SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
Page 20
Second to the last page
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hearts of readers_
*PML*
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.
.
*On ur Birthday, i would like to give u some words of wisdom smile while u still have teeth*
_many many happy returns of the day my *KHALEED*_
_Ana tare irin sosai ɗinnan_
.
.
.
.
.
Fateema kasa daure wa tayi ta ce "tsaya na tambaye ka, wannan Aunty Fareedan itama 'yar Ummi ce".
ya ce "a'a, Farida matar Dady
ce".
Da mamaki take kallon shi, "matar Dady fa kace Ahmad".
"eh haka nafaɗa, Farida tanada kirki sosai, lokacin da Dady ya aurota bakiga irin wahalan datasha a wajen Ummi ba, amma ta jure tayi hak'uri har suka zamto tamkar uwa da 'ya".
Ajiyan zuciya ta sauk'e, ta juya zata tafi yayi sauri yaja mayafin ta "Don Allah ki tsaya muyi magana, Dady bazai wuce sati ɗaya ba zai koma, tun ranar da naganki naji nasamu matar aure".
Gaban ta ne taji ya faɗi.
"zan faɗawa Dad nasamu mata, don Allah kada kice baki sona".
Shiru tayi tana nazari, can ta ɗago tace "Allah ya tabbatar da alkairi".
.
.
Abu kamar wasa Dady ya amince ya aure ta, wasa2 suka fara soyayya duk da ita hankalin ta yana kan Anwar, idan ta tuna wani abune kawai take k'ok'arin mantashi, ba wanda bai goyi bayan auren ba saboda Fateema tanada shiga tai ga hankali, sati biyu akasa biki, Ahmad murna kamar me, lokacin ta fara shirin zuwa Jos amma mahaifin ta yace shi zaije basai taje ba.
.
.
.
.
Ranar Talata Maryam anyi Arba'in, har wani shagalin biki akayi, Anwar ya zama tamkar ango yana murna zata koma gidan ta, tunda sassafe yaje ɗaukan ta, yasa mata rigima Mamy ta lallaɓa shi sai zuwa dare.
Ranar an gurji juna, Maryam sabuwa ta zame masa saboda irin gyaran da tasha, har tausaya mishi takeyi saboda baya gajiya ko kaɗan, mantawa da komai yayi yarungumi Matarsa da 'yarsa saboda yanzu ta gyara *SHIMFID'AR TA* sosai.
kwanan ta biyu da komawa ta shirya zataje Meduguri, da k'yar ya barta ta tafi, badon Mahaifiyar sa tana tsak'a me wuya a da ya hak'ura da Fatima tunda ta masa nisa.
Ranar alhamis ta nufi garin Meduguri, isar dare tayi Allah ya taimaketa batasha wahalar gane gidan ba saboda ba ɓoyayyen mutum bane, gida kam a cike ta sameshi da alama wani hidima akeyi, wajen Ummi aka kaita, bayan sungaisa take ce mata "tambaya nakeyi, Fateema wanda suka zo daga Jos".
Da fara'a Ummi ta ce "nanne gidan, kinji labarin bikin ko, wlh abunne yazo a k'urarren lokaci shiyasa bamu barta taje ta sanar muku da kanta".
Maryam tayi murmushi tace "Kingane Fateemar kuwa, itafa wannan matar aure ce".
Ummi tace "aiyo to gaskiya inaga banan gidan bane, wancan sunce mana bazawarace shekara ɗaya mijin ya saketa....
Maryam ta ce "Ba ita bace amma ko zan iya ganin wannan ɗin".
"mezai hana, muje nakaiki wajen ta".
a gajiye Maryam tabi bayan Ummi, wani ɗaki duka nufa, ta wajen babu kowa kamar ba'a cikin gidan yakeba, wani hayak'i ake turara mata me k'amshin gaske, da sauri Maryam taje ta lek'a fuskan ta, sake baki tayi tana ganin ikon Allah, wannan kam Fateema ce, to wani aure zatayi kuma bacin Anwar yace mata ba sakinta yayi ba, kodai itama bata sanibane.
jin Muryar Ummi ne yasa Fateema ɗagowa, duk hayak'in yacika ɗakin, ido huɗu sukayi da Maryam, da gudu ta rungume ta tana cewa "kece Aunty, waye ya kawo ki, ashe baki manta dani ba, ina Babyn mu, me kika haifa...
"wannan tambayo yi haka Fateema, yanzu dai a gajiye nake".
Ummi tayi saurin cewa "muje ciki tunda kinga itace, idan sungama zata zo ta nemeki".
D'akin da Fateema take kwana aka kaita, abincin da aka kawo mata ta dira akai, saida ta k'oshi tabaiwa Aysha nono sannan tayi wanka tayi sallah ta mik'e, mamaki ne fal aranta, A haka Fateema ta shigo ta sameta, ko gaisawa basuyi ba tace "Fateema bangane ba, wai auren waye za'ayine?".
Bata ɓoye ba ta faɗa mata.
"to nidai kaina ya kulle, yanzu haka zuwa nayi na tafi dake, Anwaar ya ce bai sakeki ba".
"k'arya yakeƴyi aunty, har tagadda ta ya bani".
"ɗauko takaddar mugani, kun kulle mun kai".
m
jakarta ta ɗauko ta zazzage, takaddar tananan inda ta ajiye shi, ko warewa batayi ba ta mik'awa Maryam, warware wa tayi ta fara dubawa,
_Bazan sakeki ba Fateema, kije gida idan komai ya lafa zan ɗauko ki, ki kulamun da kanki sosai_
[6:57PM, 9/24/2017] 💋Eshat aysm💋: 🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
Page 21
*END*
_END_
*NA GAJIRCE LABARIN SABODA AN KOMA SKUL SAM BANA SAMUN LOKACI*
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hearts of readers_
*PML*
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.
.
*FATA NA GARI GA DUKKAN MASOYANA AKO INA SUKE, DA WANDA YASAMU DAMAR ISARMUN DA SAK'ONSHI DA WANDA BAI SAMU BA DUKKA INA SONKU*
.
.
*SHAWARATA GAREKI*
_DUK WANI ABUNDA ZAKIYI KI TABBATAR KI. RIK'E ADDUA, BABU WANI ABUNDA ZAKIYI KISAMU KWANCIYAR HANKALI MATUK'AR KINA WASA DA IBADAR KI, AKWAI MAZA MASU TAURIN KAI KOME ZAKIYI BAZAKIGA FUSKABA, MAGANINSU KENAN ADDUA, KADA KIYI WASA KEDAI NEMI ALJANNAR KI TA GUDAN AURENKI_
.
.
*INA ALFAHARI DA MAHAIFIYA TA DA TABANI TARBIYYAH, WANDA SHI YAKE JAGORANTA NA A RAYUWA TA, ALLAH YABARMUN KE MOMY NA, YAKAREMUN KE*
.
.
.
*Wai masu cewa 'yanmata kada su karanta novels ɗinsu menene aciki, acikin online writers na media wlh 'yanmata sun kusa fin matan auren ma, tun ina jss2 nake karatun Hausa novels kuma wlh ban taɓa lalacewa ba, shifa iskanci basai ka karanta zaka zama ɗan iskaba*
.
.
.
*DUKKAN GROUPS D'INA NA FCBK DA WTSP INA ALFARI DAKU*
.
.
_PURE MOMENT BABU KAMARKU A FAD'IN DUNIYAR NAN, KO INA KA LEK'A SUNANKU NE KAD'AI KE HASKAWA, ALLAH YA K'ARA MANA D'AUKAKA_
*SABSON FAMILY GROUPS*
Kuɗin jininane har abada bazan daina fatan Allah ya karemu daga sharrin mak'iyaba.
.
.
Gaisuwa gareki *AISHA 'YAR ALJANNAH*
.
...
SAI KUNJINI A *NI AYS NAKESO*
KUSAN WANI YANKINE NA RAYUWATA LABARIN.
.
..
.
...
.
Mik'awa Fateema takaddar tayi ta kasa magana, koda Fateema ta karanta zufane ya fara wanke ta, cikin ruɗu ta ce "Aunty wallahi ban karanta ba sai
yanzu".
Maryam ta ɓata rai ta ce "yanzu da kinyi aure akan aure fa? Yanzu tashi muje mu sanar musu basai gobe ba, nagode da Allah yakawoni kafin a ɗaura aure gobe".
Mik'ewa Maryam tayi tana mita, Fateema kam hawaye ne ya fara sauk'owa, don ita harga Allah yanzu tafison Ahmad, zama da kishiya ai sai dole, kuma tasan tunda abun ya kasance haka babu yanda za'ayi Anwar ya saketa, inama da anɗaura auren ace ta zaɓi wanda take so....
Maryam ne ta katse mata tunani, "to wai kukan me kikeyi"?
Fateema ta share hawaye tace "zauna Aunty, don Allah ki fahimce ni, ni yanzu bazan ɓoye miki ba banason Anwar Ahmad nake so, ki taimakamun ki k'ira Anwar ya sakeni yau ɗinnan basai kowa yaji ba, kinga zamuji daɗin zumunci dake".
Wani murmushi Maryam tayi ta ce "kina nufin bazaki koma ɗakin ki ba"?
Gyaɗa mata kai kawai tayi, Maryam batace mata komai ba ta ɗau wayarta ta k'ira Anwar.
"Maman Baby kin kasa bacci bana kusa ko, naga yanzu muka gama waya, ki tabbatar kun fito da asuba kada ku sake kwana fa".
Murmushi tayi ta ce "sarkin 'yan son kai, kace dai ka kasa bacci".
Dariya yayi ya ce "amma kin gane, sai juyi nakeyi wajen yayi mun faɗi, ina Fateemar bata naji muryar ta kafin ki kawomum ita".
"Gaskiya akwai matsala, gobe auren Fateema".
Wani wawan tsalle ya buga sai gashi a a zaune, "what? Da auren nawa akanta, sun haukace ne, wallahi duk wanda ya kuskura ya ɗaura aure da matana sai nasa an kulle shi".
Da sauri ta mik'awa Fateema wayar, ita duk jikin ta yayi sanyi, surutu yayi tayi baima san wayar a hannun Fateema yake ba, lokaci guda tausayi ya kamata, ji tayi tana son komawa gidan mijin ta, tsinke k'iran yayi duk ran maza ya ɓaci.
I
Kukan ma kasayi tayi, itadai Maryam ta zuba mata idanuwa ko k'iftawa batayi,
Anwar yana kashewa ya k'ira numban Bilal, saida yayi kusan tsink'ewa ya ɗaga, cikin magagin bacci ya ɗaga, "Anwar yayane"?
"Don Allah kazo yanzu akwai matsala".
Mutssuka ido Bilal yayi "matsala da darennan? Kabari gari ya waye mana".
Anwar ya marairai ce yace "bazaiyiyu ba, meduguri zamuje".
Bilal ya tuntsire da dariya "to kodai ka fara shan wani abune"?
Anwar yayi tsaki ya ce "kaifa ɗan air ne, ba abunda nasha".
Ganin Bilal zai ɓata masa lokaci yasa ya zayyane masa abunda yake faruwa, Bilal ya jinjina kai yace "ba zuwa zamuyi ba, abun me sauk'ine, kayi waya kafaɗa musu baka saki matarka ba, bawanda ya isa yayi aure akan aure, kaga sai su taho da Maryam ɗin kawai".
Anwar yayi na'am da hakan.
.
.
Bayan sun gama waya da Anwar, ta faki idon Maryam ta jero numbobin Ahmad ta fara k'ira, yana ɗauka ta fashe mishi da kuka, ruɗewa yayi yafara tambayar ta lafiya, kina inane?
"ina ɗaki".
Amsar da tabayar kenan ta katse kiran, Maryam ta ce "wa kika k'ira kuma, iyayenki ya kamata ki k'ira ki faɗa musu, kinga da safe sai mu wuce ko"?
Murmushi me ciwo tayi tace "bari yazo idan nafaɗa mishi sai yasanar da iyayenshi".
Kafin Maryam tayi magana Ahmad ya diro ɗakin, hankalin shi a tashe ya nufi Fateema, kusa da ita ya zauna ya ce "me yasaki kuka, kin ɗagamun hankali, ina fata lafiyar ki k'alau"?
Wani kukan ne yazo mata, ya sake ruɗewa ya ce "kiyi hak'uri ki faɗamun, kukan yana taɓamun zuciya da yawa".
Ganin tashin hankali a k'wayar idon shi yasa Maryam ta ce "kuka bazai fissheki ba Fateema, kifaɗa masa gaskiya kawai".
mik'a mishi takaddar Fateema tayi, batajira yagama karantawa ba ta ce "Ashe Anwar bai sakeni ba, wallahi ban buɗeba, kayi hak'ur.......
faɗuwar da Ahmad yayi ne yasa tayi shiru, gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, da gudu Fateema tayi cikin gidan, batasan inda ta nufaba ma, kawai ganin ta tayi tashiga wani fankacecen falo, ashe sashin mahaifin Ahmad taje, da kuka tafara nuna mishi hanya tana cewa "Ahmad".
remot ɗin hanunshi ya ajiye ya ce "ina Ahmad ɗin, yanzu yabar nan".
dakyar ta iya cewa "ya faɗi, yana ɗakina".
Da sauri ya nufi ɗakin, Maryam sai safada marwa takeyi, tayi k'ololuwar ruɗewa, bata ɗauka zai ɗau abun da zafi hakaba, indai hakane Lallai shi yadace da Fateema ba Anwar ba, ɗagoshi yayi yafara hura masa iska a kunne, a hankali ya buɗe ido, ganin mahaifinshine yasa ya fashe da kuka, "Dad inason Fateema, ban taɓa so ba sai ita don Allah kafaɗa mata tadaina mun wannan wasan".
kanshi ya kulle ya dubi Fateema sai kuka takeyi, Maryam ne ta shaida masa abunda yake faruwa, murmushin manya yayi ya ce "haba Ahmad kamar ba namiji ba, ka godewa Allah da yasa angane kafin aure, yanzu dai maganar aure babu shi, kuma kada na sake jin ancemun kayi koda ciwon kai ne".
Kafin gari ya waye har itayen Fateema sunji wannan kwamacalan, 'yan biki kuwa da safe duk suka fara watsewa, kafin kace me zazzaɓi ya kama Fateema da Ahmad, ba k'aramin so Ahmad yakeyi wa Fateema, tanada shiga rai lokaci k'ank'ani, ta iya takunta sosai, abun duniya duk ya ishe gidan, Maryam dai ta kafe akan sai ta tafi da Fateema, Fateema ta kafe ita bazata komawa, ganin haka yasa ta shaidawa Anwar halin da ake ciki, shikam bai iya ɓacin rai ba, haushi ya kamashi, watau batason zama dashi, a tsawace yace abaiwa Fateema wayar, k'in karɓa tayi, ganin haka yasa Baba me yalo ya karɓi wayar akan zai bashi hak'uri, kafin yayi magana Anwar yafara zazzaga ɓacin ranshi, karshen furucin yace basai kin nunawa duniya sakinki nayiba saboda son zuciya, kiyi ta auren ki na SAKEKI saki UKU"....
Baba me yalo ya buga salati, yana faɗin assha, duk fa saida suka kaɗu harda Fateemar, Maryam ranta baisoba don tanason zama da Fateema sosai, tunanin ta ɗaya batasan wata irin kishiya za'a sake kawo mata ba, gashi taji ance maza idan suka ɗanɗani zama da mata biyu basu iya sake zama da ɗaya.
Aranar ta koma gida tabarsu da jimami.
Basai nabaku labarin irin murna da farincikin daya ziyarci Ahmad ba, duk da ance lokacin babu idda akan ta saida tasake sabon iddah.
watanni biyar tsak'ani aka ɗaura auren Fateema da Ahmad, tsantsan soyayya da k'warewa take nuna mishi a matsayin ta na bazawara, shikam ji yake kamar budurwa ya aura tunda dama baisan yaya budurwar takeba.
.
.
.
itakam Maryam tun daga lokacin ta rik'evmijin ta sosai, gyara kuwa tanayi ba kama k'afa, sai tazamto mace ɗaya tamkar dubu, tayi alk'awari bazata sake yin sake ayi mata kishiya ba, dak'yar suka shawo kan Alhaji ya yafewa Hajiya Jamila, yanzu nunawa Maryam so take sosai, kuma zumunci me k'arfi ya k'ullu tsakanin Maryam da Fateema.
.
.
Bayan shekara ɗaya Fateema ta haifo ɗanta na miji, Maryam kuma lokacin tanada ciki amma bansan wata nawa bane.
.
.
.
Wannan shine k'arshen *SHIMFID'AR MIJINA*
.
Wlh *SHIMFID'AR SA*
Yafi komai muhimmanci ki gyara kisha mamaki.
*DUK WANDA YAMUN EDITIN YA CIRE SUNANA ALLAH YA ISA WLH, KOWA YA IYA C&P SAI KUYITA AMFANI DA BASIRAR MUTANE, IDAN SO KAKE KA YAD'A ƁBAN YADDA A CIRE SUNANA BA, AKWAI NOVEL D'INA _SONE AJALINA_ WANDA NAYI AMFANI DA AISHATU SALIHU BICHIKI NAGA ANCIRE SUNANA ANA YAWO DASHI HAKA, TO WALLAHI DUK WANDA YASAKEMUN HAKA BAZAN YAFE BA*
0 Comments