida waye  ze bawa bako abinci?

Hmmm kuji fa Rabe da qarfin hali

 Moddibo ne ya shigo dakin hannunsa riqe da wata saiwa ya mika  mata yace maza jeki tafasata ki kawo min kinji

Da sauri ta karba  taje ta hado qirare ta bada wuta ta Dora maganin  ba'a dau lokaci me tsayiba ruwan ya fara dahuwa   seda mutar ta mutu  sannan ta juye  maganin a qwarya ta kaiwa moddibo da murna ya karba  yana sa mata albarka  seda maganin Ya fara hucewa moddibo ya dago kan matashin ya shiga  zubawa matashin abaki, dikda cewa ana zubawa wani na zubewa ansamu wani ya shiga  cikin nasa, bayan ya gama ne ya shiga  goge masa  jiki da sauran maganin

Kullum haka  suke masa  har aka shafe wata ba wani ci gaba, gashi Rabe bata da aiki  se kuka  ga jarabar Laure  ga kuma ciwon bako hakan ne yasa dik tabi ta rame  se hanci  da idanu

Abin yana dagawa moddibo hankali  to amma bashida yanda zeyi illa  kawai yayta addu'a 

Laure CE ta Shiva dakin moddibo da sallama  ya amsa mata da sakin fuska  a dakile tace  yame  jiki ya amsa mata da sauqi

Moddibo ya sake murmushi a karo na biyu yace hala  fita  zakiyi?  Da fara a tace  ae dan dama ta rasa ta India zata fara tambayar sa cewar  zata fita,  a takice yace mata seta dawo ta gaida  su iro da gwaggoji. Bata amsa ba tayi gaba bayan fitarta ne wani yaro hamisu yazo yay sallama da moddibo kan cewar  mahaifin sa ba lafiya  shine yace ya kirashi moddibo be bata lokaciba ya fito suka wuce har sun fita ya dawo yace Rabe ta koma dakinsa sabda maralafiyan 

Da sauri ta mike tare da yi masa Allah kiyaye ta koma dakin ta zauna tunda ta zauna ta zubawa matashin ido ba tare da tace  komai ba se hawaye cikin muryar kuma ta fara magana, wai kai yaushe zaka tashi ne?shin kasan yanda mukeji a ran mu? Dan Allah ka tashi ko hankalin banana ze kwanta! 

Ta jima tana suru tanta kamar wata zararriya sannan tayi shiru ta cigaba da kukanta fukarta dik tayi ba idanunta suka kumbura abin ka da far in mutum

[8:49PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 6*


Ta jima tana kukan sannan bacci ya dauke ta 

A hankali matashin ya fara motsa hannunsa daqar ya Iya daga hannun sa ya maidashi qirjinsa, jin da tayi kamar motsi ne  yasa ta bude idanunta daqar ta maida  kallon ta gareshi, ayko seta qara bude idanunta sosai alamar mamaki

To ya akai  hannunsa ya koma qirjinsa? Tambayar da take mata yawo a zuciyarta   Kenan

A nitse ta maida  kallonta kan fiskarsa, ta jima tana kallon sa  kamar bazata dena ba kamar a mafarki taga  yana motsa idanun nasa  ai seta qara zaro idanunta 😳 cike da mamaki 

A hankali ya fara bude idon  har ya gama bude shi gaba daya a kan fuskar Rabe

A firgice  ya fara qoqarin tashi yana so ya ja  baya sabida tsoratar dayayi

 Yana ja baya ya saki wata qara sabida wani azababben zafi dayaji a gadon bayan sa , bashiri ya koma ya kwanta yana maida  numfashi, da sauri rabe ta sake matsowa kusa dashi  sosai  sannan ta fara magana cikin harshen fulatanci take cemai  kayi a hankali sabda jikin ka akwai rauni! 

Tunda ta fara magana yake  kallon bakinta har ta kai harshen maganar ta dikda  cewa be gama fahimtar abinda take fada sosai ba   hakan be hanashi qare mata kallo ba  tana gama maganar ta sakar mai murmushi tare da mikewa ta fita daga dakin ,

Tana fita daki  ta nifa ta dakko wani rufaffen kwano sannan ta dawo ta sake zama dab dashi  ta zauna  ta kuma sakar  masa murmushi a karo na biyu sannan tace  masa ya tashi, dataga be gane me take nufi ba setai mai nuni alamar ya tashi

A hankali ya kuma yunqurin tashi a karo nabiyu amma kuma seya  kasa ze koma ya kwanta tai masa alamar a'a,  da taga  bashi da niyar dena kallonta seta mike ta koma bayan sa wai zata dagoshi,,  cike da mamaki yake  kallonta tare da mamakin  qarfin hali irin nata, jibeta 'yar  qarama da ita  wai zata dagashi, lallaima yarinya nan yana cikin zance zucin da yake  ne yaji ta cakume shi da sunan zata dagashi, ayko seya  sake sakin qara sabda zafin dayaji na ciwon dake bayan sa bata damu da ihun dayeke ba har seda ta zaunar  dashi,

Daqar ta Iya zaunar  dashi har tana zufa 

Tana zaunar  dashi ta zube a gurin tana mayar  da numfashi, 

Dakyar ya Iya dago idon sa da suka fara canza kalah dan azaba ya kalleta lokaci daya itama ta dago ido suka bada ido,

Suna hada ido gabanta ya fadi, da sauri tayi qasa  da idonta  a nitse Takai hannunta kan kwanon da ta dakko a daki  ta bude fura ce  da nono  ta miqa msa  tace yasha, ya gane nufinta a hankali ya fara dago hanun  amma kuma seya  kasa 

Data fahimci hakan seta mike daga inda  take  ta dauki kwanon ta matsa kusa dashi ta zauna sannan tasa  ludayi ta juya  ta debo ta miqa masa kusa da bakinsa, ya jima  yana kallon ludayin  sannan ya maida  kallonsa  kanta, 

Tambayar dayakewa kansa  itace wai shin inane nan?

Kuma wa'yannan su waye?

Wannan yarinyar wacece ita?

Waze tambaya  ya bashi amsoshin wannan tambayoyi nasa?

Data ga bashi da niyar bude bakin ne seta sake miqa masa ludayin har yana taba lips dinsa , sa'a sannan ya dawo daga duniyar tinanin da yakeyi, a nitse ya bude bakin ya fara seeping, se kuma ya kauda  kansa da sauri kamar Wanda ya tina  wani abu,

Daqar ta samu ta lallabashi ya sha sosai.

Bayan ya gama sha ne ta dakko masa maganin sa shima ta bashi yasha ,  tunda ta bara  bashi maganin yake  mamakin yarinyar

Badan komai ba se yanda take dawainiya dashi, harga Allah ya jinjinawa jarumtar yarinyar,   tana gama shafa mai maganin ta taimaka masa ya kwanta yana kwanciya moddibo ya shigo da sallamar sa aiko Rabe da gudu ta nufeshi ta rungumeshi tana fading baba ya tashi wllh ya tashi,

Kana kallonta zaka  fahimci tana cikin barin  ciki😃😃

Tunda ta fara magana moddibo yake kallonta da murmushi yace to  yanzu kuka  ya qare ko?

Da sauri ta rufe  fuskarta da zarazarn hannayenta tana dariya,

Tun  shigowar moddibo matashin yake kallon su  har zuwa sanda  Rabe ta rungumeshi, se kallon su yake cike da burgewa da alama  mahaifin tane ya fada a zuciyar sa, sabda suna bala'in kama da juna!


Wai shin wanene wannan matashin??????


INA MIQA SAQON TA'AZIYAR SURAIYYAR  surayyah ga Uwar dakin kuma aunty na Khadeeja candy

inayiwa sauran 'yan  uwa ta'aziyar wa'yanda suka rasa fatan Allah ya gafarta mana gaba daya👏(CIBADO TAKU A KULLUM😘)

[8:49PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 7*


A nitse moddibo ya qarasa kusa da matashin ya sunkuya da murmushi a fuskarsa yace sannu da jiki kaji

Cikin harshen fulatanci moddibo Yayi maganar,  ido kawai matashin yake bin moddibo dashi sabda Sam besan me yake fada ba,

Moddibo ya fahimci matashin baya jin fulatanci shiyasa yay murmushi sannan yace dashi sannu cikin harshen Hausa

Matashin ya bude baki da nufin ya amsawa moddibo amma sedai muryanshi bata fita sosai sabda mura  data kamashi ( abinka  da Wanda be saba da wahala ba lol)

A nitse moddibo ya fara magana  kamar haka

Yaro nasan zuciyarka a cike take da tambayoyi akan mu , ko?

Kuma nasan zakaso kasan meye dalilin zuwanka wannan gurin? 

To magana na gaskia itace  ina  hanyar dawo wata daga kiwo ne Allah ya hadani dakai kana kwance a cikin jini  !!

Na Dade bana bin hanyar amma dayake Allah ya qaddara semun hadu dakai seya  nufeni da bin hanyar Ashe  rabon  in taimake ka ne,

Safari nazata  ma ka rasu amma Dana tabaka sena fahimci kana numfashi  haka mukaita kula da rauni kan jikin ka har Allah ya amince mana ka tashi, 

Nan da nan idon matashin ya kawo ruwa ba komai ne yasa shi hawaye ba se irin karamcin da moddibo yay masa, 

Yanzu babbar damuwarsa yanzu be San halin  da dadynsa yake ciki  ba!

Cike da kulawa moddibo ya dafashi  yace kayi haquri yaro nasan dole zakayi kewar gida amma ka qara haquri jikinka ya qara qwari seka tafi ko ? A nitse ya amsa  tare da yiwa moddibo godia,

 Har moddibo ya mike se kuma ya sake sunkuyowa yace da matashin yaro ya sunan ka?? 

A nitse ya firta   Muzaffar Abdulwahab

Moddibo yay murmushi yace dakyau, dik wannan hiran da suke Rabe na jinsu a nitse ta qaraso  kusa da matashin  da murmushi a fiskarta tace sunan ka dama  zafar  ne?

Muzaffar yay murmushi a karo na farko yace muzaffar nace ba zafar  ba,

Tun daga lokacin da zafar  yay murmushi har zuwa sanda  ya gama magana  take kallon sa , 

Ba komai take kallo ba se tsabar kyau irin nasa  bata tabbatar da shi kyakkyawa bane seda yay murmushi,

Mutane dayawa suna fadar tana da kyau amma yau taga  Wanda ya fita kyau da tsarin halitta,

Nima kaina  seda na dan tsorata da kyansa lol)

Seda moddibo ya dafata sannan ta dawo daga duniyar tinanin da take,,,

 A daburce tace baba yaushe za'a kuma bashi abinci?

Harga Allah ba abinda tayi niyar fada ba kenan  tsabaragen daburcewa ne yasa ta fadi  haka,  sosai moddibo ya fahimci halin  data ke ciki  amma kawai seyay murmushi, ya fita daga dakin

A hankali muzaffar ya dago kansa  ya kalleta yace ya sunan ki?   A taqaice tace masa Rabe

A hankali ya kuma maimaita sunan, a taqaice yace mata thanks for everything.

Daga haka ya koma ya kwanta,, ta jima tana juya kalmar a ranta  dikda cewa bata San meyace ba amma setaji Kalmar tayi mata dadi,,

Be sake cewa komaiba har yamma 

Moddibo ne ya shafa masa magani sannan yasa Rabe ta Dora masa ruwan zabi ta kawo masa  tana kawowa tayi waje  abinta, moddibo ya tashi ya nufi inda  muzaffar ke kwance  a hankali ya fara kiran  sunan sa, 

A nitse muzaffar ya bude idanunsa  a fiskar moddibo,

Murmushi Yayi masa sannan yace ka gyara zan goge ma jikin ka , a nitse ya fara qoqarin tashi amma kuma seya  kasa tashin  moddibo ne ya taimaka masa ya tashi zaune, wani farin saki moddibo ya qara dakkowa ya tsoma a cikin ruwan ya fara gasawa muzaffar jikinsa, dik da cewa jikinsa nayi masa ciwo sosai hakan be hana moddibo gsa  masa ba

Yana gamawa ya dakko maganin shafi ya shafa masa sannan ya taimaka masa yayi alwala, sannan ya shiga  rama sallolin da ake  binsa ya Dade yana yi dik da cewa besan adadin kwanakin daya zauna a qauyen ba,

Seda ya dau lokaci me tsayi sannan ya idar, moddibo ne ya tai maka masa ya kwanta sannan ya dakko wani zanin saki ya lullube shi ba dau lokaci ba bacci yay a won gaba dashi



Kuyi  haquri da wannan bana dan jin dadi ne👏

[8:50PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 8*


Ban garen  Rabe kuwa tunda ta fita bata sake dawowa dakin ba 

Sallah ta gabatar sannan ta fito ta gabatar da aiyukan da ta saba na yau da kullum seda ta gama tsaf sannan ta koma daki  da nufin ta gabatar da sallar ishsha'i, bayan ta idar ta jima tana adduo'inta  sannan ta shafa,

Da sauri ta mike ta cire  mayafinta ta nufi katifar ciyawarta dan ta kwanta sbda sanyin daya fara busowa,

Kamar daga sama  taji an banko  mata cikin dakin aiko da sauri ta miqe sabda sanin ko wacece ta shigo, dan inda  sabo yaka  mata ace ta saba da halin  Laure,

Masifa fal ranta  ta shigo dakin tare da yi mata kallon wulaqanci tace to 'yar  gatan gata rere   to fito kiyi min ayki  dakike qoqarin kwanciya, ai wllh baki isa  kiyi bacci yanzu ba

Bata jira cewarta ba ta fincikota sukayi waje, wasu  tarin  kwanuka ta gani a jibge gefe kuma wani ruwane a cikin wata fanteka da alama  ruwan ya Dade a gurin dan haka base an fada ma ya dau sanyi  ba,,, 

Kallo daya zaka yiwa kwanu kan ka fahimci babu datti ko kadan a jikin su kawai tsabaragen mugunta ne yasa Laure tace ta wanke mata kuma tasan sanyin da akeyi ko daki  kake seka ji  a jikin ka,

Ba musu Rabe ta sunkuya ta fara dauraye kwanukan tanayi jikinta na rawa  sabda sanyi har taxi qarfin kwanukan laure  dataga bazata Iya jure  sanyi ba setai shigewarta dakin ta tabar Rabe a waje  tana fama   seda ta dau lokaci me tsawo sannan ta gama ta kikkife su, sannan ta wuce daki jikinta nata  rawa tana shiga  ta kwanta dikda cewa ta lulluba amma Sam bata dena jin sanyin ba,,

Abu kamar wasa  haqoranta suka fara haduwa da juna, nana da nan zazzabi me zafi ya rufeta  daqar ta samu bacci ya dauke ta

Ba ita  ta farka ba se bayan an idar da sallar asuba , daqar ta samu tayi alwala ta gabatar da sallar

Koda data idarma ta kasa tashi daga inda  take a gurin ta kife sabda wani irin azababben jiri data keji,

Har gari Yayi haske  sosai kowa ya fara harko kinsa amma Rabe bata fito ba,

A bangaran moddibo kuwa Yayi mamaki sosai ganin har wannan lokacin rabe bata fitoba   azatonsa ko bacci takeyi  shiyasa be wani damu sosai ba,

A nitse moddibo ya gama gabatar da komai na karyawa Wanda muzaffar zeyi Karin kumallo dashi.

Har ya gama bega  idon Rabe ba, se kuma abin ya fara damun moddibo  

Bangaren muzaffar ma ya damu qwarai da rashin ganin yarinyar  sbda daga jiya zuwa yau yana jin cewa ya saba da ita   badan komaiba se yanda yarinyar take nuna  kulawarta a Kansa

Cikeda kulawa ya dago ya kalli  moddibo tare da gaishe shi, shima moddibo ya amsa da kulawa, azahiri muzaffar yaso  ya tambayi moddibo INA Rabe take amma kuma daya kalli moddibo n seyaji baze Iya tambayar sa ba

Moddibo ya kalli muzaffar sannan yace yaro ya kamata ka tashi kaji abinci ka sbda ka samu kasha maganin ka ko?

Ba musu muzaffar ya fara qoqarin tashi dikda cewa ba iyawa zeyi ba,,

Moddibo ya saki murmushi yace yaro gaskia kana da qarfin hali sosai  ka qara haquri ka kusa fara tashi da kanka

Tunda moddibo ya fara magana idon muzaffar yana kansa  se kuma Yayi murmushi yace to baba Allah yasa , bazan gaji da qara jaddada godia ta a gareka ba sabda ka taimaki rayuwata!! Seda yayi dan shiru sannan ya sake kallon moddibo yace  thank you for save my life,,, ya qarashe  maganar tare da hawaye

Da sauri moddibo ya dafa kafa dunsa  yace kada ka damu yaro ni nayi maka dan Allah ne badan wani ba dan haka ka dena zubar da hawayenka kaima kamar da kake a gurina kuma nayi maka alqawarin zan kula da kai har zuwa ranar da zaka koma garin  Ku wajen iyayen ka ya qare maganar da murmushi,

Sosai muzaffar yake jin kalaman moddibo a zuciyar sa  harga Allah dattijon ya shiga  ransa,  moddibo ne ya share mai hawayen sa sannan ya  fara bashi kunun su irin nasu na Fulani Sosai muzaffar ke jin dadin kunun dan haka yasha sosai sannan ya cewa moddibo ya qoshi,

Moddibo yayi murmushi yace masha Allah tunda yanzu ka qoshi bari na shafa maka maganin ka se kuma kasha na shan ko?

Muzaffar yace haka ne

Seda moddibo ya gama shafa mai maganin sannan ya bashi yasha yana gamawa yace to yaro bari in je  inga Rabe ko lafia naga har yanzu bata fito ba,

Muzaffar yace hakane  kam  yakamata a duba agani ko  lfya,

Daga haka moddibo yay waje  ya nufi dakin Rabe da sallama aiko tana nan a India tai sallah jikinta se rawa  yake da sauri moddibo ya nufeta yana tambayar ta Meya sameta?

Ayko yana taba jikinta yace subahanallah!!

Rabe meya sameki be jira cewarta ba ya kinkimeta yayi dakinsa da ita  banda hawaye babu abinda ke fita a idonta a haka ya qara so dakin da ita 

Da sallama ya shigo dakin sannan ya kwantar  da Iya tunda suka shigo dakin gaban  muzaffar ya fadi ganin wadda moddibo ya kwantar  a rude yake tambayar moddibo abinda ya sameta har yana qoqarin tashi daga inda  ya ke kwance

Sosai moddibo ke kallon muzaffar tare da tsantsar so da qauna  yace yaro ka kwantar  da hankalin ka  ba wani Abu bane zazzabi ne kawai

Harga Allah moddibo yaji muzaffar ya qara kwanta masa a rai musamman dayaga  ya nuna  kulawar sa a kan tilon 'yarsa gida daya!



Fatan alkhairi ga aunty na  kuma Uwar dakina  candy komai  cibado ta zama candy CE sanadi, ngde Allah yabar qauna😘

 Ina samun  saqonku gareni masoya na kuma INA miki fatan alkairi, banyi  zaton inada masoya haka ba!

Bazan manta dake ba Aysha musa isah(nanoni)👏

[8:50PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 9*


Murmushi moddibo yay masa sannan ya juwaya ya dakko boron sa dayake sa magani  a ciki ya daukko wani farin magani  ya jiqashi a kwanon sha seda ya dan dau lokaci sannan ya dgota ya bata 

Ba tayi gaddama ba  sabda bata qin  magani

Diik abinda suke idon muzaffar na Kansu  se kallon su yake yana mamakin yanda moddibo yake Iya gane ko wani qullin maganin dake cikin jakar

Ada muzaffar be yadda da maganin Gargajiya ba sena asbiti  wai a cewarsa maganin Gargajiya baya maganin ciwo sedai ya qarawa mutum wata cutar( Niko nace dakyau bature  lol)

Segashi maganin Gargajiya yayimai  ranah, shiyasa a rayuwa kada ka raina  baiwar da Allah yayiwa wani ko wata  idan kayi hakan tabbas  bakayi Abu me kyau ba, Allah ya kyuta

A hankali seyaji abin yana birgeshi sosai  lallai ilimin baiwa ne bawai kawai ilimin sanin  rayuwa kona  addini bane kawai ilimi,  sanin  nau'ikan itace shima ilimine kinji muzaffar Abdulwahhab😊

Bata jima da shan maganin ba bacci ya dauke ta  banda zufa ba abinda takeyi, muzaffar ya kalli moddibo cike da damuwa yace  kayi wani Abu kagafa se gumi take kodai zamu kaita  asibiti ne??

Da mamaki moddibo ke kallonsa😳 yace yaro a wannan dakin kake tinanin  asibiti?

Batare da damuwar  komaiba muzaffar yace ae mana 

Nan da nan yanayin moddibo ya canza  sannan yace yaro ga ganin nan tunda na tashi da iyayena a nan muke  rayuwa asalin mu 'yan  jihar  Yola ne mu kuma maifan mu mu  uku suka Haifa  mu biyu maza se kuma qanwar mu mace guda  daya wadda bansan a inda  take ba a halin  yanzu 

Yana zuwa nan a zancensa seya  fashe da kuka, daqar ya samu ya daidaita kansa  sannan ya cigaba da cewa shi kuma qanina Wanda yake bina dashi da mahaifin da sauran yn qauyen mu ne mukayi hijjira daga dajin da muke  ciki sbda yana fashi  da suka sa mu a gaba  ba Iya fashin da  suke mana bane damuwar  har yaran mu mata qanana suke zuwa su kwana dasu a gaban  mu, wannan ne dalilin dayasa muka bar jaharmu ta asali muka komo wannan dajin   dikkan mu dakake gani  dik yana uwan juna ne,  wata rana qanina yafita  kiwo  mota ta bige shi  bamu sani ba , seda muka kwana biyu muna  Neman sa  daga baya muka tsinci gawarsa a bakin hanya,

Wata rana da yamma wasu  mutane suka shigo mana nan da sunan zasuyi mana asibiti sbda muma mu samu cigaba, muka karbe su hannu biyu Ashe abinda bamu sani ba cutarmu sukazo suyi

 Dayawa a cikin mu kasuwanci shanu suke yi   seda suka bari kowa ya dawo daga kasuwancin sa yaxo da kudi, sannan suka far make mu suka qwace komai, sannan suka kashe na kashewa, 

Tunda ga lokacin bamu qara yarda da kowa ba, kuma muka dena karbar baki koda ko daga ina  suke,  shiyasa tunda ka ambaci sunan asibiti kaga yanayina ya canza yaro,  ya qara da cewa yanzu da mutanan rugar nan zasu samu labarin zuwanka tabbas da se sun koreka kokuma ma su kashe ka

A firgice muzaffar ke kallonsa  jin kalmarsa ta qarshe wato kisa, yace to yanzu Baba meyasa lokacin da abin ya faru Baku nemi tai makon  jami'an tsaro ba ???

Moddibo ya kalli muzaffar yayi murmushi irin na takaici yace yaro  da fari  min gwada yin hakan amma daga baya se muka gane itama hukumar  se a hankali, 

Muzaffar  yayi shiru  a zuciyarsa yace  Ashe Dama a kwai  mutane masu fiskantar irin wannan rayuwa??

Tabbas Allah ne ya nufi zuwansa dan ya qara ilimi akan rayuwar duniya, 

Haqiqa baka godewa Allah da irin baiwar da yayi maka  seka ga Wanda be kaika ba sannan kake sanin Allah yayi maka baiwa

Haka kawai seya samu kansa  da jin tausayin su shiko insha Allah seya tai make su da izinin Allah

Wai ina  Laure ne  jma'a 

Tunda garin  Allah ya waye Laure ta fice  daga Gidan  sabda bata da wani buri  yanzu a rayuwata daya wuce taga bayan moddibo da Rabe  sannan kuma ta mallake dukiyar sa.

Tabdi  kujifa masu karatu!

Dama ance  yanzu ba'a maqiyin nesa ,  ya Allah ka shiga  tsakanin mu da maqiyan mu na  sarari  Dana boye


Kuyi  haquri wannan  bana jin dadi ne👏

[8:51PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 10*


A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah yau muzaffar ya cika wata biyu a Gidan moddibo, cikin ikon Allah ya samu sauqi sosai,  kuma shaquwa me tarin  yawa  ta shiga  tsakanin Rabe da zafar   sedai bazamu fassara shaquwar da sunan so ba, sedai kawai mu kirata da yan uwantaka, sabo tirken wawa, 

Washe  gari da safe  ne moddibo ya gama hadawa zafar  komai nasa  sedai rigarsa da moddibo ya tsinto shi da ita  tariga ta lalace  dan haka moddibo ya dakko masa wata rigar saqi irin tasu ta Fulani ya miqawa muzaffar da nufin ya sanya a jikin sa tare da wandon shaddar sa, ba musu muzaffar ya karba  ya sanya  rigar 

Ba qara min kyau tayi masa ba   dan fadar kyan da tayi masa ma bata lokaci ne

Bayan ya gama sawa  ne moddibo yay gyaran murya irin nasu  na dattijawa yace  yaro yau dai gashi ka warke  cikin ikon Allah kuma gashi har kana shirin tafiya, sedai kuma har yau bamu San kokai  waye ba, a yanda muka saba dakai ya kamata musan ko kai waye. Sbda mu qulla zumunci wata rana bamu San a inda  zamu sake haduwa ba 

Sosai kalaman moddibo suka shiga ran muzaffar dan harga Allah gaskia moddibo ya fada

Ya kamata ya gaya musu ko shi wanene


A hankali ya fara da cewa. Ni haifaffan garin  kano ne amma kuma ba'a farin kano na girma ba , ni kadai ne namiji a yaran da mahaifina ya haifa   kuma ni kadai mahaifiyata ta Haifa sannan ta bar duniya  

Hakan ne yasa Mayan babana suka sakoni gaba  kowacce burinta taga  bayana  hakan ne yasa mahaifina ya dauke yabar qasar dani  tun  ina  dan shekara goma ya kaini qasar India.  Gurin wata matarsa da yake aure.  Babu abinda Mami ta rageni dashi ta dauke ni tamkar dan cikinta  Allah sarki mami na.

Ban dawo Nigeria ba seda na cika shekara ashirin  sannan Dady ya dawo dani  ba yanda beyi da Mami ta biyoshi ba amma taqi sbda wani dalili nata  Wanda har yanzu taqi sanar da kowa, haka Mami tayi ta kuka da zamu dawo Nigeria

Bayan na dawo Dady ya Tara  matansa da qanne na ya sanar dasu cewar zan fara aiki  akamfaninsa na takalma dake abuja, Sam suka CE basu yarda ba sedai a hadamu da qanwata dake bina  fadilah  ai itama ta gama makarantar

Dady yayi murmushi yace shikenan babu damuwa Allah yasa haka shiyafi alkairi kowa ya amsa da ameen amma banda  Hajia  lami wadda Mike kira da  umma, tunda aka fara maganar fara aiko na har aka gama ba tace qala ba  sosai kowa ke kallonta  itakuwa ko ajikinta   seda ta gama qarewa kowa kallo sannan tace Sam bata yarda a tura fadilah abuja ba sbda it's mace ce  kuma dik macen qwari aure iyayenta suke yi mata bawai tura ta aiki na dan haka ba Inda zata sedai ta zauna a gida 

Sosai Dady ya ameence da maganganunta, dan haka ya soke  zuwan fadilah badan ran mahaifiyarta yaso ba

Washe  gari da safe Dady yace in shirya gobe  zan wuce abuja kuma jirgin sassafe zanbi  a nitse na amsa da too sannan na wuce  bangarena dan na kwanta na huta

 Yau umma CE da girki dan haka Dady a dakin ta yake. Da wannan damar  tayi Amfani gurin canza wa Dady ra'ayi wai be kamata nabi jirgi ba  ai yin hakan almubazzaranci ne kawai ya qyaleni in tuqa mota da kaina  kokuma yasa  ado ya Kaine

Da qar  Dady ya amince ado ya Kaine a mota, suna gama mganar tacewa dady tana zuwa, 

Daret dakin  Momy ta nifa wato mahifiyar fadilah tana shiga Momy tayi mata wani mugun kallo  sannan ta dauke kanta  tace to 'yar  bakin ciki meya kawoki dakina?

Umma tayi murmushi tace to sarkin jaraba  labari nazo miki dashi gobe  idan Allah ya kaimu  su ado zasu qarawa muzaffar gudu zuwa lahira,

Momy tace ke nifa ban gane ba ,

Umma tayi dariya tace to gobe  ado ze kaishi abuja  a hanyar zasu kashe mana dan iska mu huta shiyasa na shiga na fita na hana fadilah zuwa sbda mu samu mu kashe matsiyaci

Nanda nan fara'a ta mamaye fiskar Momy sannan suk tafa tayi mata sallama

Washe gari da sassafe ado yazo Dady ya rakani mota tare da yimin addu'ar suka lfy nayi sallama da kowa sannan muka kama hanyar abuja  seda muka wuce Kaduna sosai  sannan ado ya tsaida motar a wani daji babu mutane a hanyar se motocin da suke wucewa  cike da kulawa nake tambayar sa ko lfy?

Ado yay murmushi yace yallabai mtsala aka samu kozaka dan fito kafin in gyara?

Ba tare da tinanin komaiba na fito daga motar ,  INA fita ado ma ya fito sedai banyi aune ba  naji daukar qarfe a bayana  da qar na Iya juyawa dan naga waye !

Ado nagani yana qoqarin zare wuqa  da gudu na yanki cikin dajin ina gudu yana bina  har ya samu nasarar  kamani daganan ban qara sanin inda  kaima yake ba,  har zuwa lokacin da Allah ya hadaka  dani

Jikin  moddibo ba qara min sanyi yayi ba da jin lbrin muzaffar


Harga Allah moddibo ya nuna tausayawarsa ga muzaffar

[8:51PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 11*


Moddibo yay shiru tsawan lokaci sannan yace yaro idan har na fahimceka daidai, matan mahaifinka ne suke so suga  bayanka, bisa  wata muguwar manufa tasu!

Mgana ta gaskia kana buqatar abokin rakiyar da ze rakaka gida ma'ana Wanda  ze taya ka wannan yaqin dake  gabanka👉

Sosài muzaffar ke  kallon moddibo tunda ya fara mgana, sannan yace haka ne  baba amma kuma waye  zemin rakiyar?

Moddibo Yayi murmshi yace  kayi haquri yaro ka jira zuwa gobe  seka tafi  kafinnan na sama maka abokin tafiyar ko?

Cike da girmamawa muzaffar ya amsa da to baba



Zaune yake  cikin katafaren  falonsa na gani na fada  Wanda ya Tara kayan alatu na rayuwa kallo daya  zakayi masa  kasan yana cikin matsananciya damuwa gami da tashin hankalin Batan dansa namiji tilo

Duk  Wanda ya San Alhaji Abdulwahab ya ganshi  a yanzu seya  tausaya masa  musamman yanda ya rame yayi duhu sbda tashin hankali ko abincin kirki baya Iya ci  sbda tunanin halin da dansa yake ciki

Ummace ta shigo Fallon riqe  da Waya a hannunta ta nufo inda  Dady ke zaune a kusa dashi tana kallon sa sosai take Mazarin fiskarsa sannan ta fara magana da salonta irin  na yan duniya tace  

Hba alhaji sekace ba musulmi ba? Kada fa ka manta cewar  yarda  da qaddara yana daya  daga  cikin rukunan imani fa'  don  Allah alhaji ka ragewa kanka  damuwa sbda kasanfa baka  da lfy 


Tunda ta fara mgana Dady be kalleta ba amma kuma yana sauraronta  kuma ya yarda da abinda ta fada,

Sedai baze gusheba gurin roqon Allah  da ya baiyana masa  dansa ba koda gawarsa CE ya samu ya gani  yasan dole zeji sauqi a zuciyar sa 


Ganinda tayi maganganunta sunyi tasiri akansa ne yasa tace  ga wayarka a.s.p yanata kiranka

A nitse ya ya mika hannunsa ya karbi wayar, yana qoqarin kiransa ne wayar ta fara ruri sunan daya  gani a jikin wayarne yasa ya dauka  Mamie ce  take kiransa,


Ya dauka suka gaisa dashi  bayan sungaisa ne take tambayarsa ya jikinsa ?

Ya amsa mata da kulawa  sannan Yayi shiru

Hakan ne yasa Mamie ta fahimci akwai matsalar datake damun me Gidan NATA

Sosai ta nuna  damuwarta akan ya sanar  da ita meyake damunsa

Fir  yaqi gaya mata hakan ne ya qara  tayar mata da hankali

Kafin tace wani yabu yace mata gobe  kisa  ahmad ya kaiki air pot ki taho Nigeria  be jira  cewarta ba ya kashe wayar


Hakan ba qaramin tayarwa da Mamie hankali Yayi ba   se  kuma ta fashe da kukan da bata  San dalilinsa ba ta jima tanayi  har  seda kanta ya fara ciwo sannan ta haqura tayi shiru


Ban garen dady kuwa tunda ya kashe wayr umma take kallonsa cike da son qarin bayani akan wayar daya  gama, dataga bashi da niyar tanka mata  setace alhaji wacece wannan  kuma??

Be ko kalleta ba yace matata dake  qasar India itace

 Dik da cewa ta girgiza Bata nuns masa komaiba 

Seda ta dan jima sannan ta tashi ta fice daga falon ta nufi dakinta,

 Tana  shiga  ta fara zarya a dakin data ga  zaryar ba fishsheta zatayi ba ai seta nufi dakin Momy   sbda tashin hankali ko sallama batayiwa Momy ba ta fada mata daki

A tsorace Momy ta dago tana  kallonta tace  haba dan Allah wllh kin tsorata no bata  kulata ba ta kalli su fadeelah da suke zaune a bakin  gado tace  ke  Ku tafi  falo zamuyi magana 

Ba musu fadilah ta dauki laptop dinta da wayar ta  sannan ta fice  daga  dakin 


Tun  shigowar umma Momy take kallonta baki a sake tace  ke  wai meya faru ne?

Umma bata  boyewa Momy komaiba akan yanda sukayi da Dady,

Tashin hankalin  da Momy ta shiga yafi Wanda  Ummah ta shiga, cike da masifa Momy tace  tabdi lallai ma mutuminnan ya raina mana hankali wllh be isa ba, mu ze mayar 'yan iska ?

Ashe dama  gunta yakai wancen gantalallen? Wato mun gama dashi shine ze kawo mana  wata tsinanniyar ko?  To wllh be isa ba bari ma naje  falon nasa  na sameshi wllh Yayi kadan yace zega bayan mu, fuuuuu tayi hanyar  fita  dagudu umma ta rugota tace  ashe  baki da hankali ?

Yanzu idan kikaje masa  a haka kina ta jaraba ai seya zargemu akan hallaka masa dansa


Kinga  kawai mujira muga zuwanta   idan ta ishemu base mu kashe shegiya ba?


Da fara'a Momy tace  yauwa 'yar  gari dadina dake  a kwai tunani.  Suka tafa sannan suka cigaba da qulequllensu



Allah ya kyauta




Ni wacece da za'a sani a gaba ??  Har  wacece cibado a cikin marubuta?

Wllh ni ba kowa bace illa  me koyan rubutu  har  yanzu ban qware  ba!  Zefi a gareku kudena wahalar da kanku a kaina  sbda in yar  koyo CE,  kuma daga  yau ni cibado na dena rubuta sannan lbri   dan haka Ku kwantar da hankalinku


No cibado ban Iya tashin hankali ba 👏

[8:52PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

 _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page -1 2*



Sun Dade suna  qulle qullensu  sannan umma  ta nufi dakinta  zuciyar ta fal  farin ciki

 

Tunda Rabe taji batun tafiyar  muzaffar hakan ba qaramin  daga mata hankali yayi ba,  amma sedai ba yadda ta Iya dama tasan dik daran  dadewa dolene wannan ranar zata zo

Shiyasa bata son sabawa da mutane daga qarshe suzo su barta,

Muzaffar na fitowa daga daki hanyar garke ya nufa  sabda  yasan nan ne gurin zaman Rabe bata da wani gurin zuwa se nan,

Yana qrasawa kuwa ya hangeta a zaune tayi shiru da alama tinanin wani abun  takeyi,

A hankali ya fara tafiya sadaf sadaf sbda baya so ta ganshi  ayko yayi sa'a  bata ganshiba har ya qaraso  daf da ita  hannunsa ya daga ya tafa aiko seta zabura zata gudu, da sauri ya ruqo hannunta  yace ke tsaya matsoraciya kawai ya qarashe  mganar yana dariya

Kamar zatayi kuka tace yaya zafar  meyasa kake son tsorata mutum?

Cike da kulawa yake kallonta sannan yace  ke kadai nake iyayiwa haka sabida ke din qanwata ce  kuma inaji dake Rabi'atu ya qarasa maganar tare da Jan kumatunta.

Tunda ya fara magana  Rabe take kallonsa   kawai seta fashe da kuka, nan da nan hankalin muzaffar ya tashi cike da tashin hankali yake tambayar ta meke damunta!

Da kyar ta Iya bude baki tace yaya zafar  idan ka tafi Dawa zan dinga hira  ? Kuma Dawa zan dinga zuwa kiwoo? Ta qarasa maganar tana kuka me cin rai😭

Tunda ta fara maganar yake kallonta dan haka sosai ya tausaya mata be Iya CE mata komai ba ya jawota ya hadeta da qirjinsa  yana rarrashinta , ta Dade tana kukan sannan tayi shiru,

A hankali ya zaunar da ita  sannan ya fiskanceta  yace, Rabbi'atu  har ga Allah nima zanyi kewarki  bama  ke kadai ba Harda baba, amma zanyi miki wani alqawari amma se kin min alqawarin bazakiyi kuka ba gobe  idan zan tafi, 

A nitse ta dago jajayen idonta da suka fara kumbura tace  uhmm ni se kace zaka zauna tare dani anan  shine bazanyi kuka ba, cike da quruciya tayi maganar

Abin yaso  ya bawa muzaffar dariya amma kuma seya dake yace haba  qanwata idan kika CE haka to ni kuma babana  fa?

Kinga  ai ze damu tunda besan inda  nake ba  ko?

Da sauri tace to ba se shima yazo nan mu zauna tare ba?

Sosai muzaffar yayi dariya har yana tafa hannu

Sannan yace ai bazeyu muzo gidanku  mu zauna ba  sabda muna da yawa  sosai,   dasauri tace aini kai kadai nake so mu zauna tare dakai😔

Sosai maganar ta ke taba zuciyar muzaffar 

Kamar daga sama  tace nasan idan ka tafi Gidan Ku mantawa zakayi dani!

Da sauri ya kalleta sannan yace wllh bazan manta dake ba qanwat..... Bata bari ya qarasa abinda zece ba tace to kamin alqawarin komai daran  dadewa zaka dawo gareni  yaya zafar!

Muzaffar yace ki yarda dani mana!

Da sauri tace bazan yarda da kaiba har seka min alqawarin zaka  dawo gareni wata ranah! 

Batare da tinanin komaiba yace nayi miki alqawarin zan dawo gareki  qanwata

Sosai abin yay mata dadi  dan haka tayi dariya sosai  sannan suka kama hanyar gda.

Suna tafe  suna hira Har suka qaraso  gida, suna shiga da Laure suka fara arba aiko da sauri Rabe tayi bayan muzaffar, beyi mamaki ba sabda yasan tana bala'in jin tsoronta, cike da girmamawa ya gaida ta a daqile ta amsa be damu da hakan ba ya wuce daki abinsa  yana tafiya Rabe na take masa baya seda yaje  daf da qofar sannan ya tsaya  yace INA kuma zaki?

Ba tace masa komai ba ta nuna masa dakin bece komaiba ya shiga ita  kuma tabi  bayan sa



Ina miqa gaisuwata me tarin  yawa  a gareki  aunty Qween 👏

Bazan mata da cikakkiyar masoyita ba (Sadiya na Abbah )😘😘

[8:52PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 13*



Yana shiga ya nemi guri ya zauna itama zaman tayi  tunda ta zauna take kallon sa tun be lura ba har ya ya fahimci irin kallon da take masa,  amma seya share sabda yasan indai  ya kalleta dena kallon sa zatayi, shi kuma haka kawai yaji baya so ta dena kallonsa  haka kawai yaji yana son hakan,

Ta jima tana kallon sa  sannan ya dago ya kalleta se kuma ya kashe mata ido daya 🤪

Da sauri tayi qasa da idanunta sbda wani irin kwarjini da yay mata bugu da qarima ga kashe mata idon dayayi

Abine ya bashi dariya yace qanwata ta kaina  wllh bana so ki dinga damuwa nace miki idan na tafi zan dawo wani lokacin kodan sabida ke👉

Ya qarasa maganar tare da nuna ta da hannunsa, 

Sosai maganar tayi mata dadi dan haka ta saki murmushin daya qara baiyana kyawunta  sannan tace na yarda dakai yaya zafar!  Nasan bazaka  manta dani ba kuma nima bazan manta dakai ba zafar,

Da sauri ya kalleta yace amma meyasa kike kirana da zafar ?

Murmushi tayi sannan tace sbda bazan Iya fadar sunanqanwata, sbda akwai wahalar fada,

Tunda ta fara magana yake kallon ta sannan yace  oho shiyasa kike cemin zafar?  Ta daga kanta  alamar ae, dariya yayi sannan yace hakan dakike cemin ma yana min dadi qanwata,

A nitse ta kalleshi tace  yaya zafar idan ka tafi zanyi kewarka sosai  bazan gaji da gayama cewar na saba dakai ba ,  ni kaina bansan dalilin daya sa nake jin zafin tafiyarka a raina ba yaya zafar!

Sosai yake kallon ta  tunda ta fara magana  sannan yace  ni kaina  INA jinki  a raina Rabi'atu!  Ta yanda har nake jin bana so na tafi na barki! Har ga Allah naji jini na ya hadu dake,  bama  Iya nanan abin ya tsayaba  shiyasa ma nake kiranki da qanwata , 

Bayan Mamie na da  dadyna ban saba da kowa ba se ke!  Dan haka kina da matsayi a zuciyata dama rayuwata gaba daya!


Yanda ta nutsu tana sauraransa seka rantse tana fahimtar abinda yake fada , ta Dade tana juya abin a ranta  kafin ta jefa masa wata magana wadda seda yayi mamakinta , CE masa tayi yaya zafar dama ana Iya bawa mutum  matsayi a zuciya?😳


Da sauri ya kauda  tinanin ta daga maganar yace mata a'a ba'ayi,  suna cikin maganar Laure ta bankade qofar dakin tace to tsinanniya fito nan kiyi min aiki  

Kin shige daki da namiji kina lalata  dan rashin kunya se liqe masa kike yi se kace ba BAFULATANA ba !

Karuwar banza karuwan wofi,  sosai abin yayiwa muzaffar zafi a rai amma seya danne zuciyar sa, Rabe ko banda kuka ba abinda takeyi,  a  hankali ya matasa kusa da ita yana rarrashinta. Laure kuwa seda ta gama tijarar ta sannan ta fice ta bar musu dakin!

Sosai abin ya batawa muzaffar rai dan haka ya kasa cewa komai, cikin tatatausan lafazi yace  tashi kije  kiyi shirin kiwo mutafi 

Tana jinsa amma setayi kamar bataji me yace ba ta cigaba da kukanta, sosai kukanta yake taba zuciyarsa  dan haka seyaci gaba da rarrashinta daqar ya samu tayi shiru,

Suna cikin haka ne moddibo yay sallama a qofar dakin sannan ya shigo  beyi mamakin ganin su tare ba sabda hakan ba sabon Abu bane 

Da gudu Rabe ta mike ta nufi Baban nata  ta rungumeshi se kuma ta sake fashewa da kuka  cike da damuwa moddibo ya dagota yana kallon fiskarta yace meya faru kuma ?

Bata CE komaiba sabda kukan daya ci qarfin ta da qar  ta Iya nunawa moddibo  muzaffar da hannunta tace baba yaya zafar ne wai zetafi Gidan su ya barmu, ta qarashe mganar tare da cigaba da kukanta,

Murmushi moddibo yayi sannan ya dafa  Kafadunta yace haba  mamana , meyasa zakiyi haka?

Kadafa ki manta ke qanwarsa CE dole wata rana ze sake zuwa dan ya ganki  dan haka ki dena kuka kinji mamana? 

Da sauri ta daga kanta  alamar ta yarda da batun Baban nata,  dan hka ta share hawayenta  sannan ta koma kusa da muzaffar tace yaya baba yace zaka dawo wata rana dan haka  bazan sake kuka ba sbda babana  baya min qarya komai ya fadamin  gaskia nake daukar sa, tunda ta fara maganar muzaffar yake kallonta  sosai yake nazarin  yarinyar gata qarama amma tana da kaifin tunani  wannan idan ta kai shekara 20  yazata  kasance?  

Lallai Rabi'atu tana da wayo kuma yana jinjina irin soyayyah dake tsakanin ta da mahaifin ta,

Murmushi yayi mata tare da Jan hancinta da hannunsa  dikansu dariya sukayi sannan suka yiwa moddibo se sun dawo  sannan suka wuce kiwo ita da yayan nata.


Gasar India


Tunda momie ta ji  batun Dady na ta zo Nigeria hkan ne ya tabbatar mata tabbas akwai matsala, to meyasa Dady ze mata haka? Bayan yasan bata son zuwa Nigeria, sbda wani dalili nata!

To meye wannan dalilin na Mamie da ze hanata zuwa qasarta  na haihuwa?????


Jikinta ba qwari ta mike ta shiga hada kayan  da zata tafi dasu, dik wasu mahimman takardu na Dady seda ta hada su guri daya a cikin wata qaramar a kwati sannan ta kulle, dik wasu kayan da zata buqata seda ta dauka  sbda ta qudurtawa kanta cewar bazata sake dawowa qasar India ba, wannan Karon yaki zatayi  da wa'yanda suka rushe  mata farin cikin ta na rayuwa!


Nigeria 

Bangaren Dady kuwa daqar ya mike ya nufi toilet ya watsa  ruwa sannan ya fito ya shirya cikin wata farar  shadda me ratsin blue ammata din kin irin na dattijawa  ba laifi kayan sun masa kyau dik da ramar dake jikinsa  kana kallon sa zaka fahimci baya cikin kwanciyar hankali,  yaa fito cikin shirin fita  Momy ya samu a zaune a falo se su fadilah da zahra'au, se kuma ameerah da Fa'iza dake ta fada akan rumot , fitowar Dady CE ta katse ameera da fa'iza sukavar fadan da sukayi sbda sunsan  Dady ba wasa a lamarinsa !

Dady ya kalli fa'iza dake cika tana batsewa yace  dan ubanki baki da kunya ko?   Zakici qaniyanki,

Daga haka yayi waje abinsa  be sake cewa kowa komai ba , yana fita ya bude mota ya shiga  bashir driver yaja motar suka dauki hanyar Gidan shugaban 'yan sanda wato  haruna musa majia.



To se ince  a suka lafiya  dady👏





Bani da ta cewa sedai ince  Allah ya shiga tasakanina daku! 

Bani da qarfin da zan Iya kare  kaina  daga sharrin makiyana !

 A cikin Ku babu Wanda ya halicceni balle  kuma  yayimin wani Abu !

Niba kowa bacce  balle  kusa ni a gaba .

Fatan alkhairi shine fatan cibado ga kowa, ciki kuwa Harda Ku masu yimin barazana👉😘

[8:52PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 14*



Suna isa qofar Gidan aka bude musu gate suka shige kasancewar sunsan  Dady sosai 

Parking space suka nufa  suka ajiye motar  sannan ya ta sarwa qofar da zata sadashi  da falon da sp  majiya yake saukar  bakinsa  na musamman

 Yana shiga ya samu guri ya zauna sannan ya dauki wayar sa ya danna number sp  majiya ya sanar dashi cewar ya qaraso, 

Bugu daya ya dauka  ya fada masa ya qaraso  sannan ya ajiye wayar  ya zubawa TV idanu, 

Ba jimawa aka cikawa Dady gabansa da kayan motsa baki  kala kala,  kodaya Dady be taba ba sabda shi yanzu ma ko wani irin abinci ya kalla Sam baya bashi shi'awar sa, dan haka kallo daya yayiwa abincin  ya dauke kansa,  

A hankali sp  majiya ya qaraso  falon tare da sallamar sa,  har ya qaraso  falon Dady be San ya shigo ba har seda ya tabashi  sannan ya dawo daga duniyar tinanin kudan  jininsa,

A dan daburce Dady yace barka da fitowa,

Sp  yayi murmushi yace haba  alhji abdul dubi fa yanda ka damu kanka da tunani wllh Harka  rame  kayi baki kamar ba kaiba, kayi haquri ka yarda da qaddarar da Allah ya aiko maka  kaifa  musulmi ne , insha Allah zamu samo inda  muzaffar yake da izinin Allah, tunda sp  ya fara magana Dady ke kallon sa sannan yace naji abinda kace sp  kuma na gamsu da bayanan  ka zanyi qoqarin cire  ragewa kaina  tinanin kamar yadda ka shawrce ni ngde Allah ya bar zumunci,

Sp  yayi murmushi yace ba komai, kada ka damu,

Kuma insha Allah zamu zage dantse wajan gano inda  danmu yake da ikon Allah.

Sosai Dady yaji dadin maganganun majiya dan har ya samu nutsuwa a zuciyar sa kuma yadan  sake sunyi hira  kadan,

Sannan sukayi sallama da juna cikin aminci  har bakin mota sp  majiya ya rako dady , ya shiga mota  suna masu dagawa junansu hannu,

Dady be koma gda ba se 6:00pm koda ya dawo be tsaya ko INA ba  se dakinsa  alwala yayi ya sake fita be dawo ba se da yayi sallar magrib

 

RUGAR HARDO


tunda su muzaffar suka tafi kiwo bashi da aikin daya wuce kallon Rabe dik inda  tabi  idanunsa  na kanta, 

A hankali ta bude baki tace yaya zafar meyasa kake yawan kallona?

Murmushi yayi sannan yace sabda zanyi missing naki!

Sosai take kallon sa sannan tace me Kalmar take nufi?

A taqaice yace zanyi kewarki to.

Dariya tayi sosai irin wadda bata tabayi ba a gabansa a Iya zaman da yayi dasu,  daqar ta saita kanta ta dena dariyar,

Tunda ta fara yake kallonta  kamar wanda zeyi kuka yace, meyasa ki dariya haka?

Murmushi tayi tace abinda ka fada ne yasani  dariya senaji Kalmar taban dariya,


Hade rai yayi yace to kada ki sake min irin wannan dariyar bana so, kinji yanda kika tsorata ni?

Sunkuyar dakai tayi sannan ta riqe kunnuwanta dika biyun  kamar yanda yakeyi mata idan ya bata mata rai,  kamar zatayi kuka ta tsuguna qasa  tace kayi haquri yaya zafar badan qara ba, 

Dariya ta bashi sosai dan haka yay murmushi tare da Jan kumatunta yace shikenan na haqura amma kadan.

Dariya sukayi dukansu, sannan suka kamo  hanyar gida  dabda  magariba suka dawo,

Tunda suka dawo Rabe bata qara bari sun hadu da zafar ba, a cewarta wai bata so taga  tafiyar yayan nata !

Daki ta nifa tayi sallah tayi addu'ointa  ta shafa, amma kuma bata tashi daga gurin ba, 

Bangaren muzaffar kuwa tunda suka shigo  yayi sallah amma bega  shigo war Rabe ba se abin ya fara damunsa, har akayi ishsha beganta ba se abin ya fara daga masa hankali,

Daqar ya Iya bude baki ya cewa moddibo dake ta faman  dura madara ajarka yace, baba!

Ya a nitse moddibo ya dago yace yaro ya akayi ? 

A daburce yace dama,,,  dam,,,,, Rabe se kuma yayi shiru.

Murmushi moddibo yayi yace yaro INA zaton ko tayi bacci ne,

Kayi qoqari ka kwanta sbda gobe asibanci zamuyi ,

Bashi da yanda zeyi haka ya kwanta  amma fir  bacci ya gagari idanunsa ,

A hankali ya firta meke faruwa dani ne??


Bangaren Rabe kuwa baccinta take hankalin ta kwance babu abinda ya dameta ,


Qasar India


Mamie tana idar da sallar asuba  bata tsaya ko INA ba se airports dan cika umarnin mijin nata  duka  5:30am suka daga zuwa Nigeria, tun da ta hau jirgi gabanta ke faduwa   komeyasa????


Ban garan su muzaffar kuwa tunda gari ya waye suka gabatar da sallar asuba  suka fara shiri  ba yanda beyiba dan su hadu da rabe 

Amma fir taqi da abin ya isheta ma seta bar Gidan tayi tafiyarta gidansu danejo qawarta,


Ba yadda ya Iya haka suka tafi ya naji yana gani suka shiga wata a mortar shanu suka kama hanyar garin  kano  garin  alfarma! 

Dik wannan uban sammakon da sukayi  basu suka isa kano ba se qarfe 4:00pm

Wanda yayi dai dai da saukar mamie a qasarta ta haihuwa!

Cike da kulawa moddibo ya kalli muzaffar yace yaro zaka gane gida ko?

Muzaffar yayi murmushi yace zan gane,

Adaidaita sahu suka tare sannan muzaffar yace malam nasarawa g.r.a zaka kaimu ,

A take me napep yace  musu dubu daya !

Bece komaiba suka shiga suka tasarwa nasarawa g.r.a


Mamie na sauka   daga jirgi bata wani jima ba driver yazo ya dauke ta tana cikin motar  gabanta yay mummunar faduwa! 

Da sauri ta firta innanillahi wa'inna ilai hirraji'un.


Qofar wani gida na alfarma muzaffar ya nunawa me napep din  tare da bashi izinin shiga  horn  me napep din yayi amma shiru ba'a bude gate din ba ,

Muzaffar ne ya zuro qafarsa da nufin ya suka , amma se moddibo yayi carap ya riqeshi yace yaro Sam be kamata ka shiga kanka tsaye ba, dolene ka badda kamannin ka,

Cike da rashin fahimta yace ban gane ba!

Murmushi moddibo yayi ya fito da wani rawani ya CE bani kanka, ba musu ya miko  masa kan NASA ya shiga  Nada masa,

Watabara'kallahu'ahsanulkhaliqin,

Abinda moddibo ya Iya fada kenan sbda wani azababben kyau da rawanin yayi wa muzaffar

Gashi sanye da kayan Fulani seya koma kamar wani balarabe!

Horn suka sake yi a karo na uku sannan me gadin ya bude yana ganin baquwar fuska ai seya  dakatar dasu yace daga malamai daga INA?

Moddibo ne ya bashi amsa yace  daqa  rugar hardo!

Ba musu me gadi ya bude musu qofar suka shige sbda kwarjinin da moddibo yayi masa

Sauka  sukayi  shi kuma me napep suka bashi hagginsa Harda qari, mebawa fulawa ruwa suka samu su kace dan Allah ya sanarwa da alhaji abdul yana da baqi daga rugar hardo, cike da girmamawa ya amsa tare da kaisu falon saukar baqi




Se ince  fatan alkhairi mlm moddibo👏

[8:53PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 15*


Sun jima suna zaune, sannan aka kawo musu abin motsa baki.


Lokacin da aka sanar da Dady zuwansu moddibo yayi mamaki sosai sbda shi bema taba jin sunan garin ba, amma dayake mutum ne shi me jama'a da kuma son mutane shiyasa be wani yi mamakin zuwan su ba, tashi yayi ya nufi falon sa na da yake saukar baqin sa, 

Da sallama ya shiga falon, ya nemi guri ya zauna sannan suka gaisa  da moddibo.

Kwata  kwata  be lura da wanda ke zaune a qasa ba,

Sosai Dady ya sakarwa moddibo fuska, a nitse moddibo ya fara magana tare da yiwa Allah godia yace  da fari  alhaji ka godewa Allah bisa  ni'imar da Allah yayi maka a wannan rana! 

Cike da rashin fahimta Dady yace ban fahimceka ba dan uwa?

Murmushi moddibo yayi  sannan yayi masa nuni da muzaffar dake zaune da uban  rawani a kansa gaba daya ya badda  kama 

Sosai Dady  yake kallon dan nasa  cike da so da qauna, da sauri ya nufi inda  muzaffar yake da nufin ya rungume shi, haka shima muzaffar din beyi qasa a gwiwaba ya nufi mahaifin nasa  suka rungume juna suna masu zubar da hawaye😭

Sosai suka bawa moddibo tausayi, sun jima suna rungume da juna  sannan Dady ya cire  jikinsa daga na muzaffar  ya zubawa fukar dan nasa  ido sosai rama ta baiyana a jikinsa sedai kuma beyi duhu ba haskensa yana nan yanda yake!

Se kuma alamar ciwon dake gefan  kansa na dama Wanda be gama bacewa gaba daya ba.

Cike da damuwa Dady yake tambayar dan nasa  meya faru dashi? Kuma ina  ya shiga har tsawon wannan lokacin?

Muzaffar  yayi shiru kamar bazece komai ba, seda ya dan nisa sannan ya gayawa Dady komai sedai be gaya masa da sa hannun su Ummah da Momy ba akan abinda ya faru dashi ba!

Har abinda ado yayi masa be gayawa Dady ba, kawai CE masa yayi 'yan fashi ne suka farauci rayuwarsu  kuma sukayi yunqurin kashe shi, badan wannan bawan  Allahn ba da tini na rasa rayuwata, ya qarasa maganar tare da zubda hawaye! 

Da sauri Dady ya qaraso  kusa da qafafuwan moddibo ya rige  yana fadin  ngde, Allah ya saka maka da alkhairi, haqiqa banida  abinda zan biyaka dashi a wannan duniyar sedai kawai ince  Allah ya biyaka da Gidan aljannah👏

Ya qarasa maganar tareda hawaye!

Murmushin qarfin hali moddibo yayi sannan yace haba  alhaji dan Allah ka dena godemin  sbda ni nayiwa yaro taimako  ne don  Allah ba dan kayi min godiya ba, dan haka ka bari godiyar ta isa haka, sedai kawai abinda zancema  shine kayi a hankali sbda maqiyanka Dana danka  suna tare dakai  kuma sune  sukafi kowa kusanci dakai!

Cike da rashin fahimta Dady yake kallon moddibo, kai moddibo ya daga masa alamar ae, 

Kiran  sallar da aka fara kira ne ya katse Dady daga tambayar da yaso  yayiwa moddibo,

Tashi sukayi suka nufi masallaci dan su gabatar da sallar magrib, 

Bayan sun idar ne suka nufi qofar da zata sadasu da Fallon,

Horn akayi daga bakin gate hakan ne yaja  hankalin Dady da muzaffar, shiko moddibo shigewarsa yayi ya samu guri ya zauna, sannan ya fara nazari akan maganar da muzaffar ya gayawa mahaifin sa, to meyasa be gayawa mahaifin sa gaskia ba??

Lallai muzaffar yaro ne me sanin ya kamata  kuma me gudin masifa.

Sbda gudin ta da fitina yayiwa mahaifin sa qarya dan ya fanshi kishiyoyin mahifiyarsa!

Gaskia samun irin sa se'an tona  a irin wannan zamanin, haka kawai seyaji yaron ya qara shiga ransa.


Wata baqar Toyota benza ce  ta sako kai cikin Gidan  ko ba'a fada ba Dady yasan Mamie ce   parking space suka nufa  sukayi parking tana fitowa daga motar  Dady ya yiwa muzaffar nuni daya shiga falon tun kafin ta ganshi,, haka kuwa akayi  

Da sauri Dady ya nufi inda Mamie ke tsaye da murmushi a kwance a fiskarsa yace sannu da zuwa Uwar gida ran gida, 

Murmushi Mamie tayi ba tace komaiba ta nufi bangaranta visa ga mamkinta ba ta ga qura  ko daya ba  harta isa falon ta ko INA tas tas ba datti  daret bedroom dinta tanufa, tana shiga toilets ta shiga bisa  ga mamakinta dik abinda take Amfani dasu tin daga sabulun Wanka har zuwa MacLean komai a kawai a ciki kuma dika sababbi, haka ma su towels,

Murmushi tayi sannan tace  abou muzaffar kenan har yanzu kana nan yanda kake baka canza ba!


Dady ne yasa masu aiki suka shigarwa da Momy kayanta bangaren ta  sannan ya nufi falon da moddibo ke zaune shida muzaffar,

Dady ne ya yiwa muzaffar izinin yakai moddibo bangaren saukar baqi dan yaje yayi Wanka ya huta 

Haka  kuwa akayi suna fita Dady ya nufi bangaren sa dan ya samu yayi Wanka  zuciyar sa cike da farin ciki Mara musaltuwa,

 Suna isa ban garen baki ya nunawa moddibo ko INA sannan suka zauna , a nan ne moddibo yake tambayar muzaffar meyasa baze tafi bangaren sa ba?

A taqaice yace Dady ne yace na zauna a nan har seya nemeni!











Lallai akwai magana a qasa  se ince  Allah ya huta gajia  Mamie👏

[8:54PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 16*



Seda ta yi Wanka sannan ta gabatar da sallar dake  kanta, ta jima tana  adduo'inta sannan ta shafa, 

Bangaren Dady kuwa yana shiga  cikin gda  dakinsa ya wuce seda  Yayi Wanka  ya kimtsa, sannan ya gabatar da sallar ishsha'insa, sannan ya nufi falon su  momy,

Yana shiga  falon ya same su dukansu akan dining sunacin abinci suda yaransu,  kallo daya  zakayiwa Dady ka fahimci yana cikin farin  ciki, dan haka umma cike da gulma tace  alhji  da dikkan alamu kana cikin farin  ciki, kodai an sake samun  riba  a company n ka na takalma ne?

Cike da masifa Momy ta fara magana tace  riba?  Ba wata riba da aka samu, wannan farin cikin da yake  ba komai bane dalili ila zuwan matar sa, kuma wllh ka sani tunda ka jajibota cikin mu to wllh kayi bankwana da kwanciyar hankali, tana  gama magana ta mike da nufin ta wuce dakinta, 

Tsawa Dady ya daka  mata wadda seda hanjin cikin ta ya kada yace ke kishiga hankalinki niba  sa'anki bane da zaki sani a gaba  kina yimin ihu, ko ba komai ni mijin ki ne kuma uban  'ya'yanki ko banci darajar kowa ba naci darajar 'ya'yana  yana gamawa ya juya da nufin yabar falon, se kuma ya dawo yace idan sun gama suzo  falon sa  yana son magana dasu a bangaren da  aka fat din Mamie  kuma su zo da yaransu gaba  daya  sbda a kwai Abu me mahimmanci,

Yana kaiwa nan Yayi waje abinsa ban garen Mamie ya nufa da sallamar sa ba kowa a falon se qamshi dake tashi a falon sosai yake  kallon falon Yayi matiqar kyau kamar  yanda yake buqata,  hanyar da zata sa dashi da dakin Mamie ya nufa tin kafin yakai ga dakin qamshin turarenta ya baqunci hancin dady, murmushi Yayi a zuciyarsa yace salma kenan kedai Allah Yayi miki  son qamshi

 Yana shi shiga  ya sameta  tana  daura dan kwali a kanta  sallamar ta amsa sannan tayi murmushi tace  sannu abban muzaffar na sameku lfya ? 

Dariya Yayi sannan yace Uwar gida ran gida lfy. Qalau mun godewa Allah ya gajiyar hanya? 

Murmushi tayi sannan tace  gajiya kam akwai ta  Baban muzaffar.

Shiru suka dan yi na wani dan lokaci sannan Dady yace  idan kinci kin gama shiryawa  akwai maganar  da zamu  dan tattauna daku,  gabanta ne ya fadi! da sauri  ta furta  innanillahi'wa'innah ilaihirraji'un, da Sauri Dady ya matsa kusa da ita  ya dafata yana tambayarta meya faru?

Kuka  ta saki  sekace wata qaramar yarinya, beyi yunqurin hanata ba, seda tayi me isarta sannan tayi shiru, 

A hankali ta fara magana ban San meyake damuna ba Sam! Koda yaushe a ' se in dinga jin gabana yana yawan faduwa,  musamman ma yau ,

Lamarin  nifa ya fara bani tsoro  wllh, kodai wani abin ne ze faru dani? Ta qarashe maganar  tana  zubar da hawaye,

A nitse Dady ya fara magana yace haba  salmah, har zuwa wani lokaci zaki kai kina wannan kukan?

Yakamata kisani  cewa ko wani mutum da zanan qaddarar sa, kuma ko wani mutum da irin  tasa  qaddarar, don  Allah kiyi haquri ki dena zubar da hawaye haka, insha Allah zamu  samu cikar burinki da izinin Allah wata rana zamu  hadu da su!

Cikin kuka Mamie ta fara magana tabbas nayi kuskure a rayuwata Abdul, gashi hakan yajamin rashin  kwanciyar hankali da nutsuwa,

Kuka  sosai takeyi, har ga Allah ya tausaya mata dan haka yayta rarrashinta har ya samu tayi shiru,


Kicin ta nufa ta sa ruwan zafi ta hada  tie sannan ta fito ta zauna a kan dining ta fara sha,  tana  cikin sha ameerah da zahra suka shigo falon da sallamar su cike da kulawa Mamie ta amsa sallamar tare da sakin fuska sosai baki ameerah ta saki tana  kallon Mamie, zahra kuwa hankalinta yana  kan Falon musamman yanda taga  komai sabo  ne bugu da qari ma gurin Yayi matiqar haduwa, a hankali ta furta waw gaskia falon nan ya hadu,

Ta juya da nufin ta tabo ameerah ai  se sukai ido biyu da Mamie, air se itama ta tsaya tana  kallon Mamie n,  murmushi Mamie tayi sannan tace  Ku shigo Ku zauna mana  sekace baqi? Maza Ku shigo mana

Jiki a sanyaye suka shigo falon suka zauna ameerah CE ta fara gaida Mamie sannan zahra ma ta gaisheta,  sosai Mamie ta sakar  masu fuska suka dinga hira, a nan ne ameerah tacewa Mamie aunty gaskia ke kaykkyawa ce, daria Mamie tayi sosai dan har ga Allah ameerah ta bata daria,

A hankali Mamie ta sunkuyo taja hancin ameerah tace  kema ai kyakkyawa ce,

Darirya ameerah tayi sannan tace  aunty ni suna na ameerah wannan kuma zahra,  

Murmushi Mamie tayi sannan tace  ba suna na aunty ba Mamie zakice kinji?

Dariya zahra tayi sannan tace  ke in banda baki da hankali Waya fada miki  ana cewa babba  kamar  wannan aunty ? Ta qarasa maganar  tareda nuna  Mamie da hannunta, baki ameerah ta murgudawa zahra sannan tace  an fada din ta qarasa maganar  cike da tashin kunya,

Tunda ameerah ta fara zuba rashin kunyarta Mamie ke kallon ta, bata CE komaiba sema ja  baya datayi daga  kusa da ita  ta koma  kan  daya  daga cikin kujerun falon,  sun jima a dan zaune sannan Mamie ta koma  daki  dan ta dakko wayarta  a hanya suka hadu da Dady yana shirin fitowa falon shima, murmushi yayiwa Mamie sannan ya wuce ta gefanta ya nufi falon, yna shiga  ya zauna a kan kujerar dake daukar mutum biyu, yana zama zahra ta sauka  qasa tare da yiwa mahaifin nata  barka da fitowa, 

Sosai Dady yaji dadin abinda zahra ta yi shiyasa yake sonta sbda baba daya  yaransa idan ka cire muzaffar a kyawawan halaye to se zahra ameerah kuwa yana zaune da alama  ma bata da niyar sauka  daga kan kujerar.

Tsawa Dady ya dakawa ameerah da sauri  ameerah ta sauka qasa sannan ta fashe da kuka  sbda tsoratar da tayi,


Ummah CE ta fara shigowa sannan Momy ta biyo bayanta se kuma fadilah dake bayan Momy n, Ummah CE tayi qarfin halin yin sallama, 

Kallo daya Dady Yayi musu sannan ya dauke kai, a daqile ya amsa sallamar, sosai suke kallon falon sbda yanda ya hadu, koda wasa basu taba shigowa falon ba se yau, cike da masifa Momy ta fara magana tacewa Ummah kin gani ko? Ai dama na fadamiki gashi nan ai kin gani wllh dama na san  tsugune bata qare  ba, mun gudu ne bamu tsira ba da sauri  Ummah ta dannewa Momy baki, tace  haba  zuwaira me kikeyi haka sekace wata qaramar yarinya?

[8:54PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 17*



Gaskia zuwaira baki kyauta ba, kuma gaskia ya kamata ki bawa  alhaji haquri yanzunnan, ta qarashe maganar  tare da kanne mata ido daya.

Nan da nan Momy ta fahimci manufarta dan haka ta sunkuya ta bawa  Dady haquri,

Be ko kalleta ba ya juyar da kansa  yace mata ya wuce, 

Guri  suka samu suka zauna, sun dan jima a zaune sannan umma tace  alhaji ka kira mu amma har yanzu baka CE komai ba,

Shigowar Mamie ce  ta sa umma hadiye maganar  ta,  da sallama Mamie ta qaraso falon kusa da zahra ta zauna , da murmushi a fuskarta tace  sannan ku  ya gda ?

Ummace tayi carab tace  lfy qalau ya hanya? Ta qarasa maganar  tana  hararar Mamie,

Da kulawa Mamie ta amsa mata tare da jefa mata tambayar ta same su lfy.

A taqaice suka bata amsar lfy,

 Dady yana zaune a inda  yke wayarsa ya dauka a gefen kujerar daya ke zaune , ya kira wayar telho din dake dakin saukar  baqinsa  bugu daya muzaffar ya amsa, a taqaice Dady yace  kazo falon Mamien ka Ina son  Zama daku gaba daya,

Be ce  komaiba ya ajiye wayar 

Moddibo dake zaune kan sallayar  da suka idar da sallah, bece masa komai ba se kallon sa kawai daya ke yi, jiki ba qwari muzaffar ya qaraso kusa da moddibo yace , baba wllh har ga Allah ina jin tsoron muta nan nan! 

Cike da rashin fahimta moddibo yace yaro ban fahimci maganar  ka ba, tsoron me kake ji?

Muzaffar yace baba INA magana ne a kan mutanen Gidan nan, ina  jin tsoron kada su sake shirya min wani mugun abin!

Murmushi moddibo Yayi sannan yace  yaro kaifa namiji ne dan haka ka daure ka zama jarumi, kuma ka dage  da addu'a haqiqa babu abinda yafi qarfin Allah dan haka kada ka bari tsoronsu ya samu gurbi a cikin zuciyar  ka, kaji  yaro? Maza kaje kiran mahaifinka, Sam kada ka nuna  rauninka a gaban maqiyanka,

Muzaffar yayi sannan Ya nufi qofar fita  daga  Falon,

Site din Mamie ya nufa , da sallama ya shiga  Fallon  da uban  rawani kamar  wani ba Sarake, tunda ya shiga falon muta nan dakin suke kallon sa dik  da cewa basu gane shi ba , ciki kuwa harda  Mamie, murmushi Dady Yayi sannan ya miqa hannayensa alamar yazo gare shi , da sauri  muzaffar ya nufi mahaifin nasa  ya suka sake rungumar juna  , umma CE tayi qarfin halin cewa wai alhaji waye wannan din da kashigo dashi cikin gida har falo?

Ga kuma uban  rawani kamar  wani bafade!

Momyce ta qara da cewa inda  duniyar nan ba gaskia ka jajibo mana shi baka tsoron yazo ya cutar damu  a gaba?

Itadai Mamie bata CE komaiba sema kallon su da take, ta Kali wannan ta kalli  wannan,


Murmushi Dady Yayi sannan ya kalli Momy yace kin taba ganin inda da ya cutar da ubansa?

A taqaice tace  yo alhaji nawa akayi?

A hasale  yace idan kuwa kika ga da ya cutar da ubansa to wllh wannan dan ba dan halak  bane,

Ynan gama bata amsa yace zoka zauna Dana , 

Umma CE tace  danka  kuma alhaji ?

Kodai batan  muzaffar yasa kanka  ya fara kwancewa ne?

Ya zaka  samo wani bafulatanin daji da uban  rawani kace danka  ne shi?

 Da sauri  Momy tace yauwa gaya masa dai maman zahra,


Murmushi Dady Yayi Wanda yake dauke da manufofi masu yawa, sannan yace, babu tabin  hankali balle  a samu matsalar qwaqwalwa!


A yau da yamma  cin nan lbri mafi dadi a duniya ya sameni,

Ba wani lbri bane illa  labrin baiyanar gudan  jini na wato Dana  namiji tilo  wato muzaffar!


Gaban Ummah da Momy ne Yayi mummunan faduwa, nan da nan gumi ya fara karyo musu dik da sanyin Ac dake dakin hakan be hanasu fitar da zufa ba, 

Kallo daya zaka  yi musu ka fahimci suna cikin wani yanayi!


Momy CE tayi qarfin halin cewa to alhaji INA muzaffar din yake yanzu?

Bece mata komaiba se nuna  mata shi da Yayi da yatsansa,

Cike da rashin fahimta Mamie tace   abban muzaffar nifa ban fahimce Ku ba wai don  Allah meyake faruwa  ne??


Sam Dady be boyewa Mamie komaiba tun dga batan  shi muzaffar din har zuwa yanzu da Allah ya baiyana shi, da sauri  Mamie miqe daga inda   take ta saukko qasa Inda muzaffar ke zaune, ta Dora tafikan hannayenta a kan fiskarsa tana me zubar da hawaye tana kallonsa cike da tsantsar so da qauna  tace, haqiqa INA matiqar qaunarka Dana  kuma dik duniyar nan dik Wanda ze soka wllh a bayana  yake muzaffar!

Dama  abinda ya faru dakai kenan yasa kwana kin baya nake ji a jikina wani Abu ya faru da gudan  jini  na?

Ashe shiyasa na rasa kwanciyar hankali? Ta qarasa maganar  cikin kika me matiqar ban tausayi!

Daqar ta tsagaita kukanta sannan tace  INA matiqar sonka dana, idan wani abin ya sameka wllh har abada zanyi Dana sani!


Cike da  makirci umma tace ke kinga fa  bawaifa fin mu sonsa  kikayi ba!  Kin wani sashi a gaba se kuka  kikewa muta ne, kafin kisanshi fa mumuka sanshi, tunda mu muka fara auren ubansa kafin ke,

Da sauri Momy tace gaya mata dai zata yiwa mutane kini  bibi wai ita  matar uba,

Mamie batace  komaiba se kika da take, muzaffar ma kukan yake yana me mamakin  irin qaunar da Mamie take masa !

Tabbas koda mahaifiyarsa CE irin  son da zatai masa kenan,

Hawayen fiskarta ya fara goge mata da hannayensa,


Dik wannan abin Dady yana kallon su  sannan yace dikkan Ku Ku dakata  sbda wannan abin ba shine mafita ba, yau kowa zeji abinda na Dade ina  boyewa a gare Ku  

Wata qila ya bku mamaki  amma kuma Sam ba abin mamki bane

A cikin masu mama kin nasan harda  kai muzaffar!

[8:55PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 18*



Cike da rashin fahimta muzaffar ke kallon mahaifin nasa  sedai bece komaiba,


Dady Yayi ajiyar zuciya sannan ya ci gaba da magana kamar  haka

Haqiqa na boye  muku wani al'amari a Iya zama na daku, ya nuna  umma da Momy

Sannan ya cigaba da magana,

Na gwada Ku a baya ta hanyar kawo muku Dana muzaffar tin yana shekara daya a duniya na raboshi da mahaifiyar sa na kawo muku shi,

Sbda na gwada tsoron Allah n Ku da kuma tausayin Ku,

Amma se kuka  kasa riqeshi da gaskia, kuka dnga cutar da shi, abinda Baku sani ba shine mahaifiyar muzaffar tananan a Raye bata mutu ba, 

Cike da tashin hankali gami  da fir  gita muzaffar yake kallon mahaifin nasa yace, Dady kana nufin kace  min mahaifiyata tana nan da rai bata mutu  ba?

Amma Dady meyasa ka rabani da mahaifiyata?

Meyasa ka zabi na rayu da wasu  sabanin mahaifiyata?

Meyasa kace  min mahaifiyata ta rasu?  Pls Dady ka cireni a cikin rudanin Dana ke ciki don  Allah


Da rarrafe ya matsa  gurin Mamie ya riqe  hannayenta  yace Mamiena don  Allah ki cewa Dady ya kaini gurin mahaifiyata na ganta koda so daya ne don  Allah Mamie!

Ya qarasa maganar  yana kuka sosai kamar  wani qaramin  yaro,

Da qyar Mamie ta saita kanta sannan tace ka kwantar da hankalin  ka yarona baka da wata Uwar da ta wuce ni kaji ? Nice mahaifiyarka ba wata ba, 

Momy CE tace haba  malama kinga  ki dakata  ki barmu da almarar data muke ciki, ya za'ai kizo kisamu a gaba kina yimana kukan kirsa da makirci,

Ki rufe  mana baki muji qarshen zance, 


Ummah tace muma  fa muna son yaron nan kawai dai tsautsayine da kishi yasa muka kasa riqeshi tun farko, shiyasa ma ya kawo miki shi amma bawai finmu sonsa  kikayi ba


Kuka sosai muzaffar yake yi, dadyne ya katse su ta hanyar  ce gaya musu cewar  Mamie itace mahaifiyar  muzaffar,  kuma itace matar daya fara aure a rayuwar sa, dan haka itace Uwar gidansa  kuma mahaifiya  ga muzaffar!

Dikkansu seda suka girgiza musamman ma momy, sbda tashin hankalin da momy ta shiga numfashinta har sama  ya fara yi,

Umma ce  tayi qarfin halin zaunar  da momy, 

Sun jima suna alhini

 Mamie qara rungume dannata tayi cike da soda qauna,

Seda suka dauki lokaci me tsayi  babu Wanda yace komai , 

Fadilah CE tace momy tashi mu tafi  sbda ki samu nutsuwa,

Ba musu momy ta tashi dan dama  hanya take nema

Suna shirin fita  umma ma ta bisu, 

Suna fita  ameerah tace zahra zo mutafi muma, harara zahra ta zab gawa  ameerah tace ba inda  zani  kawai kiyi tafiyarki,


Tashi ameerah tayi tabar  falon kamar zata tashi sama,  

A hankali zahra ta sakko qasa daidai inda  qafafun Dady suke tace  Dady don  Allah kayi haquri da halayen da iyayen mu suke Nuna maka  nasani  dole wata rana zasuyi nadama,

Tana gama magana da Dady ta juya ga muzaffar tace yaya, haqiqa ina me jajanta ma abinda ya faru dakai ina  me yi maka  addu'ar alkhairi a koda yaushe sbda kai dan uwa na ne kuma guda  daya tilo, nasani  wata rana dole Kaine zaka  zama uba a garemu gaba daya, 

Nasani  bamuyi sa'ar iyaye ba, amma don Allah INA me roqa  masu afuwa akan abinda suka aikata maka  kana yaro don Allah yaya muzaffar kayi musu afuwa, tana maganar  ne tana hawaye,

A hankali ta daga jajayen idanunta ta kalli Mamie tace , haqiqa ke uwa CE wadda ta cancanta a yaba  mata  tunda har kika Iya sadaukar da danki guda  daya tilo dan farin cikin mijinki, wllh dik inda  uwa ta gari Takai kinkai Mamie, dama kece kika haife ni wllh danayi alfahari dake,

Tana kaiwa nan ta miqe ta fice  daga fallon tana me zubar da hawaye


A wannan rana muzaffar kwanan farin ciki Yayi, hakama Mamie da Dady

Su umma da momy kuwa kamar su mutu  din bakin ciki


RUGAR HARDO


Tunda  muzaffar ya tafi  komai ya dena yiwa rabe  dadi 

Gashi yau kwanan sa daya da tafiya amma har ta rame  sbda kuka , bugu da qari ga kuma azabar da  Laure take gana mata, abin gwanin ban tausayi,


Tashi tayi daga dakin ta fita  chan gurin garken  shanunsu  Inda suke zama ita  da muzaffar, dutsen daya ke zama a kai ta Dora hannunta akai  seta sake fashewa da matsanancin kuka me cin rai

Cikin kuka take fadin ya Allah Kaine ka bani farin ciki a lokacin da bani tsammani ba!

Ya Allah ina ina roqonka da sunayenka kyawawa, ya Allah ka cika rayuwata da farin ciki me dorewa, ya Allah ka bani ikon jure  ko wacce irin  jarrabawa!

Tanayi tana kuka sosai abin qwanin ban tausayi,,,,,,

[8:55PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 19*



Hka tayita rusar kukanta babu me rarrashinta, sda rana ta bude sosai sannan ta Tisa dabbobin suka tafi kiwo, haka ta dinga tafiya jiki ba qwari, inda  suke zama da muzaffar idan sun gaji  ko kuma zasuyi sallah, a nan ta zauna ta sake yin shiru, nan da nan ta tafi duniyar tinanin  yayan nata!

A ranar dai haka ta wuni sukuku da ita

 

Momy ce  tsaye a cikin dakinta  tana ta safa da marwa da Waya a hannunta, falo naga ta nufa  fiskarta a daure fadilah ta samu a zaune  bata ko kalleta ba tace tashi kije ki kiramin Umman zahra, bata jira cewarta ba ta koma dakin ta

Ba'a dau lokaci me tsayi ba  sega  umma ta shigo dakin , Sosai take kallon Momy sannan tace  nariga na fahimci me kike son gaya min tin daga qwayar idanun  ki, yanzu meye mafita ? Tambayar da Momy ta jefawa umma kenan,

Bata CE mata komai ba ila daga wayar hannunta da tayi da alama wani take son kira,

 Ba'a dau lokaci ba  ta fara magana cikin isa da nuna gadara tace ado haka mukayi  dakai?

Nawa muka baka a kan ka kashe mana wannan dan iskan?

Da kasan ba zaka iyaba kuka karbar mana kudi?

Cike da mamaki ado yace haba  hajjaju, ai tin tini aka gama wannan aikin dan sda  na tabbatar baya numfashi sannan na qyaleshi!

Kema kinsan  Baku taba bani aiki na kuskureba,

Momy CE ta fisge wayar daga hannun  umma ta kara a kunnenta cike da masifa tace har kana da bakin da zakace baka kuskure a aikin ka?

Kai daqiqin inane da zaka yarda shi a Inda mutane suke shige da fice?

To gashi yanzu ka jiqa mana aiki yaron ya dawo gida da ransa da kuma lafyar sa, kuma kasan dole 'yansanda zasu karbi bayanai daga bakinsa , dan hka seka zauna cikin shiri, at any time zasu Iya zuwa kamaka!

Ta qarasa maganar cike da masifa gamida tarin bacin rai


Umma CE tayi saurin karbar wayar tace ado kana jina?

Cike da tsoro yace ae Hajia inajinki

Maza- maza ka shirya kabar garinnan kayi nesa da kano Sam karka  dawo semun nemeka, da sauri yace to Hajia, sda  ta dan nisa tace masa amma dai a kwai  kudi a hannunka  ko?

A'a yace mata nan da nan tace yaushe na saka maka million daya a  account dinka da zaka cemin ba kudi?

A daqile yace sorry Hajia na shiga rudani ne, bata sake cewa komaiba ta katse wayar sannan ta bude wayar ta cire  sim din ta karya sbda gudun seta kwana!

 A hankali umma ta dafa kafadar Momy tace haba  zuwaira kada ki bada mata mana, ai yanzu damace tazo mana,

Cike da rashin fahimta Momy tace kamar ya ?

Murmushi tayi irin nasu na 'yan duniya  sannan tace  shishigewa waccan matsiyaciyar zamuyi, idan ta saki jiki damu se mu aika shegiya garin da ba'a dawowa! Koya kika CE?

Dariyar jin dadi Momy tayi sannan tace wllh kamar kinsan  abinda ke raina,,  suka sake kwashewa da dariya suka tafa(haqiqa kishi da rashin tsoron Allah yana kai mata dayawa ga halaka, mugun nufi bashida wata fa'ida illa yakai mutum ga na dama! Dan Allah mata mu gyara zukatan mu, kishi halitta ne kuma kowace mace tana dashi a tare da ita muddin tana da lfy, amma idan kika bishi ta hanyar daya dace wllh zaki zauna da kowa lfy,    wannan abin nasu  Momy Harda son zuciya gamida tarin  rashin tsoron Allah,  ya ubangiji Allah kasa mufi qarfin zukatan mu)

 

Moddibo ne zaune qasan kafet yana daure boronsa da alama shirin tafiya gda yake muzaffar ne ya shigo dakin da murmushi a kan fiskarsa yace baba,,,, se kuma yayi shiru, da sauri ya qaraso  inda moddibo yake cike da damuwa yace baba badai har ka fara shiriba tin yau?

Murmushi moddibo yayi irin na dattijawan qwarai yace  to yaro me kuma zan tsaya jira?

Tunda Allah ya amince mana min samu nasarar kawoka Gavan Iya yenka ai kuma nima sena fara shirin komawa gida kodan sbda  Rabe na!

Nasan yanzu tana nan cikin kewata , ban taba tafiya me Nisan haka na barta  a gda  ba, a Iya zaman ta dani ban taba tafiyar da takaini ga kwana ba sbda tinanin halinda zata shiga idan bana nan, 

Dan haka Gobe da ikon Allah zan kama hanyar gda ,ya warashe maganar da murmushi a fiskarsa

Shiru muzaffar yayi na dan lokaci tabbas yana mamakin shaquwa irinta moddibo da diyarsa, yanzu idan tayi aure ya zeyi?

Kafadarsa moddibo ya dafa  yace  yaro naga daga jiya zuwa yau kanata farin ciki,


Murmushi muzaffar yayi sannan ya labirtawa moddibo komai, sosai moddibo yayi farin ciki gamida yiwa muzaffar nasihu masu shiga jiki sosai, 

Jikin muzaffar haka yayi sanyi sbda nasihun da moddibo yayi masa, a ransa seyaji dama moddibo ya zauna tare dashi  haka kawai dattijon ya gama shiga ransa,

Jiki ba qwari muzaffar ya miqe sbda jin kiran sallar ishsha'i, be cewa moddibo komaiba, ya nufi hanyar fita 


Murmushi moddibo ya kuma yi sbda ya fahimci muzaffar fishi yayi sbda yace ze tafi gobe

Miqewa yayi shima suka nufi masallaci, daidai lokacin da Mamie ta loqo ta window falon ta  bayan su ta hanga sannan ta koma  taci gaba da jera abinci akan dining,

Koda aka idar muzaffar ya Dade yana addu'oinsa sannan suka shafa suka fito gaba daya, 

Dai dai lokacin da Dady ma ya fito tare suka jera  suna tafe  suna hira  anan  muzaffar ke shaidawa Dady tafiyar  moddibo, sosai Dady ma yaji ba dadi sbda yanda ya saba dashi a kwana daya  kamar sun shekara da sanin juna, moddibo akwai sauri saboda  mutane, gashi da haquri da sanin ya kamata shiyasa yake da dadin mu'amala,

Indai ya zauna dakai koda na wuni daya ne to Seka qaunace shi. Sbda dattijon a kwai shiga rai

Suna  shiga Dady yacewa moddibo tunda gobe ze tafi don Allah yazo suje bangarensa suci abinci tare amma fir moddibo yaqi amincewa , haka Dady ya haqura  badan yaso  ba  yayiwa moddibo seda safe sannan ya wuce bangaren Mamie,


Ban garen da aka sauki  moddibo suka  muzaffar yana biye dashi a baya har suka isa  a falo suka zauna,  muzaffar ne ya fita dan dakko musu abinci a bangaren Mamiensa , be jima ba ya dawo dauke da manyan  food flasks guda biyu se zahra dake bayan sa hannunta dauke da flat da spoons ajiyewa tayi sannan ta koma ta daukko wani flat dauke da kosilo Wanda yaji qwai da bama  ansa wata fara leda an rufe farantin da ita ta yanda kana Iya ganin abinda ke cikin flat din  da sallama ta shigo ta ajiye sannan ta gaida  moddibo cike da girmamawa, da kulawa ya amsa mata tareda sakin fuska, an an yake tambayar ta sunan ta murmushi tayi sannan tace zahra,

Murmushi moddibo yayi sannan yace Ashe mata nane da kanta, dukansu suka sa dariya sannan ta miqe tayi musu saida safe ta wuce bangaren su

[8:55PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 20*



Zaune suke kan dining suna cin abinci, Dady yake sanar da Mamie tafiyar  moddibo da safe idan Allah ya kaimu, gaban  Mamie ne yay mugun faduwa sbda sunan da taji mijinta ya ambata ,  take yanayinta ya sauya,


A hankali tace daga zuwansa har ze koma se kace ana korar sa?

Murmushi Dady yayi sannan yace wllh nima haka nace dashi amma fir yaqi yarda ya qara kwana ki,


Dik wannan hiran da suke itada Dady qarfin hali kawai take tinda  taji sunan moddibo, sunan da bazata taba mantawa dashi ba a rayuwata

  Dady ne ya katseta ta hanyar sanar da ita  yayi kewarta,

Murmushi Mamie tayi sannan tace abban muzaffar kenan sekace wasu yara?

Dariya yayi sannan yace mata au yara ne kawai suke soyayyah?

Bata CE masa komaiba dan ta fahimci Neman magana kawai yakeyi,

A hankali ta ajiye cokalin dake hannunta ta miqe a taqaice tace seda safe,

Sam beyi qoqarin hanata tafiya ba sbda ya fahimci yana yinta ya canza  tunda ya ambaci sunan moddibo.

Abinda ya qara daure masa kai shine meyasa bata son taji wani me suna irin hka?

  A hankali ya rintse idanunsa, sbda baya son abinda ze batawa matar tasa  rai, a daddafe ya kammala  cin abinci, ya miqe ya nufi bedroom din shima, a zaune ya sameta da alama daga toilet ta fito, kana kallon ta zakasan tayi kuka, bece mata komai ba ya shiga toilet yayi brush sannan yayi wanka  yafito, beyi mamakin ganin ta ajiye masa jallabiya ba sbda hakan al'adarta  ce, murmushi yayi sannan ya sanya a jikin sa, yana gama sawa haye  gado abinsa  bece mata komaiba ya ka bargons da nufin ya kwanta,

  Da kanta ta fahimci yayiwa megidan nata  laifi dan hka ta bude baki tace don Allah kayi haquri bani da yanda zanyi ne dolece tasa,

Sanin kanka ne kasan bazan taba mantawa da me wannan sunan ba  seta fashe da kuka,

Sosai me Gidan nata  ya tausaya mata, dafata yayi sannan yay mata nasiha sosai tareda sake nuna mata mahimmancin yarda da qaddara,

  Jikinta ne yayi sanyi sosai a hankali taba bargo ta kwanta, a nan ne Dady yake tambayar ta me take ganin zeyiwa moddibo idan ze tafi sbda nuna jin dadin abinda yayiwa dansa  Wanda yasan ko duniyar nan yabashi be biyasa ba ,

Murmushi Mamie tayi me sauti  sannan tace ka bari tukunna seda safen mayi  maganar,

Bata qara cewa komaiba tayi addu'ointa ta tofa, ba jimawa bacci ya dauketa ,

 Ban garen su muzaffar kuwa hira  suke sosai da moddibo sekace ba dare ba, sun jima suna hiran  sannan moddibo ya tashi ya wuce daki sbda bacci daya ke ji, kuma gashi fitar wuri yake so yayi,


Murmushi muzaffar yayi tareda dadin seda safe

  A hankali ya tashi ya kashe TV sannan ya rage ywan Ac dake falon sannan ya rage wutar falon ya mike ya nufi bangaren sa, bisa  ga mamakin sa seyaga an qara gyara masa dakin, ko ba'a fada ba yasan zahra CE da wannan aikin

Murmushi yayi sanan  yace Allah sarki my Darling,

Wanka yayi sannan ya fito daga toilet din sanye da wata farar  jallabiya, dik da cewa shirin bacci yayi amma rigar ba qara min kyau tayi masa ba,  a hankali ya qraso bakin makeken gadon sa qirar Italian ya zauna  yayi shiru, kallo daya zaka yimasa ka fahimci damuwa  a fiskarsa,

Wani abin hannun  roba dake hannunsa ya taba se kuma ya saki wani tattausan murmushi, a hankali ya firta I miss you Rabi'atu, I miss everything about you, murmushi ya sake yi a karo na biyu sannan ya hau gadonsa yaja  bargo ya kwanta, ya jima yana nazarinta tareda  Tina wasu abubuwa na quruciyarta gami  da yawan murmushin ta,

   Yajima  yana aikin tinani sannan bacci yay a won gaba dashi,


Kiran  sallar farko moddibo ya mike ya shiga toilet yayi Wanka yayi alwala ya kimtsa.

Masallaci ya nifa, yana shiga masallaci ya gabatar da raka'atanul fijir bayan ya idar ya dan jima a zaune yana addu'ah sannan aka gabatar da sallar asuba,

Bayan ya fito masallaci suka hadu da muzaffar suka wuce gda suna hirarrakin su,

Ban garan moddibo suka nufa  ya tayashi ya hada kayan sa ya daure seda gari yayi haske  sannan Dady ya shigo bangaren dan su gaisa  da moddibo, bayan sun gaisa  ne Dady yace masa yazo su gaisa  da mahaifiyar muzaffar sannan yayi breakfast, se su wuce, murmushi moddibo yayi sannan ya CE to babu damuwa idan ka shiga seka sanar da iyalin baka shigo war tawa, 

Murmushi Dady yayi sannan ya kalli muzaffar yace ka shigo dashi falon Mamie n  ka  idan ya kammala murmushi shima yayi ya amsa da to Dady,


Dady na shiga ya sanar da Mamie cewar moddibo ze shigo yayi mata sallama, murmushi tayi sannan tace gaskia be kamata ya tafi yanzu ba dama ya qara mana kwana 2  murmushi Dady yayi suna ta hira  abinsu,


Mamie tace ina  zuwa naji kamar abinda na Dora yana kamawa , kichin ta nifa dan ta sauke  abinda ta Dora,

Tana fita su moddibo da muzaffar suka shigo falon, guri muzaffar ya nuwa moddibo sannan ya zauna shima hira suke dan yi da Dady jefi jefi, a haka Mamie ta fito ta samesu , ko kadan moddibo be kalli fiskarta ba itama haka  ta qaraso  falon fiskarta dauke da murmushi a nitse ta zauna a gefan  Dady  sannan ta fara gaida moddibo a nitse ya fara amsawa cike da kulawa, 

Cike da tashin hankali Mamie ta dago sbda jin muryar da ko a INA take tasan mamallakinta,

   Kallon moddibo take haka shima kallon Nata yake cike da tashin hankali yake nuna ta da yatsa,

Kasa cewa komai yayi  dan haka kawai ya miqe da nufin yabar falon gaba daya,


Da sauri Mamie ta riqe qafafuwansa tana kuka me tsima zuciya, cikin kukan take fadin dan Allah Iya kayi haquri ka yafe  min nasan nayi kuskure a rayuwa ta yanda bazan Iya gyara laifi naba! Ta qarasa maganar tana kuka sosai

 Cike da rashin fahimta Dady yake kallon su haka ma muzaffar da kansa ya gama daurewa, 

 Cike da damuwa Dady yake tambayar Mamie shin tasan moddibo ne? Kuma meye hadinta dashi da har take fadin ya  yafe  mata?

Da qar ta Iya bude baki tace dan uwa nane  shine yayana moddibo da mukaje nema shekaru  a shirin da biyar  da suka wuce, to shine wannan ta qara fashewa da kuka,


Qarfin hali moddibo yayi ya fisge qafarsa daga hannunta ya fice daga falon da sauri yana zubar da hawaye, 

Ko kayan sa be dauka  ba ya fice daga Gidan gaba daya,

Yana fita ya samu keke na pep ya shiga batare da ya gaya masa inda ze kaishiba !!

Seda suka fara tafiya me napep din yace mlm  INA zan kaika?

A taqaice yace masa tashar mota  zaka kaini, don Allah idan kasan inda ake lodin abuja ka kaini gurin sabda sauri nakeyi,


A kan titin Zaria road ya sauke moddibo sannan yasa shi a motar  abuja,

 yakoyi  sa'a  ciko  ake Neman , kudinsa ya bashi sannan yayi masa godiya suka kama hanyar abuja,

[8:56PM, 2/6/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


*BAFULATANA*

   _True life story_


 *_Written By Cibado😘_* 


 _Dedicated to Khadeeja Candy_


*Page - 21*



Tun bayan tafiyar moddibo Mamie take kuka, gaba daya hankalin Dady ya gama tashi yama rasa me zeyi guri ya samu ya zauna tare da dafe  kansa daya ke masa wani irin nauyi,, falon ne yayi shiru ba'a jin komai se sautin kuka Mamie,  muzaffar ne yayi qarfin halin cewa Dady wannan zaman fa ba shine mafita ba fa,

Kawai tashi zamuyi mubi bayan sa, nasan ze sauraremu inayaso se'a gyara matsalar senake ganin hakan zefi da wannan zaman da muke,, cikin kuka Mamie tace nasan halin sa muzaffar yana da matiqar haquri amma idan yayi fishi  yana da wuyar sha'ani!

A hankali Dady ya sauke ajiyar zuciya sannan yace abinda muzaffar ya fada shine daidai ki tashi kije ki wanke fuskarki ki shiya  mubi bayansa , hakan shine mafita, haka kuwa akayi, a gurguje Mamie ta gama kimtsawa ta fito,  koda ta fito bata samu muzaffar da dady a falon ba , dan haka bata tsaya jiran komaiba ta nufi waje  tana fita ta hangi muzaffar a parking space yana tsaye a jikin wata ibgegiyar mota qirar ford,da alama fitowarsu yake jira, sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda milk colour ammata dinkin  tazarce, aikin dake jikin shaddar maroon color ne dan haka ya sanya hula maroon da ratsin milk a jiki ta kalmin qafarsa me danyasa ne shima maroon, se agogon dake hannunsa qirar Gucci, sosai yayi kyau kayan sunyi matiqar amsar jikin sa, a hankali Mamie ta qarasa inda yake kallo daya zakai  mata kasan tana cikin damuwa mara  musaltuwa, amma dik da haka damuwar  bata hana futowar kyawun da Mamie n keda Shiva, da sauri dan nata  ya matso kusa da ita ya rungumeta yace don Allah Mamie ki ya rage damuwa indai  baba ne wllh ze fahimce ki, nasan shi yana da sauqin hali a Iya zaman danayi dashi , pls Mamie ki cire  damuwa haka don Allah!

Batace komaiba se cire  jikinta zatayi daga nasa , sannan tayi wani marayen murmushi me baiyana karayar zuciya da qarfin gwiwa tace  hka dai kace yaro amma ni nasan da wuya  moddibo ya yayfemin abinda nayi masa ,

Be sake cewa komaiba  sbda fitowar  Dady  dasu umma  daya gani, a nitse suka qaraso  gurin murmushi Mamie tayi musu  tareda CE musu muntashi  lfy ?

Umma CE ta amsa mata da fara'arta , Momy kuwa ko kallon ta batayi ba, da sauri zahra ta matsa  kusa da Mamie tace Mamie INA kwana ?  Da kulawa Mamie ta amsa, muzaffar bece musu komai ba sbda shi gaba dayansu ma haushi suke bashi , daya ga abin nasu bana qare bane, se yace pls Dady Ku shiga muje sbda mu isa da wuri, daga haka ya bude driver seat ya zauna, yana qoqarin rufewa zahra ta riqe hannunsa da sauri tace pls yaya nima zan biku tunda ba school don Allah!

Ta qarasa maganar tare da langabar da kanta kamar wata yarinya,

Dariya ma ta bashi dan haka yace ta shiga suje  da gudu ta bude qofar gaba ta shige tana yiwa ameerah qwalo,

Mamie CE ta fara shiga sannan Dady   da sauri ameerah ta matso ta cewa muzaffar yaya nima, ai be jira cewarta ya daka  mata tsawa yace bacemin da gani ba inda zamu dake Mara kunya kawai!

 Da gudu ta bar wajen  tana kuka, cike da masifa Momy tace to seme in baka je da ita ba?

Ta juya itama ta bar gurin,


Be jira cewarta ba ya tashi motar  suka bar harabar gidan , suka nufi hanyar RUGAR HARDO!



Se wajen qarfe uku sannan moddibo ya isa yana hanyar sa ta shiga gida ya hangi  Rabe a zaune cikin garken  shanu ta rafka uban  tagumi, inta take ya nifa ya kamo  hannunta yana kallon fiskarta sosai yaga rama a tare da ita, ga kuma duhu da ta danyi  ba komai a fiskarta se daradaran idanunta da  suka sake fitowa  se dogon hancinta shima daya baiyyana  alamar rama, be jira cewarta ba ya ka hannunta sukayi gida, mamaki ne kwance a fiskar Laure 

Dan haka tace mlm har ka dawo?

Sbda takaici ko kallonta beyi ba  ya jata  sukayi daki



Post a Comment

0 Comments