ZARA TAWACE. HAUSA NOVELS

 zahra tawa ce*💞💞💞


Fatima Abdullahi Ibrahim *( Fatima zois*)



Bismillahir rahmanin raheem



Page1⃣





Tsaye yake a filin shi kadai yana handball cikin kwarewa tare jarumta daga ganinsa y saba,Dogo  ne s osai mai yalwar fadin kirji Wanda yake dauke da six packs wanda komai tsayin mace ta tsaya a gabansa sai ya rufeta har ma baa ganinta,jikinsa duk a murde yke d alama zaiyi karfi d jarumta.kyakkyawa ne ajin farko mai cike da kwarjini Wanda duk rashin mutuncin mutum bai isa ya kalli fuskarsa ba yaci masa mutunci,yana manyan idonuwa wnda yake kara masa kwarjini tare da dogon hanci har baki,yana da dan faffadan baki mai dauke da siraran labba d fararen hokara ,fari ne sosai Wanda saboda fari har ja yake wani lokacin,a takaice dai komai na *gadanga* mai kyau ne.



Ball din yake cikin zafin nama d sauri kamar bashi kadai yake ball din ba,wani sauti naji n tashi a system din dake kusa dashi,miss jamila ce take masa magana cikin fada ba tare da shikoma ya daina abinda yake ba,gadanga yaushe ne zaka je ka dauko cells din yarinyar nan ne Tun dazu ko alamar tafiya baka yi kasan dai akwai aiki a gabanmu, magana take yi kamar bada aliyu take ba,saida yayi kamar baxai amsa ba still koma bai daina ball din da yake b matsowa yayi kusa d system din ,yana cewa miss jamila cikin tsantsar d kasaita kamar Wanda aka sa yayi magana dole,Hava miss kinsan dai tunda kin fada min zanje miye naki n damuwa y fada still bai daina ball din ba.



Miss jamila ce tace kasan nan da 20minutes zata fito aiki please ina son kayi abun d sauri mana gadanga cos wannan ba halinka bane kodan kaga mace ce?,miss jamila t tambaya tare d sake dubansa ,are no ba hka bne ynxu xan tafy kinsan yadda nike,yayin da yabar ball din yakewa miss jamila magana,cikin sauri ya nufy cikin gidan yana waving miss saiya dawo.OK my guy see you tare da blowing kiss ,shima ya maida mata tayi ending call din.



Cikin abinda baify 10minute ba ya shirya cikin shigarsa Wanda ba Wanda ya taba ganin fuskarsa duk da cewa shi din ana nemansa ruwa a jallo cos he's wanted ya gagari manyan mutane masu kudi da attajirai,kaf naija babu Wanda bai San da wanzuwa *gadanga* bah cos aikin shi shine kawai yaje wajen manyan masu kudi hamshakai d attajiran mutane,manyan yan kasuwa da dai sauran masu fada aji na kasa yaje ya dauko wani da ake bukata,baya sata baya koma kisa,asalima yawancin abinda  ake turashi bincike 

Wanda yakewa haka Manyan fada aji masu boye wani muhimman Abu kodai cin hanci d sauransu.



Babu Wanda ya taba ganin shi acikin wannan shigar sai mutum uku:daga miss jamila sai alhaji usman abokin babansa sai koma lady saudat Wanda take karbo abinda aka turashi ya nemo xuwa wajen miss jamila.



 Domin duk wannan shakuwar dake tsakaninsa da miss jamila bai taba ganinta ba hka itama bata taba ganinsa ba aikinsu through internet suke koma basu taba samun sabani bah.miss kwararriciya a harkar zamani musamman internet   Wanda saboda haka suke cemata *hacker* komai nasu thorough system suke yi Wanda da taimakonta gadanga take samun nasara.





Duk Wanda gadanga xai yiwa  Abu saidai ya turamasa ta address dinsa na email idan mah da wata manufar kk nemansa miss jamilazata gani koda babu su CCTV data iya dubawa koda ta wayane da sauran hanyoyi da dama.


Cikin sauri y gama shiryawa cikin bakaken kaya Wanda ko farcensa baa gani koma komai kwakwarka baka isa ka ganeshi bah.cikin sauri y fito daga cikin gidan Wanda shi Kansa gidan zaiyi karamin estate amma a haka idan kaga gidan kamar kango saika yi tafiya mai nisan gaske acikin gidan tukunna xaka iske ainahin gidan, shima cikin gidan kamar irin tsohon gidan nan da aka Dade d tashi ga tarkace babu Wanda zaice ana rayuwar acikin gidan, Tukunna ka shiga ainahin inda yake rayuwarsa tamkar baa kasar gidan yake bah saboda tsananin kayatuwa d haduwar gidan Wanda idan n tsaya bayani har sai in gama wannan page din ba tare Dana gama ba,mai karatu na baka gari ka kwatanta yadda gidan yake😉.






 A tarihin wannan gida bbu mahalukin daya taba shigarsa sai iya shida alhaji usman wato abokin babansa,Wanda shi ya daurashi akan wannan Sana'a koma y koya masa dabarun fada mai karfi Wanda ko kwarzinin jikinsa ba xaka iya tabawa komai kowa karfin ka,koma ya koya masa dabarun kare kai daga technological appliances. Shiyasa ya gagari mutane masu nemansa ruwa a jallo.




Cikin sauri ya fito yazo saidai wajen da yarinyar take hawa mota cos yau ta makara a wajen aikinta,yana tsayawa ya hangota daga nesa tana tahowa cikin gudu ga wata katuwar jaka a bayanta kamar school bag tana gudu amma kamar dawo da ita baya ake saboda jakar tana son ta tsayar Bus,abun mamaki ya bashi da yaga katuwa da ita a cewarsa tana wani gudu ,saurin connecting din Bluetooth din dake kunnensa  yayi Wanda duk masifarka b xka ce Bluetooth bane cos it's new design from miss jamila tare d connecting video  din komai da akeciki  through his telescope glass.





miss jamila ce zaune tana cin snacks kamar wacca take ci da wani sai cika baki take cos ita bata ma d lokacin komai idan ba salla bah shiyasa idan tana cin abinci few minutes tayi ta gama,miss jamila data cika baki tana yiwa aliyu magana tace yawwa ga yarinyar nan ka duba jakar ko zaka samu matajin gashi ko brush ko nail cutter ko thumbprint nata or something like that ,OK hacker cewar aliyu tare dayin shiru ita koma miss jamila tana ganin komai cos tayi collecting telescope glass nashi d system, Bus yaga yarinyar ta shiga cikin sauri shima yabi bayanta ya shiga.




Hash😓 yaji yarinyar ta fada,yanzu har an wani cike kujerun gashi ina son zama a kujera yanzu dole saidai in tsaya ta fada tana yatsina fuska alamar ba haka taso bah cikin saurin t cire wannan katuwar jakar ta bayanta saboda gajiya,juyuwar da zata yi bata San da mutum a kusa da ita kawai saiji tayi sunyi gware har tana  Neman fadowa kasa,cikin sauri aliyu ya tarota tamkar wata baby saboda rashin Nauyi,fincikar da yayi mata da karfi ne yasa tayi masauki akan faffadan kirjinsa,wani irin shock hade feeling Wanda bai taba jin irinsa ba yaji a tare dashi Wanda har yaso ya manta inda yake saida yarinyar tayi karfin halin ta fincike kanta daga jikinsa.




A tsorace ta kalle shi idonta kamar sai fado saboda tsoro wata sansanyar murya hade d zaki yaji tana cewa "am so sorry please" tare da kura masa ido sosai duk da cewar bata ganin komai kallon ta yayi ya kalli fuskarta mai dauke da manyan idano bare yanzu data tsorata ga dogon hanci har baki Wanda yake karami kamar idan tayi magana kmar baa jiba ,fuskarta rounded face ce mai dauke da dimple point Wanda ko motsa fuskarta tayi sai dimple ya fito tana da yalwar gashi a goshinta Wanda suka kwanta luf.luf tare da bakin saje baki dake kwance a gefen fuskarta girarta kam harta kusa hadewa amma siririya ce kmar Anyi sharping nata, idonsa ya sauko xuwa kasa yaganta doguwa ce sosai amma  ba chan ba koma ba siririya vace baiga komai  a jikinta bah saidai zarazaran yatsun hannunta Dana kasa cos dogowar rigace a jikinta Wanda idan ka kalleta zaka ce bbu komai a jikin,duk wannan kallon yayi mata cikin abinda bai wuce few seconds bah.




Ya salam ya furta a hankali Wanda miss jamila da take cusa snacks a bakinta tana hadewa da kyar ta tsaya tana kallon komai tare da sakin baki da hanci tana kallo ikon Allah ya salam din daya fada ya ankarar da ita tace gadanga mai kake haka yarinyar nan pah kallonka take,sai a lokacin ya tuna abinda ya faru yayi saurin juya fuskarsa.



Yarinyar data ga haka kawai ta tabe  baki ta daina  kallonsa.wasu passengers ne suka fara sauka shine ta samu damar zama akan kujera,shima ya zauna a kujerar dake bayanta,kallon bayanta yake sosai daga ta juyo sai ya juya haka suke tayi har suka sauka.


Tafiya take still tana yar rawa da kmar mai jin waka, shipa abun nata mamaki yake bashi ita kenan ba zata iya tafiya ba normal saita hada da wani tana Abu kamar wata karamar yarinya,ji take tamkar ana bin bayanta amma idan ta duba bata ganin kowa,aliyu gani yayi tana Neman yi masa nisa,wani mai keke yazo wuce daya dauki wani gwangwami akan hanya ya bugawa mai keken akan tayar keken ts gaba Wanda yake saidai saitin kosa da yarinyar keken yayi kanta kmar zai bugeta nan ta jepar da jakar shikoma mai keken ya fada kan kayan mai fruit Allah yasa mai mata barna ba,sai ya shiga basu  hakuri ita da yarinya ,aliyu na ganin haka ya dauke jakar yarinyar yayi wani dan toilet da ake yi abakin hanya saboda tsaro,yarinyar na juyowa taga bata ga jakarta ba  saurin  fara nema jakar tayi amma bata gani bah zuwa hankalinta ya tashi ,hangowa aliyu tayi da Jakarta yayi hanyar toilet din cikin sauri itama ta bishi .




Aliyu ya fito da kayan ciki yaga babu komai sai tarkacen su chocolates da biscuit iri iri da kayan make up harda su pad mah y gani sai koma jotter dasu pens duk gasu nan tarkace dai babu abun kamawa aciki, miss jamila da take kallon komai through his telescope glass tace gadanga nipah banga wani komai bah yanzu ya zaayi kenan? Kafin tayi magana tuni har zahra ta iso dai dai toilet din da yake tana haki kmar wacca ta shekara  gudu,moper din dake aje a wajen toilet din ta dauko tare da sawa a jikin inda ake key wai ita a nufinta ta rufeshi,masifa take tayi tana cewa kai barawo ko yau Allah ya kama ka daga ni baza taba yiwa wani sata bah,wayarta ta dauka ta kira police tana fada musu cewar gashi wani barawo ya sace mata Jakarta suyi sauri cos gAta anan ta rufeshi har suzo,aliyu gani yayi tana bata masa lokaci cikin sauri ya daki kopar sau daya moper din ta karye tana yawwa address din gamu a toilet din bakin titin....bata karasa ba taji an fincikota wayarta ta fadi shikoma ya janyota tare da matseta a jikinsa yanda ko motsi bata iyawa ya dauki nail cutter ya fara yanke farcenta cos bai samu komai a jikin mataji da nailcutter din bah.





Jiki na karkaruwa kamar mazari tana jin yadda yanke farcen NATA cikin rawar murya tace da xafy pah! Can u wait for a while aliyu ya fada.Juyuwar da zaiyi sai gani yayi ta kafeshi da ido ta cikin mirror din toilet cikin sauri yasa hannu yayiwa mirror suka daya ya fashe.numfashinta ne yaji kamar xai dauke don tsoro da firgita har jikinta ya fara saki cikin sauri ya yaga ta dakko wani magani tana kokarin sha amma saboda karkarwar da jikinta yake ta kasa har maganin na Neman fadowa cikin sauri ya karba yana tambayarta how many pins are u taking? Ta nuna masa yatsunta biyu da sauri ya dakko ya bata tare dasa abakinta, miss jamila CE ta sake masa magana gadanga mai kake yi haka tunda ka bata maganin ka tafy mna cikin sauri ya dawo daga duniyar tunanin da yake A hankalin ta fara jin nutsuwa sai sannan ta tuna abinda ya faru kafin tayi wani yunkuri  aliyu ya fice ya tafy kmar wani walkiya.





Saurin tashi tayi da taji dama dama cos toilet din kmar baa shiga kullum yana a tsaftace ta tattara kayanta a jaka t fito kamar ba itace matsoraciyar nan ba 


Yau na shiga uku a wajen oga isah ta fada a rants cos koda zata fada komai bazai yadda saboda yasan halinta.



Cikin sanyin jiki ta karasa wajen da take aiki,Tun daga gate taga ana mata wani kallo,Tana shigowa abokanan aikinta suka hada bakin wajen kiran *zahra* irin kiran da idan aka yi maka Kasan abun babu dama daman a cewarta yan aikin nan sunfi kowa munafurci da kara kaimin fadan murguda baki tayi  tare da cewa na changa muku ne  

,Oga isa najin ance zahra ya fito da gudu yana dubanta kamar zai daketa,zahra sai yanzu kika zo? Yau koma mai ya tsayar dake wanke wanken ne ko koma girkin breakfast ko wankan yara Oooh na tuna keke ne ya Lalace a  hanya,kodai baki samu bus bane ? fada yana kara tsareta da idonsa don inda ka kalli yanda yake fadan saika yi dagaske wajen buye dariyarka,Kujera ya samu y daura daya akan daya ya rike dan gutun gashin bakinsa yana shafawa alamar ita pah yake jira ta bashi amsa, zahra dago da kanta tayi ta kalla kowa a wajen ita yake kallo wasu koma na kwasar dariya kasa kasa cos da alama sun saba da wannan fada da ake mata saboda tsananin son gulma har barin aiyokan da suke yi sukai suna kallon wanne mataki zai dauka,kallonta ta maido gun oga isah oga please kayi hakuri baxan sa...kafin ta karasa harya tari numfashinta tare da cewa kedin CE bazaki daina halinki bah oga Karka damu watarana nice sanadin daukakar wannan gidan labaran,kafin ta sake magana har ya tashi ya bita suna ta zagaye wajen tana oga Karka wani damu wlhy zahra dabance zakaga abinda xai faru a wannan gidan saboda ni ta fada very proudly, jotter dake kusa dashi ya jefa mata yana ke don  Allah yimin shiru sai dadin baki. Yau kije gida ki huta cos ko kin zauna bacci zakimin Allah yasa koma inga Gobe baki zo da wury bah.Zahra CE ta tsaya daga zagayen da suke yi cos daman kullum ya tashi yiwa zahra fada ahaka ake yi koma a haka kaf cikin maaikatansa babu Wanda yake so irin zahra cos jininsu ya hadu koma baa shiga tsakanin fadan oga da zahra idan ba hka bah xka ji kunya ne


Dagaske oga?  ta fada tana yalwata fuskarta da murmushi Wanda har sautinsa na fitowa kallonta yayi Wanda iya fuskarsa ka kalla sai cikinka ya kulle don dariya ga wani sanko da Kansa ya bayar Wanda gefe da gefe wasu tsirarin gashi ne kmar ka kirgasu,Zahra wato har ynxu ke bakisan gatse bah koh? cewar oga wani shafa wannan sidaddan salon nasa kmar Wanda ake yiwa tankal🤣 ba haka bane oga zahra ta fada tare da xuwa sit nata ta zauna.



Tuni kowa ya soma aikin gabansa,zahra CE kamar abun Kirki ta fara aiki a system dinta kafin zuwa 30minutes harta kwanta bacci kamar ba aiki tazo. 


Oga isah ne ya fito zagaye sai ganin zahra yayi tana baccinta cikin kwanciyar hankali.zahra😡 ya fada  fusace Wanda yasa kowa na wajen ya nutsu,zahra CE ta tashi tace wlhy oga yunwa nike ji shiyasa amma bari inyi sabon zubi nasan ba zaa fara drink awajenka bah please dan wuntsilo min daya mana.


Oga yace zahra tashi ki tafy gida cos naga ganki yau sai a slow Allah ya kaimu gobe. Cikin sauri zahra tattaro kayanta tare da yiwa abokanan aikinta sai gone suma hka.


Direct gida ta wuce wani hadadden gida ne Wanda ya ansa sunansa wajen haduwa daga gani naira tayi aiki a wajen.Duk haduwar gida wannan gida daga wajen Kadan Wanda a jikin gidan mah take saidai kofar shiga ba daya akwai wani ake saida duk wani kayan drinks da kake cos abban zahra ne abun yake burgeshi amma still akwai kopar da taxa sada mutum da wajen ta cikin gidan inda abbanta ya sanyawa suna *zahra tawa CE* mai karatu shima wanna ko kiyasta gidan da kanku😉

   


Zahra su uku neh a wajen iyayenta,  abdulmalik ne babba Wanda ya gama  karatun Business administration a  US yanxu shi ke Jan ragamar business din abba sai  zahra daga nan auta affan Wanda yake secondary by now,shikenan haihuwa ta tsaya musu amma kullum momma da zahra suna adduar Allah ya kawo musu mace, duk wani gata da tarairaya sun  samu a wajen Abba da momma wato mahaifiyarta Wanda idan suna Tare tamkar wasu kawaye amma duk da haka basu bar yayan nasu  sun  San Grace bah cos akwai irin kallo da idan suka yi masu  ba zaka CE suna wasa da dariya haka bah.Amma duk a gidan anfy son zahra kodan ita kadai CE mace.




Alhaji abubakar sadeeq shahararren dan kasuwa koma shahararran barrister yana da matarshi hajia ameena Wanda aka fi kiranta da momma yan asalin garin gombe ne aiki ne ya kawoshi abuja  amma duk da haka yana kokarin zuwa gombe cos baya  wuce two weeks baije yaga gida koma duk zuwan da zaiyi sai yayi musu alkhairy  mai dumbin yawa ba iya yan uwansa ba harda makwabta.wannan CE yasa yake da masoya a duk inda yake. 


Zahra tayi karatun mass com.a ABU Zaria tare da fitowa da grade mai kyau cos zahra badai  kokari bah,amma tunda ta fara aiki a DiamondTV shikenan zahra ta shiririce Wanda daman aikin tana tana  kawai.koma daman aikin iya daga Thursday zuwa Sunday ne,oga isah ne yake rike da wajen amma DiamondTV ba wani shahararran waje bane cos ba kowa bane yasan da wajen.


Zahra yarinya CE yar kimanin 23years amma a ynda take rayuwarta a sangarce da koma yanda fuskarta take baby face saika rantse kace yar 17-18 years ,doguwa CE amma tana da kirar jiki mai kyau ta gaske mah kowa cos ita CE ake kiran irin jikinsu da figure 8,akwaita da hips tare da mazaune masu daukar hankalin mai kallonta ga kirjinta a cike dai dai da jikinta wannan CE yasa momma ta dinka mata dogayen riguna masu yawan gaske tare da hijjabinsu Wanda idan tasa saita dawo karama sosai koma bazaka taba ganin Surar jikinta bah,Asali ma zaka dauka ko kwaila CE.


Zahra data dawo  saida ta Dade tana saka da Warwara cos bata San abinda zata fada a gida ba ace ta dawo daga  aiki lokaci baiyi bah.chan wata dabara ta fado mata saida ta shigo cikin gidan tukunna ta haye step taje falon dake  tsakiyar gidan  ta  saki kuka mai tsoma zuciya kamar dagaske koma a lokacin kukanta take tsakanin da Allah cos yanzu ta kara tunowa da. Abinda Gadanga yayi mata......



Am sorry reader for any kind of mistake cos this is my first novel.

[6/17, 10:02 PM] ‪+234 706 618 5922‬: 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖


 💞💞💞 *zahra tawa ce* 💞💞💞


fatima Abdullahi Ibrahim *Fatimazois* 



Page2⃣



Dedicated to *Babbar yaya* ( _ramby *011* )




Karar da zahra tayi yasa momma d Abba fitowa Wanda tuni abdul da affan sun rugasu.


Cikin tashin hankali affan ya fara tambayarta *didi* mai ya faru ?Abdul na tambayar sis mai ya faru momma da Abba kowa har rigen xuwa wajenta suke tare da ruko hannunta suna tambayar mai ya faru amma ina zahra kamar kara zugata ake sai kara fashewa take da sabon kuka har da shassheka.


Affan ne yayi sauri xuwa Despenser tare da debo ruwa mai sanyi Ya kawowa zahra,"didi ansa kisha" zahra dake kwance a jikin momma tana bubbuga bayanta alamar rarrashi,  Abdul d Abba suna rige da hannunta, saurin ansar ruwan Abba yayi tare da mikawa zahra a baki little ansa kisha.


Saurin ansa zahra tayi cos at that time she can't refuse it,saida tasha ruwan sosai tukunna Abdul ya ansa yana fadar are you OK?  Gyada masa kai tayi tare da sauke sansanyar ajiyar zuciya,momma ce tace "it's ok little take a deep breath & confuse what you want to say" cewar momma tana cigava da shafa yalwataccen gashinta daya kanta har gadon bayanta.


Sansanyar ajiyar zuciya zahra ta saki tare da sake kwanciya a jikin momma hade da riko hannu abba da Abdul ta kamo affan xuwa kusa da ita shima ya kanta a jikin ta,cikin sanyin murya wacca daman Indai suka ji wannan murya sunsan da gaske zahra take babu alamar wasa My dear one's kunsan gadanga wanted da ake nemansa ruwa a jallo Wanda kullum ana cikin maganarsa a news,news papers,radio social media da dai sauransu??? Cikin sauri har suna hada baki suka yes dear mai ya faru? Zahra ce ta kara narkewa a jikin momma tare da sake kamkame hannun Abba da Abdul shima affan ya sake kwantawa a jikin ta ta wani zare ido kmar a lokacin abun ke faruwa tace  "shi na gani yau har yanki farcena"... Bata karasa bah gaba dayansu suka zabora what⁉suka hada baki gaba dayansu😨 "are you sure you are not dreaming"??? Zahra ce cike da shagwaba ta CE am "absolutely sure nah" tare da bata rai irin na yanda bata ji dadin kin yarda da ita da sukai da ita.


Wani kukan shagwaba ta saki tare da tashi daga jikin momma tana bubbuga kafa tana Neman tashi daga wajen amma suka riketa my dear ones why you can't agreed with me??? Did I ever tell you something like that ta fada tare da turo baki tana tana yar hararar Abdul Wanda yafy kowa shiga rudu akan xancen.


Abba ne yace how" comes little"??? Sounded intentionally, zahra ce ta fada musu Tun daga farkon shiga bus har zuwa sanda ya dauke Jakarta.


Cikin sauri suka sake hada baki are" you ok"? Tace "yes" Abba ne yace "sure" zahra tace "absolutely " tare da yi masa kiss a fuskarsa.


Ganin hankalin family nata yafy nata tashi yasa ta tashi tare da fadin "nace bah"😉 cikin wata irin murya mai ban dariya nan da nan suka fara dariya  affan ne shima cikin irin murya da zahra tayi tare da shakiyanci yace "nace didi matsoraciya ya aka yine" nan fah wajen ya kwashe da dariya amma banda zahra data cika tayi fam cos tasan affan magana yake fada mata, ugh😠 you little bastard how dare you? Ta tafi da gudu kan affan Wanda ya tsere mata suka fara zagaya falon tana jefa masa filo din kujerar ka tsaya mana in nuna maka jarumtana cos nasan da Kaine kaga gadanga saika yi fitsari a wando before yayi maka komai,hka sukai ta zagaya falon har suka gaji zahra ta zube a center carpet tare da maida numfashi.su koma su Abba sai dariya suke musu.






Aliyu koma farcen zahra ya dauka yasa a Leda tare da rage kayan jikinsa Wanda babu Wanda zaice gadanga ne cos kullum daman akwai karamar bag a bayansa savoda aiki da koma tsaro Wanda kusan ya cire komai na fuskarsa sai Bluetooth din da yake kunnensa yana  communicating still da miss jamila.


Wani waje ya samo inda baida babu jamaa sosai asalima kamar bayan gari haka wajen yake still magana yake da miss jamila amma yanxu ya cire telescope glass din saita Bluetooth, Gadanga yanzu koma saika je gidansu ka nemo mana wani information akanta da koma yanayin yadda take rayuwa a wajen aikinta.


Gadanga ne yace hacker har ynxu kenan baa gama aikin ba? Miss jamila ce tayi saurin Tarar sa yimin shiru da bakinka a wajen😒,Aiki mah yanzu muka fara.



Tsara yanda aikin zai kasance suke ita da gadanga sai ga  wani hadadden bike wanda ya gaji da haduwa mai karatu kawai ka hasko bike din doom 3,lady saudat ce tazo tana ta surutu bbu ko coma bare full stop.


Gadanga ne ya miko mata ledan da farcen Zahra yake tare da yi mata sai anjima, lady saudat ce tace gadanga ina yi maka magana kayi shiru kamar baka sanni ba  at least koba komai aiki ya hadamu koda baxan iya abinda kake yiba...shakewa tayi sakamakon hular bike din da gadanga yasa mata a kai tare da buga kan nata kadan yana cewa have a good day.


Takaici ne ya ishi lady tayi zuciya tare da dukan bike din dake kusa da ita,uccch!!tare da duba inda ta buge.


Aliyune ya tafy gida ya kwanta kafin xuwa anjima yaje gidansu zahra yayi binciken abinda ya kamata akanta yana mai tunanin moment din daya wuce dazo.Tsaki ya saki cos shi bai son duk wani Abu da zai takura masa bare ya hani shi yin komai.


Dare ne yayi  amma sakamakon fitilun da security light da suka zagaye unguwar baxaka ce dare bane cos by that time wasu suke fita ma abinyi.


Gadanga ne kamar wani biri yana ta tsalle a jikin bangon gidansu zahra dai dai inda dakin zahra yake ya nufa duk da cewar akwai tsaro a gidan sosai amma hka ya tsallake ba tare da kowa ya ganshi ba har ya bude window din dakin zahra cos she's in d step koma manyan windows ne Wanda mutum zai iya shiga ta ciki.


Gadanga ne ya shiga room din zahra yana mamakin tsaruwa tare da haduwar dakin cos komai pink & white ne na dakin ,gadonta ya fara gani dai dai misalin kwanciyar mutum daya mai kyau da tsari shima pink & white ga wata resting chair dake manne da jikin gadon daga gaba,mirror dinta ya Allah Wanda shima ya gaji da haduwa komai nakai white & pink ga kayan costumetic kala kala masu tsada daban daban a jikin gadon ,Daga wani dan lungu a dakin yaga inda system dinta tare sit din xama a wajen suka pink and white ko computer mah white ce da aka yi mata kwalliyar pink mai kyau da tsari a jiki,Hatta jikin hango anmata decoration na pink & white a jiki komai na dakin pink nd white wardrobe center carpet centre table duk gava daya pink & white mai karatu har toilet dinta ma pink nd white ne har colour din fent.




 kamar wani Wanda ya shigo nasa dakin hankali kwance kamar Wanda bai tsoron wani ya gansa yake gudanar da aikinsa, Hacker ce tayi masa magana tare da nuna masa system din kusa dashi ya duba kozai samu information akai dubawa yake baiga komai ba idan ba tarkacen cartoon da abubuwan aikinta sai koma games.miss jamila ce tace ga wayarta dakko mu gani,wayarta ya dauko kirar iPad itama Anyi decorating dinta da pink & white Wanda ta lock da password.


Miss jamila ce tayi searching number nata Wanda daman already tana information na komai a sim nata.turowa aliyu number nata tayi tace ya tura mata message saboda yayi connecting din wayarta da system din hacker da koma tasa wayar,turawa yayi within a seconds hacker tayi hacking din komai na phone din nata.Magana suke yi sosai da miss jamila kamar ba gidan wasu yazo sai 

jin knocking din kopah sukai alamar zaa bude kopa,cikin sauri gadanga ya shige kasan gadon dakin cos zaa  iya shiga kasan gadon a buya,Daga kasan gadon yana hangota tana waka cikin kwanciyar hankali tare da rawa sosai kowa tana bin wakar kmar ba itace ta tadawa dasu Abba hankali ba.


Rawa take yana mamakin yadda take juya jikin ta kamar ba kashi cos headphone ne a kunnenta daga ji wakar India take saboda yanayin yanda take rawar,gani yayi ta cire headphones din daga kunnenta tare da aje wayar akan mirror duk da cewar iya daga kugunta xuwa yatsunta yake gani.



Kayan jikinta yaga ta fara cirewa tana ragewa Wanda yasa ta fito daga ita sai underwear nata,Ido har ya kara warewa cos shi bai taba ganin mace a haka ba,miss jamila ce ta saki wata yar kara a razane cewa gadanga mai nake gani😱???shikam aliyu da bai Masan a wacce duniyar yake ba yaji maganar hacker ta cika masa kunne tunni ya cire telescope glass ba tare da yasan ya cire ba yana mamakin wannan skin din kamar ta baby sabuwar haihu babu ko digon tabo a jikin ta daga gani zatai laushi.


Mamaki yake wai ba ita ce ya ganta ba dazo kwaila da ita yanxu koma zai ganta a cike anya kowa ita ce wata zuciyar ta fada muryarta yaji tana cigava da wakar shine ya tabbatar da ita ce amma wata zuciyar na iya cewa Hava dai wannan zahra yarinya Dana ganta dazo babu komai a jikinta.Bai gama zancen zucin da yake ba yaga ta shige toilet.


Zahra kowa yau kamar tasani bata cire kayanta ba a daki cos ita ta tashi shiga toilet babu kaya take shiga amma zata fito da towel.


Maganar miss jamila yaji tana yi cikin fada da alama Tun dazo take yi bai sani ba ta Bluetooth din dake kunnensa.Nan da nan aliyu ya kama yan maganganu da Kame kame yana sosai keya  cos duk maganar daya fada sai yaji ya kasa karasa🤣,hacker ce take tayi masa magana akan ya tashi ya fito tunda zahra ta bar wajen amma kafin ya tashi tuni har zahra ta fito daga wankan sanye da karamin towel Wanda iya cinya ne still wakar take yi,Oops! zahra ta fada ina iPad dita? Aliyu sauri kallon hannunsa yayi mai rike da iPad din.....

[6/17, 10:45 PM] ‪+234 706 618 5922‬: 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖


💞💞💞 *zahra tawa ce*💞💞💞

  


Fatima Abdullahi Ibrahim( *Fatima zois*)

 


Dedicated to *Babar yaya* (ramby *011*)


Page3⃣







Aliyu saurin kallon hannunsa  Yayi mai rike da ipad,A hankali ya lallaba ya  tura wayar ta fito sosai yanda zahra taza gani,zahra data juya bayanta tana Neman Wayar bataga mai yake faruwa bah.


Juyowar da zatayi sai ganin wayar tayi a bakin kasan gadonta mamaki take yi ita data ajiye wayarta akan mirror yanxu koma ta gani a kasa!sunkunya tayi tana shirin duba kasan gadon sai taji affan na kwala mata kira "didi wai baki gama shiryawan bane gashi kowa yana jiran ki a darning ni wlhy badda Abba yace ba zaa fara Cin abincin ba sai kin zo da tuni na gama ci na tafy"


Am sorry my guy yanxu zan fito kayana kawai zan sanya zahra ta fada tare da saurin surar iPad ta ajiye itama koma tayi saurin shiryawa cos tasan tunda affan ya fara mita babu sauki.


Readers hasko aliyu a kasan gado😆 yayi tsilli tsilli da idona ya samkame ko numfashin kirki bayi,Bawai don yana tsoron zahra ta ganshi ba are no saboda bai son abinda zai wargaxa masu wannan plan din.


Miss jamila CE yaji tana cewa ai saka tashi ka fito tunda ka gama kallon komai ita ta fita ok  😒.


Fitowa aliyu yayi daga kasan gadon tare da sake yan dube dubensa ya biyo ta window din dakin ya fito abinsa.


Fitowarsa kenan yasa telescope glass nashi,hango wata mota yayi wanda kullum sai ya ganta a jikin gidan Tun lokacin da yake bincike akan wacce zahra da location nata.A kullum motar tana yin kamar 1hour a wajen kafin ta tafy motar sanye da black tinted glass.


Hacker CE tace gadanga wannan motan pa kullum saina ganta mai hakan yake nufy koma baa taba fitowa bah kullum a tsaye take sai lokacin tafiya yayi a tafy?!!! Kafin gadanga ya bata amsa tuni har motar ta fara tafiya cikin sauri gadanga yace bari inje in duba wayye a ciki koma daga ina yake.


Motan yaga tana tafiya a hankali cikin nutsuwa daga gani mai motar yasan abinda yake,cikin sauri gadanga ya dinga tsalle yana gudu a saman gidagen da wajen yana bin duk inda wannan motar tayi kamar wani biri.



Haka gadanga ya dinga tafiya a saman ginin wajen yana bin motar ba tare da mai motar yasani ba har saida suje wani hadadden gida Wanda yake kato ne sosai da alama shima gidan manyan masu fada aji ne.



Mai motar na xuwa ya danna remote nasa gate din ya bude ya shige yabar gadanga a wajen Wanda baima San yana binsa bah.


Gadanga ne ya tambayar miss jamila  kamar yasan gidan? Tace ya shiga dai ya duba kowayye a gidan.lekawa yayi cikin gidan yaga wasu kartin karnuka sai haushi suke an sake su kawai a tsakar gidan,da alama sune masu gadin😅


Cikin few minutes gadanga ya zagaya ta bayan gidan ya haura katangar duk da cewar itama tsayinta ya isah amma daya taho da gudu gadanga tashi daya ya hau kan   katangar tare da yin wasu yan dabarunsa akan katangar duk da tsaron itama katangar take dashi,amma ko kwarzane babu abinda ya sameshi.


Miss jamila ce take ce masa wannan gidan kowa na wayye yayin da take kara daidaita medicated glass dinta dake fuskarta,hacker nima yanxu na shigo gidan ai😏 cewar gadanga ya fada a fusace cos daman idan da hali sun saba hakan.


Cikin gidan gadanga ya shiga ta kitchen, wata kyakkyawar mata ya gani a wheel chair ga koma komai na kitchen din dai.dai da matar da take  wheel chair ,babban kitchen ne Wanda aka tsara shi da kayan zamani Wanda koda  a foreign country sai Wanda ya isah yake dashi.A alama matar abinci take yi koma daga jin 

kamshin abincin kwararriya ce wajen yin girki.


Gadanga kallon sani yake mata kamar harda ita a pic din da alhaji usman ya basa a matsayin abokanan iyayensa,Bai karasa tunaninsa ba yaga mutumin daya fito a mota yazo ya rike hannunta?in law mai kike dafa mana ne yana mai taba cake din take ajewa a dining area din kitchen.


Juyowa yayi yanda gadanga yana iya kallon fuskar mutumin miss jamila da take shan ruwa tuni ta zubar da ruwan tare da cewa wannan bah *journalist* *idress abubakar* *Muhammad* bane ta fada sounded very surprise? Kafin gadanga ya bata amsa sunga abinda yasa gadanga saboda tsananin mamaki Neman fitowa daga inda ya buya saida hacker tayi masa magana ba kowa bane face *alhaji haruna abubakar Muhammad*.


Gadanga ne yyi saurin capturing din pictures nasu ta telescope glass dinsa tare da

 turawa hacker.


Alhaji haruna yaga ya rumgume matar nan tare da manna mata kiss ita koma ta rike hannunsa my lady ya gida ya fada cikin tsantsar kulawa daga gani son da yake yiwa matar ba karamin so bane, matar ce ta fada bayan kaki dawowa da wury koma kasan cewar yau birthday din *bintuna* ne. Am sorry miss harun tare da rike kunnuwansa  ya fada yana langwabe fuska cike da tausayi alamar ta tausayi dungure fuskarsa tayi tace my man nidai yanxu kayi sauri kaje ka watsa ruwa ka fito sai mu yanka cake din,ko so kake inzo in taya ka? Saurin rike hannunta yayi an hutar da gimbiya kiyi aikinki kawai kafin na fito na taya ki koh? "Aah an hutar dakai my guy kawai kai ake kira jira, kayi sauri nidai" ta fada a shagwabe an gama ranki ya Dade alhaji haruna ya fada tare da shigewa bed room dinsa cikin sauri.



Duk wannan abun da suke Idress yana wajen Wanda shi ko a jikinsa cos already sun saba da hakan.



Journalist Idress ne yake decorating din dining table din yana tambayar in law cewar da yanxu bintu tana nanzatayi shekara nawa eyyyyah idan koma bata Raye pah?

matar  daga gani abun har yanxu yana yi mata ciwo,yanxu ko a wanne hali take? ni ina zaune a gida mai kyau ina cin mai kyau insha mai kyau in kwanta a mai kyau!!! ta fada yanxu har tana xubar da hawaye Wanda bata San da zunbar su bah; kodai yanxu ma bintuna bata Raye ban sani bah...Aaaaaaaaaah ta fada da karfy Wanda saida kowa ya tsorata hatta miss jamila da take sharar yan guntayen hawayenta na tausayi saida ta tsorata.


Hakan bai zai taba faruwa da bintuna ba...bata kai ga karasawa ba sai ganin ta sukai ta kakkafewa idonuwanta ya kalli sama shima ya kafe ga yatsun hannunta Dana kafa sun kankame sai dirza bakinta take wani irin farin ruwa na fita,duk dauriya mutum yaga yadda wannan matar take saika zubda mata da hawaye.


Alhaji haruna ne ya fito a guje cikinta tashin hankali xuwa yayi ya kwace matar daga hannun journalist idrees daya kasa tabuka komai saboda tsananin rudewa; ba abinda yake sai  jijjigata yana fadin in law ki tashi kiyi hakuri bansan maganar zata bata miki rai haka bah in-law ki tashi! alhaji haruna yayi saurin dalla alarm  din d ake jikin wheel chair din na kiran doctor da nurse dinta  cikin sauri suka Shiga da ita treament room tare da fara aiki.


Alhaji haruna ne yake ta wankawa idress mari ba tare daya sani ba;mai yasa ka fada mata wannan maganar alhalin kasan yadda lapiyarta take?mai yasa kai min hka idress? mai yasa??? daga gani ya fita a hayyacinsa koma zai iya komai Indai baa tsayar dashi.


Journalist idress ne ya janye hannun alhaji haruna yaja da karfi suka wuce zuwa garden din gidan; tsayar dashi idress yayi cikin wata murya wacca har tafy ta alhaji haruna yana mai cewa wayye sanadin shigarta wannan halin inba kaiba?mai yasa ka raba tsakanin uwa da yayansu a lokacin da suke tsakiyar son juna?? Mai yasa ka raba tsakanin ammintattun abokai??? Mai yasa ya fada cikin tsananin fusata Wanda sai da kowa na gidan yaji,gadanga ma da tunda yaga fitowarshi ya biyosu a labe ba tare da sun sani ba saida abun ya daure masa kai.


Kana da wani dalili daya wuce na tsantsar son kai irin naka ko koma zaka cemin wannan shine dai.dai abinda kayi.alhaji haruna ne abun mamaki duk wannan fusatar tashi sai shi ya dawo yana magana cikin sanyin rai tare dasa hannunsa a kafadar idress kmar ba shibah, idress mai yasa har yanxu kaki ka fahimceni mai yasa kake min  mummunan zato akan abun da kasan bazan taba aikatawa ba kodan savoda soyayyata da *hafsa*? wani irin juyi idress yayi tare da gefar da hannun alhaji haruna gefe, karya kake komai zaka fada bazan yarda da kai ba mayaudari, maci amana, azzalumi....


Wani Marin alhaji haruna ya sake kaima idress cos kwakwalwarsa ba zata iya daukar wannan xancen bah,ni ka Mara saboda na fadi gaskiya saurin karasuwa alhaji haruna yayi yana cewa dan uwa mai zan fada mka ka fahimci...bai karasa ba idress ya daga masa hannu tare da yin part dinsa a fusace.  



Eyyyyyyyah miss harun 😟

[6/17, 10:57 PM] ‪+234 706 618 5922‬: 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖


 💞💞 *zahra tawa ce* 💞💞

 

Fatima Abdullahi Ibrahim( *Fatima zois*)

  

Dedicated to *Babbar yaya*(ramby *011*)


Page 4⃣








Gadanga Da  yaga komai; abun ne ya daure masa kai "toh mai wayannan yan uwa suke fada"?"koma meye dalilin wannan matar na samun wannan ciwon"???


Hacker ce ta katse masa tunani "gadanga ka fito mana tunda ka gama abinda kake". "OK hacker" gadanga ya fada tare da fara tafiya cikin sanda da labe labe.


Har xai wuce sai yaga wannan miss harun a kwance a wani daki daga gani Anyi an gama treating nata tunda gashi har bacci ta samu.


Samun kansa yayi da son shiga dakin,cikin sanda da da dabara ya bude dakin abinda ya gani shi ya kara jefa shi cikin mamaki still photos din da alhaji usman ya bashi ya sake a gani a bedside drawer din wajen da alama hoton an dade da yinsa,A gefe koma ga photo din hoton wata kyakkyawar yarinya yar kimanin shekara hudu an dauketa tana dariya  wanda tayi kyau sosai,still wani pic ya sake gani a wajen wadda aka dauka da miss harun da wani daya daga cikin abokanan babansa da koma yarinyar ga wasu yara maza a cikin su suna dariya suma daya dan kimanin shekara goma sha biyar dayan koma dan shekara Tara,karamin yaron sun lankaya hannunsu a kafadar juna shida yarinyar.


Cikin sauri yayi capturing din pic din  tare da turawa miss jamila,motsin matar ya gani alamar kenan zata tashi! Sauri capturing dinta itama yayiaa tare da ficewa daga dakin wanda ba Don ya kware a sanaar tasa ba da sai ha saura kadan alhaji haruna ya ganshi Wanda a lokacin daa hankalinsa yake zaiga alamar giftawar mutum amma ina! Hankalinsa yana ga hafsat.ficewa yayi daga cikin gidan kamar yadda ya shigo.



💖💖💖

Journist idrees abubakar haruna shahararran dan jarida ne yanda idan akace mah kasansa ake maka kallon mai saa, shahararre ne wanda ya shahara akan aikinsa yayi suna cikin kasarsa harma da wasu kasar.journalist idress kani ga alhaji haruna wanda a yanxu haka yake Neman takarar shugaban kasa,yan uwa ne masu kaunar juna fiye da tunanin mai karatu amma tunda wata kaddara ta gifta a tsakanin su wacca ba kowa bace sai hafsat matar alhaji harun,A kullum suke cikin samun sabani,Amma duk da haka babu abinda ya ragu daga kaunar junansu.


Hafsat mata ce ga alhaji harun wanda suke tare Tun lokacin kuruciya kawo yanxu da mijinta ya rasu diyarta koma ta bata shekera 19 dasuka wuce amma ta kasa mantawa da diyar tata sanadin mutuwar mijin nata ne da diyarta ta kamo da wannan ciwon wanda duk sanda ta tuno irin kyakkyawar rayuwar da suka yi ita da mijinta da diyarta sai ciwon ya tashi har saida ciwon ya kaita ga gurguncewa.


Duk shekara ranar birthday din bintu sai miss harun tayi celebrating birthday din bintu duk da Cesar bata da tabbacin tana Raye amma ita tana ji a jikinta diyarta tana Raye koma zata dawo gareta komai dadewa bata fitar da rai ba.


Duk sanda aka ce mata ta sani ko bintu tana Raye ko bata nan gaskiya ranar babu wanda xai fuskanci farinciki a gidan nan.


Alhaji harun babu abinda yake  so a duniya sama da hafsat wanda xai iya yin komai akan farin cikinta kawai ballantana ita kanta,da ka bata mata rai gwanda ka bata masa duk abinda take so shi yake so duk abinda yaga bata so koma har ta nuna kiyayyarta a fili akan abun har abada ya barshi in fact karshe saiya dawo ya tsani abun.


Babban abinda yake hada idress da alhaji haruna fada akan hafsat shi idress yana ganin duk shine ya jawa hafsat shiga wannan halin shima alhaji haruna yana cewa bashi bane koma sunki tsayawa su fahimci juna akan abun.


💞💞💞

Yau Tun da sassafe zahra ta shirya zata fita wajen aiki cos tace yau da wury zata je saboda report din da zata dakko.


Kamar kullum yauma doguwar Riga ce a jikinta da wannan katuwar jakar saika ce wacca wani abun kirki ne a ciki,tana sakkowa daga kan step din gidan zuwa *zahra tawa ce bay*   cos yau a nan zasuyi breakfast nasu,Wanda yayi dai dai da shigowar gadanga amma yau three quarter ne a jikinsa sai bodysuit mai hula, yau yasa gemu a fuskarsa Wanda baka iya ganeshi ba koma yau telescope glass dinshi maimakon baki sai yasa fari still da Bluetooth a kunnensa Wanda idan ka gani zaka iya tsammanin ko wani abun yasa a kunnen nasa.


Reception yaje Wanda yau abba ne dasu Abdul suke serving mutane cos daman duk weekend haka suke ,zuwansa wajen yayi dai dai da karasuwar zahra ta durkusa har kasa ta gaida momma sai yaya abdul itama affan ya gaidata.


Karasowa tayi wajen Abba cos gaisuwarsa ta dabance saida ta durkusa har kasa ta gaida shi sannan ta tashi ya kamo hannunta yana tambayar "little how was ur night"? So" boring" cewar zahra Abba ne yayi saurin tambayarta "why?" "Abba har ka manta jiya na hadu da mai bakin kaya!jiya na kasa bacci gani nake kamar xai sake biyoni mugu kawai" ta fada ta a fusace.


Gadanga ne yake ganin kodai ta ganeshi cos gani yake  kamar yanxu dashi take😆,maganar yaya abdul yaji yana cewa "kaga kyakkyawar yarinya ko harka manta abinda kake son order😏" gadanga ne ya dawo daga duniyar tunani tare da bashi order din anything liquid nd soft  da samun sit ya zauna Wanda yanxu magana yake da miss jamila,Amma babu wanda yaje ji still yana capturing photos din family nata ta telescope glass ba tare da sun sani ba.


Coffee aka fara kawo masa Wanda ya gama haduwa,jin zahra yayi tana fadawa abbanta yasa mata wannan irritating song saboda refreshment akan wannan mai bakin kayan,Abba ne ya harare take babu wani irritating song a nan tare da kokarin  kunnawa cikin sauri momma da affan suka fara rokon abba da kar ya kunna amma inaaah har Abba ya kunna.


Wata wakar da ce  ta "musa dan kwAiro" ana sawa daga farkonta ba gadanga ba hatta miss jamila da take kallon komai itama tana sha coffee saida ta kware,gadanga kam yasa coffee kenan yaji waka mai tada hankali tuni wani tari yazo masa Wanda da kyar ya karasa shanye coffee din bakinsa,Abdul ya hango Wanda takaici ya gama cikashi kawai ya dauki cups biyu ya rufe kunnensa sai faman kifkifta ido yake kamar Wanda yayi karya,idonsa ne yakai kan affan daya rungume hannunsa a kirji ga girar sama da ta kasa daya hade daga gani yafy kowa jin haushin wakar ga itama momma wacca  take binsu da ido cos ba yanda ta iya.


Zahra ce bayan wannan waka mai fada hankali maimakon ta kwantar da hankali cewar gadanga sai rawa take shima Abba yana bin wakar,saida sukayi mai isarsu tukunna zahra tace "Abba yau pah sauri nake cos oga isah yace inje in dakko report akan shirin election" tare da shan tea din da Abba yayi mata cikin sauri cos yau zahra tana shirin burge oga isah.


Abba ne yace zahra ba zaki huta bah kodan saboda mai bakin kayan nan??? Aah Abba Karka damu insha Allah zan kula ta fada tare da blowing family nata kiss ta tafy da sauri zata wuce abba yace "dakin tsaya Abdul ya kaiki mna kafin  ya karasa tuni zahra ta gudu cos ta tsani ace wani ne xai kaita wajen aiki tafy son ta tafy ita kadai ko da affan idan ya samu tym. Tana fita gadanga yabi bayanta ko takan order din bai yi ba.


Direct venue din da zaai taron ta tafy,Tunda daga nesa take hango reporters sun cika wajen da alama an Rigata,wasu abokan aikinta ta gani suna tsaye a wajen ganinta yasa suka karasu kusa da ita suna dariyar mugunta:

"Lazy sai yauzu kika zo" ya fada cikin shakiyanci da rashin mutunci


"Kai malami yau pah tazo da wury vaka gani ba har sammako ta duka", cewar wata daga cikin abokanan aikinta 


"Oh Ashe pah wannan ita ce take shirin daukaka diamondTV,Toh da wanne labaran zaki daukaka mna labaran bacci kona cartoon Kodai na cin abinci"suka fada suna kwashewa da wata irin dariya Wanda da ayi maka irin wannan dariya gwanda a wanka maka mari zai fiye maka sauka


Zahra kawai binsu tayi da harara tare da karawa gaba,Gadanga da yake kallonta ba karamin bashi tausayi tayi cos yanda fuskarta ya nuna bata ji dadi bah.


Tafiya take cikin sanyi jiki Wanda duk inda tayi gadanga yana binta har suka zo parking space saurin boya tayi sakamakon abinda ta hango, inda taga wata kyakkyawar yarinya a cikin mota ga wani a tare da ita sai fada yake mata yana gundure mata kai ga bodyguard dinsa nan a tsaye jikin motar sunfy su goma,dan bude kopa aka yi alamar fitowa zaayi murya mutumin taji yana sake dungurewa yarinyar kai cikin fada da masifa hade da tsantsar wulakanci "uban mai nayi miki kk kuka"ya fada da karfi wannan karon harda duka cikin rawar murya yarinya tace "babu komai" mutumin ne yace "ki gyara fuskarki yanxu yanxu koma kinji na fada wani yaji xancen nan har iyayenki baxan barsu ba  sannan in kashe ki na kashe banxa kiyi mutuwar wulakanci" kina jina ya tare da daga murya.


Zahra dake labe da taga wulakancin yayi yawa bata San sanda ta fito bah daga mabuyarta tana cewa "ka rabu da ita!!!" "Idan koma ban rabu da ita ba pah ? kedin mah yanxu zaki koma irin tata rayuwar"ya fada yana yin wata irin dariya mugunta suma bodyguard nashi suka tayashi,"Ku kamo min ita yanxun nan daga gani zatayi kudi"


Zahra ce ta firgita sosai da taji ance a kamota gudu ta fara tana Neman hanyar fita amma duk sun tare hanyar fita gashi koma sai kanta suke,Gudu take tare da ihun Neman taimako amma babu alamar mutane a wajen gashi harsuna daf da kamata.


Gudun data Shane yasa bata sani ba ta fadi kasa,cikin saurin bodyguards din suka rufu akanta suna Neman kamata.


Zahra har ta cire tsammanin akan abinda sukai mata  cos harta rufe ido tana jiran taji wanne mataki zaa dauka,jin shirin yayi yawa ne yasata dago da kanta wa zata gani *gadanga* ne yake dukansu kamar Allah ya aikoshi.


Zahra ce ta mari kanta don ta tabbatar ba mafarki take ba tare da rufe ido ta bude tasan da gaske take ba mafarki ba,still mai bakin kaya ne dai ta sake  gani,wata murya taji Wanda bata taba jin daddadar murya irinta ba yana cewa "zahra ki tashi Ku fita daga nan",ai zahra ji tayi bata taba jin Wanda ya iya fadar sunanta ba irins,cikin sauri tashi suka fita daga wajen tare da wannan yarinyar.


What amazing🤥a ina ya sanni? har yasan suna na?? Meye dalilinsa na taimakona??? Ya akai yasan ina bukatar taimako????

[6/17, 10:59 PM] ‪+234 706 618 5922‬: 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖


 💞💞 *zahra tawa ce* 💞💞


Fatima Abdullahi Ibrahim  ( *Fatima zois*)


Dedicated to *Babbar yaya* (ramby *011*)


Page5⃣







Zahra CE ta samu kujerar dake gefen hanya still tana tunanin gadanga tare da tunanin abinda ya faru.


Tunaninta ne ya katse dai dai lokacin da taji kuka a kujerar da take zaune.


juyowa tayi cikin sauri cos ita harta manta ma Ashe ba ita kadai bace tana tare da wannan yarinyar Wanda mutumin nan yake cin mutunci.


Zahra CE tayi saurin matsuwa tare da tambayar yariya"sis lapia kike kuka? Please koni na bata miki rai?"


Ita kam yarinyar kamar kara zigata ake.


Zahra CE a hankali ta matsu kusa da yarinyar a hankali tare da rungumeta a hankali tana dan bubbuga bayanta "calm down sis".


Sun dade a haka tukunna zahra ta saki yarinyar tare da dauko bowl din ruwa ta bata,sosai yarinyar nan tasha tare da sauke ajiyar zuciya akai akai.



Saida zahra taga yarinyar ta samu kwanciyar hankali tukunna ta fara tambayarta mai ya faru da ita???


Kara fashewa tayi da kuka zahra kowa sai aikin lallashi take,Saida yarinyar ta gama shan kukanta zahra na lallashinta tukunna ta fara bata lavarin rayuwarta:


"Ni sunana aisha garba,mahaifina ya mutu sakamakon hadarin mota da suka yi akan hanyarsu ta dawowa daga Lagos na Neman kudi.


Muna zaune a kyauyen buji dake jahar jigawa mun kasance Fulani nine Wanda duk fadin garin babu Wanda yakai mahaifina kula da iyali komai ya samu innata dani Aisha wacca naci sunan mahaifiyarsa,iyayensa gaba daya sun rasu sai a wajen matan uba ya zauna yasha wuya a wajen yan uwansa na wajen uba har Allah yasa ya girma ya mallaki hankalinsa yayi aure da mahaifiyata da yake itama ba wani gata gareta ba.


Kasancewarmu a gidan gadon da mahaifin babana ya mutu ya bari wannan CE tasa dole saidai mu zauna tare da yan uwan mahaifina Wanda suke yan ubah a gareshi.


Mutuwar mahaifina ita ta kawo mana sauyin rayuwa wacca har ta kawoni ga shiga wannan halin.


Mun kasance bamu da cin na yau bare na gobe abinci idan mun samu na safe bamu samun na dare saidai yan kame kame.hakan koma baisa yan uwan mahaifina sun taimake mana ba saima kara azabtar damu da suke yi saboda duk girman gidan da yawan gida ni nike musu wanke wanke,yin kara domin girki, diban ruwa,shara wani sain harda dafa abinci,Wanda ba hakan yana nufin bassu da yara ba, suna da yara harda Wanda suka fini,babu wacca keyin komai cikinsu sai yawon gantali da talle.


Ana cikin haka saiga wasu hajiyoyin birni sunzo Neman aiki garinmu, Wanda bamu sani ba Ashe maza ne suka yi shigar mata Wanda baka isa ka gane haka.


Ba wani sabon Abu bane a garinmu saboda daman ana zuwa diban masu aiki a garin saboda haka yan uwan babana suka hadoni mu harda yaransu tare da cewa dole sai an tafy dani xuwa ga aiki.



mahaifiyata tace ita ta yarda komai talauci ta zauna dani amma babu inda zata bari a tafy dani saboda bata San hannun wa zan fada bah.


Yan uwan mahaifina na suka nuna iko a kaina ta hanyar tirsasamin na dole saina bisu..."


Dai dai nan wajen Aisha ta fashe da wani kuka mai ban abun tausayi gani take kamar a lokacin abun ya faru ,hatta zahra saida ta zubar mata da wata yar kwalla.


Saida tayi kuka mai isarta zahra na bata baki hakuri sannan  tayi shiru ta cigaba da bata lavari


"Haka aka Tisa ni dani da sauran yan garinmu suna ta murna kamar Wanda akai musu wata babbar kyauta,sabanin ni da nike ta kuka,gani nike kamar kallon karshe nikewa mahaifiyata. 


 Haka muke ta tafiya zuwa birni Wanda ko sunan garin bamu sani ba har muka iso wani gari Wanda bansan ko ina bane amma daga ganin garin babban gari ne aka kaimu zuwa wani gida Wanda anan muka tarar da wasu mata wayanda zasuyi dai.dai da shekarunmu kowacce tana harkar gabanta.


Saida muka shigo gidan anan wayannan hajiyoyin da suka shigo damu muka gane maza ne ba mata ba.


Nan muka gane abinda suke nufi damu,ba niba hatta Wanda muka zo dasu saida suka yi kuka har muka gaji kowa ya fawwalawa allah.



A kullum sai an kawo wata mata Mara mutunci tazo ta koyar damu salon rashin mutunci da iskanci da shigar banza da duk hanya ta koyar da karuwanci,Wanda wasu a cikinmu har dibansu ake zuwa kasashen ketare,Tun wasu basu waye ba basu so har suka hakura suka koma hanyar banza.


A kullum  zamuyi shigar banza ta nuna tsaraici a  kawo manyan mutane su ganmu ka zabi wacca tayi musu kaje kayi abinda kaga dama da ita.


Duk wannan abun da ake ban watsar da mutuncina ba saboda a kullum ina tuna nasihar da innata take min na ruke mutuncina.


Abun mamaki duk sanda zaa zo duba yammatan  sai an zaba dani kamar hadin baki,nikowa duk wanda ya dauke ni ranar saidai yayi kwanan asibiti,in dawo gidan a dake ni hakan baisa na daina bah.



Alhaji bala shine shugaban masu yin wannan taasa Wanda kowa yasanshi yana da mugun kudi amma babu Wanda zaice ga inda yake samun kudin,amma koma miye an yarda da cewar duk sanaar da alhaji bala yake tana kawo masa kudi.


Da aka ga abun nawa babu kara gaba yake koma ina rage musu kasuwa duk da azabtar dani da ake sai aka hadani da alhaji bala,Wanda ya  nuna min a fili zai kaini ga mahaifiyata tunda ita nike so koma zai daina wannan harkar ya maida kowacce gaban iyayenta.



Na gama yarda da Albanians bala akan abinda ya fada koma na yarda dashi akan bazai cuceni ba.Ashe shine mugun macuci shine wanda ya fara rabani da mutunci ta hanyar samun maganin bacci a drinks din da nike sha.


Nayi kuka nayi danasani nayi allah ya isa nayi takaici wanda saida shima Kansa alhaji bala ya gane kuransa a lokacin cos fasa masa kai da kwalba na koma ce saina Sanar da hukuma abinda yayi min abi min hakkina.



A lokacin Tun alhaji bala yana jin tsoron tuna masa asiri da zanyi har yaxo ya daina ta hanyar tsoratar dani da cewa in na fadawa wani yaji sai yaje har garinmu ya kashe mahaifiyata ni koma yace daman ni karuwa ce ba wani raping dina da yayi.


Da wannan dama ya samu yanda yake so  akaina koma ya amfani dani yanda yaga dama tare da dumbin wulakanci da tuzarci da yake nuna min,gashi a kullum ina tare dashi idan ba shiba koma bodyguard dinsa ko ina zanje wani sain bani sanin sun biyoni,saidai inji ya bugo min waya yana kara razanar dani akan idan na fadawa wani abinda nike ciki.


Wannan shine tarihin rayuwata,ta karasa tana hawayen bakin ciki kamar yanzu abun yake faruwa.


Zahra tayi matukar tausayawa Aisha itama zahra ta fadawa Aisha takaitaccen tarihinta.



zahra ce ta bukaci ko zata iya  distributing wannan labarin,aisha tace ta yarda komai zai faru ya koba komai tayi taimakowa alumma koda kowa mai zai faru.


Zahra ce ta roki aisha ko zata bita xuwa gidansu amma aisha taki,Aisha ce tace ni ynxu nan da kike ganina so Nike inje ga mahaifiyata inga yanda take da lafiyarta.


Babu yanda zahra batai da Aisha ba su tafy gidansu amma taki ta sanar da ita son xuwa ganin mahaifiyatarta ne yasa,daga karshe suka yi exchanging contact. 


Duk wannan abun dake faruwa gadanga ya dauki komai.


💞💞💞

Zahra ce ta karasa wajen aikinta inda ta Tarar da abokan aikinta har sun dawo.


Oga isah ne yauma yake tambayar zahra mai ya tsayar da ita har zuwa yanzu bata dawo bah?



Gani tayi kowa ya zubo mata ido suna son jin abinda zata fada.



Zahra ce tacewa oga isah "I have something special nd also interested".


Tunda oga isah yake da zahra bata taba  yi masa magana in a serious manner irin yau ba saboda haka yace su shiga office wanda ba haka abokan aikin NATA suka so saboda sonsu a cimata mutunci yau.


Zahra ce ta sanar da oga isah komai kamar yanda aisha  ta sanar da ita tana son a sanar da duniya abinda yake faruwa.


Oga isah hankalinsa idan yayi dubu a tashe yake ya kasa ko zama sai zagaye yake a cikin office din cikin razana da matukar tashin hankali.


Zuwa kusa da zahra yayi yana cewa zahra in fada miki gaskiya tunda kika ji labarin nan da kinsan hadarinsa da wlhy ko hanyar da Aisha tayi ba zaki biba,amma yanxu ma baki makara ba nayi miki alkawarin babu wanda zai San wannan labarin kawai a rufeshi anan.


Cikin sauri zahra tace amma oga wannan pah aikinmu ne taya zamu dinga barin mutane suna halaka alhalin nuna da yanda zamuyi mu ceci rayuwarsu.


Oga ne yace "kinsan hadarin dake bibiyarki kowa zahra?bake ba hatta family ki da koma mu da muke aiki tare bamu tsira ba!!! duk da cewar labarin bai fito har yanxu ki tsaya kiyi tunani" oga isah ya fada tare da ficewa daga office din,ita kowa zahra ta daura aniyar taimakawa aisha sai inda karfinta ya kare.


💖💖💖

Gadanga ne zaune a katafaran gidansa yana aikin nasa wato communicating da miss jamila.


Miss jamila ce tace gadanga nasan yanxu dole saidai ka dinga bibiyar rayuwar zahra cos yanxu tana cikin hadari harma da wanda suke tare da ita.


Yanxu maye mafita hacker ya fada cikin damuwa.


Hacker ce tace dole saidai yaje ya nemi aiki a inda zahra take aiki domin kula da ita tare da bata tsaro.



Kamar ya kenan hecker!? 


Zaka je ka nemi aiki a wajen,but you are to be under zahra❗


Haba hacker bayan duk bibiyarta da nike sai na wani je inda take salon ta raina ni,yarinya karama daita in tsaya ina bata lokacina akan wannan bansan aikin,wlhy zan zan iya kin karasa wannan aiki.



Oh gosh! "nasan abinda kike nufy,u mean I am to act as her subordinate shey???"


Miss jamila ce tace :"Hava gadanga it's just an act not d reality so never mind about it,

Ba wani dadewa zaka yi ba wuyarta komai ya lafa kaji gadanga" 


Babu yanda gadanga ya iya yace ya amince amma babu inda zaije wai akan Neman wani aiki iyakacina zuwa wajen aiki ya fada a fusace tare da disconnecting din komai. 


Miss jamila ta CE kayi mai wuyar ai gadanga ta fada tare da tuntsirewa da dariya.


Babu wani bata lokaci hacker ta nemawa aliyu aiki ta hanyar oga isah,duk da cewar hacker kudi ta biya akan komai iyakaci a bawa gadanga salary dinshi shima don kar yan wajen su gane abinda ake nufy.


Komai ya kammala don game da fara aikin gadanga under d authority of mrs.zahra😆 ranar Thursday zai fara aiki ne kawai...

[6/17, 11:02 PM] ‪+234 706 618 5922‬:


💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖


Post a Comment

0 Comments