ALJANAR FATIMA CMPLT


 👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Part 1-2



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



*بسم الله الر حمن الر حيم*



 _*YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH MAMALAKIN KOMI DA KOWA WANDA YA DAI-DAI TA GABOBINA*_ 


 _*TSIRA AMINCI KA DADAWA FIYAYEN HALLITA ANNABI MUHAMMAD S.A.W SHUGABAN HALITTA CIKA MAKON ANNABAWA*_



 _*INA ROKON ALLAH A KAN RUBUTUN NAN DA ZAN FARA ALLAH KA IYA MINI KA BANI KAIFIN BASIRA DA HIKIMA ALLAH KASA NA RUBUTA ABUNDA ZAI AMFANE MU DUNIYA DA LAHIRA, AMIN.*_




💃🏻 GA WATA SABOWA ZAMANI MAI YAYI SABUWA. 


Bazan manta da ku ba domin kun zama My blood. 


Bazan barku ba domin in na barku na bar kaina.


Bazan ki yaban ku ba domin yaban gwani ya zama dole.



Bazan hana ku ba dole in mika shi gare ku littafin baki daya sadaukarwa ne gare ku MY BLOOD duk yan Kungiyar Zamani writers association  ®Z.W.A banga kamar ku ba bakwa taba nuna banbanci 

❤😍






💃🏻 ```Bazan taba mantawa da ku ba masoyana a duk inda kuke alherin allah ya kai muku kuna a heat na.


Bari in fara rubuto ku🤦🏻‍♂ Kash! Nawan in na fara rubuta ku bazan idasaba har karshen littafin ga ruwa biro na kadan ne. Ilove you my fans```




A Cikin kado anguwar hausawa dake babban birnin tarayya Abuja.anguwa ce mai lunguna gata da tarin bishiyoyin  mangorori hankan ne yasa anguwar take da inuwoyi hakan ta haifar wa da wajen duhu dan daga ance ma karfe 6 tayi to sai an haska fitila tsabar duhu in dai ba farin wata ba. Anguwa ce  mai tarin jama'a, ko ta ina ka duba mutane ne kowa na uzurinsa. Akwai masu saide-saide da yan shaguna da irin tsofafin nan masu saida kayan makulace na yara. 




Wata yarinya ce sanye da doguwar farar riga wacce ta koma baka dan tsabar datti, Yarinyar fara ce kallo daya zakayi mata ka gane hakan saidai dauda ta masheta baka.  Gashin kanta mai tsayo ne amma rashin gyara yasa duk ya fara cicirewa tsabar datti gashi duk ya barbaje mata a fuska sai ta dage shi tukun take iya ganin gabanta.  




Duk mai tausayi yaga yarinya to dole tausayinsa ya lunku a kanta. Domin tayi kalar ban tausan.  A hanakali take tafiya har ta isa bakin kofar wani shagon saide-saide.  Bakin kofar shagon taje tayi tsaye ta dan yace gashin da ya lilube mata fuska tana kallan cikin shagon. Shi kuwa mai shagon a lokacin ya dan duka daukar wani abu.  'Da dagowar shi duka hada ido da ita sai ji yayi gabansa yayi mugun faduwa.




Nana take yanayinsa ya canza kalo daya zaka mishi ka gane ya fusata ainun!, "Ke uban me zan baki iyee?, haka jiya ma kika zo kika min tsaye a kofar shago kina wani nuna min ciki da baki, gaki yau kin kuma Dawowo uban me zan miki". 



Dayan hannuta ta daga ta dage baki hade da nuna yatsar ta cikin bakin tukun ta sauke shi ta nuna cikin ta kamar dai yanda tayi mishi jiya. Wanda duk me hankali in ya gani zai gane tana nufin yunwa take ji tana bukatar abinci,  Shima kuma kanshi ya fahimci hakan. 




"Kaji rainin wayo ah! Lalai wannan baki sanni bane baki san bani da mutun ci ba to wllh yau zan nuna miki, to ni ubanki ne da zaki ringa nuna min kina jin yunwa ko dan kinga jiya korar ki kawai nayi ban taba lafiyar jikin ki ba.  Bari ki gani".

Nan take ya juya ya dauko dorina mai baki biyu wacce take jike dai mai dan tayi zafi yasa ta a mankyada Dama saboda yara ya saye ta. Goge bulalar ya fara yi domin abun man har yanzu akwai maski duk abun nan da yake yi yake yana surutai. Wato baki san na dade banyi zalinci ba ko ni dama zalinci ai rigata ce in banyi shi ba ji nake kamar a zigidir nake".  Juyowa yayi a zatansa tuni taji tsoro ta gudu ganin ya dauko bulala, amma sai yaga sabanin haka ta sake bude baki ta nuna mishi kamar yanda tayi dazun. 




Kara fusata yayi da sauri ya bude yar karamar kofar ta kata ko ya fito. Baiyi wata-wata ba ya fara tsula mata bulala harda riketa yana fadin, "Bari in zane ki tukun gobe ma ai sai ki dawo kaji jarababiyar yarinya ni da ba ubanki ba taya zan baki abinci" yana yi ne yana dukanta tun tana kuka a hankali har ta fara ihu! Abunda da ya jawo hankalin mutane makwabtan shagon sa kenan. Sukayo mishi can  aka kwaci yarinyar shi kuwa sai masifa yake.  Wai ta rainashi gobe ma ta dawo. 




Wani dan saurayi ne naga ya kama Yarinyar yana lalashita bai ko ji kyamar ta ba kamar yanda sauran mutanan gurin sukayi.  "Yi shiru yi hakuri yarinya kinji. Haba muktar yanzu dama rashin mutuncin naka har ya kai ga haka  ban sani ba?, Ai da na dauka rashin mutuncin ka da masifar bai wuce iya manya ba ashe hada yara". A cewar wanda ya kama yarinyar yana lalashi.


"Eh kamalu da ba ka sani ba kuma da ji kake yi yanzu kuma gashi ka gani da idanunka iyhee! Nayi rashin mutuncin in da yanda za'ayi dani ai sai ayi mugani". 

Da jin haka mutanan wajen suka watse suka barsu su biyu a gun domin kowa gudu yake ya wa Muktar magana ya mai rashin kunya, Dama a wajen kamala ne kadai baya raga mishi duk rashin mutuncin shi yana tsoran kamala.


 


"Kadai kaji kunya wallahi, yanzu wannan karamar yarinyar me tayi maka da ka dake ta?". 

Muktar ya wani taso da masifa kamar zai haiye kamal din, " Kai kamala ka bar ganin fa ina daga maka kafa wllh ba tsoranka nake ji ba, ya za'a yi kazo kana min maganganun banza a kan wata yarinya wacce gata nan dai kamar ma yar mahaukaciya domin wannan tafi karfin ace mata ma almajira, kawai tazo kofar shagona tana daga min baki wai yunwa jiya na koreta yauma shine ta dawo shiyasa zan zane ta gobe ma in ta dawo haka sai na zane ta". Yana gama fadar haka bai ko tsaya sauraren kamal ba ya juya ya shiga shagon shi.

Kamal jin saboda ta nema abinci ne ya dake ta dan takaici bai sake cewa komai ba ya kama hannun yarinyar ya nufi gidansa da ita dake ba nisa daga nan. Yana rike da hannuntq tana binshi suka shiga gidan, matarsa Khadija tana shara a tsakar gida tana jin salamar shi ta mike tsaye tana kalanshi tana kuma kalan yarinyar. 




"Baby sannu da zuwa wannan fa daga ina". ta fada lokacin da take kokarin kama hannun yarinyar. Kamar rai a bace ya kwashe duk yanda akayi ya gayawa matarsa, khadija nada mutunci sosai nan take taji tausayin yarinyar da sonta a cikin ranta.  Gogewa yarinyar hawaye tayi hade da cewa, "Yi hakuri kinji yan mata share hawayen ya sunanki daga ina kike".  Wannan tagwayen tambayoyin ta jera mata, amma shiru yarinyar batayi magana ba sai ido da take binsu da shi. 




Kamal ya maimata tambayar kamar yanda matar tashi tayi amma shiru. Sun tambaye ta ya kai sau biyar amma ko umh! Bata ce ba sai idanu da take binsu da shi. "Baby inaga fa wannan yarinya kurma ce shi yasa ma bataw Muktar magana ba". 

"Kwarai nima nayi tunanin haka,  yanzu abunda za'ayi ki taimaka ki mata wanka ki zuba mata abinci taci bari inje in sayo mata wata rigar ji kafarta ko takalmi babu bari in hado da shi".  A cewar kamal domin yasan matarsa ba mai bijirewa umarninsa bane ko  mi ya gindaya mata inda ba na sabawa allah bane tana iyakar kokarinta. 




"To baby a dawo lafiya". ta fada lokacin da ta mike shima kuma ya fita Kafin wani dan lokaci tuni khadija tayi wa yarinyar wanka ta wanke mata kai. Tsabar dauda saida ta bata kusan bokiti uku da mai tsantsami ce bazata iya ba domin ko ita tanayi tana dode hanci dan tsabar wari.  Bayan ta gama wankan bata mayar mata da rigar ba wani zaninta ta dauko ta liliba mata tukun ta shigar da ita ta zuba mata abinci. Ita kuma kamar wanda ya shekara baici ba haka ta fara ci hannu baka hannu kwarya. Tana gama cin abincin sai ga kamala ya shigo da sabuwar riga da takalmi mai kyau. Ya kawo ya mikawa khadija yace "ki saka mata ni zan koma shago karki bari ta fita waje".  


To khadija ta ambata. Kamala ya kalli Yarinyar mamaki ne ya cika sa ganin irin kyawan da ke gare ta ashe dama tsabar datti ne. Baidai ce komai ba ya juya ya wuce.

Khadija ta shafawa yarinyar mai mai kanshi tukun tasa mata kaya. Ta kuma tatara gashin kanta wuri guda tasa ribbon dinta ta daure mata kan, ta jawo ledar ta bude taga ashe doguwar riga ce mai wando harda dan gyale. Ta saka mata tukun ta mikar da ita tsaye ta tsaya ta kare mata kallo sama da kasa. Wow× Masha allah beautiful baby kenan,   yarinya da shegen kyau kamar aljana.


 (Nasmat tace, kaji min mata me ya kawo maganar aljana kuma a nan ko dai so kike ki tunawa king) 



Khadija tace "bari in saka miki jan baki da hoda kina so".  Lokacin tama manta da yarinyar bata magana. Bisa mamaki sai taga Yarinyar na girgiza kai alamun eh. Dan dariya taye hade da cewa "dama kina jin  magna ne bakya yi".   



Nan ma girgiza kai tayi alamun eh, Nan fa murna da farin ciki ya cika ta. Ta kuwa fara jero mata tambayoyi kala-kala. 




'Acikin tambayoyin ne ta tambayi ina ne gidan su ta nuna bata sani ba ta sake tambaya ina iyayanki nama ta nuna bata sani ba har da hawaye. Khadija ta shiga lalashi tace "daga yau na zama maman ki kin yarda". Girgiza kai tayi alamun eh 




Nan take khadija ta rungume ta cikin farin ciki domin allah ya zuba mata san yara kuma har yanzu allah bai bata haihuwa ba sau biyu ko ta sama cikin bari take. 


(😭 ayya allah sarki allah ka bawa duk mai irin wannan matsala haihuwa sister na allah ya kawo 👏🏽)




Haka dai ranar Khadija ta wuni cikin farin ciki duk ina tayi yarinyar na biye da ita tuni suka yi sabo har da wasanni a tsakanin su.   Da magariba haka kamala ya dawo ya tarar da su khadija ta bashi labarin duk abunda ya faru ta gaya mishi ashe tana ji magana ce bata yi.  


Nana shima yayi mata mgana ta gyada kai. Kamala yace "To yanzu bata magana taya zamu san sunanta?".  


Khadijah tace "kaji wata matsalar kuma ni nama manta in tambaye ta tun dazun. (Ta juya wajen ta) kin iya rubutu".  Yarinyar ta girgiza kai alamun a'a. Kamala yace "to mu saka mata suna waleeda mana tunda dai can dama muna san sunan". 




Khadija tayi murmushin jindadi ta kalle ta tace,"Kin yarda sunanki waleeda?". Da sauri ta girgiza kai alamun eh tana dariya nan fararen hakoranta suka bayyana.  





Bayyan isha'i sunci abinci sun suka danyi kallo kadan wajen karfe goma suka tashi ita kam yarinyar tuni tayi barci ma. Khadija ta dauke ta suka nufi daki suka kwanta a tskiya suka sakata khadija saida ta kare wa yarinyar kallo da kyau tayi murmushi tayi mata kiss haka shima kamala san yarinyar ya shiga zuciyar su lokaci guda. 





Khadija saida ta dora wa yarinyar hannu ta dan rungume ta tukun ta fara barci. 


Uhmmmmm wannan kenan😊

Misali  karfe 11:00pm   anguwar nan shiru kake ji ba motsin mutane sai kukan tsuntsaye na saman mangwaro. Badan fitulun sola da suka haske anguwar ba da duk jarumtar ka bazaka iya bi ka wuce ta cikin wannan layin ba. 




Shaguna duk a kulle sai shago daya wato na Muktar shi kadai ne a bude inda sabo an saba kowa ya watse a barshi shi kadai a gurin domin sai yayi lissafi tukun yake tashi.  Zaune yake yana kirga cinikin da yayi yana washe baki domin yau anyi ciniki sosai a shago. Ta wutsiyar ido ya hangi kamar wani bakin abu na tafiya a kan hanya zai gifta ta kofar shagon shi.  Da sauri ya dago kai dan ganin miye amma wayam.  




Komawa yayi yaci gaba da lissafin sa ba'afi seconds 30  ba ya kuma ganin wani jan abun kamar mutu kuma ya nufo shagon sa.  Da sauri ya sake dago kai a karo na biyu  nan ma baiga komai ba. Mamaki ne ya cika shi a fili yace "Kai miye haka kuma?".  Ajiye kudin yayi ya fita waje a sauri ya wa-waiga ko ina har saman bishiyoyin wajan amma shiru baiga komai ba.  Hakan tasa yace a zuciya "Ba komai kawai tsorata kaina ne nayi ashe".   Juyowar da yayi da niyar ya koma shago yayi tozali da abunda yasa ya kwada ihu! Hade da faduwa dan razana. 



Ba komai idanunsa suka gani ba sai wannan yarinyar  tsaye a kan kujerar da yake zaune.  Fararen kaya ne a jikinta amma gaba daya sun baci da jini wuyanta a yanke jini na zuba har tsartuwa yake yi. Idanunta kuwa sunyi jawur jini na bulbula daga ciki haka hakuranta sun kara zarowa sun fito waje jini cike da bakin.  Kuma a hakan murmushi take wani irin sauti na fita kadan-kadan.............



😰 Kodai aljana ya zane 🙆🏻??



Muje  zuwa 


Karkuyi zatan labarin Aljanar fatima ya canza ne 😀fa








Autan writers  KING BOY ISAH ✍🏻


👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 



Part  3-4



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



Happy birthday

   ​UⓂⓂEIY ZEE​

         I'm happy for you 1+14 year. Lolz 


Hmm gaba dayan shi pagen naku ne yanda naga kuna nuna kauna a kan littafin tun kafin in fara har dauka nayi abun yayi yawa ashe abun yafi haka. Bansan ya zan misalta yanda kuke san littafin autan nan naku ba.  Amma dai ga kyautar pagen a gare ku. Duk da nasan ban isa in biya ku da shi ba. 

 ​UⓂⓂEIY ZEE​

         PHATEEMA

         SHAZEE

            AUNTY ASY KHALIL 

           HAWWER. 


ALLAH YA BAR MUN KU YASA KUFI HAKA. ALLAH YA KARA MUKU BAIWA DA BASIRA. 



FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

Us whatsapp's number.

08096831009

----





Muktar da gaba daya ya tsorace ya gigice har ya fadi. A hankali y dago kai dan kara tabbatar da abunda ya gani shin ko gaskiya ne ko kuwa idanunsa ne kawai suka nuna mishi hakan.  Abun mamaki a dagowar da yayi wayam yaga gurin ba komai. Yana nan dai a tsaye yana tunane-tunane wannan al'amari domin yasha kai karfe sha biyu amma tun da yake yau kusan shekara daya da bude shagon amma ba'a taba tsorata shi ba sai yau "shin ko dai da gaske gamo nayi" ya tambaya kansa.  




Karar da ta doki dodan kunnan sa ne ya dawo dashi daga tunanin da yake.  Daga bangaren hannunsa na dama karar Kofatu kamar duban dawaki  ne suka nufo shi yaji.  Nan da nan ya juya a firgice yana neman fadawa shago.  Wasu bakaken hallitu ne wanda masu jikin doki dukan su bakake ne amma ba kai a jikinsu sune suka nufo shi a sukwane. 





Koda idanunsa sukayi tozali da wannan mugun abu, hankalinsa ne ya dugunzuma dan tsabar tsorata a million ya fada shago bai ko tsaya kulle shagon ba haka kuma baisan lokacin da ya tsallake dogon bincin da ke raba masu sayayya da cikin shagon ba. A bayan bencin ya sama wani dan lungu ya labe yana maida nunfashi day-day. Duk jikinsa karkarwa yake idanunsa nan-da-nan suka saki ruwa.  Kuka ya farayi shabe-shabe ya fara magana a hankali cikin muryar sa dake rawa yana fadin "Wannan wane irin bala'i ne ni kam yau na shiga uku..."  Surutai ya tayi shi kadai sai da ya dau kusan mintuna 20 a cikin shago yayi lumi ko motsin kirki baya yi kuma karar dawakin nan har yanzu a kwaita. 




Can dai yaga wannan bata yi ga zafin dake adabarsa sai gumi yake, hakan tasa shi fitowa daga inda ya labe a hankali ya dan leka kofar shagonsa wayan baiga komai ba sai karar da yake ji. Ya dade nan a tsaye ko zaiji karar ya ragu amma ba alamar raguwar. Ga zafin ya fara cin karfinsa ya fara magana cikin murya irin ta mai kuka ko gunguni. "Haba wllh fita zanyi bazan tsaya zafi ya kashe ni a banza ba. Wallahi fati zanyi ko me zai faru ya faru. Juyawa yayi ya dauki makulan shagon bai ko tsaya debe kudinsa ba. Ya fara yunkurin tsallakowa  bayan ya tsallako ne ya bi a hankali kamar munahiki ya leko shagon ta bangaren da yake jin karar.  



Leka warsa keda wuya sai yaji kamar an dauke wuta dif! Karar ta dauke. Hakan ya bashi dama da karfin gwiwa na fitowa da sauri ya garkame kofar shagon yanufi hanyar gida da gudu-gudu sauri-sauri takun da yayi bai wuce 15 ba sai gani yayi wutacen nan gaba daya sun dauke dif!. Al'amarin da tasa shi yayi tsaye cik kenan. Kamar walkiya haka yaga wani farin abu ya gifta ta gaban shi duk da duhun amma yaga abun kamar mutun lokacin tsoro ya kara rufe shi, Suman tsaye yayi a gurin tsabar tsorata da yayi.  




Sanda aka shafe kusan mintuna 10 yana wajen a tsaye ya rufe idanu alamun haske ya gani hakan yasa ya bude idanunsa ai kuwa sai yaga wutar ta dawo. Nan fa ya ranci ta kare ya zura a guje kamar wanda zai tashi sama.   Yana wuce wani mangwaro yajiyo dariya a saman shi, a cikin gudun ya wai-wayo abunda ya gani ne yasa shi har saida yayi tuntube karfin gudun yasa har sai da ya wuntsila yayi kungun bala.  Yarinyar nan ya gani kamar dazun duj jini na fita a jikinta kuma itace ta dage kai sama tana gagaba dariya marar dadin ji.




Bai kula da ko yaji ciwo ko baiji ba. Ya tashi ya ruga a guje yana ihu.  Bai daina ganin yarinyar na fito mishi a sifofi na ban tsoro ba har ya kawo gida. Da shigar sa gida ko tsayawa sa kubobin kawai banka kofar yayi. Dake yasan kyauran mai jamlock ne. 




Da gudu ya fada daki UⓂⓂEIY ZEEY

 (matarsa) na kwance a kan gado tana barci. Yabi ta kanta ya tsallaka dayan gefan tuni ya ja (blanket) bargo ya rufa duk zafin da ake fama da shi. Nauyin sa ne ya tayar da  Ummiey daga barci waigawa tayi dan ganin waye sai ganin shi tayi ya kudun-dune cikin bargo yana sauke nunfashi day-day tayi mamaki mutumin da baya san zafi ko kadan kullum in yazo sai ya mayar da fanka ta bangaransa amma yau gashi ya shiga bargo lalai ba lafiya ba. 



"Mai gida-Mai gida baban HAWWER-baban HAWWER lafiya kuwa?"  Haka ta dinga jero mishi tagwayen sunaye hade da dadabarsa tana tambayarsa. Karkarwa taga duk jikinsa ya hau yi.  Domin shi kam abunda yake ji yayin da yake ji bashi take fada ba kuma ba muryarta yake ji ba.  Domin wata murya yake ji mai abun tsoro tana fadin "Mu...ktar...m..u..ktra" a slow muryar ke tafiya.  



Ummiey ganin karkarwar da yake tayi yawa ta dan daga murya "Baban Hawwer lafiya kuwa".  Yayin da shi kuma yaji an daga mishi tsawa da wata muryar mai razanarwa ance, "Kai muktar magana fa nake maka".   Firgigit ya tashi zaune. Maimakon yaga matarshi ummiey. Yariyar nan ya gani kamar yanda take dazun dan yanzu ma tafi ban tsoro domin dogon gashin kanta mai-makon ya zuba a bayanta sai mikewa yayi tsaye cir! Yayi wani irin fadi A sama. ('Kai duk wanda yayi arba da wannan yarinya ala dole hantar cikinsa ta kada dan tsoro, In ma bai sume ba')




Muktar kuka ya farayi yana ja da baya-baya yana bata hakuri a haka har ya surmuyo kasa daga kan gado bai ko jira kuma ba yaci gaba da ja bayan.  Ummiey na gannin mai gidan nata ya fado daga kan gado yana kuma kallonta yana kuka ta tabbatar da ba'a hayyacinsa yake ba. Hakan yasa ta matso daga kan gadon ta sakko a hankali take binshi tana tambaya. "Baban hawwer wai me ke damunka ne?, ka min magana mana".  



Yayin da shi kuwa yarinyar yake gani tana tunkaro shi hakan yasa ya kara sauri wajen jan gindin da yake yana yin baya yana fadin.  "Na shiga uku yau naga ta kaina, dan allah kiyi hakuri karki kashe ni shin dan naki taimaka miki shikenan nayi laifin da za'a azftar dani har haka. *DAGA TAIMAKO*   dan allah karki kashe ni". 




Ummiey da jin wannan kalamai na fita a bakin mijin nata sai tayi tsaye cik! Tana kallon shi cike da mamaki tana cewa "Lalai baban hawwer yau ba lafiya kake ba. Yanzu ni din kake cewa zan kashe ka ni?". 

Yayin da shi kuma yake jin wani abun daban sabanin abunda take fada.  Domin shi yarinyar yaga ta tsaya tana gagaba dariya kafin ta fada da murya mai fitowa bibiyu. "Kai muktar ka sani ka debo ruwan dafa kanka, a cikin kifayen da kake kamowa yau ka kamo ajali ka. Nan take yaga wata wulshe-shiyar wuka ta bayyana a hannun yarinyar. 





Ihu! Ya fara kurmawa yana fadin "Wallahi na tuba baran kara ba, dan allah ki yafe min duk abunda kike so zan baki. Duk lokacin da kikaji yunwa ki dinga zuwa ina baki abinci ko da kuwa zakiyi ci Goma ne a rana amma dan allah ki taimaka kiyi min rai karki kashe ni".  Ummiey taga abun da mijin nata yake ya fara yawa harda ihu nan ta fara tunanin ko ta leka ta kirawo makwabcin su ne. Kuma sai dai tace bari ta karasa gare shi.  Tahowa tayi cikin sauri ta mika hannunta zata taba shi. Ihuu! Ya kurma mai razanar wa kafin ya zube kasa sumame. domin shi yarinyar ya gani ta zo kanshi ta daga wuka zata caka mishi................





Mujee zuwa.



Autan writers nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 5-6



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽


THIS PAGE DEDICATED TO YOU.


NASMAT 


ASMART


MARYAM AMIN


SIS HAFSAT


MMN AFNANN


KHADIJA BABY


KHADIJA 🤔


KHAIRAT 💃🏻


MMN SADIQ 


KAMALA MINNAH 


Love is my everything. It’s everywhere. It’s in the messages you send me, it’s in the words you say to me and it’s in your eyes when you look at me. Love is in my heart and in my thoughts. Love is you and me. 👆🏽 I love them ☺



FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----






         *Karshen pagen baya...*

Tahowa tayi cikin sauri ta mika hannunta zata taba shi. Ihuu! Ya kurma mai razanar wa kafin ya zube kasa sumame. domin shi yarinyar ya gani ta zo kanshi ta daga wuka zata caka mishi»   Ummiey gaba daya ta firgice kamar ta kurma ihu! Itama.  Ganin mai gidan nan nata a kass sumame. A rude tayi waje tana zubda hawaye. Da sauri taje ta bude randar kasar ta wacce ruwan ciki yayi sanyi sosai kamar ansa kankara tasa moda ta kwalfo tayi cikin daki da gudu. 



Tana zuwa batayi Wata-Wata ba ta kwaraya mishi gaba dayan ruwan da ta debo. Firgi-git ya mike zaune yana nishi yana yan waige-waige kamar wanda yake neman wani abu  dayan hannun sa kuma goge fuskarsa yake domin ruwanda Ummiey ta kwaraya mishi. Ganin baiga abun da yake zatan gani ba yayi saurin mikewa ya nufi kofar daki a guje ya rufe ya sakala kubobi biyu yana fadin. 



"Ummiey wllh kashe ni zatayi taimaka ki kama a jawo wardrobe  din nan a kara rufe dakin".  Ummiey kam tsaye tayi ta saki baki tana kallansa yanda duk yabi ya rikice yake abu kamar mahaukaci.  "Baban hawwer wai  lafiyar ka kalau kuwa? Ya kake wasu irin abubuwa ne haka wanda ban taba ganin kayi kwatan-kwacin kalar su ba?".  



Tsawa ya daka mata kamar yanda ya saba dama baya jiya mata dadi, ba dan Ummiey mai hakuri ce ba da tuni ta bar masa gidansa to amma sai akaci sa'a irin matan nan ne masu hakuri tayo gadon gidansu dake babban ta shine limamin masalacin juma'ar anguwar kuma baban malammi ne masani.  Itama kuma haka tayi sauka har biyu. 

Zabura tayi tsawar da ya daka mata.  "Nace miki kizo ki kama wannan wardrobe din mu kai mu rufe kofar aljana ce in ta sake shigowa kashe ni zatayi". 



Ummiey sai yanzu ta gane mijin nata gamo yayi. "Baban hawwer wacce aljana kuma"?.  "Oh! My god ya fada. Tunda bazaki kama min ba baza ki taimakawa mijinki ba so kike ta halaka ni to bari in kai ni ai zan iya". Kiki-kiki ya jawo wardrobe har kofar dakin ya danne kofar. Danne wa keda wuya yaji an fara girgiza kofar dakin da gudu ya haye gado ya lulube. Ummiey ce tazo kanshi ta fara tofa mishi addu'o'i har allah ya taimaka barci yayi gaba da shi.  



Tunda asuba da ya tashi yaci gaba da zabur-zaburansa. Ummie na tofa mishi addu'a amma taga abun yafi karfita hakan yasa ta dauki waya ta kira babanta tana kuka ta gaya mishi duk abunda ya faru. Yace gashi nan zuwa. Mukhtar ba abunda yake  sai surutai duk bayan yan mintuna kuma sai ya dinga tsorata yana boyewa yana fadar "gata nan gata nan".!   Ummiey ita kanta ta shiga rudani. 



Ba'afi mintuna 20 ba malam hamza ya karaso gidan koda Mukhtar ya jiyo sallamarsa da gudu ya fito ya makal-kale malam yana surutai saida malam yayi da gaske tukun ya raba jiknsa da na Mukhtar lokacin ya fara tofa mishi adduo'i tukun ya samu haukan da yake ya dan lafa malam yasa shi ya zauna a tabarma da ummie ta shimfida. Bayan sun zauna ne malam ya fara karanta ayyatul kursiyyu tare da sauran ayoyi masu karfi.  Ba'a dade da fara karatun ba sai ganin wannan yarinyar ta bayyana cikin kayan da Khadija ta saka mata.  A gaban malam ta zauna hade da musu sallama. Muktar har zai ruga malam ya zaunar da shi. Hatta ummie ta tsorata domin ganin abun tayi kamar a mafarki. 



Malam ya kalle ta yace "baiwar allah me wannan mutumin ya miki an bani labarin irin azabtar da shi da kika yi jiya". Muryar ta ba dadin ji tace, "ka tambaye shi malam shi ai yasan abunda yayi".  Malam baiyi gardama ba ya juya ga muktar ya tambaye shi me ya mata. "A tsorace yac malam wallahi ba abunda nayi mata shagona taje tana nuna alamun yunwa take ji a rana ta farko na kore ta a rana ta biyu kuma ganin ta takura min na dake ta". 



"Karya kake muna fiki azzalumi macuci, Ko daya ba dan wannan ne na shiga rayuwarka ba. Wannan ma nayi ne dan in tabbatar da rashin mutuncin ka da mutane ke fada sai naji kai da bakin ka ma fada kake. Malam muktar Shin har ka manta abunda kayi shekara daya da rabi baya da suka wuce?.  Yarinyar ta fada cikin tsiwa tana hararen shi. Nan fa kwakwalwarshi ta shiga juya mai yana kokarin tuno wani abu.  Ganin ya shiga dogon tunani ta sake daga mishi wani tsawan wanda ita kanta ummie ta firgita kamar ta fada daki taji.  "Kaaaai!  Mugu wato har ka manta yaron da ka kashe ka rabasu da dukiyarsu ka raba yaya da kanwa. a fadama ko?".   Dummm!  Gaban muktar ya fadi jin ta tado zancen da a tunaninsa ba wanda ya san shi daga allah sai shi sai kuma wannan yarinyar.  (What!) "Yaron da ya kashe?".  Ummiey da malam ne suka fadi hakan a tare. 




Bugun kirjinsa ne ya tsananta nan take jikinsa ya fara bari. Motsowa ya farayi gaban Yarinyar yana fadar "Dama ke aljana ce ban sani ba. Don allah ki rufa min asiri karki tona wannan sirrin duk abunda kike so  zanyi amma ki taimake ni karki tona wannan sirrin...."  Tsawar da ta daka mishi ce ta tsayar da shi nan take ta wani bata rai fuska ba wal-wala. "Bani bace domin dani ce da bazaka kwana ba a ranar. Ka basu labarin abunda ka aikata wa wannan yarinyar da kanka, in kuwa ba haka ba yanzu ka gayawa yan garin ku". Ta karashe maganar cikin daga murya. Nan take tsoran Mukhtar ya karu. "To-to bari in fada amma dan allah karki min komai".  



Malam da diyarsa ba abunda suke sai kallo da sauraren ikon allah. Ummiey tunani take shin wannan wane BOYAYYEN AL'AMARI ne? Wanda bata sani ba game da mijinta. Ita dai bayan mugun halin sa da kowa yasan da shi bata kuma san da wani ba. Mukhtar ganin kowa yayi shiru shi ake saurare ga kuma wannan aljanar da ke mishi wani mugun kallo mai tsoratarwa. Ya shiga basu labari..............................




Mujee zuwa.



Autan writers nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 7-8



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




THIS PAGE IN DEDICATED TO YOU.



_*QUEEN HAUWANCY AUTAR MARUBUTA*_ 🤓



_I love you to the moon and back, and you know that. I will never let you down, even if you make me mad, you can always ask me advice, I will never leave you._



💃🏻💃🏻 ```Duk illahirin yan writers na zamani suna ji dake yar auta kaman yanda nake ji dake nima ☺  kina sakamu nishadi Da  Littafin ki 💞💦💞ILLAR BASHI💦💞💦 🤣🤣🤣 Ni ban taba jin irin wannan gidan sunan ba hatta ruwan da za'a sha ma bashi mai ruwan ya zuba 🤣 Dan akuya za'a yanka shima bashi 🤣 Abincin gidan bashi🤣 Kayan miya bashi🤣 Ba beauty bama koni bazan tsaya ba 🤷🏻‍♂🙇🏻


Kina wuta ina binki da fetur yar kanwata 😜Allah dai ya kara basira```




FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----






         *KARSHEN PAGEN BAYA*

Mukhtar ganin kowa yayi shiru shi ake saurare ga kuma wannan aljanar da ke mishi wani mugun kallo mai tsoratarwa. Ya shiga basu labari

» Ya fara da cewa Kimanin Shekara daya da rabi baya da suka wuce, lokacin ba'a fi watani uku da yin aure na da Ummiey ba. Lokaci ne da na shiga mawuyacin hali talauci ya min dankar kazar uwar ba'u. Ba komai ne ya kara zafin talaucin ba sai matsalar da muka samu da ogan gare jin mu na bar aiki. 




Nayi buga-buga na shiga na fita domin in sama abun yi amma abun yaci tura, duk inda na nema aiki bana samun aiki. Ranar wata laraba da naga abinci sakawa a baki ma yana shirin gagarar mu, Hakan tasa na shirya na dauki gatari na nufi jeji domin nayo itace na sayar. Hanya nabi ina tafe ina tunanin yanda rayuwa duniya tamin tutsun  jaki lokaci guda na surmiyo kasa. 

 Rashin sa'a na ya tsananta ni kam bansa yama zanyi ba domin ko faskaran ban iya ba.

Naje ratsa wata fadama naji kamar maganar mutane a cikin wani dan lungu  ina lekawa naga wasu yara ne guda biyu na dan tsorata da ganinsu kamar yanda suma suka frigita yarinyar ta kankame na mijin wanda ya kasance yayanta ne. Bayan yan tambayoyi da nayi musu suka bani amsa nan na dan saki jiki da su. Nace su fito muka sama waje muka zauna na tambaye su me sukeyi a nan. Namijin ne ya kalli kanwarsa hade da cewa "Rasheda in fada mishi".  maganar da Yarinya tayi ya tabbatar min da yarinya ce mai wayo da hankali.  "Eh yaya na ganshi da manyan kaya ina ganin kamar mutumin kirki ne ba irin su kawu mansur ba".  Yaron yace "To amma amana".  Na kallesa nace mishi "yaro ka yarda dani bazan cuce ku ba. Saidai ma in taimaka muku".

Kwarai a lokacin da tausayin su a raina.




Yaron ya shiga bani labari kamar haka:  Yace mahaifinsa mai kudi ne duk anguwar babu kamarsa a dukiya. Yana da kani daya yaya daya. kawu abba da kuma kawu Mansur kawo abba shine karame wato kanin babanmu saurayi ne kuma shi mutum ne mai tausayi sabanin kawu mansur wato yayan su shida baban mu.  Kawu abba yana san mu sosai mun shaku da shi sosai dake a gidan mu yake da zama shima yana da dakinsa daban. Hatta makaranta shi yake kai mu.

Ranar wata alhamishi ce mun dawo daga school muka tarar da abban mu da kuma kawu mansur suna rikici cacar baki abun kamar a buga. bamu san me ya hada su ba, koda ganin mu sai kawu mansur ya nufo hanyar fita wajen har ya kusan zuwa kofa ya juyo yayi bakaken maganganu hade da barazana wa baban mu, sannan ya fice  baban mu yaji haushi sosai  domin a lokacin daki ya shiga ya rufo.  Kawu abba kuwa yaje yana tambayar maman mu ta fada mishi abunda ya faru amma taki gaya sai dai itama zubda hawaye take. 



Da da dare.

Har wajen karfe  sha daya baban mu baiyi barci ba domin kuwa yasan halin dan uwan nasa zai iya turo mishi barayi su kwashe kudin kamar yanda ya fada.  Kudin wasu filayan sa ne guda biyu ya sayar million biyu da rabi shine kawu mansur yazo ya tsare shi wai sai ya bashi million daya yaja jari. Shi kuwa baban mu yace yayi hakuri ba yanzu ba yanzu akwai abunda zaiyi da kudin. Shine abunda ya faru har kawu mansur yaji haushi ya hau fada harda barazana. 




Karfe 12:30am da yaji shiru-shiru ya kwanta a tunaninsa dama barazana ce kawai.  Bai dade da kwanciya bq yaji hayaniya a kofar gida kuma kamar muryan mai gadi can kuma sai yaji ya kwala wani ihu! Wanda ya shaida mishi ba lafiya ba. Cikin sauri ya dauki jakar kudin ya nufi dakin kawu abba wanda muma a can muke a kwance. Bayan ya tayar da mu ya bawa kawu abba jakar kudin yace mu gudu ta kofar baya ga barayi nan sun zo wai shi zai tsaya in suka zo yace kudin basa a tare da shi.  




Kawu abba yayi juyin duniyar nan a kan baban mu ya taso ummanmu mu gudu tare amma yaki. Jin ana bubuga kofar palo ana neman ballata a shigo yasa ya ja hannun kawu abba har bakin kofar baya ya bude muna muka shiga nan fa muka bude yar kofar muka hau gudu. Bamuyi nisa ba mukayi yo wani ihu wanda muka tabbata na baban mu ne. kawu abba ya mika min jakar yace mu shiga wani dan lungun mu buya bari yaje ya gano.  Haka kuwa akayi muka shiga wani dan guri mai duhu muka boye shi kuma ya koma,  ko da shigarsa palo sai ya tarar an kashe baban mu da maman mu 'yan daban suna ganinshi sukayi chaf da shi suna cewa ga wanda aka bawa ajiyar kudin. 



Baban cikin su wani kato ne baki mumuna fuskarsa kadai abar tsoro ce.  Shine ya tambayi kawu abba cikin tsawo ya fada mishi ina kudi amma yaki.  Nan fa suka hau bugo naushin sa da mangarar sa. Hada masu  yankarsa da dai yaga zasu kashe shi sai ya tsaida su yace zai fada.  Nan take ya shaida musu kudin na wajen mu kuma ya nuna musu hanyar da muka bi.  Koda gama nuna musu sai ogan barayin nan yasa hannu biyu ya murde wa kawu abba kai nan ya fadi matacce, su kuwa suka biyo hanya neman mu.

Tun daga nesa na hange su sun nufo hanyar da torch a hannunsu suna ha haskawa da dai naga in suka iso gare mu ba shakka sai sun gan mu. Nan take na kama hannun kanwata na dauki jakar muka ruga a guje. Har mun danyi nisa tukun suka hango mu.  Suka kuwa rufa mana baya,  tsabar gudu ban sani ba ta tsakiyar wasu masifafun karnuka na anguwar mu nabi. Ai kuwa suka hayayako har sun nufo mu kuma suka juya sakamkon jin gudun barayin nan. Nan muka barsu suna fama da karnuka inda mu kuma muka tsero fada mar nan yau kwana biyar kenan da faruwar haka in mukaji yunwa sai in dauki kudi in shiga gari in sayo mana abinci.

Wata doguwar ajiyar zuciya nayi da jin labarin yaron nan. Nace "masa yanzu ina kudin?".   "Zan dauko maka ne kawai domin na yarda da kai ina ganin tausayi a idan ka kamar bazaka cuce mu ba".   A cewar yaron, kallonsa nayi nace "gaskiya ka fada yaro ni ba kamar kawun ku mansur bane ku dauke ni kamar kawun ku abba".    Nan take yaron ya tashi yaje ya daga wasu ciyayi ya fido katuwar jakar ya kawo gabana ya ajiye.  Kwata-kwata  yarinyar bazata haura shekara 8 ba shi kuwa babban namijin  zaikai shekara 13 ko sama da haka.  




Koda ya kawo jakar gabana ya bude naga makudan kudin dake ciki kudin da ban taba ganin masu yawansu ba a duk tsawan rayuwata.  Nan take naji zuciyata ta canza daga tausayi ya zuwa rashinsa zuciyoyi suka fara aikin bani shawar wari wasu na cewa in kashe yaran nan in mallaki kudaden wata zuciyar kuwa na cewa in dauke su in kaisu gidana.  Daga karshe dai na aminta da shawara ta farko wato in kashe sun nan kuma na fara tunanin hanyar da zan bi dan kashe su. Sai kuma na tuna a kusa da ruwa fa muke, banyi wata-wata ba nasa kotar gatari na na bigi kan yaron domin nasan shine zaifi bani matsala nan take ya fadi kasa matacce, da ganin haka sai yarinyar ta fara ihu! Ni kuwa ganin zata tona min asiri na shake wuyanta har ta langabe gaba dayansu na kwashe su na zuba a wani ruwa dake wucewa ta tsakiyar  fadama. Ruwan yaja su ya tafi da su, ni kuwa na dauko kudin na dawo gida nayi karyar cewa gonar mu na sayar mutane kuwa ciki harda matata da babanta gashi suka aminta sukayi farin ciki.  Ba'a dade ba na bude shago na kama sana'a dan gudun kar kudin su kare. Ko da ganin na sama wannan kudi sai na shiga sabuwar rayuwa wato ta rashin mutunci bana ragawa kowa kuma bana san kowa ya raga min watta matata taga canji sosai a tare dani, ko ta bangaren addini na samu tawaya domin ko makaranta daina zuwa nayi wannan shine abunda ya faru inji Mukhtar.



"Innalilahi wa'inailaihir raji'un". Wannan kalmar ce take fita a bakin Ummiey da kuma mahaifinta. Nan da nan ummiy ta fara kuka tana fadin "Mukhtar haka kake dama ashe zaka iya kashe mutum ashe ba iyakar rashin mutun cin kawai kake da shi ba harda rashin imani?".  Haka ta jero mishi wadan nan tagwayen tambayoyin wanda shi kanshi baisan wace kalar amsa zai bata ba sai kawai hawaye dake fita a idanunsa da gani kasan yayi nadama. Ummiey zata daga baki tayi magana abbanta ya dakatar da ita. Lokacin aljanar tace ina zuwa.  



Bat! Ta bace lokaci daya kuma sai gata ta dawo ita da wata yarinya wacce da gani a galabaice take tana cikin kunci da tsadar rayuwa kaysn jikinta kadai zasu fada maka hakan.  Koda yarinya da aka kawo mai suna maryam taga Muktar sai ta fashe da kuka ta tashi ta ruga a guje, har ta kusa kai bakin kofa aljanar nan ta mika hannunta wanda a nan take ya kara tsawo ya kamo maryam dake shirin guduwa.  Koda ji an sakalota sai ta fara kokarin kwacewa tana fadar "Shine ya kashe yaya sadiq dan allah karku bari ya kashe ni, macuci ne". 



Aljanar tace kwantar da hankalinki kawata ba abunda zai miki tsaya baya na. Mukhtar yayi matukar girgiza da ganin maryam wanda shi a tunaninsa saida ya kasheta tukun ya Jefata ruwa. "Wannan itace yarinyar da Mukhtar ya kashe yayan ta kuma yayi yunkurin kashe ta itama amma allah baiyi ba. Ta kubuta da rayuwarta daga mutuwa wanda ta fada wata rayuwar kuma wacce gwarama mutuwar da ita.  Wannan yarinyar da kake gani fadamar nan ta koma mata gida duk sanyi duk zafi a nan take da safe take shigowa gari ta nemi abincin da zataci da dadare kuma ta koma fadama.  Kwana uku baya nazo wucewa na ganta ana mata tamkar yanda kamin wato taje neman taimako ya bata abinda zataci ya kore ta. Ta koma gefe zauna tana kuka saboda tsabar yunwar da take ji dan duk ranar bata sa komai a bakinta ba. Koda naga haka sai na rikida zuwa tsohuwa na kai mata abinci bayan taci ne nake tambayarta ina iyayenta nan ne ta bani labarin duk abunda ya faru. Kaji irin tsadar rayuwar da ka jefata kai kuwa ka shiga farinciki. Mukhtar hukuncin da na yanke biyu ne ciki ka zabi daya....………………………





Aikin ki na kyau aljanar fatima.



Mujee zuwa.



Autan writers nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 9-10



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




_Wannan pagen duk girmansa na masoya king ne a duk inda kuke._


💃🏻 *Kowa ni yake jira to gani na iso, Samari yan mata na nesa ku marmatso. Domin kar ayi babu ku haka sam! Sam! Bani so.  Wannan pagen ku ne karku bari ya wuce wanda aka baya nan bai more kallo ba* 💃🏻😜


😍 wayyo my fans you will kille me with you love. Ina sanku ina alfahari daku  *ANA TARE* supports 😘🤝



FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----






         *KARSHEN PAGEN BAYA*

Kaji irin tsadar rayuwar da ka jefata kai kuwa ka shiga farinciki. Mukhtar hukuncin da na yanke biyu ne ciki ka zabi daya.»   Mukhtar ko dai ka mayarwa da yarinyar nan dokiyar ta ta hanyar bata duk wani abu da ka mallaka ta sanadiyar dukiyar su, ko kuwa ka zame mata ahali kamar yanda ka rabata da yayanta a baya, Dole ka bata kulawa kamar wacce zaka bawa diyarka ko kuma ma tafi haka. Domin da bazarta kake rawa. 





Malam ya kalli aljanar yace "lalai wannan hukunci yayi duk mai adalci haka zai yi, saboda haka ni na aminta Mukhtar sai ka zaba daya kodai ka tatara duk abunda ka mallaka hatta gidan nan dan da a gidan haya kake ka mayar mata ko kuwa ka rikr ta zabi ya rage ga mai shiga rijiya ko ya shiga ta kai ko ya shiga ta kafa. Mukhtar yace na aminta da zabi na biyun zan riketa amana isha'allah domin ni yanzu NAYI NADAMA sannan zan ci gaba da rokon allah ya yafe min laifukan da nayi, Kuma na gode wa wannan aljana da ta tsamo ni daga cikin halaka. Maryam zo mana daga yau kin zama 'yata".  Ya mika mata hannu da farko taki amincewa saida aljanar tasaka baki tukun. 




Ummiey farin ciki tuni ya mamaye ta jin ta sama 'ya a bagas! Ta sama mai maye mata gurbin yarta hawwer da ta mutu.  Aljanar ce ta wani tashi saman iska gaba daya iskan wajen ya hau zagaya ta ita kuwa ta fara wata kalar shu'umar dariya marar dadin saurare, Magana ta fara yi muryar na fitowa uku-uku  bazaka iya banbance namiji ne ke maganar ba ko mace ko kuwa yarinya.  "Nice nan aljana SUFURATU marainiyar aljana, Sai na cika burina na ganin ba maraya da zai kasance a cikin kunci. Aikin ma yanzu na fara. Sannan Mukhtar ina gargadin ka a kan maryam kuma ka zama mai adalci domin zan dinga bibiyar rayuwar ku". 




Sama tayi kamar wacce ake ja tana tafe tana gagaba dariya, su kuwa da gaba daya in aka fitar da malam ba wanda bai tsorata ba, domin ummiey har dan fitsari ne ya fara kubice mata.   Tun suna ganinta har ta bace cikin gajimare. Malam ya kara yiwa Mukhtar nasiha sannan ya bashi addu'o'i wanda zai tuba ga allah ya kara da cewa ya yawaita sadaka, tukun ya musu bankwana ya koma. Su Mukhtar sunga abun mamaki yau kam duk cikin su ba wanda tsoro ya sake shi, nan fa aka shiga tarairaya da tattalin maryam dan gani suke kamar itace ma aljanar. 





Acan gidan kamala kuwa da asuba da suka farka sama ko kasa suka nema yarinya suka rasa sun shiga rudu da tashin hankali don har ga Allah yarinyar ta shiga ransu fiye  da zato, a cikin su ba wanda  baiyi mafarkinta ba. Khadija ta zauna tayi zugum ba abunda take sai faman kuka tana tuna yarinyar nan da irin shakuwar da ta shiga tsakanin su tun a jiya.  Yau komi bata iya ci ba har wajen karfe 9:00 ta zauna ne kawai ta zurawa kofa ido a zatanta zataga ta shigo. Kamal da yaga abun yayi yawa yayi lalashin amma kamar kara haukatata ne yake. "Khadija tunda kinki hakura tashi muje nemanta".  Firgigit ta tashi da gudu ta shiga ta dauko hijab. Sun taho sai sauri take tana leke-leke wani wajen ma har gidaje take tatan bayawa. Amma har wajen 11 babu labari. Duk sun gaji sunyi tikilis.  Sufuratu tazo wucewa ta hange su a karkashin wata inuwar mangwaro da sauri ta sauko kasa tazo daidai inda suke, ita har tama manta da su, "Allah sarki da gani nemana kuke na gode da halacin da kuka min bazan taba mantawa da ku ba. Badan aikin dake gaban Sufuratu nada yawa ba da ba makawa DAKE ZAN ZAUNA".duk abunda take fada baji ba suke kuma basa ganinnta.  Kwasar su tayi ciki  abun da baifi seconds 5 ba ta kaisu gida. Mamaki iya mamaki sunyi shi ya akayi hakan ta faru mu da muke tsaye a gindin bishiya kuma gamu a gida. Tambayar dake dauke a bakin ko wannan su kenan. 





"Na tafi sai mun sake haduwa" gaba daya sunji an fadi wannan saidai basu san taka mai-mai ta inda muryan ta fito ba. Nan fa suka shiga dube-dube.  Aljana Sufuratu kenan yarinya ce a cikin aljanun ma domin da kadan zata haura shekara 150 musulmar aljanace labarin ta nada dan tsayi da abunda yasa ta fara taimakon marayu. Kasan cewar itama yarinya ce yasa tafi shiga rayuwar yara marayu, dan a ganinta sunfi ban tausayi. Indai taga yarinya cikin wahala saita bibiya rayuwarta ta kuma san labarinta. A yanzu haka ta bar garin abuja ta nufi bauchi.  




Inda ta sauka a G.R.A anguwar masu kudi ce, kowa harkar gabansa yake yi tankama-tankaman gidaje ne tsabar rana da akeyi yasa kowa yana cikin gidansa. A farkon anguwar Safuratu tayi gamo da abunda ya bata mamaki wata yar digil gilar yarinya ce karama wace in tayi gudu takai 10 years ko 9 da rabi. Sanye take da kaya atamfa dinkin riga da sket sun mata kyau sosai da gani kasan ba yar talaka bace.  Kanta wani dan bokitin ruwa ne wanda da gani kasan yafi karfinta jan haline kawai yasa take dauke da shi sai jibi take da alamun gajiya a tare da ita daga nesa ta debo shi.  Ba wani abu yabawa Safuratu mamaki ba sai ganin gari da wuta kuma zaiyi wuya a sama gidan da ba tanki a anguwar.  Hakan yasa tace a ranta bari ta bita sai taga wace marar mutun cin uwace wannan, da take neman hallaka diyarta.   




 kofar wani gida ta kalla nan take ta saki murmushi, da kyar ta samu ta sauke ruwan ta ruga da gudu kofar gidan nan wata yar baby ce (Diyar roba ta dauka)  nan fa ta sama waje ta zauna ta fara wasa da ita ta bar ruwan da ta dauko din kan titi, dake motoci basa wucewa. "Kutumelesi lalai fatima yau kuwa zaki daku wato har kin sama damar taba yar babyn nuratu ko".  Kafin ta juyo tuni yarinyar dake maganar ta warce yar babyn hade da kifa mata mari wanda saida ta gigice. Kuka ta farayi Wiiii!-Wiii  ta juye ta kalli wacce ta mare ta din tace "Wllh sai na gayawa mama asiya".  "Jeki ki fada din kiyi sauri kar kuda ya riga ki". Cewar mai marin,




Fatimar bata kara cewa komai faman kuka da take ga hawaye ga jibi abun yayi mata biyu. Zuwa tayi taje ta fara kikiniyar dora bokiti a kai,Da kadan ta fadi ita da ruwan badan Safuratu tayi sauri ta tallafa mata ba. Dungwai-Dungwai ta hau titi ta tafi tana kugin kuka. a bakin wani makeken gida ta tsaya tana kwalla kira "Me gadi bude-me gadi".  Aljana safuratu dake binta a baya ta tsaya ta kare wa gidan kallo tas! Taga a duk anguwar gida daya ne za'ace sunzo daya da wannan gidan ta girman shi da kyawan shi, da gani kasan an kashe nera, "To ke kuwa me zakiyi a nan gidan ko wata sabuwar tsokanar ce domin bana tunanin yar nan gidan ce ke".  Safuratu ke magana ita kadai.  Mai gadi ne ya taso da sauri yana masifa "Ke ki tsaya inzo in bude mana kin ishi mutane da kira". Bayan ya bude ya gallah mata harara wa kuma ya tabaki kika zo kina bude mana baki?".  "Zulaihat ce ta mare ni". Ta fada lokacin da ta wuce ciki, "Dan an dan mare ki shine zaki ishe mu da kuka kuma, yarinyar nan dai anyi ja'ira". 




Tun a kofar falo ta fara kira "Aunty ameera-aunty ameera". Da sauri ta fito tana mata masifa to jarababa kin dawo wato har kinzo kin fara takurawa mutane".  Ameerar ke fada haka lokacin da ta sauke mata ruwan tana juyewa. Hanyar daki ta nufa da sauri ta kamota, ubanki nace Fatima dan iskanci ina zaki?. Ko kina nufin wannan ruwan ne zai ishe ni wanki?".  "Aunty zuwa zanyi in gayawa mama asiya Zulaihat ta mare ni".  Ta fada tana shashekar kuka "Muna fuka ai ba'a banxa zata mare ki ba da abunda kika mata, oya ni wuce ki karo min ruwa wllh sai kinyi sawo uku nan gaba". Rushewa tayi da kuka "wllh ni dai na gaji wajen yayi nisa aunty ki tausaya min ki deba a can". Wani tankin ruwa ne ta nuna da yatsarta ya cika sai zuba yake ma. A lokacin Safuratu ta gane cewa ba rashin ruwa yasa aka tura fatimar ba mugunta ne kawai. 





 "Kan uba! Iyee fatima ni zaki dinga fadawa kin gaji in aike ki kice kin gaji?".  Kwashe ta da mari tayi dan karfin marin  har saida ta kusan faduwa.  Wani sabon kukan ta dora dashi mai karfi. Da gudu naga wata budurwar ta fito daga falo tazo ta kama fatima tana kalan waccan, "Haba ameera wai miyasa ke muguwa ce bakya jin tausayin yarinyar nan ko kadan shin so kike ki kashe ta ne?. Kin turata debo ruwa dan iyayi bayan ga ruwa nan yanzu kuma kina dakar ta gaskiya karki kara dukanta".  




"An daka din kiyi abunda zaki yi bari ma ki gani inci ubanta a gaban ki inga ubanda ya isa ya hanani". Fatimar ta nufa ta daga hannu zata kara marinta da sauri Wacce ake kira Iddau charaf! ta rike hannun, "Ameera wllh bazaki dake ta ba a kan me wato ita batada gata ko?". Ameera tace, "Sake min hannu, sakar min hannu".  "Anki a saki ki kwace in kina da karfi".  Haba wa ai kafi ta rufe baki tuni Ameera tayi kukan kura ta chakume ta, nan fa suka hau kunce harda naushe-naushe. Safuratu na tsaye tana kallan ikon allah abun ya fara rikitata.



 Wasu yan mata ne a daki su biyu kusan kansu daya da kadan dayar ta dara daya Zan iya cewa daya shekarar ta 12 dayar kuma 14. Daga ganin su kaga mararsa jin magana ta kwaliyar da sukayi ma kadai ta isa ta sheda maka hakan ba kauya wa day ba wannan kwaliyar taci uwar ta kauyawa day a hauka. Kamar ance wa mai suna Asma'u ta kallo waje ta window.  Wani dan kara tayi na jin dadi nan da nan ta mike.Yawa bigi ciki aunty ameera, karki bari ta kada ki aunty iddau". (fiddausi suke kira da iddau) koda jin haka naga dayar ta bar abunda take da gudu tazo ta haye kan gadon itama ta fara leke. Tsalle tsalle suke suna dunkule hannu suna fadin bamu rabawa saidai mu kara zugawa bigi cikin dan bari bakin. Maganar da suke tana kaiwa har kunnuwan masu fadan amma basu bari ba sai ma kowacce ta kara dadagewa. Su kuwa su Asma'u komawa sukayi Kamar dai supports a filin Wrestling ko wacce ta zaba wacce take so............



Mujee zuwa.



Autan writers nee  king boy














👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 11-12



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



😍😽 *IN DEDICATION TO YOU OUR NASMAT* _Ina ji dake wllh in kikayi fushi dani ina zan saka kaina 😪 Da bazarku nake rawa ZAMANI You're my blood body Au!_ 🙊🤣


😍 I love you all my fans 💃🏻


Even if you haven’t found your love yet, don’t worry, with time comes a lover! 😍😘



```FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----```






*Afuwan Readers nayi amfani da SUFURATU  Maimako SAFURATU a farkon pagen baya.*





        *KARSHEN PAGEN BAYA*

Maganar da suke tana kaiwa har kunnuwan masu fadan amma basu bari ba sai ma kowacce ta kara dadagewa. Su kuwa su Asma'u komawa sukayi Kamar dai supports a filin Wrestling ko wacce ta zaba wacce take so...»Wata mata ce mai jikin sosai  da gudu ta fito tana "kai kai ku bari mana" Da kyar ta samu ta raba su a cikin su kowacce taji jiki. Sai Huci suke suna hararen juna. "Me ya hadaku kuke fada ku da kullum bakwa rabo da rigima kamar Ba yan uwa ba". "Momy wai dan na daki waccan shegiyar yarinyar shine tazo wai zata rama mata". Ameera ta fada tare da nuna Fatima dake tsaye gefe tana hawaye.  Harara matar ta galla mata tare cewa "muna fuka ai kinga ta koma gefe tana hawayen munafurci, ke kuma Fiddausi wllh hawainiyarki ta kiyayi ramata, in badan iskanci ba saboda ta dake wannan Yarinyar zaku kama fada da yar uwarki".



Asama'u da Nasima (Suke kira da nasmat) Ba karamin haushi sukaji ba ganin mama asiya taje ta raba fadan.  Mtseewwww!  A tare suka ja tsaki, "Wannan mama Asiyar gaskiya mu dai bata gyara mana ba wallahi allah ya isa". Cewar Nasmat.  Asma'u taja tsaki mtswww!,  "Ni har ta bani mugun haushi wallahi Duk da tana momy na.  ta wani taho tubur-tubur da ita kamar kaza buloras irin lutayan nan kinsan fa basa iya tafiya sosai in suka girma bari kiga irin tafiyar maman mu". 



Nan fa Asmart ta sakko ta fara nuna kalar tafiyar, harda irin Dafe kugu yanda yan lukutaye suke in sun gaji.  Da sauri nasmat ta sakko "dallah malama ba haka take ba bari kiga ni".  Itama kwakwayan tafiyar mama asiya ta shiga yi.  Bayan tayi tafiya mai dan tsayi Asmart na tsaye na kallo da gudu ta dawo tana fadar "kuma bari kiga yanda take in taci ta koshi ta kasa tashi daga kwance".  Kwantawa tayi Rairan a kan katifa tukun ta fara wani jujuyawa tana irin juyin nan da karfi abun in kagani dole kayi dariya.  Asmary ta bushe da wata irin mahaukaciyar dariya. Daga bisani kuma ta dan tabe fuska alamun tayi fushi.  Kulli ta kaiwa asmart a baya "Dan ubanki ki bari mamana ne fa".  Asmart ta mike tsaye dariya ta kusan kubuce mata,  matawa nayi kuma ai ke kika fara. Gaba daya suka saki dariya har suna rike ciki kamar mahaukata.



Fiddausi ta tace "Haba mama asiya ya za'ayi.....". Tun kafin ta idasa maganar mama asiya ta daka mata tsawa  "Ke rufe min baki wallahi ko in gwab gwabje ki yanzu a gurin nan, marar kunya"  Fiddausi tafiya tayi tana bubuga kafa tana gunguni. "Ke me kike cewa. Zagina kike ko?".  "Ni dai bance komai ba".  Kunnan fatima mama asiya ta kamo hade da jawota gabanta. "Munafuka ke kuma zo nan uwar iyayi, wato dan an dan bige ki ne kike wa motane kuka ko, to na kori mai rama mikin muga kuma uban da zai ramamiki yanzu".  




Dankwashin ta tayi a kai hade da cewa "Ameera gata nan ki mata abunda kike so inga wanda ya isa ya hana ki ko uwarta tazo nan bata isa ba balle ma tuni ta bar duniyar". Tana gama fadar haka ta tura Fatima ta fada jikin Ameera ita kuwa ta koma falo. Koda jin mama asiya ta fadi haka Sai ran Safuratu yayi mugun bace tuni idanunta soka koma jajur kamar garwashi, "Wato.marainiya ce shiyasa kuke gana mata azaba ko to kunyi na karshe". A cewar Aljana Safuratu tana maganar ne a kusa da su amma su ko kadan basa ji. 




Ameera ta dauki bokitin ruwa ta kara dorawa Fatima a kai maza wuce ki debo min Ruwa wllh sai kinyi sawu uku ko mutuwa zakiyk ba kuka ba".  Fatima tana kuka abun tausayi ta kama hanya ta koma debo ruwa, bayan taje ta debo a gajiye ta kawo amira ta juye ta kara bata bokitin wai ta koma. Fatima ta fashe da wani kukan domin ji take kafafunta kamar zasu tsinke dan gajiya, amma ba yanda ta iya dolenta ta karba ta tafi tana tagal-tagal mai gadi shi kanshi ya gaji da bude mata kofa, tuni ta bata mishi rai shi ba abun ya bigeta ba yayi ta aikinsa domin yasan yanda take a gun alhaji  Fatima na tafiya a gajiye jiri ya fara debarta  nan take ta fadi kasa a galabaice.  (Wayyo Rashin uwa)  




Wani alhaji ne yake tafe a cikin wata dan kareriyar mota tun daga nesa da ya hange ta ya fara cewa "Wa nake gani haka kamar mama ta?. Bai tabbatar da itace ba saida ta tafi faduwa, ai kuwa yana ganin ta fadi ya danno motar kamar wanda zai tashi sama dan tsabar gudu. Aljana Safuratu tayi niyar taimakawa fati kenan taga motar nan ta dirfafo gare su hakan yasa ta koma gefe. 




Wani mugun birki yaja ji kake kiiii! Kafin motar ta karasa tsayawa ya fara kokarin fitowa.  "Mamana! Mamana!" (Sunan da yake kiranta da shi kenan dan sunan kanwar mahaifiyarsa kenan wacce ta rike shi)

Tashi mamana me ya same ki, da sauri ya dauke ta yasa ta a mota sai ma da zai shiga mota tukun ya hangi dan bokitin can a gefe Ya kuma dubi jikin fatima ya ganshi a jike "tabbdijam Lalai Asiya baki so zaman lafiya ba".  Abunda ya fada kenan ya shiga motar ya fara tafiya.  Sanyin AC ne ya farfado da Fatima daga yar guntuwar sumar da tayi.  



"Oyoyo dadyna Yanzu kazo?.  Abunda ta fada kenan lokacin da ta kara matsawa jikinsa ta dan jingina da shi.  "Mamana me ya sameki ne na ganki a nan a kwance kuma da bokiti kusa da ke ga jikinki a jike ina zaki?". Shiru tayi na dan lokaci tukun tace "Baba ruwa naje debowa zanyi wanka". Hararar da ya daka mata tasa tayi saurin cewa "Aa baba ba wanka ba wanki zanyi".  Kalansa tayi taga ba annuri a fuskarsa nan take ta sake canza magana "Baba dama shukoki ne zanba ruwa basa san ruwan gidan mu". Tsawar da ya daka mata ta firgitata abunda abbanta bai taba mata ba kenan nan take ta fashe da kuka. Rai a bace yace, "Mamana ban sanki da karya ba karya ba halin mutanan kirki bane shin waya koya miki karya, in kuwa kika ce karya zaki dinga min to wllh kinji na rantse bazaki sake ganin hakoran dariyana ba". 


Cikin kuka tace,

"Dady kayi hakuri wallahi zan fada ma Aunty Ameera ce tace sai na debo mata ruwan wanki wannan sawuna na uku kenan  gashi na gaji amma taki ta hakura ta barni in huta". "What!  Yanzu duk kankartar ki ameera ta aike ki dauko ruwa?".  Kai ta daga mishi  "A ina kike dibo ruwan?, Su Asma'u basa gidan ne?".  "A can wajen makarantar mu ne. Dady suna gidan mana a daki suke ma". 



"Innalilahi!". Ji yayi kamar ya fashe da kuka domin allah ya gani ko shi bazai iya sawu biyu ba daga gidansa zuwa can balle ma wai ace wannan yarinyar kuma harda ruwa a kai. Ranshi ne yayi mugun baci Fatima sai surutu take amma saidai ya kada mata kai dan ko maganar ji yake bazai iyaba.  




Da gudu ya karasa kofar gidan ko daga odar da yake ya isa kasan ya dau zafi, dan in kana kusa da shi sai ka rufe kunnuwa,  da gudu mai gadi ya zo ya bude  yana shiga ya parking din motar ya futo a fusace ya nufi Garzali mai gadi baisan hawa ba baisan sauka ba yaji saukar mari a kumcinsa. "Garzali ashe kai aikin banza ne ban sani ba ashe a banza nake biyanka kudina in wata yayi".  Cikin murya mai rawa "Afuwan ranka ya dade bansan laifin me nayi ba". "Au bakama san miye laifinka ba ko uban wa yace ka budewa Fatima kofa yanzu in diyarka ce dan gidan ku zaka barta taje debo ruwa ne. To daga yau wllh in na sake kamaka da irin wannan laifin a bakin aikin ka".  Fuuu!! Ya wuce kamar jirgi  mai gadi ba abunda yake sai bada hakuri harda durkusawa a gun. Bayan alhaji ya danyi nisa ya tashi yace a kan wannan yar banzar yarinyar ana min barazana da aikina".  "Me kake cewa?". Inji alhji  "Aa Alhji cewa nayi ayi hakuri zan kiyaye".




Tun daga kofar falo ya fara kwala kira "Ameera! Ameera!". yana janye da hannun Fatima.  Nan danan saiga ta ta fito Jikinta na rawa dan tasan abunda ta aikata ko kadan batayi tunanin abban nasu zai zo war haka ba. "Dady gaaa..". Saukar tagwayen mari da taji ne ya hanata idasa maganar sai ihuu! da ta kwada mai karfi!  Kafin kace me falon ya kusan cika Da yara da manya bansan haka gidan nan keda iyalai da yawa ba sai yanzu. 




Asiya ce tazo ta rungume Ameera dake faman kuka. Alhaji ya fara magana. 

 "Ke dan ubanki baki da hankali ne ya za'ayi ki aiki wannan yarinyar wai ta debo miki ruwa har can wata uwa duniya baga kanan ki nan ba wanda suka fita me ya hanaki aike su ko zaluncine kawai abun, to wai ma inace dazun nan da aka kawo wuta Nasa aka kunna soma?".   "Haba alhaji dubi fa yanda ka kunburawa yarinyar nan kumatu kamar dai ba yar uwarta ta aika ba, kawai fa uniform dinta ne zata wanke kasan farare ne shine fa ta aiki Fatima ta debo mata ruwa a can kasan yafi na nan haske". Asiya ce ke maganar lokacin da take lalashin yar tata. 



"Asiya! asia! Sau nawa na kira sunanki,.?". 3 Ta bada amsa a Hatsale,  "To wllh asiya ki fita a idona zan miki rashin mutuncin da bakiyi zato ba wato duk ke kike daurewa yaran gidan nan gindi suke abunda suka ga dama ko?. To bari kiji in gaya miki wllh duk wanda yake so muyi zaman arziki da shi a gidan nan to karya ya taba mamana in kuwa mutun bai yarda ba ya gwada taba ta yaga abunda zai farubda shi".   Yana gama fadar haka ya kama hannun Fatima ya nufi dakinsa.  Ya fara tafiya kenan asiya ta fara gunguni kamar yarinya "Shikenan wato sai a raba kan yara a hana su shakuwa da juna". Maganarta ce tamai zafi sosai yaji bazai iya daurewa ba. Sakin hannun fatima yayi da gudu ya Nufe ta, Abunka da lukutar mata bata da gudu ta ruga amma baisha wuya ba wajen kamota. Koda yaje sai yasa kafa ya kwalfe ta nan  ta fadi ta fara wash! Wash! Wayyo ya karya ni.  Bai ko tsaya kallanta ba ya wuce ya dakinsa shida fati. 




Asmart da Nasmat ne suka kalli mama asiya tukun suka bushe da dariya ganin ta a kasa kamar an zaunar da buhun masara.  Kowa na gurin abun ya bashi dariya har kishiyoyin nata guda biyu dake tsaye a gefe. Saidai kowa yasan jarabarta duk gidan dama ba wanda zai iya mata dariya sai wannan biyun marar ji.  Ai kuwa kafin kace me ta yunkura da kyar ta tashi tubur-tubur ta nufe su wai da niyar ta kamosu ta daka,  kafin kace me tuni sun ruga upstairs tana biye da su koda tahau matakala na daya biyu sai sulbi ya kwashe ta ji kake tum ta fado kasa kamar an yarda buhun masara. Kanta ne ya bugu da kasa. Su asmart da suka juyo sukaga abunda ya faru sai suka dora da wata sabuwar dariyar.................






Hmmmmm Gidan nan za'a sha kallo naga alama. 




Mujee zuwa.




Autan writers nee  king boy












👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 13-14



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



THIS PAGE IN DEDICATED TO YOU


☘ *UMMU BASHIR* ☘


 *ZAINAB YUSUF*


*HUSAINI ATK (80K)*





```FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----```


               *KARSHEN PAGEN BAYA*


kafin kace me tuni sun ruga upstairs tana biye da su koda tahau matakala na daya biyu sai sulbi ya kwashe ta ji kake tum ta fado kasa kamar an yarda buhun masara. Kanta ne ya bugu da kasa. Su asmart da suka juyo sukaga abunda ya faru sai suka dora da wata sabuwar dariyar.


»» gidan ALHAJI SALIM S.O kenan babban gida ne dake cike da iyalai. alhaji salim mata hudu  gare shi saidai daya ta mutum yanzu uku ke a raye.  Asiya uwar gida  yaranta biyar biyu mata sune AMEERA DA ASAMA'U. Maza uku SAFIYANU babban danta  sai mai mishi YUSIF. Da kuma yayan ameeera ABBA. 



Mai biwa asiya ZUWAIRA 'Ya'yanta hudu FIDDAUSI.  NASIMA. ABDUL Sai ALIYU.   A  yanzu HAUWA'U Ce amarya yaranta biyu kadai kanana ILIYASU ABUBAKAR. 



Shekarar hindatu (Mamar fatima) uku a gidan ta rasu sai dai ta mutu ta bar fatima tana yar shekara biyu.  Yarinyar fara kyakyawa a duk gidan tafi kowa kyau domin ita ta dara mahaifiyarta ma kyau. Alhj kamal kuwa ya dauki duk san duniyar nan ya dora a kan fatima domin yana jin tausayinta sosai kasan cewarta karama kuma marainiya hakan yasa ya dauki amanarta yabawa asiya.




Irin san da yake nuna mata shi ya jawo mata ta zama kamar jaba a gidan in aka cire Fiddausi, maza da mata yara da manya baki daya ba mai ragawa fatima a gidan bata samun sauki da farin ciki sai abbanta na gida. 



Hakan yasa ma in baya nan sai ta shiga daki abunta wani lokacin tata barci wani tym din kuma tata kuka abunta. idan ta tuno mahaifiyarta. A labarin da nake baku yanzu fatima takai shekara 9 da rabi a duniya ta iya yiwa kanta komai. Dan ko da tana karama bayi mata ake ba, Asiya da dauda take barinta.  Fatima na shan wuya sosai Domin har ta saba da wahalar da yan uwan nata suke bata bama kamar  Asmart, da Nasmat. Wadan nan biyu ba irin wuyar da basa bawa fatima. 



*Cigaban labarin* 

Washe gari Fatima ce ta tashi daga barci ta kalli dan agogon dake ajiye a kan mirror dakin nasu firgigit ta zabura ganin karfe 6:10 bata yi sallah ba. Sauran yan uwan nata mata da suke tare a dakin ta kalla. Sai bacci suke abunsu. Fiddausi kawai ta tayar domin ita tace ta dinga tadata. fatima sauran ta kalla ita ba abun ta tashe su ba tasha fada in bataci sa'a bama har duka. Tashi tayi ta nufi ban daki a guje. Tayi alwala ta dawo ta tayar da sallah. Naji muku haushi sosai da baku ji karatun yarinyar nan ba. 




 A hankali bayan tayi fatiha take jan suratul الغا شية  ghaashiya. Muryarta na fitowa a hankali. Kamar kar karatun ya kare. Tayi zaman tahiya kafin ta karasa ta sallame. Tun kafin matar ta karaso take kwalla uban kira. "Fatu! Fatutu!" Da karfi. Fatima najin haka ta kama sauri allah-Allah take ta idar da sallah kafin matar ta shigo.





domin tasan halin mama asiya kwarai bata bata dadi kuma tafi kowa musguna mata a gidan.  Asiya dingishi take sakamakon double faduwa da tayi jiya. Banko dakin tayi. 



Kamar wacce zata karya shi. Ta tsaya a gurin ta kama baki. "Iyye! Gaga  'yar banza wato sai yanzu ma kike sallah baki tashi da asuba kinyi ba ko?. inji mama asiya. A zuciya kuwa tace "yarinya kina kokari domin kuwa ni banma yi ba tukun". Daidai lokacin fatima ta idar da sallah ta juyo ta dan risina tace, "mama asiya ina kwana". Dan ban kwana ba zaki ganni ne dan ubanki?.  Sunkuyar da kai kawai fatima tayi. "Munafuka Kaganta kamar wata salaha. To da ban kwana ba zaki ganni ne?, Tambayarki nake, Maza-maza ki iske ni a kitchen.

 Yau dake zamu hada kayan kari. Saura kuma ki ki zuwa da wuri ta kama kunnan fatima ta murda. "Kinga kunnan nan to sai na cira shi. Ko in ba-ba-laki in yaso in bada kudin dori".




 Faima sai da tayi dan kara domin zafin da taji na murda kunnan gashi har yanzu taki sakinta. Asiya tace. "Bazaki bar yiwa mutane ihu ba sai kin tada mana yara. Maza ki iske ni a kitchen kinji ko?". Gyda kai fatima tayi tace "naji gani nan zuwa mama". Mari ta wanka mata. "Wacece mamarki din?, Allah ya suttura in haifi yarinya kamarki".  Ta nuna wasu yan mata dake gefe a gado suna ta sharar barci tace "kinga yarana can ba kamarki ba". Mtseww Ta ja tsaki ta fice.





Nan ta bar fatima tana kuka. Ta zubda hawaye sosai tukun ta tashi taje da sauri ta shiga bedroom tayi brush tukun ta canza kaya ta fito. Dugi-dugi ta nufi kitchen. Fatima tasha wuya sosai a kitchen din dake gaba daya ake haduwa ayi girki a gidan. ba mai tausaya mata a cikin matan baban nata duk su ukun miko wancan kulkula wannan wanke can gyara can. Ba mai tausaya mata ko ganin kankantarta a cikin matan.  Bayan an kamala ita suka dinga dorawa kulolin abincin tana kaiwa dinner.  Saida aka kamala komai tukun suka korata daki kuma suka ce in ta shiga ta kwanta kmr mai barci kar ta yarda alhj ya gane cewa ta tashi balle ma ya gano tayi aiki. Haka ta tafi tayi yanda sukace ta hau gadanta tayi shiru. Tana ajiyar zuciya. Su kuwa kowacce. Sai ta shigo dakin ta tada ya-nata-ya-nata duk suka yi wanka sukayi brush tukun aka nufi dinner. A nan kwance suka bar fatima. Tana jinsu duk abunda suke.

...................................................


Mujee zuwa.




Autan writers nee  king boy













👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 15-16



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽





😘 Abunda yake raina zana fitar na huce takaici, suyaya ku a raina zana fada bazan boye ba.........



💃🏻 ALAMAR TAMBAYA TANA GA MAI YAWAITA TUNANI, MUSAM DA NASHI CIKIN SOYAYYAR READERS NA. NA KWANA CIKIN TA NA RASA WANDA ZAI FIDDANI SAI KU MASOYA NA WANDA KUKE DA KYAU NA KAMANNI,   NA RIKE KAUNAR KU A RAINA TA ZAUNA.. NAYI SHIRINA ZAN BAKU DUKA PAGEN GA😜😜😜😜😝


♥ BANI DA BAKIN GODE MUKU MASOYAN ALJANAR FATIMA, TUN  YANZU KAFIN AJE KO'INA MASSAGES DINKU SUN FARA RUTATOWA CIKIN WAYA TA.  INA GANIN SAKONNIN KU INA JIN DADI SOSAI, ALLAH YA BARMU TARE. DA MASU KIRANA INA GODIYA, KUNA A HEART NA MUSAMMAN .♥


'YAN PHARIDAH KHAMSHI NOVELS


SAMEE KHAIRAH NOVELS


BIGBOY ISA NOVELS


BIGBOY ISAH FANS


ZAMANIWRITERSASSOCIATION

DA MA SAURAN SU....


BAN MANTA DA KUBA 'YAN WHATSAPP GROUPS INA GANIN SAKONNIN KU INA GODIYA.  ANA TARE, ANA TAREN TARE, ANA MUGUN TARE.LOLZ





FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----



               *KARSHEN PAGEN BAYA*


~Su kuwa kowacce. Sai ta shigo dakin ta tada ya-nata-ya-nata duk suka yi wanka sukayi brush tukun aka nufi dinner. A nan kwance suka bar fatima. Tana jinsu duk abunda suke.~


```»»Wajen cin abincin bangare-bangare ne wajen yara mata daban haka maza ma daban. Bangaren uwaye kuma sunsa abincin gaba an zubawa kowa nasa saidai ba damar ci. Sai alhj ya fito. Asiya tayi tsaki tace, "wai ace abincin ma sai an sawa mutane doka a kai, ji dallah yanda ya bar mutane najin yunwa yaje yayi zamansa...". Shiru tayi sakamakon jin yara sun 

Fara hayaniya alamun shigowar alhj kenan. Idan ya shigo duk rashin jin yaro sai ya natsu domin bashi da wasa. Bayan yaje ya zauna. Uwayan wato matansa. Suka fara gaishe sa tukun suma yaran maza da mata masu dan wayo suka biyo layi daya bayan daya suna gaida shi. Yayi mamaki da baiga fatima ba a cikin yan zuwa gaishe shi din ba. Da zai tambaya kuma sai ya kyale. 




Shi ya fara yin bismillah ya fara kai abincin baki tukun kowa ya fara ci. Dokar cin abincin kenan sai ya fara cin indai yana gida tukun kow zaice. Fatima kuwa tana daki ga gajiya ga yunwa kuma sun sata barcin dole. Saidai kwata-kwata barcin yaki zuwa domin yunwar dake kwakwalar ta. Tana jin kwaram niyarsu ana cin abinci kamar ta fito sai dai kuma tana tsoran tayi laifi. Domin tasan in ta saba musu to yau ta shiga uku ko abincin rana baza su bata ba. Haka suke mata idan tayi musu wani laifin. Su sakata aiki mai tsanani kuma su sata azumin dole horo da yunwa. Haka dai ta hakura ta kwanta tana kuka.




 Bayan an gama cin  abinci kowa ya kama gabansa dake yau weekend ba makarantar sai islamiya. Alhj ya koma dakinsa amma sai ya kasa natsuwa da ya tino baiga fatima ba. Hakan yasa ya fito ya tambayi matan "wai ina fatima ni ban ganta ba". Asiya tayi farat! Tace "uhmm alhj kai da kasan halin yarinyar nan da shegiyar lalata. Tana can dakin yara tana barci nayi-nayi in tashe ta tayi sallama amma taki tashi".  Ta fadi hakan ne domin ta jawa fatima duka. 





cikin fada yace "asiya wace irin banzar magana ne kika fada min kina nufin fatima bata tashi ba har yanzu. me yasa kika zama muguwa maciya amana iyee! asiya. yarinyar nan fa marainiya ce amanarta na baki. amma yanxu dan allah ace duk kin tashi yaranki sunyi wanka har sun karya amma ita dake ba yarki bace shine zaki barta har wannan lokacin bata karya ba. yanzu karfe 9:30 fa".   Ta wani marairaice "haba alhj in kuwa kace haka baka min adalci ba.  yanzu duk irin tatalin da nake wa wannan yarinyar kana so kace baka gani alhj. Ni ai a ganina rashin tashin ta din ma da nayi duk a cikin gata ne. Na barta ne ta hutawa rant....".



Tsawa ya daka mata. "Ke dallah rufe min baki bana san wannan zakin bakin naki. Maza wuce ki kira wo min ita". Murguda baki tayi ta tashi tana gunguni. Wai irin wannan ai sai yaja a rainata a gaban kishiyoyinta ake mata wannan abun "Dama jiya ka targada ni dan mugunta". Alhj yace "me kikace". Juyowa tayi. "Aa ni banyi magana ba". Ta wani gallo mishi harara. Ta nufi dakin yara. Fatima najin turo kofarta tayi maza ta rufe idanunta kamar mai barci. 








Asiya kuwa tazo ta kama tikarta "fati!-fati!, Tashe munafuka kinzo kin kwanta wato sai barci kike.maza jeki kiyi brush ki zo wannan masifafan mutumin na kiranki". Fati bata ce komai ba ta sauko taje tayi brush ta dawo. Tazo gaban asiya tace nayi. Rigarta ta gyara mata ta kuma dan go goge mata fuska kamar da gaske. Tace "idan kika yarda kika ce kinyi aiki kuma kika gayawa alhj ni nace ki dawo daki ki kwanta to ni dake ne a gidan nan kinsan dai halina sarai".



Fatima tace "bazance ba aunty". Dankwashinta tayi a kai. "Kinci uwaki. Nice aunty wato bama mama ba ko. Wuce muje". Fatima ta shiga gaba asiya na binta baya.  Alhj kallo daya yayi wa fatima ya gane tana jin yunwa. Bata karya ba. "Momyna". sunanda yake kiranta da shi kenan. Kinci abinci kuwa. Girgiza kai tayi tace aa ynz na tashi a barci. Barci kuma?, wato bakiyi sallah ba ko?. Bana ce ki dinga kula da sallah ba ki bar wasa da ita". "Dady nayi fa tun da wari nayi sallah sannan na koma barcin".  "That good haka nake san ji momyna".  




Juyawa yayi ga matan nasa wanda duk sun Zuro musu ido ba abunda suke sai hararen fatima. A cikin zuciyqrsu kuma tsanarta na kara fadada. "Wace tayi abinci?, Ina abincinta?". Ya tambaya Zuwaira tace, "alhj wane abinci kuma ai gidan nan ba wani sauran abinci duk an cinye tana can tana barci". Alhj yace "Yanzu Dan tsabar mugun hali yarinyar bata ci abinci ba shine kukaki ajiye mata. Ko dan kunsan ba 'ya'yanku bane. Wato ita Marainiya batada uwa ko".  Bai tsaya jin abunda zasuce ba yaja hannun fatima yace "zo muje in saya miki abinci mamana". Yaja hannunta suka fita. 




Nan ya bar mata sai surutai suke yi. Har asiya na cewa "wai anya kuwa uwar yarinyar can ba asiri tayiwa alhj ba kuma har yanzu bayan ta mutu yake tasiri a kan yarta ba.nifa abun ya fara bani tsoro".  Zuwaira tace "haba aunty barta mana ai gasuwa zatayi a gidan nan domin ko yar aiki sai tafita jin dadi wllh. Yarinya karama sai kini bibin tsiya". Hauwa tace, ai wallah ni kadai nasan muguntar da na shiryawa yarinyar nan, zaku gani da idanku".  Yar guda sukayil a tare suka hada hannu. 




Mota suka hau alhj yaja saida suka je wata rumfar mai shayi tukun ya faka ya fito yajawo hannunta suka shiga suka zauna yasa a soyo mata indomei da kwai da kuma zallar wainar kwan da kofin shayi biyu. Kudi ya kashe musu dai sosai a gurin. Fatima saida taji cikinta ya cika nat! Domin kuwa rabanta da ta sama isashen abinci tun waccan juma'ar da taje gidan su wata kawarta ta wasa. Mota suka hau suka nufo gida tafiya ake fatima sai waige-waige take yi ta kalli can ta kalli can. Tana kallan shaguna. "Dady tsaya-dady-tsaya". Bai shirya ba ya take birki. Ya fara tambayarta "miye kika tsaida mu mamana?".   "Dady danyi baya, Yi baya dady". Baiyi gardama ba yayi baya da motar. Saida suka zo saitin wani shago tace ya tsaya. Da gudu ta sauko taje tana kokarin dauko wata yar baby. Wacce suke a jere duk na sayarwa ne.



Mai shagon ne ya fito yana neman dukanta alhj ya dakatarda shi. Yace "mamana miye haka kika zo zaki daukar musu abu na sayarwa ne fa ko baki sani ba?". "Na sani dady wannan nake so ka saya min ina santa sosai kaga munyi kama da ita kuma ma dady kaga wannan tafi ta nuratu kyau da girma".  Dan Murmushi yayi kadan yace "ke kuwa me zakiyi da wannan katuwar diyar robber ai tayi girma duba karama mn. Wannan tafa kusan kaiki tsayi".  "Aa baba ni wannan nake so".  Alhj ya kalli mai shagon ya tambayi kudin diyar robar. Mai shago yace "dubu bakwai".  Alhj yace ina zuwa. Mota ya koma ya dauko kudi  "kash! Ashe na baro kudin a gida".  Saura dubu uku ne a hannunsa. Ya dawo cikin yanayin damuwa gashi mutumin baisan shi ba. Balle yace in ya fito zai kawo mishi. Ita kuwa fatima rike take da yar tsanar ta fara wasa da ita. 




Ya dawo yace "malam na manta kudina ne a gida kaga saura dubu uku canjina kayi hakuri ka rike wannan ka bamu yar robar in yaso idan na fito zan kawo maka". Mai shagon yace "ai ina ban sanka ba bazan taba yarda ba. Kaga kawai in bazaka saya bane to". 




Alhj ya kalli yar tasa yace fatima "kinga yanzu bani da canji zo muje gida in dauko kudi sai mu dawo in saya miki".  Fatima ta saka kuka ta kankame yar tsanar gam a kirjinta, wai ai ita baza'a rabata da yar babyn ta ba. Alhj yayi-yayi da ita ta bari ya dawo amma taki. Ba yanda ya iya dole wayarsa ya bawa mai shagon ya rike ya basu yar babyn kafin ya dauko mishi kudin. Haka kuwa akayi. Mai shago ya karba yaje shago ya ajiye tukun ya dauko musu wata yar karamar akwati. Ta kayan yar babyn ce. Suka karba fatima sai murna take ta dauki yar babyn wacce ta kusa tsayinta tasa a mota suka tafi gida    tunda suka taho a hanya yar babyn ta fara kwai-kwayan fatima. In tayi dariya itama sai yar tsanar tayi, haka in ta bata rai! Sai yar tsanar ma ta tsuke fuska. Fatima dady ta karaji nan tata mata abubuwa har gwallo in faty tayi yar tsanar sai ta rama     ............................................... . .........```





Mujee zuwa.



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION





Autan writers nee  king boy















👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 17-18



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽


😍💃🏻 NA BAKU WANNAN PAGEN NE SABODA NAGA... 


 *TSABAR TSANTSAR TSANANIN TSAGWARAN, TSAYUWA DA TSAIDA TSABAGEN TSAIDADE SO DA YA ZARCE NA TSINTSAYE SAMAN TSAMIYAR TSANGAYAR TSAUNI TSANANIN SO DA KAUNA DA KUKE NUNA WA LITTAFAI NA.*


😍 *INA JI DAKU SABODA HAKA MA NA RUBUTA SUNAN KU A FARFAJIYAR FARAR FAIFAR FATAR FARAR ZUCIYATA DAKE FAFADAR FADAR FADAMA MAI FANFUNAN DA KE FIDA FURUCIN FITARWA  MASU FUKAFUKAI DA FANKOKIN.....*   🙊


*SALMAH QUEEN*



*ZEANAV DAWISU*

 

_INA JI DAKU ALLAH YA BAR MIN KU KUNA SAHUN GABA CIKIN MASOYAN LITTAFAINA_



_SAM KALAMAN BAKINA SUNYI KADAN DA SU BAYYANA IRIN TSANTSAR FARIN CIKIN DA NAKE JI YAYIN DA NAGA SAKONIN MASOYANA SUN SHIGO WAYATA._


FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----



               *KARSHEN PAGEN BAYA*

~In tayi dariya itama sai yar tsanar tayi, haka in ta bata rai! Sai yar tsanar ma ta tsuke fuska. Fatima dady ta karaji nan tata mata abubuwa har gwallo in faty tayi yar tsanar sai ta rama~

```»»Tun a mota yar babyn ta fara magana. a cikin wata irin karamar murya. "Sunana safuratu ina tayaki murna da sayana da kikayi". Fatima ta juya domin ganin mai magana bataga kowa ba. tace "abba kaine kayi magana Yanzu?". yace "aa magana kikaji nayi". tace magana  naji ko yar babyna ce?. alhj murmushi yayi yace "'yar baby kuma ai ba irin mai magana bace bakiga batada speaker ba...?. Kafin ya rufe baki wata siririyar murya ta kara magana, "Zan dinga saki dariya, zan dinga baki labarai masu dadi, amma ni fa ba'a barina da yunwa, kuma ni kullum sai anyi min wanka an canza min kaya anyi min make-up....."  alhj tsurewa yayi domin yaji tabbas yar babyn ce ke magana a tsorace ya fige yar robar yana dudubata wai ko zaiga speaker a jikinta amma bai gani ba. ita kuwa fatima murna kawai take da jindadi yar babynta na magana. alhj yace "fatima 'yar babynki ce fa mai maganar nan to amma ni banga speaker a jikinta ba"

.  fatima ta karbe abunta tace "Baba ai itama da baki take yi kamar mu baka gani bane?". 





yace "eh ni ban gani ba, amma bari in na koma zan tambayi mai shagon inji ko tana magana. Domin ni ta bani tsoro fa mamana".  Haka dai yaci gaba da tuki cike da mamaki har suka karasa gida. fatima ta sauka da gudu tana murna ta nufi cikin gida rungume da yar babynta a parlo ta iske duk yan gidan yara nata rashin ji masu wasa nayi masu rigima ma hk. ai kuwa yan yaran na ganin yar babyn suka yo kan fatima wannan ya karba wannan ya figa wai ko wane yaro sai ya je gurin uwarsa ya kama kuka wai a kwace a bashi. can wasu yara marar ji guda biyu daya ya kama wajen kan yar babyn daya kuma ya kama kafafun sai jayaya suke wannan yana so ya karbe wannan ma yana so ya karbe fatima kuma sai kuka take zasu karya mata yar baby gashi  ba dama tayi mgn. 




lokacin alhj ya shigo. "kai! kai! ku wane irin mararsa jin magana ne. zaku balla mata abu bata kayanta maza". mika mata sukayi. ta karba ta nufi dakinta asiya ta harare ta tace a zuciyarta "munahika ai alhajin zai tafi zaki ci ubanki". alhj yace "yanzu ku kuna gani a gabanku zasu batawq yarinya abu a gabanku amma ko kuyi magana. haba asiya kece babba fa ko sauran basuyi magana ba ai ya kamata ke kiyi mawa yaran magana". "uhm ai ni kullun a wajenka marar adalci ce to amma yanzu kai ga adalci nan a fili ka nuna mana, tunda ga yara nan da yawa a gida kuma duk yayanka ne amma ace ka ware fatima ita kadai ka saya mata abu. wannan shine adalci ko?". Ran alhj ya bace har zaiyi mgn kuma sai ya fasa ya wuce up stairs. yaje dakinsa ya dauko kudi yq fito yayi tafiyarsa. 




su Zuwaira sukayi dariya sukace "aunty asiya kin min daidai ke kadai ce maganin alhj a gidan nan". asiya tace "hmm ku kyale sa ai yau saina toya yar babyn nan muga ta tsiya sai inga me zaiyi haba ya zai dinga fifita wacce kudabukar yarinyar a kan sauran yara bari inje gurinta". su Zuwaira binta kawai sukayi da kallo. ta tashi buzun-buzun ta ta nufi dakin yara. fatima zaune take a kan gadanta ta zaunar da yar babyn tana cin bisket itama tana tura mata a baki. tana ci ci diyata daga bakin. kawai sai taga bakin ya bude. bata wani firgita ba sai ma dadi da taji. ta tura mata bisket din tace "kin koshi.?  




lokacin asiya ta karaso gurin ta kama yar babyn da hannu daya ta wullata jikin bango ta fado tim!  ta kuma wanke fatima da mari "shegiya yarinya me kike a nan tun dazu ina can ina jiranki zan aike ki kin wani shigo daki kin zauna. dama nasan wannan yar babyn da kika samu ita zata dinga hanaki aiki amma bari ynz in dauke tq in yayankata  in toya muga ta tsiya". fatima ta fashe da kuka tana bawa asiya hakuri karta yanka mata ya' abun mamaki fatima na fara kukan suka jiyo kuka a baya. asiya ta juya baya. yar babyn ta gani a zaune tana kuka harda ruwan hawaye




Abunda yayi mutukar tsorata Asiya kenan, da gudu taje ta shige karkashin gado, fatima na ganin haka ta sauko tuni tama bar kukan ta fara dariya, mama asiya ta bata dariya.  Zuwa tayi ta dauka yar babyn tana lalashinta. "Yishiru-Yishiru diyata. Mama asiya ce ta taba min ke ko?"  Kunnuwan asiya sunji lokacin da yar babyn tace "Eh itace". Cikin wani karamin voice, "To yi shiri bazata sake ba".  Asiya a dan tsorace ta fito daga nesa tace "Au! Fatima dama yar tsanar taki tana magana?". "Eh mama asiya ai tun a mota ta fara magana, babama ya dauka bata magana". Asiya tace "to dan kawo ta mu gani".  Amsa tayi ta duduba amma bataga speaker ba. "Fatima ina speaker da wajen sa battery?".  Mama ai da  baki take magana kuma ba'a saka mata battery, yanzu nayi mata wankq bata bushe ba".  




Abuda ya fadowa asiya a rai shine. Hawayen da ta gani wato ruwan da fati tayi mata wanka ne. Ai kuwa ta maka diyar da kasa tasa katuwar kafarta ta taka tabi ta samanta ta wuce tana hararen Fatima hade da cewa. "Dauki yar iskar yar tsanar ki, ko dan wannan ai tama wuce yar tsana a girm saidai ace *ALJANAR FATIMA*.  Fatima bata tanka mataba da sauri taje ta  dauki yarta taci gaba da yin wasa da abunta. 



A falo ta iske su Zuwaira suna nan inda suke basu tashi ba. Asiya tana dan dangeshi ta karasa ta zauna ta saki wani gwabran nishi. Wanda yasa su Zuwaira saurin tambayar "Lafiya dai aunty babba, fatan kin yayanka shegiyar yar tsanar nan..."  Tarar nunfashinta tayi ta hanyar cewa, "Ina fa 'yar tsana da ta tsoratani. Ashe wai tana magana, ban sani ba ina shiga dakin na karbe ta na maka a bango juyawar da zanyi sai naganta tana kuka harda hawaye. Ai kafin kice me tuni na shige karkashin gado na dauka ai aljana ce, washh! Wllh har yanzu gabana faduwa yake".  Su hauwa najin haka suka kwashe da dariya hararar da ta daka musu ita tasa su hadiye dariyar dan dole. "Wai ina su asmart ne ko har yanzu basu dawo daga wajen kitsan ba". Asiya ta tambaya. "Eh wllh kinga har yanzu basu dawo ba, Ni jirama nake su nasan su zasu lalata wannan 'yar tsanar". Zuwaira ta bata amsa. "Ai kinji shiru gidan dake basa nan". 




Su Nasmat kuwa na can gidan kitso  gaba daya su hudun harda Fiddausi da ameera.  Dake mai kitsan tasan halinsu suna zuwa tace su zata fara yiwa su tafi abunsa.kafin  a gamawa asmart kitso saida nasmat ta Zubar da duk ruwan gidan, wai wanke kai take daga ta wanke sai ta shinshina tace wari yake. su Fiddausi dama basuyi magana ba dake sunsan halin ta idan ma sukayi mata magana baji zatayi ba. Da sauri mai kitsan ta burbura tayiwa asmart kitson Nasmat duk ta jike kan, Amma a haka mai kitsan tace tazo a mata dake ya dansha iska. Haka itama asmart tata barna kafin a gamawa nasmat saida tasa yara sunfi biyar kuka a ciki harda wanda ta fasawa kai. Jini na zuba yaran tafi ya gayawa uwarsa. Asmart tazo ta kama nasmat kitsan ma ba'a gama ba sauran layi biyu. Amma a haka suka gudu, basu zame ko'ina ba sai gidan aunty Sakina yayar mamar su ce. (Wato mama asiya.) 





,

Matar yar lukuta wacce itama jikinta ya kai na mama asiya. Nan ta tashi tana musu sannu da suwa. Bayan sun gaidata. Tace, "Asma'u uwayen rashin ji ziyara aka kawo min yanzu da yamman nan?".  Bayan sun kalli junane asmart tace "Eh mama asiya ce tace mu zo kuma ma a nan zamu kwana".   Sakina tace to madallah ai naji dadin zuwanku dama ga aiki nan kaca-kaca ya min yawa a gida sai ku dan kama man muyi sauri mu gama kan magariba". Cikin daga murya nasmat tace, "Kutumelesi kiji wannan matar wai mu tayata aiki". "Yaseen ni dai bazanyi ba saidai ke ki tayata". Cewar Asmart "Kutt kinga malama yayar mamar ku ce ba yayar mamana ba. Dan haka ko kwano daya bazan wanke mata ba". "Ke zaki tayata".  "A'a wallahi ke dai". Garda ma suka hauyi a tsakanin su ko wacce nacewa ita bazatayi aikin ba, abun har ya kaisu ga kunce, ki'kir-ki'kir suka kama wai su da gaske fada zasuyi.....,.............```



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy













👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 19-20



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




IN DEDICATION TO YOU  

*KHADIJA CANDY*  *_ALLAH YA BAR ZUMUNCI, YASA KIFI HAKA NA GODE DA ADDUO'IN DA KIKE MIN. KEMA KUMA ALLAH YA KARQ MIKIN DUMBIN BASIRA DA HIKIMA DA FASAHA, ALLAH YA KARE MANA KE DAGA SHARRIN MAHASSADA DA YAN ADAWA DA MAKIYA. ALLAH YA TSARE MANA KE DAGA SHARRIN DARE. SHARRIN RANA, FATAN KOFOFIN ALKHAIRAI SU BUDE A RAYUWAR KI DUK NA SHARRIN SU GARKAME.  AMIN YA ALLAH.*_





_SAM KALAMAN BAKINA SUNYI KADAN DA SU BAYYANA IRIN TSANTSAR FARIN CIKIN DA NAKE JI YAYIN DA NAGA SAKONIN MASOYANA SUN SHIGO WAYATA._


FOLLOWING US AS:

----

Like us page.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION

----

Check us blogger.

Zamaniwriters.blogspot.com

----

 Email us your comment and reports.

Zamaniwritersassociation@gmail.com

----

whatsapp's number 

08096831009

----



               *KARSHEN PAGEN BAYA*


~Dan haka ko kwano daya bazan wanke mata ba". "Ke zaki tayata".  "A'a wallahi ke dai". Garda ma suka hauyi a tsakanin su ko wacce nacewa ita bazatayi aikin ba, abun har ya kaisu ga kunce, ki'kir-ki'kir suka kama wai su da gaske fada zasuyi.~


```»»Aunty Sakina da ta saki baki tana kallansu ita kallansu take abun yaso ma ya bata dariya kuma sai ta basar. Ta cire takalmin ta ta fara kwada musu da sauri suka saki juna. "Kaji yan iskan yara daga zuwa zaku mayar min da gida kamar gidan dambe?, To wallahi bazan iya ba ku tatara ku koma na gode allah ya baku ladan ziyara". Suna jin ta fadi haka sai suka shiga bata hakuri Da rokonta a kan tayi hakuri ta barsu.



Bacin rai tanuna musu sosai ta murtuke fuska tace, wallahi kafin in futo daga dakin nan ku bar gidan nan in kuwa ba haka ba wallahi sai jikin ku ya gaya muku". Tana gama fadar haka ta shige dakin. Su kuwa kofar dakin sukaje duk su biyun sukayi Neldown kamar wasu mutanan kirki. 



Sanda tayi kamar mintuna biyar tukun ta fito daga dakin sun bata dariya a yanda ta sansu da rashin ji yau sune roko harda durkusawa. Nan dai tace musu ta hakura amma fa aiki ba'a janyewa'.  Da sauri sukace "Mun yarda".  



A can kuma gidan mai kitso uwar yaran da aka fasawa kai ce, tazo da wani danta saurayi dauke da wata gora. Da ganin  matar kasan jarababa ce, ko yanayin tafiyarta zai iya shedama ba da alkhairi take tafe ba.  "Wace yar kutu... Ce ta fasawa yarona kai, ku nuna min ita yanzu itama insa a rotsa mata nata kan". Matar ce ta shigo gidan da wannan furucin lokacin da dan nata kuma ya daga gorar yana shirin makawa duk wacce aka nunu. Da gudu Fiddausi da Ameera suka Ruga dakin mai kitso. Tana shirin binsu Mai kitsan ta shiga gaba ta tare kofar dakin tana "ki saurara basu bane ki saurare ni, kannansu ne basu ba". Tsayawa tayi tana jijiga.  "To ai anzo a dai-dai kenan yanzu in nasa aka fasawa daya daga cikin yayyen nasu kai, kinga ai anyi 1-1 ko". Aa dan allah ba haka za'ayi ba kinga nidai kitso suka zo min nan kuma sun tafi gida tun lokacin da sukayi wannan ta'asar. So abunda yafi shine ki bisu can gidan Alhaji salim din". 



"Kutumelesi dama yan gidan alhaji salim ne. Kai zo muje ba zama lafiya yau zasu san sun takali wutar dafa kansu".  Fuwww!! Ta wuce yaran na binta bayq da kulki a hannu. Tun daga get suka fara rikici da mai gadi, yaki barinta tq wuce, sanda ta shsmmace shi tukun ta ingiza shi ya fadi da sauri suka shiga.  "Asiya! Asiya! Asiya!". Da duk illahirin karfin sautinta take kwalla wannan uban kiran. Ta cire gelen dake makale a kafadarta ta daura a ku'gu. 




Da sauri su asiya da sauran yan gidan suka fito suna tambaya "lafiya-lafiay". Cikin masifa da tsiwa tace, "Ina fa lafiya ai tunda kuka ganni a haka kunsa ba lafiya ce ta  kawo ni ba. Wannan bala'eun 'yaran naku ne suka fasawa dana kai dan haka nazo ko dai a fiddosu insa a fasa musu kai. Ko kuwa kuga tashin hankali".  Nan ta fara jijiga tana cewa dan saurayin nan ya matso kusa ya shirya.  Asiya tace "Innalilahi yanzu su asmart bazasu barmu mu huta ba, Rikicin nasu ba iya gida ya tsaya ba kenan.  Kinga mariya zo muyi wata magana". 




Mariya tace itafa ba inda zata sai an fiddo da su asmart ta rama wa yaranta tukun ta tafi daga gidan nan domin har wani hauka-hauka take tana tsalle-tsalle lokacin da Asiyar kecewa suzo su sasanta. Da kyar asiya taja hannunta bayan dakunan su. Basu fi mintuna biyu ba suka fito suna washe hakora. Gaba dayan fishin da Mariya tayi ya zama tarihi ba abunda take sai godiya wa hajiya. Sauran matan sunyi mamaki abun ya daure musu kai. Mariya tayi musu sallama tacewa Dan saurayin "Kai zo mu tafi ai na yafe musu".  "Haba mama Najeef fa aka fasa wa kai shikenan munzo a rama kice wai kin yafe".  "Kai zanci ubanka fa wai bani nake maka magana ba?".  Yana dan gungunin sa ya bita suka fita.  Sunje fita mai gadi ya leko ta kofa hade da cewa "Jarababiya kawai allah ya isa turenin da kikayi". Da sauri ta juyo a fusce zatayo kansa "Me kake cewa". Habawa ai da gudu ya shige dakin ya rufo.



Bayan su Asiya sun koma cikin falo Zuwaira tace "wai aunty dukan matar nan kikayi ne ko kusa warning kikayi mata. Naga lokaci daya ta wani saukko".  Yar dariya asiyar tayi hade da cewa, "Hmm ba ko daya daga ciki kinsan fa in kikaga mutum na irin haka to in kika bincika harda talauci a ciki, Naira 500N na bata kawai nace taje ayi mishi magani, Shine fa kinji harda su godiya".   Dariya sukayi gabaki daya Hauwa'u tace "Gwara da kikayi haka wllh dan da alhaji ya zo ya tarar da ita. Bama su asmart ba mu kanmu bazamuji dadi ba".  "Ashe dai kina ganewa gashi yau a dakina yake kinsan yanda muke da shi dama. Ai shiyasa nayi saurin watsawa Wutar nan ruwa". 


************


Kwance take a daki ita kadai  tana barci. Wata mahaukaciyar dariya mai gigitarwa ce ta daki dodan kunnan ta. Bata shirya ba ta tashi zumbur! A tsorace, tana waige-waige "Alhaji! Alhaji! Dubawa tayi gefan wajen wayam ba alhaji. Hahahahahaha! Dariyar mace ta jiyo kamar a downstairs a dan tsorace ta tashi ta bude kyaure a hankula ta laleka bataga komai ba, hakan yasa ta idasa fitowa. Da fitowarta Kofar dakin ta taji an banko da karfi kamar za'a balla, dan kara tayi ta zabura kuma. Lokaci ta nema bude kofar amma sai taji kamar an Garkameta da kwado. Abunda yayi mutukar girgizata kenan. A saman dakuna ne guda hudu dakinta ne a can karshe sai na Zuwaira sai na Hindu wanda yanzu alhaji ya mayar nasa. Na karshen kuwa na Hauwa'u ne.   Dan lungun dakunan a haske yake fes da fararen Gululuka. Lokaci daya tada wutar ta fara farfari. Kwayayen suna wata irin girgiza dariyar Yarinya ne ya biyo baya dariyar marar dadin ji.  Ahhh!  Ahhh! Da karfe ta fara ihun itama. Ta durkushe a gurin ta sa hannaye ta rurufe kunnuwanta. Hade da runtse idanu. Dif! Taji komai ya tsaya an bar dariyar haka kwayayin sun daina girgiza da farfarin da suka. Mikewa tayi cikin kuka kuka ta fara tura kofa da karfi  tana fadin "na shiga uku ni Asiya me ya fito dani.  Gashi sai tsorata ni ake yi". 




Ta baya taji an tabata wata murya yara taji ance "Mama Aciya juyo cigan ni nayi kyau?".  A hankali ta fara juyowa dan ganin mai maganar a tsorace. Koda idanunta sukayi tozali da mai maganar Aljanine yazo mata asuffar Iliyasu babban Dan hauwa. Kanshi a rabe yake gida biyu  hayaki ne ke fita da wani turiri a ko wanne bare.  Aisiya na ganin haka jikinta ya fara bari ta hau kyarma.  Dariya taji ya farayi marar dadin saurare. Ya nufo gunta yana fadin "Nayi Ceau (kyau) kuwa mama aciya(Asiya)?".  ta kwada ihu! Ta zuba guje ta nufi Downstairs tsabar firgicewa Bata iya kirga iya matatakalan da take tsallakewa. Sabanin 'da, da in zata sauka da Daya-Daya take yi a hakan ma a hankali.




Tana saukowa tayi wata uwar tirjiya a falo nauyin jikinta da kadan ya rinjayeta ta fadi.  Ba wani abu yasa ta tsayawa ba. Sai ganin wata yarinya da ke zaune a Falon cikin wasu fararen kaya masu dauke ido. Yarinyar ta juya bayane bata iya gane ko wacce ce. Hakan yasa ta fara matsowa a hankula tana kiran sunayen yaran gidan wanda take tunanin ko daya daga ciki ne. "Dan ubanki fatima me kike yi ne a nan?. Cikin wannan dare?". Shiru bataji amsa ba hakan ya tabbatar mata da ba fatimar bace. A hankali take tafiya tana nufar wajen da yarinyar take. "Ba fatim bace?. Shimsiya ce? Sa'adatu ce?. Ko dai salma ce?".  Sunan jikokin ta take ta jerowa wanda take tunanin ko sune.  Lokacin ta karasa wajen mika hannu tayi tana karkarwa kamar ta taba kamar karta taba. Tana taba yarinyar tajuyi hade da wani mugun razananen kara da ya daki kunnan ta suman tsaye Asiya tayi a gurin..............,......```




TOFA MUJE ZUWA READERS.  YANZU ZAMUGA GWANAYEN TSORO. AN FARA KENAN



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy
















👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 21-22



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




IN DEDICATED TO ALL ZAMANI WRITERS. *ALLAH SARKI YAN UWANA UBAN GIJI ALLAH YA ALBARKACI RAYUWAR MU. A KULLUM GURINA INGA ZAMANI BA'A BARMU A BAYA BA. ALHMDULILAH KULLUM CIGABA MUKE. ALLAH YA KARA BASIRA, YAN UWANA DOMIN NI KAMAR YAYYAI NA NA DAUKE KU. AUTAN KU NE KING NA AUTAR KU QUEEN. ALLAH YA BARMU TARE YA KARA HADIN KAI. AMIN* ♥



.



               *KARSHEN PAGEN BAYA*

_Tana taba yarinyar tajuyi hade da wani mugun razananen kara da ya daki kunnan ta suman tsaye Asiya tayi a gurin._

»» Aljanar a sufar shamsiya take, jikar Mama asiya hannaye biyu tasa da karfi ta shake wuyan dogayen faracen hannunta masu shegen kaifi. Bakin shamsiya wani bakin abune mai kaure ya fara zuba. Kuma idan ya zubo din a kan mama asiya yake sauka.  Mama asiya in banda ihu  da neman ceto babu abunda take. Da dai taga ba ko alamun mutane a gida wanda zasu kawo akaji.




Nan ta fara ihu tana kokarin kankare hannun Aljanar da ta makure mata wuya. Aljanar ce ta bude idonu hade da dakawa Mama Asiya tsawa. Ai kuwa fitsari ya fara zubowa harda dan guntun kashi da ya zubo.  Fitsarin matseshi take amma zuba yake tsirrr! Duk jikin ta karkarwa yake. Magana na rawa "Haba shamsiya dan allah ki sake ni karki kashe ni me nayi miki ne?, nice fa mahaifiyar babanki".  Mama asiya ce ke fadar haka.   "Keeeee!  Anji ke kika haifi mahaifina to ke kika haife ni ne ni?, Shin a yanzu ni dake waye baba ma?". Muryar mai kamar amsa kuwa aljanar ke magana da shi domin in tana yi dakin har wani jijiga yake yi.  "Wallahi kece, kwarai kece baba. Kece uwata ma. Kece ubana, kece yayana, kece yaya ta kece.....".  "Keee yimin shiru".  Gum Mama asiya tayi ta tsaya da lissafin kafafunta sai rawar karkarwa take fitsari kuwa duk sanda aljanar tayi mata tsawa sai ya subuce ya kwararo.   "Hahahhahahjahahhaha!




Aljanar ce ta dake kai sama tana wannan muguwar dariyar. Mama asiya ta dan shammace ta ta ware iya karfin da hannuwa biyu ta tura ta. Can aljanar ta fadi gefe. Tubur-tubur abu ga mai jiki ba gudun kirki, ta nufi hanyar Hawa sama, gaba daya wutar dakin ce ta dauke duf!  Mama asiya bata daina gudu ba saida ta hadu da bango kanta ta buda ji kake gum!! Ta kuma zube kasa kamar an yarda buhun gero thom!  Kanta ta dafe tana wash! Wash!  Aljanar ta gani tazo dai-dai saitin kanta da wata wuka wulshe-shiya a hannunta.  "Hahaha- wato ni zaki tserewa ko?. Wukuncin ki kisa ne". Da fadar haka ta daga takobin sama ta caka ma mama asiya a ciki.





Wani Mugun kara ta Saki ta tashi zaune tana nishi daya-daya tana laluba cikin ta jin ko da gaske ne abunda ya faru.  Karar da tayi ya tashi alhaji zumbur! Ya fara tambaya "lafiya-lafiya"? Sai yanzu mama asiya ta fahimci cewa mafarki ne take ganin cikinta lafiya lau kuma haka kanta bata jin wani radadi. Alhaji ni kam wallahi bazan yarda ba ashe yarinyar nan mayya ce da wuka fa tazo zata kashe ni a mafarki, wallahi sai na dauki mataki a kanta, to ni kuwa me na tsare mata ne take nema ta cinye kurwata danya".  Duk surutun da take alhaji binta yake da tambaya. "Wacece?, wai wace yarinyar".  Budar bakin ta tace "Wace yarinya kuwa in ba wannan mayar...". Ta dan dakata tana tunani in fa tace shamsiya abun bazaiyi tsari ba.    "Wace"?.   "Wannan mayar 'yar taka ce Fatima, duk taimaka mata da nake a rayuwa wai ashe mayya ce ni tazo zata kashe".  Tsawa ya daka mata nan da nan ya murtuke fuska, "Asiya bana san iskanci fa, bana san tambadar nan taki, kinje can kin tabo aljanunki sun motso shine zaki likawa marainiya wato. To wallahi kar in sake ji".   Gungune kawai tayi, Alhaji kuwa ya kwanta ya juya baya abunsa.  Mama asiya na zaune kamar ance ta kalli wajen mirror. Ihu! Ta kwalla ta rukun-kume alhaji kamar wacce zata shige jikinsa.  Yarinyar ta gani a cikin mirror tana kiranta.  Alhaji yana jinta ya kyale ta, can kuma saj yaji lema a jikinsa wanda yasan wannan ya wuce na gumi. 




Tashi yayi yana "Asiya wai miye a jikinki nake ji sharaf!". Har tashin da yayi a rike take gam da shi idanunta a rufe. Wata mahaukaciyar dariya alhaji ya kwashe da ita, Irin wacce ya jima baiyi ba harda kama ciki. Asiya ido a rufe taki budewa tunani take in ta bude zata sake ganin aljanar, Jin dariyar alhajin taki ci taki karewa, yasata bude ido a hankali bata ko kalli wajen mirror ba. "Alhaji ai dole kamin dariya wannan mayar 'yar taka so take sai ta kashe ni ta huta".   "Asiya kalli jikinki fitsari ne fa kika sharara duk kin bata gadon, Hahaha wai duk tsoran ne haka harda fitsarin wando?". 





Sai lokacin Asiya ta lura da jikinta sharkaf take ta jika kayan barci  da fitsari.  A kunyace ta tashi da sauri ta nufi bandakin da ke cikin dakin domin tayi wanka.  Bayan ta shiga ta juya baya tana kokarin Cire riga sai ji tayi wata kalar muryar 'Yan yara tace "Yauwa Shannunki da Juwa".   Da gudu ta fito daga bayan dakin taje ta fada kan alhaji ta shishige mishi. Alhaji na niyar tashi yaje ya canza kaya domin ta jika shi amma sam ta hana  ta rufe idanu ko budewa batayi.  A haka suka kwanta har safe. Tun da safe taje dakin su fatima ta iske ta ta idar da sallah tana barci, nan fa ta hau tikar ta wai tashin ta take a barci, kai da ka gani kasan mugunta ne abun................


Ku danyi hakuri da wannan  yaseen yau bana jin type din.


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy











👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 23-24



NA.  👑 KING BOY ISAH 👑




👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



*DEDICATED TO YOU*


QUEEN HAUCY 😘 = *ILLAR BASHI*


BEAUTY QUEEN 😘 = *BADDEEYERH*


UMMU AFNANN = *FATIMAH*


ZUWAIRA MADADA 🍼 = *MATA DA MIJI*


MARYAM 'YAR MAMA = *RAINAN KAUYE*



BEIBOH = *YASMEEN* 



😍 _DA KYAU JARUMAI NA ALLAH YA KARA BASIRA_



           *KARSHEN PAGEN BAYA*

~nan fa ta hau tikar ta wai tashin ta take a barci, kai da ka gani kasan mugunta ne abun.~

Fatima tace tayi sallah amma mama asiya bata barta ba saida tasakata kuka, "Shegiya mayya wato shine jiya kika zo zaki cinye ni ko. Harda wani canza suffofi ko kin dauka bazan gano kece ba". Faddausi ce ta farka jin kukan Fatima, "Mama asiya wallahi tayi sallah ita ta tayar dani ma".  Mama asiya tace to uwar iyayi ni ai ba bugwan  sallah nake mata ba, wannan yarinyar da kike gani mayyace ban taba sani ba sai jiya nima. A mafarki tazo min tana faman cinye ni, badan Allah yasa kurwata jaruma bace".  Fiddausi dai jinta kawai take yi tana mata kallan muguwa azzaluma domin tasan duk maganganun Mama asiya ba gaskiya a ciki.  Mama asiya ce ta dankwashi kan Fatima hade da cewa "Yi mana shiru munahika mayya kawai, ai yau sai kinci ubanki a gidan nan bara alhaji ya fita. Kuma yanzu ma ki biyo ni kitchen kina jina?".  "Eh gani nan zuwa'. Buzu-buzu mama asiya ta  juya ta fita bata jima ba Fatima ta bita baya,  Fiddausi tabi bayan Fatima da kallo tace, "Kaico 'yar yarinyar da baki wuce a goya ba amma tun yanzu kin fara shiga kitchen, Allah dai ya kawo miki mafita".   "Ameen". Fiddausi taji ance maganar ta fito daga saitin dan karamin gadan fatima ne, ganin ba kowa a gun  tsoro ya kamata da sauri taja blanket ta rufe tayi luff!. Kamar kullum yau ma fatima tasha wuya a kitchen bayan irin Aikace-aikacen da tayi ga kuma Mama asiya daga anjima sai ta rankwashi kanta tace "Mayya kawai allah yasa dai karki cinye mana 'ya'ya dan wallahi yarona daya in ya kamu da koda ciwan kaine ke zan bincika".




Dake Mama asiya tabawa sauran kishiyoyin nata labari suma sai suka hau tsangwamar Fatima da dukanta hade da bata aiki mai wahala, Wai suma kashedi suke mata karta kama musu nasu yaran. Ita dai Fatima ba abunda take sai kuka sai in sunyi maganar karta kama musu yara tace "Toh" al halin ita bata ma san miye wata maita ba. Sanda fatima tasha wuya sosai ta kuma yi kuka ba adadi kafin  a gama hada breakfast din. Bayan sun sako ta taje ta rungume 'yar tsanarta tana kuka. "baby na kiyi hakuri na barki ke kadai. Wadan can mugayen ne suka ta zalunta na".  Yar baby ce ta kama kuka nan Fatima tasa ta a kafada tana jijiga ta tana bata hakuri.  "Momy bayi inje in yama miki". Wata siririyar murya ce ta fito daga 'yar tsanar. Fatima bata ji tsoran komai ba. "A'a baby na kinga su manya ne ki kyale su. Allah zai saka mana, naji malamin islamiyar mu yace, duk wanda aka zalunta allah zai saka masa".  Yar babyn ce tace "To na fasa zuwa".    Yauwa yarinyata muje in miki brush da wanka tukun  inzo in miki kwaliya mai kyau".  Tana gama fadin haka ta warci 'Yar babyn da hannu daya ta je ban daki. (Wai aka ce 'Kuruci dangin hauka)  bayan fatima ta ajiye ta tace. "Haaa, bakinki", nan take bakin 'yar robber ya bude. Hakora ne reras! A jere fatima dake yarinya ce ba ruwanta batayi tunanin wani abuba. Ta sa brush ta fara gurzar bakin.  Tana farawa bakin ya fara jini. Fatima na ganin jini ta daka da gurzar bakin ta zuba ruwa ta wanke mata tukun tace, "Gaskiya mai shagon da muka sayo ki baya da mutun  ci kuma kazami ne duba fa yanda ya bar miki hakori suka lalace baya miki brush".  Aljanar ce tace "Ko sau daya bai taba min ba".  Nan dai fatima taci gaba da mata wanka suna hira.   






Kyauran ban dakin aka turo da karfi, Ameera ce ta shigo. "wai ke Fatima dan ubanki bana hanaki magana a bandaki ba?. Ko baki  san ba kyau ba?".   "Yi hakuri aunty wanka nakewa Baby na".  "Kutumelesi kaji 'yar banzar yarinya wato barnar ruwa zaki tarkarwa mutane ko, To daga yau sai yau kar in kara ganin kinwa wannan 'yar tsanar wanka kuma ma kawo ta nan, yanzun nan zan kona shegiya kowa ma ya huta, Kawo ta nace magana fa nake miki".  Fatima kuka ta kamayi tana boye 'Yar babyn a bayanta tana fadin "Dan allah aunty ki bar min abuna ina santa wallahi". Tsawa ameera ta daka mata wacce tasa saida ta firgita  matsowa tayi kamar zata mika mata kuma sai ta sulale da gudu ta ruga waje ai kuwa amira ta bita suka hau tsere. Ameera ta kusan kamata kenan. Fatima tayi wata zilliya ta Bi ta karkashin ameerar ta wuce, sai ji kake ameera Tum! Ameera tasha kasa. (SHI YASA BA'A SO BABBA YABI YARO, BA KYAU DAN IN BA'A CI SA'A BA SAI KA FADI. AKWAI WANI UBA DA YABI DANSA DA GUDU. A LAYI CIKIN JAMA'A YARAN YA KADA SA. YARO DA KAZA DUK KUSAN DAYA NE. WAYO AKE MASA AYI CHARAF A KAMA. IN MA KABI DA GUDU TO KARKA YI GUDU MAI NISa.) Fatima Direct dakin abbanta taje tana kuka yana ganinta ya bar abunda yake ya kamo hannunta. "Mamana zo nan waya taba min ke tun da sanyin safiyar nan?

 Cikin kuka Fatima tace "Dady wai aunty ameera ce zata toya min Babyna wai kuma tace kar in kara mata wanka, yanzu ma da gudu ta biyo ni". Ran alhaji ne ya bace. Ya kama hannun Fatima yace muje gunta. A falo suka isketa tana wash-wash.




 Alhaji  bai bi ta kan wash! Din da take ba ya bal-bale ta da fada hade da mata kashe karta kara shiga sabgar Fatima. Su Asmart ba rabuwar arziki sukayi da Mama sakina ba. Bayan tusar da suka ta banka mata da dare a daki kamar bodarai. Da asuba asmart ta tashi wai tea zata hada. Madarar da suka zuba su biyu ta wuce ka'ida domin saida shayin yayi kauri kamar wani koko.  Sakina na ganin haka basu gama sha ba ma ta kora su gida.  Da wuri suka je gidan lokacin ba'a kai ga cin abinci ba.  Tare da su aka ci sunci Sa'a ba wanda ya gayawa alhaji basu kwana a gida ba.  Bayan anci abinci an watse alhaji yayi musu salama ya tafi office.  Nan fa mama asiya ta kira Fatima suka mata dan banzan duka ita da sauran matan wai kashe ne karta cinye musu yara Mama asiya kuma na cewa karta sake biyota mafarki. Waje suka korata can Fatima ta koma bayan dakuna ta zaunar da  'Yar tsanar ta facing dinta tana kuka.  Yar babyn itama kukan ta fara.  Abun ya bawa Fatima dariya itama kuma sai babyn tabar kuka ta fara dariya.  Nan dai sukata wasanni. 





Su Nasmat da asmart makaranta suka taho basu ma ko tsaya jiran su Fiddausi ba da sauran yara kamar da gaske suka yo sakko, alhalin kowa yasan ba karatun ba suke. A hanya Nasmat ke cewa asmart

"Ni fa wallahi yau mugunta nake ji, Dan haka yau kan mai Tsautsayi".  Dariya Asmart tayi      tace 'yar iskar karya kawai".  Nasmat ta bata rai, "Ke ce dai 'yar iskar karya. Amma ni yau muguntar ce kawai a kai na".      "Yauwa yanzu zamu kure mai cika baki". Inji asmart "Ga wani makaho can yana faman tsallaka rami jeki tunkuda shi in da gaske muguntar kike ji".   Jakar kur'anin ta tabawa asmart Riko ta nufi dan tshon da aniyar tunkuda shi rami...............




Ni kuwa nace Allah yasa aljani ne 😄😃😃


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 25-26



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



_*IN DEDICATED TO 'YAN BOKO HARAM WA SOYAYYA TA.*_ 


*SHUGABAR TADA BOMB* 💣 FATIMA. (DAUGHTER) 



*MAI BADA UMARNIN KAI HARIN* 💣 Hadiza hadi (Niger) 😡


*'YAR KUNAR BAK'IN WAKE* 👧🏿💣

Zuwaira (madara) 😡😔


_Kunci nasara kai harin da kukayi  babban birni  zuciya ta, inda kuka  kashe mutum uku Biyu kuma na nan suna zubar da jini. Shi yasa ma gaba dayan yau banda sukuni. Kuma yaseen wuta Bal-Bal_ 😡 


💦 QUEEN HAUSY💦


I love you too much.

You kill me with you love 😘




  *KARSHEN PAGEN BAYA*

_Jakar kur'anin ta tabawa asmart Riko ta nufi dan tshon da aniyar tunkuda shi rami._



»»Irin tsofafin almajiran nan ne, yana yunkurin tsallaka wani rami ya kasa. Nasmat na zuwa kamar wacce zata taimaka mishi dan har magana sai da tayi mishi. Sai da ta duba ko ina taga ba mai kallan ta kawai ta ingiza shi cikin ramin,  suka ruga a guje ita da asmart suna waigen sa suna mishi dariya. "Wannan wane irin yara ne da mugun hali haka, yanzu ina fama da kai na ki zo ki hankada ni rami salon in Karashe naka shewa ko, Jeki Allah ya isa. Allah zai hada ki da gaman ki kema".   Basu ce mishi komai ba gaba suka kara suna ta jan fada har suka isa makaranta. Malamin na ganin su ya murtuke ya bata fuska, "Kai ku zo nan dan ubanku, yau sai kun gaya min ubanwa ya daure muku gindi, yanzu karfe Goma zaku shigo aji".  Gaba dayan su gunguni sukayi, kamar ba su ya kira ba suka nufi bench suka zazauna. Kowa ta fiddo al'qura'ani kamar da gaske karatun zasuyi. "Kai wai ba da ku nake magana ba?".  Nan ma basu tanka mishi ba. Abunda ya fusata malam Dalhat kenan,  Ya nufo su da zureriyar dorina.  Shaf! Shaf!  Kake jin karar dorinar da karfi yake dukan su. Bayan yayi wa ko wacce daga cikin su dorina biyu, A ta ukun Nasmat ta Rike bulalar tare da mike wa tsaye.  "Malam ya ishe ka haka". Asmart ta fada ido cike da kwalla.




 Cikin kuka-kuka Nasmat tace, "Ki kyale sa yaci gaba Wallahi ya sake dukana sai na mishi abunda bai yi zato ba". Mamaki ne karara ya bayyana a fuskar malam ya saki baki yana kallan su, a zuciya yace, 'Ashe rashin kunyar nan ta su da ake fada har ya kai haka, Ni kuwa zanyi maganin ku".  Bulalar ya fizge da karfi ya fara zafga musu kan uwa da wa bi, da gudu suka fita har suna bankade muta ne. Ko laidar Al'quranin ba wanda ya dauko a cikin su.  Ko wacce hawaye ne shabe-Shabe a fuskarta Asmart na cewa, "Wallahi bazan yarda ba dole sai na dauki mata ki, chabb! Lalai wannan malamin bai sani ba ne".  Nasmat ta ciji labe. "Hmm kyale sa wasa yake damu".  Cikin gari suka shiga yawo gida jen kawayen su, sai da suka Dai-Dai ci lokacin tashi a Islamiyya yayi tukun suka koma gida.





Shigar su gidan suka tarar gaba ki daya mutanan gidan sun fito ana faman shiga motoci, da sauri suka karasa suka tamabaya ina za'a je, Mama asiya tace, "'yan gantali har kun gama iskancin kun dawo ko?, nasan dai ba makaranta kuka je ba, kunga Wallahi ku kiyayi rayuwa gwara ku tsaya ku mayar da hankali kuyi karatu, Ni kai na yanzu haushi nake ji da bansan komai ba a karatun Alqur'ani  kuma kuma nasan ko Fatiha cikin ku da kyar in da wacce zata iya kai wa dai-dai".   Kallan juna sukayi hade da sosai kai Asmart tace, "Mama asiya ina zuwa?".   "Au! Har kun manta yau bikin Haleematu?".  Wani irin tsalle Asmart tayi "Ashe yau ne".  Kokarin shiga mota ta farayi aka hanata, Akace sai taje ta canza kaya. Da gudu taje ta canzo Ko kwalliya batayi ba tazo ta shiga mota. Nasmat kuwa tana guri   A tsaye ta wani bata Rai. "Ke bazaki je bane? Kowa na gidan zashi ko har yanzu 'yar banzar gabar nan ta rashin hankali kuna yinta ke da Haleema?".  Zuwaira ce tayi wa Nasmat magana. "Allah ya sawa ke inje gurin  bikin haleema, Ai ko mafarki nayi naje wajen sai na farka kuma in na farka sai nayi sadaka".     Juwaira bata ce mata komai ba t shiga mota. Motoci biyu ne cike. Har sun fara tafiya. Asmart ta leko. "Yauwa nasmat ban gaya miki ba. Wannan tsinaniyar yarinyar tana can tana mana wasa da kayan Makeup wai tana wa 'yar tsanarta kwalliya. Kije kici ubanta dan Allah".   Tun asmart bata karasa maganar ba Nasmat ta zungura da gudu ciki  gidan.





 Direct dakin su ta nufa, tana zuwa ta shako wuyan Fatima ta baya ta fara gallah mata mari. Fatima kuwa ta hau kuka da ihu!, "Wato ke dan ubanki 'yar baby kike wa kwalliya da kayan mu ko".   Fatimar hakuri take bata amma taki ji sanda ta mata lilis! Kamar yanda ta fada yau 'yan  muguntar ne a kanta.  Kunnan Fatima ta kama tana ja. Ba arziki Fatima ta ringa binta tana rike kunnen dan karta ji mata ciwo.  Sai da ta kai ta har kofar gida, mai gadi  duk da yana tsoran alhaji sai da ya bude kofa domin yasan Bala'in Nasmat Da Asmart. "Dan ubanki bazaki zauna a gidan ba, kuma Wallahi in kika tafi wani waje na fito waje naga bakya nanto kema kin dan sauran".  Nasmat ta juya zata shige gidan Fatima ta riko kafarta "Aunty dan Allah ki bani baby na to".  Hararen ta tayi ta kuma sa kafa ta haure ta can Fatima ta fadi tana kuka.  "Bara inje in yan-yanka babyn dan ubanta itama ke da ganinta sai a lahira in 'yar Tsana na zuwa".    Wani kukan Fatima ta ci gaba da bada wa amma Nasmat bata saurare ta ba ta shige cikin gida ta bar Fatima nan tana kuka.





Mai gadin ganin yau gidan ba kowa kuma yana da 'yan uzuririka shima. Fitowa yayi har zai wuce kuma sai ya tuna Fatima na kofa karta shiga, Katan kwado ya koma ya daukko ya zo ya garkame gidan. Yayi tafiyarsa.   Nasmat a fusace ta shiga ta daukko 'yar babyn ta nufi kitchen da ita. Wuka ta dauka mai shegen kaifi ta fara dada rawa a jikin Robar amma ko kayan dake jikin babyn sunki ko bancile.  Canza wukar taje tayi a cewar ta ba kaifi ne.  Fara da dara wukar ta ke da wuya aka fara knock din kofar kitchen din da karfi abun  kamar za'a balla.  Ta dan tsorata kuma sai ta jure. "Uban waye?".  Shiru ba'ayi magana ba. Jin anyi shiru yasa taci gaba da abunda take yi.  Ganin wuka taki ta kama babyn ta dauko galan din kalanzir ta ajiye babyn a kasa ta jike ta sharaf! Tukun ta dauko ashana. Zata kyasta kenan.  Wani mugub karan buga kofa ya kara dakar mata kunne. Ba  tsoran koma Nasmat ta daka ashar, hade da cewa"wane dan ku... Uba ne? Mai gadi nasan kai ne wallahi in na fito ni da kai ne".   Bata rufe baki ba aka kara bubugawa wannan karan harda murya ta mai gadi sak! Da yace "Ki buuuudeeee".  Abun ya fusata ta jin muryan mai gadi. Ashanar ta kyasta!  Ta wula wa yar babyn  nan  take wuta ta kama ta fara ci.  Tana ganin haka farin ciki ya kamata tayi mugunta.   Saura kai mai gadi ta fada lokacin da ta nufi kofa rai! A bace domin har yanzu bugawa ake. Tana bude wa taga wayam, bayan kuma yanzu-yanzu ko seconds 4 ba'ayi ba da bugawa. Kofar dakin su tafi an rufo garam. Alamun wani ne ya shiga...............................



🤣🤣🤣 *Yau wata zata ci uban ta. Na tausaya mata.lolz*



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 27-28



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



_*IN DEDICATED TO ALL ALJANAR FATIMA FAN'S. INA JINJINA MUKU NA YABA DA IRIN KAUNAR DA KUKE WA BOOK DIN. SANNAN INA BAKU HAKURI MASU KORAFIN PAGE YANA KADAN WALLAHI I'M BUSY. KUCI GABA DA HAKURI. IN DA JIRGIN SAMA YAJE HAWAINIYA MA TAJE IN DAI ZA'A LALA BATA. LOLZ*_






*KARSHEN PAGEN BAYA*

 Tana bude wa taga wayam, bayan kuma yanzu-yanzu ko seconds 4 ba'ayi ba da bugawa. Kofar dakin su tafi an rufo garam. Alamun wani ne ya shiga..


»»Kofar dakin ta nufa cikin fushi tafe take da sauri rai a bace, tana zuwa kofar dakin tasa hannu zata bude kenan wani makeken kadangare irin mai jan kan nan ya fado mata a kai. Wani mugun ihu ta saka, ta fara tsalle-tsalle tana zagaye katan falon tana zazage-zazage da Kara  duk ta dauka yana jikinta ashe ya fado tun tuni. Ta dade  tana yi sai da ta tabbatar baya jikin nata tukun ta dan saki jikinta  ta hau dube-dube.  Bata hakura ba kofar ta sake tun kara da niyar ta bude wannan karan ma kadangare ne karami ya fado mata wannan karan cikin riga ya shigar mata. Nan ta fara ihu ta fadi kasa tana ta mirgine-mirgine. Kadan garen ya fita. Tashi tayi zaund tana Raraba idanu.  A zuciya tace "to wai me ma ya kawo kadangaru falo?".Kuma Wallahi sai na shiga dakin".  A fusace ta tashi sanda ta dai-dai ci kofar dakin tukun ta zura a guje. Ta bankade kyauran ta fada karfin gudun nata ya rinjaye ta ta fadi sauran kadan da ta yi karo da katanga.




Suman tsaye tayi a gurin. Dan ganin wani make ken maciji da ya fasa kai yana layi da kai. Nasmat ta san tana matsawa a gurin sai ya sare ta.  Karkarwa ta fara yi sai hawaye sharr! Kuka wii! Wii cikin kukan da take tana ihu!  "Wayyo mama na na mutu na lalace, dan Allah maciji kayi min rai kayi min aikin gafara, Wallah bazan kara Fashin sallah ba, kuma Wallahi bazan kara fashin zuwa makaran ta ba".  Ihun take tana ta zuba Surutai! Da rantse-Rantse  macijin ne ya dan kara bude kai nan take yana zaro harshe yana mayarwa. Kara tsurewa tayi da taga macijin yana kara matsowa a hankali. Tsoranta ne ya karu ta fara ihu! Tana karkarwa.  Sululu macijin yaje ya fara hawa kafarta. Tana jin haka sai fitsari Sharr! Gaba daya ta jika wajen. Sannan tayi tsaye cik kamar gunki ta rufe ido. Har yanzu dai macijin hawa kanta yake. Jima kadan taji baya nan. Bude ido tayi can ta hange shi ya shige ban daki su.  Da gudu tayi waje ta zo dai dai falo kenan wuta gaba daya ta dauke, dama nefa ce. Duk da rana ce amma bata iya ganin gabanta. Juye-juye ta fara yi tama rasa ina zata nufa. Ji tayi an shafe ta ta baya an wuce. Wani razana nan kara ta saki "Wayyo!" Cik kuma ta tsaya waje daya duk da bata gani amma tana jin motsi kamar mutum ya nufo inda take. Abunda ya taho din tana jin karar tafiyan saura kadan ya kara so gurin ta sai aka dawo da wuta.  Wani gwabran nun fashi ta sauke nan ta du duba amma ba komai a gun. Kan armchair ta zauna tana nunfashin wuya. "Wash! ni Nasmat yau naga bala'i wannan katan maciji idan ya sare ni ai in ana Wuce lahira ma sai na wuce".





Sukur-sukurtu taji a baya da sauri ta juya Taga ba komai, hahhahahh!  Dariya tayi da kanta tukun tace, "Lalai yau na tsorata".  Yar baby ta tuno da sauri ta tashi ta nufi kitchen domin gano ko ta idasa kone wa?.  Tana bude kyauran Kitchen din tayi tsaye hade da Zurawa guri daya ido, mamaki ne karar ya bayyana a fuskarta. Ganin yar babyn gata nan  a kwance inda ta yarda ta amma ko alamar an jika ta da kalanzir babu balle ma Wuta.  "Kai!, ban gane ba nafa kona wannan abun kafin in fita. To ko bata jin wuta na?. To amma bari inga a gaba na zan kona ki yar iska".   Galan din gas ta dauko a wannan karon  ta bul-bulawa yar babyn ta kyasta asha na ta wulla mata. Nan take wuta ta kama bal-bal farin ciki ne  ya lulube ta domin yau mugunta ce fal! A ranta. "Kyal-kyal-kyal-kyal, hahahahahahaha, hihihihijijhehehehehrhr". Sautin wata iriyar mahaukaciyar dariya ce da ke fitowa daga falo ya daki dodan kunnan Nasmat da ke tsaye itama tana kallan yar babyn tana dariyar mugunta.  Kofar ta bude a hankali ta Leka, fatima ta hanga zaune kan kujera ita ce mai uwar dariyar nan.  Nasmat na ganin ita ce sai ta bata rai ta Idasa fitowa..





Ishar ta maka. "Fatima ku....banki".  Shiru Fatima tayi ba tare da ta wai-wayo ba, Cikin sauri Nasmat ta karasa gurin tana zuwa kuwa ta Falle Fatima da mari ta baya. Gugur-gugur kai ya fadi kasa ya fara taya jini na fita a jiki. Gangar jikin ma Kasa ta fadi jini ya fara malala. Hannuwa biyu Nasmat ta dora a kai ta maka wani uban kara, Ta nufi gurin gangar jikin fatima ta rugume ta a kirji "Wayyo Allah na na shiga uku na lala ce, Fatima Wallahi ba kashe ki nayi niyar yi ba. Dan Allah ki tashi yanzu in su momy suka zo me zan gaya musu, Yau na shiga uku".  Kuka take sosai ba kukan rashin Fatima sai kukan rashin abunda zata ce.  "Ai da raina ban mutu ba Sake ni".  Gangar jikin Fatima ce ke magana. Shiru Nasmat tayi ta tsurawa Wuyan da har yanzu jini ke zuba ido.  Domin taji kamar daga nan taji magana  sai dai bata tabbatar ba. "Ni ki sake ni nace". Wata murya ce a shagwabe ta fadi hakan. Kafin a karasa maganar tuni Nasmat tayi wulli da gangar jikin Fatima din tayi hanyar kitchen a guje kamar wacce zata tashi sama. Gangar jikin tsaye ya tashi ya je ya daukko kan ya riko a hannuwa biyu A hakan Fatima ta nufo Nasmat da ke can bakin kofar kitchn tana kokarin bude wa amma kofar ta ki bude wa. Fatimar tana fadin "Aunty nasmat mayar min da kai na- mayar min da kai na".  Kuka ne ya subuce wa Nasmat tana tura kufa tana waigen baya tana fadin "Wayyo Allah momy na".   Gangar jikin Fatima ya kusan karasowa kenan kofa ta bude. Har Nasmat ta zura kafa zata fada kuma sai taja birki.  Yar babyn ta gani ta nufo ta tana kuka ga wuta na cin jikinta kuma hawayen jini ne ke fita a idanun ta. "INNAHU MIN DAUDA WA, INNAHU MIN SULAIMANA, WA BAZAN KARABA NA TUBU KU YAFE NI".Da karfi Nasmat din ke fadar haka tana karkarwa. Da dai taga wannan ba mafita bac...........................


AYI MIN AFUWA BUSY YASEEN




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy


















👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 29-30



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



PAGEN YAYI MIN DADI SHIYASA NA BAWA BEST FRIENDS NAWA. 


Usaini atk 80k


Shamsuu Bin Yerhyer


Mustpha Rogo


Abdul King Article


Musa Umar Abdullahi


Shatu muhammed


Aisha adam


Ahmed tijjaniyu


*HAKIKA KU MASOYA NA NE NA GASKIYA, KUNA A SAHUN GABA CIKIN MASOYA NA. INA GODIYA DA BIBIYAR LITTAFAI NA DA KUKE ALLAH YA BARMI YARE.*




 Nasmat a guje ta bar wajen nan suka hau zagaye falo. Gangar jikin fatima dauke da kanta a hannu jini na zuba tana bin nasmat di  tana fadin "Auntu dan Allah ki tsaya ki samin kaina". Fadi take tana maimatawa tana biye da nasmat din. Haka itama bangaren yar babyn bin Nasmat take tana fadi  "Aunty  kashe min wuta wayyo! Wuta na cina".  Gaba daya sun zagaye falon sun mishi kaca-kaca da jinin da ke zuba.  Nasmat abun ya zame mata biyu ga tsoro ga karfin maganar tasu har cikin kwalwarta, Ta dai fahimci wannan so suke su Haukata ta. Allah ne ya bata sa'a ta ta nufi kofar fita a falo tana kamawa kofar ta bude da sauri ta rufe kofar ta jingina da kofar tana shasheka.  Hamdala ta farayi a nufin ta ta rabu da su.  "Aunty ki kashe min wutar".  Wani uban kara ta daka "waaaaaayyooooo Allah na"  ta runtuma a guje tana kiran me gadi. 'Yar babyn ta bita baya Nasmat dakin mai gadi ta leka shiru ba kowa. Nan taje ta fara kokarin Bude kofa taji a garkame da kwado.  Juyowa tayi ta zube a kan  gwiwoyin ta tana bawa aljanar hakuri.





 "Dan Allah kiyi hakuri ki yafe min, daga yau bazan sake takurawa Fatima Allah wallahi tallahi na rantsi da uwata da ubana ku....."   "Kheeeeeeeee! Yi min shiru,  muguwa kawai azzalumam".  Cikin wata iriyar murya mai karsashi da ban tsoro Aljanar ke magana.  "Daga yau sai yau idan har na sake ji ko gani kin wa Fatima ko harara, ki san da sani dan Wallahi sai na taba lafiyar jikin ki, kina jina?".    Da sauri "Eh naji *ALJANAR FATIMA* daga yau Wallahi na dai na".   Wata dariya 'yar tsanar tayi mai ban tsoro wanda kasa kanta girgiza take kamar jirgin dan kara zai tashi.  "Oya to dauke ni kije ki min wanka da kwalliya".   Zaro ido Nasmat tayi ta kara make wa a jikin gate din dan tsoro. "Keeee! Ba dake nake ba".  Jiki na karkarwa Nasmat ta taso kamar bata san tafiya hannun na karkarwa ta dauki 'yar tsanar ta wani mimike hannu kamar wacce ya dauki abun kyama. "Au! Kyamata ma kike oya Rungume ni".  Nasmat kamar ta fashe da kuka a mugun tsora ce take.  A haka taje tayi wa yar babyn wanka a tsorace Sai da 'yar babyn ta bata wuya sosai a wajen wankan. Domin sai nasmat na mata wanka ta zuro hannu ta kama hancin ta ja da karfi, ko kunne.   Nasmat sai dai yi kara kawai.   Bayan gama wankan aljanar tasa Nasmat ta zo tayi mata kwalliya ta dauko akwatin ta tasaka mata kaya masu kyau.




 "Yanzu abunda nake so shine ki dauke ni ki kaiwa Fatima kice mata dama wanka ne zaki mini, karki yarda kice mata nayi miki wani abun kina jina".  Da sauri ta amsa "Eh zanyi hakan aunty aljana".  Nasmat ta fada murya na karkarwa.   'Yar tsanar tasa dan guntun hannunta ta wanke Nasmat da mari. Da sauri Nasmat ta dafe kunnu domin zafin marin. Kuka ta fara wii!-wii!  Harda hawaye.  Tsawa aljanar ta daka mata. " Rufe min baki, Ki kira ni da *SAFURATU*  KO  *ALJANAR FATIMA* In kuwa ba haka ba zaki san da sani".  Gum Nasmat ta kame baki duk da kukan yaci karfin ta sai dai ba yanda zata yi aljana ta saka ta gaba. Hawaye ne kawai ke zuba a idanunta. "Muguwa ashe mugunta ba dadi kuke cutar marainiyar Allah kaf! Gidan nan banda alhaji da fiddausi ba wanda zan saurara wa sai na dauki mumunar mata ki a kanku.  Sannan yanzu abunda nake so shine. Bayan kin kaiwa Fatima ni ku wuce gidan baki da ita kina jina"?.   "Eh", farin ciki ne  ya ziyarci zuciyar Nasmat domin kuwa abunda take so kenan Taji maganar mugunta. Aljanar tace sai taci uban kowa a gidan.  Daukar 'yar babyn Nasmat tayi ta fita da ita anyi sa'a kuwa lokacin mai gadi ya dawo, Wata muguwar harara ta galla mishi lokacin da ta zo giftawa. A zuciya tace "Mugun mai gadi ko hada kai ma aka hada baki, Wai dan kuu... Uba sai yanzu zai dawo bayan na shiga tarkon Aljanah".





 Kwance suka Tarar da Fatima a kofar gida sai sharara barci take ta gaji da kuka.   Nasmat rike da 'yar tsana a hannnu wacce duk sanda ta kalle ta bata marmarin karawa don irin hararen da take aiko mata. A hankula ta tayar da Fatima ko ita Fatima tayi mamaki abunda bata taba gani a gun aunty nata ba kenan. Ko Nasmat taga mamaki a fuskar Fatima a zuciya yace "Yarinya wuya ce mai saka kafuri sallahr dole".   Kallan Fatima tayi Cikin fara'a "Fatima Ga 'Yar babyn ki dama fa wanka ne zanyi mata. Yanzu tashi zakiyi mu tafi gidan biki".  Fatima cike da Zumudi ta karba "Na gode aunty na tayi kyau sosai. Amma mama asiya tace baza'a je dani ba".   Murmushi Nasmat tayi, "Karki damu baza ta ce komai ba ai dani za'a je".  A zuciya kuwa tace "Yarinya ai ko Mama Asiya taga bala'in da na gani dole ta tsure ta amshi duk wani umarni ko da ta san bazai yuyu ba".  Fatima tace to "muje muyi wanka ko Ko aunty?".  Nasmat kallan Aljanar tayi irin kallan da babyn ta watso mata ya nuna mata alamun bata yarda da wannan ba.  "A'a 'yar kanwata ai sai mu makara tashi muje nima ko uniform bazan cire ba". A hakan kuwa Nasmat ta tsayar musu da napep suka hau. Har yanzu jikin Nasmat bai daina Rawa Ba.  Allah-Allah take su sauka ta bace musu a gidan  biki ta rabu da bala'i.  Ba'a jima ba suka isa kofar gidan.  Nasmat ta shiga gida kenan domin ta karbo wa mai Napepk kudin sa ta bar fatima nan rugume da babyn ta.

 Wasu 'yan mata ne suka zo wuce wa, Idan daya ya kyalla kan yar babyn Fatima hakan yasa tace wa abokiyar tafiya. "Laaaa! Kawata dubi wata 'yar tsan mai kyau muje mu ganata". Suna karasa wa gurin hadiza ta warci yar babyn ta maka ta da kasa tasa kafa ta taka.  "Haba kawata wannan gunkin abunda Allah ya tsine wa mala'iku Ma basa zuwa gidan da ke d..,.". Tasss! Tasss, Taji saukar tagwayen marika a kumatun...........................




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





Autan writers nee  king boy





👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 31-32



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




😘 *WANNAN PAGE IN SADAUKAR WA NE GA LITTAFIN👇🏽


🙆🏻‍♂ *'YAR AIKIN GIDA NA* 🙆🏻‍♂



*SHAZEE* Allah ya karo basira Aljanar Fatima taji dadin kyautunan pages da kike bata hakan ma yasa ta tasa ni gaba a kan sai na baki wannan.  🙊 Yauwa kuma ina so muyi sirri a bani number hafsat zan aike ta wajen BOKA MAI KWARAN GWAL! 😜 .lolz



👏🏼 *BADA HAKURI* 👏🏼


Masoyan littafin nan ina baku hakuri bisa rashin jina da kuka yi jiya. Naga sakonin ku da masu kira na. Na gode 😍 I luv yhuu All my fans.   






*KARSHEN PAGEN BAYA*

~"Haba kawata wannan gunkin abunda Allah ya tsine wa mala'iku Ma basa zuwa gidan da ke d..,.". Tasss! Tasss, Taji saukar tagwayen marika a kumatun.~


»»Dafe kumatu tayi, "Kai! Kai! Kai! Kut...uba yau za'ayi bala'i  a wajen nan wato dan na yarda wannan tsinanar 'yar tsanar shine zaki mare ni ai kuwa bazan taba yarda ba". Kafin kawar tata tayi magana tuni hadizar ta wanka mata mari. Nan  fa sukayi hau kunce. Fada ya kace ba. Duk abunda yake faruwa a kan idan Nasmat Ita kuwa tasan abunda ya hada fadan hakan yasa ta kyalkyalewa da dariya harda rike ciki.  'Yar tsanar ce ta mata wata iriyar harara wacce tasa bata shirya ba ta dakata da dariyar.  A hankali taje   taba wa mai adai-daita kudinsa tace wa Fatima "kinga dauko 'yar babyn ki mu shiga ciki".  Da sauri Fatima ta share hawayen da suka fara zubo mata. Ta dauko 'yar Nasmat ta kama hannunta suka shiga ciki. Safuratu ganin sunki rabuwa da fadan ne. Ta zo ta fara kan uwa da wabi. Mari sai dai kaji kara tass! Tass an rasa  daga ina yake fitowa.  Ba arziki suka rabu da gudu suka bar wajen domin sun maru ba laifi. Da shigar su Nasmat falon. falon suka iske mata ne damkam a ciki su mama asiya suka fara wurgo mata harara,






Umma ce ta taso wacce itace mahaifiyar Haleema da ake wa auren kuma yayar Mama asiya ce. Yanayin jikin su da na asiya duk daya itama yar lukuta ce. "Nasmat ke wacce irin doluwa ce?, Da zaki taho mana da wannan marar jin yarinyar. Ko zaki zo ai bai kamata ki zo mana da wannan ba, Ke kinsan cewa jina na ko kadan bai hadu da wannan kazamar yarinyar ba".  Umma ce ke fadar haka.  "Umma ni gani nayi an barp ta a gida ita kadai shi yasa ma nace ta taho mu tafi. Mama asiya ce ta taso tubur! Tubur!  "Kanwar uwarki ce ita din  da zaki ji ba dadi dan an baro ta a gida.  Dallah fidda muna ita waje kuna ji daga shigowar ta har ta dumame falon da wari".  Umma tace "Zo nan kawo 'yar babyn nan dan ubanki daga yau ta zama ta khaleel". Warce diyar tayi ta mikawa wani marar jin yaron ta dan lukuti.  Fatima kuwa ta fashe da kuka ba komai yasa ta kuka ba sai kwace mata 'yar baby da akayi.  Wani mugun dadi ne ya ziyarci zuciyar Nasmat ganin abunda su Umma suka aika ta, domin yau cikin mugunta take. Waje Fatima ta koma ta sama wani waje ta zauna ta saka kanta tsaka nin kafafunta tana kuka a hankali. Nasmat kuwa tasan amare suna sama kuma tasan Asmart ma na can amma ta tsaya kawai so take ta ga abunda zai faru.   Khaleel ana bashi 'yar tsanar waje yayi da gudu. Wajen wasu marar jin abokan nashi yaje. Suna ganin ta kuwa wani daga cikin su ya rugo da gudu ya dau ki wuka wai yanka ta zasuyi. Sai da aka kwantar kamar dan akuya wukar kawai zasu dora nan take ta fara girma kafin su ankara tuni ta koma make kiya  abun tsoro.  Rugawa sukayi da gudu khaleel ne rike da wuka sai ya daga kai yake kallanta shi yaki rugawa.  "Yanka ni mana khaleel".  Abunda take fada tana mai-mai tawa  kenan  nan take tsoro ya ziyarci khaleel din karkarwa ya fara bai ankara ba yaji saukan bulala. 




Gudu yake yana kuka hade da soshe-soshe yana kiran uwarsa. Daga ganin sa kaga  wanda ake bi ina zane wa sai dai in ka duba baya babu wani wanda yake biye da shi domin  aljanar a bace take. A million ya shigo gidan Nasmat na jin kukan sa a tsorace ta ruga a guje bayan mama  Asiya ta wani makal-kale ta. Khaleel ne ya shigo yana kuka Da sauri Umma ta tashi ta tarye shi "Auta na lafiya, auta lafiya". Bayan ta ya boye yana nuna hanyar waje matan da ke falon duk suka dubi gurin ba komai.  Da sauri ta juya tana jijiga da gani kasa  bala'i ya tashi. "Waya taba min kai auta fada min ko uban waye wallahi sai naje naci mutun cin sa, fada min waye". Cikin kuka yace "Yar babyn Fatima ce".  "Kai bana san shirme fada min waya dake ka". Amsar da ya kara basu kenan *"ALJANAR FATIMA* Ce".  "Ok kwace ma tayi kenan bari inzo". Buzu-buzu ta fita a waje ta sama Fatima rike da 'yar babyn mari ta wanka mata, "Ke dan ubanki in bawa yaro na abun yayi wasa shine zak kwace, kawo ta dan uban ki" warce wa tayi ta koma ciki Fatima kuwa kuka ta kama yi domin ita dai a iya saninta taga Khaleel ya wuce yana kuka bai dade ba kuma taga ya fito ya kawo mata yar babyn ta da kanshi.




 Umma na shiga da 'yar tsanar Nasmat tayi wani mugun tsalle a firgice ta fada bayan kujera A tsorace tayi muky! Tana saurare su.  Khaleel na ganin Umma ta shigo da yar babyn ya kara fashewa da kuka ya ruga a guje ya makal-kale Mama asiya kamar zai shige jikinta. "Bana so! Bana so! Karku kawo ta". Abunda khaleel din ke fada kenan ganin  uwar tasa bata daina nufo shi da yar tsanar ba ya sa ya tashi ya zuba a guje sama. 





 Rike baki Umma tayi "Ah! Ashe tsoranta ma yake har na wani bashi. Komawa tayi daga bakin falo ta wurgawa Fatima 'yar tsanar  "Dauki tsiyar ki gata nan tsoranta ma yake yi".  Fatima cike da farin ciki ta bar kuka ta dauki abunta ta rungume. Masu dafa abinci ne suke ta zuzubawa sun karasa kowa sai dai ya zo ya dauki nasa da na 'ya'yansa  Fatima najin yunwa tsoro take taje ta dauka  ga abincin a Take away amma tana tsoro a mata fada. Yunwa ta kai mata karo koma taga har yara na zuwa dauka ba'a hana su hakan yasa itama ta tashi dugwi-dugiw ta nufi wajen da aka jera take away din.  Tasa hannun zata dauka kenan, taji an daka mata tsawa sai da ta zabura firgi-git "Keeee!  Dan ubanki waya baki izinin ki zo nan balle ma har ki dauki abinci?".  "Dama-dama yunwa nake ji mama asiya". "Kinci ubanki maza wuce idan anyin sauran abincin shi za'a baki". Magana tayi wa masu dafa abincin tace kar wacce ta yarda ta bawa fatima abincin in kuwa wata ta bata sai ta hadu da fishinta. Tana gama fadar haka ta dauki abincin guda uku ta nufi falo. Gaba daya hudun ta saka gaba da niyar ci. Lomar farko  ta na kai wa baki ta zubdo da sauri. Nan take kowa da ya kai abincin baki sai ya zubdo saboda masifafan gishiri da ke cikin abincin duk wanda ya kai baki sai yaji kamar dai gishirin ne yayi loma da shi.  Ran jama'a ya baci hakan yasa sukayi tururuwa suka wa masu aikin abincin caaa! Kamar zasu cinye su dan masifa. Mama asiya ce ta juyo ta kalli Fatima mugunta ce ta motso hakan yasa ta dauki abincin daya tana murmushi "Fatima to ga abincin ci ko".  Da sauri Fatima ta karba domin masifar yunwa take ji.  Loma ta fara kaiwa hannu baka hannu kwarya. Gaba dayan matan gidan kallanta suke suna dariyar mugunta, Ita dai fatima kallansu take ta rasa me yake basu dariya domin kuwa ita lafiya lau take jin abincin da dadinsa. Wata tsohuwa ce ta shigo gidan bara sanye take da bakar hijab doguwa har kasa, fuskarta duk a tatabe. 




Bara tayi da farko suka ce hakuri kamar hadin baki. Ta kara nan ma suka bata hakuri. Kamar bata ji ba a karo na uku ta sake yi musu bara. "Masu gida a taimaka min da abinci ko kanzo ne ko saura in sama abunda zan zuba a ciki na rabo na da abinci tun jiya".  Sauran muta nan ne suka fara balbale ta da masifa Umma tana murmushin mugunta ta dauko abincin har guda biyu ta sa tsohuwar ta zauna. Ta bata abincin suka koma gefe dan suyi dariyar mugunta. Lomar farko tsohuwar ta zubdo tana  kakarin amai.Dariya suka hau kyakyatawa kamar me. "Haba bayin Allah ya zaku bani abincin da zai kashe ni wannan abinci ko gishiri".   Asiya ta taso cike da masifa kamar zata hade tsohuwar. "Kinga tsohuwa bama san ciki da rashin mutunci da rai nin wayo, Dan kutu....uba  ba sao da aka baki hakuri har sau  biyu ba kika ki hakura kuma yanzu an baki shine zaki wa mutane tsiya".  Cike da Tsokala da tsiya mama asiya ta juya "Jama'a ku karo mata Takeaways uku ta kara ta kai wa jikokinta".  Gaba dayan gidan dariya suka hau yi mama asiya harda dukawa tana Rike ciki.  Dagowar da zatayi taji saukar mari ya bada sauti. Tasssss! abunda ya dakatar da dariyar jama'a kenan.  Hannu Daya mama asiya tasa ta dafe kumatu, ba abunda ya bata mamaki da tsoro sai ganin ba komai a gurin tsohuwar ta bace.Saukar  Bulala  taji a bayanta...................

....



Yau wasu sun dauko ruwan dafa kansu.   


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan writers nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 33-34



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




😘 *WANNAN PAGE IN SADAUKAR WA NE GA MOMCY DIN MU.  MUNA SANKI MUNA KAUNAR KI. MUNJI SAKON KI A BAKIN 'YAR UWAR MU,

QUEEN MEARYAM ('YAR MAMARMU)*


       We love you too♥

   BY ALL ZAMANI WRITERS.


*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Hannu Daya mama asiya tasa ta dafe kumatu, ba abunda ya bata mamaki da tsoro sai ganin ba komai a gurin tsohuwar ta bace.Saukar  Bulala  taji a bayanta...~


»»Da sauri ta fara so sa baya tana ra raba ido.wata bulalar aka zubga mata wacce tafi ta dazun ma zafi abunda yasa ta rugawa tubur-tubar cikin jama'a tana ihu! Kenan duk. Aljanar binta take tana zane wa tuku  ta koma kan uwa da wabi, domin kowa duka take ai kuwa gida ya hargitsa mutum.na tsaye ko yana gudu sai dai yaji saukar bulala. Haka suka fara rantar ta kare suna yin kofa, Nasmat na jin gida ya hargitse ta kwashe da dariyar mugunta domin tasan (A rina, wai an saci zanin mahaukaciya) Wata mata ce aka biyu da gudu ta shigo dakin, karan bugo na tashi amma ba ka ganin mai dukan. Nasmat na ganin haka tayi wani juyin da bata shirya ba. Da gudu ta nufi saman bene (upstairs)  ai kuwa matar ta biyo ta tana ihun neman ce to. Nasmat na ganin haka ta kara wuta. Tana karkarwa ta fada dakin da amaren suke ta turo kofa, Tayin saurin Saka kuba. Ta jingina baya tana haki. Gaba dayan 'yan matan ne suka hayaya ko mata kamar zasu cinye ta danya. "Ke wace iriyar ce da zaki shigo wa muta ne ko sallama babu kin tsorata muta ne". Wasu 'yan mata uku ne suka fadi hakan cikin daga murya.  "Kuyi shiru Aljanu ne aljanu". Haleema ce ta taso cike da masifa. "Kutumelesi Lalai yau zakiyi bayani wato ke dan rashin kunya har kika iya tako kafarki zuwa wajen biki na oya to wallahi kama hanya in ba so kike yanzu mu kwashi 'yan kallo da ke ba.




 Bar ganin ina amarya wallahi sauke gwa-gwaran nan zanyi inci ubanki".  Duk da Nasmat taji haushin zancen Amma sai ta basar domin jin Matar nan ta zo bakin kofa sai bubugawa take tana fadin "dan Allah ku ce ce ni ki bude zata kashe ni". Karkar wa Nasmat ta fara yi tsoranta ya karu abun ya zame mata biyu ga masifar haleema ga kuma wacce aljana ta biyu.  "Sister Haleema dan Allah kiyi hakuri zan fita, Wallahi nima ba da gangan na shigo ba aljanu ne a gidan yanzu ma aljanace ta biyu mu ni da wata kinji ta nan tana bubugawa". Wani dogwan tsaki amaryar taja tare da kama hannun Nasmat tana kokarin bude kofa ta tura ta. "Aljanu ko to wallahi sai dai su kashe ki amma sai kin fita. Ke sunci kut.....ubansu ma aljanu". Kafin ta rufe baki taji saukar wani lafiyayen mari wani har sai da taga taurari.  Juyo wa tayi, "Kai kai kai kika mare ni Nasmat. to wallahi  yau banga mai raba ni dake ba a gidan nan". Nasamt kafin ta bude baki ta ce l ba ita ta mare ta ba.





 tuni Haleema tayi kukan kura ta kai mata chakuma (kamar zakaru na fada) suka fara bige-bige da naushe-naushen juna su kuwa 'yan matan amaryar sun kai su shabiyar a dakin harda Asnart a ciki amma ba wace tayi yunkurin rabawa. Haka dai suka ci gaba. Saukar bulalin da suka fara ji kamar daga sama yasa suka dan saki juna ko wacce idan ta cike da kwalla. Jin an dakata da dukan nasu kamar hadin baki suka kara cakumar juna. Wani Razana nan kara ne ta cika dakin wanda suka rasa daga ina ya fito. "Kaaaaaa!". Nan fa suka saki juna suka durkushe ko wacce ta rufe kunnuwan ta domin karar yayi yawa. Haka 'yan matan amarya ma gaba dayan su kowa ya rufe kunne suna raraba ido. "Kuuuuu taaaashiiii tsayeee". Wata murya ce wacce in kaji ta kai kanka sai ka firgice gata da karfi ga tsoratar wa. Haleema da Nasmat tsatsaye suka mike ko wacce karkarwa take kamar su ruga su bar dakin. Haka yan matan amarya wasu suka shige cikin (wardrobe) wasu suka haye kan gado suka rufe da blanket kowa dai  da wajen da yake nufa neman mafaka. Asmart kuwa kofa ta nufa da gudu nufin ta ta bude ta gudu. Tsawa aka daka mata. "Keeee inaaaa zakijeee". A wajen ta fadi ta fara zubda hawaye "Ba ko ina". 





 Ta fada murya na karkarwa cike da tsoro. Tana waige-waige saman Silin ta kalla da taga kamar wani baki baki ta wutsiyar ido. Ihuu! Ta kurma hade da Runtse idanu tasa hannaye ta rufe kanta. Kan mace ne a yanke gashi buzu-buzu fuskarta babu kyan gani abun tsoro. Kan reto yake a sama shine ke maganar.  Su Nasmat koda suka daga kai suka kalle ta sai tsoran su ta karu ba wacce ta sake yunkurin Motsi da kanta balle ta kalli sama.   "Watooo kuuuu waiii gabaaaa kuuuuukeee yiiii tsakaaaa niiiin kuuu koo?".  Cikin sauri suka hada baki gurin cewa. "A'ah".  Cikin tsawq "Ku rufe min baki marar kirkin banza da akayi kuna 'yan uwan juna kuma ku musulmain ne amma kuke gaba da junan ku. Ku rungumi juna daga yau kar in sake ji. Ko bayan auren haleema  ne".   Cikin sauri suka Rungumi juna suna karkarwa.  Hahahhahhhah!  dariya ce mai firgitar wa ta kaura de dakin. "Sauran kuma in sake samun labarin kuna gaba. Sannan Kar wacce ta yarda ta fita daga dakin nan a cikin ku in dai ba lokacin kai amarya ne yayi ba kuna jina?".  Wannan karan har 'yan cikin Durowa (wardrobe) sai da suka amsa da karfi "To". Bat! aljanar ta bace.




Tsakar gida gaba daya ya hautsine tun daga farkon layin zaka iya juyo masu ihu nayi masu kuka nayi haka ma masu karatu addu'o'i nayi.  Kofar ta kulle har yanzu kuma zanar su ake ba'a dai na ba. Fatima kanta ta tsorata da gudu ta tashi rike da yar babyn ta nufi wani  keji ta shige ta boye dan gudun kar a banke ta. Kafin kace me Mata wajen biyar ne suka shiga keji dan ce tan kansu. fatima kam matse ta akayi gam. Macen da ke bakin kofar Kunama ta gallawa cizo ihu ta kwada ta fita a guje tana Soshe-soshe.  Gida gaba daya ya hargitse kowa ta kansa yake yi. Abincin ma tuni an zubda shi an tatake. Ga kofa ta kulle taki buduwa.  'Yar tsohuwar nan ce ta bayana a sama kamar tsutsuwa fuska a murtuke. Wata tsawa ta daka wanda tasa gaba ki dayan gidan ya kara hargitse wa. Ba abunda ya kara haddasa cin kosan gidan sai falo da shima yaki buduwa. 






 Mata kam wasu ban daki suka shige harda masu shiga cikin tukunya dan tsoran bulalar.  "Kowa ya tsaya kar ya matsa a inda yake".  Aljanar ce tayi magana cikin daga murya abunda ya tsayar da guje-guje da ake faman yi kenan.  "Wato ku marar imani ga abinci a gaban ku ba na uwarki ba bana ubanki ba almajira tayi bara harda masu daga sauti gurin bada hakuri. Ke kuma Waccen 'yar lukutar matar (Ta nuna Mama asiya da yatsa)  kece muguwa har da bani abinci mai gishi ri nayi magana kika ta so baki ga girma na ba a haka kamar zaki bige ni ko?".   Mama asiya jikinta ne ya hau bari murya na rawa "A'a dan Allah kiyi hakuri bansan ke aljana bace, wallahi dama taimaka miki ne zanyi dan na.....".   "Rufe min baki, (Aljanar ta daka mata tsawa) Makaryaciyar banza, Ku kuma abunda yasa nayi muku wannan hukuncin dan ku kiyaye gaba ne. Ni Aljana ce ba mutum ba. Da mutum ce da kun wulakanta banza kenan. Wai ace a cikin ku kuna ganin wannan matar zata ci min mutunci ba mai bada hakuri ko dakatar da ita sai ma dariya. Kunci sa'a ni musulmar aljanah ce ba muguwa ba amma da yau sai nayi muku tatas a gidan nan duk da sai na farfasa muku jiki".  




Shiru sukayi babu mai ko motsawin kirki kowa a tsora ce yake. "To abunda nake so da ku yanzu shine Ga mai gidan nan da 'yan anguwa a kofar gida sunzo jin me ke faruwa, kar wacce ta yarda ta bude baki ta fadi abunda ya faru, Duk wanda aka tambaya yace ba komai.  Sannan baku ba fita daga gidan nan sai bayan an kai amarya. Duk wacce tayi yunkurin fita kuwa zata hadu da fishina".  Tana gama fadar haka ta bace bat!  Kofar gidan kuwa da su Alhaji ke  faman ballawa ta bude wayam. Shigowa sukayi suka ga gidan yayi kaca-kaca nan suka hau tambaya me ya faru kowa sai dai yayi shiru da bakin sa. Masu dan kokari da rashin tsoro ne ma suke cewa babu komai. Nan dai su Alhaji suka gaji da tambaya sukayi fushi suka bar gidan suka  koma harkokin su na shirye-shirye daurin aure. 




Tsakar gidan tsitt! Kake ji babu mai wani kuzari duk sun jigata marar dauriya ma daga cikin su kuka suke wasu kuma na Soshe-soshen inda suka sha bulala. Wata Yar siririyar mata ce ta mike tana fada. "Wallahi ni sai na fita na tafi gida. Sai dai in kashe ni zata yi ta kashe kawai dan zalunci daga zuwa wajen biki a tsare mu kamar wani gidan maza".  Jakar ta ta dauka tasa takalmi ta nufi kofa buzun-buzun da niyar wuce wa. Har ta kusan kai wa kofar gida, taji an kama kafarta ta baya an wani warto....................................



*TASHIN HANKALI* 


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 35-36



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




DEDICATED TO YOU:

☺ *SISTER NA HAFSAT IBRAHIM* ☺

NAGA DOGON COMMENT, NAJI DADIN ADDU'O'IN KI DA FATAN ALKHARIN DA KIKA MIN. NA GODE KUMA KEMA ALLAH YA BAKI DUK ABUNDA KIKA ROKAR MIN. (Ana tare)


😘 _All my fans thanks 4 You love and supported. Allah ya bar zumuncin. Ina ji da ku sosai da bazar ku nake rawa._😘


🤣😂 _*WATO YAU INA TYPING INA DARIYA BAN TABA DARIYA GURIN TYPING KAMAR NA YAU BA. UHMMM BA SAI NACE KOMAI BA KU KARANTA TUKUN. NAJI DAGA GARE KU MY FRIENDS I LUV U OLL*_ 🤣😂



*FOLLOW US ON THIS DETAILS:*

----

*LIKE OUR FACEBOOK PAGE:*

↓↓

*Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION*

----

*CHECK OUR BLOG'S*

↓↓

*Zamaniwriters.blogspot.com*

----

*DROP YOUR COMMENTS AND REPORTS ARE HIGHLY WELCOME ON THIS EMAIL ADDRESS:*

↓↓

*Zamaniwritersassociation@gmail.com*

----

*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Jakar ta ta dauka tasa takalmi ta nufi kofa buzun-buzun da niyar wuce wa. Har ta kusan kai wa kofar gida, taji an kama kafarta ta baya an wani warto.~


```»» Kafarta ta fadi Janta akayi kiiii! Tana ihu hade da wuntsile-wuntsile, Zaka ga ana janta amma idanunka baza su gano maka mahalukin da ke jan kafar tata ba. Sai da aka kai ta can gaban mutane sannan aka barta, Zaune ta tashi tana kuka tana wage-wage, jama'ar wajen wanda basa da jumurin dariya har sun fara gagaba ta. Suka ji wata tsawa wacce tasa kowa yayi tsi!. Gidan shiru kake ji ko fitsari ba wanda ya yarda ya tashi yara da manya, haka suma can saman beni suna cikin daki sunyi tsi! Sunyi zugum suka ji ana Kwankasa kofar daki. Wasun su tuni sun kankame juna kowa na ihu yana kiran momynsa. Shiru ba wanda ya sama damar bude kofa hannun mace suka gani ya zuro ta jikin kaure ya murda key nan take ya bude. Nan fa tsoran su ya karu ba abunda ya kara tsorata su sai ganin wata kyakyawr zankadediyar budurwa fara ce tas!. Sanye da doguwar farar riga daga ka ganta kaga balarabiya. Wannan ya tabbatar musu da ba mutun bace aljana ce domin basa da alaka da Larabawa. Hannun budurwar rike take da Wani dan karamin akwati mai marika. Nufo su tayi tana murmushi. "Ina Amaryar ta so in miki makeup". Ta fada lokacin da ta durkusa tana kokarin bude dan akwatin. Haleema da Nasmat kamar ba abokan gaba ba domin haleema makal-kale Nasmat tayi Nasmat kuwa kokarin raba ta da jikinta take domin karta jawo mata.  Aljanar ta tsaya tana kallan su gaba dayan 'yan matan amaryar kokarin turo haleema suke gaban aljana ita kuwa tana kara make wa.  Sakin baki aljanar tayi tana kallan su ganin haleemq bata da alamar tahowa. Tsawa ta yi musu wanda ya rikita dukan su kanta ya fara futar da hayaki. Gaba daya sun firgice jikin halima na rawa ta taho tana wani kwabe fuska jiki na rawa. Daga tayi tako daya sai ta tsaya ta wai waya baya kamar ta ko ma. Aljanar ce ta wani harari kawayen amaryar da idanunta wanda sukq fara komawa ja. Da sauri mutum uku suka turo haleema da karfi. Ta fada jikin Aljanar ta dan rungume ta "Haba 'yar uwa ta ya kike tsoro na bafa cutar da ke zanyi ba". "To", din karfi da yaji Haleema ta fada jiki na bari.   Nan Aljanar ta zaunar da ita ta fara Gyara mata fuska. Wasu kayan shafe-shafen ma kai baka taba ganinsu ba. Sai da ta gyara mata fuska ta fito fes! Tayi kyau sosai, Aljanar ce ta juwa musu fuskan Haleema "Tayi kyau kuwa 'yan uwa". Da karfin su kamar hadin baki ba wacce aka bari wajen cewa. "Eh tayi kyau". Duk tsoro suke ji. Sai da Aljanar ta gama gyara ta sosai har gwagwaran sai da ta sake hada mata mai kyau.  "Kuta shi mu fita yau kowa sai yawa amaryar nan huduba. Cikin hanzari suka tashi saboda tsabar tsoro. Gaba Aljanar 




Amaryar na binta baya sai 'yan matan amarya da suka rufo musu baya. A tsakiyar falo Aljanar ta zaunar da haleema ta ce su dakata ta kira wo muta nan. Ba garda ma duk suka ce "To". Fita tayi waje mutane anyi Tsuru-tsuru kowa sai tunani yake, wannan gidan biki baiyi dadi ba. "Sannun ku da hutawa uwayen amarya ko?, To ban ware kowa ba ku shigo ku mata hudu ba".  Kamar daga sama suka jiyo maganar da sauri suka waiga duk wanda ya kalle ta ya san Aljana ce hakan yasa duk a tsorace suka tashi dan bin umarnin ta har rige-rigen shiga daki ake. Kuri sukayi wa amaryar inda ita kuma Aljanar ta tashi sama tana kallan kowa.  Jin sunyi shiru sun saka amarya gaba kowa sai raraba idanu yake Ta daka musu tsawa. "Kuyi mata hudu ba nace ba ku sata gaba ku kalla ba". Kafin kace me dakin ya cika da hayaniya kamar makaranta haya-haya wani bai ma san abunda ke fitowa a bakin sa ba, kawai tsabar tsoro ne. Jin sun cika mata kunne ta kara musu wata tsawar wacce tafi ta farkon kara da ban tsoro. Da yawa sun zabura koya ya kama bakinsa yayi tsitt!.  "Au! Dama haka ake huduba a garin ku?. Oya daya bayan daya zakuyi"   mama asiya ta nuna da doguwar yatsa. "Ke fara".  Mama asiya na karkarwa. "To, Amarya kina jina ki bi mijin ki sau da kafa kiyi masa ladabi da biyaya banda Rai ni shi shugaba ne a gare ki. Banda daga mishi murya duk abunda ya saka ki kiyi".  Shiru ce ta biyo baya. "Au! Shikenan kin gama?". "Eh, A'ah" ta bada amsa.  "To duk ke kina wa mijin ki hakan?".  "Eh ina mishi mana". Ta fada tana murmushin dole. "Shikenan zan bibiyi rayuwar ki idan naga akasin haka to ke ma kin san sauran".  Cewar Aljanar bata tsaya sauraran amsar ba.cikin daga murya ta nuna Zuwaira Da yatsa ke da kike noke-Noke oya saura ke".  Zuwaira a firgice kamar ta saki fitsari ta fara karkarwa tsabar tsoro. "Too too niii dammmaa abuuu!!!...".   "Ke ki natsu kiyi mana magana sak!, In ba haka ba yanzu in mayar dake Mage".    Hannu zuwaira ta dora a kai. "Na shiga uku dan Allah kiyi hakuri karki mayar ni kyanwa.



 Haleema ki tsaya kiyi tunani yanzu kin girma kin zama cikakar mace ki natsu ki zabi kawayen kirki masu nuna miki hanyar tsira karki dauki masu Janki juwa hanyar halaka. Wannan wani zama ni ne ya zo mana wanda shawarar kawaye ke bada babbar gudun muwa wajen kashe aure. Ki tsaya ki natsu ki gane aure shine darajar 'ya mace ki zauna da mijin ki lafiya......". Taf! Taf! Taf!  Aljanar ta fara tafawa zuwaira da jin haka sau duk suka dau tafi..Aljanar tace kinyi kokari.  A haka aka tayi  duk illahirin matan da suke dakin hatta kawayen amarya kowa sai da ya to fa bakin sa ko baka da abun fada sai ka lalibo.  In kaki kuwa sai dai kaga ta zuro hannuta tun daga can sama ta wanke ka da mari. Haleema tun tana dauka har ta kai ga sai dai ta ce "Eh", Kawai ko ta daga ma kai.


Wasa- wasa Dai abu har dare yayi anawa amarya nasiha. Dare nayi lokacin kuwa 'yan daukar amarya suka zo ko ta kan Alhji yayi nasiha ba'a bi ba. aka dauka Kowa na zumudin aka basu amaryar su.mata ko daya ba'a sama wacce ta tafi rakiyar amarya ba. Domin duk wacce ta fito daga cikin gidan. Sai tace "Alhmdulilah". Ta ari ta kare ko mai wai-wayen gidan babu. Haka 'yan matan amarya ma duk wacce ta fito sai ta ruga a guje ta nufi hanyar gidan su. Kamar dawa ki haka mata suka cika layin da guje-guje.  Ganin za'ayi abun kunya ba 'yan rakiyar amarya yasa  mama asiya da umma suka roki su Zuwaira da su taimaka a raka amarya.  Su Fiddausi da su nasmat sune a matsayin kawayen amarya su hudun su kuwa su zuwaira a matsayin manyan mata. A tsorace suka kai amrya gidan ta suna kai ta kuwa kowa sauri yake ya fito. Ganin suna shirin tafiya su kyale ta ita kadai gata itama a tsara ce take. Kuka ta saki ta biyo su tace wallahi sai dai a koma tare baza su barta ita ka dai ba. Ganin da gaske take da kyar Fiddausi ta ce tayi hakuri su zauna har angon ya zo. Nan ma da kyar ta yarda. Su mama asiya ansha bulala duk jiki sai radadi. Ana tafiya a mota sai cewa direba (Driver) yayi sauri take. Kowa a tsora ce yake sai da suka karasa gida tukun hankali ya dan kwanta. Su Juwaira a kujerun fali suka zube kowa najin jiki hade da tsinewa gidan bikin. Nasmat da asmart Dakin su suka nufa domin suyi fitsari dan ya matsi ko wacce a ciki. rige-rige suka fara da gudu wajen shiga dakin. Sai da aka .  kusan zuwa toilet din Nasmat ta tuno da macijin nan na dazu. Birki taja a gurin tayi baya.  Taki fada wa Asmart dan mugunta.  Asmart na bude bayin ta kwala uban ihu! Ta juyo a guje. Nasmat na ganin haka itama sai tace kafa me naci ban baki ba. Da gudu suka fita falo. Su mama asiya na ganin su a wannan hali basu tsaya tambaya ba ko wacce ta tashi a guje aka nufi hanyar fita a............................```



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 37-38



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



🤧 DEDICATED TO YOU,  🤧BIEBOH  habibalo🤧.  2mro is ur bazday



😁 happy birthday to You 😁  Ni ne na farko 🙋🏻‍♂.



*Note* BA SABODA *SURBAJO* KADAI AKAYI WANNAN BA, 👉🏽🎀  DAN HAKA BA KO WANNE NOVEL DA AKAYI AMFANI DA WANNAN 👉🏽🎀 ZAI ZAMA NATA BA. ABUN KAWAI RA'AYI NE KUKAN JAKI. 





*KARSHEN PAGEN BAYA*

 ~Taki fada wa Asmart dan mugunta.  Asmart na bude bayin ta kwala uban ihu! Ta juyo a guje. Nasmat na ganin haka itama sai tace kafa me naci ban baki ba. Da gudu suka fita falo. Su mama asiya na ganin su a wannan hali basu tsaya tambaya ba ko wacce ta tashi a guje aka nufi hanyar fita a.~


»» Su mama asiya Har karo suke yi ita da kishiyoyin ta wajen fita. Har anzo tsakar gida tukun Aamart tace "Nasmat wai miye ake wa gudu?".  Tambayar da sukaji Asamart tayi ne yasa duk suka ja birki suka tsaya. Nasmat cike da mamaki tace "Me kika gani  a bandaki kika yi ihu!?". Kyankyaso na gani mana, Shine na tsorata ke kuma sai naga kin rugo ai na dauka wani abun ne kika gani". Dogon tsaki sukaja kusan tare, kowa na haki tukun suka fara wa junan su dariyan. "Kaga 'yan iskan yara kun tsorata mu ai mun dauka Aljanar ce ai ta biyu mu har gida".  Inji hauwa.  Komawa sukayi cikin gidan gaba dayan su a tsorace suke ga barci ga gajiya amma ba wacce take da karfin halin shiga dakin ta ita kadai. fatima ita kam tuni har tabi lafiyar gado tun shogowar su ta farko.  Suna nan zaune a falo har alhaji ya dawo. Da ya dawo suka tayar mishi da rikici domin ko wacce sai da ya rakata daki sai ta rufa da bargo tukun yake fitowa.  Fiddausi kuwa sai wajen karfe sha daya angon haleema ya zo tukun tace gida zata. Da kyar suka lalaba ta ta yarda zata kwana a dayan dakin sai safe ta tafi.  




Yau kusan kwana Biyar da faruwar hakan, kusan kullum sai Nasmat ta hadawa Asmart tarko domin ta taba Aljanar ko fatima amma har yanzu shiru kake ji.  Abun na matukar cin ran Nasmat domin tasha zuga Asmart ta ci uban fatima ko kuma ta yiwa 'yar babyn wani abu amma ba abunda yake faruwa. Suna zaune a tsakar gidan kan but din motar baban su Fatima ta zo wuce wa Rike da 'yar tsanar ta.  "Ke dan ubanki zo nan".  Cewar Asmart, Fatima ta zo. "Muga 'yar babyn nan kullum kina tare da ita kamar mayya". Fatima bata so ba dan  gudun kar a dake ta, ta mika wa asmart 'yar tsanar. Nasmat a tsorace take tun da Nasmat ta zo shiyasa ma ko uffan bata ce ba, Yanzu ma badan ta so take zaune a gun ba kawai dan mugunta ne, So take kawai asmart ta tsokalo wa kanta.  Asmart na karbar 'yar tsanar ta juya ta ciki da bai, tana kare mata kallo. "Fatima naji ance wai babyn ki na magana ko?".  Cikin fara'a Fatima tace "Eh mana tana cin abinci ma kuma idan aka bige ta ko na barta ita kadai har kuka take yi".  Asmart ko da jin haka sai ta buga 'yar tsanar da kasa da karfi Tum!.  Fatima sai binta kawai tayi da kallo. Asmart ta wani dauke Fatima da mari har sai da ta fadi nan take ta fara kuka. "Shegiya  ma karya ciya kince tana kuka idan an dake ta to yanzu me ya hana tayi kuka?".  Asmart ce ke fadar haka lokacin ta diro daga kan bayar motan.  Taje ta dauki 'baby Doll din ta kama kan ta murda da iya karfin ta, da mugunta so tayi ta cira kan amma yaki cire wa.  Fatima kuwa kuka take tana fadin "Aunty dan Allah karki kashe min babyna".  Nasmat har yanzu zaune take kan mota sai kallan drama take, Cikin ranta farin ciki cike fal! Dariya ce ta mugunta ta kamata lokaci guda ta fara kyal kyalata. Suna hada ido da 'yar tsanar tayi gum baki. Domin gani tayi kamar hararen ta take.



 Asmart kuwa 'yar babyn tayi a kasa ta fara tataka ta tana tsalle tana dira a kanta. "Wato har rai ne da ita da kike cewa karna kashe miki ita kenan, To gashin nan ta mutu".  Wani tsalle da tayi gefan takalminta ya dan Daki gefan gashin kan 'yar robar wanda har wani dan guntun gashin  ya tsinke daga kan.  Fatima na ganin haka ta kara fashewa da kuka. Da sauri taje tana kokarin kwatar 'yar ta tana cewa. "Dan Allah aunty kiyi hakuri kinga har kin fara tsinka mata gashi".   Asmart ta sunkuya ta dauki diyar "Au! Ashe fa gashi gare ta aunty yolash! Kenan, amma fa idan aka dan rage wannan gashin zata fi kyau dan haka bari inje in mata aski".  Tana fadar haka ta nufi falo da gudu Fatima kuwa ta bita tana kuka tana cewa ta bata diyar ta.




Nasmat na ganin haka ta kyalkyale da dariya harda rike ciki tace "Asmart yau zaki ci ubanki, kin dauki ruwan da zai dafa ki".   Haka su asmart suka wuce su mama asiya a falo da gudun tsiya fatima na binta tana kuka. Asmart na shiga dakin tayi sauri ta rufe dakin tana dariya. Fatima nan ta tsaya tana kuka tana faman bu buga kofar.  "Ke fati uwarki nace, ko baki ji ba". Hauwa ce ke maganar. "Kaji 'yar iskar yarinya mutane na zaman su suna hutawa zaki zi ki ishe su da kuka".  "Mama hauwa aunty Asmart ce ta kwace min babyna".  Fatima ta fada tana kara rushewa da kuka.  Afusace hauwa tayi kanta tana mata fada har da duka ta kora ta waje. Asmart na shiga dakin ta wullar da 'yar babyn a kasa hade da taka ta ta nufi wajen kayan kwaliyar su tana neman reza ita da gaske iski zatayi wa 'yar tsanar.   Wani dan tsalle tayi na jin dadin ganin rezar nan fa ta zo ta zauna ta aske wa




 'Yar tsanar kanta tas!.  Tana kallanta ta kyalkyale da dariya, "Amma fa kinyi kyau sosai yar yarinyar fatutu, bari in ma kan nan kiss".  Ta fada cike da zolaya ta manna wa kan 'yar babyn kiss. Uhhhmmahhh, Ai kuwa taji bakinta da kan kamar ansa gam an like. Jatayi da niyar raba bakin ta da kan 'yar babyn ai kuwa yaki rabuwa bakin nata ya manne  Tun tana daukar abun wasa har ta kai ta ga fara kuka tana jan kan ki!ki!-ki!ki!  Amma yaki fita. Hawaye shabe-shabe ta tashi ta nufi kofa tana kuka tayi-tayi ta bude kofa taki buduwa. Ihuu! Ta farayi tana neman dauki amma shiru gidan kamar ba kowa.Hannu tasa ta kama gangar jikin 'yar babyn taja da karfi sai ji tayi ta fizge ta. Ai kuwa ta wullar da ita can jikin bango a tsorace tana mai da nunfashi daya-daya. Fitsarin wuya taji da sauri ta shiga ban daki lokacin taji harda kashi ma.  Tana tsugune ta fara jin wata 'yar siririyar dariya na fitowa daga dakin. tun anayi a hankali har aka fara da karfi abun yayi matukar tsorata ta domin bata san mai kalar dariyar nan ba a gidan. Wani hayaki kuma taga ya fara shigowa ta kasar kofar toilet din. Bata gama ba ta wanke a hankali ta dan bude kofar a tsora ce. Hayaki ne cike da dakin baka iya ganin na gaban ka ga kuma dariyar har yanzu yi ake. Mamaki da tsoro suka kara ziyartar Asmart a lokaci guda. Wajen da take jin dariyar ta nufa tana tafe a hankali duk da ba wani ganin gabanta take sosai ba.  Tana tafiya taji tayi karo da wani abu tana kallan kasa taga wani abu ne lulube da Bakin zani kuma daga ciki dariyar ke fitowa.  Karkarwa ta farayi tana tunanin ta daga ko ta barii.......................


*Kuyi hakuri kadan neee*  



Ni kuwa Idan nice Asmart sai na daga naga ko ma miye. Kai/ke fa???. Lolz



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy













👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 39-40



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽


 *DEDICATED TO YOU, ZAINAB ZEE*


*Hip hip hip hurray, Happy birthday to you*


🍰 *ZAINAB ZEE* 🍰


And 


🍰 *BIEBOH*  🍰


*Ina taya ku murnar zagayowar haihuwar ku. Allah ya karo wasu shekarun masu amfani. Ya yafe zunuban da kukayi a shekarun da suka wuce. Ya kuma linka ladar* 😹 It's you day.




~Tana tafiya taji tayi karo da wani abu tana kallan kasa taga wani abu ne lulube da Bakin zani kuma daga ciki dariyar ke fitowa.  Karkarwa ta farayi tana tunanin ta daga ko ta barii.~


»»Hannu na karkarwa cike da tsoro ta kama dan bak'in mayafin ta fizge karfi. 'Yar babyn ta gani kwance rufda ciki itace mai dariyar.  "Aikin banza ashe wannan abarce ma har na tsorata".  Asmart kafa tasa ta dan buge ta abunda ta gani yasa ta fara ja da baya. Idanun 'yar tsanar ne wani irin bak'in jini ke fita a matsayin hawaye ga wasu manyan hakora da suka zazaro waje wani abu take taunawa tana dariyar kamar danyan nama hakan yasa bakin ta shima yayi ja idanunta kuwa sun koma baki da ja. Sabanin bakin da fari.  Heheheheheheheh, "Baki san nice ba ko?. To da kin dauka wace a ciki?". 'Yar babyn ce take magana cikin wata 'yar siririyar murya. Nan take jikin asmart ya fara rawa saboda tsoro magana na rawa-rawa, "Dan Allah kiyi hakuri ki rabu dani Wallahi bansan ke aljana bace. Wallahi na dauka diyar roba ce".  HahahahHahhha "Wata dariyar mai karfin gaske 'yar robar tayi wacce tasa sai da Asmart ta rufe kunnan ta. "Wato ke azzaluma ko kina zatan zan kyale azzalumai irin ku ne? Muddun da rai! Na da lafiya ta bazan dinga sasauta wa azzalumai irin ku ba. Musamman masu cutar marayu.  Yanzu in kina so in hakura ba abu mai wuya bane kawai zo ki dauke ni ki min wanka ki mayar min da gashi na".  "To, To".  Da sauri asmart ta fada, Lokacin taje da niyar Daukar 'yar babyn amma tayi iya kokarin ta ta raba ta da kasa ma abu ya gagara. Ita kuwa aljanar sai gagaba wata kalar dariya take marar dadin ji. "Oya daga ni mana ko so kike yanzu in fara taba lafiyan jikin ki?". Dan Allah kiyi hakuri *Aljanar fatima,* wallahi nayi-nayi na kasa ne".  Hihihihihihh. "To tunda dai kika ce min Aljnar fatima naji dadi kuma na rage miki aiki amma da ko shekara zamuyi baza ki iya rabani da kasa ba. Yanzu abunda nake so jeki ki tsinto gashina ki zo ki mayar min abuna".






Asmart na karkarwa tace, "To ai dakin duk hayaki ne bana ganin gaba na.  Tana rufe baki hayakin ya dauke gaba daya taga kamar ba'a taba yinsa bama.  Da sauri ta nufi wajen ta fara tsinto gashin da ta aske a kan Aljanar 'yar babyn.  Sai da ta tsinto gaba daya tazo ta mikawa aljanar a tsorace tace "To gashi". "Au! Miko min kawai zakiyi?  Zo ki mayar min kamar yanda kika aske min in kuwa ba haka ba yanzu kiga karshen mugu". Da sauri Asmart ta matsa kusa ta fara kokarin mayar da gashin da ta aske. Daga ta dora sai taga gashin ya fado, aljanar kuwa sai dariya take. Asmart tuni ta gaji, ta kuma gaya wa aljnar itabkuwa tace dole sai ta mayar mata da gashin ta kamar yanda yake a da.  A smart taci gaba. Tana yi ta fashe da kuka da karfi. "Keeeeeeee!!!". Wata muguwar tsawa aljanar tayi wa asmart tana yi kuwa dakin yayi duhu rundum. Asmar bata iya ganin ko tafin hannunta balle aljanar da ke gabanta. A zuciyar ta tace " wannan dama ce ta in tsere dan haka yanzu bari inyi nan nasan ta nan kofar fita take".  A hankali ta tashi kamar barauniya take sanda. Kafarta taji tana takawa kamar a cikin hakukuwa. Abun ya bata mamaki  ta fara zance a zuci, "To me ya kawo wannan hakukuwan cikin daki kuwa?, dakin da ake share wa kullum. Ahhh! Wayyo Allah kafa ta". Asmart tace yayin da taji ta taka wani abu kamar kaya ya kuma shige mata cikin kasa. Dake har yanzu mugun duhun na nan bata san ko me ta taka ba. Kuka ta fara tana Yarfa hannu tama manta da Aljanar. A wajen ta zauna sai lokacin ta tuno da ashe aljana na kusa. Hakan yasa ta rike baki ta gam. Rintse ido tayi hawaye na zubowa ga radadi zafin da take ji.  Bude ido tayi haske fayau sai dai kuma a inda ta tsinci kanta ne abun yayi matukar girgiza ta da bata mamaki. Wani mugun daji mai wasu irin itatuwa wanda bata taba ganin kalarsa ba ko a TV gasu dogaye ga kuma fadi. Duk sunyi inuwa wa waje. Yanayin wajen kadai abun tsoro ne ko kukan tsuntsu babu balle kayi tunanin zaka sama mutum.  Wa-waigawa tayi ko ina iya ganinta bata hangi karshen dajin ba. Kuka ta kara fashewa da shi, domin wannan ba karamin tashin hankali bane a gare ta. Sai yanzu idanta ya kai ga kafarta  da ke zubda jini ashe kaya ce ta taka. Kara rudewa tayi ganin jinin dake zuba hannu ta dora kai ta fashe da kuka tana surutai na neman taima ko daga uwar ta da dangin ta.Da dai taga kukan baya yi. Sai ta fara kokarin cire kayar, daga ta dan sai ta sai ta saki kara, "Wayyo",  Haka dai tatayi. "Kee! me kike a nan". Wata muryar ce katuwa ta fadi hakan, Kamar daga   sama Fatima taji maganar






A firgice ta juya firgigit!. Wasu irin mutane ta gani masu mugun abun tsoro. 'yan kanana ne kamar yaro dan shekara 6 haka. Amma kawunan su a mulmule suke kamar kabewa Gasu manyan  idanunsu kananu 'yan mitsi-mitsi. Ko wanne daga ciki gashi ne buzu-buzu a kan ba tsari.  Asmart ihu ta kurma ta sa hannu ta fizge kayar ta tashi ta ari ta kare.  Su ma kuwa sunkai su goma suka rufa mata baya. Sa'arta  daya basa da gudu domin kan yake rinjayar su. Suta faduwa. Gudu suke cikin wannan kunkurumin daji asmart  duk da tayi musu nisa bata tsayawa wai waye. Sai da tayi gudu sosai tukun ta sama gidin wata bishiya ta jingina tana haki.




Bata fi mintuna biyar ba taji wani irin gurnani a bayanta. A hankali take juyawa a tsorace.  Wata bakar damusa ce mai jajayen ido. Sai bude baki take yi tana lasar harshe. Mugun tsurewa asmart tayi, da baya-baya ta fara tafiya damusar na kara matsota.  Saurin da damusar ta fara ne yasa asmart ta juya ta runtuma a guje tana ihu! Da musar kuwa tace dake aka hada mu. Gudu take iya karfin ta tana waige. Wani makeken gida taga ya bayyana a gabanta. Batayi wani tunani ba ta Afka! Ciki  ta rufo kofar, gida ne makeke mai kayan kwaliya da filawoyi iri-iri sai dai bata ga kowa a cikisa ba. Sannan ba dakuna sai daki daya wani wangame me wanda yake a bude sai wani jan labule dake sanye a kofar dakin shi ya hana aga cikin dakin. Asmart tunani take taje ko kuwa ta tsaya nan. Daga karshe dai ta yanke hukuncin gwara ma taje in ma kashe ta aljanar nan zata yi gwara ta kashe ta ta huta. Gadan gadan ta nufi dakin ta yace labule cike da jarumta tana shigewa Kyauren dakin ya rufe gam. Can Asmart ta hango wata mata tsaye Sanye da riga baka doguwa. Gashin kanta dogo ne shine ya barbazu ya hana q ga fuskarta. Cikin Masifa da daga murya Asmart tace "Ke.............



Yaseen na gaji. Kuyi hakuri da wannan.




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 41-42



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



*DEDICATED TO YOU* 😍 👇🏽


*Mzz Dady*


*Rabi'atu Shua'ibu*


*Layuza*


*Phateema*


*Teemah*


*Maimunat (Aunty maimuna)*



*Ummu Azza..*


😍 Thanks d luv an supporting This book❤ Duk masoya na Ana mugun tare 🙋🏻‍♂




 

🎤🎼 *YAU TAMBURAN GIRMA NA BUGA DOMIN MASOYA NA,* ☺


🎤🎼 *INA MASOYA NA?. KU FITO* 👯


🎤🎼 *INA MASOYA NA?. KU FITO* 👯


🎤🎼 *INA MASOYA NA?. KU FITO* 👯


🎤🎼 *INA MUKU FATAN ALKHAIRI,*  👏🏼 *DAN ALLAH MASOYA KUYI HAKURI* ☺



🎤🎼 *INA MUKU FATAN ALKHAIRI,*  👏🏼 *DAN ALLAH MASOYA KUYI HAKURI* ☺



🎤🎼 *INA MUKU FATAN ALKHAIRI,*  👏🏼 *DAN ALLAH MASOYA KUYI HAKURI* ☺



👸🏻🎤 Dan Allah masoya Kuyi hakuri 


🤴🏻🎤 Dan Allah masoya kuyi hakuri.


M INUWA 2 🤡




       *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Gashin kanta dogo ne shine ya barbazu ya hana q ga fuskarta. Cikin Masifa da daga murya Asmart tace "Ke....~

 "Ke wai wace ce, me kika zo yi gidan mu?, Ke wacce irin muguwa ce?". Cikin karfin hali Asmart ke watsawa matar ta tsaye wacce ta tabbatar da itace Aljanar. Duk yanda ta ci cije ta kafe ta cire tsoro. Dariyar da aljanar nan ta bushe da ita sai da ya tsorata Asmart din dan sai da taji kamar ta ruga. "Keeee!". Aljanar ta fada lokacin da ta dago kai da karfi  gashin kanta ne ya wani mi mike tsai-tsaye idanuwanta jajawur Wasu ba kaken abubuwa kamar  tsutsotsin suna yawo a ciki. Fuskar tata a tabe take bakin ya wani jirge share gudu, Hancin ta a wani tabe yake. Idan kawa Aljanar nan kallo guda baza kayi marmarin karawa ba. Ko asmart kauce kai tayi da taga hakan. "Lalai samun waje wato kece yau har kike ce min Muguwa ko Asmart?".  Da wata iriyar murya Aljanar ke magana wacce tasa Asmart cikin tsoro da fargaba. Duk rawar kan da take da farko yanzu ta daina karkarwa ma ta somayi. "Sunana Safuratu Ko kice *ALJANAR FATIMA* ko kadan bani bari ayi zalunci balle ni inyi. Ko da yake inayin zalunci sosai ma amma fa a kan irin ku azzalumai, Yarinya ce 'Yar karama gaba daya kun fita do wai me ta tsare muku miye abun zaluntar ta in baku taimake ta ba marainiya ce fa".  Murya na rawa Asmart ta daga baki da niyar magana. "Baaa.....". Tsawa Aljanar ta daga mata "Me zaki ce min baki da abun cewa Kalmar *YI HAKURI* Kuwa ke ma baki dauke ta a komai ba yayin da kika tashi zaluncin ki, Dan haka nima yanzu dole in zalunce ki ba sani ba sabo".  Aljanar na rufe baki ta nuna Asmart da yatsa. Sai gata tayi sama tana ihu! Tana harbe-harben iska Da kafa. "Hahhhahhhhahhahhahah. Yanzu kuma kinsan me zanyi?, Kasa zan sake ki kanki ya daki Dutsen can ya rabe biyu kinga an rage mugun iri".  A smart ihu! Ta fara tana bada hakuri hade da rantsuwa baza ta kara zaluntar Fatima ba.






Kafin ta rufe baki tuni Aljanar ta sake ta kasa tayo tana ihu!.  Ganin ta kusan zuga kasa gashi saitin dutse ne, Ta rintse idanu ta sadaukar. Ji tayi ta fado a katifar ta. Abunda yayi matukar bata mamaki kenan. Tashi tayi da sauri tana waige-waige cikin dakin abun ya daure mata kai, Tunanin da take wannan mafarki ne ki gaske. Ganin ba kowa a dakin yasa tayi magana a bayyane. "Shegiyar Aljanar muguwa yar...".  Kafin ashar din da tayi niyar fada ya karasa fitowa taji wani abu ya diro a kanta ta baya. Ihu ta fara yi "Wayyo  Allah na na shiga uku na lalace Dan Allah dan annabi kiyi hakuri Wallahi bazan kara ba". Da karfi Asmart din ke magana. 'Yar babyn ce ta diro gabanta. Tana mata dariya.





 Mai wani irin siririn sauti. "Dama zuwa nayi in gaya miki wannan abun da ya faru a tsakanin mu ni dake in kika 'yarda kika fadawa wani Ke ma kinsan sauran". Tana fadar haka ta bace bat!. Asmart na ganin haka ta Tashi ta fito da gudun tsiya daga dakin. Nasmat na zaune a Falo ita da Ameerah suna kallo sukaga Asmart ta wuce a guje tayi waje. Nasmat ta tashi ta bita a guje tana wai-wayen  kofar dakin. Haka ameera ma ta biyo su. A tsakar gida Asmart ta tsaya tana Maida nunfashi. "Ke uban miye kika wani rugo da gudu. Kin tsorata mutane".  "Kyankyaso ne". Asmart tace wa Ameera. "Asmart Wallahi in kika kara mana wannan iskancin san naci ubanki. Ya zaki ringa fitgita mutane?.





Ameera na fadar haka ta juya ta koma ciki. Asmart tsuke baki tayi tana kwaikwayan maganar Ameera din. Nasmat ce ta Dan dake ta. "Ke gaya min me akayi ni dai nasan yanzu ba kyankyaso bane. Tunda naga baki fito da 'yar babyn ba".  Wata muguwar harara asmart  ta dakawa Nasmat. "Yar banza ni ai ba ruwa na dake ke dama ashe kinsan abunda ake ciki shine kika min shiru inawa aljanar tambada. Waii!! Ai yau naga ta kai na. Al'quran har na fidda rai!".  Labarin  abunda ya faru da ita taba wa Nasmat tace harda targa de. Sai dai tana duba wa kuma taga babu. Abun ya bata mamaki matuka. Nasmat ce ta fara gagaba dariya mai makwan taji tausayi dariya harda rike ciki. Sai da taba wa Asmart haushi ta cika tayi fam! Kamar wacce zata fashe tsabar zuciya. Sai da Nasmat tayi dariya mai isarta tukun ta tsagaita ta bawa Asmart labarin abunda ya faru da ita ranar Biki ta kara da cewa "Zuwan da nayi Gidan bikin ba dan Allah bane Aljanar ce ta tilasta ni tasa nayi mata wanka harda kwaliya". Hahahhahhahahhaha Asmart ta fara gagaba dariya ta rike ciki. Nasmat ta bata rai "Bansan iskanci fa Asmart kinsan dai ni yayarki ce".  Hhahahhahh "Sorry ni kinsan abunda ya bani dariya ma wau da Kika mari fatima kan ya guntule kuma ta dauko ta biyo ki da shi zan so inga ya kika yi a lokacin.





 "Nasmat ta danyi murmushi Sannan tace "Hmm ai ranar naga tashin hankali wallahi.  Kai a yanke fa ya biyo ni yana magana".   Asamrt tace "Ai kinyi kokari da nice da suma zanyi a gun". Yatsa Asmart ta dora a kan habarta alamun tana tunani. Can kuma sai tace "Nasmat ni kuwa inaga mun sama hanyar da zamu ringa yin mugunta a sauka ke". "Ban gane ba me kike nufi?".




"Yanzu zan fahimtar dake, Sa nin kanki ne gaba daya mutanan gidan nan mugaye ne ga Fatima, abu kada take musu su hauta da duka ko Zagi. To kinga kuma a yanzu daga an taba ta aljanar  ke rama mata".  Tsallan murna da jin dadi Nasmat tayi"Shegiya Asmart kanki yana ja sosai. Kinma san me na tuno da kika fadi wannan maganar. Wallahi sai na tuno malamin islamiyyar mu shi ya kamata mu danawa bomb".  Hahhahaha "Kyale mugu Ai mu shikenan mun sama hanyar mugunta kum....".  Fatima ce ta Rugo da  gudu hannunta rike da 'yar baby, ta nufo su tana cewa "Aunty 'Ya ta na kuka wai madaya take so". Su kuwa suna ganin ta suka yi waje da gudu..

_____________________


Kullum tunanin su Nasmat a kan yanda zasuyi su hada malamin su da Aljana ne. Yau ma zaune suke su biyu  a falo asmart ce tace. "Ni Wallahi bana so mu fara yin muguntar nan a kan kowa sai malam, Wai shi mugu zai ga mugunta ai. Yanzu dai hanyar da zamu bi dan mu hada su fada ya kamata mu nema".   Nasmat tayi tsaki, "Ni fa tsoro ma nake aje yafi karfin ta kinsan fa duk karfin aljani malami in dai mai tsoran Allah ne sai yaci ubansa".  Hahhaha Asmart tayi dariya "To ai kinji yanda kika ce in mai tsorab Allah ne, kin manta irin zaluncin Malam habib Jifa dan yana san wannan tsigai din duk wanda ya ko harare ta ne sai ya dake sa. Wani lokacin ma fa ba'ayi mata komai ba sai ta hada mutum da malam dan mugunta".  Nasmat tace "Zainab  ba, Ai ni haushin ta nake ji Allah yasa Aljanar ta hada har ita yanda take 'yar siririyar nan kuwa zatayi gudu". Dariya suka yi gaba daya. Suna cikin dariyar sai ga Ameera ta shigo hannunta rike da leda baka. A yangace ta zo ta zauna a gefe daya ko kallansu batayi ba. Su kuwa tun da ta shigo ledar suke kallo sun san saurayin ta ne ya kawo mata wani abun.






 Tana bude ledar kamshin soyayar Kaza ya daki hancin su kamar wanda aka kira suka zo suka zauna a gefanta suna Lasar harshe kamar mayu.   Kaza ce dankwaleliya da Robar Madara katuwa mai sanyi. 😒 Muguwar harara   Ameera ta wulla musu hade da tsawa. "Nasmat Asmart ku kiyaye ni Wallahi zanci uban yarinya. Kaji yara kamar mayu daga ganin abu sai ku wani taso kamar an kira ku".  "Haba auntynmu ai gani mukayi kayan Allah na Annabi ne". Cewar nasamt  "Kaji uwar iyayi wato duk zaman mu dake ban isa a ce min aunty ba sai yau dan an ganni da dan abu na ko. To wallahi ba wanda zan bawa". Zumbur Asmart tace "al'quran sai munci".



"Sai kunci saiku.....".  Ameera jin wayar ta na kara ta tsaya da maganar da ta dauko, Ta kara wayar a kunne. "Hello Habibina, Ok in fita?. To gani nan. (Just 5mints). Tana fadar haka ta tatara kayanta ta tashi cike da zumudi ta nufi dakin su. Kallo kawai su Nasmat suka bita da shi.  Tana shiga dakin taga Fatima a kwance rungume da 'yar ta sai barci take. Da har tayi niyar tayar da ita kuma sai ta fasa a cewar ta idan ta tashe ta Fatima ma cewa zatayi sai ta bata namanta. Bayan ta tabbatar da ba kowa a dakin su nasmat basu biyo ta ba kuma. Karkashin gado ta  tura ledar ta lulube da bedsheet ta fita da sauri amsa kiran masoyin ta dake kofa yana jira.  Su Asmart kamar jira suke ta fita da gudu har rige-rige suke wajen shiga dakin. Bincike suka farayi da kyar suka gano ledar a karkashin gado. Kamar kazar ta uwarsu ce, Kowa ya ciri cinya daya-daya da sauri suka cinye abu ga marar gaskiya. Yegot din kuwa kowa korba Uku-uku suka yi suka hakura. Dariya Nasmat tayi na mugunta can kuma tace "To yanzu ya zamuyi". Dan jum kadan


Asmart tayi tukun ta kyalkyale da dariya. Nasmat tace "Miye?".  "Kinga kalle ni dai kawai samin ido". Inji Asmart tana fadar haka kuwa ta dauki ledar naman taje ta ajiye a kan gadan Fatima da take ta barci ba ruwantan mai ta goga mata a hannayen ta Sannan ta shafa mata abun madara a baki da kagani kace ita tasha. Tana ganin haka ta...................................




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 43-44



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽



*DEDICATED TO YOU* 😍 👇🏽


*HASSAN ATK TANKO*


*HUSAINI ATK TANKO*


*UMMU BASHIR*


*BEAUTY QUEEN*


*SAMEE KHAIRAH NOVELS*

_Jinku nake a can karkashin Zuciya na_


*PHAREEDA KHAMSHI NOVELS*

_Kuna sani inji kamar ni King din gaske ne_ lolz


*BIGBOY ISAH FANS*

_Kukan na daban ne banda kalaman da zan yabe ko ko gode muku sai dai ince. Allah ya saka muku Allah ya barmu tare_


*KINGBOY ISAH NOVELS*

_Kun riga da kun zama 'yan uwa na jinku nake kusa da Raina. Auntys da sisters king dai na ji daku Allah ya bar zumunci_


😍 Thanks d luv an supporting This book❤ Duk masoya na Ana mugun tare 🙋🏻‍♂




 *KARSHEN PAGEN BAYA*

~"Kinga kalle ni dai kawai samin ido". Inji Asmart tana fadar haka kuwa ta dauki ledar naman taje ta ajiye a kan gadan Fatima da take ta barci ba ruwantan mai ta goga mata a hannayen ta Sannan ta shafa mata abun madara a baki da kagani kace ita tasha. Tana ganin haka ta.~


»»Kara bushewa da dariya. Da sauri suka fita daga dakin suka koma falo suka zauna suka ci gaba da tadin su kamar basuje ko'ina ba.  Ameera na dawowa dakin ta shiga a bakin kofa tayi birki tana kallan kan gadan Fatima.  Murje idanu tayi domin ta tabbatar da abunda idan nata ke hangowa gaskiya ne ko kuwa.  "Kutu...". ta kawo ashar ta maka yayin da ta nufi wajen Fatima din a masifance. Dim! Dim!  Ta hau ta da kulli baji ba gani, bata ma da kuka ta farka bata sana hawa ba batasan sauka ba sai duka kawai da taji. "Wallahi, yau sai naci ubanki a gidan nan wato har ni zan ajiye abu ke munafuka ki dauko ki ci min".  'Yar babyn ta dauka tayi tulli da ita a bango sannan ta kama Fatima da hannu biyu  ta daga chamak!. A falo ta dire ta ta dauki wayar charger ta fara bulala ta.  Kuka sosai Fatima tak tana fadin "Aunty me nayi miki?, me nayi miki?".  Ita kuwa baji ba gani kawai dukanta take, Fiddausi na kitchen tana jin kukan Fatima ta fito a guje tana zuwa kuwa ta dauke Ameera da mari. Dafe inda aka mare ta din tayi "Kanbuh!  Ni kika mara".  "An mare ki azzaluma kawai so kike ki kashe wannan yarinyar ne ko dan kinga bata da mai rama mata ne".  Safuratu dake gefe wadda su basa ganin ta tace, "Ga mai rama mata nan kuwa".  kukan kura Ameera tayi ta cakumi wuyan Fiddausi nan itama kuwa ta kamata suka fara kunce da da naushin juna. Can Allah bawa Fiddausi sa'a ta wulla Ameeera da kadan ta fada kan Asmart  t goce tana dariya. Ameera a fusace ta taso ido cike da kwalla ta kara kama Fiddausi. Su Nasmat kam gefe suka koma suna ta kyalkyala dariya suna kuma kara zugawa. Karar dariyar su ce ta fito da mutanan gidan. Fitowar mama asiya tayi dai-dai da kwada Ameera da kasa a karo na biyu. Da gudu ta rugo tubur-tubur tana zuwa kuwa ta nufi Fiddausi ta dauke ta da mari.




Kaji 'yar iskan yarinya mutuniyar banza kawai, kashe ta zakiyi sanin kanki ne kin fita karfi amma ki ke mata irin wannan kadi?". "Ai in ban kashe taba ita zata  Fatima". Inji Fiddausi ta fadi tana kara murtuke fuska.  Mama asiya ta rike baki cike da mamaki "Innalilahi, Wai dama saboda wannan mayyar yarinyar ne kike nema ki kashe 'yar uwarki. To Wallahi bari kiji daga yau Sai yau kar in sake ganin kunyi fada da 'yar uwarki a kan Waccan tsinanar Fatimar ko kashe ta zata yi ba ruwanki to ta mutu mana miye amfanin ta dama".  Fiddausi hararen Ameera tayi da take gefe ido ya kawo kwalla. "Chabb! Wallahi bazai yuyu ba. Taya ina kallo za'ayi zalunci a gaba na Wallahi ko yanzu ta dake ta sai na rama mata. A'ah a kan me".  "Haka kika ce, Haka kika ce. Wai ni kam Fiddausi yaushe kika zama marar kunya fitsara ra haka ne. Wai yau har ni kike kallo idona kina mayar min da magana san ranki?".  Duk abunda ake Su Zuwaira gefe kallo kawai suke ba wanda yayi magana a cikin su. Mama asiya ta kama hannu Ameera ta tura ta. "Je ki daki Fatima muga a gaba na zata rama mata din ne?".  Ameera kuwa ba kunya ta nufi gurin Fatima da sauri da nufin Fatima ta wanke ta da mari da juyowar ta kuwa Fiddausi ta dauke ta itama da mari mama asiya ce ta nufo ta da sauri da nufin ta dake ta. Da sauri zuwaira ta shiga tsakanin su. "A'a Wallahi bazaki dakar min 'ya ba haka kawai. Ai idan ki zo bincike ya kamata ki fara yi ba zartar da hukunci ba".





Mama Asiya tace "Au! Ni zaki wa gorin 'ya zuwaira, To naji malama bari inyi bincike kamar yanda kike so. Amma fa in aka kama Fatima ce da laifi yau ba mai kwatar ta a gidan nan ni da kaina zan ci uwarta". Ta kalli Ameera  tace "Ke gaya mana me Fatima tayi miki, Duk da dai nasan kece mai gaskiya amma tunda Su malama Bincikatu ansa mu ai dole muyi bincike".  A shagwabe Ameera ta fara magana "Mama wai fa habib ne ya kawo min Kaza da yegot Nazo na zauna kafin in fara ci shine ya kira ni.To dan kar in barwa wadan can jarababun su cinye min shine na tashi naje na kai karkashin gado ashe Fatima na jina shine tayi kamar barci take sai da taga na fita ta dauki ta cinye min cinya biyu Yegot din ma ta kusa shanye wa bari kiga sauran da ta bari". Tana fadar haka ta Nufi daki da sauri domin ta dauko. "To kinji ko?, Kinji ai ke mai Fatima to kinji munafurcin da tayi ko har yanzu kina goyan bayanta?, Bari ta zo da kazar Ai Kinga sai ki biyata tunda har kinda Karfin halin rama mata in an dake ai bazaki Rasa zuciyar biya ba in tayi barna".  Mama asiya ce ke kallan Fiddausi tana fadar haka. Fiddausi kam bata ce komai ba amma a zuciyar ta tana shakkar maganganun Ameera. Asmart Rai a bace ta dan matsa wajen kunnan  Nasamat tace "Assha abu ya baci fada ya tsaya a kan mutane ni kuwa Wallahi Aljanar na so taci uban Ameera".   "Ke dai bari ai nima naji haushi Wallahi, Bomb din nan bai tashi a  dai-dai ba".





Ameera na bude kofa taga mage ta kama ledar Kazar da baki ta nufi ban daki da gudu. Ai kuwa ta bita tana "Keeey! Keeey!".  Tana wurwurga hannau alamun korarta take.  Tuni magen ta Shige Toilet din. "Wallahi sai na amso abuna ba bandaki ba ko cikin kashi zaki shiga. Shegiyar mage ko daga ina ma oho".  Ameera ke maganar yayin da ta nufi bandakin da sauri.  Tana bude kofar ta Zura kafa sai ji tayi kamar anja kafar ta fadi kasa sharaf!.  Magen ce tazo tabi ta kanta da gudu har yanzu da ledar a bakinta. "Wash! Wash!". Ameera ta fada ta kuma tashi cikin karfin hali ta bi magen dake taga karkashin gadan Su Nasmat ta shiga. Zuwa tayi ta durkusa ta tura kai Tana lekawa. Magen taji ta kama hancin ta. Wani mugun ihu!  Ameerar tayi. Dan ji tayi kamar zata cire mata hanci  da sauri ta fiddo kanta tana laluba hancin ko jini ya fito. Sai da taga babu tukun ta dan sama natsuwa. Kamar daga sama sai jin magen tayi ta duro a kanta ta fara yakushin ta tana karta mata farce a ko'ina Ihu! Ta fara tana faman kaka be ta. Can Allah ya bata sa'a ta yi wurgi da magen. Magen na zuwa kasa sai kuma ta mike da kafa biyu ta fara tafiya irin ta mutana. Murmushi magen ta nufo Ameera tana yi "Kawata ni zaki di ga yiwa iyen wannan?. Ce kace dai baki shan ko ni wacece ba ni ce fa". Magen ke magana wa Ameera maganar irin ta yara. Karkarwa Ameera ta fara. Mugun tsoro ne ya kamata nan take ta fara kuka domin tama rasa abunda zatayi.





Durkushe wa tayi kasa tana bada hakuri hade da cewa magen tayi mata rai!.  Wata 'yar siririyar dariya magen tayi lokacin da ta zo tana zagaya Ameera da kafafunta biyu biyun kuwa tana jujuya su kamar hannu.  "Haba kawata ni fa ba abunda zan miki ko baki gani ni ba ni ce fa".  Aljanar ta fadi haka lokaci da ta tsaya a gaban ameera ta tsura mata idanu da suka juye suka koma Ja Blue. Ameera kallo daya tayi mata ta kara tsoracewa. Domin ko a tarihi bata taba jin mage mai (blue eyes) ba, wannan  ya tabbatar mata da cewa aljana ce. "Dan Allah kiyi min rai!. Me nayi miki dan Allah me na tsare miki idan naman kike so ki dauka Wallahi na yafe miki, kuma Wallahi nayi alkawarin zan sayo miki rago dan Allah amma ki kyale ni".  Murya na rawa Ameera ke magana haka duk jikinta rawa yake. Magen hannu tasa a bayanta ta fiddo w wani dan  bakin glass (ko daga ina oho) makala shi tayi a fuska. "To shikenan tunda kin tsane ni na tafi bazan kara kawo miki ziyara bama".  Ameera cike da farin ciki tace  "To Mama na Allah ya tsare hanya". Magen ce ta juyo "Au! Na manta ban gaya miki ba na iya kitso ko za'ayi miki?".  Da sauri Ameera ta dago "A'a Wallahi na gode jiya aka min". Ta bude kai "kin gani ma". Ta bude kai kafin ta dago taga ba magen sama ko kasa. Tashi tayi cike da tsoro tana waige-waige a dakin.  Fitsarin tsoro ne yazo. Da sauri ta nufi ban daki dan ta juye shi.  Bude ban dakin tayi hade da ihu!.  Itama ta cikin ihu tayi.  Ameera ce  ba bambanci ko kadan har kayan jikin ta. Baza ka iya banbanta su ba.  Kanta ne ya shiga juyawa hannu na karkarwa ta nuna ta cikin da dan yatsa "Ke wace ce ke mai kama dani. Ko Aljana ce?". Ta cikin ce itama ta mai do da shigen tambayar "Wacece ke ko aljana ce?...............................................




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 45-46



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽


*DEDICATED TO YOU QUEEN HAUSY* 😘


Wannan page kyauta na baki, Ina taya ki murnar kammala littafin ki 


💧💦💧💦💦💦💧💦💧💦

*ILLAR BASHI PART 1*

💦💧💦💧💦💧💧💦💦💧


Littafin ya fadakar kuma ya tunatar hade da Tsoratar wa ga masu cin bashi Suki biya. Ina fatan wannan ya zama izina ga masu irin halin Cin bashi Su tuba su Daina In kuwa ba haka ba Suma  Zasu iya ciyo bashin Aljana kamar yanda Yake a littafin😘



Mun gode kwarai da gaske Allah ya saka da Alkhairi Allah kuma ya baki hakuri kici gaba suburbudo mana Littafai. Muna jiran Next 😘







*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Kanta ne ya shiga juyawa hannu na karkarwa ta nuna ta cikin da dan yatsa "Ke wace ce ke mai kama dani. Ko Aljana ce?". Ta cikin ce itama ta mai do da shigen tambayar "Wacece ke ko aljana ce?.~


»»Bangane me kike nufi ba. Ai nice Ameera dama akwai wata Ameera ne mai kama dani komai-da-komai kamai ni?.  "Aljanar ce ta kwada ihu! "Wayyo aljana" Ta nufi kofa a guje da ganin haka itama Ameera ta da sauri.  Mama asiya a tsaye sai fada take kirtawa Fiddausi ba wanda ya kula ta ihu! Suka ringa ji har na mutum biyu ta cikin dakin.  Hakan yasa suka tsare kofa da kallo. Ameera Aljana ce ta fara fitowa a guje tana ihu ta rukunkume Mama asiya da kadan ta kayar da ita. "Miye-miye?". Haka mama Asiya ta fara jero wa Ameera aljana tambaya ita kuwa kofan daki take nuna wa tana fadin "Mama Aljana...".  Kafin ta rufe baki sai ga Ameera ta Asali ta fito daga daki sautin Muryar ta da kuma ganin ta da akayi shi ya firgita duk  'yan dakin gaba daya akayo waje da gudu. Ameera kuka ta fashe da shi ta bisu a guje tana fadin "Mama ni ce fa wannan ce aljanar".  Mai gadi na dakinsa da jin ihun jama'ar gida da sauri ya dauko Adda ya fito ya nufe su yana kiran  "Mine ne-Mine ne?.  Nasmat da Asmart sune gaba wajen gudu da su ya fara cin karo basu tsagaita da gudun ba suka bashi amsa "Aljana ce". Da fadar haka ya buga ta kobi a kasa tayi dan kara cike da kuri yace. "Kul!-Ubanta Aljanar".  Ya nufi falo a guje Ya kusan isa kofar falo kenan sai ga Ameera ta  fito da ganinta yaja wani uban burki ya fadi kasa a tsora ce domin yaga Ameera a cikin 'yan gudu




"Dan Allah Aljana kiyi hakuri ki rufa min asiri na tuba bazan kara ba. Duk abunda na fada Wallahi cika baki ne  ban dauka da gaske Aljanar bace". Da sauri Mai gadin ke fadar haka yana jan kugu yana da baya-da baya,  Hannu Ameera ta mika mishi "Mai gadi Wallahi nice Ameera. waccan ce Aljanar Wallahi taba ni ka gani".  Ai kafin hannuta ya karaso gare shi tuni yayi wani irin juyi Ya tashi ya zabga a guje. Duk uban gudun da su Nasmat suke yi sai da mai gadi y tarar da su har ya wuce su, Bai bi ta kan bude gate ba domin gani yake kamar bata lokaci ne Ta kan Gate din ya haura su Nasmat lokacin suka karaso ganin sunja gate din a kulle yasa suka fara kokarin hawa ta gate  suma.  Tuni Suka haye Su juwaira mama asiya da hauwa Duk sun tsure Ga Nin Ameera ta nufo su Tana fadar "mama nice Wallahi ta kusa da ku ce Aljanar". Itama kuma Aljanar abunda take fada kenan cikin tsiwa Kara rikita Su mama asiya take da fadin "Gata nana aljana Aljana". Gaba dayan su rudewa suka yi kowa jikinsa rawa yake. Ganin wannan ba mafita bace Juwaira da Hauwa suka fara kokarin Haurawa ta gate din suma.  Mama asiya dake tasan jikinta yayi nauyi ko gwada wa batayi ba. Sai bada hakuri wa Ameera take.  Juyawa tayi ta kalli su Juwaira da har sun kusa haye wa. Wani mugun bakin ciki ne ya ziyarci zuciyar ta. Domin taga zasu gudu su barta. Kafafuwan su ta kama da nufin itama ta hau kan gate, Abunka da mai jiki tana kamawa kuwa ta rinjayo su. Da nauyinta suka rikito kasa gaba daya. Ameera Aljana ta faki idanunsu ta mayar da hannunta key ta bude gate din Da gudu ta fita tana "kufito karta cinye ku". Tashi sukayi Kamar ba sune suka fado daga sama ba a million suka fito daga gidan Ihu! Suke da karfi suna fadin jama'a Aljana Ita kuwa Ameera bata dai na binsu ba.  Su kuwa su asmart lokacin da suka diro daga gate tuni mai gadi har ya kusan fita daga layin ai kuwa suma suka bishi tuni sun bar layin.




Tafe suke shida amaryarsa A tsakar gida sun nufo wajen mota da alamu fita zaiyi.Dam matashi ne cikin shigar sa ta 'yan sanda ASP Abdul King Article kenan. Ba abunda yake zurarwa amaryar nan sai karya. "Ai in gaya miki Zainab ba karami dace kikayi ba da kika same ni a matsayin miji. Wallahi kin gama dace wa".  "Allah mai gida". Amaryar ta fada cikin mamaki. "Allah kuwa. Ke kinsan irin jarumta ta kuwa?. Duk garin nan magana ta ake duk inda kayi sai dai kaji ana maganar Asp Abdul King Article, Irin barayin da nake kamawa da 'yan iska Allah yayi yawa da su. Ke ni fa ko Aljani yayi sata in dai a yanki na ne ina tabbatar miki kafin Gobe sai na shako shi".  "Kai mai gida Aljani kuma?, Ni fa gaskiya tsoran Aljanu nake yi".  Hahahaha 'yar kuntuwar dariya ya yi "Kamar dai kin manta labarin da na baki ranar nace na kama barawo Aljani kin dauka wasa nake ko?. To ai shekaran jiya ma na kama aljani barawo". Ya fada yana  wulwula yar feston din dake hannun sa.  "Innalilahi, bani labari mai gida". "Wani dan iskan barawo muka kama a Kasuwa ya saci waya ashe   Alja...". Bai karasa maganar ba suka jiyo ihun su mama asiya Ana Aljana-Aljana. Mai gida kamar fa Aljanar nake ji




 Ana fada kuma kamar neman taimako suke".    "Ai na gaya miki da na damki wuyan  barawan nan na fara jibga..." Asp ne yake wannan maganar dan a manta da Zancan. Zainab ta fahimce sa hakan yasa ta takura mishi Sai da ta tursasa shi a kan sai yaje ya gano. Bai so ba cike da tsoro ya nufi gate din tana biye da shi a baya. A hankali ya bude gate din ya dan leka lokacin kuwa yaga su Juwaira a guje sun wuce suna faman ihu ciki har da Ameera ya gani. Juyawa yayi baya dan ganin abunda ke binsu din. Yana ganin wannan ameerar sak! take da ta gaban. Tsoro ne ya kamasa dan yagane alamun wannan ce aljanar. Da karfi ya juya ya banke  Amaryar tasa ta fadi kasa bai bi ta kanta ba ya Ruga daki a guje. Itama kuta tashi ta bishi da gudu. Yana zuwa cikin wardrobe ya shike ya rufe duk da a mats........................



Alqur'an Na gaji 🙊 Dama yau bajin type din nake ba.



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy





👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 47-48



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽


*DEDICATED TO YOU* 😘 ♥♥

Mineert Jibir

Jiddah A Adam

Musa Umar Abdullahi

Bilkisu Yusuf

Ummu Muhsin

Sadiya Bala

Hauwa Agabi

Maryam M Gidado

YearRya Yr Abba

Rabiu Shehu Ps

Jamila Mahmud

Naseer Saleh Babaiye

Sunusi Yusuf Jammo

Yariman Masoya

Maman Kawu

Yusuf Jibril Umar

Aslamiyyat Islam


*HAKIKA KU MASOYA NE. ALLAH YA BAR ZUMUNCI NA KUMA GODE DA ADDU'O'IN KU. HAR KU WANDA BAN AMBATA BA. KUMA RAI NA. A KWANA A TASHI WATA RAN ZAKU GANKU.*


Nasha dariya ba laifi. Saura kuma yanzu zakuyi taku. 




*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Da karfi ya juya ya banke  Amaryar tasa ta fadi kasa bai bi ta kanta ba ya Ruga daki a guje. Itama kuta tashi ta bishi da gudu. Yana zuwa cikin wardrobe ya shike ya rufe duk da a matse yake...~

_»»Haka itama Zainab haka Duk da wajen ya matse su Sai da ta kutsa ta shiga. Shiru suka yi na 'yan mintuna. Zainab tace "Mai gida wai miy...".  Kafin ta rufe baki yasa hannu ya toshe mata baki. Yana cewa. "Kiyi shiru karta jimu". Ciki  rada.  Sun kai kusan mintuna 10 a cikin sunyi mukwai. Tukun can Asp ya dan leko dakin ganin ba komai yasa ya karashe fitowa. Kai gado ya fara yana wash! Wash!. "Mai gida gaya min wai me ya tsorata ka haka ne?. Nayi mamaki abunda ya tsorata ka yanda kake jarumin dan sanda mai fada da Aljanu..." Zainab ce ke maganar kafin ta karashe zancen da ta dako. Asp ya katse mata  "Keee!. Rufa min asiri wane ni fada da Aljani kinga karki jawo min".  "Haba mai gida kamar ba kai ne yanzu ka gama fada ba. Kace kana kama aljanu kana cin...". Nan ma bata karasa zancen ba ya dakatar da ita.   "Zainab nafa ce miki ki raba ni da zancen aljanun nan. Ke inda kinga Aljanun da suka biyu wadancan muta nan da daga nan sai dai a dauko ki kinyi dogon suma. Kai!, Ban karashe tabbatar da jarumta ta ba sai yau".  Asp ya fada yana kallan Zainab dake tsaye bakin ta dauke yake da uwayan tambayoyi. "Bani labari mai gida dama ba Aljana daya bace, ni ji nayi kamar suna fadar Aljana-Aljana".  Asp ya gyara zama tukun yace "Ai in gaya miki ba aljana daya bace. Aljanu ne sunkai dari tun daga farkon layin nan in gaya miki aljanu ne har kofae gida.abunda yasa kuma kika ji su suna fadar Aljana, Ai wata Narkekiyar Aljana ce a gaba. Kingata wata makekiya kamar bishiyar kuka. Idanunta in gaya miki sun kai girman tulu. Ga wasu uwayen hakora Kai fin su da gani sunfi Raiza. Hancin ta kuwa sai a tusa mu mu biyu. Gashi a wani tabe Bama wannan ba wuta ce ke fita ta cikin sa. Kanta kuea wani makeke duk girmansa ba gashi sai wasu kwara uku dogaye wanda suka zubo mata har kusan gwiwa. Gata baki kirin"._






 _Karkarwa Zainab ta farayi domin tuni Tsoro ya kamata. "Innalillahi, Mai gida Wallahi har naji mugun tsoro ya kama ni. Da gaskiyar ka da ni ce na ga wannan mugun abu Wallahi da suma zanyi a gun. Na gode Allah ma da yasa ban gani ba".  Tana fadar haka ta nufi kofar daki ta garkame cike da tsoro ta dawo ta haye kan gado can ta dukun-kune wai ita da gaske tsoro ya kamata.  Dariya yayi, "Hahahhahah kai haba dai Xainab karfa ki bani kunyi. Ba'a san matar dan sanda jarumi irina da tsoro ba, Ai ke baki ma san wani abu ba. In gaya miki lekawar da nayi Wai Aljana nan tayi man nuni da hannu alamun in zo. Ni kuwa naga tama raina min wayo hakan yasa na dalla mata wata muguwar harara irin wacce nake wa kananun aljanu suna zabgawa a guje, nan take itama kannun aljanun da suke tare da ita wajen guda goma suka zube sume.To wai ashe ita har ta ji haushi Nan fa ta fusata   ta nufo ni gadan gadan.  Abunda fa yasa na rugo da gudu kenan._





_"Lalai mai gida kai sadauki ne kuma jarumi. Ai in da ni ce da sai dai a dauko ni a group".  Wani dan kara ne suka ji alamun an dan taba kyaure, Ai kuwa Zainab ta kwadda ihu! Kafin kace kwabo Asp king Abdul tuni har ya haura gado ya Shige blanket. Jin shiru ba abunda ya shigo dakin ne ya sa ya fito nan ya fara kokarin Cire kayan 'yan sanda dake jikinsa. "Yallabai ya naga kana faman cire kaya kai da zaka p

Office?". Zainab ta tambaya, "Amma sai yau na gane bakya kauna ta. In fita wato aljana ta wujijiga ni ko?. To in gaya miki ina nan ba inda zani yaseen yanzu bara in kira Dpo in sheda mishi bani da lafiya"_.    



_Asmart da Nasmat tare da mai gadi ashe da suka sha kwana wani waje suka samu suka boye. A cewar mai gadi "Aljana ta fimu gudu duk gudun mu sai ta kamo mu gwara mu labe kawai ta zo ta wuce".  Ameera aljana ita ce a gaba wajen gudu sai Zuwaira da Hauwa suna biye da ita. Can baya kuwa Mama asiya ce a tubur-tubur Gudun da take yau bata taba yin kalarsa ba. Ameerar gaskiya tana ce mata "mama ki tsaya ni ce".  Duk sanda Ameera ta fadi haka ita kuwa sai taji kamar cewa tayi. Tsaya in yanka ki hakan ke sawa tana kara kaimi  a gudun nata duk da ta gaji.  Ameera Aljana tsakanin kwana-da-kwana ta bace bat!.  Su Zuwaira na shayo kwana suka ga ba mutum. Tsayawa sukayi cik!  Suna haki. Su asmart ne suka fito daga inda suke a boye suka fara Wa su Juwaira tambayoyin "Ina Aljana". Juwaira tace "Bakugwa Ameera ta shayo kwana ba?".  "Ko daya mu bamu ga wata Ameera ba".  Cikin daga murya Hauwa tace "To alqur'an wannan itace Aljanar tunda kuka ga...".  Bata karashe magana ba sai ji tayi anyi ciki da ita. Dake bakin kwana take kuma lokacin su Mama asiya suka karaso a guje.  Sanda suka wuntsula domin da karfi mama Asiya  ta bangaje ta.  Ameera na shayo kwana gaba daya suka yi shirin rugawa. "Ku tsaya- Ku tsaya wallahi ni ce Ameera ta gaban ce Aljana wacce ta fara zuwa".  Tsayawa suka yi a tsorace suna kare mata kallo. Kallan zargin da suke mata yasa ta miko hannun "Ga hannuna wata ta taba ma taji Wallahi ni ce"._




 _Kowa baya-baya ya farayi Hauwa ce ta kama Asmart tana kokarin Turo ta wai ta taba taji. Ita kuwa Asamrt ba abunda take sa kakafe wa tana cijewa, Ihu! Ta fara da taga hauwa ta fara turo ta da karfi ga Ameera na matsowa. "Wayyo Allah uwa ta, wayyo baba wayyo jama'a ku taimako zasu kashe ni".  Asamart ce mai fadar haka da karfi.  Abun ne ya bawa Juwaira haushi Zuwa tayi ta tunkuda Asmart da karfi. Ta fada jikin Ameera ta rungume ta. da ganin haka sai kowa yayi duk sai suka ji dadi sai yanzu suka 'yarda da Ameerar ta gaskiya ce. Nan fa aka fara tafka mahawara wasu na fadin a koma gida wasu na cewa Wallahi ba abunda zai mayar da su. Har yanzu mai gadi Bai fito  ba daga inda yake a Labe domin shi gaba daya kunya ma yake ji. Kamar daga sama suka jiyo maganar alhaji. "Innallilahi Wa'inna illaihir raja'un, Mai zan gani haka".  Alhaji ne ya fadi haka lokacin da yake kokarin fitowa daga mota.  "Me ya faru Asiya nake ganin ko a Waje Cikin ku ba ko mai gyale?". Mama asiya da take a tsugunne dan tsabar gajiya da tayi ta Dago. "Yo alhaji tunda m ma baka ganmu ba zannuwa ba Ai sai ka gode wa Allah. Aljana ce  fa Ta koro mu daga gida".   Alhaji ya bata rai yace "Bana san zancen banza Aljana ko dai tsoran ku. Oya kowa ya shiga mota". Yana fadar haka ya juya ya shiga gidan driver ba yanda suka iya domin sun san halin Alhaji dole suka hakura suka shishiga.   Sai da suka isa kof Alhaji yata oda a nufinsa mai gadi ya zo ya bude. Sai ma lokacin suka tuno da mai gadi. Fiddausi tace "Baba ai harda mai gadin muka gudu tare ma muka buya da shi". Tsaki alhaji yaja kawai ya fito ya bude Gate din da kansa suka shiga. A falo suka tarar da Fatima tana kallon Tv  tana wasa da Babyn ta ba abunda ya dame ta._




 _Su mama Asiya jaraba suka bita da shi wai wata kil ma itace aljanar. Alhaji na shigowa duk sukayi tsi! "Gobe zanyi tafiya wajen wani aiki kuma zanyi kwana biyu can, Yanzu ma shirye-shirye na taho in fara domin Tashin asuba zamuyi. Idan da mai matsala zata iya biyo ni ta fada".  Yana fadar haka ya kama hannun Fatima yaja ta suka nufi sama.     Suna tafiya Mama Asiya tace "Wai baku lura da wani abu kuwa". Gaba daya suka tambaya "Kamar me kenan?".  "Wannan yarinyar ni fa ban yarda da ita ba. Dama ban fada muku mayya bace ai inaga itace ta zama Ameera dan ta tsorata mu domin gaba dayan mu mun tsora ta mun gudu amma ita kungo a kanta".  Wasu basu yarda ba amma dan mugun ta kawai sai suka amince da hakan. "Mama asiya tace amma ku barni da ita ai gobe alhaji zai tafi zata ci uban......................._




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 49-50 



NA.  ✍🏼KING BOY ISAH👑



👉🏽✍🏻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*  ✍🏻👈🏽




DEDICATED TO YOU BLOOD ME 😍😘


*TRIPLE QUNEENS*😉


*QUEEN HAUWA HAUSY* 😘👸🏻


*BEAUTY QUEEN* 💋😍


*QUEEN MARYAM 'YAR MAMAR MU* 😍😘


☺ _→ABUNDA YAKE DAINA, ZANA FITAR NA HUCE TAKAI'CI, SOYAYYAR KU A RAI NA ZANA FADA BAZAN BOYE BA←JINKU NAKE A CAN KARKASHIN ZUCIYAN.   INA SANKU SOSAI IRIN TOTALLY DIN NAN_ 😁


'YAN UKUN ZAMANI KENAN 😉


*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Wasu basu yarda ba amma dan mugun ta kawai sai suka amince da hakan. "Mama asiya tace amma ku barni da ita ai gobe alhaji zai tafi zata ci ubanta…~



_»»Washe gari tun da asuba Alhaji yayi musu bankwana bayan ya bar musu duk abunda zasu buka ta kafin dawowarsa. Mama Asiya kule take da Fatima hakan yasa tun da Asuba taje ta taso ta ta zo ta fara saka ta Aikace-Aikace. Wai sai tayi mopping din gaba daya falo. Har wajen karfe 7  Fatima  na fama amma bata gama  Ba, lokacin Duk matan gidan sun fito domin yin girki. Juwaira da hauwa ne suka taho a jere. Lokacin Fatima na faman goge TV din da ke makale jikin bango sai dadage take yi domin tsawanta bai karasa wa.  Zuwaira ce ta lalabo ta bayanta ta yi  mata wani mugun Dundu kamar wacce ta sama sa'arta. Fatima kuka ta kwalla da karfi. Da fara kukanta hauwa ta Wanka mata mari "Ke rufe mana baki dan uwarki ko in kara miki yanzun nan".  Fatima ba dan taso ta matse bakin ta da hannu kukan na dan fitowa a hankali. "Shegiya kinibabba uwar iyayi, Yau shine zaki tarki wani goge-goge Na karya wato kinga alhaji baya nan dan kinsan yau dakuwa zaki yi a gidan nan shiyasa kika fara aiki tun yanzu ko?". Inji hauwa, Zuwaira tace "Dubi ma duk kin bata wa mutane waje da jurwayi Baki iya komai ba 'yar iska kawai". Kama kunnan Fatima tayi ta murda. "Fada min Uwarwa ta saka ki mopping kika bata mana Falo...".  Maganar Mama Asiya suka ji wacce ta taso yanzu daga barci. "Ni na saka ta domin Yau bata da hutu a gidan nan". Gaba daya suka juya a tare "Au! Aunty babba ke kika saka ta ashe. Af! To ba laifi ai". Lokacin  Mama Asiya ta karaso gurun tana murmushi mugun ta tana kare wa Falon kallo. A zuciya tana cewa "Lalai yarinya kin aikatu". A fili kuwa wata muguwar harara ta daka wa Fatima. "Muna fuka kin wani tsare ni da idanu kamar mayya kina wani kukan karya, Maza wuce kitchen".  Ta Make ta a kai da hannu.  Fatima tana kuka Ta shiga gaba suka bita baya su ukun sai zagin ta suke.  Da aka shiga kitchen Fatima ta aikatu sosai. Domin wani abun ma yafi karfin ta kawai saka ta suke. Su ukun ma sun wa aikin yawa amma dan mugunta suka ki barin Fatima ta tafi ta huta.  Yau dan wake suke yi da Tea ba'a dauki lokaci ba  aka karasa. Zuwaira ce tace wa Fatima ta Tsiyayo man gyada a galan. Duk da tasan Fatima da kyar take iya karka ta galan din. Fatima ba gardama ta dauki mazubi taje ta fara Kokarin bulbulowa. Wani mai ne dan kadan ya Zuba a kasan mama Asiya na juyowa ta gani. Sai ta hau Fatima da duka da kuma masifa haka suma sauran._




 _Fatima ta sha wuya gashi sun bige ta sun kuma wanata kuka. Hauwa ce tace, "Munafuka wato kin zubar wa da mutane mai salon yayi saurin kare wa ubanki yazo ya kama mana jaraba yace Ban nata sa muke yi ko. To Wallahi bari kiji Duk yau bake ba abinci a gidan nan". Mama Asiya tace "yauwa kinyi min dai-dai Abunda nake shirin yi kenan. Dan ubanki tunda watan azumi ya kusan kamawa ai dole ki fara koyan azumi. Dama azumi ba sahur yafi lada".  Da fadar haka suka bushe da dariyar mugun ta harda tafa hannuwa.  Fatima kuwa kuka ta saka domin tasan halin su in suka tashi mugun tarsu har fiye da haka yi mata suke. Aljana Safuratu dake tsaye Tana kallan su duk abunda suke. Itama dariya tayi Tace "Tunda kuka yanke wannan hukuncin. Nima na yanke irinsa a kanku. Ni da ku muga wanda zai cika, Ni nace kune bazaku ci abinci ba sai gobe".  Da fada Haka ta sake fashewa da dariya. Duk abunda take kuwa babu mai jinta kuma babu mai ganinta.  Mama asiya ce ta Juye dan waken a wata katuwar kulu wanda tasan Fatima baza ta iya dauka ba. Amma tace dole sai ta dauka Ta kai dinner room,  Fatima  ba gardama taje aka dora mata a kai tana kuka. Tun a nan ta fara Kokarin faduwa. Badan Mama asiya tayi sauri  rike wa ba da duk ya zube. Ai kuwa zagi suka bita da shi gaba dayan su. "Tsinanna so tayi ta zubar kowa ya rasa, To Allah baiyi ba". Zuwaira ce ke fadar haka. Oya karbi wannan saura kuma suma ki zubar, Wallahi da sai na daure ki a gidan nan na zane ki. Na kuma sa kowa na gidan nan ya miki bulala Goma-Goma". Mama asiya ta fadi haka lokacin da ta Dorawa Fatima wasu uwayen farantai da Cokula ta kai Dinning. Fatima da kyar ta kai su domin sun mata Nauyi Haka ta dawo ta kuma jidar wasu kayan abincin. Sai da aka shirya komai tsabb! Dan wake kusan cike da wani katuwan kula. Ga kuma tea da bread._





_Mama Asiya ce tace wa Fatima taje ta sako kayan islamiyar ta tazo ta tafi makaranta.  To kawai ta fada ta nufi dakin su tana shashekar kuka. Gaba dayan 'yan dakin barci suke sai Asmart da Nasmat Da suke zaune suna tsara wani abun suna dariya da gani kasan ba abun Arziki suke kitsawa ba.  Suna ganin Fatima ta shigo suka taso daga inda suke da sauri suka nufe ta ganin tana shirin kuka kuma fuskarta da gani ta sha uban kuka.Nasmat cike da iyayi ta kama Fatima ta dora ta kan gado ta fara share mata hawaye,  Tana fadin, "'yar kanwata waya taba muna ke ne kika taho kina kuka?".  Tana shashekar kuka tace "Ba su mama asiya bane suka ta saka ni aiki kuma suka ce baza su bani abincin kari ba, Wai sai dai in tafi makaranta a haka".  Asmart cike da tausayawa Tace "Ayya 'yar kanwata yi hakuri bar kuka taso muje in miki wanka Kuma in zaki tafi makarantar ma sai in baki Naira Hamsin ki karya". Cike da zumudi Fatima ta Amsa "Toh Aunty Na na gode".  Tashi tayi Asmart tayo mata wanka nan suka zi su biyun suke yi mata kwalliya.  Ko Fatima kanta da take yarinya abun ya bata mamaki, Sai dai hankalin ta bai ka ta gano akwai wani abu a kasa ba.  Asmart ce tace "Fatima daga yau mun daina dukan ki. Kuma mun daina Zagin ki kinji?". Cike da farin ciki Fatima ta Rungumi Asmart "Na gode aunty amma har 'yar baby nama kun dai na Dokanta ko?". Kamar hadin baki da sauri suka ce "Eh daga yau baza mu kara ko taba ta ba". Suna fadar haka suka kalli juna dariya ce ta kusan Kubuce musu jin Sunyi  magana a tare. Nasmat  ce ta datse dariyar ta kalli Fatima tace, "Wai in tambaye ki, 'yar babyn ki ta iya Karatu?".  'Yar dariya Fatima tayi tace "Sai dai magana ko in dauko ta kiji?". Da sauri Nasamt tace aa ba sai kin dauko ta ba, Abunda nake so dai shine yau mu tafi da ita Islamiyya dan ta koyi karatu, Ai kina so kiji tana yi ko?".  Eh fatima tace. "Yauwa yau da ita zamuje Islamiyya ta koyi karatu Daukko ta in goya miki". Cewar Asmart.  Da sauri Fatima ta dauko kayanta  na islamiyya ta saka. Tukun ta daukko 'yar babyn A tsorace suka goya mata ita._





_Suka saka mata hijab dake hijab din doguwa ce Ta rufe 'yar tsanar ba'a ko ganinta. "Karba kudin, Kije wajen mai.shayin can kice ya baki tea Da bread kinji?. In kinci sai ki tsaya a gun ki jira mu yanzu zamu shirya mu fito kinji?". Fatima tace to ta Nufi hanya ta fita. Da fitar ta su biyun suka fara gagaba dariya. Harda rike ciki Dariyar ce ma ta tashi sauran 'yan uwansu da suke barci. Asmaet ce ta dan tsakaita da dariyar ta kalli Nasmat tace "Kai sister amma kwanyar ki naja  ba lalai ba malam ya tsallake wannan target din gaskiya kin iya mugunta".  Nasmat tace "Kyale dan iska Nasan yanda ya tsani Diyar roba. Ko 'yar karama ce. Balle wannan katotuwar. Nasan sai yayi boll da ita in ma bai ce zai toyata ba. Kinga kuwa ita Aljanar ba kyale sa zata yi ba. Wata kil tun a gaban mu ta fara cin ubansa". Wafa dariyar suka dora da ita.  Hauwa ce ta shigo tayi musu magana tace su fito su ake jira ayi breakfast.  To suka ce tukun suka tayar da sauran. Suka je suka yo brush.  A falo aka  baje kowa yayi Ready Mama Asiya kawai ake jira ta fito. Ba'a jima ba sai gata ta fito. Bayan ta zaun. Kamar yanda aka saba hauwa ce ta tashi da  niyar Zuzubawa kowa, Budewar da zatayi taga kular da ke cike da dan waken a wanke ko alamar lema ma babu balle..............._




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 51-52



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑



💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



*DEDICATED TO YOU MAH BLOOD NASMAT ('YAR MUTAN ARKILLAH, AUNTY AMA. KU KAM NA DABAN NE A GARE NI* 😍😘



😍 *SO AKAN CE HADI NA RABBAH, ZUCIYA KU TAKE YABAWA. NASMAT HAR DA AUNTY AMA,  IN BABU KU SAI DAI A DAKAH GUMBA* 😔 *BAYYANAR SO GA WANDA KAKE SO, YA FI RIBA NI KU NA ZABA* 😘


☺ _KOMAI DADI AI BAYYI ZAMA DA MASOYA BAH. SO YAY MIN RANA DAMA DA BAZARKU NAKE TA RAWA KUMA INA._ ☺ 


_INAI MAKU FATAN ALKHAIRI. DUK ZAMANI WRITERS KU FITO_ 🙋🏻‍♂





*KARSHEN PAGEN BAYA*

~A falo aka  baje kowa yayi Ready Mama Asiya kawai ake jira ta fito. Ba'a jima ba sai gata ta fito. Bayan ta zaun. Kamar yanda aka saba hauwa ce ta tashi da  niyar Zuzubawa kowa, Budewar da zatayi taga kular da ke cike da dan waken a wanke ko alamar lema ma babu balle.~


_»Kular kamas da ita ko alamar dan wake babu, Domin  a bushe ma take,  Sakin baki hauwa tayi tana kallan Su Mama asiya, Ganin kallon yayi yawa asiya tace "Ya dai hauwa lafiya kuwa, Ki zuba mana dan wake mana kowa fa ke yake jira". Karkato mata kullar tayi suka ga kular wayam, "Kutu.... Me zan gani haka?, To ina dan waken  da yake kusan cike da Kula". Asiya ta karbi kular har shinshinawa tayi taji ko alamun dan wake ma babu. "Kutt! To alquran Wannan ba kular da muka zuba dan wake ce ba. Haba kuji fa ko kamshin dan wake babu a ciki". "Tashin hankali gobarar gemu, To waye zaiyi mana wannan aika-aika ina Fatima?".  Zuwaira ke maganar tana kallan su Nasmat da suma sunyi tsuru-tsuru sai kallan iyayen nasu suke. "Fatima ai tun  dazun ta tafi makaranta tace mana kunce yau baza ku bata abinci ba".  Dajin haka gaba daya hankalin Fiddausi ya tashi Ta bata rai "Haba mama yanzu kun kyauta kenan?. Ya zaku kora yarinya da sanyin safiyar nan makaranta ba tare da ta karya ba. alhalin kuma kunsan ba'a taso wa sai Karfe sha biyu ake tasowa".  Gaba dayan su wani mugun kallo suke wa Fiddausin " buhun ubanki Fiddausi ah! Kaji 'yar zamani, Yanzu mu zaki wa wa'azi To abinci dai in gaya miki yau ko kwaya fatima bazata ci ba acikin gidan nan. Bama iya yanzu ba". Cewar Mama asiya, Zuwaira tace 'Kyale 'Yar banza kamar yanda ta tafi da yunwa ke ma haka zaki tafi da ita tunda kinga kular dan waken, Kuma ba mai sani in kuma shiga Kitchen"_





_Gaba daya su Mama asiya ma haka suka fada, "Dan haka kawai Hauwa raba burodin nan kowa ya zuba tea yasha ya hakura".   Tashi tayi ta jawo daya daga cikin maka-makan biredin wajen guda takwas. Wuka tasa ta yanka tsakiyar biredin mamaki ne ya bayyana a fuskarta ta tsaya tana kallan biredin Cikinsa yayi baki kirin wasu 'yan kananan kwaruka ne ma a ciki suke yawo.  "A'a jiya fa aka sayo wannan biredin bai kamata ace ya lalace yau ba". Asiya ce ta taso daga kan kujerar da take a zaune "Lalacewa kuma kamar ya?". Hauwa ta mika mata biredin tagan shi rube, "Ikon Allah, A inaga wannan shine marar kyau din bara muga".  Wani ta dauko ta yanka shima dai haka ba kyau. Gaba daya sai da suka fasa sauran bire din duk Sun lalace daga ciki amma bayan Ko alamar lalacewa babu. Asiya ta hau jaraba. Tana zazagen Gidan biredin.  "Wannan ai rainin hankali ne, da zalunci. Ya zasu bawa mutane Rubaben Bread to Wallahi sai na mayar musu anjima". Tsaki Ameera taja. "Mtseewww! Mun kusan makara ga malamin mu bashi da mutunci  bari mutum ko tea ne ma yasha". Tashi tayi ta dauki kofi ta karkata wani filas nufin ta ta tsiyayi shayi. "Kan uba!". Abunda ta furta kenan. Gaba daya aka juyo aka zuba mata na mujiya. "Wai ku yau kawai so kuke kuyi mana horo da yunwa kenan. Nan ai ruwa ne zallah ko zafi ma babu". Hauwa tace "mu gani" Ta dauki kofin "lah! Wallahi da gaske take ruwa ne zallah  bayan kuma Ni da kai na na zuba tea a cikin nan"._





 _Shiru su mama Asiya suka yi ido kawai suke bin Jama'ar gun da shi. "Mtseew To Wallahi ni dai bazan kuma shiga kitchen a yanzu ba. Haba kamar wata jaka?". Cewar Mama Asiya.  Zuwaira tace "Wallahi ko ni bazan shiga ba".  Fiddausi tace "To mu dai makaranta zamu tafi sai a bamu kudin Break".   Dari bi biyu mama asiya ta bisu da shi. Tace "Kowa yaje ya sayi abunda zai ci mu dai ba wanda zai kara koma wa kitchen".  Watsewa akayi kowa yaje yayi shirin makaranta.   Su mama asiya kuwa mai gadi suka bawa Naira Dubu suka aike shi yaje ya soyo musu Indomie da kwai.  Asmart da nasmat a wajen mai shayi suka tarar da Fatima ita har ta karya Tana zaune tana jiransu. Suma kudi suka bayar aka dafa musu indomie tukun suka nufi makaranta._ 

*______________________*


_Zaune yake yana cin Garau-Garau Yana ci yan girgiza kai daka ganshi kasan yana jin dadin abincin Sai da abincin ya rage baifi Cokali hudu ba ya kare, Mutumin ya Wani murtuke ya bata rai!. "Rafi'at!  Rafi'at!  Rafy!".  Kiran yake kwalla mata da karfi. Ba'a jima ba sai ga wata budurwa ta fito ba laifi tana da kyau dai-dai gwargwado. Gaban shi ta durkushe "Mai gida gani". Mari ya kwada mata wanda har sai da taga Taurari nan fa ta kwada ihu!. "To fa safiyar ai tayi, Ke dai Rafy baki yi dacen miji ba ko kadan Wallahi".  "Wai har yanzu Umar bai dai na dukan Rafy ba". Makwabtan su ne ke wannan Hirar. "Ina fa malam ai kullum sai ya dake ta".  "Ashsha! Kai amma dai Allah ya shiryi Umar, gashi daga kayi masa magana sai ya hau ka da masifa yace Ai ba matar ka bace".  "Ai lamarin sa sai Addu'a, Rafy tana da hakuri"._


_"Cikin bacin Rai da masifa umar yace "Yanzu ke Dan Uwarki kinsan wake bai dawo ba shine zaki kawo min abinci wato inci inshiga mutane Ina tusa ana kallona Ana dariya, Haka kike so ko?".  Ya fada yana kallanta. Cikin kuka tace "Mai gida dan Allah kayi hakuri Wallahi na dauka ya dahu ne".  Cokali ya dauka ya kara cika shi ya kai baki, Sai da ya kusan hade shi gaba daya ya Furzo!. "Kan uba!  Ai banji bama sai yanzu haka kika cika yaji a abincin ashe, Ashe so kike ki kashe ni". Da sauri ya tashi ya nufi daki. Kamar tasan abunda yake shirin yi ta fara fadin "Mai gida dan Allah kayi hakuri bazan kara ba Allah". Fadi take da karfi tana mai-maitawa. Da wani Bakin Belt ya fito yana zuw kuwa ya fara Zane ta. Yana Fadin "Bari ni in illataki kafin ki kashe ni".  Ihu! Take tana bashi hakuri amma shi ko kadan baya da alamar Sasautawa balle ma ya kyale ta. Da dai taga yana neman ya hallaka ta sai ta tashi ta ruga da gudu waje, Domin Tasan ba wani wanda zai kawo dauki. Haka yake in yana bugon ta mace ta zo Kwatar ta har ita yake hadawa ya daka. In kuwa namiji ne ya kore shi._






_Fitar ta tayi dai-dai da isowar su Fatima sai tin gidan. Haka ta fito tana kuka shi kuwa ya biyo ta yana fadi "Oya zo wuce ki koma ciki, Ko kuwa Wallahi yau in farfasa miki jiki". Hakuri kawai take bashi tana karawa. Dake tasan halinsa Ba dan ta so ba ta shige gidan a guje.  Su Asmart kuwa abun ne ya basu mamaki. Nasmat tace "Kuturun uba!. Lalai akwai masu hakuri yo ai ina kamar wannan Wallahi mutumin nan bai isa ya dake ni in kyale sa ba, Wai dan yana aure na, Haba kamar wani ubana".  Dariya Asmart tayi. "Wai ke sai yau kika taba ganin wannan azzalumin kenan. Ranar mu ai har ciki sai da muka shiga ni da Ameera ai kuwa ya biyo mu da kadan y zabga min bulala".  Gaba suka yi Aljana Safuratu kuwa tun da taji zancen su nasmat ta fita daga Jikin 'yar tsana,Tace "wannan matar tana bukatar Taimako na, Kuma zan taimaka mata.  Cikin gidan ta shiga ta iske su ya zaunar da ita yana fadar, "Yi min shiru muna fuka. Yanzu zan fita kuma ga naira Hamsin can a cikin aljihun rigar da na cire ki dauka ki auno shinkafa kiyi Cefani ki dafa min Farar shinkafa da miyar tumatur (Jar miya). Cikin kuka tace "Haba mai gida naira hamsin ai baza ta isa ko cefane ba".  Tsawa ya daka mata hade da daga hannun " Yi min shiru ko in make ki Shegiya ni hka na yi niyar badawa kuma dole kiyi min. Kuma Wallahi idan na dawo na tarar bakiyi ba. Hmm kema kinsan sauran".  Yana gama fadar..........................._



*TABB! LALAI ANYI MUGU A NAN*



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









mu kayi like.


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 


https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 53-54



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑



😒 *YAU SAI INGA WANDA ZAICE NAYI MINTSILI, (KARAMI) PAGE* 🤔


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


_*WANNAN PAGEN DIN NAKU NE*_


✍🏼  *ZAINUDEEN ZAIN* ✍🏼  😘


✍🏼   *SANAH S. MATAZU* ✍🏼😘


✍🏼 *SANAH SHAHADA* ✍🏼 😘

  

✍🏼  *RASH KARDAM* ✍🏼 😘



_Malamai kuma abokai a gare ni. Ubangiji Allah ya albarkaci Rayuwar ku, Yasa ku gama da duniya lafiya. Ku Ukun Allah ya baku mazaje na gari wanda zasu zame muku rahama, wanda zasu zare mayafin bakin cikin ku, su lulube ku da na farin ciki.  Haka kai ma dan uwa Zainudeen, Allah ya baka Salahar mace mai sanka dan Allah mai hakuri da juriya. wacce zata Zame maka haske ta kore duhu a cikin rayuwarku._ 😎 Ameen Allah ya amsa....



*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Yi min shiru ko in make ki Shegiya ni hka na yi niyar badawa kuma dole kiyi min. Kuma Wallahi idan na dawo na tarar bakiyi ba. Hmm kema kinsan sauran".  Yana gama fadar.~


 _≥»Yana gama fadar haka ya juya ya fice daga gidan. Safuratu tsaye tayi tana tunanin ta ina zata fara ji da wannan matsala, Can kuma sai ta bace bat!. Rafy na zauna sai kuka take abun duniya ya ishe ta ita kam yanzu bata ma san miye abun yi ba. Wata dattijuwa ce tayi salam  Rafy cikin Kuka-kuka ta amsa matar ce ta zo daf! Da ita ta sama waje ta zauna Rafy ba abunda take sai binta da idanu wanda sunyi jawor dan tsabar kuka. Matar ce ta danyi gyaran murya tukun ta kalli Rafy cike da tausayawa "Rafy Nasan kina cikin matsanan  matsanan ciyar damuwa, Naji labari kullum wannan mugun mijin naki sai ya dake to dan haka ne ma..."  Da sauri Rafy ta daga mata hannu  "Dakata baiwar Allah naji na gode da tausayawa amma ba ruwan ki wannan Kaddarar rayuwa ta ne, Dan haka dan Allah tashi ki tafi abunki". Matar ta dan muskuta kadan tace, "Haba Rafy ki saurare ni mana ni taimakon ki zan...". CikinTsiwa Rafy tace "Dakata malama nace bana bukata ki tashi ki tafi abunki, Wai ke din wace ce me ruwanki". Rafy ganin matar na neman dauko wani sabon zance ta tashi ta kama hannunta ta jata har waje tana cewa. "Naji na gode da shawara".  Tana tura matar waje ta garkame gidan da sakata sama da kasa. Juyowa tayi da wani kukan na Takai'ci A zuciya cewa take "Ba taimakon bane bana so. Amma Nasan bazaki iya taimaka min da komai ba".   Daga bayanta taji maganar matar tace "Rafy kiyi hakuri amma fa ni bazan bar gidan nan ba sai na taimaka miki"._





 _Rafy na juwa taga Wannan matar ce sai ta kwada ihu! Ta ruga daki a guje nan ma ta rufo dakin._  

*__________________*


_Su mama Asiya ne zaune a falo har wajen goma da rabi basu karya ba suna jiran Mai gadi har yanzu bai dawo ba. Mtseeww Mama Asiya tayi tsaki, "Wannan mai gadin sai naci ubansa in yazo Wallahi. Haba wannan ai iskanci ne. Ya zai barmu ko kari babu ya tafi uzurinsa". Tana rufe baki sai gashi ya shigo da sallamar sa.  Mama Asiya kular take kallo tana mata  fassarori Iri-iri kamar da abu ciki kamar babu.  Yana karasowa ya ajiye kular a kasa ta saki sauti Kwangal! Daga ji kasan ba komai a ciki, Gaba daya binsa suke da mugun kallo, Jira suke kawai yace bai samo ba su bal-bale shi da masifa. "Hajiya Wallahi matsala aka samu wajen Mai shaye Biyar naje Duk inda naje sai in samu indomie din ta kare". Zuwaira tace "Kuturun uba!, Amma wallahu kayi mugun rai na mana wayo Akwai mai shayin da za'a je gunsa A rasa Indomie ne?"._





 _Haba kyale shi Zuwaira, Inaga dai Wa'adin zamansa a gidan nan ne ya cika. Amma in ba iskanci da rainin wayo ba ya za'ayi ace kamar mu mu aike ka ka dawo mana da kula wai babu".  Mai gadi ganin Aikin sa ya fara tangal-tangal yasa shi fara bada hakuri. Yana cewa "Dan Allah kuyi hakuri karku min sanadin aiki na Wallahi in kuna ma so yanzu sai inje in sayo in dafa muku".    "Kutumelesi Dallah tashi ka bace mana karka fusata ni yanzu in sallame ka a aiki, Dan ma ka raina mana wayo mune zaka yiwa girki?".  Tashi yayi ya fita da sauri ya barsu nan suna tsaki.  Hauwa ta kalle su "Ni fa Wallahi bazan iya wannan abun ba, wannan ai cutar kai ce kawai ku tashi muje mu dafa ko indomie ce".  Zuwaira tace "Sai dai in ke zaki yi taimako ki dafo min ki kawo min. Amma ni tunda nace bazan shiga kitchen ba to bazan shiga ba sai rana tayi".  Mama asiya tace "Wallahi ko ni bazan shiga ba sai dai ki taimaka ki daho ki kawo mana".   Mikewa Hauwa tayi zumbur! "Kuturun kare, To alqur'an ba wacce zanje inyi aiki in dafa abu in kawo mata tana nan ta Mimike kafafu a falo tana shakar AC".  Mama Asiya ta tashi tana nuna Hauwa da yatsa "Ke karki kuskura, Wallahi karki kuskura ki zage ni".   "Ni kam ban zagi wata ba amma dai maganar abinci nace bazan daho in kawowa wani ba". Tana fadar haka ta wuce ta nufi kitchen._






 _Inda suke ajiye kayan abinci ta shiga. Tsaye tayi tana kallan dan Sito (store ) Taga wayam ko Kangon buhu babu balle ma asama mai wani abu a ciki. Haka ma kwalilikan indomie babu ko daya. Tsawa tayi cik! A wajen tama rasa abunyi. "Aunty Asiya!, Aunty Asiya!".  Tun daga can take kwalla kira Asiya na jinta amma tayi kunnan uwar shegu, ta kyale ta. Sai da ta gaji da kwalla kiran tukun ta fito ta gayawa su mama Asiya abunda ke faruwa. Tubur-tubur ta tashi da sauri ita da zuwairar suka nufi kitchen din hauwa na biye da su.  Tsaye sukayi suna kallan Store din suna kallan juna._ 

*_______________*

_Rafy na daki duk tsoro ya kamata kallan kofar kawai take.  Mace ta gani ta ratso ta cikin kofar, Wani mugun kara tayi a tsorace ta haye kan gado ta wani kudun-dune cikin blanket. "Sunana Safuratu  ni aljana ce amma ba muguwa bace ni. Dan ni nama tsani mugu, Naga mijin ki kuwa mugu ne shiyasa ma nazo dan in taimake ki. Dan haka ki saki jikin ki karkiji tsoro na".  A hankali ta dago tana hada ido da Matar kuma sai ta kara shigar da kanta cikin bargon. Tana magana cikin tsoro, "Dan Allah kiyi hakuri ki tafi na gode amma mijina ba mugu bane dazun ma laifi nayi masa shiyasa ma ya dake n...."  Kafin ta rufe baki Aljanar ta daka mata Tsawa wanda sai da ya rikita ta gaba daya. "Bana san iskanci fa, Wato dan kinga ina lalabaki shine kike min wannan kafiyar Yanzun nan zan mayar dake kaza kuma in kashe mijin naki in baki bani hadin kai nayi abunda ya kawo ni Salun alun ba".  Dajin haka Rafy tayi sauri ta fito. "Dan Allah kiyi hakuri karki mai dani kaza Wallahi zanyi duk yanda kika ce Aljana".  Aljanar ta dan matsa kusa da ita ta zauna. Rafy duk a tsorace take. "To da dai yafi, Kuma ina so ki saki jikin ki ki kaddara a ranki Kamar da mace 'yar uwarki kike magana Ba Aljana ba.  Yanzu fara bani tarihin rayuwar Auren ku shin baya sanki ne Yake miki irin wannaj duka ko kuwa?".   Hawaye ne yq fara Go slow daya bayan daya a idanunta kafin tayi magana cikin kuka._






 *A social net muka hadu da Umar har soyayyar mu ta zama ta zahiri Domin dan anguwar mu ne ban sani ba sai daga baya. muna san juna sosai. Nida umar matsalan da aka samu shine Iyayena masu kudi ne Shi kuwa umar Okada yake da shi yake ciyar da iyayesa ma. Bayan nayi candy sai baba na yace aure zaiyi min kuma auren gida. Wato da dan yayan shi zai hada ni. Ni kuwa na nuna rashin amincewa ta nace umar nake so. Yayan baban nawa dake shi ya kawo shawarar a hadani da dan nasa da yaji nace umar nake so sai ya hakura ya janye. Yace ba laifina bane tunda ba'a tambaye ni wanda nake so ba. Mahaifina kuwa gaba daya ya kasa fahimta. Daga karshe ma cewa yayi zaiyi min Aure da Umar din kuma zai min duk abunda uba kewa 'yarsa amma idan wata matsala ta biyo baya kar in ko nufi hanyar gidansa. Haka na amince domin ji nake bazan iya rayuwa da kowa wanne namiji in ba Umar ba. Haka aka daura auren mahaifina duk a fusace yake dani ko hudubar kirki baiyi min ba. Wannan gidan umar ya kama mana haya muna zaune lafiya lau ba wata matsala kullum sai farantawa juna rai. na tsawan wata biyu, A cikin wata na uku umar ya bullo da wani sabon tsari wanda gaba daya ban sanshi da shi ba. Yau wata na biyu kenan Kusan kullum sai umar ya dake ni. Ba fira mai dadi irin ta ma'aurata. Na kai kararsa gurin iyayensa Suka kira shi a gabana suka mishi tatas, Suka mai fada sosai a nan yace bazai kara ba. Ranar da muka dawo gida Kashe ni ne kawai umar baiyi ba.  Gida kuwa sau daya naje da suna yaji Babana ya koro ni yace ma karya kara ganin kafata a gidansa duk abunda ya faru dani ba ruwansa wai ni naja wa kai na. Ranar da Umar yake jin mugunta yasan bani da kudi kuma yasan babu mai bani haka zai dauki Kudi kalilan kamar yanda yayi yau. Yace in mishi wani abincin mai tsada wanda yasan kudin da ya bani bazasu yi ba. Idan ya dawo ya iske banyi ba haka zai same ni yata maka kamar jaka.  Nayi kuka na zubda hawaye a kullum kuma addu'a nake Allah ya kawo min mafita Ni kam ba kudi nake so ba. Farin ciki da soyayyar da Umar ke min a da su nake bukata su dawo.*





_Safuratu tayi ajiyar zuciya tukun ta dafa Rafy tace, "Allah sarki haka rayuwar take, wani sai kayi masa tuwan shinkafa idan ya tashi sai kaga ya biya ka da bak'in kanzo. Ina so in miki Albishir da cewa Allah ya amsa addu'ar ki. In sha Allah zan mayar miki da mijin ki kamar da zan sai ta shi. Amma fa sai kin bani hadin kai".   Rafy ta kalle ta cikin kuka, "Me zaki mishi, dan Allah karki taba lafiyarsa Wallahi ina sanshi duk abunda yake min ban taba fatan rabuwa da shi ba. Ni kam fata na a gare shi Allah ya shirya min shi".  Dan murmushi Safuratu tayi, "Karki damu ba abunda zai same shi nayi miki alkawari, Misali yanzu idan umar zaiyi tafiya na kwana biyu haka, Zai iya kai ki gidan ku yq musu bayani kuma su amince?".   Rafy girgiza kai tayi alamun aa. "Sai dai gidan Yayan babana". Aljanar tace "Ok dauko hijab dinki mu tafi can".  Tana fadar haka ta tashi ta fito waje. Ita kuwa Rafy ta yi sauri ta dauko hijab da fitowar ta maimakon ta tarar da Safuratu sai Umar ta iske tsaye cikin manyan kaya ya wani bata rai!.  Durkusawa tayi tana karkarwa dan tsabar tsoransa da take ji. "Me gida sannu da zuwa, yaushe ka dawo".  Cikin fada yace ban sani ba ina abincin da nace kiyi".  In-ina ta farayi "Um um, dama-dama.."  Harara ya wurga mata. "Dama me?, Shin yanzu da kika sako hijab ina zakije?".  Kuka ta fara tana fadin Wallahi ba "Inda zani".   Dariya Umar din ya fara yi ita kuwa ta saki baki tana kallansa cikr da mamaki domin rabun ta da ganin umar na dariya Tun baya da wata biyu.  "Matsoraciya ashe haka kike mugun tsoran Umar din. To ba Umar bane wannan *ALJANAR FATIMA* ce, Nice nayi sufarsa nayi kyau kuwa?"._





 _"Eh kwarai mai gida kayi kyau".  Ta fada da sauri Aljanar ta fahimci har yanzu Rafy bata yarda ba shiyasa ma tayi mata Muryanta, Sai a lokacin Rafy ta yarda ta mike tsaye. "Yanzu zuwa zamuyi in kai ki gidan yayan babanki ince masa zan danyi tafiya ne na kwana biyu, Kuma ba dadi a barki a gida ke daya shiyasa ma na kaiki ce, Ni kuma sai in koma sufarki in dawo nan in saita Umar tukun. Kina ganin yayan babankun zai yarda kuwa?".   "Eh zai yarda". Inji Rafy "Ok to muje".  Fitowa sukayi suka nufi gidan yayan baban nata Safuratu tayi kamar yanda ta tsara suka ci sa'a kuwa ya amince ya karbi Rafi'at.  Safuratu kuwa ta fito ta koma gidan a matsayin Rafy din...._

*________________*


_Su Asmart suna ganin an kusa zuwa makaranta sai suka kunce wa Fatima 'yar babyn daga bayanta suka bata a hannu. Nasmat tace "Yauwa 'yar kanwata kinga daga yau 'yar ki zata iya karatu. Yanzu muna shiga cikin makaranta ki Je ki kaiwa malam ita kice karatu za'a koya mata kinji".  Murmushi Fatima tayi wanda ya fito da gibinta ya kara bayyana kyawanta. "To aunty Nasmat amma Dai A kusa dani zata ringa zama ko?".   Asmart tace "Eh mana ai a ma kan cinyar ki zata ringa yin karatun".  Su nasmat Tare suka shiga makarantar. Suna shiga suka jiyo sautin karatun malam din a Aji na 4. Ajin su kenan Asmart tace, "Yauwa Fatima kinji Malam can a jinmu dan tsaya anan ki bari muna shiga muka zauna sai ki kai mai kinji?.  "To". Fatima tace nan ta sama waje ta dan zauna. Tana wasa da yarta. Su Asmart gaba suka yi suna dariya harda rike ciki. Nasamt cikin dariya tace "Har naga ana yin sama da malam ana bugawa da kasa, domin nasan sai ya daki Fatima ko yayi wa 'yar babyn wani abu".   Asmart tace "wannan ai a zaune take ke dai muyi sauri muje yanzu zaki sha kallo. Bayan sun shiga sun zauna ba'a dade ba sai ga Fatima ta shigo ajin da sallama tana murmushi, hannunta rike da 'yar babyn. Malam ya jawo wata aya yaje rabi kenan ya tsaya cik!  Yana kallan Fatimar.  Haka gaba dayan 'yan aji zurawa Fatima ido suka yi. Wasu suna tausaya mata domin sunsab yau ta banu tunda ta shigo wa da malam har cikin aji da 'yar tsana. Fatima kuwa tafiya ta fara ta nufi ind.……………………………………………………_



😰 *MUGAYE SUN HADA MATA BOMB. ALLAH YASA MA YA TASHI HAR DA SU.••••*



*DOMIN SAMUN FARKON LABARIN DAMA WASU LITTAFAN. SHIGA CIKI BLUE DIN NAN, KA/KI YI LIKE NA PAGE MU, TUKUN KA/KI DUBA KASA.*


*Fb.me//Zamaniwritesassociation*


Ko nan

*Fb.me//Bigboyisahfans*


Autan marubuta nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 55-56



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


😎 *WANGA PAGE SADAUKARWA NE GARE KI AUNTY NA. 'YAR MUTAN KATSINAWA.* 😎


🌹 *FATIMA MAMAN ALI* 🌹




*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Haka gaba dayan 'yan aji zurawa Fatima ido suka yi. Wasu suna tausaya mata domin sunsab yau ta banu tunda ta shigo wa da malam har cikin aji da 'yar tsana. Fatima kuwa tafiya ta fara ta nufi ind.~


_»»Malamin Fatima ta nufa tana murmushi, sai da taje gabansa tukun ta tsayar da 'yar babyn da kafafun ta ta kalli malam da ya murtuke ya bata Rai yake kallanta. "Ina kwana malam, dama 'yar babyn na kawo a ringa koya mata karatu ta iya Surutu karatu ne kawai bata iya ba. Kuma so nake ta ringa yi".  Kafa yasa yayi Ball da 'yar tsanar da karfi ta bigi jikin bango ta fada kasa tum!. A fusace ya juya ya kalli 'yan aji  "Ina nasmat da Asmart?".   Gamu nan suka fada a tsure. "Oya ku fito nan".   Sumi-sumi suka tashi suka je gaban sa suka durkushe.  "Kune manya ku zan wa hukunci domin ita yarinya ce bata san komai ba. Me yasa kuka bar Fatima ta taho makaranta da wannan Tsinannan abun?".  Cikin hadin baki suka ce "Wallahi Malam ba tare muka zo ba".  Karya kuke tare da ita kuka zo mana". Rantse-Rantse suka hau yi wai su alambaran ba tare suka zo da Fatima ba. Da malam yaga suna so su Bata mishi lokaci sai ya juya ya kalli Fatima. "Ke Fatima fada min gaskiya in kuwa kika min karya sai na yanka ki. Tare kuka zo ko A'a?".   Su Nasmat ta kalla ko wacce a cikin su Uwar harara yake Tillo mata hade da gatsina duk dan karta fada.  "Eh Malam wallahi tare muka zo".  A fusace ya juya gare su.  "Da Ni zakuyi wa karya ko Dan uban ku?. To ku jira hukunci kar wacce ta motsa daga nan". Hakuri suka shiga bashi shi kuwa bai ko tsaya sauraren su ba. Ya fita waje bai jima ba ya dawo hannunsa da wuka.  'Yar babyn ya dauka a yaje saitin gaban allo, "Kai ina so duk ku saurare ni, daga yau duk wanda ya sake yin ganganci ya shigo cikin makarantar nan da 'yar tsana, Kai bama a makaranta ba Ko a hanya na hadu da mutum da ita wallahi sai jikinsa ya gaya masa._



 _Ya kalli su Nasmat  tukun yaci gaba da cewa, "Sau nawa ina yi muku bayani ina fada muku Mala'iku na rahama basa zama a wajen da wannan gunkin yake, mu kuwa so muke mu kasance da su a ko da yaushe. Dan haka in kunje gida ku gaya wa babban ku na kwace 'yar babyn Fatima".  Yana gama fadar haka ya sa wuka ya yayanka 'yar tsanar har gida shida. Tukun ya kwashe ta ya fitavda ita ya watsa saman soro. Dadi da farin ciki ne suka ziyarci su Nasmat. "Shikenan malam ya jawo wa kansa yau zai gane kurensa". A cewar Asmart, Nasmat tace "Ke ni fa tsoro nake ya zo ya dake mu wallahi".  Ya daka din mana ai ba komai ni kam bazan ji zafi ba ko ya bige ni domin kuwa nasan shima yau zai bugu kum...".  Bata karashe maganar ba Sai ga malam ya shigo hakan yasa ta garkame bakinta tashi shiru. Yana zuwa kuwa ya dauki bulalar sa sai da yayi musu goma-goma da karfi tukun yace su koma mazaunin su Fatima ma yace ta koma Ajin su. A cikin su Nasmat ba wacce tayi kuka Dan farin ciki ma suke yi wai yau malam ya tabo Alkakai._

*_______________*



 _Umar kuwa yana fitowa daga gidan ya nufi gidan iyayensa ya gaida su dauki mashin dinsa ya fito bai zame a ko'ina ba sai wajen abokinsa mujaheed bayan ya parka mashin Ya sauka fuskarsa dauke da murmushi yaje ya mika mashi hannu suka gaisa shima yana kallansa yana 'yar dariya. "Abokina ashe kana gari shiru kamar kayi tafiya baka ko lekowa mi gaisa kai da kake da mashin".   Umar sai da ya sama waje ya zauna tukun yace, "Haba mujaheed ya za'ayi in ki zuwa gurin ka da gangan, Wallahi kawai ayyukan ne sai a  slow".  "Gaskiya ne abokina to me ke Going?. Tun da naga fuskarka dauke da murmushi nasan a kwai labari".  Hhhhhhhhh Umar yayi Dariya, "Gaye shiyasa nake san zama dakai Wallahi, domin kai din akwai kwalwa. Gashi dai har ka gano ni".    "Eh mana bani nasha".  "Kasan dai zance gizo baya wuce na koki, Maganar shawarwarin da kake bani ne kai gaskiya abun nayi min dadi, Yanzu gidana sai abunda nace ayi shi za'ayi Rafy gaba daya tsorona take ji. Yanzu fa idan na ajiye kara baban ta ma ya ajiye mu kowa yace karta tsallaka to Wallahi a yanda take jin tsorona idan nace ta tsallaka na baban ta sai ta tsallaka wallahi"._




 _Dariya sosai Umar yayi yace "Gaskiya ne abokina ai nake gaya maka mace kullum kana bude mata hakora kuna wasa da ita wallahi gaba daya raina ka zatayi ta ringa ma abubuwan da taga dama, amma idan ya kasance tana jin tsoran ka, Haba Malam a nan zaka ji dadin rayuwa. kai ni fa yanzu haka maganar nan da muke yi gidan nan haka na fito ban bata ko kwandala ba kuma nace Dambun nama nake so da gasasar kaza. Dan tsabar tsoran da take min har russuna wa take tana godiya tana cewa an gama mai gida. Yanzu nasan ko bata da kudi sai ta ara ko kuma ta sayar da wani abun nata taje ta sayo min kafin in dawo".  Duk maganar da yake Umar sakin baki yayi kawai yana kallansa. Dajin yazo karshen zancen umar yace "Kanbuhu! Ashe ni wannan yarinyar rainani tayi. Ni fa nake gaya maka Yanzu Naira Hamsin ne na bata nace ina san shinkafa da miya amma shine ta tsaya tana min surutai wai kudin ko cefane bazai isa ba balle Ma a auno shinkafa ashe kawai dukan da nake mata ne har yanzu bai sa tayi hankali ba".  Muhajeed ya kama baki "Kai! Kai! Lalai kuwa bata horu ba. A hakan ma nake gaya maka dan fa baka sakar mata hakoran dariya ne amma da farat! Daya ma cewa zatayi bazata yi ba".  Daga jin haka Umar ya mike jikinsa har rawa yake, Muhajeed yace "Abokina naga ka mike ina zaka?"._



_"Hmm, abokina kenan ai mikewar nan da kaga nayi ba inda zani gida kawai zan koma. Domin a yanda ka bani labarin matarka take ma in dai ba haka Rafy ta ringa min ba zuciyata baza tayi sanyi ba. Kuma wallahi in taki min biyayya yau sai na sumar da ita dan ubanta".  Yana fadar haka ya mikawa Muhajeed hannu sukayi masabaha ya hau mashin dinsa yayi dogon ja. Mujahedeen na ganin Umar din yayi nisa sai ya kalle shi ya kashe da dariya yace "Banza kawai gara ka hadu da mace mai hakuri sai azbatar da ita kake. Uban waye zai wa matarsa duk abubuwan da nake fada maka in ba irin ku dolaye ba. Shege ni dama KA SAKE TA NA AURA".  Umar har ya kusa gida ya sama passenger nan ya tsaya ya dauke sa. Shine ya juya akalarsa i zuwa cikin gari...._

*__________________*

_Mama Asiya, Zuwaira, Da Hauwa  babu abunda suke yi in ba uwar hamma ba ta yunwa."mun shiga uku wannan wanne irin bala'i ne to wai me ke faruwa a gidan nan ne.  Dazun a gurin kari Munzo mun iske babu Dan wake biredi a rube haka store ba komai. Gashi mun aika Mai gadi sayan indomie babu yanzu mun aike shi sayan abinci Ya dawo nan ma babu. Gashi har Azahar tayi gaskiya ni bazan iya jurewa zama da yunwa ba. Wallahi gidan mu zani ina dalili Azumin dole".   Kamar hadin baki suma sauran suka mike "Ai muma bamuga ta zama ba wallahi". Kowa dakinta ta nufa ta daukko hijab kusan tare suka fito. Zuwaira ce a gaba ta nufi kofar fita a falo da niyar bude wa. Tana bude wa ta zura kafa da niyar fita sai ji tayi an hankado ta baya, Haka tayi baya ta fadi Tabar!, Dariya mama Asiya ta kyalkyala, "Saurin me kika haka harda faduwa?". Dan mugunta Zuwaira taki fadawa Mama Asiya turo ta akayi. Ai kuwa Asiya na zura kafarta da niyar fita. Da karfi aka hankado ta baya kamar buhun Hatsi haka tazo kasa Tum!. Badan Zuwaira ta goce ba da a kanta zata fado.  Zuwaira da Hauwa me zasuyi in banda dariya, Dariya harda rike ciki Suna cikin Dariya suka ji kofar ta koma ta rufe da kanta da karfi. Hauwa taje tayi-tayi ta bude amma ina..._

*_______________*


_A cikin islamiyya karatu ake amma su Nasmat hankalin su kan malam duk motsin da zaiyi idansu na kanshi. Ko waje ya fita sai sun bishi wai su kawai sai sunga yanda zata kare shi da Aljana. Bayan sun dawo aji an shigo littafan Fiqhu  Malam ya kalle Nasmat "Ke Zanyi miki tambaya a cikin littafin.Ahdhari (Ahalari)  Minene farkon abunda yake waje ba ga Baligi?".  Tsuru Nasmat tayi tana zara idanu ta kalli Asmart cikin Rada "me zance?".   "Oho alquran nima ban sani ba". Malam ne ya daka mata tsawa "ke tambayar ki fa nake yi"  A zabure tace "Malam abunda ya kamata baligin ya sani shine Mahaifiyar sa da uwayen sa da kannansa da abokansa da makwabtansa".  Ta juya ta kalli Asmart "Dan Allah ko ba haka bane". "Haka ne mana" Nasmat ta bata amsa a takai'ce. Gaba dayan ajin suka bushe da dariya.  Malamin kansa yaso yayi dariya kuma sai ya bata rai tsabar takai'ci bai kuma ce mata komai ba yace. "Maryam minene farkon abunda ya wajaba baligi?". Mikewa tayi cikin zazakar muryar ta ta fara bayani._


 *"Farkon abunda ya wajeba ga baligi  ya Inganta imanin sa sannan yasan abunda zai Kyauta farillan Ainihinsa kamar hukunce-hukuncen  sallah Dana tsarki da azumi. Yana wajaba a gare shi ya kiyaye hakokin ubangiji, Ya tsaga ga umarnin Allah da hanninsa, Ya tuba ga Allah (SWT), Tun kafin yayi masa azaba".*  

  _"Attakah biirrr".  Malam ya fada gaba daya ajin aka kaurade da fadar "Allahu akbar!". Wajen Nasmat ya zo ya mata bulala biyu, Hade da yi mata fada._

*______________*


_Tunda umar ya shiga gari bai dawo ba sai Wajen magariba.  Yana fara'a amma da shigar sa gidan ya wani daure Fuska. "Rafy! Rafy!"  Kira ya fara kwallawa sai can tukun ta amsa ta fito Tsaye kerere tayi masa. "Gani".  "Ina abincin da na saki kiyi min?".   "Banyi ba" ta bashi amsa a hatsale  Hannu ya daga da karfi Da niyar kaura mata Mari, Charaf! Ta rike hannu........................._




🤣😂  *Tabb! Ramin mugunta su Nasmat a gina sa gajere*


🙆🏻‍♂ *Umar kuwai baisan Aljana bace, Pls aci gaba inji ya zasu kare* 😁


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 57-58



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



*DEDICATED TO MY JIGO ZAMANI WRITERS ASSOCIATION * IN san duk masoyan wagga kungiya


✈❤ *JIRGIN ZAMANI* ❤✈

*Mun hau mun shillah Ahhha ha* 😁 *JIRGIN SO ZAYA TASHI KU KADAI MUKE JIRA 'YAN GATA DUNIYAR SO KUNE DA SARAUTA.* 

☺ 🎶🎵🎶 _Ku na gano da ku nake san rayuwa._ 


🎶🎵🎶 _Naga kuna da tausayi kunyi a rayuwa._ 


🎶🎵🎶 _Zanen dutse hali kuce bashi goguwa._

___


🎶🎵🎶 _Tarbiya ko a harshe ashe akan gane mai itta littafan ku da kansu sun nuna._ 😘


🎶🎵🎶 _Nayi dare ku ban masauki gidan ku in kwana._  😛 _Kuzo ku shigo har abinci zamu muku kwadan rama_ 🙊 ZAMANI WRITERS ASSOCIATION 😘❤ *WE LOVE U ALL ZAMANI WRITERS FANS*



'YAN PHAREEDAH KHAMSHI NOVELS KUYI HAKURI WALLAHI PAGES DIN NE YAKE TSAYI IDAN NAYI COMMENTED SAI SU NUNA YAYI NAUYI. TO KAFIN RABASHI BIYUN SAI WANI UZURIN YA FIZGE NI. PLS



       *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Kira ya fara kwallawa sai can tukun ta amsa ta fito Tsaye kerere tayi masa. "Gani".  "Ina abincin da na saki kiyi min?".   "Banyi ba" ta bashi amsa a hatsale  Hannu ya daga da karfi Da niyar kaura mata Mari, Charaf! Ta rike hannu.~


 _»»Gam ta rike hannun, Umar yaja-yaja  ya kasa kwace hannunsa hakan yasa ya kara kai dayan hannun ds karfi da niyar ya dake ta shima rike shi tayi. Yayi juyin duniyar nan ya ware iya karfin sa domin ya kwaci hannun sa amma ya gaza hakan yasa ya bar kokarin kwatar hannun ya wani bata Rai!, "Sakar min hannun"  yana fadar haka ta sake shi, Tsayawa yayi a gurin yana kare mata kallo har haske ta yayi da Torch ya tabbatar kums matar shi ce. A zuciya yake fadar "Anya kuwa wannan Rafy ce?. Dama Rafy na da wannan karfin take bari ina jifgarta?". Juyawa yayi ya kara kallan ta. "Bakiyi ba kika ce saboda me  to kika ki yi?".  A fada ce yake maganar "Saboda baka bar min kudi isasu ba mana". "Au! Kuma dan na baki kudin da basu isa ba shine ke baza ki cika ba kiyi yanda matan Kirki suke yi ko?".  Da sauri ta bashi amsa "Sana'ar me nake yi?, ko kuma kana bani kudinka ne?. Kare mata kallo yake sama da kasa Mamaki ne yake karuwa a gare shi. Shi badan ma ya haskata kuma yaji muryar matar shi ce ba da sai yace ba ita bace, Domin yanda yasan Matarshi a kwana nan mugun tsoranshi take yi. Yanzu tsoran dokan ta yake tunda yaji Wani sabon karfi a gunta. Juyawa yayi ya nufi kofa da niyar fita. Ai kuwa ta baya ta kama rigar shi ta jawo shi kamar wani karamin yaro "Ina zaka je baka bani abinci ba?".  "Sakar min riga malama masallaci zani". Murmushi tayi tukun tace, "To mai gida a dawo lafiya. Amma maganar abincin dare fa?". Bata rai yayi "zan sayo na kawo". Yana kokarin tafiya tace "To naji amma fa wallahi in ka dade sai na saka hijab na bika na lalubo duk inda kake".  Bai ko saurare ta ba ya kada kai yayi gaba  Sai sake-sake yake a ranshi._

________________

_Fatima tunda taga an yanka mata 'Yar baby an jefa sama take kuka. Gaba daya yau batayi karatu ba kuka kawai take malamin ajin ya dake ta amma take yin shiru Haka lalabo ma ba wanda baiyi ba. Ita kuwa taki. Ba yanda ya iya dole ya korota waje. Waje ta samu ta sauna ba abunda take sai kuka tana kallan saman soron da aka jefa mata 'yar baby. A haka har aka tashi gaba daya makarantar,Fiddausi ce tazo da kyar taja ta suka tafi gida domin da kiyawa tayi wai ita bazata je ba sai an dauko mata babyn ta. Sai da Fiddausi ta dake ta tukun.   Su Nasmat kuwa gaba daya ajin aka watse aka barsu zaune ba abunda suke sai leke wai jira suke malam ya fito su bishi baya suyi ganin kwaf!._




_Nasmat tace "Asmart anya kuwa wannan ya fada tarkon da muka haka mishi?!".  Asmart tayi 'yar dariya tace "Haba ke kuwa me kike ci na baka na zuba, Ki jira mana ni nasan bazata taba kya...".  Bata karashe maganar ba taga malam ya fita daga makarantar da sauri ta dauki jikar ta ta nufi hanyar fita a ajin. "Yauwa taso, taso gashi can zai fita".Baya suka bishi ba tare da ya sani ba daga Sunga zai waigo sai su labe. haka in suka ga ya tsaya wata majalissa sai su sama waje su labe suna lekensa. Haka dai suka ci gaba da tafiya ba tare da ya gansu ba har ya isa gida. Yana zuwa ya shige gida su kuwa a bakin kofa suka tsaya suna kace-nace.  Malam na shiga gidan ya fara jin kauri na tashi. "Masa'auda! Masa'auda!". Ya shiga kwalla wa matarsa kira. Gyaran muryar tayi alamun tana ban daki. Da sauri ya nufi daki domin daga nan kaurin ke tashi. Heater ya iske jone a socket An sata cikin ruwa. tayi  daga gani ta dade a jone domin ta kusan tsotse ruwan tayi daga sama kuwa tayi jawur har  wayar ta fara narke wa.  Cikin hanzari malam ya kai hannun da niyar ya zare ta a jikin socket din, Ai kuwa yana kamawa  abun ya hade masa biyu ashe robar ta fara narke wa ga kuma shocking. Wani mugun ihu ya kwada yayo waje a guje yana yarfa hannu yana fadin "Innalillahi!".  Su Nasmat da suke kofa kamar jira sukeyi suna jin ihun! Suka afka cikin gidan a guje. A tsakar gidan suka ja burki ganin malam tsaye yana yarfa hannu yana kallansu. Lokacin Masa'uda matar malam ta fito daga ban daki da sauri tana tambaya lafiya.  Malam kuwa harara ya watsa wa su Nasmat "Kai uban me ya kawo ku nan?".  Kallan juna suka tukun suka juya suka kallesa kamar hadin baki suka ce. "Taimako muka zo yi, (Emergency)".  "Taimako to uban waya yace muku ana bukatar taimako a nan".  Asmart da sauri tace "Malam munzo wuce wa ne sai mukaji anyi ihu! Shine muka zo dan muga me ke faruwa"._




_"Oh!  To daga ina kuke yanzu ko kuna so kuce min da aka tashi daga makarantar ba gida kuka tafi ba yawan ganta kuka fito?". Malam ya fada rai a bace.  "Wallahi A'a malam ziyara muka je mu".  Malam ya zaro idanu "Ziyara gidan wa a nan layin?.   Ba nan layin bane can ne gaba kadan gidan wata kawar momyna ko a gida ka ansan zamu zo".   Malam yace "To Shikenan naji kuma Wallahi in gaya muku in na tambayi Fiddausi ko Ameera gobe suka ce min ba haka ba, to jikin ku sai ya gaya muku maza ku wuce gida".  Cike da haushi da takai'ci suka juya suka fita a gidan. Tsabar bacin Rai sun dade suna tafiya amma Ko kala ba wanda yace Sai Tsaki kala-kala da yake fitowa a bakunan su. Can asmart ta kalli Nasmat, rai a bace kamar tayi kuka tace "Ashe dai dama Aljanar nan  mu ta raina?, kinaga fa duk abunda malam yayi mata ko tsawa batayi mishi ba".    Nasmat tace "Ke dai bari abun ya kona min rai, Wai ace duk abunda mukayi munyi a banza malam sai ma kara mana duka da yayi. Amma fa kuma inaga Aljanar ta mutu ne?".   Da sauri Asmart ta kalli Nasmat "Haba dai, Dama aljanu suna mutuwa ne?".  "Eh mana baki ji malam adamu yace Idan suka rikida suka koma wani abu  idan ka kashe abun shikenan ka kashe su ba.  Misali idan aljani ya koma maciji in kika kashe macijin shikenan Aljanin zai mutu, To kinga kuma Wannan 'yar tsana ta koma kuma malam ya yayanka 'yar tsanar shikenan  ta mutu kenan"._





_Asmart najin haka tayi wani tsallan farin ciki da jin dadi. "Wayyo da kuwa naji dadi Wallahi, Domin da Fatima ta shiga uku kullum da sai na sakata kuka sau uku. Kuma duk dukan da aka mana a Islamiyya sai na rama a kanta".  Hhhhhhhhhh Nasmat tayi dariya ta dora da cewa "Ke dai bari mu isa gidan Ai ni kadai nasan abunda zanyi wa Fatima yanda Aljanar ta gasa ni itama sai ta gasu".  Suna hirar har suka karasa gidan. Yanayin da suka tarar da gidan yasa basu nema Fatima bama kowa ta kansa yake. Domin Duk wanda ya shigo gidan ba damar fita sai gida ya garkame in kaje da niyar budewa Kuwa kasha mari. Haka suka kwana a ranar su mama asiya ba wanda yasa ko kwayar gero a baka._  

_____________________



_Umar ne zaune gurin mai shayi ya saka a dafo mishi Indomie da kwai. Sai washe baki yake ana hira. Bayan wani dan lokaci daban aka miko Mai indomie mai zafi a flat wacce aka lulube da wainar kwai sai tururi Take kamshi na tashi. Karba yayi sai Hadiyar mugun yawu yake.  Cokali daya yayi ya kai na biyu ya lumshe ido domin dadin da yake ji na Wainar kwan. Kamar daga sama yaji anyi ciki da Filet din indomie din duk ya warwatse masa a jiki. Da bude idansa da fitowar "Kutumar uba!".Daga bakinsa Duk daya, ba kowa bane Rafy ce tayi kwallo da Farantin indomie din takuma yi tsaye kerere tana hararen sa. "Ke dan iskanci da rainin wayo ni kika biyo har nan kika zubarwa da Abinci?".   "Eh an zubar din mugu macuci kawai". Ta bashi amsa a hatsale   Hannu ya daga ya kai mata mari cikin hanzari ta Duke. tana dagowa kuwa ta wanka mishi mari Tass!!!....................._



Yaseen na gaji


*Turkash!!!*





Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 59-60



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


*DEDICATED TO YOU*


❤ *FATIMA MUSA* ❤


❤ *AISHA LAWAL* ❤


❤ *KHADEEJAT ABDULLAHI* ❤


😘 _HAKIKA KU MASOYAN ALJANAR NAN NE. ALLAH YA BARKU TARE YA BAR ZUMUNCI A TSAKANIN KU_ 😂



❤ I LOVE U ALL MY FANS ❤

Da bazar ku nake Rawa. In baku sam! Bazan iya ba. 🙋🏻‍♂ Autan Zamani na gaishe ku



      *KARSHEN PAGEN BAYA*


 ~"Ke dan iskanci da rainin wayo ni kika biyo har nan kika zubarwa da Abinci?".   "Eh an zubar din mugu macuci kawai". Ta bashi amsa a hatsale   Hannu ya daga ya kai mata mari cikin hanzari ta Duke. tana dagowa kuwa ta wanka mishi mari Tass!!!...~


_»»Dafe kunci yayi. "Ni kika mara?, Ni kika mara?".   Ya maimata sau uku, "Eh an mare ka azzalumi kawai ai irinku bama mari ya kamace su ba, Duka da bulala ne ya kamace ku..." juyawa tayi ta kalli mutane dake wajen masu shan shayi da masu cin indomie wanda duk sun zura mata ido, Tace "Munafukan banza dubeku dallah, ba kunya ba tsoran ido da yawa daga cikin ku magidan ta ne, Sai ku baro matan ku da tuwan masara miyan kuka. Ku kuma kuzo nan a fashe muku kwai shayi hadin kauri. Wai abinci mai kyau to ku da mata waye ne yafin bukatar abinci mai kyau mai gina jiki da kara lafiya?. Su fa haihuwa suke. Kai Tirr! Da irin halin ku".  Ta juya ta kalli Umar "To  kai malam zaka wuce mu tafi gida ne ko kuwa?".  Abun ne yayi mugun kona mishi rai yaga idan ya kalle ta mutanan wajen daga yau zasu raina shi in ba sa'a bama su ringa ce mishi mijinta ce.  Wawurar ta yayi da kokowa ai kuwa suka tayi tututur-tututur.  Sun dade suna yi amma Umar ko raba ta da kasa ya kasa yi.  Haushi ma abun ya bata ai kuwa tq daga umar ta nuna wa Allah tukun ta maka shi da kasa. Jin jama'a sun kwashi ihu! Yasa shi yayi sauri ya mike._




 _Yana kallanta cikin fushi yana huci "Ke dani zaki Wallahi karki kuskura kice zaki ja dani yanzu sai in ka karya ki, Yanzun ma sa'a kika ci nayi tuntube kika shammace ni bar ganin mutane na ihu! Wallahi zasu kai ki su baro ne kuma bari ki gani".  Da karfi yake maganar ita kam Rafy a tsaye take cik! Tana kallansa ko hijab dinta bata cire ba. 'Yar wayar sa da 'yan canjin sa ya kai wa mai shayi ya ajiye masa tukun  ya dawo fili. Ya tsaya yana mata surutai sai da ta sakankance tukun ya durfafe ta cikin shammace. Kamar dazun haka ta kara yin hajijiya da shi ta maka da kasa. Mutane da tune sun cika gurin suka bushe da dariya ana ihu! Tashi yayi ya ka kabe Wandan sa. A zuciyarsa cewa yake, "Anya kuwa wannan Rafi't dina ce kuwa, Haba ai karfin yayi yawa  yaseen wannan ko kona za'ayi a nan bazan iya kayar da ita ba. Abunda yafi kawai shine in fece".  Jama'ar wajen ne suka fara ihu! Suna fadin "Raggk mace ta kada shi".  Umarvya kalli wasu daga ciki yace, "Aikin banza abunda ma ban shirya ba". Kamar dazun a hankali ya ringa matsawa kusa da ita yana shirin kama kafafun ta ya kadata.   Ita kuwa tsaye take ba abunda take in ba kallansa ba. Wawura ya kai mata cikin rashin sa'a kuwa ta sake Damke wuyansa kamar ta kama kaza haka ta fara wulwulawa da shi. Umar ihu! Ya farayi yana neman taimako jama'ar wajen kuwa ba abunda suke in banda dariya. Wasu na cewa mai kashi daya ce, Basu san *ALJANAR FATIMA* Bace.  Sai da tayi juyi kusan hudu da shi tukun ta sake shi ya fada kasa sharaf!._





 _Nan ma mutane suka fara kyalkyala dariya. Umar ya dan jima a zaune domin hajijiyar da tayi da shi kansa ya dan fara juyawa. Mike wa yayi cikin fushi ya nanade kafar wandansa. Yana mikewa ya kwasa a guje mutane kuwa suka ta mishi ihu!  Yaji tsoran mace.  Sai da ya danyi nisa tukun ya tsaya ya juyo da karfi ya fara magana. "Ke ba dai ni kika wa haka a cikin jama'a ba, Wallahi yau sai nayi maganin ki yau bazaki kwanar min a gida ba kuma Wallahi idan kika shiga hannuna sai na dandana miki azabar da baki taba tunani ba. Yana fadar haka ya juya ya nufi gida a guje bai ko tsaya karbar wayar sa da 'yan canjin sa ba na wajen mai shayi.  Da shigar sa gida ya saka kwado a kofar gidan ya kulle yana cewa. 'Yar iskan banza yau sai muga a inda zaki kwana nasan dai gidan ku ko kinje koro ki zasuyi.   Tun daga tsakar gida yaga hasken fitila a daki a zuciyarsa yace, "Ashe ma a kunne ta bar fitilar ta fita masifa".  Yana shiga dakin yaga mace kwance sai dai ta juya baya. Baya iya ganin fuskarta, da alama barci take yi.  Tsaye yayi kofar dakin ya tsare ta da kallo kamar matar shi kamar kuma ba itaba. A hankali ya fara matsawa  sai da yaje gaf da ita yaga ashe ta dan lulube fuska da Wani gyale. A hankali yasa hannu da niyar ya Cire yaga ko wace ce. Shi dai yasa a baya ya baro matar shi.  Yana taba gyalan Firgigit!  Rafi'at ta tashi. "Mai gida ka dawo sannu da zuwa". Ta fada tana mamakale wa dan tsoran shi kamar yanda ya saba.  Da ya tsora ta kuma sai wani tunanin ya zo mishi yace, "Haba kaga mata ta nan ga tsoro nan a fuskarta waccan Aljanar ce ba ko shakka".   Tsawa ya daka mata, "Dan ubanki bana hanaki kwantawa a kan gadan nan ba?".  Da sauri ta sauka tana bashi hakuri.   Tsaye ya mike yana kallanta yana dariyar mugunta farin ciki yake ji. Na ganinta domin yanzu zan rama duk abunda Aljana tayi min, Haka ya ayyana a Ranshi.   Mari ya galla mata dan tabbatar wa. Ai kuwa ta saki kara ta fara kuka tana bashi hakuri.  Wani murmushi yayi na mugunta domin yanzu a ganin sa ya tabbatar da matarsa ce ba aljanar._




_Murtuke fuska yayi ya kalle ta, "Wato in ma yi hakuri kike cewa ko, Da nayi niyar yi miki babban hukunci amma tunda kin bani hakuri bulala 20 ce ba yawa".  Ya juya ya nufi kofar fita a dakin domin ya dauko bulala.  Rafi'at abun tausayi har kafar shi take kamawa wajen bashi hakurin amma sai dai ya fusge.  Nan ya barta zaune a tsorace sai kuka take tana bashi hakuri.  Umar ya fita ya dauko bulalar katuwar Dorina ce mai baki  biyu.  Ya shigo da ita dakin, Ba abunda ya daure mishi kai sai ganin Rafy a tsaye ta tsare shi da kallo fuskar nan tata babu annuri. Shi da ya barta tana kuka yanzu kuwa ko hawaye babu a fuskanta. Da ganin haka ya yarda bulalar domin ya kyaro Aljana ce. "Mai gida me zakayi da bulalar nan?".  Rafy  ta tambaya cikin bacin rai!.  A  tsorace yace "Wallahi dama can din ne inda nake ajiye ta naga rana an dakar ta shine na daukko zan canza mata wajen ajiya".  Ok ta fada lokacin da ta nufe shi ta durkusa ta dauki dorinar Umar karkarwa ya farayi dan a tunanin sa zane sa zatayi. Kamar yayi waje da gudu kuma sai ya tuna gida a kulle yake da kwado.   Sanda ta wulwula bulalar tukun ta dorq mishi daya. Ihu! Ya kwada "wayyyo!!..".   Da sauri tace "Haba sweetheart karka bada maza mana. ni fa dama tambayar ka zanyi akwai zafi?".    "Ehh   A'aaa".  Ya bada amsa biyu a jere, yana sosa inda ta dake shi domin taji bulalar. Daga wa tayi da niyar kara mishi.  Da sauri  yace "Akwai akwai zafin". Sannan ta wullar da bulalar gefe.  Sweetheart to muje mu kwanta mana.   To ya fada da sauri yaje ya haye gado. Itama taje ta hau ta wani shishige mishi. shi kuwa duk a tsorace yake a haka har barci ya kwashe shi.  Tana ganin haka ta bace cikin abunda baiyi Minti daya ba taje ta dauko Real Rafy ta hada su hade da cewa karta kuskura taji tsoran shi....._

__________________


_Fatima tunda tajw gida ta shiga daki ba abunda take sai kuka sai da tayi mai isar ta tukun barci yayi gaba da ita.  Kamar yanda ta saba kullum idan ta tashi zata fitsari da babyn ta take zuwa dake a gado daya suke kwana. Yau kuwa tana farkawa taga ba yar baby ta tuna abunda ya faru jiya sai kuwa ta hau kuka. Ameera ce ta farka a lokacin, Sai da taci uban Fatima tukun Fatima tayi shiru.  Washe gari tun da asuba Mama Asiya ta fito daga dakinta tafiyar kamar marar lafiya domin yunwa taci-taci. A falo ta zube a kasa  ita kam tama rasa abunyi har jiri take gani.  Tashi tayi ta nufi kitchen kamar ance ta bude store ta bude. Komai nasu ya dawo abun ne taga kamar gizo yake mata, hakan yasa ta murjw idanu.  Haba gaba daya yunwar da wani rashin karsashi tafiya sukayi a lokacin. Kira ta fara kwallawa su Zuwaira.  Ko wacce na dakinta suma ba barcin suke ba yunwa ce taci ubansu.   Shiru suka mata Alhalin kuma suna jinta. "Hauwa Zuwaira ku fito kuga ikon Allah abincin mu ya dawo".  Haba kafin ta rufe baki tagan su kowa ta fito a sukwane. Kitchen din suka koma suna gani kuwa suka fara murna Zuwaira kam duk da tana jin yunwa har da rawa.  Indomie suka zuba a tukunya wajen guda 10. Tun kafin ta Dahu mama Asiya taci Indomie danya leda biyu.    Cin hauka sukayi wa indomie din domin ko bari ta huce basuyi ba. Sai da kowa ya cika cikin sa mama asiya kam tayi zari da yawa dan har sai da tayi amai._





 _Da safe bayan kowa ya karya akayi shirin islamiyya domin ba boko an bada hutu,  Fatima tace bata da lafiya kanta ke ciwo mama Asiya tace "Munafuka wato makarantar ce bakya san zuwa shiyasa kika azawa kanki ciwan karya ko?. To Alqur'an sai kinje maza wuce ki sako Uniform dinki". Fatima kuka ta fashe da shi ta nufi daki tana cicila kafa.  Mama asiya ta juya ta kalle ta. Ta kama baki alamaun mamaki. "Iyeeee! Fatima ni kika wa wannan rashin kunyar dan na taimake ki nace ki tafi makaranta ko, oya zo nan dan ubanki dawo". Fatima ta dawo tana kuka ta durkusa a gaban mama asiya, "jiya dama naji kin shigo kina kuka ana ta lalashin ki miye kike wa kuka?". Zuwaira ta tambaya.   Cikin kuka Fatima tace "Ba malamin mu na islamiyya bane ya kwace min Babyn na ya yanka min ba". Da jin haka mama Asiya ta bushe da dariya "Shegiya Allah ya kara, dama ni wannan Aljanar ba santa nake ba, ni gaba daya ma na tsane ta".  Zuwaira tace "Au!  Dama a kanta ne kike kuka ake ta rarashin ki amma kika ki ji, Ai ni dana sani wallahi da duk da ina jin yunwa da sai na taso na fafala miki mari, mu wannan ai rahama ne ma rabuwar mu da ita".  Korar ta sukayi ta tafi daki tana kuka, Su Asmart suna canza kaya suna sa na islamiyya ta shigo tana kuka. Nasmat na ganin ta ta nufo ta tana zazaginta. Wai ta musu shiru, Fatima duk da ta so ta rike kukan amma yaki rukuwa.  Nasmat dunkule hannu tayi ta Dankwashi Fatima a kai, haba ai kuwa sai ta kara fashe wa da kuka, Fiddausi na ban daki jin kukan Fatima yasa tayi sauri ta fito.  "Keee! Keee!  Wallahi in kika sake dukan ta sai naci uwarki". Fiddausi tace lokaci  da ta nufi inda suke.  Maganar ce ta dakatar da Nasmat da tayi niyar yiwa Fatima dundu.  Nasmat tana gunguni ta koma gun Asmart dariya asmart tayi tace "Nasmat mugunta ko wato dake Kinga *ALJANAR FATIMA* Bata nan".     Nasmat tace "ai sai na rama duk abunda tayi min"._



_"Asmart tace bari a dawo daga Islamiyya zata daku ai a waje na".  Fiddausi ta tambayi Fatima me take wa kuka Fatima ta fada mata mama asiya ce yace sai taje makaranta kuma kanta ke ciwo. Fiddausi hannu  ta dora a jikin Fatima taji da zafi, hakan yasa taje ta dauko mata magani ta bata tashi tukun tace ta kwanta. Sunzo tafiya mama Asiya tace ala dole sai Fatima taje makaranta, Sai da Fiddausi tayi yaki sosai tukun mama asiya ta barta.  Ai kuwa suna fita mama asiya ta koro Fatima waje. Wai ta koma cikin rana Mai zazabi baya san sanyi dan salan mugunta. Aljanar Safuratu ce tafe cikin iska tun daga nesa ta hangi mama asiya sai jaraba take wa Fatima tana dankwashin ta ita kuwa tana kuka hakan  yasa ta kara sauri....................................._





Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy















👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 61-62



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



👏🏼 *NASAN NAYI MUKU LAIFI KUYI HAKURI DAN ALLAH MASOYA.*


🙃 _JIYA KAM NAGA MASOYAN ALJANAR FATIMA. HAR KARFE GOMA MASSAGES BASU DAI NA SHIGOWA WAYA TA BA. DUK MASU JIRAN POST NE._



👏🏼 _NA GODE MUKU MASOYAN WANNAN LITTAFIN NAWA, SANNAN IN BAKU HAKURI BISA RASHIN POST DINA. WALLAHI INA CIKIN TYPING TUN KARFE 5 BIYAR BACCI YA DAUKE NI BAN FARKA BA SAI WAJEN 9. TO BAKU KADAI NAWA LAIFI BA HAR DA UBANGIJINA_ 😭



😍😘 I LUV OLL MY FANS.  ANA MUGUN TARE 🙃



   *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Aljanar Safuratu ce tafe cikin iska tun daga nesa ta hangi mama asiya sai jaraba take wa Fatima tana dankwashin ta ita kuwa tana kuka hakan  yasa ta kara sauri.~


_*K*afin Safuratu ta karaso wajen mama Asiya ta shige ciki,  Tana ganin haka ta bace ta dawo sufar Ameera,  ta kofar gidan ta shigo taje gurin Fatima. "Ke wai miye tun jiya kike tayi wa mutane kuka?".  Fatima ta dago cikin kuka tace "Malam ne ya kwace min Babyna jiya ya yayanka".    Sai a lokacin Safuratu ta lura yar babyn a hannun Fatimar,  Da sauri ta juya tana fita daga gidan ta bace bata zame ko ina ba sai kofar mai shagon, inda aka sayo 'Yar babyn  shagon ta gani a kulle_

________________


_A gidan Umar kuwa Safuratu na ganin Asuba ta kusa to sai tayi sauri ta dauke Rafy ta mayar da ita gida ba tare da tama sani ba tana barci, Ita kuwa ta juye zuwa rafy din ta zo ta kwanta. Da asuba Umar ya farka zaune yayi ya zuba wa Rafy da ke barci ido, Tunani yake a ranshi  wannan Rafy din ce ko kuwa, Da dabar ta yayi Rafy! Rafy! Tashi asuba tayi_





_Firgigit! Ta tashi a dan tsorace shi kanshi ma sai da ta tsorata shi.  "Sannu mai gida lokacin sallah yayi ko?".  Ta fad murya a sanyaye daga jin haka a zuciyarsa yace "Wannan Rafy ce ba Aljanar ba".  Kai ya daga mata alamun eh, Ita kuwa ta saukko taje tayo alwala shima alwalar yaje yayi yazo ya tada musu sallah.  Bayan sun gama salar ma ya juyo y kalle ta yaga dai alamar Rafy din ce. domin kamar yanda ta saba ko Ido bata iya hadawa da shi haka ma yanzu Safuratu alamun tsoro take nuna mishi. Bayan ta gama adduo'i da sauri ta rissina cikin Ladabi ta gaishe shi ya amsa. Ta shi tayi ta cire hijab din jikin ta koma kan gadan ta kwanta.  Umar da ganin haka ya murtuke fuska ya shiga zancen zuci. "Amma fa yarinyar nan in ita ce ta raina min wayyo._




_Harda wani hayewa kan gado, Amma bari in gwada ta inga Aljanar ce ko kuwa".  Da karfi ya fara maganar "Rafy! Rafy!  Saukko kasa malama kin wani je kin daare gado kamar na ubanki".  Da sauri ta tashi ta sauko a tsorace. Murmushi yayi yace Yauwa wannan Rafy dita ce.  "Yauwa ke abunda nake so kiyi min a yau zan zana miki yanzu kuma Wallahi in bakiyi daya daga ciki ba har kika 'yar da na dawo,..Kema kin  san sauran".   "To mai gida ina jinka".    Ya wulla mata harara tukun ya fara lissafi da yatsun sa yana kirga mata aikin. "Na farko yanzu ki tashi kije ki dafa min ruwan wanka, Kafin in fito ki dafa min abun break.  Na uku kinga kayana can sun taru sun kusan kala ashirin  ki wanke min su ki goge,  Na hudu kiyi min Taliya da farfesun kaza kinji ni da kyau".   Kuka ta fashe da shi, cikin kuka tace "Haba mai gida so kake yi ka kashe ni wannan aikin ai sunyi yawa Wallahi bazan iya ba duk ni kadai a rana. Kum..." Tass! Taji saukan mari a fuskan ta, "Kaji 'yar isakar 'yarinya to idan baki min ba wa zaiyi min wato a nufin ki in baki ci da sha in barki gida mimike a kan gado kamar  gasasar kaza ko?. To Wallahi ban lamunta ba, oya maza tashi".  Ball yake shirin yi da ita hakan yasa ta tashi ta fita a guje shi kuwa ya zauna a bakin gado. Dariyar mugunta ya fara yi. Juyowar da zaiyi yaga Rafy tsaye tana kallansa.  Tsayawa yayi da dariya  tukun yace "Ke me kika yi a nan maza wuce kije kiyi abunda nasa ki". "Kai tashi maza je ka dafa min ruwan zafi ka kai min bayi, Kuma mintuna 15 kadai na baka".   Kamar daga sama yaji magana, juyawa yayi yaga lalai Rafy ce ke maganar, "Kanbuhun uba!.   Wato ina baki Umarni kema kina bani da Alamar dukan safe kike bukatar ki karya da shi yau".  Ta sowa yayi da hanzari zai dake ta ai kuwa ta rike hannun ta murda shi. Ihu ya kwalla Tukun ta sake shi. "Oya wuce kayi abunda na saka ka kafin raina ya baci"."Rai nin wayo ma, ina mijin ki ne zaki sa in miki wani ruwan zafi To Qur'an bazan yi ba. To ni in gaya miki a tarihin rayuwa ta ban taba tsugunna wa gindin ba".  "Au bazaka yi ba kenan!".  "Eh bazan yi ba"  ya fada a dan tsorace domin  ya gano ba Rafy bace._




_Juyawa tayi ta dauki Bulalar jiya ta nufe shi, Tun kafin ta karasa wajen shi ya farq ihu! Yana bata hakuri. Batayi wata-wata bata fara zura mai bulala,  shi kuwa ba abunda yake sai ihu! Dake a daki ne ba'a ji sosai waje. Sai da ta mishi wajen  bulala ashirin tukun tace "Yanzu zakayi ko kuwa?"  Da sauri yace "Eh Wallahi zanyi Allah zanyi ko ma abincin kike so zanyi miki, Amma dan Allah ke wace ce"   kaji dan rainin wayo Nice matar ka au! Dama duk abun da kake min baka san kyale ka ne nake yi ba saboda san da nake yi ma?, To yanzu kuma naga ba wata soyayya a tsakanin mu kullum sai dai ka dake ni, Hakan nema yasa nima sanka ya fita fit!  A raina yanzu in kaga ka dake ni to kyale ka nayi, Maza tashi kaje kayi min abunda na saka ka".    Cikin  hanzari ya tashi ya fita yaje ya dora ruwan sai da yasha wuya tukun wutar ta huru.  Ruwan har yayi zafi ya kusan tafasa Rafy ta fito.  "Yauwa uwar gida ruwan ya kusan tafasa ya fada yana kallanta yana dan murmushi yak'e".  Da sauri ta zo wajen sa ta kama hannun sa. "Mai gida tashi mana miye kake haka, ina ce ni kasa in dafa maka ruwa, Ashanafa kawai naje daukkowa shine kuma zaka zo ka fara dafa wa. Haba sahibina ai sai kaja min tsinuwar Allah haba mai gidana koma daki abunka kar sanyi ya illata min kai".  Tunda ta fara maganar ya saki baki Galalah yana kallanta, Tunanuka iri-iri suke ziyartar kwalwar sa. Mike wa kawai yayi ya fara tafiya ya nufi daki, Ya saka kafa daya cikin dakin kenan yaji ta shako rigar sa ta baya. "Munafuki ina zaka ka wani nufi daki, Au! Wato ko dukan ne bai ishe ka ba kari kake so?. Maza malam kaje ka karashe dafa min ruwan zafi na". Umar ji yayi kamar ya fashe da kuka dan bakin ciki, Abu biyu yake tunani ko dai Aljana ce ko kuwa Aljanar ce ta shiga jikin matar sa. Sai da ya tafasa ruwan duk tana tsaye kansa tana zafga mishi masifa, yaje ya surka ya kai mata ban daki. Ta saka shi ya dafa musu tea kafin ta gama wanka. Ba yanda ya iya domin zuwa yanzu yayi sanyi sosai mugun tsoran ta yake.  Bayan ya dora tea din ne ya lura ba sugar sai da ya jira ta fito ya sanar mata. Tace yaje sayo kamar jira yake dama ai kuwa ya tafi da sauri har ya kusan zuwa kofar yaji ta ambaci sunansa. "Wallahi in ka wuce minti 15 sai na bika har inda kaje na babalaka, ba daka tafi da sauri a nufin ka ka gudu ba".    Kamar kuwa tasan niyar guduwa yake.  Maganar da tayi kuwa ta tuna mishi jiya hakan yasa jikin sa yayi sanyi.  Fita yayi daga gidan yana tafe a hankali ji yake duk duniyar tayi masa kunci baya jin wani dadi balle farin ciki._




_Abokin sa Muhajeed ya tuna, "Yes". ya ambata direct ya nufi gidan Muhajeed din. Bayan yayi sallama Muhajeed ya fito nan suka zauna ya kwashe labarin duk abunda yake faruwa a gidan sa daga jiya zuwa yau ya fada wa Muhajeed.  Dariya sosai Muhajeed yayi tukun yace "Kai amma Wallahi ban taba sanin kai so ko ne ba sai yau, Haba dai nawan karka bada maza mana Uhmm!  Ace mace ta ringa buga ma irin wannan game din haba ai yanzu an wuce wannan yayin".    Dan bata rai Umar yayi yace "Abokina baka fahimta bane irin karfin da naji a jikinta ya nuna ba ita kadai  bace da aljanu a tare da ita".      Mtseeeew   "Aljanaun banza ni fa ban wani 'yar da da akwai wasu aljanu ba, Malam kawai jamfin mutane ne, Ni da mata ta ce ta tsuro  min da wannan iskancin Wallahi da tuni  nayi maganin ta".    Umar ya kada kai yace "Shin yanzu idan na baka dama zaka iya zuwa ka Ladaftar min da ita?".   Muhajeed yaji zancen mugunta da sauri yace, "Kwarai kuwa abokina. idan ban mayar ma ita kamar mata ta ba daga yau mu raba abotar nan".  Umar yace "ok to 

shikenan yi sauri tashi muje mintuna 15 dam ta bani".  Muhajeed dariya ya tashi tana wa umar wai ya zama mijin hajiya har tym.ake bashi.   A zuciyar sa kuwa tunanin irin bugon da zaiwa Rafy yake,  Yana murmushi mugunta yana kara ganin wawancin abokin nasa._


_______________________ 


_Wajen karfe 11 tukun mai shagon ya bude. Safuratu a sufar alhaji salim taje ta tambayi irin 'yar babyn ai kuwa taci sa'a saura daya irin ta Ta kuwa sayo.  Fatima na zaune har wani gyangyadi take daga zaune. Domin kanta sosai ciwo yake. Karar bude gida taji abunda yasa ta bude idan ta ta zurawa kofar ido kenan dan ganin  mai shigowa.  Bisa mamaki taga 'yar tsanar ta ce ta taho. Dungwai-dungwai Hannun ta rike da jakar kayanta.  Wani ihun! Jin dadi Fatima tayi hade da tashi da gudu ta tarye ta tana mata oyoyo. Daukar ta tayi tun dag nan take kwalla kira "Mama Asiya! Mama Asiya! Babyn ta dawo".  Haka take fada har ta karasa falo a iske su mama Asiya suna kallo. Kan mama Asiya Fatima ta fada tana murna,  da karfi mama Asiya ta tura ta kasa suka yi daya-daya da babyn da dan akwatin. "Ji 'yar iskan yarinya karya ni zakiyi?".  Fatima dan bata rai tayi dan taji zafi daukko babyn tayi tace "Mama Asiya babyna ce ta dawo".  Sai yanzu ma suka lura da babyn "waya kawo miki ita malam din?,"  Kusan a tare suka yi tambayar "Aa da kanta fazo". Inji Fatima Asiya tace "Zo Fatima". Tana zuwa kuwa ta zafga mata mari, "Dan ubanki bana hanaki karya ba?".   Kuka Fatima ta fara cikin kuka tace "Wallahi mama ba karya nake ba".  Gashin kan Fatima ta kama taja da karfi kamar zata cira shi. "Dan ubanki Bana ce karki kara ce min Mama ba?".  Hakuri Fatima ta shiga bata bata. Ita kuwa kamar kara tunzurata take. Lafiyayun marika har biyu mama asiya ta wa Fatima. Hade da yin ball da ita ba tausayi da ganin karamtar ta.  Daukar 'yar babyn da Jakar tayi ta fita waje ta tulla su can saman kwano. Ta dawo tace "Inga ubanda zai daukko miki".  Ran Safuratu ya baci sosai, Bat ta bace ta dawo falan ba tare da suna ganin ta ba.  Muguwar harara kawai take bin Mama Asiya da shi Allah-Allah take mama Asiya ta bar cikin falon.................................._



🙆🏻‍♂😰  *YAU WASU ZASU DAKU, MAMA ASIYA, MUJAHEED*  


😔 *KAICO FATIMA*




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 63-64



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


*KIN CANCAN Ce SHI. NA BAKI PAGEN DUK DADIN SA. KE KADAI. (ROUKIE BABY)*


🌺🌺🌺 *LABARI NA*🌺🌺🌺



✍🏼 *Writing by*

ROOKIE BABY


👯 JINJINAR BAN GIRMA GARE KI RUKKAYA.  DAYA KIKE TAMKAR DA DUBU. INA GWANIN WANI GA  TAWA GWANAR BA GWANAR A GUN FADA BA KO ZAGI. JINI NA MIJIN FAMA. HADARI SA GABANKA INDA KAKE SO.GIWA KIKA BAKI WAI WAYE IN KUN NAUSA. GWANKI MAI RANGWANGWAN.  ZAKI SA MAZA GUDU. KABEWAR KAN KABARI BAKIN CIKKN MAI TAUSHE.  MURUCIN KAN DUTSE. MAHASSADAN KI A YAU SUNE FADAWAN KI. LA'ILAHA ILLALAHU".👻🙊.


🤙🏽 _Hakika kinyi rawar gani kin kawo abunda ake so labari ne mai dadi cike da ma'ana labarin da zai sa matasan mu su hankalta musamman ma mata.  Labarin da akayi amfani da salo mai burgewa wajen jan hankalin mai karatu. Idan na fara karanta page ya kare  kamar in daka wayar da kasa nake ji._ 😘 *Godiya muke yi yar uwa Allah ya kara basira zakin hannu. Allah ya kara hada kawunan mu.  All Zamani Writers.  Wuta kawai kuke ina biye da ku ina barbada Fetur*


🤤 Autan ku ne. *King boy*



  *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ta dawo tace "Inga ubanda zai daukko miki".  Ran Safuratu ya baci sosai, Bat ta bace ta dawo falan ba tare da suna ganin ta ba.  Muguwar harara kawai take bin Mama Asiya da shi Allah-Allah take mama Asiya ta bar cikin falon.~



 _»» *S*u Umar hanya suka biyo sai sauri suke Muhajeed har ya matsu aje gidan dan hannun shi kaikayi yake, Abun da basu sani ba duk abunda suke yi Aljana Safuratu na gurin tana jinsu. Mujaheed yayi mugun bata haushi, A ranta tace yanzu fa da Rafy ce da sai y same ta ya Zane baiwar Allah.  Lokacin su Umar suka karasa gidan, dake ba bulala kusa Umar da kanshi ya dauki wani itace dan dogo ya mikawa Mujaheed. Shi kanshi Mujaheed yaga Girman iccen, Amma dan mugunta sai bai ce yayi girma ba. Umar ya bashi Izinin shiga. Kamar wani uban ta haka ya fada dakin. Dake dakin da dan duhu Rafy ta kunna fitila yana shiga ya iske ta  a bakin gado cikin shiga ta bakar doguwar riga. "Munafuka algunguma, Tazo yayi wani mukus kamar wata salaha to yau dai Allah ya toni Asirin ki kashin ki ya bushe. Umar ne ke fadar haka lokacin yana kokarin saka kwado ya garka me dakin kwadan ne yaki rufuwa dan haka ya saka kubobi kawai ya barshi.  Haka tagar ma. (Window) ya rufe ta. Juyowa yayi ya nufi Rafy da har yanzu tana kan gado duk abun da yake yi ido kawo take binsa da shi, Duk wanda yasan  Rafy in yaga ta yanzu yasan idanunta sun kara girma.  Bai yi wata-wata va ya fara zura mata bulala. Yana dukan nata da karfi yana fada._





 _Yayi mata kusan bulala goma amma yaga shiru ne domin ko motsawa batayi ba In  banda manyan idanun ta da take binshi da su ga ta wani daurw fuska. abun ya daure mishi kai sai ganin iri  dukan da yake mata ko icce ne sai haka.  Umar na waje jira yake kawai ya fara jin ihu!  Rafy amma shiru.  Mujaheed ya daka iccen dake a matsayin bulala zai narka mata kenan, cikin hanzari ta mike saurin su irin na Aljanu ta kwace icen ta bace da shi. Mujaheed waige-waige ya kamayi a cikin dakin yana neman ta.  Hihihihihihhi-hihihihi. Wata siririyar dariya ce ta fara cika dakin. "Waye? Waye waye mai dariyar nan?  In ba tsoro ba fito mana. Ni fa nan da kike gani na a shirye nake ba raggon namiji bane".  Aljihu Umar ya laluba ya dauko wata laya ya rike a hannu yaci gaba da cewa ta fito mana. Ta baya yaji an turo da karfi ya nufi bangon dakin kafin   ya isa bangon yaji  an tare shi da hannu ba tar da yaga wanda ya tare shi din ba. Mari fasss! Fasss! A duk kumatun  nashi biyu,  Rike kumatun yayi kamar yayi ihu kuma sai ya yi tsoran kar abokin sa yaji ya kunyata.  Ji yayi an dan dadabe shi.  "Kaaaa!" Yana juyawa baiga kowa ba sai saukar wasu tagwayen marukan.  Wayyo! Mujaheed ya fada a hankali ba da karfi ba ya dafe kumatun sa. "Muguwa kawai wannan tsoro ne ma. Ku fito fili mana mana ayi ga da ga, in ba tsoro ba".  Mujaheed ke maganar ya dunkule hannu kamar dan dambe sai juye-juye yake so yake kawai yaga ta bullo._





_Dariya yaji da karfi a bayan sa.  Hahhahhhhhhhh!  Yana juyawa kuwa abunda ya gani ya tsorata shi sosai.  Wai katan dodo ne mai bakin gashi buzu-buzu ko'ina jikinsa gashi ne. Hannunsa kuwa wasu mugayen farcina ne masu kaifi, Girman abun ya kai A hade Mujaheed biyu ko uku. Babban abun tsoran shine kan Rafy ne, Idanun ta sun juye sunyi baki. A haka take nufo inda Mujaheed yake tana dariya, Duk lokacin da ta wangale bakin ba abunda zaka hango ciki sai wasu rubabbun hakora.  Duk jikin Mujaheed ya fara rawa mugun tsoro ya kama shi, faduwa yayi kasa yana ja da baya yana bata hakuri cikin kuka kuka."Dan Allah kiyi hakuri, Wallahi bazan kara ba, kuuuummaaaa maaa..." Ya fara magana karkarwa ganin abun ya kusan iskoshi.  Daga waje yace Umar yace "Abokina wai ya dai naji shiru ne har yanzu bata fara ihu ba, Nafa gaya maka karka raga mata kaci ubanta sosai ni na saka ka". Cike da takaici Mujaheed yace "Ka yanzu zakaji ihu na ni...".  Kafin ya rufe baki yaji an shaki wuyansa kamar wani zakara an daga shi sama Ihu! Ya fara "Wayyo! Allah na Wayyo! Wayyo!". Da karfi yake ihun! Fitsari ne ya fara zuba shaaa! Wulli tayi da shi ya maku jikin bango. Sa'ar shi Daya ba kan shi ya budu ba._




_Tashi yayi a guje ya nufi wajen kofa, ai kuwa wutar dakin ta dauke duf!  Baka iya ganin komai ko'ina duhu ne.  Inda ya nufa ya azo kofa zai ji, Kawai sai yaji yaci karo da mutum haka kuma aka dalla mishi mari, Wani bangaren ya sake nufa nan ma yaji saukar mari. Ba abunda yake in banda kuka da ihu! Yana neman agaji domin yanzu abun yayi yawa mari da duka ta ko'ina kawo mishi ake. Umar daga waje ihun yake ji kamar na matar shi haka yasa ba abunda yake yi sai murna yana fadin "'yar banza gobe ma ki kara".  Mujaheed ya daku sosai dan fuskar sa har sai da ta fara kunbura.  Yana nan duke ya rufe kanshi da hannnuwa dan dukan shi da ake. Ba abunda yake sai ihu da neman agaji. Tsik! Yaji an dakata da dukan nashi,  a hankali ya fara bude ido yaga ashe haske ya dawo. Yana bude idan ya ga ashe tsugunne yake gaban gado Can kuma kan gadan rafy ce ke kallan sa tana murmushi.  A tsorace yaja da baya. "Dan Allah, Dan annabi kiyi minn Rai ki barni in tafi gida ki yafe min Wallahi ko can dam ni wa'azi nazo in miki kibi mijinki...".    Tsawa ta daka mishi wanda sai da yayi muguwar zabura. "Wa'azi kazo ko dai kara rikita al'amura?, Ashe dai dama kai ne muna fuki wanda ka raba su da farin ciki da shawarwarin ka na mugun ta da ke ta. Umar  Ya dauke ka tamkar dan uwa ne komai zaiyi sai ya sanar da kai amma kai gurinka ka na ya za'ayi ka saka su cikin damuwa ne shida matar sa ko?"._





_Duk hawaye ne da majina da a fuskan sa. Da sauri yace "Aa Wallahi ba haka ban...".  "Rufe min baki ko in kara maka dukan da ya fi na dazun".  Hannu yasa ya kame bakin sa. Aljanar taci gaba da cewa "Tunda kai ne wanda ya jefa su cikin wannan halin to Wallahi kasan yanda zakayi ka dawo musu da farin cikin su. Daga yau zuwa gobe na baka.  Sannan kuma ina so in gaya ma karka yarda ka fadawa Umar cewa na dake ka".  Wani zane ta wurgo mishi tace "Oya goge hawayen da majinar. Ka fita a hankali kana murmushi".  Da sauri ya dauka ya gogo ge.  Tashi yayi zai fita alamun tsoro ta gani a fuskan sa gashi har yanzu yana 'yar karkarwa. "Kai dawo ka fita kana Murmushi nace ba karkarwa  ba". Wani mugun yake yayi tukun ya juya ya fara cire kubobin.  Yana ganin daki ya bude haba wa sai ya kwasa a guje kamar bai ji duk abunda ta fada mishi ba. Safuratu ta girgiza kai tace "Hmm yaro bai san wuta ba aka ce sai ya taka". Umar na tsaye yaga mutum ya wuce a guje kamar wanda aka harbo. Ai kuwa ya rufa mishi baya. Sai da sukayi gudu mai nisa. Duk wanda ya  tambaya lafiya Sai  Mujaheed yace "Aljana! Aljana!  Haka ya ta tsorata wasu suna rugawa suma. Sai da ya gaji da gudu tukun ya tsaya ya zauna a wata inuwa duk jikinshi yayi sharkaf da fitsari ga Gumi ga hawaye. lokacin bai ko san Umar na biye da shi ba. Da karasowar umar da zai tashi da gudu sai kuma ya tsaya da yaga Umar ne._




_Umar na zuwa ya fara tambayar sa "abokina wai ya haka naga ka fito a guje bayan dazun naji tana ihu".    "Dallah can ni rufe min baki ta gama ihu ko na gama ihu!.  Ashe kasan haka matar ka take da kartin Aljanu shine ka hadani da ita".  Umar yace "Abokina sai fa dana fada maka wannan matar Aljanu ne da ita kaki yarda. To yanzu miye abun yi danni gaskiya tsoran komawa ma nake yi".   Mujaheed yace "In dai kana da kudi wannan ba matsala bane akwai wasu 'yan bori da na sani aikin su kenan fidda aljanu nake gaya ma fit! Daya zasu fidda wannan Aljanar karamar kwaro ce ai.  Dan ko ni nan abunda yasa taci galaba a kai na ban shiryo bane........_

: _________________


_Mama Asiya zaune take suna hira ta fara jin wata murya na kiran ta.  "Aaaaasssssiyyyyaa!"   Da sauri ta waiga baya wayam ba kowa.  "Aaassiyya".   Ta kara juyawa ba kowa.  "Wai dan Allah bakwa jin ana kiran sunana?".  Ta tambaya gaba daya suka ce su basuji ba.  Tashi tayi ta nufi dakin ta wanda daga nan guraren ne take jin kiran.  Da bude kofar da wartar ta ciki duk daya.  Duk kibar ta kiiii!! Taji an jata bata ganin mai jan nata. kasa kofar kuwa ta koma ta rufe gam! Jikin bango aka makata.  Wash!  Ta fada. Wutar dakin ta fara rawa zuwa can kuma wata iriyar dariya marar dadin ji ta kaurade dakin.  Ahhhhhhhhhh!  Mama Asiya ta saki ihu!  Mai karfi hade da rufe kunnuwan ta.  An dan dau lokaci a haka ta rufe idan ta gam ta kuma toshe kunnuwa da hannaye. Zuwa can taji an tsaya da dariya wani abu taji na jika ta. Kamar ruwa.  Da sauri ta bude ido.  Ahhhhjh!  Ta kara sakin Ihu!  Jini ne gaba daya ya malaye dakin  tashi tayi tsabal!-tsabal tana taka kafa cikin jinin ta nufi kofa da nufin ta gudu.  Har ta kusan zuwa taji kamar an jawo kafafun ta shuuuu!  Sulbi ya kwashe ta ta koma. Hahahahaha! Taji dariya hade da wani irin gwalan gwalantu na fitowa daga Cikin wardrobe.  Karkarwa take duk ta rude kayan jikin ta sun koma jawur kamar wacce ta fito daga kwata. Tashi tayi ta nufi wardrobe din hannun na karkarwa ta bude. Ihu! Ta saki mai shegen kara Ahhhhhhjjhhhhjhhhhhhhhhh!.  Su mammiya ta zube a gurin..........................._


😰 *MUJAHEED* 😰

Karfin hali sata a jikin gawa.   Wato baka ma daku ba kenan.  Ai kuwa in dai Safuratu ce zata yi maganin ka...


👻 *MAMA ASIYA* 👻

Allah yasa yau ki daku ki kusan zaucewa ma


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 65-66



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



*GODIYA NAKE MASOYA*


JINJINA GA ALL MEMBERS NA 

📚 *ANSHOLLY NOVELS* 📚

✍🏼 *KING BOY ISAH NOVELS* 📚

_Na yaba da kaunar ku gare mu_


🌺 *HADIZA TUNAU(.* 🌺

Na ga sakoki Allah ya saka. 



*IDDAH*


*MEERAH DANFODIO*


*MISS PRETTY*


*ZAYYNERB*


*SUWAIBA*


_Allah bazan iya lisSafo ku ba._


🙋🏻‍♂ *king dai Nata dago hannu masoyan Aljana wanda na sani dama wanda ban sani ba.* 😉 Ana mugun tare



🤦🏻‍♂ _KUYI HAKURI DA DAN WANNAN PAGEN NIMA KAI NA NASAN YAYI KADAN.  WAYAR TAWA CE YAU KAMAR TA SHA GIYA SAI YANGA TAKE_




     *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Karkarwa take duk ta rude kayan jikin ta sun koma jawur kamar wacce ta fito daga kwata. Tashi tayi ta nufi wardrobe din hannun na karkarwa ta bude. Ihu! Ta saki mai shegen kara Ahhhhhhjjhhhhjhhhhhhhhhh!.  Su mammiya ta zube a gurin.~


_Ta dan dade a suman zuwa can ta farfado. A kwance kan gado ta tsinci kanta idanta a rufe sai kanta da take jin yana mata zogi.  Har zuwa yanzu bata bude ido ba kan ta dan dafa wash! Wash.Tana  Bude ido ta saki wani kara Ahhhhh!  Da sauri ta mike ta sauka kasa. Wata tsohuwa ce ta gani kwance a gefan ta tana mata murmushi fuska duk a yamutse.  "Wace ce ke?".  Mma Asiya ta tambaya.  Tsohuwar ta tashi zaune ta kalli Mama asiya ta wangale baki tayi mata dariya sai yanzu munin ta ya kara bayyana domin hakoran gaba duk babu su sun zube. Ga bakin jajur da shi kamar wacce taci danyan nama. Duk zaman da nayi gidan nan  baki sanni ba?.  Amma anyi yarinyar banza makaryaciya  nasha dazun kika wullani saman soro, To ni Aljana ce sunana Safuratu".





  _Karkarwa Mama Asiya ta farayi  baki na rawa "Daddadda dan Alllllah ki yyiiii  hakkkkuurrrri karkiiiii ki kashe ni".  Kwashe wa da dariya Aljana tayi tace "oh! Baki so in kashe ki ko?".  Da sauri Mama asiya da haryanzu ko'ina jikin ta karkarwa yake ta daga kai alamun eh.  "To shikenan kinyi alkawari duk abunda nasaki zakiyi a wunin yau?. Wannan shine zai kubutar dake kar in kashe ki". Mama Asiya ta zube kasa "Eh Wallahi na yarda duk abunda kika ce komai wuyar shi zanyi in dai bazaki taba min lafiyan jikina ba".     HHHHHHHHH Aljanar tayi dariya "To yanzu tashin farko maza tashi kije ki hau kan Soro ki daukko wa fatima 'yar babyn ta. Dama kince kiga uban da zai daukko ta to ba ubanda zai daukko ta sai ke maza tashi". Aljanar ta karashe maganar cikin tsawa ta kuma murtuke fuska. A razane mama Asiya ta tashi da sauri tubur-tubur da ita tazo ta wuce Su Hauwa dake falo. Zuwaira na ganin Mama Asiya a haka tace "Aunty Asiya lafiya kuwa?".  Juyowa tayi tace "Ina fa lafiya, ku dai da kuke lafiyan kuna da amm...".  Aljanar taga ta bayyana a Kan sofa kusa da Juwaira. Haba ai kuwa bata karashe maganar ba tayi waje a guje. Da fitar ta ta fara kira maigadi yana daki ya fito da sauri. "Yauwa aiken ka zanyi dan Allah jeka gidan Alhaji mudi ka karbo min aran kuranga. (Tsani)".  "To"  ya fada da sauri ya juya ya fita nan ya barta sai bari take ta kasa zama gu daya. Kai ta daga ta kalli gurin taga da dan nisa. "Kai amma fa hawa can gun zai min wuya anya kuwa zan hau".   A fili take yin maganar Wannan tsohuwar taga ta bullo "Bazaki hau ba kenan".    "A'a ni nama isa dama kawai fada nayi". Ta danyi murmushi mai wuyar gane ma'ana._



 _Mai gadi ne ya shigo ba kuranga.  Mama Asiya na ganin sa bata ma tsaya jin  ta bakin sa ba kawai ta hau shi da masifa. "Kai dai musa mugun mashiririci ne. Ban ma taba ganin mai gadi irin ka ba, To ina abunda aka aike ka ka kawo din?. Ka wani dawo wa mutane hannun bibiyu baka san abun Emergency bane".  Shiru yayi har sai da ta kai aya tukun yace "Hajiya wai cewa sukayi An amsa aro ne sai dai wai muje gidan Naseer mu daukko".  "Ah!  To me kake jira kuma da bazaka je ka daukko din ba".   "Hajiya gaskiya ni kam bazan iya daukko wannan kurangar ni kadai ba. Tayi min nauyi".  Aljanar ta bayyana bayan Mai gadi tana hararta da sauri tace "Maza muje in  kamo ma mu daukko".    Mai gadi  yayi mamaki sosai shi tunani ma yake, ko mi za'ayi da kuranga bayan yasan ba wani gyara za'ayi ba yana san tambaya kuma yana tsoran masifa. Ko gyale Mama Asiya bata sako ba a haka suka je har can suka daukko kurangar sai wani sauri take saka shi, Bayan sunje aka aza kurangar a saitin gurin da zata hau din. Mai gadi ganin tana shirin hawa yace "Hajiya me za'a daukko miki bari in daukko miki".  Ta juyo kenan suka hada ido da Aljanar "A'a bari".  Ta fada lokacin ta fara hawa kurangar a hankali take tafiya gata lutuyi  ba dan kurangar karfe bace da ta ballata dan can kake hango ta tuli guda. Har tayi dan nisa ta waiwayo kasa. Tsoro ne ya kama ta ta fara karkarwa ji kakae ratsatsam!  Suka zubo kasa tare da kurangar.  Mama da jin haka sai gaba dayan mutanan dake  cikin gidan suka fito. "Lafiya! Lafiya" ake ta tambaya "Lafiya lumi".   Ta fada lokacin da ta mike ta fara kokarin mayar da kurangar. Mai gadi dake tsaye Dariya taci karfin sa tun yana matsewa har ya fara saka ta fara fitowa fili.  Yana 'yar dariyar ya nufo ta lokacin  tana kokarin hawa. "Hajiya na gaya miki kinyi nauyi bazaki iya hawa ba bari in hau in dauko miki.  Kama jaki haka Mama asiya ta harb mishi kafa ta kuwa ci sa'a ta same shi a baki ba wanda baiyi dariya ba a gun. Mama asiya a hankali ta hau  har can ta ta daukko 'yar tsanar har da jakara._




 _Bayan ta sauko tace wa Mai gadi ya mayar ma da masu kuranga abunsu. Aljanar ce ta bullo "Kinyi kokari sosai, yanzu abunda  nake so dake shine ki Je kiyi wa diyar nan wanka ki mata kwalliya mai kyau irin ta amare in bakiyi ba kuma sai naci abunki". "To". Kawai su Zuwaira suka ji mama Asiya tace ta nufi daki da sauri rike da 'yar baby su dai basu ga wanda take magana da shi ba._

_____________________


_Umar ya kalli Mukhtar   yace Abokina yanzu dai bani da kudi a jikina amma idan kana da su ka ara min muje a daukko yan borin nan gwara a fidda Aljanar nan ko na sama zaman lafiya". Mukhtar yace "Ai kai ba a baka Rancen kudi ba ka ki biya da wuri amma ga kudi nan wurina kudin uwar gida ne dubu 20 Zan sayo mata fulawa da mai, kasan sana'ar ta kenan".  Umar yace "Haba abokina ai ka sani bama 'yar haka da kai Wallahi ina da kudi a gida yanzu haka ba dai ina tsoran Aljanar nan ba da munje na daukko. Amma tunda kai jarumi ne ko muje in kwatanta maka inda kudin suke ka daukko".  Da sauri Mukhtar yace "Kaiii! Amma kama raina min wayo waye zai yarda ya koma hannun Aljanar can.  Kaga tashi muje in ara maka kudin kawai".  Tashi sukayi suka hau mota basu zame ko ina ba sai wani kauye gida daya-daya. Tun daga farkon gari su Umar suka fara jiyo garaya kidan 'yan bori na tashi. Gidan suka nufa suna shiga suka iske masu kids daban masu rawar bori mata da maza daba. Sarkin borin wani dan gajeren mutun ne baki_





_Wani dan baki dashi sanye yake da wasu jajayen kaya jikin sa duk layoyi da guruka.  Ga wata hular gashi da ya da ya saka a kai sai ta kara mishi muni. Duna kenan sarkin 'yan bori na wannan yanki. da ganin su ya daga wa masu kidan Hannu duk sai suka dakata. "Mai ke tafe da ku?". Ya tambaya yana zazare musu idanu.  Mukhtar ne ya dan Risina ya dan kirara shi tukun yace "Mun kawo karar wata shedaniyar Aljana ce da ta takurawa wannan bawan Allah. Nine na bashi shawarar mu zo gurin ka nasan kai ne kadai zaka iya maganin ta. Aljana ce ta shiga jikin matarsa sai azbtar da shi take yi".    HHHHHHHHH Sarkin borin ya kece da mahaukaciyar dariya sai kawai suma fadawan sa suka fara yi sai da yayi mai isarsa su dai su Umar tsaye kawai suke suna kallan ikon Allah. "Shegiya 'yar mintsila tayi kamu".inji sarkin bori. Ya hade gira yace "'yar mintsila ce wannan aikin ku mai sauki ne bama sai naje da kai na ba yara na zan hada ku da su suje su fatatake ta. Ko jiya mun fitar da ita daga gida uku da take kokarin raba aure. Fatan a shirye kuke?".   Mukhtar yana dan murmushi yace "kwarai kuwa a shirye muke Sarkin bori".   Kudin aljihunsa ya fiddo ya ciri dubu biyar yaje ya ajiye agaban sarkin bori. HHHHHHHHHH Duna yayi dariya tukun yace Lalai wannan ashirye kuke.  Da mutane Biyar ya hadasu masu kida guda biyu 'yan bori uku.  Nan suka hayo mota suka nufo gidan Umar.   Tun daga zaure masu kidan suka fara kidan Su kuwa Masu borin kamar da gaske suka farayi sai hauka suke wai su gasu sunzo gida mai aljanu.  Shugaban yan borin da aka hado su da shi ne yace wasu umar su kulle gidan. Ai kuwa suka fita daga gidan daga waje suka garkame gidan da padlock. Safuratu abun mugun dariya ma ya bata ganin wannan  mutanan masu hauka wai sun zo wai su ita suka zo  fitarwa.  Fitowa tayi daga cikin dakin da sufar Rafy Sai dai idanunta Tsanwar shar._





 _Ta kuma murtuke fuska ba abunda take bisu da shi sai harara. Da ganin haka masu ku kidan suka kara kaimi haka masu borin ma kara haukata sukayi har kusa da ita suke zuwa. Sun dade suna yi amma shiru basu ga wani sauye ba domin tsaye take cik! Sai zuba musu idanuwan ta masu abun tsoro.  Ganin rainin wayan su yana yawa yasa ta nuna daya daga cikin matan 'yan bori.  Wani iska ne ya fito daga hannun nata ya kwashi matar yayi sama da ita......................_



 😂😂😂😂

*SU MUKHTAR ABUN HARDA MUGUNTA A KULLE 'YAN BORI DA ALJANA A GIDA*


😁😂 

*MAMA ASIYA YAU AN ZAMA SOJAN SAMA*



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy








👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 67-68



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*




~Ganin rainin wayan su yana yawa yasa ta nuna daya daga cikin matan 'yan bori.  Wani iska ne ya fito daga hannun nata ya kwashi matar yayi sama da ita...~



_*D*a ita ya dawo da ita kasa tum!.   Sannan ta mika hannunta ya zama wani zakalele  ta daukko abun da ake kidan duk ta farfasa su. Da ganin haka duk suka rude.  Rafy bacewa tayi ta koma daki taje ta daukko dorina. Suna tsatsaye kowa yasha jinin  jikin sa sai gani suka yi bulala ta fito daga daki ta nufo su ba tare da sunga mai rike da ita ba. Nan fa bulalar nan ta fara binsu daya bayan daya tana zane wa nan da nan gidan yacika da ihu! Ba abunda kake ji sai ihun su da kuma karar bulalar. Da gudu wani ya nufi kofa ya hau bubugawa yana cewa. "Ku bude, Ku bude zata kashe mu".  Saukar bulala yaji abunda yasa ya zabura kenan ya koma suka hau zagaye-zagaye Gaba daya sun rasa maboya. Su Umar najin Mutanen na ihu!  Amma suka ki bude haka makwabta duk lokacin wani ya fito ya tmbaya lafiya sai suce mishi "Babu komai ana dan wani aiki ne".  Umar kalli Mukhtar yace "Abokina ni fa ina tunanin Aljanar ce take dukan 'yan  borin nan. Kamar ihun bana mutum daya nake ji ba".  Mukhtar ya kalli Umar yace "Haba dai kamar dai wasu garori. Yo ai nake gaya maka wannan su aikin su kenan suna cire manyan aljanu ko sunkai dubu ne ma balle wannan kwara dayar kuma ma mace".  Umar dai baice komai ba.  Cikin gidan kuwa tuni tayi musu rudu-rudu wata mata ce daga cikin masu borin ta sake komawa wajen  kyauren da karfi take girgiza wa tana cewa "Dan Allah dan Annabi ku bude karta kashe mu wannan Aljanar ko kadan bata da imani".  Umar yace "kaji ko, To Wallahi gwara mu bude kar muyi kisan kai". Mukhtar ya kalle sa yace "Kai dai Wallahi ka cika naci to bari dai na bude ka ganwa idan ka, Ni dai nasan Aljanar ce ake suburbuda. Shine take neman agaji". Mukhtar  y fara bude kofa da cire kwado matar nan  ta fito a guje kamar an harbo ta. Ai kuwa duk da suna maza sai da ta bangaje su suka fadi har kasa. 'yan borin nan daya bayan daya suka ringa bi ta kansu daga karshe dai da kyar suka samu suka tashi suka rufawa 'yan borin baya. Wanda har yanzu dorinar bata dai na binsu tana  Shadar su haka yansa basu daina gudu ba.  A kasa suka je har kauyen. Sai da Safuratu taga an  kusan shiga kauyen tukun ta shafa musu lafiya ta koma gida._





 _Da gudu suka ringa fadawa gidan sarkin bori haba wa wasu daga cikin masu kidan da masu borin duk wartsakewa sukayi  suka fara zabgawa a guje ganin mutane na shigowa a jere.  Shi kanshi sarkin borin kadan ya hana ya tashi ya gudu kawai dan dai kar  yaji kunya ne kuma yaga iya mutanen sa ne.  Har dubawa bayansu yake ko zaiga abunda ke biye da su shima yayi ta kansa amma bai gani ba.  Zubewa sukayi a gabansa sai huci sukeyi kowa yasha gudu hatta su Umar sun galabaita. "lafiya-lafiya!".  Sarkin bori ya fara tambaya ciki  su ba wanda ya iya daga baki yayi magana domin duk a wahalce suke. Sai zuwa can Mukhtar yace wa sarkin borin "Wallahi Aljanar ce duk taci ubansu ta farfasa kayan su. Bama wannan ba har nan ta biyo mu tun daga can  a kasa muka zo tana basu kashi.  Sai da suka zo bakin garin nan tukun ta koma".  HHHHHHHHHHHHH  Duna Sarkin bori ne ya ke ta kyalkyala dariya. Zuwa can kuma kamar dauke war nepa dif!  Ya dakata da dariyar ya murtuke fuska. Mikewa tsaye yayi ya fara magana.  "Shegiya 'yar mintsila, Ashe tasan wasa ma guri gare shi. Tasan da ta karaso nan. Kai da ta ma karaso garin nan da kwanan ta ya kare kenan  bama wahalta ta zanyi ba, Yaseen da kashe ta zanyi, Yo me ake da masu irin halinki 'yar mintsila". Gatsine-gatsine ya fara yi kamar wani mahaukaci. Mukhtar ya kalle shi yace "sarki yanzu miye abunyi?. kaga dai wannan bawan Allah 'yar mintsila ta hana su sakat! Ta hana su wali shi da matar sa...".  "Dakata malam".  Cikin daga murya sarkin bori ya fadi hakan. Shi kadai ya yata magana "To, Naji, Aa, Baza a kara ba, Sunyi kadan ko, hihihihihi, Zanja musu kunne".  Duk maganganun da yake shi kadai ne idanunsa kuma rufe._





 _Bude idanu yayi fuskarsa a murtuke ya gallawa Mukhtar harara yace "Aikin banza, ai duk abunda yafu kune kuka ja domin kudi kadan ka bayar, Wannan dalilin ne ma yasa sarkin aljanun da muke aiki tare da shi yayi fushi lokacin da na aika yara na yaki  ya bisu, Dan haka sai kun karo kudi yanzu ni da kaina ma  zanje in furtume ta, Mintuna 5sunyi yawa tabar gidan".  Mukhtar ne ya kalli Umar da alamun yana so ya tambaye shine ya kara ko kuwa?. Umar da ya fahimci haka tun kafin Mukhtar yayi magana yace, "Sarkin bokaye in dai kudi me ba matsala. Mu dai gurin mu ta bar gidan".  Naira dubu biyar Umar ya karba a gun Mukhtar ya kara musu. Amma sarkin bori yace Sai dai Goma.  Ba yanda suka iya dubu goma suka kara mishi kudin wajen sa suka zama 15K.  Shiri sosai sarkin bori yayi layoyi da turaren magani. Ha tayar da mutum Kusan goma daga cikin yaran shi Masu Kida da masu borin.  Duk da yasan wajen akwai nisa amma da isa da takama da nuna shi sarkin borin ne a kasa ya taho.  Mutum biyu rike da kasko hayaki na tashi daya bayanshi daya a gabanshi.  A haka suka nufi gidan umar........._


___________________

_Mama asiya da sauri ta karasa ban dakin ta. Ta farawa 'yar baby wanka. Tana cikin gurza mata soso kawai sai kan ya kille. Mama Asiya juyawa tayi gabas da yama kudu da arewa bata ga Aljanar ba ga kuma kan 'yar babyn a hannunta.   Tsoro ne duk ya kamata tama rasa abunyi nan ta fara kokarin mayar dashi amma daga ta lika sai ya fado.  Suuuuuuuuuu!  Taji wani kara hade da iska a bayanta  a tsorace ta juya. Tsohuwar nan ta gani tsaye cikin wata doguwar jan riga yanzu tama fi muni ga abun tsoro idan nata sunyi wani kwala-kwala gasu jajaye farin ba yawa.  Fuskar duk a jagule take abun tsoro da kyama. Mama Asiya karkarwa take domin ta tsorata sosai.  "Kiiii kii yi haaakuuurii Da dada dama".  Matar ce ta daka mata tsawa "Munafuka ba abunda zaki gaya min harda wani karkarwa. Ashe dama haushin Babyn nan kike ji ko? Gashi kin dai cire mata kai da gangan".   Da sauri Mama Asiya tace,  "A',a Wallahi ina mata wanka ne ya fita. Kiyi hakuri please".   "Kina so in hakura?!.  "Eh". Mama asiya ta fada da sauri. "In kina so in hakura to ajiye 'yar babyn ki jiyo". Da sauri ta ajiye 'yar babyn a saman Bath din, ta juya suka fuskanci juna da Aljanar. "Ba wani abu mai wuya bane kawai kuka da dariya nake so ki min a lokaci daya. In bakiyi ba kuma yaseen sai na maida ki kuli-kuli"._






_Dajin haka mama Asiya ta fara. Hahahahaha wiiiiiii wiiiiiii hahahaha yiiii yiiiii Hahahahaha Uhmmm uhmmm hahahaha.  Ta dade tana yi Aljanar ce ta Wanke ta da mari Tats!! "Dan ubanki haka ake kuka dama a garin ku ba hawaye?".   Zafin marin da mugun takaici sune suka saka Mama Asiya kukan gaske hawaye suka fara kwaranya.  "Yauwa haba ko ke fa. Yanzu naga kina kukan gaskiya sauran kuma Dariya".   Mama Asiya da tuni kuka yaci karfin ta rasa ya zatayi dariyar tayi. Hakan yasa ta kama Bude hakori tana yak'e.  Da gani haka Aljanar tace "Wannan ai ba Dariya bace maza yiwa kanki chakulkuli. Kiyi Dariya".  Chakulkulo tahau yi wa kanta Ta karfi da yaji sai da dariyar ta zo mata ta hada da kukan tana yi. Aljanar kanta abun ya bata Dariya Hakan yasa tace wa mama Asiya "Oya yanzu na yafe miki kuma na gyara kan  babyn juya kici gaba da mata wankan".  Da fadar haka ta bace, Ita kuwa mama Asiya ta juya taci gaba da wa 'yar baby wanka.   Safuratu a wani  *KURMIN DAJI* ta bullo ba abunda take sai Dariya.   Mama Asiya bayan ta gama mawa 'yar tsanar wanka ta tsane ta tas!. Taje da ita gaban mirror ta fara mata kwalliya.  Irin kwalliyar da Asiya ta tsaya ta tsara wa 'yar babyn ko ita kanta bata taba  yin ta ba._



_Ji tayi kawai 'yar babyn tace "Daukko zani ki goyani". Da sauri Mama Asiya ta bude wardrobe ta daukko zani tazo zata goya ta kenan taji tace, "Yaseen kin ma mugun Rainani, Da wannan tsohon zanin zaki goyi gimbiya guda?. Maza ki daukko sabo". Komawa tayi ta daukko sabo a cikin kayanta wanda bata ko taba sawa bama, Tazo ta goya 'yar habyn da goya ta kawai sai ji tayi ta kama kuka.  Mama Asiya tsuru tayi jira kawai taji me yasaka ta kukan. Wani mugun tsunkuli taji an mata wanda har sai da tayi 'yar kara. "Shegiya muguwa wato kina ji ina kuka shine baza ki ringa jijiga ni irin "yanda ake wa jariri ba ko?.  Maza fita dani ki ringa jijiga ni ko nayi shiru".  Da fadar haka 'yar babun taci gaba da kuka. Ai kuwa mama Asiya ta hau jijiga da lalashi kamar ta sama jaririn gaske.  Su Zuwaira na falo suna hira. Kawai sai ganin Mama Asiya sukaye ta fito daga dakin ta goye da 'yar baby Sai faman jijigata take tana fadar "Yi shiru- Yi shiru. su basa ko jin.........................._


😰 *Yaseen na gaji



 


😂 MAMA ASIYA 😂 *RENAN DOLE YA SAMU...*


😧 *SARKIN BORI DUNA* 😰


An nufo gidan Umar.  Allah yass kai ma a raka ka har gida kamar yanda akawa yaranka 😂😂😂




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy





👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 69-70



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*




🎀🎀

*BADDEEYERH*

               🎀🎀


Written; *BEAUTY QUEEN*

🤙🏽 _JA MUJE GWANA TA. ALLAH YA KARA BASIRA DA FASAHA. KINYI ABUN A YABA. TABBAS MUTANE ZASU KARU DAKE SOSAI. KICI GABA KUMA KI MAIDA HANKALI WAJEN ZAKULO IRI-IREN MATSALOLIN NAN DAKE ADDABAR MU A WANNAN ZAMANI. HAKIKA DA YAWA ZASU HANKALU TA DALILIN LITTAFIN_





🍒

🍒🍒

🍒🍒🍒

*ZUBAR HAWAYE*


Written by. *ZEETTY*


Cogrt Sis kinyi rawar gani, Kinyi abun azo a gani.  ZUBAR HAWAYE.


BABBAN DARASIN DA KE CIKI.

_GARE KU SAMARI MAYAUDARA. FATAN IN KUKA KARANTA LABARIN NAN ZAKU HANKALU KU GUJE YAUDARA. SHIN KUNSAN YAYA TA KWASHE DA AHMED AMARYARSA DA FEEDO?_  



_MASU SOYAYYAR_ SHAN MINTI.🤔 _KU BAKU TUNANIN NAKU YAN UWA MATA IDAN KAGA ANAYI DA KANWAR KA ZAKAJI DADI?.  KUMA MATA AI DA LAIFIN KU SHIN IDAN KIKA KI AMINCEWA ZAI MIKI DOLE NE? IDAN KUMA YA DAI NA ZUWA GURIN KI RASA MIJIN AURE ZAKIYI NE?. UHMMM ZEETTY TAYI KARIN HASKE A LITTAFIN NAN NATA ZUBAR HAWAYE_



🤗 ZAMANI NA ALFAHARI DA KU. MUNA JIRAN SABABBIN LITTAFAN KU



 💃🏼 KU BANI KIDAN BIRTHDAY A SAMA💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU


💃🏼 YAU BIRTHDAY QUEEN NE MUKE KU SANI 💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU


💃🏼 BIRTHDAY HAUSY FA DAN KU SANI 💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU


💃🏼 DUK ZAMANI MUNA MURNA💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU


💃🏼 NI NE RARA NAZO IN FADI💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU


💃🏼 ALJANA TA ZO BIRTHDAY, KUJI YA 💃🏼

🗣MASU GUDU SU GUDU 

🎂🎂🍰🍰

🤗 *HAPPY BIRTHDAY TO YOU MY QUEEN HAUWA HAUSY* 😘


 *Ina Wishing u More Albarka Years Ahead Dear.* 😘



*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Kawai sai ganin Mama Asiya sukaye ta fito daga dakin ta goye da 'yar baby Sai faman jijigata take tana fadar "Yi shiru- Yi shiru. su basa ko jin.~


_Tafe yake jama'ar na binshi baya har da su Umar sune masu gwada mishi hanya.   Har kofar gidan, Kaskon Hayakin  ya karba ya fara shiga gidan  sannan yaranshi suka rufa mishi baya, Su Umar kam a tsorace suke sai da suka bari kowa ya shiga tukun da labe-labe suka shigo a hakan ma suka tsaya a bakin kofa.  Sarkin bori tsaye yayi a tsakar gidan yana wani zazarr ido yana waige-waige cikin tarwatu Da gagautawa ya fara cewa yaransa "Kuyi sauri ku kukuna hayakin nan ga shegiyar nan tana fama ta gudu, Kuyi sauri, Kuyi sauri". Da sauri yaran nashi suka daukko wani kullin magani suka zuba a kaskwayan  kusan guda shida aka kunnawa wuta. Ai kuwa hayaki ya cika gidan ba abunda kake ji sai tarin su, Gaba daya har sarkin borin. Su Umar kuwa dajin haka sukayi waje nan makwabta 'yan gaf! Da gidan su suka fara fitowa suna mishi masifa. Shima dake ya iya Mukhtar ya kama mishi suka ta  Bala'i da 'yan anguwa. Sarkin bori da yaji ba haza hayaki na neman illata su da sauri yake cewa "Ku kashe-Ku kashe, Ai ga Aljanar nan ma har mun sumar da ita, Yanzu karasa ta kawai zamuyi_





 _Ruwa aka debo aka kwarayawa kaskunan suka mutu. Safuratu na dakin tana jinsu duk abunda Suke ta kyale su. Sarkin bori yasa aka fara kida. Nan da nan Suka fara bori Har shi din sai wani girgiza kai yake, Bori suka cika gidan sunayi. Aljanar ce ta fito yanda taga gaba dayan su sun haukace kowa da irin haukan da yake, Wasu har tsalle suke su fado kasa.  Kawai sai abun ya bata dariya, ji tayi kawai tana so ta gwada taga shin borin gaskiya ne ko kuwa iskanci ne.  Wasu mata ta kalle su uku sai bori suke A cikin su har da mai kwantawa kasa tana malolowa.Safuratu ta saura zuwa wani make ken Kadangare irin jankwatakwalan nan.  Da gudun tsiya kadangaren ya nufi matar nan mai birgima a kasa tana bori.  Tana kyalla ido ta ganshi haba wa sai ta saki ihu! Ta tashi a guje Taje tana kokarin Kama katanga ta haura. kamar ba ita ke bori ba Haka sauran matan ma da ganin kadangaren suka wartsake suka tashi zasu tsere.  Sama ko kasa su kuwa su Sarkin bori basu ko ga kadangaren ba. "Mine ne?-mine ne?".  Sarkin Bori ya ke tambayar Ruzaina wacce ta nufi katanga tana kokarin haurawa. Juyowa tayi tana dube-duben ba ko alamar Bori a  tare da ita. "Kadangare na gani ya nufo ni".  Cikin masifa sarkin bori yace "Kadangaren banza kadangaren Wohi!. Ai yanzu gashi kin bata mana aiki. Ga Aljanar har ta fara kuka, tana Bani hakuri tana cewa in kyale ta in mata Rai. Aiki yayi nisa Amma kin dawo damu baya".  "Ayi hakuri sarkin sarakunan 'yan bori, Kadangaren ne ya tsorata ni".   Dakuwa ya mata "Kinci ubanki ke da kadangaren. Yo ni ba kadangare ba ko zaki na gani ina bori ai bazan ma kula da shi ba". Yana fadar haka yayi tsaki ya juya yace aci gaba da kidi. Nan fa suka dora daga inda suka tsaya._





 _Aljanar ta ji maganar da Sarkin bori yayi, Ai kuwa tace bari mu gani sarkin bori yana tsakar haukansa ta bori yayi tsalle ya fado kasa dabar! kenan yaji maciji a wuyansa kamar an cillo shi. Ihu! Ya fara yi yana kokarin kankare macijin a wuyansa. Da sauri macijin ya nanade sa cikin hanzari. Yaransa masu bori tsayawa sukayi yana kallansa kawai domin su basa ganin macijin. Haka Su Umar sun kwalalo mishi idanu.  Macijin Ta gabanshi ya zagayo ya fasa kai dai-dai fuskar Sarkin borin. Shaaaaaa! Kake ji Sarkin bori ya saki fitsari. "Dan Allah kayi hakuri karka sare ni Wallahi na daina". Waaaaa! waaaaaa!  Ihu! Sarkin bori yaci gaba da yi. Sulalewa macijin yayi ya sauka ya nufi wani waje. Sarkin bori yayi ajiyar zuciya Hade da cewa "Wash!!" Sai yanzu ma ya lurada idanuwan da aka zubo mishi kowa bakin sa da Alama dauke yake da tambaya. Wani ne daga cikin masu kidan ya nufi gurin sarkin bori yana tambaya lafiya?. Sarkin bori da jin haka sai abun ya bashi mamaki wannan ya tabbatar mishi da cewa basu ma ga Macijin ba. Hakan tasa ya tashi ya takarkare ya bushe da Dariya.tukun yace "Yau naga sakarkari Wai dama duk borin da kuke baku taba ganin nayi kalar wannan ba?". Kamar hadin baki sukace "Ina fa muka taba gani sarki".  Dan murmushi yayi tukun yace "Karku damu zan koya muku. Yanzu aci gaba da gashi, Aljanar nan karshen ta ya zo, Yanzun nan ta tashi ta gudu daki. Dan haka yanzu zan bita inci ubanta"  Su Umar ya kalla tukun yace, "Kashe ta kuke so ayi ko korar ta?"._




_Da sauri Umar yace, "Haba a kashe 'yar banza kawai, Me ake da wannan shedaniyar Aljana".  Sarkin bori yace, "Ok ku saka kubobin ku rufe gidan dan ma kar ta sama wajen guduwa in na furtumo ta daga daki".  Shiri ya shiga yi ya dauki karin layoyi ya nufi dakin.  A hankali ya dan daga labulen ya leka. Da lekawa kuwa akayi charaf! Da kan aka rike. Nan fa ya fara kokarin kwato kanshi, Da ake faman janshi cikin dakin. Hannu yasa a kufar dakin yana cicije wa amma ina. Sai da aka ja shi cikin dakin da karfi._




_Kii! Ake janshi kasa ana zagaye tsakar dakin da shi. Tun yana shiru har ya fara Ihu! Domin da gudu ake janshi bayanshi na gurzuwa a kasa.  Har yanzu baiga mai jan nashi ba. Ji yayi an kama kafarshi daya anyi sama da ita kamar wani dan akuyan da ake Fida. Kanshi na kasa yana reto,Wata irin Dariya ce marar dadin ji ta kaurade dakin, Magana akayi wacce bazaka ce gata bangaren da ta fito ba a dakin, Cikin wata Siririyar murya "Wai kai  sarkin bori ko".  "Kwarai ni ne sarkin bori".  Ya fada yana cicira ido duk a tsorace yake.  Saukar Tagwayen marika yaje a fuskar Tas! Tas!. Maganar sake ji "Kai ne sarkin bori ko".  Da sauri yace, "A'a Wallahi bani bane, Ni sunana Duna".  Wani Saukar marin yaje, Abunda ya sashi saurin cewa. "Wallahi sunana na gaskiya mamuda". Cikin Tsoro da tashin hankali yake maganar.  Hhhhhhhhhh! "Makaryacin banza makaryacin Woofi! Wai kai sarkin bori kazo ka fidda Aljana ko kama kashe ta kace ko?".  "Aa Yaseen kawai ina fadar haka ne amma a zuciya ta nufina in na ganki in miki Nasiha  ince ki fita ki bar musu gidan su".   Cikin Tsawa yaji Ance Rufe min baki, Dan iskan Karya kawai, Ai naga duk abunda kake da idanuna. wai ni in tambaye kama Me yasa ka farq bori har kazo ka zama sarki".  "Wallahi tallahi Sharrin shedan ne".  Kayau! Aka sake wanke shi da mari. "Munafuki, Ai kai ne shedan yanzu kuma tunada ka tara yaran mutane maza da mata, Kana koya musu wani haukan banza wai bori.Yanzu abunda nake sanka da shi, Shine ka biya su Umar kudin su sannan kuma daga yau ka ajiye bori haka suma yaranka, In kuwa bakayi haka ba to fa ba kai bs zaman lafiya"._





 _"Zanyi kamar yanda kika ce kuma nayi miki alkawari na dai na bori sai dai ma in ringa wa masu bori Wa'azi su bar bori".  Dim! Aka saki kafarsa ya fado kasa, Da ganin haka ya tashi ya fita a guje. Har yanzu yaranshi kidan bori kawai suke ba abunda yasha musu kai. Dakatar da su yayi yaje ya bawa su Umar kudin su yace musu Ai yama kashe Aljanar amma kyauta yayi baya san kudin. Lafiyayun mari aka mar har biyu. "Kan uba! Wannan shine SAKAMAKON ALHERIN? naga dai ni kyauta nayi muku Amma shine zaku mare ni?"  Sukam tsayawa kawai sukayi suna kallansa.  A bayan Umar wata mumunar Aljanar marar kyan fasali mai shegen abun tsoro ta bayyana, Sarkin bori take harara da wasu manya-manyan idanunta, Karkarwa ya hau yi Jiki na bari ya juya. "Daga yau ina so in gaya muku cewa na daina bori Ba ruwana da maiyin bori. Sannan kuma kudin ma ina so in kara tunatar muka da cewa wannan ba hanya mai bullewa bace, Ku tuba ku dai na bori kuma daga yau kamar yanda nayi".  Nan sarkin bori ya fara cire kayan borin layoyi da guruka.  "Shirman banza shirman wofi! Wannan ai maganar banza ce, To in mun bar bori wacce uwar zamuyi. Kaga in bazaka iya ba kawai ka sanfe ni fa dama na dade ina mafarkin hawa karagar nan taka ta sarkin bori Sai yau ga... Marin da aka dauke shi da shine ya dakatar da shi. Juye-juye y fara yi "Cikin ku uban waye ya mare ni?". Gaba daya suka ce basu bane.  "Au! Dan nace bazan dai na bori ba shine k turo Aljana ya mare ni. To bazan dai naba din kuma bori yanzu ma na fara". Ya juya ga sauran Yan uwansa yace "duk wanda yake tare dani ya daga hannu", Kafin kace me gaba daya suka dadaga hannunwa. Da faruwar haka sai ji kake Fass! Fass! Dum! Dum! Mari da kulli ta ko'ina kai musu ake ba tare da sunga mai dukan nasu ba..............._



🤧😪 MURA

*KWANA BIYUN NAN SAI KUYI SORRY. ABUBUWA BIYUN SUN HADE GA DAUREN AURE GOBE. GA WATA MURA SABON KAMU. IN GAYA MUKU WANNAN PAGEN TUN JIYA NAKE RUBUTA SHI. WANI ABUN MAMAKI DAGA NA FARA RUBUTU SAI BARCI YA KWASHE NI.HHH YASEEN KUSAN SAU UKU ANA HAKA. TO DAI IN KUNJI NI SHIRU KU MIN UZURI. DAN YANZU HAKA MURA TAUNANA TAKE.'YAN ZUWA DUBIYA KAR A MANTA DAI DA KAN RAGO. LOLZ*


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy












👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 71-72



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😭😭😭  KING BOY NAYI KUKAN RABUWAR MU  DAKE NI FA BAN SO BA.  RAI NA YANA RADADI NI DAKE GASHI ZAMUYI BANKWANA SAI WATA RAN! 😭😭😭

🚶🏻





 DEDICATED TO YOU 😘 AMÆL  NA GODE DA ADDUO'IN KI GARE NI ZAN IYA CEWA KINFI KOWA KAGUWA AKAN LITTAFIN NAN.🙊 AU! ASHE FA NAKIN NA SANI BANSAN NA WASU BA. 🙋🏻‍♂ JAMA'A NA GODE DA ADDUO'I  BAZAKU LISSAFU BA DANA LISSAFA. 😘 ANA MUGUN TARE 🤝



 👯 NA GODE AL'UMA NA GODE. NA KARA MUKU GODIYA MATAN KU DA MAZAN KU. KING BOY ISAH, GANI INAI MAKU BAITIN GODE WA, KU FADA NA GODE. 👯


👦🏻 🎼🎤 BAN RAINA ADDU'A DA KUKAI TA YI MINI BA  


👧🏻 🎼🎤 MUN GODE 'YAN UWA


👦🏻🎼🎤 NAI KUKA HAR NA ZUBDA 'YAR KWALLA. 


👧🏻🎼🎤 MUN GODEEE



👦🏻🎼🎤 NAGA YANDA MASOYA SUN KA MIN JAJE


👧🏻 🎼🎤 MUN GODE 'YAN UWA



👦🏻🎼🎤 CUTA BA MUTUWA BA HAKAN NA FADA



👧🏻 🎼🎤 MUN GODEE 



👦🏻🎼🎤 DUBI YANDA NA KOMA DUK NA RARAME 🙊... 


👦🏻🎼🎤 NA GODE KU FADA.


👧🏻 🎼🎤 MUN GODE 'YAN UWA💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼


ALHMDULILAHI ALAH KULLI HALIN. 🙍🏻‍♂


*HAUSAWA CUNCE CIWO BA MUTUWA BA.  NA DAWO YAU DAGA JINYAR 'YAN KWANAKI WACCE NAYI. ALLAH YA BANI LAFIYA, SAI DAN ABUNDA BARA A RASA BA. NA GODE DA ADDUO'IN KU A GARE NI. ALLAH YA SAKA MUKU DA ALKHAIRI. NASAN KUNYI MISSING NAWA KAMAR YANDA NIMA NAYI NAKU.* 😘 NA DAWO GARE KU ABOKAI. ACI GABA DA GASHI, 🙄 AMMA FA BA *ALJANAR FATIMA* CE BA TA SHAKE NI. 😘 INA KAUNAR KU MASOYA NA. 🤡





*KARSHEN PAGEN BAYA*

~Kafin kace me gaba daya suka dadaga hannunwa. Da faruwar haka sai ji kake Fass! Fass! Dum! Dum! Mari da kulli ta ko'ina kai musu ake ba tare da sunga mai dukan nasu ba.~



_*N* an fa kowa ya fara neman wajen tsira, Wasu suka nufi kofa wasu kuma katangu suke kamawa da nufin su tsallaka gidan makwabta. Sai dai duk wanda ya nufi kofa kafin ya karasa gurin sai yaji an turo shi da karfi sosai.  Wanda kuma suke kokarin hawa katanga sai sun kama kawai suji an jawo kafar mutum yayo kasa. Umar Muktar da sarkin bori su kadai ne ba'a maka.  Suma kuwa sun sama wajen sunyi tsugunnin biri Najin sanyi.  "Kaiiii!  Kowa ya dakata a inda yake ya kuma saurare ni" Cikin wata muguwar tsawa mai kamada maganar basamude suka ji anyi maganar. Tsi! Kowa ya tsaya inda yake suka hau waige-waige matan kuwa tuni har sun fara kuka suna dora hannun a ka!.  "Nasan zuwa yanzu kunnuwan ku ba abunda suke bukata sai sanin waye mai magana sannan gangunan jikin ku ya zuwq yanzu sun mika wuya neman ceto kawai suke daga duka da mari.  Ba wani bane mai dukan ku kuma ba wani bane mai magana. Sai Aljanar da kuka zo gidan nan domin ku kore ta ko ku kashe ta. To in kun shirya bari in bayyana ku kashe ni". Haba wa da fadar haka suka fara zubewa kasa ba abunda kake ji sai bada hakuri magiya da Neman afuwa. "Munahikan banza wato kunsan bazaku iya ba kuma kuka tarka?, Ai ni a zato na_





_Gaskiya dokin karfe ce Ko ku dubu kuka hau bazai karye ba. Ba’kon munafuki ba na mutum ‘daya ba ne". Dan haka daga yau ina umartar ku gaba daya da ku daina bori in kuwa Bah...".    Da sauri suka fara "Wallahi mun  daina daga yau, Dama  duk abun karya ne".  Hahahhahahaha ta saki wata uwar dariya.  Kofar gidan suka ta bude da kanta. "Na bude muku gidan, Kuzo ku wuce kuma daga nan idan kuka fara gudu bana so ku tsaya a ko'ina sai a garin ku. Ko hutawa ban yarda kuyi ba. Sannan zan dinga bin didigen ku. Duk wanda ya yarda ya koma borin karyar nan to fa kwanan sa ya kare". Hhhhhahaha Tayi dariya, A guje suka ringa fita gaba daya har su umar din.  Sarkin bori a gaba sai tika uban gudu yake, Bayan shi kuma jama'ar sa ne. Su Umar kama tuni sun sabe.  Matai makin sarkin borin ne ya tsaya. "Kai ku dakata Ni fa yaseen bazan iya tafiyar nan a guje ba. Haba kawai asaka mutane gudu kamar wanda 'yan BH  suka tasi gaba. Kunga kawai mu tafi a hankali abun mu, Kai idan muka sama mota ni da kai ma ma zan biya mana kudi mu hau".  Da gama fadar haka suka hau shewa suna fadin "Sai oga".  Alamun dai maganar tashi tayi musu dadi.  A hankali suka tafi suna hira abunsu. Shi kuwa sarkin bori tuni yayi nisa sai gudu yake. Kamar ance wa daya daga cikin su ya waiga baya.  Haba yana juwa kuwa ya hangi wasu bak'ak'en karnuka wanda yawan su sunkai ashirin.  Ko wanne sai fiddo harshe yake gasu da masifar gudu.  Ai bai ko tsaya gaya ma su oga ba, A million ya zabga a guje ya wuce su.  Da ganin  haka sai sauran suka juyo.  Lokacin kuwa karnukan sun kusa karasowa. Duk wanda ya juya yaga karnukan nan sai ya ari ya kare. Kafin dan wani lokacin sai gasu sun isko sarkin bori a hanya. Karnuka na biye da su baya. Ko da sarkin bori ya juya shima yaga mugun abun da ke biye da Jama'ar tasa. Haba shima sai giya ta tsinke. Gudu kamar wanda yaci kafar  barewa._


_____________________



 _Mama Asiya sarfa da marwa take kawai a falo tana jijiga diyar roba tana fadin, "Yi shiru-Yi shiru".  Su Zuwaira suka bushe da Dariya harda dage kafa.  Hauwa bayan ta dan tsagaita da dariyar tace "Aunty Ladiya kuwa ?".  Harara ta watso mata ba tare da Tayi musu magana ba.  Zuwaira tace "Allah ina tunanin ba lafiya, Baki ga wai 'yar babyn Fatima bace a bayan nata".  "Humm Na gani mana yau kam, Ina ga wata sabuwar kauna ce ta kullu tsakanin Fatima da Aunty Asiya".  Nan ma harare ta wullo musu. Daga bayan ta taji 'yar tsanar tace "Yunwa nake ji zansha madara".   "To, To".  Mama Asiya ta fada lokacin ta nufi dakinta da sauri.  Wata sauran madara da tasha jiya ta daukko ta sauke 'yar babyn kafin ta dungura mata kofin a saitin bakinta.  Kafin kiftawar ido taga ba komai cikin kofin, Mamaki ne da tsoro suka ziyarce ta a lokaci daya domin har kara daga kofin take tana leka kasar kamar wata sokuwa.  Shaaaaa 'yar babyn tayi aman duk madarar. Mama Asiya bata san hauwa ba bata san sauka ba sai ji tayi an dauke ta da mari mai karfe. Da sauri ta dafe kumatun ta. Da wata siririyar murya babyn ta fara magana.  "Muguwa azzaluma kinsan madarar ba sanyi shine zaki bani?.  Wato ke gaki 'yar bak'in ciki in sha in mutu, To ta Allah b taki ba".   Mama Asiya cikin kuka-kuka "Dan Allah kiyi hakuri, Naga sanyi sanyi ake shiyasa ma bansa ta...". Rufe min baki yanzu tashi ki goye ni mu fita waje tsakar gida. Dan iska nake so insha". Mama Asiya jiki na rawa ta dauki 'Yar babyn ta goya ta nufi waje. Su Hauwa na ganin ta wuce suka kara kwashe wa da Dariya. Juyowa tayi a fusace "Zanci kaniyar mutum Wallahi, Kaji 'yan iskan karya".  Lokacin ta juyo ta dawo gaban su. "In da wacce ta isa ta sake yi min Dariyar".  Shiru sukayi kowa ta matse Dariyar.  Mama Asiya na tsaye gaban su sai surfa masifa take. Bayan ta taji wani mugun tsunkuli  kamar za'a ciro fatar jikin ta.  Ihuu tayib"Wayyo bayana". Ba shiri ta juya sauri-sauri gudu-gudu ta bar falon._






 _Da isa tsakar gida Sai ganin matar nan tayi tsaye sai harare  ta take, Yanzu kuwa tama fi abun tsoro. Idanunta sun wani kara girma. Girman da ya haura ka'ida. Da wata iriyar murya, marar dadin ji matar ta nuna wani bango wanda wajen yayi dukun-dukun da datti. Fetin Yellow ne amma an mayar da gun ja. "Waya mayar da wajen can ja haka?".  Jiki na karkarwa Mama Asiya tace "Wannan shegiyar fatim...". Da sauri ta rike bakin ta. Kafin sunan ya idasa fitowa. Dum!  Taji dundu a bayanta mai karfi. "Munahika ke wato kamai na gidan nan 'yar marainiyar nan kike likawa ko. To naji ita ta bata gun ni kuwa nace kije ki sa soso da sabulu ki wanke bango ya fita tas!". "Aummm! Ummmm Naaaan Ceee baaaaaa". Inina ta fara yi cike da tsoro domin jin uban aikin da aka tsiro mata da shi, wanda ita kuwa bata saba da wahala ba. Nan dai take tsaye, Ita kuwa matar ta bace. Mama Asiya ta kalli bangon wajen da dan tsayi ji tayi kamar ta fashe da kuka.  Cikin gunguni take cewa. "Shikenana yanzu rayuwa ta zama abunda ta zama. Duk wanda yaga ya fika karfi sai yata zaluntar ka. Wallahi ni dai Allah,..".  Cikin wata tsawa wacce sai da cikinta ya kada. "Keeee wai ba aiki na saka ki ba".  Haba da jin hka mama Asiya ta rude. Da sauri ta nufi wajen tanki ta dauko boki ta cika da ruwa Dubi-tubi ta kai wajen bangon ta ajiye.  Mai gadi na daga can kan dan benchin sa kallanta kawai yake, sai tunani yake ya gaza gano me hajiya take shirin yi. Mama Asiya taje ta daukko wani dan karamin bokitin tasa soso ta kada kumfa duk abunda take 'yar babyn Fatima na goye a bayanta. Sosan ta dora jikin bango ta fara gogawa. Da ganin haka mai gadi ya taso da gudu yana fadin  "Dakata Dakata hajiya".  Tsaye ta mike tana aika mishi wani mugun kallo ranta a bace.  Yana kara sowa gurin ta ya fara cewa "Hajiya me kike shirin yi ne haka. Naga dai alhaji yana iyakar kokarin shi kusan ko wacce shekara sai ya canza fenti yanzu haka ma nasan yana gaf! Da canza wa..."  Hannu ta daga mishi hade da dan juya mai fuska "Ya isa haka dan Allah.  Ko na kira ka ne da zaka zo ka fara jawo min wannan doguwar aya da tun kafin ka shigo gidan nan na harda ce ta harar yafi a kirga?. Malam koma kayi aikin dake ganka ka barni inyi nawa aikin"._





_Da gama fadar haka ta tsoma soso cikin kunfa ta juya taci gaba da dirzar bango. "Haba Hajiya ko dai aikin nan ya zama dole ne ai bake ya kamata kiyi  shi ba tunda gamu a gida". Bata ko kula shi ba sai kara da dagewa tayi ta kara kaimi wajen dirzar bangon ta.  Mai gadi  ya kara matsawa domin ya karba yaci gaba. Wani wawan duka ta kawo mishi, Takuwa ci sa'a ta same shi a wuya gata dama abu ga mai jiki. Mai gadi ihu ya kwada ya nufi cikin falo yana fadar "Jama'a gida ku fito Hajiya ta haukace". Juyawa tayi ta harare shi tace, "Shege dan sa ido kadan nayi ma. Allah yasa ka kuma dawowa".  Hauwa Zuwaira da sauran 'yan kananan  yara duk akayo waje. Su hauwa abun Dariya ya basu amma sai suka basar. "Haba Aunty Asiya miye kike haka kamar wacce ta sama tabuwa, Bango ne fa kike wanke wa".  Zuwaira ce ta fadi haka lokacin da ta dan matsa kusa da Asiya din.  Mama Asiya ko kallanta batayi ba kawai aikin ta take tukuru. Hauwa'u ta kalli  Zuwaira tace "Gaske fa aunty wannan ba abun kyale wa bane kina ganin fa abun yaci gaba, Mama Asiya hauka kawai take a yi gagawar nemo malami y duba ta...". Sakin aikin da take tayi ta nufo Hauwa tana nun mata yatsa.  "Inji uban yace na haukace, Gaya min ko kuma ke ma yanzu inyi kasa- kasa dake a nan wajen".  Da sauri Hauwa ta boye bayan Zuwaira tana bada hakuri.  "To kiji in gaya miki  lafiya ta garas ki  ganni nan  nama fiki lafiya". Ta fadi hakan ne cikin daga murya a fada ce. Harda dakar kirji ya bada sauti Dum! Dum! Ta wani gir-gir za. Zata kwaso wani zancen ta hangi wannan Aljanar a bayan mai gadi ta nufo su.  Haba ai kuwa da sauri ta koma bakin aiki ta.  Wayar Zuwaira ce tayi ringing da sauri ta daga. Abba ne dan Mama Asiya. Wato yayan Ameera. "Hello Mama Zuwaira wai lafiya na kira wayan maman mu shiru, Dama ina so in sheda mata ne gani nan a hanya".  Zuwaira tace, "Eh to da sauki dai, Dan Allah kayi sauri ka karaso".  Da fadar haka ta tsinke wayar suka ci gaba da bawa Asiya baki wai tayi hakuri ta daina Wankin bango. Amma ko sauraren su taki tayi._



^^^^^^^↓



_Ameera, Nasmat, da Asmart ne suke tafe jere an taso daga islamiyya.  Asmart tace,  "Yau bari muje gida nayi target din duk abunda Fatima zatayi mu. Domin wallahi ba sasauci". Nasmat tace,"Ke dai bari, Ni ai nafiki tsara mugunta a kanta. Kinga yau sai nasa ta share duk gidan nan. Sai nasa tayi mopping din duk dakunan gida. Kaya na ma wajen sat 5 sunyi shegen datti amma sai nasaka ta wanke su, Ke in gaya miki da ace ni nake girki da ita zansa tayi duk  wani abu da nasan zai ban wuya".  Dariya asmart ta kwasa, Kafin tace "Gaskiya ke babbar muguwa ce".  Ameera da jinsu kawai take sai yanzu tayi magana cikin murya kasa-kasa.  "Kai Wallahi ku kiyayi kanku da wannan yarinyar in kuwa ba haka ba zaku ci uban ku".  Cikin hadin baki suka ce "Saboda me".  Ameera kamar munafuka ta kalli gabas ta kalli yamma, Cikin rada tace "To in gaya muku wannan 'yar babyn ta Fatima Aljana ce". Da jin haka suka bushe da Dariya. "Ashe ke sai yanzu kika sani?, ai mu in gaya miki ni da Asmart tuni mun san da wanna. Kawai mugunta ne ya hana mu fada muku".  Suka kara sakin wata Dariyar. Asmart tace, "Yanzu ma kuma abunda yasa muke tsara wannan muguntar saboda mun san an yanka 'yar babyn ne jiya a Islamiyya".  Ameera tace "Aiho! Kuma fa haka ne, ai kuwq nima sai na dauki fansar abunda Aljanar tayi min ranar nan".  Lokacin suka karaso kofar gida.  Da sallamar su suka hangi su Zuwaira sai fama da Mama Asiya suke suna so su hanata wankin bang amma taki hanuwa.  Suna karasawa wajen  Zuwaira tace wa nasmat tayi sauri taje gidan ASP ta kirawo shi tace Aljanu sun kama Mama asia.  Da sauri Nasmat ta juya data falla a guje bata tsaya ko'ina ba sai gidan ASP. Da shigar ta kuwa batayi birki ba har cikin falo. Ta shiga Ko sallama babu, A falo ta iske su shida matar sa. Cikin shigar kayan aiki da alama ma tafiya zaiyi. Nasmat daga ka ganta kaga wacce take a rude. "ASP, ASP kayo taimako gida mu ba lafiya".  Asp cik da san yaji me ke faruwa yace, "Ke miye akayi". Cikin rudu Nasmat kamar uwar da danta zai mutu take fadar "Dan Allah ka taimaka ASP kataho mu tafi, Banda bata lokaci karsu kashe ta". Lokacin da Nasmat ta kama hannunsa tana kokarin jawo shi.  Shi kuwa sai kara tatogewa yake. Da sauri cikin hadin baki shida matar sa suka ce "Suwa?"._





_A zabure tace, "Aljanune suka cika gidan mu gasu can kuma sun kama mama Asiya sai azabtar da ita suke". Da fadar haka ASP yasha jinin jikinsa. Domin shi in dai harka ta aljanu ce akwai shi da tsoro ta bangare.  "Aljanu?".  Ya kuma maimata maganar. Nasmat tace "Eh".Zainab matarsa tace, "Mai gida ya naga kamar ka tsorata ne daga yin maganar Aljanu".  Wani shegen yak'e  yayi,  "Haba ke kuwa Zainab kamar baki sanni ba. Kamar ni jarumin jarumai A duk cikin 'yan sanda kice wani  ina tsoro?. Haba dai".  Ya kalli Nasmat yace, "Ke yi gaba gani na  tahowa bari inje in daukko bindiga ta. Kunsan ko Aljanu tsoran bindiga suke yi".  Asp ne ya fadi haka yayin da ya juya ya nufi dakin sa. Zuciyar sa sai sake-sake yake yanda zai tsere. Domin Allah ya gani bazai iya zuwa gidan ba. "To ni in naje ma uban me zan musu?".  Ya tambayi kansa.  "Kai alquran bazan je ba".   Ya fada cikin dan daga murya............................._



☺ ```Wayyo mama Asiya nayi miss dinki 🤣 yau kam kina gasuwa. Ai gwara ki dinga irin wannan aiki ko jikin ki ya sabe. 😆 yau duk wanda yaje kusa da mama Asiya zaici ubansa. Dan na lura neman wanda zata huce haushi a kansa take. 😂 Haba asp karka ba maza kunyi mana.  

😘 I love All my fans. I'm  back``` 🤡





Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy





08144420347






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 73-74



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


😍😍😍

     *ZAMANI WRITERS*  _*SUNAYEN KU A RUBUCE SUKE DAYA-BAYAN-DAYA A ZUCIYATA.  BANSAN YA ZAN BAYYANA IRIN KEWAR KU DANAYI BA.*_  _*KULLUM TUNANIN KU NAKE. NAKAN CE "Ah Duniya kenan, kamar jiya ne nake tare daku yau gashi rashin ta ya nisanta ni daku".   SAI DAI INA MAIYI MUKU ADDU'AR DAUKAKA KUYI KWARI KU ZAMA GANJI, DUK BAKIN CIKIN MASASAKI SAI DAI YA SASSAKA YA BARKU.*_ _*ZAMANI WRITERS ALLAH YA SAKA HASKE A RAYUWAR MU ALLAH KASA MU RINGA RUBUTA ABUNDA ZAI AMFANI JAMA'A.*_


🤠Dan autan ku ya dawo.  A dora daga inda aka tsaya


✍🏻  

 _MARUBUCIN KWARE BABBAN BURINSA SHINE YA RUBUTA ABUNDA ZAI AMFANI AL'UMARSA, KO BAYAN RAISHI.  SHI BA GORIN SHI YA TARA MAGOYA BAYA DA DUMBIN MASOYA BA._



😭😭😭😭😭 

 MATSALAR DA TA AFKU KUKAJI NI SHIRU

*Makon da ya gabata lafiyan ta lau ina tsaye sai gani nayi ta fadi kasa kanta ya bugu da kasa. Tayi tsalle ta kara mirginawa a galabaice. Nan take ni da wasu jama'ar wajen muka nufe ta dan ceto rayuwar ta.  Kafin mu karasa wajen har ta sume. Nan fa na shiga rudu da kidima.  Wani bawan Allah ya kawo pure water aka yayyafa mata amma shiru bata ko motsi balle ta bude ido. Da ganin haka na kara tsurewa. Nan take na fara kuka ina rairawa baitotin kauna. Domin duk wanda ya sanni ya sanni da ita. Duk wanda ya taba ta batawa nake yi da shi. Duk inda muke tare ko barci baya raba mu. Itace abokiyar hira ta. Ba komai ne ke kara burgeni a game da ita ba. Sai ilimin ta zakuyi mamaki idan nace muku duk yaren duniya tana jin shi. Takan koya min karatu takan tunatar dani ta min nasiha.  Ko kadan bata bari raina ya baci. Duk lokacin  da muke tare kuwa har mantawa nake da na kusa dani. Uhmm abun dai da yawa. Sungumar ta nayi da gudu na nufi asbiti mafi kusa.  Nan take akayi emergency da ita. Likitoshi gaba daya sukayi kanta. Da kyar suka samu ta fara bude ido. In takaice muku labarin dai Sai jiya Dr. Tasi ya samu nasarar ceto Rayuwar wayar tawa bayan jinya mai tsanani da tayi.*

 😂😂😂😂😆😆 Nayi missing dinta sosai




 _ALHAMDULILLAH.  ​YANZU DAI JIKIN NATA DA SAUKI. SAI DAI DUK TA RARAME. MUNA KYAUTATA ZATAN ALJANA KURSIYYA CE TA SHAKE TA DAN HAKA MUKE CIGIYAR SARKIN BORI EMERGENCY. WANDA YA GANSHI KO YAJI LABARIN SA_


      *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Asp ne ya fadi haka yayin da ya juya ya nufi dakin sa. Zuciyar sa sai sake-sake yake yanda zai tsere. Domin Allah ya gani bazai iya zuwa gidan ba. "To ni in naje ma uban me zan musu?".  Ya tambayi kansa.  "Kai alquran bazan je ba".   Ya fada cikin dan daga murya.~


_*"M*ai gida tana jira fa" Zainab ce ta kwalo kira. Asp Abdul naji yace "gani nan  bindigar ce ban gani ba".    Cikin dan daga murya.   Ganin bashi da wani zabi ne yasa ya dauki bindigar ya fita. Yana fita falon yaga Nasmat tsaye. "Au! Ke ba cewa nayi kiyi gaba gani nan zuwa ba?". Nasmat tace "Dama kai nake jira ai mu tafi". "Kaji yarinya da rashin kunya wato ke dole sai mun jera kugu, Tukun mun tafi tare?. Ai kuwa abunda bazai yuyu ba kenan, idan kina so inje to fa sai kin fara yin gaba".  Asp Abdul ne ya fadi haka lokacin da yake kokarin zama a kan armchair.  Nasmat da dai taga mutumin da gaske yake idan bata tafi ba bazai je ba sai ta juya tace, "Na tafi to dan Allah brox kayi sauri karsu kashe ta Aljanun basa da imani".  Da fadar haka ta juya ta fita shi kuwa da ganin haka sai ranshi yayi fari ya tashi yace wa Zainab "Yau zan baki mamaki zaki ji jarumtar mijin ki. In gaya miki aljanun  ko irin na ranar nan ne sai na fatataki aniyar su. Sai ni asp na Xainab ba gaba da gaba ba yiiiihuhu". Yayi dan ihu irin na kauraye. Zainab ba abunda take bishi da shi sai "Allah mai gida".  Daga karshe kuma ta bushe da dariya jin  yayi ta kauraye. Sallama yayi mata ya fita hade da cewa "Daga can bazan ko dawo gida ba wajen aiki zan wuce".  "Ok Allah ya kiyaye min kai ya dawo min da kai lafiya jarumina"  shine abunda Zainab ta fada. "Ameen godiya nake gimbiyar mata".  Ya fada kafin ya fita har a zuciyar sa yaji dadin addu'ar.  Yana fita daga gidan ya kalli gabasa wato saitin da gidan su Nasmat yake. Wata hayaniyar mutane yaji da dan karfi-karfi. Ji yayi kamar an cewa. "Kuyi sauri ku kira ASP din". Ai kuwa dajin haka a zuciyar sa yace ai kuwa ko kurata bazaku samu ba.  Yamma yayi a guje. Kafin asmart da aka sake aiko wa ta fito tuni har ya sha kwana. Asmart ta koma gidan Asp tace wa Zainab  "Ance ASP din yayi sauri".  Zainab tace ai ya fita yanzu-yanzu bai je gidan naku bane?".   "Eh kawai Asmart tace ta juya da sauri ta koma tacewa su Zuwaira ance ya taho nan._




_Tsuru su Zuwaira sukayi domin su kam sun rasa abun yi. Mama Asiya sai faman wankin bango take, Duk wanda ya matsa kusa kuwa domin ya amshe sosan sai ta nufo shi da duka.  Su Nasmat kam abun tsokala ma suka samu. Domin da gangan suke zuwa suce ta bashi su tayata dan ta biyo su ko ta xage su suta Dariya.  Ana cikin haka sai ga Abba ya shigo jaye da akwatin sa. Da ganin sa su Nasmat suka kwashi hayaniya "ga yaya Abba! ga Yaya abba!"   Ihun da suke ne ya tayar da Fatima da take  can daki sai barci take. Da sauri Asmart ta karbi akwatin ta tafi kai mishi daki.  Shi kuwa mama Asiya ya nufa sai tambayoyi yake. "Momy lafiya-lafiya".  Bata ko kalle shi ba. "Mama Zuwaira me ya same ta ne haka take abu kamar na yara?" Abba ya tambaya. Zuwaira tace "Kadai gani Wallahi tun dazun muke fama da ita ta bari amma taki, Watakil dai iskokai ne".  Dake Abba ya biyo jikin Asiya shima irin babbar jikin nan gare shi in ka kalle shi a fuska ne zaka gane yaro ne.  Baiyi shakka ko tsoran tunkarar Mama Asiya ba, Hannuwanta ya rike yana mata magana cikin sanyi. "Haba momy miye kike yi haka?. Dan Allah ki bari". Hararen shi tayi "Kai sakar min hannu ko inci mutuncin ka. Miye ruwan ka da abunda nake yi".  Abba yace "Momy bango ne fa kike wanke wa. Bayan kuma an kusa sake fentin ma baki daya".  "Ok wato kaima a mahaukaciya ka dauke ni ko? Kana nufin bansan me nake ba. Ai nasan bangon ne"._





_Abba ya dan marairaice cikin shagwaba. "Please momy ki bani ni zan wanke gun. Ke muje ki huta". Nan ma kin yarda tayi magiya kala-kala yayi mata taki yarda ta bari hakan yasa ya fara janta da karfi.  Ba yanda ta iya ganin zai kadata tace. "Abba nema kake ka balla ni ka cike naci. To naji muje in huta amma fa sai na dawo na karasa aiki na".  Abba.yace "Eh naji muje dai".   Haka suka runkuta Cikin falo su zuwaira, Hauwa, Nasmat, Da dai sauran su suka rufa musu baya. Mama asiya duk ta gaji ji take kamar an bubuge ta. Domin aikin da tayi yau bata taba yin kalar sa ba tunda aka haife ta.   Fatima ce ta fito daga daki  gaban tane ya fadi ganin Abba. Shima kuwa yana ganin ta ya fara hararen ta domin ko kadan jinin su bai hadu ba.  Cikin hanzari Fatima ta dan rissina tace,  "Yaya abba ina wuni?. Kazo lafiya".    Maimakon ya amsa sai ya murtuke fuska rai a bace yace, "Zo nan". Jiki na rawa ta fara matsowa gurin sa tafiyar kamar wacce aka sawa Dabai-bayi.   Tsawa ya daka mata. Hakan yasa ta karasa wajen nashi da sauri. Tana isa bai ko dubi kankantar ta ba ya kwashe ta da mari da karfi.  Dan karfin marin sai da Fatima ta fadi. Ai kuwa ta fasa ihu!.  Da faruwar haka mama Asiya ta Juya wanka wa Abba mari hade da cewa. "Baka da hankali ko so kake yanzu ka jawo mana masifa, Me tayi maka ne da zaka daki yar mutane daga zuwan ka".   Abba cikin bacin rai kamar ya fashe da kuka yace, "Mum yanzu a kan wannan Yar banzar Yarinyar ne kika daga hannu kika mare ni? Abunda baki taba yi min ba. To Wallahi ta shiga uku tunda tasa aka mare ni ni kuwa a kullum kuma duk haduwar da zamuyi sai na mare ta".  Yana fadar haka ya tashi yana gunguni ya nufi bangaren sa.  Mama Asiya na kiranshi amma yake ko waigowa.  Da sauri ta kama Fatima ta dorata a kan kujerar da take kai. Da zanen jikin ta ta share mata hawayen fuskar ta ta shiga lalashi. Ita kanta Fatima abun yayi mugun daure mata kai, Ta rasa dalilin yin hakan.  Haka suma su Zuwaira abun ya basu mamaki yanda Mama Asiya ta tsani Fatima yau kuma ita ce harda lalashin ta._





_Ita kuwa ko kula da su batayi ba sai  wani rawar jiki take gani Fatima sai kuka take tsoro take Aljanar taci ubanta duk da dai ba ita ta mari fatin ba. Fatima kuka take tayi domin fuskar ta sai zogi take. Da sauri Mama asiya ta kunto yar babyn Fatima ta mika mata "Yi shiru Fatima na, Ga babyn ki ma na daukko miki kuma nayi mata wanka da kwaliyya kalli tayi kyau kuwa?".  Fatima sai a yanzu taga babyn nata. Dakatawa tayi da kukan ta wani wangale baki cike da farin ciki ta karbi yar babyn nata tana jujawa. "Mama Asiya ke kika mata wannan kwaliyyar?. Amma tayi kyau sosai".  Itama mama Asiya cike da farin cikin ta rabu da alkakai tace, "Eh ni nayi mata tashi ki kaita daki barci take ji".  Fatima tace to Mama Asiya Ina akwatin kayan ta?".  "Jeki kawai yana dakina anjima zan kai miki". "To Fatima ta fada ta juya ta wuce dakin su cike da farin ciki.  Tana shiga dakin Mama Asiya tayi ajiyar zuciya. " Ita kuwa ko kula da su batayi ba sai  wani rawar jiki take gani Fatima sai kuka take tsoro take Aljanar taci ubanta duk da dai ba ita ta mari fatin ba. Fatima kuka take tayi domin fuskar ta sai zogi take._




_Da sauri Mama asiya ta kunto yar babyn Fatima ta mika mata "Yi shiru Fatima na, Ga babyn ki ma na daukko miki kuma nayi mata wanka da kwaliyya kalli tayi kyau kuwa?".  Fatima sai a yanzu taga babyn nata. Dakatawa tayi da kukan ta wani wangale baki cike da farin ciki ta karbi yar babyn nata tana jujawa. "Mama Asiya ke kika mata wannan kwaliyyar?. Amma tayi kyau sosai".  Itama mama Asiya cike da farin cikin ta rabu da alkakai tace, "Eh ni nayi mata tashi ki kaita daki barci take ji".  Fatima tace to Mama Asiya Ina akwatin kayan ta?".  "Jeki kawai yana dakina anjima zan kai miki". "To Fatima ta fada ta juya ta wuce dakin su cike da farin ciki.  Tana shiga dakin Mama Asiya tayi ajiyar zuciya, Hade da wata doguwar mika tace, "In Allah yaso falke sai kayan sa su tsunke a gindin kaba. Komai kayi hakuri kaga karshen sa".   Da fadar haka sai ganin wannan tsohuwar ta bayyana a gefan ta "Wannan maganar dawa kike?".  Aljanar ta tambaya. Mama Asiya na ganin ta ta wani wuntsila ta saman kujera ta fada kasa. Tana faduwa ta tashi tayi daki a guje._




👺👺👺👺👺👺👺👺👺👺


_Umar tun ranar da wannan abun ya faru ya dai na bin layin gidan sa. Kullum sai dai yaje gidan iyayen sa ya kwana. Yau kusan kwana biyu kenan sun tambaye har sun gaji amma yaki gaya musu me ya ke hana shi kwana gida. Haka yauma sai da Inna ta tambaye shi Rafy Yace mata lafiyan ta lau yaja mashin dinsa ya fita aiki.  Misalin karfe daya na rana Safuratu Cikin sufar Rafi'at Taje gidan su Umar Inna na ganin ta ta tarye ta cikin fara'a Rafy kuwa tun daga bakin kofa tq fara kuka.  Nan kuma Inna ta shiga jero tambayoyi "Aa Rafy lafiya zaki shigo lafiya kuma ki kama kuka. Me  yake damun ki?".  Inna ta kama hannun ta tajata suka sama waje suka zauna. Rafy tayi ajiyar zuciya bayan dan shiru da tayi Inna na tambaya. "Inna Umar ne gaba daya ya fita lamarina tun Shekaran jiya waccan Umar baije gidan ba. Haka kuma bai fada min inda zashi ba.... .......................  ............._


😰 Al qura'an na gaji


☺I'm back My Fans aci gaba da gashi 










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 75-76



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😍😘 DEDICATED TO ZAMANI. ABAR ALFAHARINA  KUN ZAMA YAN UWANA. 💃🏻💃🏻 BANA GAJIYA DA JIN ZANCEN KU KARKU BARI. KO BACIN RAI NAYI IN NA TUNO KU SAI INJI FARIN CIKI ALLAH YA KARA MANA SAN JUNA DA HAKURI DA JUNA. ALLAH YA KARA DAUKAKA YAN UWA NA 🤔




👷🏻👷🏻👷🏻👷🏻👷🏻👷🏻👷🏻👷🏻 *KAMAR YANDA AKE YIWA AMARYA KAYAN DAKI. MUMA MAZA TA KAMATA A RINGA WA ANGO WADANNAN ABUBUWAN SABO DA TSARO.*


KNIFE PROOF


TABARYA PROOF


MUCIYA PROOF


BULLET PROOF


HAKORI PROOF


MAGANIN TAURI


ACID PROOF


MAGANIN RUWAN ZAFI


KAI ALQURAN HAR ALLURA PROOF A HADA 😂😂😂😂😂


*IRIN WANNAN KISA NA RASHIN IMANI.  TO MAZA SAI A KULA A RINGA GOGE CHAT KO TEXT IN ANYI DA BUDURWA.* 😆😂 *KUMA MAZAN AURE A BAR SAKACI DA WAYA HAR UWAR GIDA TA DAUKA. KAI SAN SAMU MA KULLUM KA RINGA CHANGE SECURITY* 😆😆😂💃🏻




        *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Rafy tayi ajiyar zuciya bayan dan shiru da tayi Inna na tambaya. "Inna Umar ne gaba daya ya fita lamarina tun Shekaran jiya waccan Umar baije gidan ba. Haka kuma bai fada min inda zashi ba.~


_*R*af'iat taci gaba da magana. "Lokacin da zai tafi inna bai bar min kudin abinci ba. A kwana biyun nan ni nake sayan abinci yan kudin hannuna duk sun kare. Da na dauka Umar garin ya bari. Sai dazun wata makwabciyar mu take cewa ta ganshi a nan"._



_Inna ta rike baki hade da jijiga kai. "Ahhh! Ni RashidahYanzu Dama duk tambayar ki da nake a gun Umar yana cewa lafiyan ki lau ashe karya yake yi".  "Eh Wallahi Umma rabo na da shi tun jiya".  Inna ta bata rai sosai tace "Shikenan barni dashi zauna har ya dawo".    Rafi'at tace "To"  na ta shiga taya Inna aiki har yamma tayi amma Umar bai ko leko ba.  Umar yana yawon acabar shi suka hadu da Mukhtar shima yana jan yar kurkurar shi.  Nan suka tsaya suna gaisawa Mukhtar yace "Abokina ya kwana biyu bana jin motsin ka ko dai Aljanar kace ke boye ka a gida?".   Umar ya hade gira yace "Kaga bana san wulakanci ya zaka ringa sako mana maganar Aljana ana maganar kirki".  Mukhtar yayi dariya yace "Ai kuwa dole in tambaye ka kai da matar ka dan me bazan tambaye ka lafiyan ta ba?".    Mtseeww  Umar yaja tsaki kafin yace "Ni fa wallahi in kana yi min maganar wannan Aljanar yanzu sai inja mashin dina inyi gaba".    Mukhtar yayi murmushi yace "Aa abun har yayi zafi haka?".   Umar yacr "Ya ma wuce haka domin in gaya ma Tun fitowar da mukayi da Yan borin nan ban sake lekawa gidan ba"._





_Mukhtar ya kece da dariya harda buka kafa. "Kaji matsalar ka fa. Sai mutum yazo ya gaya maka matsalar shi amma ka ringa mishi dariya mtswww".  Umar  ya bata rai. Lokacin Mukhtar ya dan tsagaita da dariya yace "Haba abokina karka ce haka mana. Abun ne   ya bani dariya, Amma kasan me Na samo mafita in dai zaka amince". Umar yace "Rike abunka bana so nasan yanzu zakace ka samo wasu yan borin". Hhhhh Wata yar dariyar Mukhtar yayi tukun yace "Haba ai koni yanzu ba ruwana da wasu yan bori.  Wato naji labarin wani shahararren boka ne wanda ya kware yayi matukar iya aiki.

Domin shi din aiki yake da Aljanu kuma walllahi na yarda da wanda ya fada min sosai, Sannan kuma shi wannan bokan ba zuwa zamuyi mu daukko shi ba, Shi wannan daga munje mun fada mishi shi da kanshi zai kirawo Aljanar ya daure ta yaci ubanta a gaban mu".  Umar yaja dogwan lunfashi da jin wannan dogon jawabi na abokinsa. Kasar zuciyar sa kuwa ta rabu biyu. Wani barin na gaskata zancen wani na karyatawa.  Zuwa can yace wa Mukhtar. "ka tabbata baza'a sake samun matsala ba kuwa?. Gudu nake a je  a kara yin irin na sarkin bori  Duna".  Muktar yayi kasa da murya yace "Abokina ka yarda dani ni sam bani da gurin cutar da kai a rayuwa. Duk Shawarar da kaji ta fito daga bakina to mai amfani ce".  Umar yace "Na fahimta na gode sosai abokina yanzu dai kaga Yamma tayi dan haka ka bari gobe mu shirya muje".  Mukhtar yace "To Allah ya kai mu amma ka tanadi yan karraffa".   Dariya Umar yayi yace "Karka damu abokina ai ni in dai za'a rabani da waccan Aljanar a dawo min da mata ta to ko nawane zan iya kashe wa".  "Su Umar an zama MIJIN ALJANA". Sukayi dariya gaba daya tukun sukayi ban kwana Umar  yaja mashin dinsa shima Mukhtar yaja Adai daitar sa kowa ya kama gaban shi.    Safuratu na gidan su Umar tana jira ya dawo har dare yayi tara ta kusa.  Da har tace zata tafi gida Inna ta hana tace dole sai ta jira Umar din ya dawo sun tafi tare._





_Wajejen karfe Tara Umar ya nufo gida domin yau aikin kawai yake ko abinci yakin saya yayi  wai tara kudin zuwa wajen boka yake. Tafe yake a kan mashin din yana yan wake-wake yana jijiga kai. Da zuwa kofar gida yaje gaban shi yayi wani Dum! Ya fadi bai kula ba ya kutsa kai da mashin dinsa ya shiga har yayi parking  bai kula da mutanen dake zazaune suna kallan shi ba.  Da juyowar sa sukayi ido hudu da Ummansa da kuma Rafi'at. "Innahumin sulemanu wa'innahu bissmillahi rahmanurrahim". ×3  Da sauri yake ambatar ayar zuwa can kuma ya durkushe a gun ya fara cewa "Dan Allah dan annabi ki taimaki rayuwa ta, ki fita daga jikin mata ta. Kin hanani zama a gidan mata ta. Na taho gidan mu nan ma kin biyo ni, Wai ya kike so inyi da raina ne?.  Me nayi miki".  Da jin haka Rafi'at ta  fashe da kuka tace Umma kinji fa ni yake cewa Aljana".  Cikin fushi Inna tace "Au!  Umar wato duk abunda take fada ashe gaskiya ne?.  Kai wanne irin marar imani ne da zaka baro matar ka a gida kazo ka ringa kwana a nan?. Ba dan jaruma bace ai da tun ranar zata biyo ka".  Shi kam Umar gaba daya

Kanshi ya kulle yama rasa abun da zai ce._ 





_Inna taci gaba da cewa. "kalli yar baiwar Allah duk ta rarrame  Ka baro ta da yunwa ashe duk cewa da kake yi lafiyar ta lau karya kake ko gidan baka lekawa?".  Umar dai baice komai ba tunani yake shin wai Rafy din shi ce wannan ko kuwa Aljanar ce. Ita kuwa Rafy sai faman kuka take. Inna ta dafa kafadar Rafy tace "yi shiru kinji share hawaye. Kai kuma maza ka tashi ka koma gida da matar ka. Kuma in na sake ji ko na sake gani ranka sai yayi mugun baci".  Umar kamar yayi kuka ya fara magana "Inna dan Allah kiyi hakuri amma ni gaskiya bazan koma ba Wallahi munafuka ce Aljana ce wannan ba Rafy ba". Rafy na jin haka ta kara Karfin kuka. Tana cewa "Inna kina ji fa ni yake cewa aljana". Da sauri Inna ta rungume ta tana lalashi. Cikin fada da masifa tace "Kai Umar tashi  maza na gaya maka ku kama hanya ku tafi gida kai da matar ka tun kafin rai ya baci bana san jin komai daga bakin ka. Dan iskanci Matar taka kake cewa Aljana?".  Har Umar zaiyi magana Inna ta taso ta nufo shi zata daka da gudu ya nufi waje. Rafy tayi wa Inna sallama ta bishi.  A jere suke tafe har gida ba wanda yace wa wani uffan daga cikin su.  Umar shi kam jikin shi sai rawa yake duk a tsorace yake.  Suna shiga yaga gidan a gyare tsaf! Ko ina ba wani datti. Sai da ma suka shiga dakin abun ya kara burge shi. Dakin sai uban kamshi yake. Komai kuma gyare tsaf babu ko kyalle a yadda a kasa. Cikin wata irin murya mai Dadi da sanyaya  Zuciyar masoyi, Rafy tace "Sannu babyn na da gani kasha rana ka wahalar min da kanka. Dan haka bari in hada ma ruwa kayi wanka tukun kazo in baka abinci kaci". Rafy na fadar haka ta fita tsakar gida dan ta kai mishi ruwa ban daki. Umar suman tsaye yayi gaba daya ji yake kamar ba shi ba.  Har Rafy ta dawo bai ko motsa daga inda yake ba_




_Tana shiga ta kama hannun shi taja shi har bakin kofar ban dakin ta kara kashe murya tace. "Sahibina ni fa ji nake kamar bazan iyayin hakuri in jure har ka fito ba domin idanuwa na Basa iya jure rashin ka na dan lokaci kalilan. Badan wani boyayyen dalili ba dani zan shiga in ma wankan babyna. Luuuu! Umar yaji kamar zai fadi dan dadin kalaman matar tashi.  Wani murmushin jin dadi ne ya kubuce mishi ba tare da yayi niyar yi ba. Bai san lokacin da yace "Karki damu My onlyone yanzu zan fito nazo gare ki".  Yana fadar haka ya shige ban dakin wanka yake yana bangala dariya kama bashi ne mai tsoran Aljana ba. Farin ciki yama mantar da shi cewa akwai Aljana a gidan.  Allah-Allah yake ta fito daga wankan.  Bai dau lokaci ba ya fito sai zumudi yake ya nufi dakin. Yana daga labulan yaga Rafy tayi maza ta kauce kanta hade da Rufe idanu da hannuwa.  Abun ne ya kara burge shi nan take ya fara tuna rayuwar su ta baya irin ta masoya da sukayi shi da Rafy.  A hankali ya dinga takawa har yaje daf! Da ita tana jun nunfashin  shi  a wuyan ta ta baya. "Haba Rafy tawa. Ya zaki nemi mayar dani kahon karfi da yaji?. Idan kika hanani kallan fuskar ki idanu zusu makance. Juyo ki kalle ni Mana baby na".   "Dan Allah kai baka jin kunya na ne?".  Rafy da ta juya baya ido rufe ta fadi haka.  Umar yace "Kunya kuma my ai tsakanin miji da mata ba kunya".  Rafy tace "Kwarai haka ne annurin zuciyata. Amma ai ya kama ta ko gajeran wando ne ka...". Ai kafin ta kai aya tuni Umar yayi waje da gudu sakamakon Zumudin da yake na ya fito ashe ya ma manta ko Gajeran wando bai sa ba Tsirara yake. Sai yanzu da ta fada ma ya lura hakan yasa yayi waje a guje................................._



😧 Umar abun ya kasu biyu. Kenan Muktar ya sake janka gun boka 😂😂😂 Ga Safuratu da Salon So.


AUTAN MARUBUTA KING BOY NEEE












👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 77-78



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😍😘 DEDICATED TO ZAMANI. ABAR ALFAHARINA 



ZAMANI WRITERS BOOKS💻


*ZAMANAWA BOOKS*


Dan Allah tambaya nake yi nan *GIDAN MARAYU* ne?. Kunsan f ni *MARAINIYACE* Amma fa hakan bai hanani *RAYUWAR 'YANCI* ba. Ko kunsan cewa *ABOKIN YAYA NA*. *JA'JIRTACCE* Ne?.

 Karkuyi mamakin ganina a guje *ALJANAR FATIMA* ce ta biyo ni, Tun daga *KURMIN DAJI*.  *ABU KAMAR WASA* Wai So na take. Kunsan kuma *SO MAKAHO NE*. Shiyasa Zan baku *LABARINA*. Kamar yanda na bawa wasu *MATA DA MIJI*.In nayi haka Watakil na rabu da ita *HAR ABADA*. Kunsan fa ni *RENON KAUYE CE*  Hakan bai hanani zama *MARUBUCIYA* Ba. Kunsan abun *HUKUNCIN ALLAH NE*. Allah nake gode wa da bayyi ni da *KAZAMIN BURI* Ba. *HANYAR LIBIYA* Zaku nuna min. Domin can nake so inje Cigiyar *DEEJA DA SANGAMI* , Sai dai ance min garin akwai wata *FATIMAH*  Kuma wai *AHLIL KITAB* ce.Bazadai kuji labarin *BABY KHAUSAR* a bakina ba.  Kafin in tafi dai zan gaya muku cewa *IDAN XURCIYA* ta gyaru to fa komai ya gyaru. 


😍😘💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 We love you Too much  our following☺



     *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ai kafin ta kai aya tuni Umar yayi waje da gudu sakamakon Zumudin da yake na ya fito ashe ya ma manta ko Gajeran wando bai sa ba Tsirara yake. Sai yanzu da ta fada ma ya lura hakan yasa yayi waje a guje.~



_*B*an daki ya koma ya sako kayan shi tukun ya dawo duk kunya ta cika shi. Lokacin da ya dawo tun daga bakin kofa yake jin kamshin abinci. Yana shiga dakin ya iske Rafy zaune tana zuba mishi abinci a plat "Babyna zo zauna in baka a baki".  Yana murmushi ya karasa wajen ya zauna. Kallan ta kawai yake yana kara jin santa a ranshi yana tuna rayuwar su ta baya.  A baki ta fara bashi abincin kamar yaro. Tana mishi hiraraki masu dadi. Har ya koshi,  Tukun ta janye abincin gefe. Shiru  ta biyo baya Kafin Umar yace "My wife ban tambaye ki mana?".   "Ina jinka Uban 'ya'yana".  Umar yace "Dan Allah ina kika samo wannan shinkafar gashi naga miyar harda nama?". Dan murmushi tayi tace "Hmm mai gida kenan. Da kudina na saya kawai dan in faranta maka. Domin nayi miss din dukan ka da zagi".  A kunya ce ya sunkuyar da kai. (Kamar wanda yaje kwartanci gidan surikan shi)  Rafy tace "Dama ina so in maka wata tambaya in ba damuwa babyna".  "Ba damuwa inajinki"  ya fada ba tare da ya dago kai ba. "In zaka tuna lokacin da mukayi aure Mu masoya ne na azo a gani. Ko kadan bana san abunda zai bata maka rai. Kullum cikin hidimar ka nake. A kanka har matsala muka samu da iyaye na. Amma Umar wata biyu baya sai ka mayar da gidan nan kamar gidan kaso a guna. Zuciya ta da take cike da farin ciki lokaci guda kasa kafa kayi facali da shi. Fuskar ka da ta zame min abar bege wanda nake kallo ina jin dadi. Sai ka mayar da ita Abar tsoro, abun gudu. Jikina da ya kamata ya sama kyakyawan kulawa daga gare ka. Amma sai ya zama abun duka. Umar mamaki na shine lokaci daya canjin yazo. Meyasa?_






_Umar yaja dogon lumfashi yayi kasa da murya yace "Ba wani abu yasa ba sai ganin lokacin idan na yarda mukaci gaba da zama a haka zaki rainani ki daina jin maganata. Hakan yasa..."  "Karya kake Umar ba wannan bane fada min gaskiya in ba haka ba yanz in wuji-jiga ka a anan domin Ni ba Rafy dinka ta gaskiya bace".  Cikin wata iriyar murya mai tsoratar wa Sufuratu tayi mishi maganar  cikin tsawa.  Wani iska kamar doguwar guguwa ya zagaye inda take Sai gani yayi ta canza hallitta zuwa wata dodanuwa mai ban tsoro. Mugun tsoro ne ya ziyarci Umar lokaci guda domin har fitsari ya fara kubce masa.  Da baya aya fara ja yana Mata magiya yana cewa "Dan Allah kiyi hakuri Wallahi zan fada miki gaskiya. Zan fada zan fada".   Aljanar cikin murya ba dadi tace "Ka sani cewa in ka yarda kayi min karya na kuma bincika na gano haka Wallahi sai ka gane kuren ka".   Umar ya fara mata magana wanda bata fahimtar ma abunda yake cewa domin rawar darin da yake saboda tsoro. Tace mishi ya kwantar da hankalin shi ba abunda zata mishi muddun bai yi mata karya ba.  Nan ya fara kora mata bayani._





_"Mukhatar dai babban abokina ne tun kafin in auri Rafy muke tare duk wasu abubuwana shi yake ban shawara. To bayan auren mu da wata biyu muna zaman lafiya da matata sosai idan na shigo wasa da dariya irin na masoya abun gwanin sha'awa. To wataran muna hira da Mukhtar sai nake gaya mishi irin zaman mu ni da matata. Ina gama bashi labarin sai ya bushe da dariya yace ashe ni banza ne marar wayo. Na tambaye shi dalili yace min ai wasan nan da muke yi da Rafy shi zai jaho raini a tsakanin mu raini na har abada.  Da na musa mishi amma ya cika ni da zance har dai na yarda yace in gwada Murtuke wa.  nuna mata wasa ya kare amfanin abun da yake gaya min.  Ni kuwa na amince a zuciya nace zan gwada in naga abun baiyi min ba sai in dakata.  To washe gari haka na tashi abu kadan idan tayi min sai in kyare ta idan ta nuna wasa take min nan ma in hantare ta.  A ranar dai na canza mata sosai kuma tun a ranar ta fara jin tsoro na. Hakan yamin dadi nan na koma na fadawa Mukhtar sai yayi dariya yace Sai ma na ringa hada mata da duka zata na min ladabi kamar babanta. To ni kuwa dake na yarda da shi sosai dan ya fada min cewa shima haka yake wa matar shi. 

Da yaga na nuna rashin amincewa washe gari yaja ni gidan nashi. Nan fa naga idan ya mata magana har rawar jiki take. Haka duk abunda za'ayi bata ko iya daga kai ta kalle shi  dan tsoro. A gabana ya bata naira Dari yace ta sayo masara da kayan miya da nama tayi musu tuwo da dare. Ko.gardama batayi ba ta amsa tana godiya kamar wacce ya bawa dubu. Nan na tambaye shi nace ya dari zata isa a sayo masara nama da kayan miya. Nace ai ko kayan miya kadai wanda za'a saya sunfi na dari. Yayi dariya yace ai ita zata cika a cikin kudinta. Dake naga tana sana'a shiyasa ban ko musa ba. Kuma abun ya burge ni  Kwadayin hakan yasa nima na hau hanya. Wannan shine gaskiyar zance._






_Dajin haka Safuratu ta bushe da wata irin mahaukaciyar dariya. Ta dade tanayi tukun ta da kalle shi cikin dariya tace, "Amma Wallahi ka bani mamaki wannan ai shirme ne da rashin hankali. Daga baka wannan banzar shawarar dan karta rai naka shikenan sai ka maisheta jaka kata duka Wai ni kuwa kana santa kuwa?".  "Da sauri Umar yace sosai ma ina santa Wallahi".  Safuratu ta watso mishi wata irin harara da idanuwan ta irin na dodannin wanda in ka kalle su baka shirya ba sai ka sume tsabar tsoro. Da sauri Umar ya kauce kanshi.  "Karya kake baka santa Umar. Domin masoyin gaskiya haka kawai bazai ringa azabtar da masoyiyar sa ba. Masoyi kullum burin sa shine yaga masoyin sa cikin farin ciki. Shin kai kuma kayi hakan?.  Ai ko kadan ba wanda zai yarda cewa kana san Rafy dan haka ni yanzu zanje in sama iyayen ta in basu hakuri kai kuma maza rubuta mata takardar saki".  Durum!  Gaban Umar yayi mummunan fada ji yayi kamar jiri na debar shi. Bai san ma yana san Rafy har haka ba. Tunanin irin wulakanci da cin zarafin da yayi mata amma ta jure take zaune da shi haka yayi. Nan ya zube gaban Safuratu magiya da roko ko wanne kala yazo bakin shi fada yake. Yana hadata da Allah ta rufa mishi asiri karta rabashi da matar shi.  Safuratu tace "wato ma da ita kaci gaba da jibgarta  kana cin zalin ta ko?. To bazai yuyu ba". Kuka Umar ya kama tun karfin shi yana magiya Ita kanta ta tausaya mishi batayi zatan yana san matar tashi har haka ba. Abunda ta lura dashi shine duk abunda yayi bayin kansa bane laifin Mukhtar ne._







_Cewa tayi "Umar bazan rabaka da matar kaba amma in kamin alkawarin bazaka sake mata irin abubuwan da kake mata na wulakanci duka da sauran su a baya". Da sauri Muktar yace ya amince. Safuratu taci gaba da cewa  "Sannan kamin alkawarin zaka rabu da Mukhtar domin Mukhtar munafuki ne duk abunda yake gaya ma ba gaskiya bane domin kamar mijin hajiya take tsoran matar shi yake. Duk lokacin da kaje ka iske shi a waje to laifi ya mata ta koro shi wajen".   Umar zugun yayi zuciyar shi sam.bata amince da maganar da Safuratu tayi a kan Mukhtar na tsoran matar shi ba.  Safuratu tayi wata yar guntuwar dariya tace "Nasan bazaka yarda da zancen da na fada maka ba. Domin ganin yanda matar tashi ke nuna maka idan kuka shiga gidan nunawa take tsoran Mukhtar. take wanda kuma hakan wani plant ne shi Mukhtar din ya hada. Duk wannan zabure-zaburen da yake mata da zarar ka fito a gidan sai ya biya ta kudi dake kasan mayyar kudi ce.  Amma abunda nake so dakai yanzu Bari inje in dawo ma da matar ka gobe zan nuna ma a zahirin waye abokin ka". Kafin Umar ya daga baki Safuratu ta bace nan ta barshi sai cicira ido yake. Ita kuwa can taje gidan kawun Rafy a sufar Umar ta dakko Rafy.  Da kawun nata yace ta bari sai da safe ta shirya amma taki yarda dake ita kant ta gaji da zaman gidan duk da ba takura amma tafi san gidan mijin ta. Kuma tun da taga Umar tasan Safuratu ce kuma tasan akwai wani abun.    Tun a hanya Safuratu ta kwashe labarin duk yanda sukayi har da labarin su sarkin bori ta bawa Rafy.  Rafy tayi dariya sosai a zuciyar ta kuwa addu'a take tana fargaba game da Umar.  Tare suka shiga har cikin daki Umar ba karamin tsorata yayi ba ganin Safuratu da sufar shi sak! Har kayan jikin sa ba banbanci. Da har ya tashi zai ruga ya boyi Safuratu ta tsayar da shi. Rafy kuwa dariya ma abun ya bata.  Domin ita yanzu bata ma tsoran Safuratu ko kadan dan ta gane ba macuciya bace.  Safuratu tace kaga malam ga matar ka nan na dawo ma da ita ni na tafi sai da safe gobe ka shirya zamuje gidan Mukhtar ka gane wa idan ka.  Da fadar haka ta bace Battt!..............................._


Ganin Safuratu ta bace nima nace bari in gwada bacewar.  Batt!! .Lolz


*NA GAIDA SAFURATU. KIN KUSA SAITA NAN GIDAN SAURAN SU MAMA ASIYA*



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy








👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 79-80



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😍😘 DEDICATED TO ZAMANI WRITERS. JINKU NAKE KAMAR YAN UWA NA NA JINI. ROKON ALLAH NAKE YA KARA DAUKAKA DA BASIRA. ALLAH YA TSARE MU SHARRIN MAHASSADA. ALLAH YASA ALBARKA A WANNAN KUNGIYA TAMU.  


💃🏻  Yanzu halin wasu bakin hanga.. »Baki na hanga...


💃🏻 Basu ganin wani yanada burga...

»Yanada burga...


💃🏻Sai su bi daya biyu su zaga..

» biyar su zaga..


🕺🏻 Munsan arzikin mune.. Zaya bimu...


🕺🏻 Inadai lokacin mune za a jimu...  


🕺🏻Kalmomi adansune Tubalin mu...


🕺🏻Harshe zamu tsarkake har ya kaimu.... 💃🏻💃🏻🕺🏻🕺🏻🕺🏻💃🏻🕺🏻💃🏻🕺🏻💃🏻🕺🏻


🕺🏻Kyan lafazinka kwaliyar ka...


🕺🏻Inka biyata sai a dauka...


🕺🏻Sai makiyin ka ma yabika...


🕺🏻Ayita fada dashi a kanka...



💃🏻 Kada harshe ya kai ya barka... 

» Yakai ya barka..


💃🏻Yi tunanin amo ka saka...

»Amo ka saka...


💃🏻 Adabi shi ka gyara littafi 😆

» ya gyara littaf...


🕺🏻Nazarin duniya misali....




          *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Domin ita yanzu bata ma tsoran Safuratu ko kadan dan ta gane ba macuciya bace.  Safuratu tace kaga malam ga matar ka nan na dawo ma da ita ni na tafi sai da safe gobe ka shirya zamuje gidan Mukhtar ka gane wa idan ka.  Da fadar haka ta bace Battt!.~


_Washe gari da safe bayan su Umar sunyi wanka ya sayo musu abun kari sun karya ya  sun zauna suna hira sai gani sukayi Wata yar farar Yarinya ta bayyana a gaban su tana kallan su tana murmushi. Tsorata sukayi dan Umar har zai tashi ya ruga. Yarinyar tace "Nice fa Safuratu *ALJANAR FATIMA".* sai ta yaji haka tukun ya dawo ya zauna suna wa junan su dariya shi da Rafy na tsorata da sukayi.  Rafy tace "Kai dai Wallahi raggo ne kamar ba namiji ba. Ace mace ma ta fika rashin tsoro".  Umar yayi dariya yace "Ah! Ke kuwa ai da gaskiya ta wa zai tsaya kallan ruwa kwado ya mai kafa". Hhhhh Rafy tayi dariya tace "Ai duk Safurat ta bani labarin ka har da kokowa wajen mai shayi nayi dariya sosai.  Ga kuma Sarkin bori mai cire Aljanu".   Gaba daya  suka kwashe da dariya.  Nan dai suka gaisa da Safuratu da take a sufar Yarinya. Tace "To dan Allah Umar ko kai fa. Yanzu zaman a haka ba yafi dadi ba?.  Kuna hirq da matar ka kuna dariya.  Amma da in ka shigo sai ka wani bata fuska kamar wanda aka kai gaban sarki bai karya ba aka mai bulala dari".   Dan murmushi Umar yayi hade da sosai keya yace "In sha Allah hakan bazai sake faruwa ba. Wancan karon ma sharrin Mukhtar ne".  Safuratu tace "Yauwa haka ake so. Amma fa akwai mazan da suke haka wanda a waje_





_Zakaga suna ta bude baki suna  wangale hakora kamar wanda aka wa alkawarin Hajji bana.  Haka in suna hira suta zuba sai kace Anyiwa waziri aku gorin labari. Amma da zarar sun zo gida shikenan sai kaga sun daure fuska maganar ma sai kaga dakyar suke wa matan kamar wanda aka makure akace suyi dole.  Kai wani fa hirar arziki ma bata hada shi da matar shi, balle wasa da Dariya. Wani abu kadan da matar shi tayi masa sai hantara in bata ci sa'a ba harda duka. Kamar dogari a fadar sarki haka suke wa matan  da kinyi kuskure kadan.  Haba wai su me yasa basa fahimta ne aure fa ana yinshi ne dan cika Umar nin ma'aiki sannan ba'a ce ka auri wacce baka so ba. Wai wasu kamar dai kai yanda ka zaunu a shawarar Mukhtar.  Wai suna yin duk hakan ne dan kar matan su raina su.  Haba muma matan muna da hankali fa shikenan dan ina wasa da mijina sai in raina shi a kan me?. Raf'iat ko kina ganin zaki iya raina Umar dan wasan da kuke yi".  Safuratu ta mayar da kallan ta zuwa ga Rafy shima Umar haka.  Rafy tace "Haba-haba  ko da wasa Wallahi bazan rainashi ba. Duk abunda kuwa zan mishi cikin wasa ne irin na masoya domin ni tun a waje lokacin ina budurwa na tsara zamana a gidan miji kamar yanda ko wacce mace take tsara nata. Tsarina zan Girmamashi zan kuma maida shi abokin wasa na duk da kuwa nasan cewa shugaba na ne. Amma a nawa tunanin wasa tsakanin ma'aurata na kara dankon soyayya a tsakani. Amma fa ba mugun wasa ba wasa dai irin na masoya. Kamar yanda Addini ya Halarta mana._






_Sannan wasan yana taka muhimmiyar rawa ta bangaren Fushi. Wani abun idan nayi mishi daga naga alamun yayi fushi sai in mayar da abun wasa. Haka wani lokacin ko mun fara cacar baki mun fara fada sanadin wasa da muka sabayi sai kiga abun ya juye ya koma wasa. To ni dai gaskiya bana tunanin zan wasan da muke zaisa in raina shi ko da yaushe zan bawa mijina girmanshi in lokacin wasa ne ayi. In kuwa ba lokacinshi bane a bari".  Raf!  Raf! Raf!  Safuratu ta fara tabi tana kallan Rafy tana murmushi. Shima Umar tafa mata yake.  Safuratu tace "gaskiya kin burge ni kuma ni banga kuskure a maganar ki ba.  Umar bari muje gidan Mukhtar yau zaka sha mamaki. Karbi wannan abun ka hadiye".  Hani farin abu kamar magani ne ta mika masa ba gardama ya karba ya afa baki. Yana hadiyewa ya bace wa Rafy bata ganin shi.  A rude ta mike "Innalillahi, Ina Umar din".  Umar yana zaune agun yana kallanta amma ita bata ganin shi. Umar da baima san ya bace ba'a ganin shi ba ya kalli Rafy da duk ta rude tana cewa Safuratu ina yake. "Rafy miye haka gani nan a gaban ki ki ringa cewa wai ina nake".   Rafy kam bata ji maganar shi ba._






_Dariya Safuratu tayi Ta kalli Umar tace "Ai yanzu ba wanda zai ganka kuma ba wanda zaiji maganar ka daga Allah sai ni. Yanzu haka ka bace Rafy bata ganin ka. Maganar da kayi yanzu ma bata ji ba". Mamaki ne ya kama Umar. Safuratu tace wa Rafy "Ke ma kwantar da hankalin ki ga Umar dinki nan ba sace shi nayi ba. Yanzu zamu tafi gidan Mukhtar ne da shi to har ciki zamu shiga dan haka bazasu gan mu ba. Mun tafi sai mun dawo".  Da fadar haka sai suka bace ita da Umar din sai gasu sun bayyana a gidan Mukhtar.  Da bullowar su suka ji Murja a daki sai masifa take surfawa Umar hakan yasa Rafy tace su karasa cikin daki.  Umar kam duk a tsorace yake dan gani yake kamar Mukhtar zai ganshi.  Sai da suka suka shiga dakin ya tabbatar da cewa ba'a ganin shi Nan sukayi tsatsaye suna kallan su Mukhtar din.  Mukhtar ne zaune gefan gado Murja matar shi a gefan shi ta rike kugu cikin daga murya da kakatu tace "Kai malam tun dazun magana nake maka amma kayi shiru kamar ina magana da dutse. Kasan dai cewa gidan nan ko kwayar hatsi bama da shi balle kace ayi dan banzan kokon nan da ka saba cewa ayi a karya da shi._






_Dan Wallahi yau bazan karya da koko ba. Duk kayana na saide-saide mun cinye su baka  bani kudina ba. Gashi yanzu ina so inje kasuwa inyo sari amma ba kudi a hannuna duk suna gunka.  Dan haka tattaro min gaba daya kudina rankatakaf! Ka bani in yaso karka bada kudin Abin karyawa din ma".   Duk masifar da take yi Mukhtar yayi shiru bai ce kala ba. Sai yanzu ne ya dago cikin sanyin murya yace "Haba Murja ni fa mijin ki ne ko kin manta ni shugaba ne a gare ki kike daga mun murya haka. Wallahi kiji tsoran Allah Murja".   Ya nuna ta da yatsa.  Makr yatsar tayi da hannu ta rike baki "Iyeeeh daga bani kudina sai wa'azi?.  To Allahu akbar amma fa in kana so wa'azin da kake ya dinga shiga kunnena to a bani kudina".  Mukhtar tsabar jin haushi kamar wanda zaiyi kuka yace "Murja ni kike bigewa hannu?".  A hatsale tace "Au! Tambaya kake kenan, Baka ma yarda da hakan ya faru ba kenan".   Bai bata amsa ba ya tashi da niyar ya fita waje. Ya fara tafiya kenan ta shaki wuyanshi ta baya ta wani jayoshi. "Malam ba inda zaka, Wallahi sai ka biyani kudina".  Nan fa Umar ya saki baki yana kallan Muktar a zuciya yana jin haushi abunda ya sashi yayi wa Rafy.  Mukhtar da aka shake ma wuya ta baya. Dakyar ya samu ya markayi hannunsa baya ya kwace cikin fushi yace "Cewa nayi bazan baki kudin ki bane?. Inace dai sai naje na samo tukun zan baki?"._






_Murja tace "Kaga malam ni yanzu nake san kudina domin kaji wani yaro can ma yana a bashi mai. Amma babu duk ka cinye min kudi a bashi. Yanzu fa dubu biyar nake binka".  Muktar yace "Naji yanzu sakar min riga Yau yau zan biya ki kudin ki in dai huta da jaraba da masifa".  Zazaro ido tayi Cikin daga murya tace "Ni kaks cewa masifafiya?.  Ni kake cewa jarababiya ko Mukhtar?".  "Ni fa ba dake nake ba".   Sakar mishi riga tayi hade da cewa. "Jeka ga hanya nan. Kuma Wallahi tallahi yau in baka kawo min kudina ba zaka ga jaraba da masifa da kake fa. Badai ni kake cewa masifafiya ba. Hmm".   Mukhtar bai sake magana ba waje kawo yayo. Zuciyar sa sai kuna take._






_Yana fitowa su Safuratu suma suka biyo shi baya.  Umar ya girgiza kai yace "Kai amma gaskiya ba karamin rashin hankali nayi ba. Wai ashe haka matar Mukhtar take mishi amma shine har da bani shawara wai kar matata ta rainani. To dan Allah wane raini yafi wannan?.  Kai gaskiyar masu iy magana da sukace (RASHIN SANI *YAFI DARE DUHU*).  Wallahi zanso inga ya zasu karata in bai biya ta kudinta ba".   Safuratu tace "ka dai gani da idanka. Idan kana so kuma ni zan iya hana shi kawo kudin".  Uamr yace "Tayaya zaki hanashi".   Gaba ta shiga ta fara tafiya. "Muje kaga ta yanda zan hanashi ya kawo kudin".  Baya suka bi Umar har wajen ogan su inda yake karbo napepk din.  Nan fa Safuratu ta juya zuwa wata jabebiyar mata. Ta shiga yar kurkurar ta zauna gaba daya ta cika kurkurar in aka cire inda umar zai zauna baza'a samu wajen zaman wani ba. tace wa Umar ya shigo.   Baiyi gardama ba ya shiga.   "To kaga yau  a nan zamu ta yawo ba wanda zaima tsayar da shi in yaga mutane a ciki".  Umar ya girgiza kai shi dan a tsorace yake. Dan girman matar yayi over. Mukhtar zuwa yayi ya dan kakabe kurar yar kurkurar ya hau ba tare da yasan Su Umar na ciki ba.  Haka yata zuba gudu yana bi lungu da sako ko mace daya bata tsayar da shi ba. Tun abun bai damunsa har ya fara damunshi. Domin yaga abun ba kamar yanda ya saba ba._







_Haka ya ringa wuce mutane wanda kuma ya tabbata Napepk suke jira amma da sun ganshin suka hangi Safuratu sai suki tsaida shi.  Abun har ta fara bashi haushi ya fara zage-zage. Wasu yan mata ya hanga su biyu sun ci kwaliyya abun su sai kallan hagun da dama na titi suke. Alamu sun nuna cewa abun hawa suke jira. Muktar ya kalle su yace. "Matsala ta da mutane kenan wasu yan rainin wayo ne Wallahi.  Yanzu wadancan fa da gani Napepk suke jira amma ina zuwa sai kaga sun ki tsayar dani. Amma bari mu gani".  Ta gaban su yaje ya wuce ganin wannan katuwar mata yasa basu tsayar da shi ba.  Muktar har yayi gaba kuma cike da takaici yayo baya. Diiiiiit!  Ya musu hon hade da cewa "Tafiya ne?".  Dayar tace "Eh tafiya ne ya akayi?".   Yace ok to ku shiga mujr mana ina za'a kai ku?".   Yar siririyar cike da masifa tace "Malam bamasan rainin wayo ya Napepk dinka  cike kuma zaka zo kana cewa wai mu hau.  To nan ina xamu hau?.  Ko kan wanna tikekiyar matar mai kama da giwa zamu hau?".  Tana fadar haka suka kwashe da dariya ita da kawqr ta. Safuratu kuwa dajin abunda suka fada sai ya bata mata rai. Kanta ya juye ya koma na giwa. Yan matan nan na ganin kan mata ya koma giwa. Yar karamar ta banke Mai dan jikin ta fadi itana ta wuntsila tsukakun kayan jikin su Bai hana su zabgawa a guje ba.  Dan ko tsayawa tata re sket ba wucce tayi.  Takalman su kuwa tuni kowacce a ciki ta yi wulli da nata dan tafiya da su bata lokaci ne. Wani gida suka shige a million suka fada daki. Matar gidan na gani  haka ta bisu daki itama a guje ta turo kyaure._




_Mukhtar sakin baki yayi yana kallansu. "To su kuma wannan me suke nufi?.  Ko dai maciji suka gani a ciki".  Juyawa yayi baya ya leka har karkashin kujerar baiga ko kiyashi ba.  Bai aminta ba. Ya fito sai da ya zagaye Napepk din ya duduba baiga ko mai ba. Yaja tsaki ya hau Napepk dinshi yayi gaba............................. ...   .........._




😰😰😰

     TASHIN HANKALI 

                 😰😰😰



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 81-82



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻


            ​GIDAN MARAYU​

🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻🙎🏻


          _Story&written by✍🏻

          ​​Beauty Queen​​💋💋


​ZAMANI WRITERS ASSOCIATION


 *INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIN RAJUN*


KULLUNAFSIN ZA'IKATUL MAUT.  

 *UMMU RUMMA,* WACCE KUKA FI SANI DA *BEAUTY QUEEN* ALLAH YAYI WA YAYANTA MAI SUNA *ABDURRAHMAN* RASUWA.  MUNA ROKON ADDU'A DAGA GARE KU ALLAH YA JIKAN SHI YA MAI RAHAMA. ALLAH YASA ALJANNA CE MAKOMARSA AMIN.  SU KUMA ALLAH YA BASU HAKURI DA JURIYAR RASHIN SHI.  



       *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Juyawa yayi baya ya leka har karkashin kujerar baiga ko kiyashi ba.  Bai aminta ba. Ya fito sai da ya zagaye Napepk din ya duduba baiga ko mai ba. Yaja tsaki ya hau Napepk dinshi yayi gaba.~ 


_*H*aka yaci gaba da zaga gari amma shiru.  Wata mata ce ta tsayar da shi har ya tsaya kuma sai taga su Safuratu tace, "Sannu ko baiwar Allah ai ban ganku ba".  Safuratu tace "yauwa sannun ki dai". Mukhtar yace "Yauwa hajiya shiga muje ina za'a kaiki?".   Matar a fadace tace "Kan cinyar ka kake so na hau ko ina?.  Amma kai dan rainin wayo ne ma wallahi kasan napepk dinka ta cika shine ma har ka tsaya".   Muktar  juyawa yayi set din baya shi dai ko kwaro bai gani ba. "Kinga malama ba rainin hankali nace kiyi min ba. Kinga mutum ne a ciki da zakice wai a ciki take. Kinga dallah malama ware kama gabanki tunda ba hawa zakiyi ba".  Jan Napepk dinshi yayi cike da haushi.  Can wani tunanin ya fado mai. Wanda yasa ya juya kan napepk din ya nufi gida.  Da isar sa ya sauka ya shiga ciki. Su Umar suka saukko suka bishi.  Murja na ganin shi ta haushi da masifa wai ya cika lalaci tun yanzu har ya dawo. Nan yace ta saurare shi dakyar ya samu ta dakata da masifar.  Nan ya fada mata cewa tunda ya fita gashi har larfe sha biyu ta kusa amma ko mutum daya baiyi ba. Nan  fa ta sake rikicewa wai wannan karyar banza ce yake fada. Ai ba yanda za'ayi yace wai har yanzu bai kama ko biyar ba. Tace "Wannan ai salon munafirci ne. Wato so dai kake ka hanani kudina to wallahi baka isa ba. Tashi ka koma"._





_Mukhtar yayi ajiyar zuciya yace, "Ni fa kinji matsala ta dake kenan. Ke gaba daya baki sasauta mun, Ji yanda kike masifa dan Allah kamar ba da mijin ki kike magana ba. To ni dama ba wani abu ya kawo ni ba. Kamar yanda naji ance idan mutum basuyi rabuwar arziki da matar shi ba idan ya fita kasuwa bata mishi dadi. Shiyasa na dawo domin mu fahimci juna amma kin wani hau masifa".   Murja na jijiga kamar wacce aka kunna tace."To wace irin fahimta kuma?. Ai ni in ba kudina ka kawo min ba ba wani zancen fahimta dan ma kaji. Ni in ba Dumus! Naji ba da matsala".  Takaici ne ya cika Mukhtar yayi waje ba tare da yace mata uffan! Ba.  napepk ya dawo ya shiga  yana surutai. "Wai matan yanzu me yasa basu da lura ne. Haba mutum yaje yata fama wani idan yaje neman abincin ma har duka yake shi, Amma daga karshe in ka dawo gidan baza'a kwantar ma da hankali ba. Ji wannan matar wai na dawo mata da laluma amma ta wani dau zafi. Da ace zan samu mata kamar Rafy matar Umar ai Wallahi da yau-yau zan bata takarda".  Baki Umar ya rike jin abunda Mukhtar din ya fada. Nan take tsanar sa ta karu a zuciyar sa dan ji yake kamar ya buge sa._






_Mukhtar ya koma ya hau napepk din ya sake dannawa cikin garin.  Har wajen karfe daya yana yawo amma  ko an tsayar da shi ma sai ace taje abun duniya ya isheshi nan ya sama wata inuwa ya faka hade da cewa "Yin barci na ma yafi mini da inta kone maina a banza. Nan ya fiddo abun sallah ya shimfida ya dan ringesa.  Yana ta masifa shi kadai. Bai dade da kwantawar ba barci yayi gaba da shi. Su Safuratu kuwa suna cikin. Wasu gayu ne guda biyu dagani kasan yan shaye-shaye ne. Gudaya ya kalle guda yace "Baabah yau fa nake gaya ma dawa tayi nama. Kalli can".  Ya nuna mishi Mukhtar dake kwance yana barci.  Dayan yace "Kambuh!  Laili yau Allah ya kai damo ga harawa.  Kaga zagaya ta can ka dubo mana key nasan yana jikin shi".  Wanda ake kira da Muhsan yaje jikin Mukhtar ya fara dube-dube ko zaiga makulle.  Can ya hange shi a Karkashin kan Mukhtar a hankali ya zare shi.  Ba tare da Mukhtar ya farka ba. Safuratu tace Umar ya sauka ya jire Mukhtar ita zata bi barayin. Da sauri ya sauka.  Su kam barayin basa ganin su Umar. Yana ciro makullin ya mikawq abokin nasa wanda shi tuni har ya dare napepk din. Ai kuwa ya tayar yaja ta a guje.

Duk abun da ake Mukhtar ko motsawa baiyi ba. Barci yayi dadi. Da gudun yake jan yar kur-kurar sai da yayi tafiya mai nisa dan har ya fara fit daga garin tukun ya ratse ya sauka daga titi yabi wani jan birji nan ma sai da yayi nisa sosai ya kara kutsa ta cikin daji. Sai da ya shiga cikin wasu bishiyoyi tukun ya tsaya.  Kallan juna sukayi kamar hadin baki kuma suka kwashe da dariya. "Kai baabah lalai yau dawa tayi nama yanzu ya kake gani zamuyi?".  Dan siririn ya tambaya wanda ya jawo kurkurar. "Ai nake gaya ma abun duk bige ne bari zamuyi kawai dare yayi sai muyi wuf! Mu shiga da ita gari mu shigar da ita". Dan siririn mai suna Rafson yace kai mutumina nake gaya maka in dai muka shigar da wannan. Kaga na daya Zan sayi kwalin sigari giya wiwi Kai Wallahi har koken sai na saya".   Muhisan yace "kaji banza gara Kai duk a yan bushe-bushe kawai zaka kare.  Ai ni nake gaya ma zuwa zanyi gidan magajiya wuuuuyyif!  (Yayi fito)  ta dorani a hanya ka dai gane".  Ya daga mishi gira. Safuratu kallansu kawai take suna hirar rashin hankali. A zuciya tace yanzu su wannan shikenan fa sun bata rayuwar su da shaye-shaye ga abun har ya kai ga sata. Yanzu haka kuma in ka bincika rashin aikin yi ne ya jefa su".

Sai wajen karfe uku Mukhtar ya farka.  A gigice ya tashi ganin ba kekenapepk dinsa............................._


*Ayi Hakuri dan tsito ne*


😳😂😂  

Su malam Rafson fa an dauko babban kaya lalai yau dawa tayi nama. Dan kura da kallabin kitse😆


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 83-84



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😍 DEDICATED TO YOU 👇🏼👇🏼😍



✍🏻 SALMA QUEEN ✍🏻


✍🏻 ZUWAIRA MADARA ✍🏻


✍🏻 ACTION BABY ✍🏻


✍🏻 BEAUTY QUEEN ✍🏻


✍🏻 FATIMA(UMMU BASHIR) ✍🏻


✍🏻 AUNTY MAIMUNA ✍🏻


✍🏻 RABI'AT SHU'AIBU ✍🏻


✍🏻MMN NAJWA✍🏻


☺ NA ROKI ALLAH YA KARA MUKU BASIRA ALLAH YA TSARE MIN KU. ALLAH YA KARA FIKIRA DA FASAHA☺




        *KARSHEN PAGEN BAYA*

~A zuciya tace yanzu su wannan shikenan fa sun bata rayuwar su da shaye-shaye ga abun har ya kai ga sata. Yanzu haka kuma in ka bincika rashin aikin yi ne ya jefa su". Sai wajen karfe uku Mukhtar ya farka.  A gigice ya tashi ganin ba kekenapepk dinsa.~


_*G*aba daya a gigice ya tashi nan fa ya dora hannu kamar ya fasa ihu!  Waige-waige kawai yake yana rasa abun yi. "Anan fa. A nan nayi parking".  Juyawa yayi wajen  wani mutum dake taho wa. A rikice ya taryi gabansa "Malam dan Allah baka ga wanda ya daukar min  napep ba?".  "Ban gani ba wallahi".    Cewar mutumin da Mukhtar din ya tambaya. Durkushewa Muktar yayi ya kama kafar mutumin."Dan Allah dan annabi in kaga wanda ya dauka ka taimaka ka gaya min please wallahi ba tawa bace sojan haya na daukko".   Mamaki ne ya kama shi. "Kai bawan Allah wai napepk waya ce ko wani karamin abu da za'a sata ba tare da ka gani ba?. Abun naka rainin wayo ne ma". Yana fadar haka ya fizge kafarsa yayi gaba.  Mukhtar haka ya ci gaba da taryar mutane yana tambaya amma kowa cewa yake bai gani ba. Duk abunda yake Umar na kallan shi. Amma shi baya ganin Umar din. Mukhtar kamar yayi hauka duk mutumin da ya gani yaro ko babba mace ko namiji sai ya tambaya. Da dai yaga abun bayayi sai kawai ya sama waje  ya dora hannuwa a kai ya fashe da kuka. Cikin kuka yake cewa."Yanzu ya zance wa Bash da wanne idanu zan kalle shi ince an satace Napep dinshi tama za'ayi ya yarda". Kara fashewa yayi da kuka. Umar  ya tausaya mishi sosai a nan gurin duk da yasa Napep din bazata salwanta ba.  Mukhtar nan ya zauna sai kuka yake yana tunani ya saka wannan ya kunce ya saka wannan. Har yamma tayi magariba ta kawo kai suna wajen. Can dai Mukhtar ya mike ya nufi gidan yana tafe yana yan surutai yana zubda hawaye kamar wanda akawa mutuwa.  A haka har ya karasa gida sallama ciki-ciki ba'a ko ji yayi. Murja na daki batama ji sallamar sa ba. Waje ya samu ya zauna yayi tagumi. Shi kam tunanin ya zaicewa Bash. (Mai napepk) din yake. Nan fa ya fara zance har yana fitowa. "Yanzu Inje incewa bash duk yau ban yi ko sisi ba kuma ina barci an sace Napep din.  Kash! Sam! Bazai yarda ba wallahi"._







_Murja ce ta fito daga daki tana yan wake-wake, Tana ganin Mukhtar tace. "Au! Malam dan karka bani kudina shine kazo ka wani zauna a waje?".  Karasawa tayi gaban shi tana zuwa ta wani gyara dan kwali daurin (Ture kaga tsiya) ta rike kugu da hannu daya.  Dayan kuwa ta mika wa Mukhtar hade da kauce kanta ga barin kallansa. Alamar ba mutunci. "Malam bani kudina bana san wani waye ya mutu waye ya tashi. Dan Wallahi duk wani plant dinka na gama gane shi". Cike da takaici Mukhtar ya kalle ta a zuciya yace " Wai wannan mata ta ce. Bata ma lura da irin halin da nake ciki ba".  Hawaye ne suka gangaro mai a fuska.  Murja ganin taji shiru yasa ta kalle tana ganin hawaye a fuskar shi cikin kwaratsi tace. "Dole ka zubda hawaye. Wai ance Saurayin budurwarka ya mutu. Kukan munafurci kenan ma to wallahi baka isa ba malam. Yau naga sadodo wai harda kirkirar hawaye, Eh lalai Malam Mukhtar zaka iya film daga bani kudina sai  hawaye to a nufin ka. In durkusa gabanka ina share ma hawayen ina baka hakuri ince kabar kudin ko yaya?. To Wallahi bari kaji yau in baka bani kudina ba bar ganin dare yayi wallahi sai na dauki wani abu naka wanda yayi kudina na sayar na dauki kudina".  Mukhtar magana kasa-kasa yace "Haba murja me yasa kike haka ne. Baki san damuwar mutum ba kizo ki kara mai wata damuwa. Ko so kikr hawan jini ya kamani ne in fadi in mutu".   "Wannan kuma kai ta shafa. Ni kudina kawai nake bukata in baka bani ba kuma kaga tashin hankali harda rufu'a Wallahi".  Muktar yace "Murja An sace napep din da na daukko sojan haya".   Murja ta dan sasauta murya kamar abun kirki. "Kaico!  Napepk din aka sace ashe ai ni baka gaya min ba tun da wuri in maka jaje.  Allah yasa a ganta ya tsare gaba. In ba'a ganta ba Allah yasa mai ita ya maka afuwa".  Mukhtar yace "Amin yanzu abun..".  Kafin ya karasa ta taryi nunfashin sa. "To an sace napep nayi maka Jaje kumaa gode wa Allah da ba kudina ne a ka sace ba.  Da danaji kana zancen sacewa har gabana ya fara dukan uku-uku na dauka  kudina aka sace.  Tunda basu ne ba Alhmdulilah. bani kudina in adana kar suma garin sakaci irin naka kaje a sace. Atoh! Wanda ya bari aka sace napep ai kudi bazasuyi wahalar sata a gunsa ba. Bani kudina malam"._







_Maganar tayi mugun bata wa Mukhtar rai ji yake kamar ya tashi ya hauta da duka. Matsalar daya yasan ba abunda zai dauka a jikinta. In ma fadan ne bata kashi za'ayi. (Ragas).A zuciyarsa yake tunani cike da tsanar murja "Wannan wai wace irin mata ce. Anya kuwa Murja ba shedaniya ce ba. Kai ai ko shedan ne ke bina kudi na gaya mishi abunda ya faru ya daga min kafa...".   Shirun da taji yayi yana tunani ta wani daka mishi tsawa. "Kai malam ka bani kudina wallahi tun muna sheda juna".  Nan ma shiru yayi dan yama rasa abunda zaice mata. Kukan kura tayi ta chakumi wuyan rigar sa. Ta fara magana dan masifar kamar mai shirin yin kuka gashi da karfi take maganar. "Mukhtar yau fa ba mutun ci Wallahi sai ka biyani kudina. A take a nan ko kuwa yanzu in maka lahani Wallahi".   Mukhtar kokarin kwacewa yake daga shakar da tayi mishi amma ya gaza. Murya a makure yace. "Sakarni ni yanzu ba ko kwandala a jikina in na saaamu zaaan baaki".   Maimakon ta sake shi sai ma ta kara shakar shi. Nan shima ya fara kokarin shake nata wuyan jin tana kokarin ta kar shi. Amma ina ya shaketan amma a banza.  Ihu! Ya fara kugawa.  Wani makwabcin su ne ya shigo sa gudu yazo yaga abunda ke faruwa dakyar ya kankare mukhar a hannun Murja. Nan ya tambayi murja me ke faruwa ta gaya mishi.  Tambayarta yayi nawa ne kudin tace dubu biyar. Da sauri Mukhtar yace karya take hudu da dari biyar ne. Ibrahim ya zaro Dubu biyar ya mika mata. Yana bata Mukhar yace "An biya ki kudin ki to na sake ki saki daya. Zama dake ai bala'i ne".   Murja cikin nuna rashin damuwa ta wani jujuya kudin dake hannunta tayi guda yiiiriiyirri. "To dan ka sake ni sai me. Kai ne a kasa wallahi domin nice rufin asirin ka kuma  dan kaji in gaya ma saki daya ba inda zani. In ka cika dan halak ka karashe biyun".  Mukhtar har ya daga baki da sauri Ibrahim ya rufe mishi baki da hannun yaja shi waje.  Nan suka bar Murja nata masifa.  Duk abunda ya faru Umar na gani sai dai bashi da ikon rabawa ko magana domin yana cikin plan din Aljana._



********************

_Lokacu misalin karfe takwas na dare ne amma shiru kake jin dajin in ba kukan tsuntsaye ba shima ba sosai ba.  Kasancewar ba farin wata rudum! Wajen yake duhu in kana tsaye bazaka ga abunda ke kasa ba. Muhisan da rafson ne jingine da yar kurkurar ba abunda suke sai busa sugari. Can kuma Rafson ya kalli Muhisan yace "mu tafi yanzu mana".  Muhisan yac "Kai mahaukaci ne naga alama. Yanzu fa dare baiyi ba bar ganin duhun nan sauyin yanayi ne yanzu haka ko tara batayi ba".  Shiru Rafson bayi magana ba. Daga cikin Napep din Aka zuro hannu aka dan ja kunnen Muhisan. A fusace ya juya ga Rafson yana mishi jaraba wai ya daina kama mishi  kunne. Shi kuwa yace baima san anyi ba. Kafar  Rafson yaji anja daga kasar napepk din da sauri ya janye kafar hade da cewa "Baabah akwai matsala fa. Kafata naji ana ja daga karkashin nan". Muhisan yace "Kai dallah can rufe muna baki to me kake nu..".  Kafin ya rufe bakin yaji anja tashi kafa"Kuturun uba! Bari inga uban miye ke ja min kafa".  Durkusawa yayi da nufin lekawa Wani abun kulli aka mai a duron baya wanda ya bada sauti Dum!. "Kai! Kai! Yau banga mai hanani inci kut... Ubanka ba a jejin nan. Me nayi ma da zaka min dundu"?. Muhisan ne ke fadar haka yana dagowa ya wanka wa Rafson mari shima kuwa ya rama nan fa suka hau kunce. Shuuuuuuuuuu! Sukaji wata irin kara mai karfi ta nufo gunsu. Tsayawa sukayi da kuncen suka fara waige-waige_




_Ji sukayi an watso musu wani abu kamar ruwa. "Kai waye ke watso mana ruwa?".  Suka fada cikin hadin baki.  Muhisan yaji abun da dan danko hakan yasa ya fiddo leta ya danna. "Jinine yaseen".  Abunda ya furta kenan. Da sauri Rafson ya matso kusa. Yana ganin jinin sai suka hau dube-dube  wata kururuwa sukaji marar dadin ji a bayan su da sauri suka waiga gefan. Wani katan abune ga dukan alamu baki ne. Idanunsa kawai suke hangowa masu kamar singnonin mashin abun ya durfafo su yana wani irin gunji. Da gudu suka fada napepk  nan fa sukayi sukayi ta tashi amma taki.  Ga abun na kara kusantowa karar shinna cika musu kunne.  Da dai sukaga bazata tashi ba sai gaba daya suka fita suka runtuma a guje._





_Gudu suke sosai a birjin hasken da suka ga ya nufo su a baya yasa su juyawa. Napep din ce ta nufo su ba kowa a ciki. Da ganin haka suka kara kaimi wajen gudu. Basu ankara ba sai gani wannan Bakin Aljanin ya duro a gaban su kamar an cillo shi yana musu wata iriyar dariya mai karfi ga rashin dadin ji a kunne. Wata uwar turjiya suka ja gaba dayan su sai da suka fadi domin tsayuwa ce bata san rai ba.  Sunyi yunkurin tashi kenan sai ganin wanna aljani sukayi a gaban su. Abunda ya kara tsoratu su kenan. Cikin murya marar dadin ji yace. "Kuje ku shiga mu tafi".  Tashi sukayi suka shiga napepk din jiki na karkarwa.  Ba tare da sunga mai tukin ba sukaji anja napep din a guje.  Ihu! Suka fara yayin da wata murya ta mace tace "Kuyi mun shiru barayin banza".  Shiru sukayi haka napep tata shara gudu har suka kusan isowa gari inda suka tarar da  wani gate na yan sanda masu binciken motoci a hanya. Haka suka bi layi ana ta bincike ana zuwa kansu dan sandan yaji ance. "Barayi ne na kawo muku ku hukunta su".  Dan sanda ya bata rai hade da cewa su Rafson kai ku fito dan ubanki.  Fitowa sukayi ya ja su har wajen ogansu dake can zaune kan benci.  "Yallabai ga wasu yan iska nan. Wai mu suke cewa su barayi ne. Wasa suke da hankalin police sir!".  Ogan harara ya gallawa su Rafson yace "yan iska dama daga ganin ku yam shaye-shaye ne dan...".  "Nice nan na kawo chu bachu chuka kawo kanchu  ba". Wata yar Yarinya ce wacce bazata wuce shekara 4 ba ta bayyana a gaban su sanye da bakaken kaya idadun ta manya sun wuce kima. Gata baka.  Ai kafin ta rufe baki tuni Ogan yan sanda ya wuntsila daga kan bencin yayi kundunbala ya tashi ya zabga a guje haka suma duk sauran yaran shi da su Rafson kowa ya kama gabansa........................................._



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 85-86



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


😍 DEDICATED TO YOU 👇🏼👇🏼😍


My Dear 💦💧  *Queen Hauwa Haucy* 💧💦


💃🏻 Na yabba da kaunarki gare ni. Bansan da wanne irin kalamai zanyi amfani wajen yaba miki da godiya a gare ki. 🚶🏻


Sai dai ince Allah ya barmu tare Allah kara basira da daukaka na gode matuka da irin Kaunar da kika nuna min. ☺




        *A PAGEN DA YA GABATA CIKIN LITTAFIN ALJANAR FATIMA. LOLZ* 😜

~Wata yar Yarinya ce wacce bazata wuce shekara 4 ba ta bayyana a gaban su sanye da bakaken kaya idadun ta manya sun wuce kima. Gata baka.  Ai kafin ta rufe baki tuni Ogan yan sanda ya wuntsila daga kan bencin yayi kundunbala ya tashi ya zabga a guje haka suma duk sauran yaran shi da su Rafson kowa ya kama gabansa.~



_*M*ukhtar da Ibrahim suna fitowa Ibrahim ya bada shawarar suje police. Haka suka dunguma suka nufi police din suna cikin tafiya kawai Mukhtar ya hange napepk dinshi anyi parking dinta a gefan tati. Da ganin haka ya ruga da gudu cike da zubudi yaje yana lalekawa yana fadar "Wallahi itace"2×. Umar Safuratu ya ga ta leko daga cikin napep din tace ya shiga. Dajin  haka yaje ya shige napepk din. Mukhtar sai murna yake ya shiga gidan baya yana duduba wani abu sai ji yayi anja adai-daitar a guje. Nan ya fara kwalla ihu yana neman agaji. Ba abunda ya kara tsorata shi sai ganin ba driver  napep din ita kadai kejan kanta.  Ibrahim yayi kokarin ya sama abun  hawa ya bisu amma ina. Lokacin da ya samu ya tsayar da wani mashin su tuni har sun bace mai baima san inda sukayi ba. Safuratu bata tsaya da napep din ba sai a kofar gidan Umar da isar su ta sauya zuwa yarinya. Ta kuma bawa Umar wata koya tsanwa yana sha sai gashi ya bayyana. Mukhtar tsoro ne ya kamashi dan ya gane Aljanar gidan Umar ce.  Safuratu tace mishi ya fito su shiga daga ciki nan fa ya fara kakafe wa. Umar yayi iya bakin kokarin shi amma Mukhtar yaki  yarda ya shiga gida. Abun ne ya bawa Safuratu haushi. Da hannu ta nunashi sai ji yayi an daga shi sama ana nufar kofar gida da shi. Nan fa ya fara ihu yana bada hakuri. Safuratu tace ba komai zasuyi mishi ba amma yaki yin shiru.  Daga dayan hannun ta wata wulfefiyar wuka ta fito taje ta tsaya saitin makogwaran Mukhtar Safuratu tace "kayi min shiru ko in umarci wakar nan ta cire ma kai". Shiru yayi ko uffan bai kara cewa ba har suka shiga gidan. Ba nefa gida duk duhu ne Safuratu ta kalle kwan nepar sai wani haske ya fito daga idanun ta ya shige shi nan take gidan yayi hask fayau!._





_Nan suka zaunar da Mukhtar Rafy kam tuni ta gaji da jira har tayi barci. Safuratu tace "Zanyi ma wasu tambayoyi. Amma kasan da sani in ka min karya zan gano ka dan haka gwara ka taimaki kanka a fadan gaskiya".   Mukhtar bakin shi na rawa yace "To, To zan fada miki gaskiya".  Safuratu ta kalle shi ta  nuna Umar "Miyasa ka bawa Umar abokinka shawarwari na banza. Wanda kasan kai ba haka kake wa matar ka ba?".  Mukhtar yayi jim! Kadan tukun ya nunfasa yace. "Hakikanin gaskiya na bawa Umar shawarwari na banza ne domin tun muna yara mu abokai ne kuma na riga shi yin aure sai kuma naga ya fini jin dadin auren wannan yasa na kirkiri hanyar da zata dakushe jin dadin nashi shima ya dawo kamar ni. Amma daga karshe nayi nadama".   "Karya kake mugu azzalumi macuci'. Umar ya taso mai da fada da niyar ya shake shi. Safuratu ta miko hannunta ya zama xankalele ya shiga tsakanin su. Can Umar ya koma yana hararen Mukhtar yana huci._






_Safuratu ta kalle Umar "Haba kai da nake ganin ka mai hankali shin bakaji abunda Mukhtar din yace bane?. Kai yanzu bazaka tausaya mishi ba. Kalle fuskar shi ka kalle cikin idanunshi kaga cike yake da nadama da tarin dana sani. Umar na kawo shi nan ne dan in muku sasanci  ba fada ba dan haka ka saurare mu kawai in bance kayi magana ba karka kara saka baki".  Umar jikin shi yayi sanyi da jin haka.  Safuratu ta kalli Mukhtar taci gaba da magana, "Mukhtar amma kai miyasa ka auri mata kallar wannan?.  Shin auren soyayya ne ko hadi ne".  Mukhtar yace "Auren soyayya mukayi da murja sai dai tun tana budurwa ake fada min irin mugayen halayanta. Amma nake kauda kai wasu abokan nawa har rikici muke in suka aibata ta a gabana. Ni a ganina duk rashin kyan halinta ai ni bazata min ba tunda ni mijinta ne. Sai da na aure ta tukun na karyata kai na. Domin kuwa abubuwan da murja take sam basuyi kama da na mai neman gidan aljanna ba ita fa duniya kawai ta saka gaba. Kullum zancen ta kudi-kudi lokacin da mukayi aure idan na bata kudin cefane sai ta murkushe rabi. Idan na auno shinkafa ko Masara sai ta kwashi san ranta taje ta sayar daga nayi magana sai tayi fushi tace wai zarginta nake yi.  Da dai naga abun yayi yawa lokacin inada dan arziki na sai na hada yan kudade kusan dubu dari da goma ne. Na bata nace taja jari ni a gani na ai rufin asirin ta nawa ne kuma rufin asirina nata ne._







_Taja jari kuma sana'ar ta karbe ta tana sayar da fulawa. Man kwanti. Shinkafa. Da dai sauran kayan miya.  Kwanakin baya sai aka kore ni daga wajen aiki na dawo zaman gida. Duk da ni na bata jari amma kullum bata da abun yi min sai gori wai na zama mijin hajiya ita take cida ni. Da abun ya bani haushi sai naje nace ta bani kudina dubu dari dana bata jari. Nan fa tace ta cinye kai tsaye. Abun yayi kamari har ta kai mu ga dambe. Nayi mamakin karfin murja dan dagani tayi ta ringa nunawa mahalicci tana bugawa da kasa.  Da dai naga tana neman jinyata ni sai nace na hakura. Bayan kwana biyu sai na sama wani mashin din ina achaba. Mun dade a haka ina ciyar da ita duk da ta fini samun kudi. To ranar sai mai mashin din ya sayar da shi. Nan na sake komawa gidan jiya kekenapap din nan itace ake bani duk sati to kinga kuwa ko ni kadai ne baxata iya rike ni ba balle ma harda mata ta. Wannan yasa na fara cin bashi a gurin domin ita bazata bada ba sai bashi a haka har na tara kudade da yawa. In kinga irin rashin mutuncin da take min a kansu bazaki taba cewa ni mijin ta bane".  Safuratu taja dogon nunfashi tace, "Tabdijam kaga irin abunda ake gaya muku. In kun tashi aure ku nemi mace mai hankali tausayi da sanin ya kamata. Amma sai ku bige da neman mace Fara kyakyawa doguwa. Baku ma damu da kalar tarbiyar ta da halayyarta ba. Hmm in kuwa kuka cigaba da haka lalai zaku ta tsintar kanku cikin irin wannan matsala Mukhtar. Umar abunda nake so daku shine ku yafi juna nasan duk hassadar da yake maka sharrin shedan ne".  Umar ya sauke ajiyar zuciya ya kalle Muktar yace "Ba komai abokina na yafe maka Allah ya rabamu da sharrin shedan kuma".    "Na gode abokina ameen Allah ya saka da alkhairi".  Umar yace mu duka Safuratu ce ya kamata muyi wa godiya. Muna matukar godiya Safuratu. Hakika da za'a samu irin ku a cikin al'umar aljanu da wasu abubuwan sun saitu a cikin mu mutane".   Murmushi tayi kafin tace. "A komai ai ana samun na gari ta yuyu bani kadai bace ma.  Yanzu Mukhtar ya zakayi da matar ka?". Mukhtar ya bata rai yace "Ni fa na sake ta saki daya. Amma kuma tace bazata bar gidan ba". Dariya Umar da Safuratu sukayi.

Safuratu tace "Ji shegiya kamar gidan ubanta. Bari inje in korar maka ita". Mukhtar yace "Jira bari in karashe sauran saki biyun su zama uku domin na tsani murja gaba ki daya bazan iya zama da ita ba". Takarda aka samo mishi ya idasa sakin Safuratu ta amsa ta bace.  A kofar gidan Mukhtar ta bayyana cikin sufar Mukhtar din.  Ta shiga gidan bata iske murja a tsakar gida ba hakan yasa ta wuce daki. A zaune fake Mukhtar din ya iske Murja a bakin gado da gani ranta a bace yake. Yana shigowa ta fara binshi da harara. Shima martani yake mayarwa. Takardar ya fiddo daga aljihun shi  ya mika mata. "Sauran saki biyun ne wannan ki hada da na farko na sake ki saki da uku".  Karbar takardar tayi ta lunkuma a baki ta tataune tukun ta bushe da dariya daga bisani ta bata rai ta tashi cikin tsiwa da bala'i. "Kai Mukhtar To bari kaji karyarka tasha karya wallahi.baka isa ba wannan sakin bai saku ba.  Ni da kai mutu  ka raba ba inda zanje".   Mukhtar yace "Ki tatara ya naki-ya naki kiyi gagawar barin gidan nan tun kafin jikin ki yayi tsami".   Yar dariya tayi irn ta raini wayyo hade da cewa, "Ayyiriri iyye nanaye.  Kai baka ma ji kunya ba da ka fadi haka?.  Waye zai karya ni kai ko kuwa wani?. Na ma ga alamun dukan kake so dan haka bari kaga". Juyawa tayi da sauri waje taje ta daukko tabarya ta nufi Mukhtar tasha mamaki ganin ko motsi baiyi ba duk da kuwa a haukace ta taho da niyar buga mishi. Tana kawo tabaryar yayi charf! Ya rike hade da wanka mata wani wawan mari wanda sai da ta gigice bata ma  san lokacin da ta saki tabaryar ba ta fadi kasa. Belt Mukhtar din ya daukko ya fara bulalata tana ihu! Bai sasauta mata ba duk sai da ya farfasa mata jiki tana ihu! Da jan jiki ta fito daga dakin kafin ta tashi ta fita a guje bata ko sake wai-wayo baya ba. Safuratu tace "Yar nema gobe ma ki kara"................................................_



😂 Murja yar masifa yau anji jiki 😜



Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy













👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 87-88



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


_*THIS PAGE DEDICATED TO ELOQUENCE ASSOCIATION*_ 


🌟 ELOQUENCE WRITERS ASSOCIATION 🌟


💃🏻😍 *MUSA MELODY, AUTA* 💃🏻😍

_(Autan Eloquence)_


💃🏻😍 *MUHIEVERT INDIA* 💃🏻😍

 _ єя ιи∂ια Er love)_ 


💃🏻😍 *SHAMSIYYA SALIS* 💃🏻😍

 _(Autar Eloquence)_ 


💃🏻😍 *BASIRA N. DABO* 💃🏻😍

 _(Basira)_ 



🤗 Kai dama duk members wanda ban sani ba. Ina muku Fatan alkhairi. Allah ya kara daukaka. Allah ya kara muku basira da Hazaka. 


*ZAMANAWA*

Nayi muku fatan alkhairi 💋❤❤




    *A PAGEN DA YA GABATA CIKIN LITTAFIN ALJANAR FATIMMA*

~Belt Mukhtar din ya daukko ya fara bulalata tana ihu! Bai sasauta mata ba duk sai da ya farfasa mata jiki tana ihu! Da jan jiki ta fito daga dakin kafin ta tashi ta fita a guje bata ko sake wai-wayo baya ba. Safuratu tace "Yar nema gobe ma ki kara".~


_*S*afuratu ta bayyana gaban su Mukhtar dake zazaune a tsakar gida hannun ta rike da wasu daurinan kudi. "Mukhtar na kori Murja kuma ina kyautata zatan bazata sake ma irin rashin kunyar da take ma da ba".  Daurin kudi ta mika wa Umar da Mukhtar kowa daya-daya hannun har karkarwa yake wajen amsa. "Wannan kudin da kuke gani kar kuyi tunanin a banki na sato ko kuma kudin wani. Aa kudina ne mallaki na inada dukiya mai yawa a boye a inda mun biye su ne a wani waje wanda mu biyu kadai muka  sani daga ni sai Ummana. Wacce yanzu ita bata raye.  Dubu dari-dari ne ku samu koja jari da shi domin neman na kanku. Sallama nake muku sai kuma wani jikon. Umar karka yarda inji ko inga kawa matar ka wani abu makamancin wanda kake mata a baya. Dan in na kama ka da hakan bazaka ji dadi ba. Idan ta tashe kuce mata ni na tafi sai Allah ya sake hada mu". Tana kaiwa nan ta bace bat!. Godiya suka kamayi mata kala-kala suna murna.  Mukhtar tunowa yayi bata bashi makulin napep ba. Har ya fara rudewa da tunanin ina zai ganta kuma sai ya hangi keys din a kan tabarma.  Da safe da suka gayawa Rafy bata ji dadi ba sosai. Har hawaye tayi tana fadar Safuratu bata kyauta mata ba. Ya zata tafi basuyi bankwana ba. Umar kuwa lalashin ta yake yana cewa ai zata dawo tace......_

______________________


_Gidan shiru kake ji ba hayaniya hakan ya nuna cewa yara sun tafi makaranta kenan. Zaune suke sun tattara hankulan su gaba li daya sun mikawa TV dake makale a bango.  Mama Asiya ce ta shigo itama ta sama waje ta zaune hade da cewa "Sannun ku".  "Yauwa suka amsa gabaki daya".   Kafin Zuwaira tace "Aunty Asiya tun washe garin ranar da abun nan ya faru nake tambayar ki me yasa kika yi duk wannan abubuwan harda goya babyn Fatima amma kinki bamu labari". Asiya ta waiga hagun da dama  tace "Yanzu zan fada muku amma abun sirrine dan haka ku dawo nan".  Tashi sukayi gaba daya suka koma kan sofa chair din suka hada kai da ganin kasan abun munahinci ne. Mama asiya tayi kasa da murya ciki-ciki tace "Wato ni kaina ina so in sanar daku abunda ke faruwa to sai dai duk lokacin da zan fada muku sai inga wannan shegiyar Fatima. Sai inyi shiru.  Shin ko kunsan wannan yar babyn ta hannunta Aljana ce?".  Kallan juna Zuwaira da Hauwa sukayi cikin rashin fahimta "Bamu gane ba aljana kamar yaya?".  Mama Asiya ta lumfasa tace "Kwarai Aljana nima ban zata ba sai ranar. Duk abubuan nan da kukaga inayi to ita take saka ni. Har bullo min take a cikin wata irin suffa abun tsoro".  Kwashewa sukayi da dariya gaba dayan su harda ma rike ciki. Hauwa tana fadin "Wai Aljana sai mu zauna ki mayar damu aljanu ai". Zuwaira tace "Heheheheh!, Kinji fa dama na gaya miki ai motsa jini ne take ba komai ba. Shine zaki bige da ce mana wai Aljana ce..."._


_Asiya ce ta mike a fusace. "Dariyar ta iska haka kuma in kuma mutum bai bari ba Wallahi yanzu zan narki kayan banza. Aa kaji mun yan rainin wayo. Ni dai na gaya muku kuyi hankali da Fatima. Dan yanzu ba ita kadai bace ba kamar da bane da muke mata duk abunda muke so. To yanzu in mutum ya zalunce ta akwai ma rama mata. Dan haka kuyi hankali. In kunne yaji to jiki ya tsira".  Tana fadar haka tayi gaba ta nufi dakin ta. "Ni dai cikin abubuwan da nake wa Fatima ba abunda zan fasa sai ma karawa da zanyi Wallahi.  Bari ma ta dawo inci ubanta sai muga Aljana.  Hhh kawata wai kinji mu za'a mayar Aljana". Zuwaira ce mai wannan maganar. Asiya kam bata ko juyo ta kalle su ba ta shige abunta._




_Safuratu na dawowa gidan taga Fatima bata nan wannan ya tabbatar mata tana makaranta ne. Jikin yar Babyn taje ta shiga. Lokacin tasowa Fatima Nasmat, Da Asmart tare suka shigo gidan sai wasa suke a tsakanin haka ya tabbatar wa da Safuratu cewa Fatima bata cikin wani damuwa._








_Kwana biyu nan Zuwaira da hauwa suna so su taba Fatima su gani kuma suna tsoro. Dan kar suje abunda Asiya ta gaya musu gaskiya ne. Haka shima bangaren abba kullum cikin target yake na yanda zai yiwa Fatima mugunta wacce zai huce haushin marin da mama Asiya tayi mishi a kanta.  Safuratu kuwa da taga kwana biyu hankalin Fatima kwance  ranar nan tana zaune sai ta tuno da su Kamal da matar sa  Khadija hakan yasa tace bari ta nufi can taga irin halin da ake ciki ga Muktar ma._

**************

_Zaune yake a tsakar gidan yana goge takalmin sa da alama fita zaiyi.  Yarinyar ce cikin uniform dinta na makaranta tazo ta durkusa ta gaishe shi ciki-ciki ya amsa mata rai a bace. Kamar dai ta bari kuma sai tace "Baba bani naira hamsi".  Cike da masifa da hargowa yace "Kinci ubanki ke da hamsin din kaji marar kunya marar tunani yanzu duk halin babu da ake ciki ke baki gani da zaki ce wani wai in baki Hamsun to ko kwandala bazan bayar da.  Bace min da gani ko in make ki". Hannu ya daga kamar zai bige ta. Da ganin haka ta tashi ta ruga a guje tana kuka. Ummiey ce ta fito Cikin nuna bacin rai tace "Baban Hawwer gaskiya abun da kake baka kyautawa ko kadan. ko dan kaga Aljanar nan bata dawo shiyasa ka fara wa yarinyar nan rashin mutunci?".  Muktar ya dago cikin fushi "Ummiey bana san haka fa. Miye ruwan ki in ma Aljanar ta dawo nasha dai ba wajen ki zata zo ba ko?. Kin anta irin gatan da na nuna wa wannan  yarinyar ne?.  Ai ko hawwer ban mata abunda na mata ba. Na mata ada lokacin da nake tunanin Aljanar nan zata dawo. Yanzu kuwa tunda naga bazata dawo ba, Ai sai in sakata in wala".  Ummiey Tace "To ai ita wannan dukiyar ta ce. Sannan kuma kaga tunda Allah ya karbi Hawwer bai sake bamu wata yar ba. Ya kamata mu rike maryam kamar Yar mu hawwer Domin ni jinta nake sosai a raina kamar yar dana haifa".  Mtsww.. Muktar yaja tsaki tare da sa takalman sa yace "Naga alamar maganar kike so to ai ga bango nan sai kiyi da shi. Nasan bazai taba gajiya ba. Ni dai na tafi". "A dawo lafiya". Shine abunda Ummiey ta fada bai ko amsa ba yayi gaba.  Safuratu da duk abunda ya faru a gabanta ya faru kai ta girgiza "Lalai wannan ashe bakayi hankali ba. Zamu hadu da kai"._







_Gaba dayan unguwar an taru sai kallan masu jigilar watso kaya waje. Ba mai bada hakuri balle a hana. Wani mutum mai sanye da Jacket ranshi a bace sai cewa yake "Yauwa ku fito da su bana so inga ko cokalin su a gidan nan. Yau yau nake so su tashi su bar gidan nan".   Can gefe kamalu ne zaune yayi tagumi yayi wani tsamo-tsamo kamar bera ya fada ruwa an fiddo shi. Gefan shi kuwa Khadija ce ba abunda take sai kuka tana  zubar hawaye. Tana tunanin irin wannan bakar rana wai yau sune ake watso musu kaya a kan titi. Kaddara kenan.  Safuratu na ganin haka ranta yayi mugun baci. Nan take ta Juye suffarta zuwa wani saurayi mai kwarjini.  Tsakiyar mutane ta ratsa ta fara bin masu fiddo kayan tana Fasfaska musu mari tana fadin "Ku mayar da kayan nan kafin Rai ya baci". Ai kuwa basuyi gardama ba suka fara dibar kaya suna  mayarwa.  Daga baya wannan mai sanye da jacket ya fara bala'i ya nufo Safuratu. Yana zuwa ya duma mata kulli. Da juyowar ta ta shaki kwalarsa da hannu daya ta dage shi sama. Kafafun shi na reto...................................................._




🤔 *NAN FA AKE YINTA*


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 88-90



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


🤗 *WANNAN PAGEN NAKU NE MASOYAN LITTAFIN ALJANAR FATIMA A DUK INDA KUKE*


💃🏻 _A KULLUM FARIN CIKINA DA JIN DADI BAYA MISALTUWA IN NA TUNO DA KU MASOYA NA. INA JIN DADIN _COMMENTS NAKU KUNA A RAINA._  COMMENTS NAKU NADA MATUKAR MAHIMMAN CI A GARE NI. KO BA KOMAI ZAN KARA SAMUN KWARIN GWIWA._



😰 _*DAN HAKA YAU DUK WANDA YA KARANTA BAITI COMMENT BA SAI NASA SAFURATU TA SAKO MAI DUTSE A KAI*_ 🙊😜


Luv u oll supporting ❤😍😍😍

🤗 Har  Unsupported din ma 😉



        *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ai kuwa basuyi gardama ba suka fara dibar kaya suna  mayarwa.  Daga baya wannan mai sanye da jacket ya fara bala'i ya nufo Safuratu. Yana zuwa ya duma mata kulli. Da juyowar ta ta shaki kwalarsa da hannu daya ta dage shi sama. Kafafun shi na reto.~


_*H*arbe-harbe ya kamayi yana neman kubucewa amma ina rikon da tayi mai ba na wasa bane. Wulla shi tayi ya fadi kasa. Da ganin haka wasu yan kallon suka fara sabe wa suna guduwa. Masu fito da kaya kuwa suka kara azama wajen mayar da kayan cikin gida. Mutumin da Safuratu ta koma shi ya nufi Mai jacket din nan a jiki. ya fara da cewa. "Lalai kai ka cika marar imani da tausayi da har zaka sa a watso wa da mutane kayansu tsakiyar titi. Wannan wane irin cin mutunci ne?. A kan kawai basu biya ka kudin hayaba ko mai?. Shin kai baka tunanin in kai ne ake wa hakan baza kaji dadi ba". Mai jacket din ya mike yana kaka be jiki, kafin  mutumin ya karaso gare shi ya nuna shi da yatsa. Yace "ba dai ni kawa haka ba a bainar jama'a. to ina tabbatar maka da cewa sai kayi nadamar abunda ka aika ta min. Domin alhaji dayyabu sam! Bazai rabu da kai ba dole ya dau kwakwaran mataki a kanka". Da fadar haka ya juya ya tafi. Safuratu kuwa tace, "Ina nan ba inda zani ina jiran alhji Dayyabun. Ko uban waye yazo inaji dashi. Banza wanda bai san mutuncin dan adam ba".  Mai jacket din wanda ake kira da Dan ladi na alhaji Dayyabu. Ya juyo ya kalle Safuratu. "Alhaji kake zagi?. Lalai yau mai kwatar ka a hannun alhaji sai Allah". Juwaya yayi ya hau mashij dinsa ya buga ya tafi a guje._






_Kamalu ne ya taso yana mishi godiya. Safuratu tace "Ba komai ai yi wa kai ne". Kamal fuskar shi cike da damuwa yace "Mun gode da abunda kayi mana, Kuma naga abunda ya faru dan haka nake rokon ka da ka bar gurin nan domin alh. Dayyabun nan da kaji ana fada hatsabibin mutum ne. Yana da kudi sosai shi yasa yake takada duk wanda yaga dama. Yanzu nasan in yazo ya tarar da kai a nan sai ta Allah. Dan Allah ka taimaka ka bar nan".   Safuratu dake suffar namiji tace "To wai wannan gidan nashi ne. Haya kuke a ciki ne?".  Kamal ya kama hannun mutumin suka shiga daga ciki dan ganin mutane na kallan su. Khadija ma tashi tayi ta bisu. Bayan sun zauna kamal yace, " Wannan da kake gani. Gidana ne kwanakin baya wata kaddara ta fado mana matata ta kamu da wata cuta. Asibiti suka nemi kudi million daya da rabi. Na hada jarina gaba daya Dubu dari hudu ne.Na nemi taimako wajen masu kudi da dangi amma ban samu ba. Gidan nan shi kadai ya rage min. Kuma Allah ya gani a kan matata ba abunda bazan iya yi ba. Da har nayi tunanin sayar wa sai wani abokina ya bani shawara inje wajen Alh. dayyanu yana bada aro amma ya shaida min cewa, Baya ba mutum aran kudi sai ya tabbatar da mutum nada wata kaddarar da tafi abunda ya ara. Yace mutumin baya da mutunci idan kuka sa lokaci baka kai mishi kudin sa ba. To zai zo ya sayi gidan ka ko mota ko wani abun yanda yaga dama ya cika ma kudin ya kuma kore ka. Da naji haka da har nace ban amince ba. Koma sai na canza shawara na amince. Naje na aro million daya da dubu dari na cika da kudin gurina na kai asibiti akayi wa matata aiki. Bayan ta sama lafiya da wata daya alh. Ya fara aiko min dan ladi shine wannan mai jacket din da ka gani._








_Hakan tasa ni  dole na saiyar da gidan kuma shi Alh. Dayyabun shi na sayar wa.

Da sukaga watan ya shude ban kai musu kudin su ba shine Alh. Ya turo wasu matasa yan daba suka dauke ni, Suka kai ni wajen sa. Nan yake gaya min tunda naki bayan kudin sa to ya saya gidana. 1.5 million.  Yanzu zai cika min dubu dari hudu. Da na nuna rashin amincewa sai yace wa da yan daban nan suta duka na har sai na amince. Nan fa suka fara jifga ta da dai naga suna neman hallakani sai nace na amince. Nan yayi dariya ya kawo dubu dari hudu ya bani. Wannan abun da nake gaya ma ya faru shekaran jiya ne. Yace in tattara kayana in tashi daga gidan in ba haka ba ya min korar kare. Nace to, jiya nayi neman duniya in sama gida ko na hayane in biya shekara amma abun ya gagara.  Shine fa yau tun safe ya turo dan ladi da wannan matasan suka zo suka fara watso mana kaya waje.  Mutumin ya ja dogon nunfashi yace "Lalai wannan mutumi ya cik...". Hayaniyar da sukaji a kofar gida ce ta tsayar da mutumin bai karashe magana ba.  Kamal jiki na rawa yake cewa. "Wallahi Alh. Ne kaga sai da nace ma ka gudu-ka-gudu amma kaki, to yanzu gashi nan ya debo yan daba".  Mutumin hankalin shi kwance yace "Abunda nake so da ku yanzu shine kuyi sauri ku shige daki kai da matar ka".  Ba gardama kuwa suka shiga suka kulle dakin._





_Alh. Dayyabu Ne a gaba Gefan shi Dan ladi sai kuma wasu garada su hudu Katti ne majiya karfe ko wanne ka kalla fuskar shi zata gaya ma ba imani. Kursiyya tsakar gida ta zo ta yi tsaye ta dan bubuda kafafu ta mayar da hannuwa baya. Irin tsayuwar guards. Alhji ba abunda yake in banda zage-zage. Yana ganin mutumin da tsayuwar sa sai ya tsaya cik!  Suma gaba ki daya suka tsaya. Alhj._






_Ya kalle mutumin sama da kasa tukun ya bushe da dariya yace "Kai Amma Dan ladi ban taba sanin kai mashiririci ne ba sai yau. Yanzu dan Allah a kan wannan dan Yarinyar ne ka taso mu ni nama dauka wani jibeben gardi zan gani har na kwaso karti hudu. Hakan ma cewa kake wai na kara wasu. Yo wannan karamin alhakin ko ni ai sai in tumurmusa shi".  Dan ladi ya kara matsawa kusa da alhji yayi ya mai rada a kunne. "Alhj bar ganin shi haka kashi daya ne da shi. Da hannu daya fa ya dagani sama".  Cikin fada da bacin rai alhaji yace. "Kai rufe min baki matsoraci   kawai bari kaga insa ayi min guduwa-guduwa da shi. Tiger Da Musa lion ku kamo min yaran nan yau sai ya gaya min gidan na ubanshi ne da har zan sa a fitar da mutane ya ce a mayar".  Rufe bakinsa ke da  wuya, Sai kuwa karti biyu suka nufi Safuratu ko wannen su a murmurde yake fuskokin ba annuri. Safuratu  Da  ganin sun nufo ta sai ta ruga a guje ta shige bandaki.  Su tiger suka bita a guje suma. Da zuwa suka tarar da ba kowa a ban dakin sai wata yarinya dake kallan su tana murmushi. Musa Lion ya chakumi rigar ta ta baya ya dage ta sama da hannu daya. A haka suka fito sa ita. Alhaji tun kafin su karasa gurin sa yake cewa. "Kai bana san iskancin banza fa. Ya nace ku kamo min wancan dan Yarinyar zaku kamo min wannan karamar tsakuwar".   Tiger ya bude baki maganar shi ita kadai ta isa ta tsorata mutum. "Alhaji ai shine ya koma haka dq alamu yana da layar zana"._






_Alhaji yayi dariya. Hehehehehehe, "Au! Wato shine ya koma wannan Yarinyar nufinshi zamu kyale shi ne".  Alhaji ya matsa gaf da Safuratu dake rike a hannun tiger sosai alhaji ya matsa kusa da ita yana mata wani irin kallan raini. har hancin shi na gogar nata. "Wato kana nufin da ka koma wannan Yarinyar muyi hakuri mu kyale ka ko. To kuwa kayi kuskure domin da ka tarye ni fada gwara ka taryi RUNDUNAR SADAUKAI. Domin ni nan da kake gani na nafi kububuwa hadari. Sannan bani da imani ko miskala zarratun, Saboda rashin imanina cinnaka ake cemin baka san na gida ba ciji Jariri in uwar ta motsa in galla ma..." Ai kafin ya rufe baki Safuratu ta cije shi a hanci harda jini. Kafa tasa ta harbi tiger a ciki. Dan zafin da yaji baima san lokacin da ya sake ta ba.  Da gudu ta nufi wani bangare na gidan. Alhaji rike da hanci yace "Ku kamomin wannan dan iskan ku cinye shi danye". Da fadar haka su duk hudun suka bi Safuratu da gudu. Kamar biri haka ta kama gini makal-makal ta haye kan soro. Su tiger na zuwa sukayi tsaye suna kallanta. Irin dutsen da ake dorawa a saman kwano gudun kar iska ya dauke ya yace kwano. Shi Safuratu ta dauka ta daga sama alamun jefowa zatayi. Da ganin haka suka tsaya cik suna kallanta. Dariya Safuratu kafin tace "In da mai so ya bakunci lahira a cikin ku ya karaso"._ 






_Cik! Suka tsaya suna kallan ta domin kuwa sun san cewa duk wanda aka bugawa wannan dutsen ba a kai ba ko a  wani bangare na jiki ne ya banu. Ganin sunyi tsaye ba mai niyar zuwa alhji yace, "Tiger dama abunda na daukko ku kuyi kenan?. Bana san iskancin banza fa". Cikin maganar su irin ta yan daba yace "Wannan maganar rai ce fa ake, ahhee Bar gani na a haka daga ta kwada min shi zaka ga na fara ah yane a nan gurin. Allah. Alhaji".  Ran alhaji ne ya baci nan ya fara tattare babbar riga "Bari ni inje tunda ku bazaku iya ba". Da sauri dan ladi ya rike shi. "Aa alhaji karkaje wallahi Waccen daga gani ba imani zatayi ba". Safuratu ajiye dutsen tayi ta kalli tiger suna hada ido sai kuwa idanun shi suka koma bakake wul! Ba ko alamar baki a ciki. Da faruwar haka ta diro daga saman Soran.  Musa lion da sauran biyun suka nufe ta a guje kafin su karasa sai ganin Tiger sukayi ya shige gaban ta. Da ganin idanuwan shi suka gane ba lafiya ba. "Ku tsaya". Tiger ya fada da karfe muryar kamar wanda yayi magana a Loudspeaker. Cik suka tsaya. Abun mamaki duk wanda suka hada  ido da tiger sai shima idanun su koma baki kirin gaba dayan su haka.Alhaji da Dan ladi suna tsaye kallan ikon Allah kawai suke. Da faruwar haka Safuratu tace "Kuje ku daukko min alhaji da yaran sa dan ladi ku kawo min shi gaba na".  Gaba daya su hudun suka juya suka nufi alhaji. Da gudu dan ladi ya juya da niyar ya tsere ai kafin ya isa kofa tuni wani yasha gaban shi. A kafada aka sabo su alhaji aka dire a gaban Safuratu. Alhaji na karkarwa yace...........,......................_




🤔 *KAIKAYI YA KOMA KAN MASHEKIYA* 😳




Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 91-92



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😘😘 DEDICATED YOU MY SON *MUBASHSHIR*​



     ​HAPPY BIRTHDAY *MUBASHSHIR*​


🎂🎂🎂🎂🎂?

💃🏻💃🏻 Allah ya karo shekaru masu albarka 


Happy  2+ 😘😘😘


?🎂🎂🎂🎂🎂🎂



💃🏻 *I'M HAPPY* 💃🏻


 *HAPPY MAULIDIN NABIYYU SALLALAHU ALAIHI WASALLAM*  ☺💃🏻


*Bazamu taba mantawa dake ba ya masoyin Allah.*


 *Bamu da kamar ka ya shugaban mu..* 


 *Mun san cewa duk irin so da kaunar da muke maka bazamu yi rabin san da kake mana ba ya Habibullah* 



 *Mun gode wa Allah muna kara gode masa a kullum.da ya bamu kai ya Rasulillah.* 



 *Bamu da komai bamu da kowa sai kai manzan Allah. Ka cece mu ranar da ba mai ceto sai kai. Ba dan matsayin mu ba dan girman Allah ya Rasullillah* 👏🏻💃🏻



Makiyan ka sun tabe. Masoyan ka baza su taba tabe wa ba. Saka mu cikin masoyan ka👏🏻.



Dole muyi murna da zuwan ka ya shugaba. 😟 Wanda basa murn bakin ciki ya kahe su 🤷🏻‍♂


*YA ALLAH KA KARAWA ANNABI DARAJA. AMIN*



       *KARSHEN PAGEN BAYA*


_*"D*an Allah dan annabi kiyi min afuwa ki ceci rayuwa ta wallahi bansan ke din Aljana bace".  Safuratu ta harare shi. "To ai yanzu kasan ni Aljanar ce. Naga kamar ka kwaso wadan nan kartin banzan ne domin suzo su tumurmusa ni dan na hana a  watsar wa da nayin Allah kayan su ko". Da sauri alh. Yace Aa wallahi sam ba da niyar haka na zo ba. Ni nazo ne ma in c na bar musu gidan su rike. Amma dan Allah karki yi min komai".  Kamal da kadija da sukaji shirun yayi yawa basu ji ihun mutumin nan ba. Sai kamal ya taso ya leko. Yana ganin Yarinyar nan kuwa kwalwarsa ta shiga aikin bincike yana kokarin tuna inda ya santa amma hakan ya gagara. Khadija ya kari itama ta leka kamar dai shi. Itama taso ta san Yarinyar amma ta manta a ina._




_Safuratu tace "Aa  ka rike gidan ka ai yanzu idan ka basu kyauta. Watakil wata mai tsayuwa zaka zo kace su tashi ka fasa. Dan haka bari a biya ka kudin gidan ka". Bat! Safuratu ta bace. Sai bayan kamar mintuna biyar ta bayyana rike da jaka. Ta mikawa alhj. Dayyabu hannu na karkarwa ya karba. Tace ya daga ya gani. Ya daga kudi ne bandir-bandir na dubu-dubu. Safuratu ta dauki biyu daga ciki tace. "Kudin nan Million daya da dubu dari ne. Ina ce dai sune kudin da ka arawa kamala".  Kai ya jijiga alamun eh. "Wannan dubu dari biyu da kaga na dauka kuwa Khadijah zan bawa matar kamala domin ta sasayi duk abunda yaranka suka lalata mata wajen fiddo kaya. Daga yau karka kuma kallan gidan nan balle ma kayi mafarkin zai zama naka".   Alhj. Duk a tsorace yake kamar kace arrr! Ya zurq aguje. Yaran shi kuwa sunyi tsaye kem! Kamar wanda aka sasaka. "Kamala! 2×". Safuratu ta kwala mai kira. Da sauri ya amsa suka fito tare da matarshi suma duk tsoro ya kamasu domin idanun su sun gane musu abunda duk ya faru._





_Safuratu tace "Na biya wanna mutumin kudin shi da ya ara maka. Yanzu wannan 400k din dake wajen ka kaja jari ke kuma ga wannan ki saya duk abunda suka lalata miki wajen fito da kaya".  Kamal da matar shi mamki suka cika da shi sai godiya suke. Kana kallan fuskokin su kuwa zaka gane akwai alamar tambaya.  Tsaya Safuratu ta dakawa alhji. Da yaran shi, tashi  yayi ya runtuma a guje haka suma yaran firgigit! Ko wannen su kamar wanda aka tayar daga barci sukayi waje a guje. Safuratu ta mike tace "To ni zan tafi kuma sai wani lokacin. Cikin su ba wanda yace uffan!. Har ta fara tafiya Kamal yace "Dan Allah ke din wace ce?". Jiyowa tayi fuskar ta dauke da murmushi wanda shi ya kara fito da kamanin Yarinyar kwanaki nan take suka gane ta. Safuratu tace "Ni ce Yarinyar da kuka taimaka kwanakin baya. Wannan sakamakon alkhairi ne. Kunsan Allah ma yace . "Shin kyautatawa nada wata sakamako?,Face Kyautatawa".RAHMAN 60 AYA:._





 _"Kuyi hakuri wancan karon da na tafi ba tare da nayi muku sallama ba. Ni kaina naji dadin zama daku. kuma zan so ci gaba da zama daku duk da ni ba mutum bace sai dai kuma ayyukan gaba na baza su barni in zauna tare da ku ba shiyasa ma kawai na tafi a lokacin".  Hawaye ne ya fara zubowa Khadija. "Shin dan Allah yanzu ma tafiya zaki ki barmu?. Kinsan irin Son da ake miki kuwa. Tun ranar da Kamal ya kawo ki gidan nan ya fada min cewa baki da kowa kuma gaki kurma. Hakan yasa na kamu da tsantsar sanki da kaunar ki dan a lokacin sai naji kamar an yaye min bakin cikin da nake ciki na rashin haihuwa. Kwatsam kuma a daren ranar sai kika gudu kika barni. A ranar ga kamal nan wuni nayi ina kuka domin ji nayi kamar Na haihu 'yar ta mutu ne".  Tana zuwq nan ta fashe da kuka Kamal ya kwanto ta jikin shi yana lalashi. Sosai ta bawa Safuratu tausayi domin itama sai da hawayen suka zubo mata. "Khadija kiyi hakuri ki sani cewa aikin da na daukko babban aiki ne bazan iya tsayawa a nan gidan na wasu kwqnaki ba domin in nayi hakan wasu da dama zasu shiga matsala. Zan dai riga zagayo ku in na sama dama in sha Allah. Kuma zan na taya ku addu'a Allah ya baku haihuwa". Da karashe fadar haka Safuratu ta bace._





_Bata bayyana a ko ina ba sai kofar shagon Muktar. Ta bayyana ne a cikin shigar wata tsohuwa almajira fuskar ta duk a yaya mutse, Duk wanda yaga tsohuwar nan sai ya tausaya mata. Faced din shagon matar ta nemi waje ta zauna.  Ba abunda take sai kallan Muktar. Duk juyowqr da zaiyi sai yaga sun hada ido da matar a zuciya yace "Waccen fa ina ga yunwa take ji. Kuma yaseen ko mutuwa zakiyi bazan baki komai ba".  An kwashi mintuna ya kara juyawa yaga dai again shi take kallo abun ne ya bashi haushi a fusace ya fito daga shagon dan bala'i ko rufe wa baiyi ba kanta yaje ya tsaya yana ta surfa masifa sai kace ya sama sa'ar shi. Ita dai ba abunda tace sai idanu da ta kwalalo mishi ko kiftwa batayi. Daga karshe yace "Kinga malam in ma ke mayya ce wallahi kurwata tafi karfen ki. Haba wannan kallo kamar naci ban biya ba". Ganin taki tankawa ya juya ya koma shago. Abun haushi da takaici har yanzu bata daina kalla shi ba. A zuciya tunanin abunda zai mata yake domin iya bacin rai ranshi ya gama baci. Wai tama rasa wanda zata je ta tsare da kallo duk shagunan makwabtan shi sai shi. A fusace ya kara fita ya koma wajen ta masifa har kamar ya dake ta yake. Mutane na ganin haka suka je suka bashi hakuri hade da tada tsohuwar daga wajen.  Can da yamma kuma sai gata hannun ta rike da kwanan bara.  "A bamu saraka a bamu ta annabi. Alllah ya baku mu samu. Ka bada Qalilan rabbana ya maiyar da Kasirran"._






 _Shiru Mukhtar yayi ba tare ya dago kai ya kalle ta ba. Kamar dazun sake maimaitawa tayi "A bamu saraka a bamu ta annabi. Alllah ya baku mu samu. Ka bada Qalilan rabbana ya maiyar da Kasirran". Dogan tsaki yaja.  Tsohuwa bata tafi ba kara fada tayi "A bamu saraka a bamu ta annabi. Alllah ya baku mu samu. Ka bada Qalilan rabbana ya maiyar da Kasirran". A fusace Muktar ya dako "Anki a bada malam dallah ki ware ki  ishi mutane". Kara murtuke fuska yayi "Ke wai me zan miki ne tun dazun kin takura min haba malama ni kadai ne mutum a nan ne. Ko kuma sadakar dole sai ni ne zan bayar..."   Fada yake surfa mata kamar wanda ya sama diyar shi.  Kyalkyale wa tayi da dariyar mugunta. Hannu tasa ta kwaye rabin fatar fuskar ta. Abun da yayi mutukar girgiza Muktar kenan nan take ya kama karkarwa ya zube a wajen yana bata hakuri domin ya gane wace ce._





_Muryar ta ba dadi Tace "Wato dama abunda duk na gaya maka bai shiga kunnen ka ba ko. Naga ma yanzu saura kadan ta rage ma ka fara dukan maryam yarinyar da na baka amana. Da kudin ta fa kake ci kake sha. Amma naira hamsin ka kasa bata".   Muktar yama rasa ya zayi yasan dai yanzu bashi da wani abunda zai kare shi.  Magiya hadata da Allah da annabi yake. Safuratu ta daka mishi tsawa hade da cewa yanzu zan yi ma hukunci kuma irin shi zanci gaba da yi ma muddun baka dai na abunda kake ba. Zan raba ka da duniyar mutane can zan kaika in da bazaka ga kowa ba sai Dabbobi su kuwa sun fika rashin mutunci, kaga sai ku hadu kutayi in baka ci sa'a bama Kora ko zaki wani ya cinye ka".  Tana rufe baki bat! Suka bace yare muktar sai ganin shi yayi a wani kurkurmin daji ba abunda kake ji sai kukan tsuntsaye ga kuma kukan namun jeji. Wata murya da Muktar ya rasa daga ina take fitowa "Muktar wannan shine hukun cin da ya dace da kai zan barka a nan kayi yan kwanaki nasan zaka kara daukan darasin zaman duniya ka gane cewa rayuwa ba komai bace". Hannu muktar ya dora a kai ya fashe da kuka "Dan Allah dan annabi kiyi hakuri wallahi na tuba bazan karaba karki min wannan hukunncin". Shiru yaji ko uffan ba'a ce masa ba. Nan ya durkushe yana ta kuka........................................_




🙆🏻‍♂😧 *MUKTAR DAGA YAU SAI ASAN MUTUNCIN DAN ADAM. KO YA YAKE BA ABUN A WULAKANTA BANE. BAKA SAN KALAN BAIWAR DA ALLAH YA MASA BA*


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 93-94



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



😘😘 *DEDICATED MY ASSOCIATION ZAMANI*


 👏🏻😰 ```FATAN ZAKUYI MIN AFUWA. MUNYI BIKI NE BANA SAMUN TYM DIN TYPE. AMMA YANZU IN SHA ALLAH IDAN NA FARA SAI NAJE KARSHE``` 😟


INA ALFAHARI DAKU MASOYA NA 💃🏻 ANA TARE 😘


_Bayan ya gama kukan ya tashi ya hau zagaye dajin, Yayi yawo sosai amma ko alamar gida balle mutum bai gani ba. Safuratu kuwa gida ta koma ta juye zuwa Muktar din. Haka taci gaba da kula da harkokin sa har na tsawon sati guda. Muktar kuwa na can dajin wani lokacin ma abincin da zaici wuya yake masa,_




 _Loaci daya rayuwa ta juye mai barci sai dai ya sama wani dan kogun dutse ya shiga ya kudundune. Haka kuma ruwa sai dai yaje wani dan gulbi da yaga ruwa na taruwa yasha. Yayi kuka sosai kuma yayi nadamar abunda ya aikata. A zuciyarsa ya kudurci niyar cewa bazai sake aikatawa Maryam makamancin wannan ba. Yayi kudirin zai rike ta da gaskiya kamar yarsa. Haka kuma kwanakin nan  da yayi duk lokacin da yunwa ta takura mishi sai ya dinga tunowa da almajirai masu zuwa wajen shi, Abunda yake zuwa mai a rai shine suma fa haka suke ji yayin da suke jin yunwa. Mukhtar a zuciya yake kudurtar niyar bazai kara hakan ba. Yau aka cike kwanaki bakwai cik! Da kawo Muktar daji. Tun da safe Safuratu ta bayyana mishi nan ta zaunar da shi yana ta tuba yana neman afuwa. Tace "Muktar ya zuciyar taka tayi sanyi ne ko har yanzu cike take da rashin imani da gurin cutar yar da take a matsayin sana'ar ka. Rufin asirin ka".  Muktar da yake durkushe gwiwowin sa a kasa. Harda hawaye, Cikin kuka yace, "Dan Allah dan annabi kiyi hakuri dan Allah ki ceci rayuwa ta ki fitar dani daga wannan wahalar._




_Nayi miki alkawarin cewa bama Maryam ba in sha Allah duk wani wanda yake neman taimako zan taimaka masa gwargwadan iyawata".  Safuratu tayi mai wani irin kallo na tuguma, Kafin tace "Na saba dajin rantse-rantse daga bakin ire-iren ku na karya. To ka sani cewa in har baka daina cutar da maryam Allah, Allah kaji na rantse ko. To gaba daya sai  na amshe duk dukiyar ka ka dawo kamar dai da yanda kake a lokacin da ka karbe musu kudi. Zanje kuma in nemi mutumin kirki in bashi amanar Maryam. Da wannan karon ma abuna nayi niyar yi kenan. Kuma in kana ji wasa to ka sake kwatanta Rashin imanin da kake"._






_Muktar ya sauke ajiyar zuciya yace, "Na rantse miki har da Allah na canzu zaki same ni ba kamar da ba. Domin wannan horan da kika min ya ankarar dani abubuwa da dama. Dan haka ki taimaka ki mayar dani gida. Nayi kudirin ko da kuwa kin kwace Maryam da dukiyar ta daga hannuna bazan fasa wannan kudirin ba. In sha Allah zan taimaka wa duk wanda ke da bukatar in taimaka wa". Wasu kaya Safuratu ta mika mishi tace yaje ya saka su.  Ba dade ba sai gashi ya sanyo su. Makulin shagon ta bashi kafin kiftawar ido sai ganin shi yayi a kofar daki. Dake ya saba da shiru na cikin daji yanzu duk sai yaji hayaniyar nan ba dadi. Bankwana Safuratu tayi mai hade da kara nanata mishi cewa ya kula ya canza hali.  Safuratu yau din nan ta tashi ne da tunanin Fatima kuma zuciyar ta na raya mata ba lafiya ba.  Hakan yasa ta tashi da niyar komawa bauchi yau._


_____________________


_A bangaren Fatima kuwa bayan kwana biyu da tafiyar Safuratu Zuwaira da Hauwa suka  taso ta gaba wai su sai sunga abunda mama Asiya ta gaya musu ko gaskiya ne. Ai kuwa suka fara takura wa Fatima tun suna zaginta har suka fara dankwashi. Ganin ba abunda ya faru ne yasa suka kara kaimi wajen cin zalin ta. Daga karshe ma a gaban jama'a har da kuwa Mama Asiya  hauwa da Zuwaira suka karbe yar babyn Fatima sukayi gutsun-gutsun da ita. Nasmat, Asmart, Ameera, da Mama Asiya duk sai suka fara tausaya wa su Zuwaira a kan abunda suka wa yar babyn dan a tunanin su Aljanar in bata kashe su ba sai ta kusa. Su kuwa su Hauwa hankalin su ko tashi baiba._





_Daga karshe ma tatara yar babyn sukayi suka kone ta rumus a tsakar gida. Fatima ta fara kuka   ai kuwa suka same ta suka ta narka taci duka har sai da ta gode wa Allah.  Bayan kwana daya-biyu su Mama Asiya sunyi mamkin ganin ba abunda ya faru da su Zuwaira gashi kuwa kullum cikin duka da zagin Fatima suke. Hakan yasa suma gaba daya gidan suka koma ruwa. Wato kowa ya koma kamar da zalluncin da ake wa Fatima har ya kusan linka na da ma. Haka abba yanzu kusan kullum sai ya daki fatima ko ya aike ta gu mai nisa. Fatima na shan wuya sosai. Dan ko yau haka ta tafi makaranta ko guntun biredi bata ci ba. Safuratu na isa gidan tace ta duba dakin su Fatima bata ganta ba. Shiyasa tayi tunanin ko tana makaranta ne. Sai dai  kuma ta duba inda Fatima ke ajiye babyn ta amma bata ga komai ba. Hanyar makarantar ta nufa. Dan daga nan har sai da ta shiga gidan Umar. Kallo daya tawa Rafy ta gane cewa tana cikin farin ciki. Domin sai aikin gida take hankalin ta kwance tana wake-wake._





_Nan dai ta bayyana suka gaisa take tambayar Rafy ya zama gidan. Rafy tayi mata godiya tace ai yanzu suna zaman lafiya sosai da mijin ta. Hamdalla Safuratu tayi nan dai suka hau hira. Safuratu kam hankalin ta duk yana wajen Fatima. Lokacin ta so su Fatima nayi tayi sallama da Rafy ta fito ta taryi Fatima.  Tafe take tana wani rangaji kamar zata fadi, sai zubar hawaye take. Ba komai akayi mata ba yunwar ce kawai ke cinta domin bata saba kai war haka bata ci komai ba.  Daga nesa Safuratu ta hange ta. Karasa wa kusa da ita tayi tana kare mata kallo. Irin  ramar da Fatima tayi ne abun ya tsorata Safuratu. Domin in ba kayi wa Fatima kwakwaran sani ba. Bazaka iya gane ta ba a yanzu. Dan duk kashin wuyanta ya fito ta rame sosai. Tangal-Tangal din da Fatima keyi har idanta na rufewa hakan ya shedawa Safuratu Fatima najin matsanan ciyar yunwa._







  _Sharf!  Fatima ta fadi kasa Safuratu na ganin haka tayi sauri ta shiga jikinta. Mutane har sunyo kanta da niyar agaji kuma sai sukaga Yarinya ta mike.  Karasowa sukayi wasu na kakabe mata jiki suna mata sannu. Idanun Fatima suka kara zarowa daga ka ganta zaka ga ba kamar da ba. Yar ledar littatafan Fatima ta dauka ta nufi gida. Kwan! Kwan! Kwan! Kwan! Da karfi Fatimar ke buga gida. Mai gadi najin haka ya taso a rikice yana fada yana fadin "Waye wannan yake mana irin wannan buga gida kamar tashin duniya".  Buga gidan bana wasa bane domin da karfi Fatima ke bugawa.  Har mai gadi yazo yana kokarin budewa amma bata dai na bugawa ba. Yana budewa yaga itace. Ya tsaya tsabar haushi har karkarwa yake. Dan ji yayi kamar ya mare ta duk da tana yar gidan. Fatima ganin mai gadi baya da niyar matsawa. Fuuu! Ta bangaje shi ta wuce can ya fadi kasa a gigice. Domin irin bangajewar da Fatima tayi mishi ba karamin kato bane zai yi masa ita har ya fadi. Yayi mamaki sosai. Tashi ya kakabe jiki ya juya yana kallan Fatimar domin ya kara tabbatar da ita din ce ko wata.







_"Tabbas Fatima ce, to amma ina ta sama wannan karfi haka".  Shi kadai yake kallan ta yana magana shi daya. Kofar falo Fatima ta ja da karfi kamar zata ballata. Yanayin yace labulan kadai kai in ka gani kasan bana arziki ba.  Hauwa ce kadai a dan ringeshe kan sofa tana tauna Cingum tana daddana waya. Tana jin shigowar Fatima ta tashi zaune. Ita Fatimar ta nufo. Ita kuwa wani matsiyacin kallo take bin Fatima da shi mai dauke da harara._






_"To shegiya har an taso daga makaranta wato za'a zo a ishi mutane da kuka. To kafin ki fara komai ajiye kayan makarantar ki shiga dakina kiyi mopping dinshi ki gyara komai kafin kizo in fada miki next work naki". Fatima kam tsaye take ta kafe Hauwa da ido bata ko giftawa. Hauwa ganin Fatima taki wuce wa tayi abunda tasaka ta tace. "Ke dan uwarki ba kiji abunda nace kije kiyi ba. Yar buhun uba kin wani tsare ni da wannan shegun idanun naki. Ko dai na jaki kike so yan...".   "Ina abincina?".  Shine abunda Fatima ta fada hakan yasa Hauwa bata karashe maganar da ta fara ba.  "Iyee Fatima ni zaki wa rashin kunya?.  To bari kiji dan ubanki ko langen taliya bazaki ciba yau a gidan nan. Oh! Baki ji abunda aunty zuwaira tace ba ken...".  Cikin tsawa da kagara Fatima ta kara fadar, "Ina abincina na ce?".  Abun ne ya fusata  Hauwa hakan yasa ta daga hannu da zafin ta da niyar wanka wa Fatima lafiyayan mari. Charf! Fatima ta rike hannun hade da Wanka wa Hauwa mari da dayan hannun ta................................._


😳😰 *MU GYARA ZAMA KENAN SAFURATU TA SHIGA JIKIN FATIMA KOWA ZAICI UBANSHI* 😂😂😂


Domin samun farkon labarin shiga pagen mu kayi like.

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


Shiga nan ka/ki yi  like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn 

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  king boy







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 95-96



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



🤣🤣😂😂 *KU KARANTA KU TAYANI DARIYA. FATIMA TA FARA ZAMA ABUN GUDU* 😱


DUK DANIN PAGEN SADAUKAR WA NE GARE KU 👇🏼👇🏼

_*NERBEELERT LADY NOVELS*_ 





💃🏻💃🏻💃🏻 _INA MAKU FATAN ALKHARI... DAN ALLAH MASOYA KUYI HAKURI_

          💃🏻💃🏻💃🏻


💃🏻💃🏻💃🏻

_KOMAI ZAI DADI A DUNIYA BAIYI MASOYA BA.... SO YAYI MIN RANA DAMA DA BAZARKU NAKE TA RAWA KUNA INA?.._👯👯🕺🏻


🥁 _WANI TAMBURAN GIRMA NA BUGA DOMIN MASOYA NA. DA BAZAR KU NAYI RAWA AN MIKA HANNU A HANNU NA. MAMAN HANAN TA NUNA LALI KUNA SONA.  MAI ZAN MUKU IN RAMA._ 👯🕺🏻 _A RAI NA INA SAKA. INA MASOYANA?._ 🗣 _KU FITO_

 

_*NERBEELERT LADY NOVELS*_ 

🖕🏼 SAKONIN KU YA RISKE NI. HAKIKA KU MASOYA NA NE. INA MATUKAR JIN DADI. SANNAN INA MUKU FATAN ALKHAIRI DAGA ADMINS HAR MEMBERS NA WANNAN GIDA MAI ALBAKA. 😘 *ANA TARE*




           *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Cikin tsawa da kagara Fatima ta kara fadar, "Ina abincina na ce?".  Abun ne ya fusata  Hauwa hakan yasa ta daga hannu da zafin ta da niyar wanka wa Fatima lafiyayan mari. Charf! Fatima ta rike hannun hade da Wanka wa Hauwa mari da dayan hannun ta.~


_*G*alala Hauwa ta saki baki tana kallan Fatima cingum din da take ci ma bata san lokacin da ya fado ba. Rike kunci tayi tana jin radadi a zuciyar ta tana fadar "Anya wannan Fatima ce?".  Hannu Fatima ta sake dagawa da nufi mari "Ina abincina nace?".  Da sauri Hauwa tace "Bari in daukko bari in daukko miki". A tsorace ta mike ta nufi kitchen din Fatima na binta da wani malalacin kallo._





  _Hauwa taje ta zubo mata abincin ta kawo. "Yauwa Fatima ga abincin".  Ta mika hannun ta na dan karkarwa.  Fatima na amsa ta zauna a nan ta fara cin abincin hannun baka-hannu kwarya. Juyawa Hauwa tayi da nufin haurawa upstair dakin ta. "Ina kuma zaki je dawo ki zauna". Fatima ta fada ba tare da ta dago kai ta kalle Hauwa ba.  "Umm umm da... Da.. Ma zanje ina... Jin fitsari nee".  Hauwa tayi maganar murya na karkarwa. Dan duk ta tsorata da Fatima tasan ba ita kadai bace, Akwai lauje cikin nadi. "To ba yanzu ba dawo ki zauna". Fatima tace ba tare da ta kalle ta ba. Hauwa har zatayi magana. Fatimar ta daka mata tsawa hakan yasa ta gimtse bakin ta. Sumi-sumi ta zo ta zauna. Sai kallan Fatimar take wanda sai cin abincin take kamar wacce tayi shekara bata ci ba. "Innalilahiwa'inailaihirraji'un 2×, Me zan gani haka".  Zuwaira ce ka fadar haka lokacin da take saukko daga kan matakalar tayo kasa._





_Da sauri ta karaso gurin ta tsaya kan Fatima tana zazaga masifa. "Hauwa haka mukayi dake wato in kafa doka har kin isa kisa kafa ki shure ko?. Wato wuyanki yayi kwari, Ni dake waya fara shigowa gidan nan ko da baki min biyayya a matsayin ki na kanwata wacce nafi shekaru ba. Ai ya kamata kiyi min biyayya a matsayina na wacce ta riga ki shigowa gidan nan". Hauwa kallan Zuwaira kawai take tana kallan Fatima dake faman dibar Shinkafa fara da miya. batace ko kala ba. Zuwaira taci gaba da cewa "Sanin kanki ne nace yau yarinyar nan bazata ci ko kwayar shinkafa ba a gidan nan amma gashi nan kin dauka kin bata. Wato ke uwar tausayi. Zanyi maganin ki kuwa". Hauwa kallan Zuwaira kawai take tana mata wani kalan uku goma hudu shabiyar. Kasan ranta kuwa  addu'a take Allah ya kai damo ga harawa._




_Fatima ce ta mike rike da filet din abincin. Kamar jira take Zuwaira na juyawa kuwa ta yaba mata shi a fuska. Bata jira komai ba ta juya ta nufi dakin su.  Hauwa na ganin abunda ya faru ta kwashe da dariya harda rike ciki. Zuwaira kuwa cik ta tsaya kamar wacce suka gasar tsayu ita da gunki. Haushi ya kule ta can kasar ranta tunanin abunda zatayi wa Fatima take. Dan kakabe jikin ta tayi miya duk ya bata mata kaya. In ka ganta sai ka rantse wasa da miya tayi.  "Ni ni ni Fatima tayi wa haka,_





_Lalai Yarinyar daga ni kuwa bazaki kara ba. Yau ko makiyin ki sai ta tausaya miki Fatima".  A fusace tayi waje, Nan take zuciyoyi suka shiga aikin bata shawarwari na mugunta wanda zatayi wa Fatima. Dakin mai gadi ta zarce. "Fito-fito mai gadi, Ina wannan dorinar taka mai baki biyu?".  "Tana daki Hajiya". Har dan jijiga take yi dan kaguwa "Bani aranta yi sauri dan Allah".  Kallan ta ya tsaya yana yi "Hajiya wa kuma za'a daka da ita. Naga yaran duk suna makaranta?". Tsawa ta daka mai, Nan da nan ya zabura ya shiga daki ya daukko mata. Yana bata ta nufi wajen tankin ruwa ta debi ruwa a irin yan kananun bokitin nan. Ta nufi falo da shi. Fridge ta nufa da sauri ta daukko kankara ta zuba a ciki tukun ta shiga tsiyayya ruwan sanyi. Ita kadai take magana. "Dan ubanki ai yau kin shiga uku sai na jikaki da ruwan sanyin nan tukun in miki dukan kawo wuka. Badai ni kika wa wannan wulakancin ba".  Tana gana matse pure water mai sanyi ta dauki dorinar da bokitin ruwan wanda zuwa yanzu tuni ruwan yayi mugun sanyi. Ta nufi dakin su Fatima. Hauwa dai na zaune a falo ido kawai take binta da shi._






_"Ayi dai mu gani in tusa tana hura wuta".  Inji Hauwa ta fada da dan karfi. Zuwaira taji ta amma bata kula ta ba. Dashigar ta dakin ta fara kwallawa Fatima kira. "Fatima! Fatima! Fito dan kut...uban ki. Yau ai sai kin raina kanki". Shiru bata ji ko motsi ba. A tunanin ta  Fatimar na ban daki. "Ki fito na gaya miki dan Wallahi in na iskeki a bandakin nan bazamu kwasheta da kyau ba. Sai nayi miki jini da majina Wallahi". Nan ma shiru bata ji an tanka ba. Bulala da bokitin ruwa ta dauka buzun-buzun ta nufi ban dakin da zuwa tasa kafa ta haura kofar da karfi. Kofa na budewa taga wayam. "Shegiya asbe ta gudu daga dakin". Falo ta fito "Hauwa ina wannan shegiyar Yarinyar ta nufa da ta fito?". Hauwa ta kalli Zuwaira Mamaki karara a fuskanta. "Au! Fatiman fitowa tayi ne?". "Kina nufin baki ma ga wucewar ta ba?. Fatima zaki gama guje-gujen ki kidawo ki iske ni har gida". Zuwaira ta fadi haka ta ajiye bokitin da bulalar a gurin, ta nufi Upstair da niyar taje dakin ta canja kaya._





_Da bude daki ta tsaya cik! Tana karewa tsakar dakin kallo Fatima ce gaba daya ta bince ke wardrobe din da su kabbet duk ta wurwatsa kaya a  tsakar daki. Yanzu ma sai bincike take tana bubude lokoki. "Aunty Zuwaira jan baki nake ta nema tun dazun a ina kika ajiye shi". Wani kululun bakin ciki ne yazo wa Zuwaira makogoro. Nan take ta kai dubanta Mirror ta hangi duk kayan kwaliyar ta har da jan bakin ma a wajen, "Wai amma dan rainin wayo wannan yarinyar tace wai jan baki take nema. Kai kawo dai wani tashen iskanci da rainin wayo ne. Amma bari inyi maganin ki yanzu". Jawo dakin tayi da sauri ta koma falo da gudu ta daukko bokitin ruwa da bulala.  Tana dawowo  ta bude daki kuma sai gani tayi wayam! Ba kowai sai tilin barnar da Fatima tayi mata. Domin shirya kayan da Fatima ta warwatsa kadai jarabar duniya ne. Gashi wasu kayan a goge ma suka amma Fatima ta kara tattake su. Hauwa na zaune a falo taga Fatima ta fito daga saman beni bayan ita kuma bata ga fitowar ta daga dakin su bama. Abun ne ya kulle mata kai. Fatimar tafe take hannun ta rike da dan karamin mirror na kallan fuska dayan hannun kuma jan bakine da take ta faman Gogawa a lips inta.  Tsaye taje tayi a kusa da Hauwa tana shafa jan bakin. Zuwaira tun daga sama kake iya jiyo jarabar ta. "Yarinyar kamar Aljana,yanzu nan fa na baro ta a dakin nan wai amma bata nan. Hmm dani kike zancen Fatima._





_Ai Wallahi in dai kere na yawo zabo na yawo wataran a hadu. Wai ni ta...".  Bata karashe fadin abunda tayi niya ba hango Fatima da tayi a falo. Nan take ta fara sauri tana kokarin sakkowa. Fatima hanyar dakin su ta nufa. Zuwaira dake rike da bokiti da bulala a hannu da gudy taje tasha gaban Fatima. "Ina zaki munafuka Allah ya kama ki. Yanzu zan chaskwala ki".  "Bani waje in wuce". Fatima ta fada cikin kagara. "Iyeee! Lalai Fatima arzikin rashin kunya yaci uban na da.Har ni zaki iya kallan kwayar idona kice wai in matsa ki wuce. Bari ki karbi hukunci tukun sai ki wuce ko da jan gindi ne". Kokarin ajiye ruwan take. Ai kafin ta ajiye wata irin bangaza da Fatima tayi wa Zuwaira can ta fadi kasa bokitin  ruwan yayi sama ya fado duk ya jijika Zuwaira da Carpet din falon. Wata mahaukaciyar  dariya hauwa ta kwashe da ita. Har da rike ciki hade da hawayen dariya._


_Zuwaira tace "Hauwa wai Giwa ce ta bangaje ni ko Saniya ko Rakumi?".  Hauqa kara kwashewa tayi da Dariya. Cikin matsanan ciyar dariya tace, "Duk ba ko daya a ciki".  "To dan Allah jirgin kasa ne ko mota._




_Domin kuguna ji nake kamar ya karye bani iya tashi yanzu".  Hhhhhhhhhhhhhhh Dariya kamar zata kashe ta. Karar dariyar ta ne ya tashi Mama Asiya dake can sama tana barci. Da sauri tayo Downstairs tana "Lafiya-lafita mi yake faruwa ne?".  Falan taga kaca-kaca Can an watsar da shinkafa da miya. Nan an kwarayar da ruwa. Hauwa ta kalla dake ta faman Dariya. "Ke kuma wanne irin iskanci ne zaki bata mana falo haka. Nan fa ba falon ki bane ke kadai balle kiyi mana kazanta".  Hauwa ta dan rage dariyar kadan tace "Aunty Asiya Wallahi bani bace aikin Fatima ne".  "Kuturun kareee!  Wace Fatimar?".  "Fatima tamu ta nan gidan mana". Cikin fusata Mama Asiya ta nufi dakin su Fatima tana fadar. "Ina take dan ubanta Wallahi sai ta gyara dakin nan tsaf!"................................................_



🤣😂 *Wayyo cikina* _HAUWA DOLE IN TAYA KI DARIYA. SU ZUWAIRA MADARA ANJI JIKI, SAI KUMA A TASHI AJE AYI JINYA_ 🤧


_*KU BIYO NI ZAI-ZAI DAN WANNAN KARAN WANDA AKAYI BABU SHI BAI MORI LITTAFIN BA*_ 🤝



DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah










👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 97-98



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*



DAN KADAN NE DAI. KUNSAN ANCE *"DA BABU GWAMMA BA DADI".*




*DEDICATED TO* 👇🏼👇🏼



😍😍

      *BIGBOY ISAH FANS*

        😍😍

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

               😍😍

*GIDAN MARAYU FANS CLUB*

                       😍😍

*3STAR HAUSA NOVELS* 💃🏻

😘 GODIYA TA MUSAMMAN GARE KU TARE DA FATAN ALKHAIRI. BANI DA KALAMAI KO AZANCI DA ZAN IYA MUKU GODIYA DA SHI. SAI DAI KAWAI ALLAH YA BAR MU TARE.



      *KARSHEN PAGEN BAYA*

~MUN TSAYA A INDA HAUWA TACE, "Aunty Asiya Wallahi bani bace aikin Fatima ne".  "Kuturun kareee!  Wace Fatimar?".  "Fatima tamu ta nan gidan mana". Cikin fusata Mama Asiya ta nufi dakin su Fatima tana fadar. "Ina take dan ubanta Wallahi sai ta gyara dakin nan tsaf!".~


_Mama Asiya na shiga ta iske Fatima zaune a gefan gado ta juya mata baya. "Fatima! Fatima!2×".  Shiru fatima ko waigowa batayi ba. Kara matsawa wajen ta tayi "Ke dan iskanci da rainin wayo kinaji ina kwala miki kira amma kikayi banza dani. Zonan dan ubanki". Gashin kan Fatima ta kama ta jawo ta kiiii! Har cikin falo, "Maza jeki daukko kayan mopping kizo ki tattara shinkafar nan da kika zubar ki wanke wajen miyar nan da kika zubda. Sannan in kin gama ki daukko tsumma kizo ki matse wannan carpet din da kika zubda ruwa a kai". Harara kawai Fatima ke binta da shi. Hauwa da Zuwaira dake zaune kan armchair tana wash-wash ba abunda suke sai kallan Mama Asiya da fatima. Zuwaira fatan da take shins Allah yasa Mama Asiya tayi ganganci wa Fatima._






_Duk maganar da Mama Asiya take Fatima ba abunda take mata sai mugun kallo. Mama Asiya da ta gama jawabin nata ta juyo taga Fatima na hararen cikin fada tace "Ke Fatima ba magana nake miki ba. Wallahi tallahi in raina ya baci bazaki ji dadi ba. Dan ba wanda ya isa ya kwace ki a gidan nan...". Duka ta kaiwa Fatima dim!  "Ni kike wa gatsine da uban ki. Bari ki gani".  Juyawa tayi ta dakko dorinar wajen Zuwaira. Fatima na ganin haka ta kyalkyale da dariya lokci daya kuma sai ta hade girar kasa da ta sama. "Zaki iya duka na da bulala. Na baki offer nan. Amma ki sani cewa duk bulala daya idan kika min ni goma zan miki". Mama asiya bata dakata ba ta nufo Fatima tana zuwa ta lafta mata balula. "Wuce kiyi abunda na saki". Wani malalacin kallo Fatima tsare mama Asiya da shi. Dan bulalar da aka mata sai ka rantse ba jiki aka daka ba domin kuwa ko motsi batayi ba. Mama Asiya ta kara buga mata bulalar tana nuna mata hanya da hannu._






_}"Ki wuce kiyi abunda na saki nace ko?".  Zata kara mata ne Fatima ta rike bulalar.  "Bulala ashirin ya ishe ki dan wannan jikin naki ba lalai ya dauki talatin ba". Tunanii mama Asiya ta shiga yi nazari take akan maganar da Fatima ta fada. Domin ita bata gane nufin ta ba. Tana tsakar tunani sai ji tayi Fatima ta fisge bulalar daga hannun ta ta Zura mata._





_"Wai-wai wai.. Fatima ni kika dak..". Ai kafin ta rufe baki ta kara jin saukar wata bulalar. Hakan yasa ta nufi Fatima da nufin ta kwace bulalar. Da gudu ta shige ta. Hakan yasa Fatima tayi saurin gocewa kuma tasawa Asiya kafa. Rigijimmm!  Kake ji ta Fatima. Su Zuwaira in banda dariyau ba abunda suke yi. Sai dai kuma daga Fatima ta harare su sai kowacce ta matse bakin ta. Fatima kan Mama Asiya taje tana Maka mata bulala tana kirge. "3..4..5..6..". Mama Asiya na tashi ta kara nufar Fatima a fusace. Tana Zuwa kusan ta Fatima ta kara sa kafa ta hangiza ta baya._





 _Tagal-tagal ta tafi zata fada kan Coffee tabal din dake tsakar falo. Ganin in ta fada kanshi ya gama aiki dake na Glass ne  da sauri Fatima ta rike hannun ta. Ta mike tsaya. Ko da taga ta mike sai taci gaba da dukan ta. Wannan karan Asiya da gudu ta hau zagaye falon tana neman dauki. Fatima na binta tana zana. Duk wacce mama Asiya ta nufa. Hauwa ko Zuwaira sai su arce a guje. Sai da Fatima tayi mata bulala ashirin cik!. Tukun ta zauna kan kujera tasa Mama Asiya tayi Kneltdown a gabanta. Dage kai tayi gefe ta fara wa mama Asiya magana kamar yanda tayi mata dazun._





_Cikin gadara fatima tace, "Maza jeki daukko kayan mopping kizo ki tattara shinkafar nan da na zubar, ki wanke wajen miyar nan da kika zubda. Sannan in kin gama ki daukko tsumma kizo ki matse wannan carpet din da kika zubda ruwa a kai".  Jikin Asiya har yana rawa tace "To to an gama ranki shi dade". Zuwaira da Hauwa sun jin haka suka nufi Hanya zasu tsere._




_Kan Fatima a kasa ba tare da ta dago ba tace, "Ku muna fukai na baku damar tafiya ne?". Tsaye cik! Sukayi suna kallan juna. "Ku dawo nan ku tayata wannan aiki.  Bari inje in siyo halawa. Kuma saura inzo inga wata bata abun da na sata. Uhmmm Wallahi da jaki ma sai ya tausaya mata".  Fatima na fadar haka ta mike har ta nufi kofa kuma ta juyo. "Au!  Ashe ba kudi a guna". Kallan su tayi daya-bayan-daya Suma ita suka kwalalowa ido kamar wasu mujiyoyi. "Mai nera dari ta bani kun wani kwalalo min idanu. To tubarkallah kuci kanku".  Dajin haka suka shiga raba idanu, Suna kallan junan su. "Kaaaaaaaaaaaaaa! Daku fa nake". Wannan muguwar kuwwar ta daka musu wanda yasa duk sao da suka rufe kunnuwa. Dajin haka har rige-rige suke wajen daukko kudin._





_Zuwaira ce ta fara kawo mata. Hannu na karkarwa kamar wacce ke rawar sanyi ta mika mata  hade da cewa "Gashi dari biyar ne ba canji".  Wata muguwar harara Fatima ta bita da shi tukun ta karbi kudin fuuuuuu! Ta wuce. Dai-dai lokacin Mama Asiya da Hauwa suka fito da sauri ko wanne rike da kudi.  Zuwaira ta juyo "kudin ku sun huta. ta ai ta tafi". Mama Asiya tayi ajiyar zuciya hade da kallan su gaba daya "Shin mai kuka fahimta game da lamarin nan".  Kamar hadin baki su hauwa sukace. "Aljanar ce ta shige ta ba wani abu ba". Mama Asiya tace. "Haba nima nayi tunanin haka. Ji yanda Yarinyar ta juye lokaci guda ta zama abar tsoro. Ai kuwa sai munyi taka tsantsan domin Wallahi wannan zata iya sabauta mutum".  "Ahh! Ni Zuwaira yau naga tashin hankali. Gaskiya dole mu dauki matakin gagawa". Hauwa ce tace "Kunga Wallahi gwara muyi abunda tace kafin tazo ta fatatake mu". Mama Asiya ce ta koma kan kujera ta zauna._







_Da ganin haka itama Zuwaira ta je ta zauna.  Hauwa tayi musu wani irin kallo a gantsare tace "Shin me hakan ke nufi?. Ko kuna nufin bazakuyi aikin bane?". Su Mama Asiya kallo kawai suke binta da shi.  "Chabb! In kuwa haka ne Wallahi nima bazan yi ba. Gwara in Aljanar ta dawo tayi mana koma miye a tare".  Hauwa na fadar haka ta nufi wajen su ta nemi waje itama tayi zamant...................................................._



😰👏🏻 Kuyi hakuri da wannan kuyi min afuwa. Wallahi sai da karume-karume nayi type din nan. 😆 Sai na fara sai kawai wani uzurin ya zo. Yanzu haka wani abokina ne  ya kawo min ziyara. I'm busy 😰


DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 99-100



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ✍🏼  *®Z.W.A*


_*WANNAN PAGEN NAKA NE AUTAN ELOQUENCE. ALEWAR KANKANA MELODY*_



_Ku bani kidan birthday a sama._


💃🏻💃🏻 Autan- Eloquence,  Kuce min Auta Eloquence Today is u birthday 💃🏻 Today is you birthday 💃🏻💃🏻.


🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂

*HAPPY BIRTHDAY MUSA MELODY AUTAN ELOQUENCE*


🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰


_Happy birthday Melody wish you many more Albarkakun years  head_ 😍😘


🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂


Allah ya yafe maka zunubanka na shekarun da suka wuce. Kuma allah ya baka wasu shekarun Masu albarka 💃🏻💃🏻​





     *KARSHEN PAGEN BAYA*

 ~"Chabb! In kuwa haka ne Wallahi nima bazan yi ba. Gwara in Aljanar ta dawo tayi mana koma miye a tare".  Hauwa na fadar haka ta nufi wajen su ta nemi waje itama tayi zamant.~


_*M*ama Asiya na ganin hauwa ta zauna sai tace, "Haba hauwa wai ke a zatan ki bazamuyi aikin bane?. Haba mu mun isa. waya isa yaki yi aljana ta zo ta karyashi. Kinga dama ni jira nake ki daukko kayan ne fa".  "Yauwa nima abunda na gani kenan". Cewar Zuwaira. Hauwa tace "To ai da na dauka  nufin ku bazakuyi ba ne". Fita tayi ta kwaso kayan mopping Har su tsintsiya da abun kwashe shara.  "To ku tashi gashi na daukko".  Mika mama Asiya tayi "Wayyy! Wallahi ni kam duk na gaji please dan fara. Kafin in taso". Zuwaira tace, "Ashe bani kadai ba gajiyar nan. Kinji kuwa yanda kuguna yake kamar zai balle"._




 _Cikin hantara "Dallah yi min shiru muguwa kawai. Ai ban taba sanin ku mugaye bane azzalumai yan bakin ciki sai yau". Kallo suka tsare ta da shi, Yayin da ita kuma taci gaba da magana. "In ba zalinci ba kunsan cewa Yarinyar nan Fatima ba lafiya lau take ba, Kuna ganin zan mata ba dai-dai ba amma kuka ki dakatar dani...".  Tun kafin ta krasa maganar Zuwaira ta karbe ta da cewa "Wannan kuma Hauwa zaki cewa muguwa. Domin tun farko ita tasan cewa Aljanu sun shiga jikin Fatima amma taki wa mutane magana".Yar dariya Hauwa tayi hade da cewa, "Daga baya kenan. Ku tashi muyi aikin nan tun wuri Wallahi". Ganin basu da alamar tashi ita ma hauwan ta zauna hade da cewa "Wallahi bazanyi sharar nan ni kadai ba. Gwara in ta zo ko kashe wa zatayi ta kashe mu tare"._






_"Kanki ake ji".  Cewar Zuwaira.  Zaune suke kowa da tsoro a zuciyar shi, amma cikin su ba mai so a gane yana jin tsoran. Karar bude kofa sukaji.  Ai kafin kace kwabo, Tuni ko wacce daga cikin su ta tashi da sauri ta dauki abun ta fara aiki.  Su Asmart ne suka shigo gidan. Su mama Asiya na ganin su. Kowacce ta yarda abun hannun ta ta koma ta zauna. Mtsweeee!  Mtsewwww! Mtsewww Sautin tsaki kawai kake ji yana tashi. Su Nasmat kuwa mamaki ne ya cika su. Daga shigowar su sunji an tarye su da tsaki.  Har sun nufi dakin su Zuwaira ta kira su. "Kuyi sauri ku cire uniform din islamiyar nan kuzo ku share gurin nan".  To suka ce ciki-ciki suka wuce suna gun-guni. Bayan sun fito ne suka kama aiki, Fuskar su ba mai annuri kamar ta shanu sai gunguni suke. "Wai daga dawowar mutum daga makaranta ko hutawa baiba a saka shi wani shar...".   Shigowar Fatima ya hana Asmart karashe maganar zucin da take._





_Lollipop ne a bakin ta yana tsotsa ga wani biscuit a hannunta. Su mama Asiya gaba daya sun tsorace dan Zuwaira har yar karkarwa take. Nasmat tace "Wannan Yarinyar kuma uwar wa ta bata kudi har ta sayi wannan katan biscuit din?". "Uwarki ce ta bata".  Zuwaira ta bata amsa.  Shiru tayi tana kallan uwar tata da duk ta lura da yanayin ta a tsorace take. Asmart tace "Ke Fatima zo nan dan ubanki ki share wajen nan kal!, ki goge". Da sauri Mama Asiya tace "Sai dai ni uwar ki in share". Da fadar haka su Asmart suka fara tunanin akwai lauje cikin nadi. Fati dake bin su Zuwaira daya bayan daya da harara sai yanzu tayi magana tace wa su Asiya "Ku ku tashi ku tafi abun ku". Har rige-rige suke wajen tashi. Zuwaira har ta kusan zuwa Stairs ta juyo. "Uhmmm! Fatima chanji na fa". Cikin gadara Fatima tace, "Na bawa almajirai sadaka. Ko da magana?". "Aa"._




_Zuwaira tace ta wuce sama da sauri Fatima rufe ido tayi kamar me gyangyadi. Cikin tsawa Asmart tayi magana "Ke Fatima in kika yarda na  karaso wajen ki wallahi sai kin raina kanki". Shiru bata bude ido ba balle tayi magana. Nasmat dake kallan tace, "Ke wai ba magana ake yi miki ba?. Kin wani rufe ido kamar kazar dake gwaida".  A fusace Asmart tayo kanta da nufin ta dake ta._






 _Fatima na bude ido tayi turus! Asmart taja birki tayi baya a guje. Haka itama Nasmt bata san lokacin da ta tsallake kojera ba ta wuce.  Kofar dakin su sukaje zasu shiga kenan sukaji an turo kofar da karfe.  Ba komai ne ya tsorata su ba. Idanun Fatima ne suka koma baki kirin gashin kanta ya wani mimike tsaye. "Ku dawo ku share gun nan. Ina zaku?". Suna karkarwa hade da kankame juna suka juyo. "ba inda zamu".  Cikin tsawa tace suzo su share gun. Da sauri suka taho suka hau aiki. Rufe ido Fatima tayi ta sake bude wa nan take kuma idanun ta suka dawo Normal. Su Asmart sai shara suke suna goge carpet ita kuwa Fatima ta mike kan Sofa Sweet take sha abunta tana wasa da Biscuit dinta.  Abba ne ya shigo yana jin waka._






 _Ganin su Asmart na aiki Fatima a kwance ya daka mata tsawa wai ta tashi ta taya su aikin.  Fatima ko kallon shi batayi ba. Su Asmart ne suka ce yaje ba komai zasu karasa aikin. Washe gari da safe. An zuba wa kowa abun kari Indomie da biredi sai tea.  Asmart da Fatima gefan su guda. Fiddausi da amira ma. Haka suma yan kanana yaran. Sai abba da ya dawo falo ya zauna a nan yake break din.  Fatima ce ta fito daga dakin su ta nufi Dinner. Bata wani tambayi ina abincin ta ba taje ta dauke Tea da indomie na gaban Mama Asiya. Da ganin haka Abba ya daka mata tsawa. "Ke dan ubanki sa'ar kice da zaki daukar mata abinci".  Wata muguwar harara ta watsa mishi. Hade da murguda baki "Nata nake so kuma shi zanci in ka isa ka hana. Kuma ko da naka naga damar ci shi zanci".  Fatima ke kallan shi tana maganar. Tashi yayi ya nufi dinner din a fusace._




_Mama Asiya kamar ta dakatar da shi kuma wata zuciyar sai ta bata shawarar cewq ta barshi watakil Aljanun Fatima mata kawai suka raina.  Abba yana zuwa ya daga hannu ya kai mata mari, cikin hanzari ta goce.  Duka ya kara kai mata da kafa. Nan ma ta goce tana binshi da wani shu'umin kallo tana murmushi.  Mama Asiya da ta lura d Fatima da sauri ta zo ta janye danta dan kar a sabauta mata shi. Shi kuwa tuni ya hau daukin zuciya sai huci yake. Yana hararen Fatima da ita kuwa ko kula da shi batayi ba taje kusa da Fiddausi ta zauna tana shan tea.  Tana gamawa ta tashi  zata fita waje. "Ke dan uwar ki dawo kije kiyi shirin makaranta". Cewar Abba.  Ficewa tayi ba tare da tace mushi komai ba.  Abba yace_






 _"Fatima ina tausaya miki. Dan Wallahi in na kamaki daga ni sai ke sai nayi miki fata-fata, Dan yau naga kin tashi da wani sabon salon iskancin". "Ko?". Fatima ma juyo tace mishi. Kofin shayin dake hannun shi ya wulla mata.  Ba abunda ya bashi mamaki sai ganin da yayi kofin yayi Kwana ya nufi wani wajen. Bayan ya gama shan shayin ya tashi ya nufi dakin shi domin yaje ya huta.  Yana shiga kafin ma ya bude kofa yaje kofar ta rufe kanta da karfki. Tsuru Abba ya tsaya yana kallan Kan bad dinshi wani abu ne cikin Blanket dinshi Yana gurnani marar dadi yana kuma mamotsawa._






 _A hankali Abba ya nufi wajen hannun shi har karkarwa yake. Duk ya gama tsoracewa domin shi bai bar kowa a dakin ba. Kuma baima taba jin gurnani kalar wannan ba. Zuciyoyin suka shiga bashi shawara wata zuciyar na cewa ya bude yaga miyr wata zuciyar kuma na cewa ya fita ya gayawa su Mama Asiya. Ta wani fannin kuma ceqa yake "inje in sanar da su kamar dai ni din va namiji bane. Bari kawai in bude inga miye.  Hannun na karkarwa sai ya kusa kama bargon kawai sai yaja baya a tsorace. Kusan sau biyar yana yin haka. A na shida ne ya daure ya kama bargon yaja da karfi. Ahhhhhhhhhhhhhh! Ya sakk ihu!............................?.....?......._






DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah









👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 101-102



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_



        *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ta wani fannin kuma ceqa yake "inje in sanar da su kamar dai ni din va namiji bane. Bari kawai in bude inga miye.  Hannun na karkarwa sai ya kusa kama bargon kawai sai yaja baya a tsorace. Kusan sau biyar yana yin haka. A na shida ne ya daure ya kama bargon yaja da karfi. Ahhhhhhhhhhhhhh! Ya sakk ihu!.~


_*I*tama ihun ta kwada. Yana ganin Fatima ce sai ya bata rai hade da watsa mata harara. "Ke uban me kike a nan dakin?. Wa yace ki shigo min daki?". Shiru tayi tana kallan shi ba tare da ta bashi amsa ba. Dube-dube ya shiga yi yana neman abun da zai dake ta. Ganin ba bulala ko wani mabugi a wajen ne yasa shi tsawa yana mata mugun kallo. "Oya tashi ki bar dakin nan ko inyi kasa-kasa dake a nan wajen".  "Bazan tafi ba din yau a nan xan wuni".  "Ke ni kike gaya wa wannan maganar?".  Ya nufo wajen ta ya daga hannu zai mare ta yaji hannun ya tsaya cik! a lankwashe. Hahahaha ta kwashe da dariya. Abba kuwa fama yake ya mike hannun shi amma ina abun ya gagara.  Ga Fatima sai Dariya take mai.  Abun ya kara fusata shi nan take ya kara daga dayan hannu da nufin ya wanka mata mari.  nan ma hannun ya tsaya cik! Duk hannuwan nashi biyu suka makale suka tsaya a lank'washe.  Fatima da ganin hakan ta tashi ta fita daga dakin a guje tana Dariya. Su mama Asiya lokacin sun gama cin abinci yara kuma duk sun tafi makaranta. Sai su uku zaune a falo suna tadi._






_Fatima suka gani ta zo ta wuce a guje tana dariya. Zuwaira da Hauwa har yun kura zasu tsere suma a tsorace sukaji Abba a daki sai kwalla kira yake. "Mama! Mama!". Da sauri suka nufi  dakin nashi a hanya sukayi kicibus. Hannuwan shi biyun duk a lankwashe. Ya rasa yanda zaiyi har ya fara zubar hawaye. Su duk  ukun tambayar shi suke me ya faru. Cikin kuka ya  fada musu duk abunda ya faru. Da jin haka mama Asiya tana jin haka tac "Kaico!  Wai kai Abba me yasa baka gane wa ne.  Yarinyar nan tunda kaga ina raga mata ai ya kamata kasan cewa akwai lauje cikin nadi. Aljanu ne suka shiga jikin Fatima. sau tari ina nuna maka ba ruwanka da ita amma kaki yanzu gashi ka jawo mana bala'i. Dama yanzu nake so in zo in gaya maka cewa ka fita harkar ta kar ta sabauta min kai. Ban sani ba ashe har ta faru ta kare". Ta kalli su Zuwaira tukun taci gaba da magana. "Dan Allah yanzu miye abun yi?. Kunga ta mayar min da da Masaki"._





_Jugum! Su Zuwaira sukayi suna nazari can Zuwaira tace, "Wannan abun ba wani abu ne ya jawo shi ba sai rashin sani wanda kuwa kowa yasan cewa *YAFI DARE DUHU*. To amma yanzu abun da ya dace shine muje mu roki Fatima ta taimaka ta mikar mishi da hannun shi. Tunda durkusa wa wada ba gajiya wa bane in dai za'a sama biyan bukata". Gaba daya suka aminta da shawarar Zuwaira. Kofar dakin su Fatima suka nufo tun daga nesa suka jin sautin dariyar ta. Mama Asiya tace "A gaskiya gidan nan ba lafiya. Aljanun jikin fatima rikakkun gardawa ne. In bamuyi a hankali ba duk sai sun babala mu. Kuma ya kama ta mu sanar da alhaji ya tafi wannan shegen aikin nashi ga gida yana so ya fi karfin mu".  Hauwa tace, "Gaskiya ne amma ai naji yace ya ran Friday zai dawo". Zuwaira tura kofar tayi taji a rufe gam! kwankwasa kofar ta shiga yi tana fadar "Fatima! Fatima!. Dan Allah ki bude mana. Ba dan halin mu ba dan Allah".  Shiru fatima taki bude wa. Sun dade a wajen kowa na tofa albarkacin bakin sa na magiya. Abba ma cikin kuka yake rokon ta ta bude ta mikar mai da hannun shi. Domin yaga wanki hulana neman kai shi dare.  Fatima ta bude kofar cikin uniform dinta na islamiya rai a bace tace,_






_"Ku gafa in wuce ko in hangiza ku gaba daya kuma ko mutum ya karyw ba abun da yasha ruwana".  Ta make kafada alamun ko Oho. Mama Asiya da Abba lokaci daya suka zube kan gwiwoyin su suna magiya. Fatima ta kwashe da yar banzan Dariya. Wai yau su Mama Asiya ce da durkusawa gaban Fati ana  bada hakuri. Sai da Fatima tayi dariya mai isar ta cikin isa da iko ta kalli asiya tace, "In kina so in mikar mai da hannu sai kinyi tsallan kwado".  Tsuru!  Suka zazaro ido gaba dayan su. Hauwa da Zuwaira kamar su kwashe da dariya.  Zuwaira da san gulma ta wa Hauwa rada a kunne. "Yau zamu ga tsallan kwado a gun Asiya. Tubur-tuburtu kenan".  Wata muguwar dariya ce ta zo wa hauwa. Da kyar ta iya samu ta matse bakinta.  Asiya tayi misisi da ido ta marairaice, "Haba Fatima kiyi hakuri mana ni yanzu ina zan iya tsallan kwado?".  Fatima tayi hanyar wajen "Bakya so hannun danki ya mike ashe?"._





_Da sauri Asiya ta mike ta shiga gaban Fatima, "Yi hakuri dan Allah karki tafi ki bar Abba na a cikin wannan yanayin".  "To maza ina jiranki fara". Mama Asiya ta tsuguna. Juyawa tayi ta kalli Su Zuwaira dariya suke mata sosai amma ciki-ciki ba yanda Fatima zata ji ba. tsalle mama Asiya taso tayi amma ko rabuwa da kasa kafafunbatayi ba saboda nauyi da jikin ta yayi. Hahhahhahah Fatima ta kwashe da dariya, "Malama kiyi sauri kiyi ina jira kinga dai na makara makaranta". "To....To. Bari in kokarta".  Tsalle mama Asiya tayi niyar yi a karo ma biyu. Akayi rashin sa'a kuwa kafarta bata zo a dai-dai ba. Sai ji kake rigijif! Ta fadi._






_Fatima ta tuntsite da dariya. Haka ma su Zuwaira. Sai da Fatima tayi dariya har tana rike ciki. Tace, Kin fadi jarabawa amma tun da dai kin sani dariya Abba mike hannun ka na dama". Tana fadar haka ta juya ta wuce, Kamar wasa Abba ya mike hannun shi na dama yaka ya mike lafiya lau kamar bai taba lankwashe wa ba. Yayi murna sosai sai dai kuma hannun hagun har yanzu  a lankwashe yake.  Tun daga tsakar gida Fatima ke kwalawa Mai gadi kira yazo ya bude mata.  Da sauri ya fito yana ganin Fatimar ce yayi tsaki. "Wai ke wannan yarinyar yaushe kika koma haka ne?.  Ina tarbiyar ki take. Wato naga kwana biyun nan tashen rashin kunya kikeyi".  Gatsine da harara kawai take binshi da shi.  Haushi abun ya bashi ya nufo ta zai daga. "Wallahi kana dukana kayi ta aikin ka. Sanin kanka ne Alhaji baya san abunda zai taba ni kuma ran Friday zai dawo".  Yanq ji ta fadi haka sai jikin shi yayi sanyi.  Tsaki yaja yaje ya bude mata kofar._





_"Zo ki wuce jarababa kawai. Ke ma dai su Asmart sun koya miki wannan masifar ashe".  Bata tanka mishi ba dungwai-dungwai ta wuce har makaranta.  Makaranta ta cika makil! Sai karatu ake Fatima ba tare da wani fargaba ba ta shiga ajinsu. Malamin su na ganin ta ya fara binta da harara. Ita kuwa ko a kwalarta. Domin yunkurin wucewa ta zauna ma take yi. Malam yace, "Ke gidan ku, Ina zaki ko baki san kin makara bane?".  "Ayi hakuri malam, na tsaya yin wani abu ne".  "Kaniyar ki. Zo nan". ba gardaa taje. Tana zuwa kuwa ya fara zafga mata bulala. Sai da yayi mata uku. Yace "Oya maza wuce ki nema waje ki zauna".  Tsaye tayi ta kafe shi da ido tana hararen shi. Tsawa ya kara daka mata amma taki tafiya.  Hakan yasa ya kara juyowa yaci gaba da dukan ta abun yayi matukar tsorata malam yanda yasan Fatima da shegen kuka bulala daya ko biyu yake mata ta fashe da kuka yau kuwa gata sai duka yake amma ta kafe shi da ido tana harara ko kwalla babu. Sai da ya gaji da dukan dan kanshi ya barta yaje yaci gaba da darasi yace, "In kinga dama ki kwana a nan tunda bazaki je ki zauna ba.  Da fadar haka Fatima ta wuce ta zauna. Abun ya daure wa Malam kai a zuciya yake saka "Anya kuwa wannan Fatima ce?"._





_Basarwa yayi yaci gaba da darasi. "Yara yau zamu ga mai tsantsar hazaka daga cikin ku. Idan baku manta ba kwanaki munyi bayanin taimama a cikin littafin ahdari. Sanan kuma mun kwana biyu munayi wanda sai da na tabbatar kun hardace tukun na daina biya muku. Dan haka yanzu ina bukatar Dalibin da zai tashi ya mai-maita mana. Kuma zan bawa duk wanda ya karanta min dai-dai kyauta. Yara biyu ne suka tashi daya mace daya namiji sai duk sai sun fara sai su kakare. Fatima ce ta mike. "Ni zan karanta kuma bana bukatar kyautar". Malam kallo kawai ya bita da shi. Nan take ta fara_





_*"Tafiyar da bata sabon Allah ba. Da marar lafiya, (Wanda yaji ciwo ko kuma dai yaa jin matsanan cin sanyi, Yana iya Taimama). Sallar farillah ko ta nafila. Mazaunin gida lafiyayye. yana iya Taimama dan Gudun fital lokacin sallah. FARILLAN TAIMAMA: Niya da bigiri (waje) mai tsarki. Shafar fuska, da shafar hannuwa zuwa dantse. Da bugun kasa na farko da gagautawa. Shigar lokaci da sadar da ita zuwa sallah.  BIGIRE: (WAJE) Wajen da ya hallata ayi taimama a shi. Turbaya tubali. Da dutse da kankara da waje mai danshi da makamantan su. Taimama bata halatta da suminti ko abun dafawa. Ko kan tabarma. Da itace da ciyayyi.*_





  _*Anyi rangwami ga marar lafiya ya shafi bango in dai bai sama wanda zai samo mishi kasa ba. SUNNONIN TA: Sabun ta bugun bigiri wajen shafar hannuwansa da shafar abunda ke tsakani  Ku'i biyu da dantsen sa. Da jerantawa. MUSATAHBBANTA: Yin bisimillah,  Gabatar da Zhirin Zura'i (Tsuntsuyar hannu). A bisa badinin sa. Farkon sa a bisa majinkircinsa. MASU WARWARE TAIMAMA: Masu warware ta daya suke da masu warware alwala. Ba'a yin sallar nafila biyu da taimam daya. Wanda yayi taimama domin yin Sallar farillah ya halatta a gare shin yin farillah bayan ya gama. Ya halatta ka taba Alqurani dawafi, da Tilawa. Da sadar da ita kafin fitar lokaci. Ya halatta ayi duk abunda aka ambata da taimama. Wanda yayi taimama yayi sallar isha'i yayi sha'i da wuturi, ba tare da ya jinkirta ba. Wanda yayi taimama yana da janaba. Babu makawa sai yayi niyar ta".*_





 _Tana kaiwa nan ta koma ta zauna abunta. Malam kuwa tun da ta fara kallan ta kawai yake yana kada kai da alamun mamaki. Bai san lokacin da bakin sa ya furta. "Attakabir" Ba. Yara suka kwasa. ",Allahu akbar". Har aka tashi daga islamiyya malam na mamakin Fatima yau gaba daya ta canza.  Fatima tunda aka tashi daga makaranta ta tafi gidan Rafy. Rafy kuwa dake tasan halin Safuratu sai tayi tunanin ko itace tayo sufar fatin. Nan sukata hira Fatima na taya ta wasu aikin gida.  Bayan la'asar Fatima ta koma gida. Yau ma kamar yanda ta sabawa mai gadi haka tata buga get din da karfi. Wannan karan yana budewa ta bangaje shi ya fadi can gefe ta wuc fuuuu! Abunta. Asmart Nasmat Ameerah da Fiddausi dake gefe tana karanta novel a Facebook. Sune a falon. Suna kallon Mtv. Fatima na shigowa ta nemo remote ta rasa. Kawai sai zare Socket din tayi. Asmart na ganin haka tayo kanta da masifa........................................._



DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 103-104



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com


👏🏻 *MASOYA AYI HAKURI DANI. WALLAHI KWANA BIYU INA BUSY NE BANA SAMUN TIME DIN TYPE* 😒😏 *MASU CEWA JAN AJI NE. DUK SAI NA HADAKU DA ALJANU* 🤧


       *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Asmart Nasmat Ameerah da Fiddausi dake gefe tana karanta novel a Facebook. Sune a falon. Suna kallon Mtv. Fatima na shigowa ta nemo remote ta rasa. Kawai sai zare Socket din tayi. Asmart na ganin haka tayo kanta da masifa.~

_"Ke Fatima bana san iskanci da tambada mayar mana da socket ko in lakada ki yanzun nan Wallahi". "Baza'a mayar ba".  Asmart da taga Fatimar bata da alamun mayar da socket din dai ta nufo ta a fusace, Kafin ta karasa wajen ta. "Kai! kai! kai!._




_Rufa mana asiri in ba sokikr mu shiga uku ba yanzu". Hauwa ce ta fadi haka lokacin da ta fito daga kitchen. Asmart dakata wa tayi tana kallan Hauwa'u. Fatima tace, "Duk wanda ya kunna tv din nan yau ni da shi ne a cikin gidan nan". Da fadar haka ta juya ta wuce daki. Asmart tace,  "Me ke faru Aunty Hauwa?".  Hauwa tace. "Wato ku duk baku san me ke faruwa a gidan nan ba kenan?.  Ai tun jiya Aljanu sun shiga jikin Fatima su suke sakata duk wani iskanci da take. Kuma gasu da shegen karfi. Kai dazun ma Abba da yaje dukan ta Wallahi hannun shi tsayawa yayi a lankwashe, Da kyar muka samu ta mikar mai da hannun daya, Dayan kuma taki mikar mishi wai sai Aunty Asiya tayi tsallan kwadi". Hhhhhhhhhh Nasmat tayi dariya, "Lalai Aunty Hauwa kin iya tatsuniya.  Wai yanzu kina nufin daga naje dukan Fatima kawai dai hannuna ya makale".  Hauwa tace, "Kwarai in kuwa baki yarda ba gaki gata. Inda ba kasa nan ake gardamar kokowa".  Asmart tace, "Kai nima dai ban yarda da wannan jawabin ba. Haba dai yo ai ni ko a Tv ban taba gani ba. Kuma wallahi yanzu zan kuna TV din tayi abunda zatayi". Hauwa tace, "To marar kunya wato duk da ina auren baban ku matsayina bai haura karyatawa kai tsaye ba.  To shikenan ni na barku lafiya. Ba dani ba raban fadan Zakuna. Wanda baiji bari ba yaji hoho, Ni kunga tafiya ta".  Hauwa na fadar haka ta haura sama abunda. Asmart tsaye tayi abun nayi mata yawo a kwakwalwa.  Tunani take ta Mayar da socket din ko ta fasa. Nasmat ganin asmart ta kasa kunna tv yasa ta tashi ta nufi wajen "Dallah matsoraciya matsa ni in jona in ke tsoro kike. Abunda dama wannan 'yar tsanar ce Aljanar kuma an toyata"._






_Asmart na jin haka tace "Kuma fa haka ne". Nan suka fara rige-rigen mayar da socket din. Fiddausi na jinsu duk abunda suke ko uffan bata ce musu ba. Ta dukufa wajen karatun novel da take a waya. Ameera kuwa game take a waya sai ihu! Take kamar zautacciya. Nasmat da Asmart daga wannan taje saka  socket din sai dayar ta ture ta. Wai kowa na fadin shi zai mayar. Da suka dade suna haka sai kuma suka tsaya suka sasanta a kan a kama a saka a tare.  Da mayar da socket din da dauke war wutar dakin duk daya. Juye-juye suka shigayi. Fiddausi da ameera su kansu sai da suka dakata da abun da suke.  Gam! Gam! Gam! Windows din falon ne suke rufe kansu da karfi. Duk da rana ce a lokacin amma sai falon ya zama duhu rudum, kamar tsakar daren da ba farin wata. "Nasmat!, Fiddausi!, Ameera!. Kuna ina?"._






_Suma din gabaki daya a rikice suke sai kiraye-kirayen juna suke. Domin duhun yayi yawa ko tafin hannun ka baka iya gani. Fiddausi ji tayi kawai anyi sama da ita ana ja kamar wacce iska ke tafe da ita. Ihu! Take tun karfen ta hakan yasa su Nasmat suka kara rikicewa suma. Kofar falo ta bude Fiddausi sai ji tayi an watso ta waje.  Mai gadi ne yayo kanta yana tambaya "Lafiya-lafiya me ke faruwa".  "Aljanu ne". ta fada tana nuna mishi falo yayin da take kokarin tashi. Tana tashi ta zangara  a guje. Mai gadi ma da gudu ya koma daki ya garkame kanshi. Su Asmart da sukaji ihun! Fiddausi ya lafa sai suka shiga kiranta. A hankali Asmart ke fadar "Aunty Fiddausi! Aunty Fiddausi!". Shiru bata ji an amsa ba. A tafiyar da take tana lalube irin na makafi sai taji hannuwanta sunci karo da mutum. Nan take ta fara lalubata tana kiran sunayen su. "Nasmat ce?, Ko aunty Ameerah ce?.  Fiddausi ce?. Yi magana mana".  Shiru bata ji yarinyar tayi magana ba.  "Wai Fatima ce?". Ta kuma tambaya tana shafa fuskar.  Tana zuwa saitin bakin sai ji tayi an gallara mata cizo.  Ahhhhhhhhh!.  Ta saki ihu! Abunda ya kara dugunzuma su Nasmat kenan suma suka rikice. Gudu suka ringa yi ba tare da sun san ina suka nufa ba. Bango birki. Nasmat na tafe a cikin duhu taji tayi karo da mutum. Tunani  ta Asmart ce. Cewa tayi "Asmart wai duhun miye wannan?".  Shiru  bataji tayi magana ba._






_Lalube ta kamayi kuma sai taji ai yarinya ce taci karo da ita din. "Fatima! Fatima!". Wata irin walkiya suka gani kamar an kawo nepa an dauke. Nan take suka kara dimaucewa.  Hahahahhaha gaba dayan dakin ya kwashi dariya, Zuwa can kuma sai wani ja  haske ya cika dakin  gaba daya. Nan take suka ga junan su bayan sun hadu waje daya ne suka kuma jin wata irin dariya kamar ta yara a bayansu. Ahhhhh!  Suka fasa ihu a tare. Ba komai bane suka gani sai kan Fatima na tafe q kan iska wuyan wani irin jini ne mai kauri ga danko yake zuba kasa. A bakin ta kuwa wani danyan nama ne take ci duk jini na zuba. Ga kuma gashin kanta da ya koma wasu murda-murda ba kyan gani sai motsin yake da kanshi kamar macizai. al'amarin duk wanda yaga abun dole ya tsere in ba'aci sa'q bama mutum sai ya suma. Wannan kan na Fatima mai shegen abun tsoro n ya nufi su Asmart su kuwa kamar wanda aka rike wa kafafu sun kasa guduwa. Suna nan tsaye sai tsala ihu! Suke. Kan na zuwq saitin Ya wangare baki ya wani kara fadi. Kamar zai hade su baki daya. Luuuw! Suka ringa zubewa sumammu.  Kafin kiftawar ido falo ya dawo yanda yake. Su Mama Asiya duk ihun da ake baya zuwa wajen su hakan ne ma yasa basuji ba. Zuwaira ce ta sakko daukan wani abu. Tana ganin su Nasmat a shimfide ta rude nan-da-nan ta fara kwallawa su Mama asiya kira. Suma da gudu suka sakko downstairs din suna tambayar me akayi.Zuwaira ta nuna musu Asmart da yatsa. Ai da sauri hauwa ta dakko ruwa mai sanyi aka fara yayafa musu._






_Duk wacce ta farfado sai ta kankame ta kusa da ita a firgice suna sambatu da ambatan sunan Fatima. Mama Asiya da duk ta rude take tamabay me akayi. Hauwa tace, "Ni dai dazun na barsu nan lokacin Asmart zata daki Fatima shine na dakatar da ita na fada musu cewa Fatima nada aljanu. Shine har suke karyata ni. Sannan kuma Fatima ta zare socket tace duk wanda ya mayar zatayi maganin sa". Hauwa ta kalle gurin socket din taga an mayar, "Af!  Socket din suka mayar ai yanzu gashi sun jawa kansu". Mama Asiya cikin masifa ta fara magana. "To Wallahi bazai yuyu ba. Dole a dauki mataki Wallahi ko in bar gidan nan yau. Haba ya zan tsaya ina kallo aljanun Fatima su kashe min yara. Bari in kira alhajin shima da yaje yayi zaman shi a kasar mutane kamar can aka yanke mai cibi". Da sauri ta koma daki ta daukko wayar ta kira Alhaji. Ko gaisawa basuyi ba ta fara binshi da masifa take gaya mishi duk abunda ke faru. Alhaji kuwa wufantar da zancen yayi. Yake cewa. "Wato Asiya kuma ta nan zaki bullo wa Yarinyar nan ashe har yanxu wannan zaluncin da kike wa Fatima baki daina ba. In banda karya da sharri ya zaki ce wai Fatima ta addabi gida kaza-da-kaza?".  Mama Asiya cikin masifa ta kara kai'mi. "Au! Abun da zaka ce kenan. To Wallahi in haka ne zan tatara yarana in tafi da su gidan mu. Haba ina dalili yaseen bazan yarda Aljanu su kashe min yara ba. Yanzu haka ga su Asmart nan rai hannu Allah Aljanu sun dadake su duk sun ji musu ciwo".  Daga can alhaji yayi magana da alamun shima ya fusata. "To naji zaki iya tafiyar ki amma karki sake ki fitar min da yaro ko daya. Ke in ban isa inyi iko dake ba ai na isa inyi da yara na. Kuma in sha Allah wannan juma'ar zan dawo sauran inga kuma ba dai-dai ba. Ko inji Fatima tace min zalumtar ta kuke. Wallahi da sai na dau kwakwaran mataki wanda bazai miki dadi ba".  Yana fadar haka ya kashe wayar._






_Tsaki mama Asiya taja, "Wato kai kana can ka bar mu da Aljana na neman sabautamu". Haka dai gidan ya wuni cikin dar-dar, Fatima kam ta zama abar tsoro dan in tazo waje gaba daya sai suyi tsit. Da dare da kyar suka yarda da su kwanta a dakinsu. Wajen karfe 11 na dare Fatima ta tashi ta tafi sama mama Asiya na barci taji ana tashin ta. Tana farkawa kuwa taga Fatima. "Fatima me akayi kike tayar dani tsakar daren nan?".  Mama Asiya take maganar cike da tsoro.  "Murya na fitowa biyu-biyu Fatima tace, "A nan zan kwana dan haka ki tashi ki koma falo ki kwanta".  Mama Asiya na karkarwa ta tashi ta yayimi bargo ta fita a dakin.  Tun kafin ta sakko daga kan matakalar ta hangi mutum a zaune a falo mace ce kin bakaken kaya. Ta juya mata baya........................................._



🏃🏻🏃🏻🏃🏻🏃🏻🏃🏻 A dakace ni yaseen na gaji🙊





DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 105-106



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com


 *DEDICATED TO YOU* 😁


QUEEN HAUCY 


MINEERT 


AMÆL


SALMAH


MINEERT


QUEEN MEIMIE


PHATEEMA


MARYAMU 🙊


MUHIEVER INDIA



❤  KUNA A RAINA KU DIN NA DABAN NE A HEAR DIN KIN. 💃🏻 INA SANKU MASOYANA. ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MUKU A  DUK INDA KUKE. 



        *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Mama Asiya na karkarwa ta tashi ta yayimi bargo ta fita a dakin.  Tun kafin ta sakko daga kan matakalar ta hangi mutum a zaune a falo mace ce kin bakaken kaya. Ta juya mata baya.~



_Cikin muryar tsoro mama Asiya ke magana. "Wacece?. Waye a nan?". Shiru bata amsa ba. Kara matsawa tayi tsoran ta na dada karuwa. Sai tambya take amma anyi mata shiru. Nan ta tsaya tana sake-saken ta juya ko kuwa ta karasa. Zuciyar ta ce ta bata shawarar cewa taje ta gane wa idan ta waye a zaune. Gwara nan da can din wajen Fatima.  Cikin Kwarin gwiwa ta nufi wajen matar ta dan kauda tsoran ranta. "Waye-waye". Ta kara tambaya firgigit matar ta juyo Hauwa ce, da alamu gyan-gyadi take. Mama Asiya na ganin Hauwa ce tace, "Hauwa wannan wane irin kaniya ce. Kina ji ina miki magana kika share ni, Wallahi har kin bani tsoro". Hauwq na murza ido tace, "Ni wallahi cikin barci ne ma naji kiran ki".  Mama asiya tac, "To ke kuma wace uwar ta dawo dake falo ga dakin ki can kin baro?". Hauwa ta waiga baya alamun marar gaskiya. Murya kasa-kasa tace "Wallahi Fatima ce ta bini daki ta koro ni wai in dawo falo ita zata kwanta a dakin". Zagayawa mama Asiya tayi ta zauna._





_Cikin rada mama Asiya tace, "Taf! Di jam, Kika ce Fatima ce ta koro ki".  "Eh Wallahi ita ce, Yanzu haka tana can saman gado na tayi kwanciyar ta".  "To Fatima aljanun nata ko har sun fara raba ta gida biyu ne?. Domin yanzu ta koro ni fa daga daki na wai...". Sautin saukkowar da suka ji daga stairs ne ysa mama Asiya bata karashe maganar da ta fara ba. Suka juya su biyun suka zura wa wajen ido dan ganin wanda zai sakko. Ba kowa bane Zuwaira ce itama rike da bargon ta a hannu kamar almajirin da ya fito rani. Mamaki ne ya kama ta ganin su Asiya a falo. "Aunty Asiya, Me kuma kuke yi a falo". Zuwaira ke tambay. Asiya tace, "Ai ke ya kamata mu tambayi me ya fito dake daga dakin ki da tsakar daran nan harda kwaso blanket".  Zuwaira ta juya baya tukun tayi kasa da murya tace, "Aljanun Fatima ne suka koro ni. Wai fa dan daukar alhaki ina kwance abuna sai ji nayi ana tayar dani, Bayan na bude ido naga Fatima ce, Kar kuso kuji cikin irin muryar da take magana. Da shi abar tsoro shine ta koro ni falo".  Su mama asiya suka ce ai sai kizo ki hau layi domin muma nan da kike gani ita ta koro mu".  Zuwaira tace, "A gaskiya ya kamata mu dauki mataki haba Aljanu ma ai suna da maganin".  Asiya tace, "Rage murya kar su jiki, Dan Wallahi yanzu zakiji ana gaura miki mari". Da sauri Zuwaira ta matse bakin ta da hannaye.  Bayan sun baje a falo.  mama asiya tace, "Nasan matakin da zan dauka. Ku bari gobe zan gaya muku"._







_Washe gari tun da asuba kafin su mama Asiya su tashi daga barci, Fatima taje ta debo ruwa a waje mai shegen sanyi. Nan tazo ta fara kwara musu. Gaba daya a gigice suka ringa tashi. Suna tashi suka ganta zaune kan 3Stars tana musu dariyar mugunta. Daga bisani ta bata rai tace, "Maza ku tashi aje ayi sallah sannan a zo a shiga kitchen".  Suna rawar dari suka tashi ko wacce ta nufi dakin ta dan yin sallah.  Fatima ta tashi ta shiga dakin su, Nasmat, Ameera da sauran yaran sai barci suke abun su. Fiddausi ce kadai ta tarar kan sallaya tana karatu.  Da sauri Fatima ta koma ta kara debo ruwa ta zo ta dingi watsa musu tana tashin su suje suyi sallah. Ameera watsa mata ruwan da akayi, abun yayi matukar bata mata rai. A fusace ta nufi Fatima, Batayi wata-wata ba ta kwasa mata mari. Sannan ta dora da fada, Yayin da ita kuma Fatima ta sadda kai kasa. "Ke Fatima bar ganin ana cewa wani kina da Aljanu. Wallahi ni ba raga miki zan ba. Aljanun banza, Shikenan dan kina da Aljanu sai kita takura wa mutane. Miye zaki wani watsa wa mutane ruwan sanyi da safiyar nan. Anki ayi sallahr".  Firgigita Fatima ta dago kai. Dagowar da tayi idanun ta sun koma kamar garwashi har wani tartsatsin wuta ke fita a idan.  Gabaki daya mutanan dakin sai da suka tsorata. Su Asmart kam kankame juna sukayi hade da runtse idanu. Fiddausi kanta da take karatu abun ya firgitata. Nan take ta fara karatun da karfi tana tofawa saitin  Fatima.  Fatima bata kula ba. Hannu ta mika saitin Ameera dake baya-baya a tsorace kamar tayi kuka. Ameera sai ji tayi an shake mata wuya. An dage ta sama ba tare da subga wanda ya daga tan ba. Sai da aka wul-wulata kafin aka mako ta kasa._






_Sa'arta daya kan katifa ta fado. Fatima cikin wata murya mai zaburar wa tace, "Maza kafin in kirga goma kowa yaje yayi alwala,.....1....2..".  Ai da gudu aka ringa rige-rigen shiga ban daki dan yo alwala. Bayan sun yo alwalar sun fito kuma sai sukaga fatiman bata nan. Daki-daki.Fatima tabi ta tattaro su mama Asiya aka shiga kitchen domin hada abun kari.  Tukun taje dakin Abba ta tayar da shi shima yayi sallah. Har ya fara mata magiya a kan ta mikar mai da dayan hannun shi, Ta daka mai tsawa hakan yasa ya kyale ta. Su mama Asiya sunji jiki sosai yau a Kitchen, Domin kamar yanda suke wa Fatima. "Dake wannan kul-kula wancan kwashe can gyara nan", A da. Haka itama Fatima yau ta ringa  juyasu, kamar ta sama bayin ta.  Haka wajen cin abinci ta ringa bada doka. Domin ko katuwar loka taga mutum yayi sai ta kwala mishi Cokali. Gaba dayan gidan kuwa tsoranta karuwa yake a gare su. Ana gama cin abinci Fatima tace to masu zuwa islamiyya a tashi ayi shiru, Ku kuma matan gida a gyara gida shara wanke-wanke da goge-goge. Tana fadar haka ta wuce daki. Yayin da suma masu zuwa islamiyyar tuni sun fece sun bar wajen. Mama Asiya ta rike baki alamun mamaki "Oh! Duniya kowa ya sama waje sai kiga ya baje kolin shi. Yanzu dai ga Fatima aljanu sun sata tana mana iskancin yanda taga dama kamar mu yaranta ne"._





_"Ke dai bari wannan abun takaici. Ya muka iya haka zamuyi hakuri mu jure har Alh. Ya dawo muga irin matakin da zai dauka". Cewar Zuwaira. Asiya ce ta katse mata hanzari ta hanyar cewa. "Kai aradu bazamu jira har sai ya dawo ba. Yau fa laraba kuma shi yace sai ya kai juma'a tukun zai zo, Dan haka yau zamuyi maganin abun ku dai bari wannan aljanar ta tafi makaranta  tukun".  Nan suka fara share-share suna kakauda kayan da suka ci abincin. Ba'a jima ba sai ga fiddausi da Fatima sun fito cikin uniform din islamiyya. Wani dan iskan kallo fatima ta jefa wa su mama Asiya kafin tace, "Ai na dauka da bazakuyi abun da na saka ku ba"._





 _Tana fadar haka bata ko jira sun tanka ba ta kama hannun Fiddausi suka fita. Ita dai Fiddausi duk a tsorace take da Fatima gudu take cutar da ita.  Bayan yara duk sun tafi makaranta su mama asiya suka shirya mama asiya tace musu malami zasu je su samo yayi masu Ruqiya ya fitar da aljanun.  Gaba daya suka amince da haka. Ga motar alhaji amma suka fita a kasa. Kasancewar a cikin su ba wacce ta iya mota. Suna tafe har sun kusan barin layin sukayi kicibus da wata mata da alamu yar anguwar su ce, Tafe take tana rausaya kamar wata budurawa, Ba hijab bane a jikin ta gyale ne ta dan yafa a kafada. Fuskar tasha hudar wacce zan iya ce muku har taso tayi yawa. Cingum ne a bakin ta tana tauna lips din yasha jan baki. Da gani kasan yar duniya ce. "Asiya Anguwa za'a fita, Da safiyar nan?".  Washe baki su Asiya sukayi "Eh wllh Nafisa daga ina haka".  Asiya ta fada.  Matar tace Wallahi naje sayo abu ne. Ina zaku je haka". Asiya ta kwashe duk  abunda ke faruwa ta fada mata.  Rike baki nafisar tayi hade da cewa "Aljana fa kika ce?. Tabb! To yanzu ina zaku sama malami".  Mama asiya tace "Aa gamu dai mun fito da wajen limamin masallacin jama'a zamuje watakil a dace".  Nafisa ta roke baki "ah!  Liman to bari kuji in  gaya  liman ba abunda zai muku. Sai dai yace kuje kuci gaba da addu'a. Amma akwai wani malami da na sani ya kware wajen fitar da aljanu, In kun amince na hutar daku ni zanje in kawo muku shi har gida"................................._




DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 107-108



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com


🏕🏕🏕🏕🏕🏕

🏕🏕🏕🏕🏕🏕


​SAI NA AURE TA​


🏕🏕🏕🏕🏕🏕

🏕🏕🏕🏕🏕🏕



   ωяιттєи ву: 

​shamsia salis​



​Eloquence Writers Association

____________________________________

Na tayaki murnar Autar Eloquence. Allah ya kara basira. Allah yasa mu amfana da darrusan cikin littafin amin

____________________________________

 

      *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Amma akwai wani malami da na sani ya kware wajen fitar da aljanu, In kun amince na hutar daku ni zanje in kawo muku shi har gida".~

_Su Zuwaira sukace "ba dai boka ne ba ko?". Nafisat tace "Aa ko daya wannan shahararren malami ne. In kun amince yanzu ma daga nan bazan karasa gida ba sai in juya in daukko muku shi".  Mama Asiya tace "To shikenan je sanar wa mai gidan ki to sai kizo ki karba kudin mota, ko kusa ne?".   "Aa Wallahi can wani kauye ne kudin motar mutum biyu Dubu daya ne. Dubu biyu zuwa da dawowo. Batun mai gida kuma da kike. Dallah rabu dashi miye na sai naje na gaya mishi".  Hauwa da Zuwaira tabe baki sukayi suna kallan Nafisa din.  Asiya bata ce komai ba ta fiddo dubu uku a handbag dinta ta bawa Nafisa "Gashi kije ki daukko shi muna jiranshi. Mu in dai zai cire mana wannan Aljanar to ko nawa ne zamu iya bashi". Ta juya ta kalle su Zuwaira "Ko ya kukace yan uwa".  Da sauri suka ce "Kwarai kuwa ko nawa ne zamu iya badawa mu dai gurin mu ta bar gidan".  Nafisa tace "Karku damu aikin wannan malamin sha yanzu magani yanzu ne".  Su Asiya suka juyo suka koma gida inda ita kuma Nafisa ta tsayar da napep ta hau tace a kai ta Sabon layi, Daga anguwar su nan naira saba'in ne.  Tana sauka ta nufi wata kofar gida wanda kofar gidan wasu samari ne ke zaune ba abunda suke sai busa sigari da gulmar masu wucewa kan hanya.  "Sannun ku dai dan Allah Aliyu ko ta bare yana gida". Gudan ya kalle ta yace "wani abu yayi mike ne?.  Ko dai yayi tsiyar ne". Nafisat tace "Ba abunda ya min ni dai kawai ina neman shi ne in yana nan".  Dayan yace mata "Yaje can sama wajen wata cuwa-cuwar sa amma yanzu zakigan shi ya dawo".  "To na gode". Nafisat tace ta koma gife tana jiran  Ko ta bare. (Sunan da ake kiran aliyu kenan). Bata jima a wajen ba ta hange shi ya taho, Duk da kasancewar shi dattijo hakan  bazai hana ka gane cewa dan duniya bane. Yana hango nafisat ya fara wasa ta yana mata kirari.

"Kaga shegiyar uwa mai saka 'ya'ya biyayyar dole, Kaga kaska rabi mai jini wanda ke da dan kadan ma abishi a tsotse. Ke ba maciji ba kinfi macijin dafi.  Da ganin nasan bakin ki a kwai batu. Dan banza bata kai zomo kasuwa._






_Kuma Wallahi da kaga kura ta ba nama ka tabbata ba dan Allah ta barshi ba. Yanzu dai miye labari ne".  Nafisa kam kallo kawai take binshi da shi tana murmushi domin ita da shi kar ta san kar ne. Daya baya neman daya sai za'a aikata wani mugun abun wanda za'a dan fizgi wani abu a ciki. Tana yar dariya tace "Shege Ko ta bare, Wato ka san dai in ka ganni gidan ka  ba banza ba". Yace "Eh mana ai nasan bazaki taba wanke kafafun ki takasan ki kawo min ziyara ba. Da gani nasan akwai wata harkar ne".  "Tabbas kuwa akwai babbar harkar.  Wacce in dai ka yarda zakayi nake gaya ma zamu sma kudi sosai".  Aliyun yace "Gaya min mana kinsan fa ni dan kasada ne bakiji suna na bama. Ai kawai ko miye na zanyi in dai za'a sama yan karafa".  Nafisat tace "Yauwa mutumina. To dama can wasu makwabtan mu ne suka neman za'a fitar musu da aljanu, kuma gidan masu kudi ne. Watakil ma ba wani Aljani kawai firgitane suke. Shine wai na hadi da su a hanya zasu je neman malami mai fidda Aljanu to kawqi ganin za'a sama wani abu shiyasa ma wannan shawarar ta zo mun".   Tsuru ya tsare ta da ido yana mata kallan yan iska. Lura da hakan yasa tace "Kai malam bana san wulakanci ya zaka wani zura mun na mujiya. Ko naci ban biya bane".

A fusace yace,"Ina fa kika biya, ai bansan dan banza kika dauke ni ba sai yau".  Cikin rashin fahimat da neman karin haske tace, "Ban gane na dauke ka dan iska ba?".  "Kwarai kin dauke ni dan iska tunda. Har wai ni zaki ce naje na cire Aljanu. Yo na cire Aljani ko kuma Aljani ya cire ni".  Kwashewa da dariya Nafisa tayi, Zuwa can kuma ta dan tsakaita hade da cewa,"Ko ta bare, wallahi ban taba sanin kai mugun matsoraci ne ba sai yau". "Aa ba tsoro bane, ai gaskiya ne. Duk iskancina ai bazanyi wa Aljani ba.kinsan ance aikin guguwa ta dau kara da karmami, bata shiga rumbu ta dauko dammunan hatsi".  Nafisat tace, "To kwantar da hankalin ka. Wannan kar ya dame ka, dan bana tunanin aljanun gaske ne. Ni ina tunanin ma kag'e ne sukeyi mata". Aliyu ko ta bare yace,"Au! Kina tunanin ba aljanun bane". Nafisa tace,"Kwarai ba Aljanu bane iskancin sune kawo irin na masu kudi".  Ko ta bare yace, "To in dai haka ne na amince". "Yauwa ko kai fa. To yanzu abunda za ayi shine, ka shiga gida ka sako fararen kaya sababbi, masu babbar riga da katan charbi sannan ka fito muga ko kayi kama da malami. Dan in bakayi kama da malami ba wallahi wani zan nema in sashi wannan aikin".  Gemun shi yaja hade da cewa,"Haba ai ni din nan da kike gani in  nasha manyan kaya bazaki iya banbanta mu da limamin anguwar ku ba. Yanzu bari in sako kayan sallah na". Ciki ya shiga ya sako shadda ce fara kal har dauka ido take, yasha malum-malum ga hula zannah.  Matsalar daya baya da charbi. Nafisat na ganin shi tace komai yayi. Nan yake gaya mata cewa bashi da charbi. Nafisat tace ba komai suje kasuwA._„





_Nan take suka nufi kasuwa ta sayo mai katan charbi hade da wasu turaruka. Ya fashe jikin sa sai kanshi yake kamar sabon ango. Sun taho a hanya Nafisa ke tsara mishi yanda zaiyi take fada mai sunce Yarinya ce karama mai aljanun dan haka abunda zaiyi shine yace a saka su daki daya su kwana idan yaga asuba ta kusa kawai sai ya shake yarinyar ta suma. In yaso da asuba sai yace ya gama fitar da aljanun a sallame shi sai ya gudu.  Fashewa yayi da dariya yace ya fahimta. Bayan sun kamalla duk shirin su suka nufi gidan. Nafisa ta fara shiga ta sanar musu gashi ta zo da malamin, Su mama Asiya suka ce ta shigo da shi ciki.  Makeken carbi ne a hannun shi yana ja bakin shi na motsi ka rantse da Allah kace tasbihi yake, Alhalin shi kanshi bai san abunda yake fada ba kawai motsa bakin ne.  Da shigowar shi falon ya kwashi kamshi. Su Asiya na ganin shi suka zube kasa cikin ladabi da girmamawa.  Nafisa a ladabce ta nuna mishi 1star tace ya zauna. Da bismillah ya zauna nan take su Mama Asiya suka fara kwasar gaisuwa. bayan ya gama gaisawa yayi hamdala tukun ya fara daga kai yana kare wa falon kallo sama da kasa yana jijiga kai alamun a kwai magana. Cikin ladabi Nafisat tace "Malam me ke faruwa?. ko aljanun ne".  Gyaran murya yayi tukun ya kalli mama Asiya yake cewa sunyi sakaci da har suka bari Aljanu suka cika musu gida haka. Cikin hanzari ya nuna wani bangare a falo, kunga ga fatalwa can ma ta fito daga dakin can zata gudu. Kunsan fa aljanu ko fatalwu basa yarda su hada wajen zama dani in dai ba masu shegen taurin kai ba. Su Mama Asiya kallan wajen da ya nuna sukayi wayam ba kowa, Zuwaira tace,"Allah shi gafarta malam fatalwar da ta gudu yanzu mace ce ko namiji?". "Mace ce gata can fara ce kuma siririya".  Sallalami suka fara gabaki dayan su. Nafisat ta tambaya me suke wa sallalami, mama Asiya tace, "Kin manta kishiyar mu uwar Fatima wacce ta mutu". Nafisat tace "Na tuna ta, ko kuna tunanin itac fatalwar?".  Zuwaira tace, "Kwarai ita muke zargi domin aljanun ma duk a kan yarta Fatima suka tare".  Aliyu yace, "Ba mamaki itace, Domin kuwa nayi mamakin ganin gadajen Aljanu ba adadi a tsakar gidan nan. Wannan ke tabbatar min da cewa Aljanu da yawa ne ke rayuwa a gidan nan". Asiya ta kalle shi hade da cewa, "To yanzu malam miye abun yi"._





_"Karku daga hankulan ku tunda dai gani nan na zo yau-yau sai na kore duk aljanun gidan nan. Dan haka yanzu ku kawo min yarinyar mai suna Fatima da kuke zargin ko yar fatalwar can ce". "Ai suna makaranta. Amma sun kusan dawowa". Inji  Hauwa da sai yanzu tayi magana.  Aliyu tace, "To ai shikenan bari mu jira ta ta dawo. Dan in san ta inda zan faro".  Mama asiya tace, "Yauwa Allah shi gafarta malam, Akwai wani dana mai suna Abba da Fatima ta lankwasar mishi da hannu. Munyi-munyi taki ta mikar mishi da hannun".  Aliyu yace,"Ina yake ku kawo shi inga". Hauwa ta tashi da sauri ta nufi dakin Abba ta kirawo shi. Yana zuwq ya zube gaban malam yayi gaisuwa. Bayan Aliyu ya amsa, yace Abba ya miko mai makalallen hannu. Ba gardama Abba ya mika mishi. Malam Aliyu ya ware karfin shi yasa hannaye biyu yaja hannun da niyar ya mikar da shi ta karfi. Ihu! Abba ya kwada hade da cewa. "Wayyo zai karya min hannu". Malam na jin haka yayi saurin sakin shi. Ana cikin haka sai ga Fatima da Fiddausi sun dawo daga islamiyya. Da shigowar su falon, Fatima ta fara hararen malam aliyu ko ta bare.......…………………………………………………………_



🤔 Lalai Malam Aliyu cire Aljanu da kyau 😂😂😂


DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


Page 109-110



©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com





          *KARSHEN PAGEN BAYA*

"Wayyo zai karya min hannu". Malam na jin haka yayi saurin sakin shi. Ana cikin haka sai ga Fatima da Fiddausi sun dawo daga islamiyya. Da shigowar su falon, Fatima ta fara hararen malam aliyu ko ta bare.~



_Tunda yaga tana zare mai ido ya gane cewa itace Fatima hakan yasa yayi saurin mikewa tsaye yana kallanta yana tofe-tofe.  Su  Zuwaira sukayi saurin mikewa suma. suna cewa, "Yauwa malam itace wannan din".  Malam yace ai ba sai kun gaya min ba. Domin tana shigowa naga Aljanu da ifiritai kusan million a tare da ita. Amma ni naga ma kokarin ku da har kuke iya kwana a gidan nan. Shin wai basa baku tsoro ne".  Zuwaira tayi sauri tace,"Ai ba tsoro kadai bama har da duka. Mu dai malam ka taimaka".   Aliyu yace,"Karku damu, Yau bazan bar Aljani ko daya ba a gidan nan.  Amma aikin ku fa nada wahala sosai gaskiya domin ma yau ta kama dole ma sai na kwana a gidan nan".  Gaba saya suka ce ba damuwa su dai gurin su a fitar da aljanu. Nafisat kallo kawai take bin Aliyu da shi.Yanda ya takarkare yana zuga karya wa su mama Asiya. Kamar wani malamin kwarai._





 _Fatima da Fiddausi basu wani tsaya sauraren su ba. Kai tsaye dakin su suka wuce. Malam na kiran Fatima! Fatima! Ko wai-wayen shi batayi ba. Balle ya sa ran zata juyo.  Zaunawa yayi yace da su mama asiya yana bukatar kayan aiki. Domin yanzu zai fara. Su mama Asiya suka tambaye shi dame-dame yake bukata. Nan yake gaya musu cewa Yanzu dai yana bukatar daki guda. Sannan a sayo soyayyun kaji amma a tabbatar da farare ne.yaci gaba sa ce musu a samo abinci kamar fillet biyar pure water leda daya. Domin ina so zan kafawa Aljanun gidan nan tarko ne dan akwai masu shegen gudu. Wanda zan kama ta dalilin abincin nan. Sai da ya gama lissafin shi su mama asiya suka tura mai gadi yaje ya hado duk abuda malam ya bukata. Dakin da aka ware mai yace a kai kayayyakin.  Sannan ya tashi ya shiga dakin hade da ce musu yana zuwa.  Wani mugun kallo Nafisa tabi shi da shi. Wato sai yanzu ta idasa gano tantirancin Ko ta bare. Asiya tace "Mu ko nawa ne zamu iya kashewa, in dai za'a fitar da Aljanun nan"._






_Nafisa tace,"Karku damu ai in dai wannan malamin ne bani da shakka a kanshi. Aikin shi kenan kama Aljanu". Su mama asiya sukace Allah yasa su fita domin kuwa yan taurin kai ne.  Aliyu na shiga dakin ya fara debar girki sanda yaci abinci sosai yaci ya koshi yaci nama san ranshi tukun ya sha ruwa ya goge bakin shi. Filet biyu ko wanne da kaza a kai ya fito da su yana tofe a ciki. Kamar mai addu'a da gaske. Yace wa su mama asiya su sa a daukko sauran abincin da naman a kai bayan dakunan amma a rufe. Yake cewa yasan aljanu da shegen kwadayi suna zuwa dauka zasu makale. Dan karfin addu'ar da yayi a ciki. Su mama asiya da kansu suka shiga suka dakko sauran abincin sunyi mamakin ganin anci abincin har hauwa ta kasa daure wa da ta tambaye shi. Sai yace Aljana ce taci lokacin da mai gadi ya kai su. Wai kafin ya karasa Aljanar taci  kuma ma wai ya kashe ta._






 _Haka dai suka raraba abin cin nan harda ruwan. Duk abunda suke mai gadi na kallan su ga muguwar yunwa da yake ji. Nafisa kuwa banda harara ba abunda take aikawa Aliyu.  Waje ya samu ya zauna a falo aka kunna fanka aka kawo gaban shi aka kuma kawo abinci da lemu. Malam yace ai shi ya koshi domin Aljanu ke kawo mishi abinci duk lokacin da ya bukata.  Baici ba sai Nafisa aka bawa ta cinye. Yana nan gidan  har dare yayi ita kuwa Nafisa sallama tayi musu a kan cewa gobe zata dawo.Aliyu Da yaga ish'i tayi sai ya faki idanun mutane ya zagaya bayan daki wajen abincin nan yana zuwa yaga duk an cicinye naman nan haka abincin ma duk an babata gun. Daga can yaga wani flat din wanda ba'a taba ba. Sai da yaci ya koshi tukun ya goge bakin shi yaje yace wa su mama asiya suzo su gani. Suna zuwa sukaga duk anci abincin nan an rage wani wajen an fara cin cinya an yar. Ruwan ma duk an fafasa anyi wasa da shi. Tambayar shi sukayi a kan waya ci abincin.  Nan ya karkace hula ya fara zabga musu karya wai ai Aljanu ne sukaci addu'ar da yayi ne ya manta baiyi bismillah ba shiyasa wai Aljanun da suma zo ci basu makale ba. Su Asmart najin haka suka kyal-kyale da Dariya. Su mama Asiya suka tambaya me suke wa Dariya. Basu bada amsa ba suka ci gaba da dariyar hakan yasa Zuwaira taji haushi ta kora su da gudu suka koma falo suna daria. Nasmat taks cewa Asmart ita gaskiya bata yarda da mutumin nan ba.wai tana zargin ko ba malamin gaske bane. Asmart kam cewa tayi, "Au ke ashe zargi ma kike?. Kina gani fa gashi kiri-kiri ya maka karya. Wai yace Aljanu sukaci abincin bayan kuma mu muka ci".  Nasmat ta kyalkyale da Dariya Dariya tace,"Watakil mune aljanun".  Asamrt tace,"Yanzu mu rufa mishi asiri ne ko kuwa?". "Kyale shi muga iya gudun ruwanshi tukun. Ba dai yace zai cire Aljanun Fatima ba yau". Dariya Asmart tayi hade da cewa."Ai kuwa dai mu rufa mai asiri zuwa goben mu gani"._






_Acan kuwa su amam asiya suka cewa malam ya yake ganin za'ayi. Ce musu yayi shi yasan yanda zaiyi wai in ya kama aljanun Fatima zasu kawo mai sauran. Falo suka dawo aka kawo mishi abinci nan ma yace ya koshi wai Aljana ta kawo mishi yaci.  Fatima yasa aka kawo mai gaban shi nan yata tofe ta da miyau kallan shi kawai take yi tana hararen shi ba tare da tayi magana ba. Da abun ya bashi haushi sai ya fara kashe ta da mari yan cewa tayi magana. Su mama asiya suke cewa mai yasa yake dukan ta. Sai yace musu ba ita yake duka ba Aljanun ne wai dama yasan sai sun mishi garda.  Nan yata jifgar Fatima amma taki cewa ko uffan!. Wajejan karfe goma na dare Aliyu yace a kai Fatima daki domin a can zaiyi aikin kuma yace a daren duk tauri  kan aljanun sai ya cire su.  Daki aka kai ta ya shiga ya kulle bayan yace wa kowa ya shiga daki ya rufe. Bayan Ya musu gargadin kar wanda ya fito ko da fitsari ne.  Gado ya dale abu  shi ya kalle Fatima dake tsaye tana zare mai  idanu yake ce mata in kinga dama ki  zauna ko ki kwana a tsaye ma ni ba ruwa na.  Barci yake abun shi har da munshari.  Can cikin barci yayi mafarkin wasu mugayen halitu masu ban tsoro gasu da girma sukata tsorata shi suna firgiya shi daga karshe suka kai shi wajen wata yarinya da ba kai a jikinta sai iya gangar jikin. Hannun ta rike da wuka._






_Ko da yaga haka sai tsoro ya kara kama shi. Wannan halittun suka kai shi gaban ta bata jira komai ba ta daga takobin ta jaka mai a ciki. Da cakawa ya farka firgigita.  Ya tashi da ihu mai makon yayi addu'a.  Fatima ya gani tsaye yanda ya barta lokacin da ya kwanta har yanzu haka take bata ko motsa ba. Kasancewar dakin da hasken dake akwai nepa. Ya kalli agogon dake makale a bangon dakin yaga karfe biyu.  Ya juya gax. Fatima da niyar yi mata magana. Wayam yaga wajen ba kowa. Dube-dube ya kamayi. Ya sakko kasa  yan kiran sunanta dake yaji an fada mai. Ya duduba duk inda yake tunani  bai ganta ba. Sai karkashin gado. Yana lekawa da nufin yaga ko ta na nan yaji an rike mishi kai. Ihu! Ya farayi yana neman agaji. Jan kan nashi ake shima yana iya kokarin shi yana neman ya kwace amma ya gaza. Sai da yasha wuya sosai tukun aka sake shi.  Da sauri ya yashi ya koma kan gado ya lulube da bargo yana lumfashi day-day.  Dif!  Yaga wutar dakin ta dauke. Nan take kuma yaji dakin ya gauraye da wata ibilishiyar dariya wacce kunnuwanka bazasu iya sanar da kai inda take fitowa ba. Domin in kaji Dariyar sai kace gaba daya ma dakin ne da kanshi yake dariyar.  Ga dariyar ba dadin saurare. Aliyu yasa hannuwa ya toshe kunnuwa hade da kara dukun-kunewa.  Kiii!  Yaji an kama kafar shi an jawo shi kasa cikin duhu ya mike tsaye yana lalube-lalube.   Can yaji ya dafo wani abu kamar mutum mari aka dauke shi da shi wanda karfin marin yasa har sai da ya wuntsila.  Ihu! Ya kwalla mai uban kara ya fara bada hakuri. Wata dariyar ta kara kaurade dakin. Ba tare da hasken dakin ya dawo ba ya kara mike wa tsaye.  Kamar iska ya kwashe shi yaji an maka shi da bango. Kafin ya yunkura ya dawo yaji an kara fisgar shi an maka da kasa. Ji yayi kamar bayanshi ya karye. Ihu ya fara kwallawa va kaf!-kaftawa su Zuwaira na dakunan su sai da karar ihun ya tashe su. Su kuwa basu kawo a ransu cewa malam ne ke ihu ba. Su wai zatan su aljanu ne. Hakan yasa suke kara dukunkunewa.........................................................._





DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah






👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


*Before last Page 112-113*


©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com



❤ DEDICATED TO MASOYAN LABARIN *ALJANAR FATIMA* ❤


🤗 Kun taka rawar  gani a yaba ba kadan ba. Masu bibiyar labarin nan. Dole nayi jinjina na kuma yi muki fatan alkhairi masoya na.  Hakika in baku bazan iya ba. Allah shi bar kauna. Safuratu na bankwana *HAUSAWA NA CEWA A JURI ZUWA RAFI. WATARAN TULU YA FASHE.* 🌝





          *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ihu ya fara kwallawa va kaf!-kaftawa su Zuwaira na dakunan su sai da karar ihun ya tashe su. Su kuwa basu kawo a ransu cewa malam ne ke ihu ba. Su wai zatan su aljanu ne. Hakan yasa suke kara dukunkunewa.~


_Haka Fatima taci gaba da tsorata malam Aliyu tana bashi wahala. Kafin safe sai da ta sumar da shi.Har Waje-jen karfe bakwai su mama Asiya basuga malam ya fito ba balle suji ya akayi. Nan wasu ke cewa aje a bude a gani. wasu kuwa cewa suke abar shi watakil aikin ne bai gama ba.  Suna zazane a falo bayan sun karya sai ganin Fatima sukayi ta fito daga dakin ranta a bace. Fuskar ba wal-wala.  Batayi wa kowa magana ba. haka kuma ba wanda yayi mata magana, Taje ta shiga dakin su jimawa kadan sai ta fito. Tana zuwa ta makore wuyan mama Asiya da karfe. Ba tare da tace mata komai ba. Mama Asiya tayi iya kar kokarin ta ta kasa kwabcewa. Sai da ta nemi agaji tukun da kyar sauran jama'ar suka kwace ta. Ana kankare ta daga nan ta sake shake wuyan Hauwa nan ma da kyar aka kwace ta. Nan fa ta shiga layi daga an rabata da wannan sai ta malale wa wannan. Kuma shakar da take bana wasa ba._






_Dan ji zakayi kamar wani Rikakken gardi ne ya shake ka. Kuma kafin a kwace kaji jiki. Da gudu su nasmat suka fita waje aka nemo mutane. Aka daure Fatima da kyar. Domin su kansu masu daure tan sunji jiki. Wasu duk tajiji musu ciwo.  A nan falo aka hadata da karfen jikin Matatakala (Stairs)  aka daure ta. "Duk sai na kashe ku ranar da na kunci". Abunda ke fita daga bakin Fatima kenan. Bayan hankalin yan gidan ya dan kwanta ne. Su mama Asiya suka tuna da aliyu. Da sauri suka nufi dakin kwance suka tarar da shi har lokacin a sume. Aka kawo ruwa aka yayafa mishi a firgice ya tashi yana raraba ido. Yana mikewa ya zabga a guje Kamar wani sabon mahaukaci. Ana kiran shi ko waigowa baiba. Da ya isa falo yaga Fatima a daure na hararen shi sai ya kara kaimi wajen guduwa. Asmart da Nasmat dariya kawai suke su. Zuwaira ta daka musu tsawa take tambayar su miye na dariya. Nan suke gaya wa mutane cewa Da gani Aliyu malamin karya ne. Nan suke fadar cewa su suka ci abincin da Aliyu yace Aljanu ne suka ci. Sallalami su Asiya suka kwasa. Zuwaira ke cewa in kuwa haka ne sai sunyi maganin Nafisa. Asiya tace "Ai ba wani ba wata zuwa zamuyi ta biya mu duk kudin da muka kashe kawai"._






_Zuwa sukayi suka same ta da masifa. Da kyar suka kankaro dubu uku a gunta. Haka Fatima ta kasance a gun a daure abinci ma hanata suka ringa yi sai dai fiddausi ta bata a sace. Abba kuwa har yanzu hannnun shi daya a makale. Sunyi-sunyi Fatima taki gyara mai hannu. Su Asiya duk a tsorace suke kullum fargabar kar Fatima ta kunce suke. Dan suna shan barazana da kashe di a gunta. Domin cewa take in dai aka kunce ta sai ta kashe mama Asiya Zuwaira da Hauwa. Hakan yasa ma suka gagauta kiran alhaji. Cewa yayi sharri suke mata. Hankalin shi bai tashi ba yaji ya matso ya dawo gida sai da yaji sunce sun daure Fatima. A lokacin ne yaje ba abunda yake so sai gida. Yau take juma'a ranar da Alhaji zai dawo. Tun da safe akata shirye-shirye aka gyara gidan tsaf!. Safiyanu da matar shi da yaran su uku sunzo. Haka ma Yusuf shida matar shi. Kowa yaci kwalliya in banda Fatima dake daure. Su Safiyanu da basu san me ke faruwa ba sai a lokacin suka tambaya mama asiya ta zauna ta shirya musu karya da gaskiya._





_Abba murna yake sosai domin yasan in dadyn su yazo dole Fatima ta mikar mai da hannu. Tun wajen sha biyu su Safiyanu suka yafi airport domin tarbo Alhaji.  Sai wajen karfe uku jirgin su ya karaso. Suka runkuto a mota suka taho gida.  Ba abunda yake tambaya sai Fatima. Haka da suka shigo gida duk iyalai sun fito kofar gida cik da farin ciki. Shi kanshi yaji dadin irin taryar da aka mai a tafiyar yan watanni kamar yaje yayi wani shekaru. Abunda ya rage mai farinciki shine kawai da baiga Fatima ba.  Aliyu da Abdul suka shiga jidar kayan da Alhaji ya kawo suna shiga da ita. Alhaji na shiga falo sukayi ido hudu da Fatima dake daure jikin karfe. Ta fashe da kuka hade da fadin "Dady kaga yanda suka daure ni ko?". Hankalin shi a tashe ya nufe ta tausayi ya kama shi kamar ya fashe da kuka. Nan take yaji wani irin haushin su Mama Asiya.  Kunce ta yaje ya farayi. Mama Asiya Zuwaira da Hauwa. Hankalin su yayi matukar tashi ganin abunda Alhajin ke shirin yi. Asiya da sauri tanufo shi tana hada shi da Allah karya kunce Fatima. Tsawa ya daka musu hade da cewa "mutanan banza marar tausayi. Wato abun naku har ya kai ku daure ta dan kunga uwar ta ta mutu ko?". Zuwaira da hauwa suma magiya suke binshi da shi akan ya hakura karya kunce Fatima ya saurare su amma. Yaki. Yana kunce Fatima ya warware mata igiyar dake jikin ta. Nan take suka rungume juna. Alhaji Salim tsabar tausayi sai da ya zubar da hawaye. Safuratu na ganin an kunce Fatimar sai ta koma jikinta. lokaci daya Alhaji yaji Fatima ta zabura ta kwace jikinta daga jikin shi kamar wacce aka tsinkula. Nan take idanunta sukayi jajur kamar wacce ta kwana tana kuka. Da gudu ta nufi kitchen kamar wata mahaukaciya. Bata jima ba akaga ta fito hannunta rike da wukA._





_Da gudu ta nufi su mama Asiya. Sa ganin haka sukayi waje da gudu. Fatima ta bisu. Alhaji Safiyanu da yusuf da sauran matasan da gudu aka bi su. Sai da kyar aka samu aka rike Fatima su mama Asiya kam har sun kusa fita daga layin sai da sukaga lala-lalai an rike ta an kwace wukar tukun suka juyo.  Kusan karti biyar ne ke rike da Fatima amma sai juyasu take kamar wanda  suka rike giwa. Hankalin Alhaji a tashe yasa aka nemo masu Ruq'yah. Bai wani bata lokaci ba malamin mai suna Bashir Halilu Tabiyyah. Ya karaso.  Yana shiga ya tarar sai fama ake da Fatima ana rirrike ta. Kai tsaye ya nufi gunta ya tofa mata wasu addu'o'i. Yace su sake ta. Ba tare da gardama ba suka sake ta.  Sunyi mamakin ganin ta tsaya cik ta natsu. lokacin su mama Asiya suka shigo. Kukan kura tayi ta warci wuka ta nufe............................................,..................._



🌝 Komai yayi farko zaiyi karshe 🤹🏻‍♂🤹🏽‍♂


DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah







👺👽👽👽👽👽👽👺 


   *^^^^^^^______^^^^^*

    *ALJANAR FATIMA*

   *^^^^^^_______^^^^^*


👺👽👽👽👽👽👽👺 


*THE END*


©🤴🏻 *KING BOY ISAH* ✍🏼

👑


.               👩🏻‍💻👨🏻‍💻       .

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*​

.         ✍🏼  *®Z.W.A*     .


.              📝         .

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_


​📚 _*Zaku iya samun littafan mu a Facebook*_ 👇🏽

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


📩 _*Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu*_ 👇🏽

Zamaniwriterassociation@gmail.com


*JIJINAR BAN GIRMA GA MAKARANTA LABARIN NAN. KAMAR YAU NE NA FARA DA ONE PAGE YAU DAI GANI A END*



       *KARSHEN PAGEN BAYA*

~Ba tare da gardama ba suka sake ta.  Sunyi mamakin ganin ta tsaya cik ta natsu. lokacin su mama Asiya suka shigo. Kukan kura tayi ta warci wuka ta nufe.~


_Su Mama Asiya. Da gudu suka koma. Malam yayi caraf! Da Fatima. Nan take ya fara tofa mata wasu addu'o'i shiru tayi tana kallan mutane. Malam ya mata karatu cikin kunnenta na hagun. Tukun ya dafa kirjinta yaci gaba da karanta ayoyin ruk'yah.   Ji sukayi ance "Dakata malam ni ba azzaluma bace".  Cikin bacin rai malam yace, "Ke kuwa ce azzaluma tunda gashi kin shiga jikin yar karamar yarinya kina kuma yunkurin kashe wasu". Aljanar tace, "Kwarai na shiga jikin Yarinya kuma hakan kariya ne daga wadancan azzaluman matan ubanta. Domin in ban kashe su ba su zasu iya kashe ta ita".  Tsuru aka zurawa Fatima ido da bakinta ne kawai ke motsi amma ba ita ke maganar ba. Alhaji har rawar jiki yake domin sosai yake san Fatima. Nan malam yasa aka kirawo su Asiya a tsoarace suka zo suna baya-baya da Fatima wacce sai hararen su take kamar idanun zasu fado kasa.  Malam yace wa Safuratu me su Asiya sukayi wa Fatimar na zallunci.  Bata boye komai ba duk ta kwashe abubuwan da su Asiya da 'yav'yan sukayi wa Fatima ta fada. Malam ya juya gare su ya tambaya haka ne. Jiki a sanyaye ta amsa cewa eh duk abunda ta fada gaskiya ne. Alhaji a zuciye ya nufi Asiya da niyar ya dake ta yana fadin "Amma Asiya kin cika macuciya maciya amana. Amanar ma ta marainiya kuma yarinya". Ba dan malam ya dakatar da shi ba kuma ta gudu da sai ya ji mata ciwo. Nan malam ya kwantar mishi da hankali ya kuma ga Safuratu yake tambayar ta ta yaya akayi ta zo gidan har take taimakawa Fatimar. Bata boye musu komai ba ta sheda musu cewa wannan aikinta ne. Ta dade tana irin taimakon nan da sasanta matsalolin ma'aurata.  Gaba dayan falon sunyi mamaki malam yake tambaya. Shin a kwai irinta ne dama a cikin Aljanu. Tace ita dai bata sani ba amma tasan cewa. Ba duka aka zama daya ba._





_Malam ya tambaye ta a kan me yasa take irin wannan taimakon. Tace "Dogon labari ne amma dai bari in baku shi a gajarce yanda kuma zaku fahimata. Uwata da ubana mutanen kirki ne a cikin mu aljanu tun kafin a haife ni a kasarsu wani babba daga cikin aljanun shi ne abun bautar su. Wata rana sai sani Aljani wanda shi ya kasance musilmi ne. Yaje garin bisa batan hanya. Da yaje kasar kuma mahaifina ne mutum na farko da suka fara haduwa da shi. Kuma shi ya sauke shi a agidan shi. Ko da lokacin sallah yayi. Ya tashi yayi su sai suna kallanshi ba tare da sun ma san ko me yake ba. Bayan ya gama sallar yaga sun tsura mai ido basu tashi sukayi sallah ba. Da ya tambaye su sai suka nuna basu ma san me yayi ba. Nan suke fada mai su ai shugaban su suke bautawa. Natsuwa yayi ya musu bayanin Islam sosai kuma suka fahimata suka gane. A kwana a tashi iyayena da wannan bakoj aljanin suka ta zagaye gari suna shedawa mutane addinin da suke ba na gaskiya bane. Muslinci shine addini  gaskiya suna amfani da hujjoji kwarara wanna yasa aljanu da dama suke aminta su karbi muslinci. Ana haka har magana ta kai ga wannan shugaba nashi. Nan take ya bada umarnin duk wanda aka kama a kashe shi daga iyayen nawa har wanda suka karbi muslinci.  An kama wasu an kashe wasu kuma sun tsira. Cikin wanda aka kashe harda mahaifina. Mahaifiyata da wannan bakon aljanin da kyar suka sha. A ranar suka bar kasar. Suna fitowa daga kasar mu aka ci sa a ya gano hanyar kasar su. Suka nifi can shi da uwata. In takaice muku labari a can garin mahaifiyata ta haife ni. Ta haife ni da kwana daya tace ga garin ku nan. A hannun matar wannan aljanin na taso labarin irin wuyar da nasha a gunta da 'ya'yan ta nada tsayi. Da naga dai abun yayi yawa suna neman sabautani saboda sunga ni marainiya ce bani da kowa. Sai na gudu. Garin yawo na har na iso kasashen mutane. Lokacin ban taba ganin dan adam ba.  Wacce na fara gani kuma yarinya ce yar karama. A wani daji_






_Ta jifgo itace da yawa a kanta. Da kyar take tafiya. Al'ajabi da mamakin ya cika ni. Hakan yasa na bita a baya ba mukata tafiya domin lokacin na lura da bata gani na. Sai da muka kusan zuwa gari na ringa hangen mutane kalar yarinyar. Da muka shiga nata ganin su kala-kala fari da baki. Ban  daina bin Yarinyar ba dai da mukaje har gidan su. Nasha mamaki ganin yanda mater wacce da farko nayi zatan uwarta ce. Tata dukan Yarinyar wai ta debo itace kadan. Sannan ta sake sata wani aiki. Haka dai naci gaba da bibiyar ta har dare. Abun ya bani mamaki sosai ganin ni irin abunda matar wancan Aljanin da yaranta suke min. Haka itama wannan Yarinyar matar nan da Yaranta suke azabtar da ita. Da na tsananta bincike sai na gano cewa ashe ita din marainiyace bata da uwa. Ubanta kuwa baya cewa komai ko a gabanshi aka mata abu. Hakan yasa ni kuwa nayi amfani da damata nata taimakon Yarinyar nan ina rama mata duk abunda aka mata. Dan dole suka shafa mata lafiya. Daga karshe na bayyana a gabansu na tsoratasu a karsu kara cutar da ita.  Kuma nayi musu kwakwarar kashe di.  Sai da na tabbatar sun daina mata duk abunda suke mata sannan na rabu da su.  Da nayo gaba a garin da na iske still na sake iske wata marainiyar haka dai naci gaba dayi zuwa yanzu bansan yarinya nawa da mata nawa na gyara wa rayuwa ba. Bana barin azzalumi. Kuma ni bana kisa. sai dai in wahalar. Ko su Asiya ma kawai ina musu barazana ne. Wannan shine takaitaccen labarina".  Ko da Safuratu. ta zo nan a zancen ta kusan mutum biyar sukayi ajiyar zuciya a lokaci daya. Nan malam da sauran mutane suka jinjinawa Safuratu hade da karfafa mata gwiwa. Su mama Asiya nadama ce  karara shimfide a fuskokin su. Malam yayi musu nasiha mai ratsa jiki. Ya kuma fadi musu illolin cutar da maraya da zaluntar sa. Da kuma irin ladar da mai kyautatawa maraya yake sama a gurin Allah. Sosai sun ji wa'azin dan wasu daga cikin su harda hawaye. Nan suka dauki alkawari cewa bazasu sake musgunawa Fatima ba. Suka kuma nemi gafara gun Safuratu. Tace ita ba ita sukawa laifi ba Fatima ce. Ta kara da cewa kyautata mata da yi mata alkhairi shine zai tabbatar mana da kun daina abunda kuke kun tuba. Sannan ku sani zan dawo ko ba yau ba. Da fadsr haka sukaji Fatima na attishawa. Daga bisani wani farin  hayaki ya fito daga bakin ta. Nan da nan gumi ya jike ta sharaf! Ba'q jima ba sai barci. Su mama Asiya har rige-rigen daukar ta akata daki ake. Alhaji shi kam baic komai ba. A zuciya yake addu'ar Allah yasa su Asiya su cika alkawari._



_Alhmdulilah kwana biyu gidan ya canza kowa san Fatima yake. Dan a cikin su Asiya har rasa wanda yafi san Fatima Alhaji yake. Haka bangaren yara ma. Su Nasmat duk inda zasu sai suja Fatima. Godiya Alhaji yayi wa Allah. Domin Allah shine mai saita komai. Gashi a lokaci daya Allah ya shirye matanshi sun gane gaskiya._


A nan nima nake cewa.


TAMMAT BIHAMDULILLAHI RABBIL ALAMIN 📿🕋


```A nan na kawo karshe labarin Aljanar Fatima. A yanda na tsara littafin yafi haka. Saboda wasu dalilai yasa na yanke shi. Ina rokon Allah ka kurakuran dake cikin littafin nan wanda nayi da sani da wanda nayi ba da sani na ba. Ya Allah ubangiji ka yafe min. Allah kasan kudurina a kan littafin nan nayi shi ne dan fadakarwa Allah ka shiryar da masu irin halin  nan ta Dalilin littafi na. Domin kai ne mai shiryarwa.```

 👏🏼👌🏼


SADAUKARWA:


Tun farko n sheda cewa na sadaukar da wannan littafin ne ga duk daukacin 'yan kungiyar mu. Wato *ZAMANIWRITESASSOCIATION*

👇🏼

Nasmat_____Ama Alhaji


Asmart_____Beauty Queen

Zeetty_____Xeenat 


Mmn nour_____mmn twinx


Sarah adiya _____Hafsat Ibrahim


Roukey baby_____Action baby


Kamal minna _____ Zaidu Ibrahim B.


Bamai dabuwa _____ Aysha mmn..


Maryam yar mama _____Zuwaira madara

Baby Maryam _____maryam bello


Nabila _____Jidda


Layuza _____Bestiyn Nanah 


Fareeeda ____Mmn najwa


Zulaihat rano _____Zulaihat b haladu


....... 😰😰 Yan uwa yaseen kun yi yawa. Wanda ban saba yayi afuwa

*SAKON GAISUWA GA:*


ZAINUDEEN°°° RASHIDAT A. KARDAM


SANAH SHAHADA°°° SANAH MATAZU



KHADIJA CANDY°°° KHADIJA AUTA.


MUHIEVER IND.°°° PURE GREEN


MUSA MELODY°°°SHAMSIYA SALILS


BASIRA N. DABO Y°°°QUEEN SALMA 


AUNTY MAIMUNA°°° ZAINAB YUSUF



HASSAN ATK°°°USAINI ATK



QUEEN HAUCY°°°AISHA A. GARKUWA


RAHMA NLELE°°°BILKISU BILYAMIN 


ALHASSAN °°° AVVA OMAR


DOCTOR MUBARAK °°°MUKTAR MUSA KARAMI.



*BAN MANTA DAKU BA MASOYA NA*


QUEEN SALMA ❤ MIZZ DADDY


LITTLE PRINCESS ❤ BEIBOH


AMÆL ❤ PHATEEMA


NANA AISHA ❤ SAKEENAT 


UMAR D UMAR ❤ ABDUL KING ART.

ZAINAB ♥ NABILA


HAFSAT ♥ KHADIJA


ISMA'IL AUTAN MAWAKA ♥ ISLAMIYYAT 


FARIDA ♥ AISHA


😰😰 Wallahi kuna da yawa masoya duk wanda baiji na ambaci sunanshi ba yayi min afuwa. Ina sanku 😘❤.


JINJINA DA YABO GA GROUPS:


ZAMANIWRITESASSOCIATION 


ELOQUENCE FANS


ZAMANI WRITERS FANS


BAIWA WRITERS ASS.


BIGBOY ISA NOVELS


3STAR HAUSA NOVELS


UMMU BASHEER


 HAUSA NOVELS GRPS


ALJANAR FATIMA FANS


MARUBUTA


ONLINE HAUSA WRITERS


PEN WRITES ASS.


GIDAN ZUMUNCI GRP


AMAL NOVEL GROUP


NASMAT NOVELS 


GIDAN MARAYU FANS


ONLY WRITERS



😰😰😰😰😰

🙆🏻‍♂ Groups din ma ko rabi na kasa rubutawa. ☺ Ko dan ko bqn saku ba kunsan cewa nasan kuna san Aljanar Fatima kuma na yaba sosai. Na gode da  bada tym dinku da kukayi na bibiyar littafina. 


Mu hada a littafi na gaba mai suna


🛩♥✈ *JIRGIN SO* ✈ ♥🛩


LABARIN SOYAYYA MAI TABA ZUCIYA. 


TSANTSAR SOYAYYA


BAN TAUSAYI 


SAN MASO WANI.


WAHALAR DA MASOYI


HAKURI 


JURI 


DAUKAR KADDARA


ILIMINTAR WA


FADAKARWA


NISHADANTAR WA. 


LABARIN SOYAYYA NE DA YA FARU A GASKE WANDA NA TSARA SHI NA TACE SANNAN. NAYI AMFANI DA KALMAN SOYAYYA MASU TAYAR WA DA MASOYA TSUMI. UHMMM KAR DAI IN CIKA KU DA SURUTU.  BISSALAM SAI MUN HADU A LITTAFIN 


🛩♥✈ *JIRGIN SO* ✈ ♥🛩


WASHHH! MUN RABU DA ALJANU.LOL



DOMIN SAMUN FARKON LABARIN, DAMA WASU LABARAN MASU DADI DA MA'ANA. SHIGA PAGEN MU KA/KIYI LIKE. 

Fb.me/ZAMANIWRITERSASSOCIATION


SHIGA NAN KA/KI YI LIKE. DOMIN SAMUN FARKON LABARIN. DAMA WASU LITTAFAN KING BOY ISAH.

https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks


Autan marubuta nee  King Boy Isah






Post a Comment

0 Comments