SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
Page 17
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.
*Ali Sufi*
"We don't just entertain and educate we also touch the heart of readers..... Gsky ni die hard fan dinkune PML writers. Long live Hausa novels,long live readers and long live PML".
*ALI SUFI*
PURE MOMENT
_tana matuk'ar godiya_
.
.
.
Fateema suna zaune da Sakeena Maman tana hura wuta sukaji tyayuwar mota, Sakeena ta ce "yau kuma Anwar ya tuna dake kenan yazo".
Fateema ta taɓe baki ta ce "idan yak'irani yana wani maganar kamar baisan ya sakeni ba, harda bani umurnin kada naje kasuwa, kada na tsaya da wani, kinji fa wani kulle kamar zanyi ta zama masa babu aure ne".
Sakina mamaki ya kamata ta ce "kinsan yana sonki, shima babu yanda ya iyane, ɗaukomun takaddarma naga saki nawa ne".
Fateema taja tsuka "Don Allah manta da takaddarnan ko saki nawane ai anriga da anyi, ni so nakema na canza layi yadaina k'irana, kullum famamun ciwon sonshi yakeyi".
Maman ta tanajin su, ajiyar zuciya tayi ta ce "kullum bakuda taɗi sai Anwar, zanga ranar da zaki cire shi aranki....
Bata k'arasa ba Baba me yalo ya shigo, sai washe baki yakeyi.
"yau akwai alamar nasara a kasuwa, sai farinciki kakeyi".
Ya ce "sosai ma, nan ya kwashe yanda sukayi da Matannan ya faɗa mata, itama washe baki tayi tana adduar Allah yasa k'arshen talauci ne yazo, Fateema kam kuka tasa tana cewa babu inda zataje, itama Sakeena kuka takeyi kada atafi mata da k'awa, masifa ya shiga surfa musu, yana ganin zai huta yara zasu masa buk'ulu, dole ma ta bishi su tafi ko kuma ya ɗaura mata aure yau yayi tafiyar sa.
Cikin k'ank'anin lokaci yayun ta suka zo, suma sunyi murna, su hakanma yafi musu tunda basuda 'yan uwa agarin sungaji da ganin mahaifin su yana saida yalo, su Ummi kam tunda suka ajiye Baba me yalo suka koma masauk'insu akan da asuba zasu zo ɗaukarsu kafinnan sun gama shiri, dak'yar aka shawo kan Fateema ta amince sai da taga da gaske duka zata sha.
.
.
Hajiya Jamila zaune ta rabka tagumi, nadama ne ya cika ta sosai, tunanin ta ɗaya bai wuce ta ina zata fara ba, gashi tunda Alhaji yaji maganar ya daina kula ta, dabara ne ya faɗo mata, ta ɗauko wayar ta tafara k'iran Anwar, yana kwance sai juyi yakeyi, kewar matan sa duk ya addabe shi, musamman Fateema dayake jin wani bugun zuciya idan ya tuna ta, ga tsananin sha'awar datake takura mishi, duk yayi wani zuro a kwana biyu.
Jin wayar shi ta fara ruri ya tashi a kasalan ce, ganin Hajiya yasa shi watssakewa yana tunanin ko lafiya.
"Hello Anwar kana ji na"?
"inajin ki Hajiya".
"kayi hanzari ka dawo da matar ka".
Anwar me zaiyi idan ba dariya ba "yaufa kwanan ta biyu da tafiya kuma sai tayi kwana arba'in zata....
Katse shi tayi da sauri "Ubanka na ce, ni zaka raina ko Anwar, kasan wacce nake nufi".
K'unshe dariyar yayi yace "Gobe insha Allah zanje, kina tsoron Dady....
D'uf ta kashe wayar tana zage2, yaronnan ya raina ni wallahi.
shikam dariya yayi ya ce uwata sai Dady, yayimun dabara.
.
.
Washe gari da safe bayan yaje yaga Baby Aisha ya nufi garin Jos, hankalin shi a kwance.
yana isa ya tarar da gidan gark'ame da kwaɗo, can ya hango yaro ya k'ira shi, tun kafin ya tambaye shi ya ce "mutanen gidan sunyi tafiya jiya, amma inaga bazasu juma ba naga basu ɗauki kayansu ba".
Anwar yayi jum sannan ya masa godiya yabashi 1k.
Zuciyar shi fal tunani ya koma gida, gidan Hajiya ya wuce kai tsaye, tana ganin shi ta hau tambayar shi ya ɗauko ta, girgiza mata kai kawai yayi yaje ya kwanta abunshi.
.
.
Tafiya me tsayi sukayi kafin suka isa garin Meduguri, isar dare sukayi duk sun gaji musamman su Baba me yalo da ba'a saba tafiya me nisa ba, duk da darene haka masu aiki suka shiga aikin kawo musu abinci, wani part aka kaisu me ɗauke da ɗakuna biyu, sai kitchen da toilet a gefe, wankan gajiya Fateema tayi, ta cika cikin ta da abinci sannan ta hau Sallah, tana idar wa, ta ɗauko jakarta zata ɗauki wayar ta, waya yace ɗaukeni inda kika ajiyeni, ba irin neman da batayi ba amma babu, haka ta hak'ura ta kwanta tabari akan yana wajen su Baba me Yalo.
Ƴ
.
.
Washe gari da safe Ummi ta aika aka k'ira mishi Baba me Yalo, yauma matashiyar nanne ajikin ta, sai zuba mata surutu takeyi, Ummi bata mishi magana ba har saida ta lura ta gama surutun, rabin surutun ma k'anzon kuregene.
"kamar yadda muka rabaku da garin ku, ina fata zaka mana aiki cikin aminci, nidai banida wasu yara a gidannan, yaro na guda ɗaya ne kuma bashi da futuna, zaka rik'a yimana gadi muna biyanka 50k a wata, tunda ka taho da iyalan ka, zasu iya shigowa suna mana wankau sai ana biyan su, ko yaya ka gani".
russunawa yayi yamata godiya.
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
Page 18
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.
.
.
Maman Fateema sosai tayi murna, ita dai Fateema taɓe baki tayi ta ce "nidai wallahi babu aikin da zanyi".
"sai kiyi ta zama ai".
Inji maman ta, Baba me yalo kuwa cewa yayi "kiyi zamanki, dama ba nufina kiyi wani abuba, su suka buk'ata, tunda bakiso babu dole, amma da zaifi miki zaman kaɗaicinnan".
"Baba ni yanzu waya ta zaku bani"
Ya kama baki, "ni kuma me zanyi da waya Fatee, kidai duba cikin kayan naki".
Shiru Fateema tayi, don tasan babu irin duban da batayi ba, shikenan wayata ta ɓata kenan, ta faɗa a ranta.
.
.
Zaman gidan babu yabo babu fallasa, mahaifiyar ta tana shiga ta musu share2 harda wanki, da yake Mama akwai tsafta ga raha yasa har suka fara sabawa da Ummi, abu ɗayane yake damun ta, ta rasa wannan me cikin 'yarta ce ko kuma, kome tace tana so a gidan shi akeyi, ga wani girma da Ahmad yake bata duk k'ank'an tarta, shagwaɓa da iya shege babu wacce batayi, kuma taji Ummi ta ce ɗanta guda ɗayane, itadai bata tambaya ba
Satin su biyu a gidan Maman Fateema ta tashi bata jin daɗi, don haka da asuba tacewa Fateema taje tayi aikin kamar yadda ta saba, zunɓura baki tayi kafin tace "Nifa bansan kan gidan ba Mama, kuma ai bansan aikin da kikeyi ba".
Mama ta taɓe baki ta ce "gidan zaki share musu, sai ɗakunan su, sannan ki haɗa kayan da suka cire ki wanke su".
Fateema tayi tsaye tana kallon Mama.
"yanzu wai duk wannan aikin ke kaɗai kike yi, bansani ba da ina zuwa ina tayaki".
Dungure mata kai tayi ta ce "Ina nan akace kije kika k'i".
Tafiya tayi tana k'unkuni.
Dak'yar ta gane kan gidan sannan tahau gyarawa, saida yayi k'al sannan ta nufi ɗakin da taga Ummi ta nufa ranarda suka iso Garin, akan Sallaya ta samesu itada me cikinnan, Ummi ta ɗaga hanu tana addu'a "Allah ka gafarta wa mijina, Allah ka shiryi mijina, Allah kasa mijina ya shiga Aljannah, Allah kabaiwa mijina arziki na duniya da lahira me anfani.....
Duk abunda tace me cikinnan tana cewa Ameen, har suka shafa sannan Fateema ta russuna ta gaishe su, da fara'a suka amsa, Ummi tace "badai ciwon kan ya hanata zuwa ba"?
"Da sauk'i dai yanzu".
Fateema ta faɗa tana murmushi, Ummi ta dubi me cikinnan tace "Farida je ki haɗo mata wankin ɗakin ki".
Saida ta shagwaɓe fuska ta ce "wallahi ban iya tashi yanzu".
Ummi tayi murmushi ta ce "bari naje na dubo dakaina".
Itadai Fateema sake baki tayi ta kallon su, mik'ewa tayi ta gyara ɗakin sannan suka nuna mata ɗakin Ahmad akan idan 8:30 tayi kafin taje ta gyara saboda ba'a shiga sai ya futa.
"to".
Kawai tace taci gaba da aikin ta, k'arfe 8:30 tanayi ta nufi ɗakin Ahmad, ba damuwar komai tunda lokacin akace taje, ɗakin ta gyara duk da taga agyare yake kawai ɗan gyara wani wajen tayi, tana gamawa ta kwashe kayan da tabbatar su ya cire ta nufi toilet kai tsaye, wani mahaukacin k'ara ta saka ta fito a guje, bata gama maida numfashi ba taji an fizgo ta, ko ɗauraye jikin shi baiyi ba ya fito, sake wani k'aran tayi ganin mutum tsirara a gaban ta, ya wanke ta da mari, "ke mahaukaciyar inane, k'aramar 'yar iskace ke, tunda kin iya lek'a mutum yana wanka baki iya kallon shi ba, waye ya faɗa miki ana shigomun ɗaki".
Kuka ta rushe dashi da iya k'arfin ta, ya ware ido yana kallon ta yana mamakin to me yasa tashiga tasan yana wanka, cikata yayi ya koma wankan sa, aikuwa da gudu tabar ɗakin tana haki, ko wajen su Ummi bata nufa ba, ɗaki ta wuce ta kwanta, duk haushin Ahmad ya cikata, harda cemata k'aramar 'yar iska alhalin ahine ɗan iska da iya biyota haka, aikuwa ba inda zan sake zuwa.
.
.
Ruɗewar da tayi yayi masifar bashi dariya, tun yana wanka yake ta dariya har yafito ya gama shiri ya nufi wajen Ummi, har k'asa ya tsuguna ya gaishe ta, sannan ya juya wajen Farida, "Aunty ina kwana".
Ta ɗan shafo kanshi ta ce "bazan amsa ba sai nasan dalilin da yasa naga fara'a kwance a fuskar ka".
Murmushi yayi yace "Naga wata jerry taje gyaramun ɗaki, yau ina Maman tata"?
Farida tayi dariya ta ce "jerry fa kace, Fateema sunan ta, yau naga ka makara meyasa"?
Kafin ya bada amsa Ummi ta ce "kefa idan ba Ahmad kika gani ba sam baki warewa, yanzu ai sai kin makarar dashi zakiji daɗi"
.
.
.
.
.
.
.
.
.
Hajiya Jamila fa hankalin ta ya fara tashi, duk bayan kwana uku sai tasa Anwar ya tafi Jos amma har yau Fateema basu dawo ba, kullum Alhaji daɗa mata rashin mutunci yakeyi.
Anwar duk abun duniya ya isheshi ko yak'ira ta awaya har tagama ringn ba'a pickn, yanzu hankalin shi ya fara tashi, dama baka sanin kana son mutun sai ya maka nisa.
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
Page 19
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.
.
.
*Wayyyyyyo cikina*
*Ban taɓa dariya a novel irin wannan ba, SWEET SADNAF kina cin mutuncin Abdl ycn, hhhhhhhhhhhhhhhhhhh wallahi inason ku 'yan Pure moment, ta ko ina Novels ɗinsu dabanne*
🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣
.
.
.
.
.
Tana zaune a bakin gado a ɗakin da aka bata, tana baiwa Baby Aisha nono, ta zuba mata ido tanajin wani sanyi a ranta, Anwar yayi sallama ya shigo, idon shi yana kanta yana murmushi, itama murmushin tayi ta ce "Abban Aisha sai yanzu, nidai kwana biyunnan nakasa gane meke damun ka".
D'an murmusawa yayi lokacin da yake zama kusa da ita, yasa hanu ya shafa kan Baby Aisha, yace "Yaushe zaki dawo".
Binshi tayi da kallo ta ce "ko sati uku fa bamuyi ba".
Bakinshi yakai saman nonon, sauk'an numfashin bakinshi taji akai tayi saurin ɗago dakan shi, "me kakeyi haka Anwar"?
Susa kai yayi yana dariya ya wayince da cewa "inaso nafaɗa miki wata magana Maryam, naje garin su Fateema yafi a k'irga bana samun ta, kullum gidansu a rufe, wallahi hankalina ya fara tashi".
Da mamaki take kallon shi, ta ce "me kake zuwa yi mata, bacin ka saketa kuma kake wani hankalin ka ya fara tashi, to Allah yasa Aure tayi ma".
Ta karashe tana zunɓura baki.
Karɓan Baby Aisha yayi ganin tayi bacci, yakai ta wajen kwanciyar ta yana cewa "menene kike ɓata rai to, kuma adduan ki ba ameen ba".
Shima yafaɗa yana ɓata rai.
Shiru tayi batace komai ba, ya zauna ta bayan ta ya ɗaura kanshi a gefen wuyan ta, ya ce "fushi kike yi don naje wajen Fateema"?
Sai da ta harari iska ta ce "Ni munafunci ne bana so".
Ya zagaye hannayen shi akan k'irjin ta ya ce "Nine munafukin"?
ture shi ta fara yi, ya ɗan matsa nonon ya ce "menene kike tureni kuma, ko idan antafi wankan gidan ba'a komai ne".
a ranta tace yau rigima ta tashi kenan, tamaga k'ok'arin sa.
hannu tasa ta janye hannayen shi ta ce "meyasa kake zuwa wajen Fateema har yanzu"?
Dariya yayi ya ce "tau kishi ta motsa".
kai mishi duka tayi ya rik'e hannun ya ce "zan faɗa miki, lokacim da Hajiya ta matsa na saketa ai ban saketa ba, nayi hakane saboda hankalin ta ya kwanta, kafin Dady ya dawo nasan zaisa indawo da matata, to yanzu lokaci yayi ne, inaso ta dawo".
Shiru tayi batayi magana ba, ya ci gaba da cewa "yanzu hankalin Hajiya yafi na kowa tashi, har 'yar rama tayi".
Kallon shi tayi tana neman k'arin bayani, "Dad ya ce idan Fateema bata dawo ba zai sake ta".
Dariya Maryam tasa harda sunkuyawa, ganin ya ɗaure fuska ne yasa tayi shiru, ya ce "Hajiya ta kikewa dariya"?
Ta waro ido ta ce "ni na isa, kawai dariyar ne tazo, yanzu sai kusan nayi tunda abun hakane".
da dariyar ta k'arasa maganar, ya ce "musan nayi ma zakice, ko wayarta fa na k'ira bata ɗauka".
Wani sabon dariya Maryam ta saki ta ce "Da yanzu ni ce nake gida, Fateema tamun abunda bazan iya kishi da ita ba, Hajiya kuma ta so taga bana raye, saboda rabuwarmu yana nufin mutuwa ta, da zanbi ta zuciya ta, danayi adduar Allah yasa kada kaga Fateema har abada, idan kuma nayi haka ban kyauta wa Fateema ba, don haka zan taya ku binciken inda sukaje, ta shafo sajen shi ta ce "zan nemo maka Fateema insha Allah".
murmushi yayi ya ce "kiman ta da abunda Hajiya tayi, tayi nadama sosai, bana burin auren ta ya samu matsala Maryam kinsan uwata ce".
Saida ya jagwalgwala ta ya rage sha'awa kafin ya tafi.
Tagumi tayi tana tunanin ta ina zata fara, wannan wani damane da zan daɗa gyara shimfiɗa ta, tabbas idan nayi k'ok'ari Anwar zai sake ganin girmata da daraja ta.
wayar ta ta ɗauko ta k'ira numban Sakina, bugu biyu ta ɗauka.
"Hello Aunty Maryam ashe zaki tuna damu"?
"Ai kullum ina tunawa daku, ina mutumiyar ko na k'irata bata ɗagawa".
Sakeena tace "wallahi nima haka, tun tafiyar su Meduguri aka daina samun ta".
Cikin jinjinawa Maryam ta ce "Meduguri kuma? Me yakaita"?
"sun koma can da zama fiyeda sati biyu data wuce".
Maryam ta ce "ikon Allah, yanzu bawani numban da za'a sameta"?
"Gaskiya babu sai dai ki k'ira su Aunty Hadiza ko suna da wani numban da suka k'irasu".
sallama sukayi tare da mata godiya.
koda ta k'ira suma magana ɗayane babu wata hanyar da zasuyi magana, sai dai kafin su tafi Ummi ta bata address ɗin inda suke, nan Maryam ta buk'ata.
Anwar daya dawo da dare daɗa kwantar mai da hankali tayi ta ce dazaran tayi arba'in zata nemo masa Fateema, da yafara gardama kada tasa kanta a wahala ta nuna masa ita tayi niyya kuma ai kamar yiwa kaine.
.
.
.
.
Ahmad fa tun daga ranar tunanin Fateema ya hanashi sakat, sosai yaji yanason yarinyar, har Allah2 yakeyi gari ya waye
ta sake zuwa mishi gyara ɗaki.
Ita kam da tace bazata sake zuwaba, ganin Mama bata warkeba yasa ta koma, kamar jiya tare tasami su Ummi suna addua, saida suka shafa ta gaishe su, bayan ta gyara ko inane Ummi ta k'ira ta, "Yau me gidan zak dawo, ki zauna ki tayamu aiki".
Amsawa tayi da "to".
Farida ta ce "idan kin gyara wajen Ahmad sai kidawo".
Nanma "to".
ta ce.
Itakam wajensu ta koma tayi kwanciyar ta, ba abunda takeyi sai kewar Anwar, yanzu nasan Aunty ta haihu, ko me ta haifa oho.
Sai juyi takeyi ita kaɗai, sai k'arfe tara ta mik'e ta koma wajen su Ummi.
Ahmad yana gefen Ummi yana karyawa, Farida tana jikin Ummi, can nesa dasu ta zauna ta ce "Me za'ayi yanzu"?
Ahmad da tun shigowar ta yabita da kallo ya ce "me yahanaki gyaramun ɗaki"?
Bata kalleshi ba tace "nagyara".
Shima shiru yayi don yasan bata gyaraba, Farida ce tace "muje mufara".
Itadai binta tayi kawai, inda ta zage tana aiki Fateema bata ɗauka tana aiki haka ba, taga kullum tana mak'ale a jikin Ummi, ita kuwa Ummi ko wajen da suke aikin bata nufa ba, sun dafa abinci yayi kala goma, abunsha yafi kala biyar, abunda ba'a magana, basu gama ba sai wajen 5 na yamma, Sallah kawai suke tsayawa yi, saida suka jera komai Fareeda ta wuce ɗakinta, itama Fateema ta juya zata tafi Ummi ta ce "idan kinyi wanka kizo ki karɓa muku naku".
.
.
wanka tayi tashirya sannan ta jira akayi magriba tayi, Mama ta ce "yau wani irin aiki kuka sha haka"?
"Kedai mama bari kawai, kuma mu biyu mukayi, bansan me cikinnan tana aiki hakaba, gashi ta iya girki k'amshin duk yacikamun hanci, yanzuma zanje na karɓo".
Gyaɗa kai Mama tayi "to ko k'anwar matar gidanne"?
Fateema ta ce "Inaga k'anwar tace, bakiga yanda take dangarta ta ba".
mama tace "ni zanbaki labari wannan, yanzu dai tashi kije kada suga kink'i komawa".
Mayafin ta tajanyo ta tafi.
a bakin falon sukayi kusan cin karo da Ahmad, wani malalacin murmushi yayi ya ce "ni zaki raina wa hankali ko"?
Tsaki tayi ta ce "daga isowata har nayi laifi"?
ya ce "wani rainin hankalin zaki kuma yimun, cewa kikayi kin gyaramun ɗaki ɗazu".
Saida ta watsa mai harara ta ce "mezan sakeyi a ɗakin ka bacin ko inama wajen wankan kane, dama bani bace me aikin kajira ta warke ta koma bakin aikin ta".
kafin yayi magana sukaji hayaniya ya karaɗa gidan, murmushi Ahmad yayi ya ce "Boss ya iso".
"to matsamun na wuce".
b
"bazaki wuceba sai yafara cin karo da surkar sa".
Kallon rashin fahimta ta masa ta ce "zan koma kawai".
da sauri ya bata hanya ta wuce shi kuma ya nufi inda hayaniya ke tashi, yana isa Dad ɗinshi yana fitowa a mota, ma'aikatan gidanne cike awajen kowa yana murna, da gudu Ahmad ya faɗa jikin shi yana murna, shima Dad cikin farinciki ya daɗa rungumeshi.
.
.
wani irin kwalliya Ummi da Farida sukayi, Fareeda tayi masifar kyau ga wani k'amshin da yake tashi ajikin ta, itadai Fateema sake baki tayi aranta tana cewa "wannan kam akwai shiga uku, har ta fi matar gidan haɗuwa".
Tunanin ta ne ya tsaya cak lokacin da taga Dad ya shigo, cikin wani irin taku Fareeda ta k'arasa ta rungume shi ta saki kukan shagwaɓa, sai bubbuga bayan ta yakeyi yana rarrashin ta, wai tana kukan tayi missing ɗinshi, yana rungume da Fareeda ya mik'a wa Ummi hanu, k'arasawa tayi itama taɗan kwanto ta gefenshi fuskar ta cikeda murmushi.
ganin irin kallon da Fateema take musu ne yasa Ahmad Yayi sauri yaja hanun ta suka bar wajen.
.


0 Comments