MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽
_Wannan shafin naku ne_
_Zainab Abdullahi_ (Abuja)
_Kamar yadda kika ce ina burge ki, ke ma kina burge ni_.
Fatima Bintu Kano (‘yar garin mu)
_Hadiza Murtala_ (Maiduguri)
_Yusra_
_Na gode da kulawar ku da kuma fatan alkhairi, na kuma ji dad’in yadda kuke son wannan novel d’in_.
_Ni ma ina muku fatan alkhairi a duk inda kuke._
*NUMBAR YABO*
_Kamar yadda nake gabatar da shirin question of the day ne a cikin wannan novel d’in nawa, hakan yasa na fitar da wasu daga cikin shirin dan karrama su da ba su number yabo a cikin shirin_.
_Sunayen wanda suka samu wannan karramawar sun had’a da_:
*Aisha matar Abdul* (Auta mama)
(Queen)
*Xarah Auwal*
(Ass Queen)
*Meeynah*
(Princess)
*Insha Allah, akwai kyauta ta musamman ga wanda ta kasance ita ce ta farko zuwa na uku*
*Wannan karan, Meeynah ita ce ta amsa duka tambayar, yayin da Aisha (Auta mama ta amsa d’aya daga cikin tambayar)*
*Allah ya k’ara muku ilimi mai amfani da sauran d’aukacin musulmi baki d'aya*.
*Amsar tambayar ita ce ‘A cikin shekara ta 35 ne, k’urayshawa suka jaddada sabunta gina ka’aba*.
*K’urayshawa sun samu sa’bani ne akan d’aura dutsen hajarul aswad* .
*TUNATARWA*
_Ka/ki zamo mai neman ilimi, amma kar ka/ki yadda ya kai ka/ki ga girman kai_
_Ka/ki zamo mai Magana, amman kar ka/ki yadda ya kai ka/ki ga zalunci_
_Ka/ki zamo mai Magana, amma idan z aka/ki fad’i alkhairi_
_Ka/ki zamo mai k’arfi, amma kar ka/ki yadda ya kai ka/ki ga k’eta_
41&42
Ko da muka koma class, mun tarar da citizenship har ya fara lectures, sai da ya barmu na tsawon minti 15 a waje, sannan ya fito ya tambaye mu ina muka je? Mun fad’a mishi daga asibiti muke sannan ya bar mu muka shiga kasancewar yana da sauk’in kai.
Bayan mun yi closing ne, Halima ke tambaya ta, wai da naje ganin likita mai nace mai yake damu na?
Dariya nayi nace "Tun da kin sa aka kai folder mu, na shirya k’aryar da zanyi in naje gurin likitan, ce mai nayi ciwon mara nake fama dashi, ya rubuta min magani, har yana ba ni shawara wai in dage, course d’in mu na da wahala".
"Allah sarki, wasu likitocin ai na da kirki" cewar Halima.
Amsar zancen nayi da cewa "gaskiya yadda na lura kamar bai da matsala, wasu likitocin ma in kaje gurin su, suyi ta maka fad’a har ka kasa fad’an me yake damun ka".
Dariya Halima tayi tace "wlh kuwa, haka wasu likitocin suke".
Ci gaba da hirar mu muka yi, muna cikin sakkowa daga upstairs ne, na hango motar yaya Khalil.
Yau ina jin yaya Khalil bai da wani lectures ne da yawa, tun da ya samu zuwa d’aukan mu" na ce ma Halima.
Halima da murmushi a fuskar ta tace "Ai ku ‘yan gatan yaya Khalil ne, ni kin ga yaya Jamal, idan ya dawo aiki, Maman mu tace yazo ya d’auke ni, sai yace wai an ci ka shagwa’ba ni, in dinga dawo wa da kaina.
Dariya nayi nace "ki ce shima kamar yaya Faruk yake, shima fad’a kamar ya ari bakin wani, ga sa mutum purnishment".
Haka muka ci gaba da conversation har muka k’araso in da motar yaya Khalil take, yaya Khalil ne da Anisa a cikin mota, gaisawa suka yi sannan ta tafi.
Mun fara tafiya ne na ga yaya Khalil da Anisa suna hira k’asa- k’asa wanda ban san mai suke ce wa ba.
Katse musu zancen da suke yi da cewa "wai yaya Khalil ban fa gane bane?"
Murmushi yayi yace "da aka yi me sister?"
"To na ga sai hira kuke yi k’asa-k’asa ba ku sa ni a ciki ba"
Anisa ce tace "To ke Fatima tun da kika ga muna Magana a hankali ai ba a so ki ji zancen ne" ta k’arasa maganar tana murmushi.
Cikin shagwa’ba nace "Yaya Khalil na ga so kuke ku had’e min kai da Anisa, in zama ni kad’ai"
"Mu mun isa mu had’e miki kai, ke da kike da babban yaya soja" ya fad’a da alamar tsokana.
Gintse fuska ta nayi saboda nasan yanzu yaya Khalil zai samu hanyar ci gaba da tsokana ta.
Hirar mu muka ci gaba da yi cikin wasa da dariya har muka k’arasa unguwar su Anisa muka sauke ta kana muka nufi gida.
Da daddare ina kwance a d’aki ina chating da friends d’ina naga wata sabuwar number an min Magana da ita.
"Assalamu alaikum" abin da na ga an turo min.
"wa alaikumus salam’ na tura reply.
"Kin gane da wanda kike Magana? aka sake turo min.
Reply na tura da cewa "ban gane ba gaskiya"
Ki na Magana da Bregadier Umar Yusuf, yanzu ina fatan kin gane".
Sai a lokacin na gane yaya Faruk ne, saboda ba da ordinary numban shi yake chat ba.
"Oh yaya Faruk, sai yanzu na gane ka"
"good, ya studies? ya tambaye ni.
Amsa mishi nayi da cewa "karatu lafiya lau, ya aiki?
"Aiki Alhamdulillah, yanzu ma muna shirye shiryen tafiya Adamawa ne wani aiki, a taya mu da addu’a".
"To yaya Allah ya taimaka"
"Amin".
"Bari in bar ki haka ki huta tun da gobe ki na da lectures, ki kashe data d’in ki dare ya fara yi".
Ba a lokacin nayi niyar sauka ba, saboda a group d’in mu na Statistics class rep d’in mu ya turo man da working d’in da function & geometry ya ba mu, ganin yadda yau ya min Magana ba tare da fad’a ba yasa na tura mishi reply
"Ok yaya, yanzu zan sauka".
"that is good, good night & have a sweet dream" abin da ya turo min kenan ya kasha data d’in shi.
Ni ma kashe data na nayi ina mamakin yadda yaya Faruk yau ya zauna yana chating da ni, yanzu kam na yarda yaya Faruk yana so mu fara shiri dashi.
But ban san me yasa na kasa samun peace of mind akan yaya Faruk ba, duk da ko a da d’in ba wai yana min wani abu ne da zai sa in tsane shi ba, sai dai fad’an da purnishment d’in da yake mana ne yasa nake jin haushin shi wanda nake ganin kamar ya tsane ni ne, amma zan yi k’ok’arin in ga na sake dashi a matsayin yaya d’an uwa na kuma yaya na.
Da wannan tunanin na kwanta barci.
A can ‘bangaren yaya Faruk kuwa, tun da ya gama waya da Teeman shi yaji wani farin ciki ya lullu’be shi, yanzu dai gashi ba wata hira suka yi irin ta masoya ba amma ya tsinci kanshi da jin dad’in haka, wai a hakan ma dan bai ji sirrin zuciyar ita Teeman ba, kenan idan ta amice dashi zai tsinci kanshi ne a birnin masoya wand aba kowa ne ke tsintar kanshi a ciki ba sai wanda suka aminta da junan su, in ko haka ne zai ci gaba da addu’ar Allah ya mallaka mishi Fatima saboda ita ce Farin cikin shi.
Zai k’ara ba ta time kan ya tuntu’be ta akan ra’ayin ta game dashi.
Da wannan tunanin barci ya d’auke shi.
Tafiyar su yaya Faruk ta rage yau saura kwana biyu, kiran su aka yi a waya da akwai meeting da su Bregadier General da su Major General za ayi akan tafiyar, ko da suka halarci meeting d’in, an fad’a musu cewar an d’aga tafiyar ne zuwa next week sabida wasu dalilai.
Da wannan damar yaya Faruk ya nemi permission akan yana so yaje Kaduna yayi 2 days.
Sallama yayi Ma Mus’ab ya kamo hanyar zuwa Kaduna.
Yana sauka ya shiga side d’in Momi ya gaishe ta, bayan sun gaisa ne take tambayar sa ba su yi tafiyar bane ta ganshi unexpected.
Sanar da ita yayi an d’aga tafiyar zuwa next week, shi yasa yayi deciding d’in zuwa yayi 2 days a nan.
Momi ta ji dad’in haka saboda tasan yaya Faruk mutum ne mai son iyayen shi da ‘yan uwan shi.
Tashi yayi ya nufi side d’in shi ya watsa ruwa, fito wa yayi ya sami Anisa a falo tana karanta handout d’in ta, a gefen ta wani exercise book ne ta take jotting.
Dad’i ne ya kama Anisa ganin ya kwana biyu bai zo ba, ba ta yi tsammanin ganin shi a wannan lokacin ba tun da Momi ta fad’a mata za su yi tafiya.
Da fara’a tace "yaya sannu da zuwa".
"yawwa Anisa, ya karatu".
"Lfy lau yaya Faruk, amma gaskiya yaya karatun Polythecnic akwai wuya, gashi exam is approaching".
Murmushi yayi yace "Anisa ko wani karatu da kike gani yana da wuyar shi both polythecnic & University, sai dai d’an banbabcin da ba za a rasa ba, ki dage sosai dan ki fito da grade mai kyau".
"zan dage insha Allah".
"yawwa my Sis".
Jefi-jefi suka ci gaba da hirar, a gurin Anisa kuwa tana jin dad’in yadda yanzu yaya Faruk yake jan su a jiki ita da Fatima, ita ma ta na so ta ga yaya Faruk yana jan ta a jiki kamar yadda yaya Khalil ke jan su.
Momi ce ta fito daga side d’inta ta k’araso falon ta zauna.
Hira suka ci gaba da yi irin na happy Family, a ran Momi kuwa dad’i ne ya kama ta ganin yadda yaya Faruk ya fara rage miskilancin sa.
Kasancewar yau ranar asabar, ba mu da lectures, hakan yasa na tashi da marmarin cin samosa da spring roll.
Kitchen na shiga na duba dan in ga ko akwai duka kayan da nake buk’ata, samu nayi da akwai kayan had’in da zan buk’ata.
Iya talatu na kira ta taya ni yanka cabbage da karas, ni kuma na ci gaba da sauran aikin,
Saboda yadda yake da cin time, sai da na d’au lokaci kan na gama, ina gama wa na had’a ginger amma ban cika cittar ba saboda ka da yayi yaji sosai.
Ina fito wa falon na tarar da su Abbu da Ummu da yaya Khalil da kuma yaya Faruk suna hira.
Ja nayi na tsaya kamar wadda aka rik’e a gurin, ban yi zaton zuwan yaya Faruk a wannan lokacin ba.
Yanzu idan ya turke ni akan in fad’a mishi matsayin shi a guri na, me zan ce mai? Ni kaina nasan ban da wannan amsar, da wannan tunanin na k’araso falo na nemi guri na zauna.
Tun da na zauna yaya Faruk ya tsare ni da kallon shi wanda hakan yasa na tsargu.
Gaishe shi nayi na mik’e na shiga kitchen na zubowa kowa a plate da wannan ginger wanda yayi sanyi a fridge.
Ina lura da yaya Faruk da yana cin Samosa har wani lumshe ido yake yi, ko dad’i ya mai ne ban sani ba, ko da yake na lura lumshe ido a gurin shi kamar nature d’in shi ne.
Mik’ewa nayi ganin time d’in zuwa islamiyya ya kusa duk da mun nemi excuse a makarantar ba kullum za mu dinga zuwa ba, saboda yanxu mun fara d’aukar lectures, ran sati da lahadi kad’ai Mu ke zuwa.
Shiryawa nayi cikin Uniform d’ina, ina sa bak'ar socks ne naji waya ta tayi ringing.
Sunan yaya Faruk na gani a jikin screen d’in yana yawo.
Sai da na d’an yi jim kafin na d’auka saboda ban san me zai ce min ba.
Sallama na yi bayan na d’auka, amsa min yayi kana yace "me kike yi ne ban ga kin dawo falo ba?
"Ina shiryawa ne, time d’in makaranta ne yayi".
"Ok har yau dama kuna zuwa ne? ya tambaya.
"Eh muna zuwa, amma ran weekend kad’ai muke zuwa".
"Hakan na da kyau, in kin gama ki fito in kai ki, ina waje".
Amsa mishi na yi da "Toh".
Ba haka na so ba, nasan in dai na shiga motar shi sai ya tambaye ni a inda muka kwana akan tayin soyayya shi wanda har yanzu na rasa me yasa na kasa samun mafita.
Gun Ummu naje na fad’a mata cewa yaya Faruk ne zai kai ni.
Kujera mai zaman banza na zauna, ina wasa da ‘yan yatsu na.
Mun fara tafiya ne ya fara tambaya na game da karatuna, ina bashi amsa.
cikin wasa yace ‘yan k’idaya kenan, kuna fama, dan naji an ce ku lissafin naku har motoci sai a saku ku k’irga sannan ku fitar da data saboda tsananin lissafi, in na samu time zan zo in kai ki barrack d’in mu ki k’irga mun yawan mutanen da ke shiga da fita".
Dariya tayi tace "haba yaya Faruk, ina zan iya tsayawa k’irga motoci sai kace wata injin".
"Gaskiya course d’in ku nasan akwai wuya amma ki dage, course d’in ku yana da amfani a ko ina, infact ku professional ne da ko ba aiki za a neme ku a ko ina, ko wani course da kike gani yana da challenges d’in shi, in ka mai da hankali, sai ki ga kin yi achieving goal d’in ki".
"na gode yaya Faruk da shawarwarin ka".
K’asaitaccen murmurshi yayi yace "Kar ki damu Teemah, you are my sister, it is my responsibility to give you advice at any time".
Har raina naji dad’in shawarar da yaya Faruk ya bani, yanzu na k’ara yadda da zancen yaya Khalil da yake cewa yaya Faruk mutum ne mai dadin zama in ka fahimce shi, gaskiya a kwanakin nan ina jin dad’in yadda yake sake wa da mu.
Ko da mu ka k’arasa gidan su Anisa, cewa yayi in yi sauri in shiga in kira ta, ba ya son jira.
Sanin halin shi yasa ina shiga na tarar da Momi da k’awarta suna duba kayan da Momi ta saro, da fara’ar ta muka gaisa kana na gaishe da k’awar ta, bayan mun gaisa ne nake tambayar ta
"Momi ina Anisa take?".
"Tana d’aki, ina ganin ta shirya, ki shiga ki gani".
D’akin na shiga na sameta ta shirya, ta tsaya sa powder.
Hararar wasa na mata nace "ke matsalar ki cin time a gurin make up".
"kin san Make up na son natsuwa, shi yasa nake tsayawa in yi shi a tsanake".
"yanzu dai ba wannan ba, yau ba yaya Khalil bane ko Driver zai kaimu bare ki ‘bata musu time".
Ci gaba tayi da Make up d’in ta tana cewa "To waye zai kai mu?
"yaya Faruk ne zai kaimu, kin san kuwa ba ya son jira, kuma ke da zaki sa nik’ab, wani make up zaki tsaya yi"
Anisa ba tayi wani mamaki ba, ta san yanzu yaya Faruk is a change person, ba abin mamaki ne dan yace zai kai su Makaranta.
Tasan duk canzawar shi ba zai hana in ka mishi laifi ya zartar maka da hukunci ba, tasan yaya Faruk bai son jira dan ba ta manta da purnishment d’in da y aba ta ba kwanaki na filling d’in ruwa da k’aramin cup ba.
Cikin sauri ta d’aura nik’ab d’in ta fito muka nufi motar shi.
Wannan karan miskilanci ya motsa, tun da muka shiga motar ya kunna wa’azin Sheikh Yahaya Haifan yana saurare, mai taken Tsantseni, gaskiya ko ni da nkae sauraren wa’azin jiki na ne yayi sanyi saboda yadda Malamin ya kawo bayanai akan Tsantseni a rayuwar d’an adam, tambayar da nayi wa kaina a yanzu mutane nawa ne masu Tsantseni a duniyar nan, ko za a samu k’adan ne.
Addu’a kawai nake yi akan Allah yasa mu dace, ya kuma ba mu ikon yin tsantseni akan duniya.
Sauke mu yayi a wajen makaranta ya juya ya tafi.
Ko da aka tashi ga Mamakin mu, shine yazo d’aukan mu.
Lallai mun zama ‘yan gatan yaya Faruk kamar yadda yaya Khalil yake tsokanar mu.
Wannan karan a mota ya ja mu da hira amma ba mai tsawo ba, tun da shi ba ma’abocin surutu bane.
Sai da ya fara sauke Anisa a gida, sannan ya nufi gida da ni.
Kallo na yayi yace "Teemah Samosan da kika yi da Spring roll ya min dad’i, in ba damuwa za ki min gobe in nazo?" ya tambaye ni.
Duk da procedure d’in yin su Samosa da Spring roll yana da wuya, hakan ba zai hana in mishi ba, dan gaskiya nima yanzu na fara jin dad’in zama dashi.
"Ok ba matsala, zuwa gobe insha Allah zan maka".
Murmushi yayi yace "ki barshi wasa nake miki, amma in zan tafi sai ki min".
"Lalacewa zai yi, sai dai in ran da zaka tafi in yi in ajiye a fridge, in yaso in kaje can ka soya"
"Zan ba Maryam ta soya min in na koma, ni ina zan wani iya soya wa"
A raina kuwa tambayar wacece Maryam nake yi, dan ba na tunanin abokiyar aikin shi ce.
Kamar yasan abin da yake raina yace
"Nasan zaki ji nace Maryam, matar aboki na ne Mus’ab, da muke Barrack d’aya"
Shiru nayi ban ce mai komai ba tun da ba tambayar shi nayi ya min bayanin wacece ita ba, sun fi kusa koma wacece.
Da haka muka k’arasa gida, ya ajiye ni a bakin gate ya juya motar shi ya tafi.
[4/16, 12:31] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽
*Wannan shafin na sadaukar dashi ne ga duk wanda yake cikin wata jarabta ko cikin wani hali*
*Allah 🙏🏽🙏🏽🙏🏽na yi tawassali da sunayen ka da kyawawan ayukan mu, ka kawo mana mafita a al’amuran mu, ka bamu ikon cin dukkan jarabawar da ka mana*.
*Alllah dan sunayen ka tsarkakakku, ya ubangijin Sammai da k’assai, ya Ubangijin fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (s.a.w) Allah ka bi ya mana buk’atun mu na alkhairi*
🙏🏽🙏🏽🙏🏽🙏🏽🙏🏽
_Plsss fans ina barar addu’ar ku akan wasu buk’atu nawa, Allah ya amsa min da sauran ‘yan uwan musulmai baki d’aya_
*Question of the Day*
_A cikin matan manzon Allah s.a.w, wacece ta lurar da manzon Allah (s.a.w) game da wata dabara da zai jawo hankalin sahabban sa a ranar hudaibiyyah, kuma dabarar taci nasara sosai_
_Menene cikakken sunan ta?_
43&44
Bayan na shiga d’aki ne, hirar da muka yi da yaya Faruk a cikin mota da kuma shawarwarin da ya din ga bani game da karatu ya dinga fad’o min a rai.
A yanzu na sa a raina da cewa yaya Faruk ya samu wani matsayi a raina ta ‘bangaren zumunci, wata zuciyar kuma ta na ce min mai zai hana in bashi matsayin da yafi dacewa shine in amince da soyayyar shi, me yasa har yanzu zuciya ta ba ta anshi tayin shi ba?
Wata zuciyar tawa kuwa shawara ta ba ni akan mu ci gaba da zumunci irin na ‘yan uwantaka.
Da wannan sark’ak’en tunanin na tashi na nufi d’akin Ummu.
Washegari ina zaune a falo, ina karanta wani online novel a cikin waya mai suna *Rayuwar yusra da Afshan*, wanda Maryam Ahmad Paki ta rubuta, labarin yayi touching d’ina na yadda soyayya ta canza ma Afshan hali, duk a dalilin soyayyar Muhsin da ta fad’a kuma mijin Yusra wacce ta rik’e ta kamar ‘yar uwarta ta jini, ba ta saka mata da komai ba sai soyayya da Mijin Yusra wanda take son shi kamar ranta, ko yaya labarin zai kasance a k’arshe? Gaskiya na yadda da marubuciyar da tace labarin Soyayya mai rud’ani da tausayi a cikin novel d’in, Shine na k’osa na ji k’arshen labarin.
Sallamar yaya Faruk ne ya katse min karatun da nake yi.
Amsa masa sallamar nayi da sassanyar murmushi na.
Kusa dani yazo ya zauna, yana min kallon gefen ido.
"yaya ina wuni" na gaishe shi.
"lfy amma ba lau". ya amsa min
Kallon shi nayi jin amsar da ya ba ni, a yanayin shi ban ga wani abu da yake damun shi ba.
Shiru na yi ban k’ara cewa komai ba.
Wani tsadadden murmushi yayi kana yace "Teemah ba ki tambaye ni me ya same ni".
"yaya ai ni ban ga alamar ba ka da lafiya ba, na gan ka normal ne".
Kallo na yayi sannan yace "Teemah, ni ko ke rashin lafiya?".
Da sauri nace "Me yake damun ka?" Na fad’a da alamar tausayi.
K’asaitaccen murmushi yayi yace "Ba irin ciwon da kike tunani bane, wannan daban ne, kuma ke ce maganin ciwon nawa".
Gaba na ne ya fad’i, sai yanzu na gane mai yaya Faruk yake nufi, yana so ya d’akko min maganar da muka yi kwanaki ne akan amsar tayin soyayyar shi.
Yanzu in ya tambaye ni mai zan ce mai? Gaskiya bazan iya fito wa direct in ce mai ban yi na’am dashi ba duk da matsayin da na ba shi a guri na.
Katse min zancen zucin da nake yi yace "Teemah!"
nasan kin gane me na ke nufi, ba komai ke damu na ba illah fama da ciwon son ki da ya min dabaibayi a zuciya ta wanda har yanzu ban san matsayi na a gurin ki ba, ina so ki bani amsa ta Teemah, dan zuciyata ta samu peace of mind".
"An zo gurin".abin da na fad’a a raina kenan.
Zuciya ta ce ke kai kawon me zan ce ma yaya Faruk a yanzu da zai yadda da hujja ta, dubara d’aya ce ta fad’o min akan in lalla’ba shi mu rabu lafiya.
"yaya Faruk, kai ma kasa ba zan k’i ka ba, ko dan darajar ‘yan uwantaka dake tsakanin mu, ko a da damu ke samin misunderstanding rashin fahimtar juna ne, amma yanzu na gano kai mutum ne mai dad’in zama da dad’in mu’amala, sai dai ina neman alfarmar ka yaya ka k’ara min time, saboda kasan har yau ban gama sanin mecece soyayya ba"
Tsura min ido yayi kamar yana so ya gano gaskiyar maganar da na fad’a mishi.
Sunkuyar da kai na nayi dan gaskiya ba zan jure kallon da yaya Faruk yake min.
"Fatima!" ya kira ni da wani irin salon maganar shi da ya banbanta da sauran lokuta.
"Na’am yaya"
Sai da yayi shiru kamar ba zai ce min komai ba, can ya d’ago ya kalle ni.
"Teemah, zan iya k’ara ba ki time kamar yadda ki ka buk’ata, ina so duk san da na k’ara tambayar ki ya zama kin samo amsar".
Ci gaba yayi da cewa "Teemah, ina son ki wanda ni kaina ban san adadin son da nake mi ki ba, ni mutum ne da ba na soyayya sai akan ki da na fara, akwai ‘yan mata da suke so na amma ni ke ki ka min, ba na so in yaudari mutum, dan haka Teemah ina rok’on ki kar ki yaudare ni, gwara tun wuri ki fito ki fad’a min abin da ke ranki, zai fi min sauki".
Jiki na ne na ji yayi matuk’ar sanyi da maganganun da yaya Faruk ya fad’a min, yanzu gaskiya ba k’aramin girman yaya Faruk nake gani ba.
"yaya insha Allah ba za ka same ni da aikata haka ba".
Murmushin jin dad’i yayi wanda hakan ya nuna a fuskar shi.
"Teemah, kinga kin sa na koyi surutu duk saboda son ki" ya fad’a da alamar wasa.
Dariya nayi nace "Ni ba ruwa na yaya".
Girgiza kai kawai yayi bai ce min komai ba.
Haka muka ci gaba da zance jefi-jefi, yana k’ara jaddada min irin son da yake min.
Tambaya na fara yi ma kaina "wai yaya Faruk wani irin so yake min haka? ni kaina na san ba ni da amsar amma alamu sun nuna ba k’aramin so yake min ba.
Muna cikin haka ne, yaya Khalil yayi sallama ya shigo falon, ka sa ‘boye mamakin shi yayi ganin mu tare da yaya Faruk a kujera d’aya muna hira.
Hannu ya mik’a mishi suka yi musabaha kana ya nemi guri ya zauna.
Yaya Faruk ne ya kalle shi yace "Ashe ba ka nan, shi yasa ban ga motar ka ba"
"Na d’an fita ne, naje gurin friend d’ina" yaya Khalil ya ba shi amsa.
"Ok" yaya Faruk ya fad’a a gajarce.
Ci gaba yayi da min Magana k’asa-k’asa yana fad’a min gobe zai koma Abuja, kar in manta in mishi Samosa da Spring roll d’in in ba Ummu ta ajiye mai, zai biyo ya amsa.
Sauraren shi kawai nake yi ba tare da n ace komai ba saboda na ga yaya Khalil ya maida hankalin shi gare mu.
Shi kuwa yaya Khalil kallo ya bi mu dashi ganin yadda mu ke Magana k’asa- k’asa, yana so ya tabbatar da zargin da zuciyar shi take yi akan mu.
"Tun yaushe yaya Faruk da Fatima su ka shirya? An yaya babu wata alak’a tsakanin yaya Faruk da Fatima kuwa? Duk wannan tambayar da yake yi ma kanshi yasan ba mai ba shi amsar sai Faruk ko Fatima, shi kanshi yasan ba zai iya tunkarar yaya Faruk da wannan zancen ba, gwara dai ya tambayi Fatima.
Kallan tsadadden wrist watch d’in shi yayi wanda ke d’aure a hannun shi, kallan time yayi ya juyo ya kanne min ido ya ce min cikin murya k’asa-k’asa
"Teemah, zan tafi, nasan gobe in nazo ba zan same ki ba, mai za ki bani wanda zan dinga tuna wa dake" ya tsura min ido yana jiran ji mai zan ce mai, shi ko kunyar yaya Khalil ba ya ji.
Murmushi nayi nace "yaya ni ban san me zan ba ka ba, amma dai zan maka addu’ar Allah ya kai ka lafiya, ya kuma baka nasara a aikin ka".
Lumshe ido yayi saboda yadda yaji dad’in addu’ar da na mishi.
"Na gode Teemah da wannan addu’ar taki, ko ita kad’ai ta wadatar dani".
Had’a ido muka yi da yaya Khalil ya sakar min murmushi, saurin kau da ido na nayi dan nasan yau zan sha tsokana a gurin yaya Khalil.
Mik’ewa yayi yace "Bari in shiga gurin Ummu mu gaisa, sai mun yi waya".
"Ok sai mun yi waya" na ba shi amsa.
Hannu yaje ya ba yaya Khalil suka yi musabaha yace
"Khalil bari in lek’a gurin Ummu, gobe zan koma Abuja, may be ba ka nan, kana school".
"Gaskiya may be ba za ka same ni ba, gobe da wuri nake so in shiga school".
"Don’t mind, sai na dawo daga Abuja kenan".
"Safe journey yaya Faruk"
"Thanks Khalil" ya fad’a ya nufi d’akin Ummu.
Samun ta yayi tana zaune tana muraja’ar Alk’ur’an, sanye da medicated glass a fuskar ta.
Sallama yayi ya nemi k’asan carpet ya zauna kusa da ita.
Amsa masa tayi da murmushi a fuskar ta.
Gaisawa suka yi ta tambaye shi ya su Momi, Daddy da Anisa.
Amsa mata yayi da suna nan lafiya.
Ce wa tayi ya fad’a ma Momi tana nan shigowa wannan sati.
Hira suka ci gaba dayi, a ciki hirar ne yace "Ummu gobe zan koma Abuja"
"Da wuri haka Faruk, ni ina sha zaka yi mana kwanaki a Kaduna".
"Ummu da kwana biyu na nemi permission zanyi saboda prospond d’in tafiyar mu da aka yi".
"Allah dai ya taimaka, gwara da ka fad’a min da wuri, gobe sai in maka dambun naman ka tafi dashi".
Yau tsintar kanshi yayi da kunyar Ummu duk da ba ta san me ke tsakanin shi da Fatima ba, yana mai k’ara ganin girman Ummu na yadda take nuna kulawar ta gare shi.
"Ummu da kin barshi, saboda Fatima za ta min Samosa da Spring roll in tafi dashi, gobe zan biyo in amsa".
Dad’i ne ya kama ta ganin ce wa Fatima ce za ta mishi Snacks ya tafi dashi, hakan na nuna yanzu sun shirya kenan.
"Faruk ai Snacks daban, danbun nama daban, ka biyo gobe sai ka amshi duka".
"Ummu na gode, Allah ya k’ara girma".
"Amin Faruk, amma na sha ce maka in na maka abu ba godiya a tsakanin mu".
"To Ummu bari in k’arasa gida"
"Ka gaishe su"
"Za su ji".
Yana fito wa daga d’akin Ummu, d’aga mana hannu yayi ya fita daga falon.
Yaya Khalil ne ya dawo kusa dani yana kallo na.
Ni kaina kallon da yake min nasan akwai Magana a bakin shi, sai ban nuna mishi ba.
Dariya nayi ganin yadda yake min kallon tuhuma yana murmushi.
"yaya Khalil wai lafiya wannan kallon"
Bai ba ni amsar tambaya ta ba, sai ce min yayi "Sister kun sa ni a confusion"
"Ni da wa?" na tambaye shi.
"Ke da yaya Faruk"
"Da aka yi me?"
Hararar wasa ya min yace "Fatima kinn gane abin da nake nufi, amma tun da kin nuna ba ki fahimta ba, bari in miki filla-filla".
Ci gaba yayi da cewa "Fatima wai yaushe kuka had’e da yaya Faruk ban sani ba? na fara zargin ko akwai wata alak’a a tsakanin ku, sister tell me the truth".
In akwai wanda ya cancanta yasan alak’ar mu da yaya Faruk bai wuce yaya Khalil da Anisa ba, sai dai kash, hakan ba zai yiwu ba, dan muddum yaya Khalil ya ji maganar nan kamar kowa yaji ne a family, hakan na nufin dole in amince da yaya Faruk duk da har yau zuciya ta ba taji wani alamu na kamuwa da son shi ba, ya zama min dole in bar maganar tsakanin ni da yaya Faruk duk da nasan duk daren dad’e wa dole a ji abin da ke tsakanin mu, ina fatan a lokacin na yanke hukunci tsakanin amincewa dashi ko akasin haka.
Yaya Khalil ne ya katse min tunanin da nake yi.
"Sister tunanin me kike yi ne?"
"No ba tunani nake yi ba, ni ba abin da ke tsakanin mu ni dashi, kawai dai yanzu muna shiri ne, shi yasa ka ke ganin kamar akwai wata alak’a a tsakanin mu".
Kallon tuhuma ya min yace "Kin tabbata abin da kika fad’a min gaskiya ne".
"haka yake yaya Khalil".
Girgiza kai kawai yayi amma ba dan ya yadda da abin da na fad’a mai ba.
Tashi yayi yana cewa "bari in je gurin Ummu, na ga ban gan ta a falo ba".
"Ni ma yanzu zan tashi in shirya, lokacin makaranta ya kusa".
"Ok ki biya ma Anisa sai driver ya kai ku, akwai abin da zan yi ne yanzu, zan zo in d’auke ku in time d’in tashi yayi".
"To shi kenan, sai kazo" na mik’e na tafi d’aki, shi kuma yaya Khalil ya tafi gurin Ummu.
Kamar yadda yaya Khalil ya mana alk’awarin zuwa d’aukan mu idan aka tashi, hakan ce ta kasance, shi yazo d’aukar mu.
A hanyar tafiyar mu muka ce ya biya damu bakery ya siya mana ice cream sannan yace mu za’bi abin da muke so.
Beaf bread da pizza na d’auka, Anisa kuma ta d’auki Shawarma da sponge cake, shi kuma yaya Khalil ya d’auki meat pie da burger, gurin biya yaje ya biya sannan ya fara sauke ni a gida kafin ya tafi kai Anisa.
Tun bayan sallar asuba, na fara had’in Samosa da Spring roll, sai da na tabbatar na gama, na d’auki had’in na sa a fridge, ko a lokacin har gari ya waye.
Wanka na je na shiga, bayan na fito ne na shirya cikin cotton material kalar purple wanda ya sha d’inkin bit work, na d’akko gyale na light purple na yafa, na sa flat shoe, na rataya jaka ta side bag mai launin purple.
Gaskiya ni kaina nasan kwaliyar ta amshe ni sosai.
Fitowa nayi na tarar da Ummu da Abbu zaune a dining area suna kalaci, d’aya daga cikin kujerun dake zagaye da dining table d’in na nemi guri na zauna.
"Abbu Ina kwana, Ummu an tashi lafiya?"
"lfy lau Auta" Ummu ta amsa.
Murmushi Abbu yayi yace "Fatima kin tashi lafiya?"
"lafiya lau Abbu".
Juyawa nayi ina tambayar Ummu "yaya Khalil bai tashi ba ne?"
‘"Ina jin bai tashi ba, dan ban ji motsin shi ba, ina jin bai da lectures d’in safe ne".
Abbu ne ya kalle ni yace "Tun da na ga kin shirya, in kin gama break fast d’in ki same ni a falo, sai in yi dropping d’in ki, akwai in da na ke so in je da safen nan, tun da na ga Khalil bai tashi daga barci ba"
Amsa masa nayi "To Abbu".
Tashi yayi ya koma falo yana kallon labarai.
Kallon Ummu nayi na ce "Ummu, in yaya Faruk yazo, Samosa da Spring roll na cikin fridge sai ki ba shi".
Ummu murmushi tayi tace "Har kin yi kenan, gaskiya kin kyauta".
"Tun bayan sallar asuba na fara yi saboda ina gudun kar in makara".
Dariya Ummu tayi tace "Lallai kin yi k’ok’ari, Auta an shirya da yaya Faruk d’in ta kenan, ba sauran fad’a".
Cikin shagwa’ba na turo baki nace ‘ko da shi yake ja, amma yanzu mun shirya".
"Ai hakan yafi kyau Fatima" ta mik’e ta tafi falo.
Bayan na gama ne naje na sanar da Abbu na gama, tashi yayi muka nufi parking space ya d’auki motar shi muka tafi.
Sai da ya kai ni har department d’in mu ya sauke ni sannan ya tafi.
Can ‘bangaren yaya Faruk bayan ya shirya ya tafi side Dadi, inda ya samu Momi a can.
Yau Dadin bai samu zuwa aiki ba, kasancewar bai jin dad’in jikin shi.
Gaishe su yayi suka amsa.
Sun d’an ta’ba hira sannan ya mik’e da niyyar tafiya.
Addu’a Dadi da Momi suka yi ta mishi da fatan nasara a tafiyar da za suyi.
Kud’i ya ciro a wallet d’in shi ya ajiye ma ta.
Tana matuk’ar son Faruk saboda son kyautata ma iyaye da ‘yan uwa, ga kyauta, fatan ta Allah yasa ya ci gaba da wannan halin nashi.
Momi sai sa mishi albarka take yi irin wacce iyaye ke ma ‘ya’yan su.
Sallama ya musu, ya nufi ma’ajiyar motoci, ya shiga ya nufi gidan mu.
Ko da ya shiga falon, Iya Talatu ya samu a falo tana mopping, gaishe ta yayi ya tambaye ta "Ina Ummu take?"
Amsa mishi tayi "Tana kitchen, ko in kira maka ita ne?
"A’ah ki bar shi Iya Talatu, bari in k’arasa gurin ta".
Kitchen d’in ya nufa ya same ta tana juye dambun naman da ta mishi a plastic mai d’an zurfi.
"Sannu da aiki Ummu"
"yawwa Faruk, ba dai har ka shirya ba ba?".
"Yau da wuri nake so in tafi, akwai abin da zanyi ne in na koma".
"Ka ga ko yanzu na gama dambun naman, bari in d’akko maka Snacks d’in da Fatima ta ma ka"
Wani farin ciki ne ya kama shi a lokaci guda, ganin yadda Fatima ta tashi ta mishi snacks d’in kamar yadda tayi alk’awarin za ta mai, hakan na nuna kenan ta damu dashi.
Bai san lokacin da murmushi ya su’buce mai Abuja
D’akko mishi tayi ta samu d’an k’aramin basket ta jera mai a kai.
Kud’i ya ciro a wallet ya ba ta.
Ummu k’in amsa tayi tace "Haba Faruk, ni kam yau kayi hak’uri b azan amsa ba, tun kullum cikin ba mu ka ke yi, Allah dai ya k’ara bud’i".
"Ummu plss ki amsa ba yawa".
Murmushi tayi tace "Faruk ai ba raina wa nayi ba, wani lokacin na amsa, amma Allah a yanzu ba zan amsa ba".
Bai son suna jayayya shi yasa ya hak’ura, amma ba haka yaso ba, yaso ta amsa.
Sallama ya ma ta ya kana ya nufi Abuja.
[4/20, 20:29] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽
*Wannan Shafin na ba ku shi ne kyauta*
*Rabi’atu sk msh* (llileee)
(Marubuciyar Haramtaccen zama)
_Ummerherny Nerserllerh_
(Marubuciyar Da Aurena A Kanki)
_Ina muku fatan alkhairi a duk inda kuke, Allah ya bar zumunci_.
_BA ABIN DA ZANCE MUKU SAI GODIYA_
*Hak’ik’a ina jin dad’in yadda kuke k’ok’arin ba da amsar kun a question of the day, ba da amsar ko ba daidai ba ne zai sa mutum ya k’aru, saboda shirin tambayoyin musulunci ne, ta hakan nima nake k’aruwa saboda nobody is perfect, ba wanda ya wuce kuskure*
*Da fatan za a ci gaba da min gyara a cikin shirin, dan har yau nima d’aliba ce.*
*Xarah Auwal*(Ass Queen)
*Maman Walida*
*Sakina iliyas* (Maman Khalil)
*Ku ne ku ka ba da amsar daidai na question of the day, A matan manzon Allah (s.a.w) wacce ta lurar da manzon Allah (s.a.w) game da wata dabara da zai jawo hankalin sahabban sa a ranar hudaibiyyah, kuma dabarar taci nasara sosai itace Ummu Salma, cikakken sunan ta shine Ummu Salma Hindu ‘yar (bn) Umayyata.*
*TUNATARWA*
_* Ka/ ki zamo mai hikima, amma ka/ki yi amfani da hikimar ka/ki ba tare da ka/ki ‘batar da wasu ba_.
_*Ka/ki zamo mai adalci, amma kar ka/ki ce sai ka/ki iya wa kowa_
_*Ka/ki zamo mai neman na kai, amma ka da ya kai ka/ki ga neman haram._
45&46
Ko da ya isa Abuja, basket d’in da Ummu ta bashi ya ajiye a falo, bathroom ya shiga ya watsa ruwa ya fito.
Canza shigar shi yayi zuwa k’ananun kaya.
Fridge ya wuce ya d’auki favourite d’in shi wato exotic da glass cup d’in da ke ajiye a saman fridge d’in.
1-sitter ya nemi guri ya zauna ya d’akko dambun naman da Ummu ta zuba mishi ya d’auka ya fara ci, a lokaci d’aya yana kora wa da wannan ruwan exotic din.
Wayar shi da ke gefen shi ya d’auka yayi dialling d’in numban Mus’ab, bugu d’aya, ana biyu Mus’ab ya d’auka.
"Asslamu alaikum Bregadier Faruk na Teemah" abin da Mus’ab ya fara fad’a kenan.
Murmushi yayi don yasan Mus’ab so yake yi ya zolaye shi, amsa wa yayi "Wa’alaikumus salam, kana gida ne?".
"ina gida, ba dai har ka dawo ba?".
"eh na dawo, ina nan zuwa".
"Ok sai kazo".
Remote ya d’akko ya canza channel d’in zuwa tashar Aljazeera yana kallon labarai.
Bayan ya gama abin da yake yi ne ya kasha tv d’in, ya d’auki wannan d’an basket d’in ya nufi block d’in Mus’ab.
Sallama yayi ya nemi d’aya daga cikin kujerun ya zauna, gaba d’ayan su suna kallon wani hausa film mai suna *HAKK’IN RAI* wanda ake haskowa a tashar Arewa Tv.
Maryam ce ta gaishe shi tana tambayar shi mutanen gida.
Amsa mata yayi da duk suna lafiya.
Nana ce cikin zazzak’ar muryar ta gaishe da yaya Faruk.
D’ago kai yayi ya kalle ta wanda sai a lokacin ya lura da ita.
Da fara’a a fuskar shi ya amsa mata yana cewa "ashe ba ki koma school ba?".
"ban koma ba, sai next week".
"Ok" ya amsa a gajarce.
Yamutsa fuska yayi ya maida kallo shi ga Mus’ab yace "wai me kuke fahimta ne a hausa film, ni ban ga abin kallo ba, saboda a tunani na basa film mai ma’ana da wanda za a k’aru, sannan ba yin film akan al’adar su".
Mus’ab ne ya cewa "Ni ma dan ba inda za ni ne, shi yasa na zauna ina kalla, kuma madam na so, dole in biye mata mu kalla".
Maryam ce ta kar’bi zancen da cewa
"Mu dai ba za mu k’i yaren mu da al’adar mu ba duk lalacewar su, kuma Hausa film d’in da kuke Magana, ai akwai masu ma’ana da kuma wanda suke nuni da al’adar su, kamar wannan film d’in da kuke gani da aka sa a Tv, ya ta’allak’a ne akan ku masu kaki, duk da ba duka aka taru aka zama d’aya ba, amma shi wannan d’an sandan saboda kwad’ayin kud’in da zai samu yasa ya d’auki wanda bai da laifi ya kai aka harbe shi, ya saki wanda yake da laifi saboda ya bashi kud’i, k’arshe kud’in shi bai mai amfani ba saboda rai da yakai aka kashe, kaga kenan *Hakk’in Rai* ba zai bar mutum ya samu kwanciyar hankali ba".
Mus’ab ne ya kalle shi da alamar tsokana yace "mutumin ai ban zaci za ka dawo da wuri ba, ina sha ai Fatima za ta rik’e ka".
Murmushi yayi yace "kaima kasan ba yadda zanyi ne na dawo, amma ni ban k’i in zauna gurin Teemah na ba".
Maryam ce ta sa bakin ta a zancen nasu tace "wai Bregadier, kai nake jin kana maganar budurwa? Kai da kake cewa ‘yan mata ba sa gaban ka, amma ko wacece Fatiman nan, ta burge ni da ta kama zuciyar soja" ta k’arasa zancen tana dariya.
Bai ce mata komai ba illa murmushi da yayi.
Basket d’in da ke d’auke da snacks d’in ya ajiye a gaban Maryam yace
"Madam in ba damuwa plsss ga Samosa nan da spring roll za ki taimaka ki soya min, Teemah nasa ta min a d’anyen shi, may be ma ya lalalce saboda naji tace yana da saurin lalacewa".
Mus’ab cikin tsokana yace "ai ko ya lalace sai an soya kaci shi, tun daga hanun masoyiyar ka ya fito, ba zai maka komai ba illa k’ara maka son ta da zai yi".
"kan ka ake ji, naga alamar ka maida ni wani kakan ka" yaya Faruk ya fad’a.
Maryam ce ta bud’e food flask d’in taga bai yi komai ba, kallan Nana tayi tace "Nana d’auka kije kitchen ki soya mai, sai ki zubo mishi a plate yaci a nan".
"To Anty Maryam" ta mik’e ta d’auki basket d’in ta nufi kitchen.
Sai a lokacin ya d’aga kai ya k’ara kallon Nana, yana mamakin shirun ta yayi yawa, dan tun da aka fara maganar ba ta sa bakin ta ba, illah wayar ta da take pressing, bin ta yayi da kallo san da ta nufi kitchen, yana yabawa da natsuwar ta.
Ko da ta shiga kitchen d’in, mai ta d’aura akan wuta, sai da yayi zafi sannan ta fara soya wa.
Cikin ‘yan mintuna ta gama soyawa ta zuba a glass plate, ta had’o da ginger drink d’in da ke cikin fridge wanda sai k’anshin citta da lemun tsami da yake tashi.
Tana zuwa ta ajiye a kusa dashi tace "yaya Faruk gashi".
Da murmushi a fuskar shi yace "sannu da aiki khadijah, an sa ki aiki ko?"
Fad’ad’a murmushin ta tayi tace "ba wani aiki yaya Faruk".
D’aukar wayar ta tayi dake kujeran da ta tashi ta fara tafiya, da alama d’aki za ta tafi.
Yaya Faruk ne ya kira sunan ta
"Khadija".
Juyowa tayi ta kalle shi da oily eyes d’inta ta amsa "Na’am yaya Faruk".
"ya za ki tafi ba ki ci ba".
Rasa me za tace mai tayi, dan haka tace "Samosa da spring roll bai cika damu na ba, na k’oshi ne yaya".
Kallon ta yayi kawai yace "Ok, za ki iya tafiya".
Kamar jira take yi, ta nufi d’aki ba tare da ta k’ara juyowa ba.
Mus’ab ne yace "ko da mu ba a mana tayi ba, bazan yi zuciya ba, ci zan yi in ji ko gimbiyar hannun ta na da zak’i".
Girgiza kai kawai yaya Faruk yayi saboda yasan in ya biye ma Mus’ab sai ya sa shi Magana don ya fi shi Magana.
Yaya Faruk ne ya kalli Maryam yace "bismillah madam, zo ki d’ibi yanda zai ishe ki".
Cikin wasa tace "da ba dan na k’oshi ba, da sai na ci naji, amma dai yanzu a min hak’uri soja, snacks d’in nan ba zai shiga ba".
Shiru ya mata saboda yasan Maryam da tsokana kamar mijin ta, in ya biye musu sai sun sa shi Magana.
Mus’ab ne ya d’auki d’aya yasa a bakin shi, lumshe ido yayi ya bud’e ya kalli Maryam da ta mai da hankalin ta ga tv.
"Maryam! Mus’ab ya kira ta.
Kallon shi tayi tace "ya aka yi ne Nurul k’albi".
Cikin tsokana yace "gaskiya kar ayi ba ke, bud’e bakin ki in sa miki ki ji, snacks sai kace a bakery, kice dole mutumin ya rud’e akan ta".
Dariya tayi tace "tun da naji ka yaba, to lallai Fatima ta ciri tuta".
Bud’e baki tayi, Mus’ab ya d’auki samosa ya sa mata a baki.
Taunawa ta fara yi a hankali tace "wow! Delicious, amma dai Faruk catering Fatima take karanta ko?".
Ta’be baki yayi yace "Santi take karanta".
Gaba d’ayan su suka sa dariya, saboda sun san rama tsokanar da suke mai yayi.
Mik’e wa yayi yace "Ni kin ga tafiya ta, kai da matar ka kun tasa ni a gaba sai tsokana ta kuke yi akan Teemah, bari in na koma Kaduna sai na fad’a mata abin da kuke min".
"Tuba muke yi na Teemah" Mus’ab ya fad’a yana dariya.
Tafiya ya fara yi yana cewa "Maryam sai anjima".
"To sai anjima Faruk".
Mus’ab ne ya mik’e dan ya taka mai.
Nana Khadija tun da ta shiga d’aki, ta fad’a kan gado, ta rasa abin da yake mata dad’i tun da taji an fara zancen Fatima,
Me hakan ke nufi? Me yasa za taji haushi dan yaya Mus’ab da Anty Maryam suna tsokanar yaya Faruk akan Fatima? Mai yasa ba ta ci snacks d’in da ta soya ba, duk kuwa yadda take son Samosa da Spring roll? Hakan na nufin dan ya fito daga hannun Teemah ne kamar yadda ta ji yaya Faruk na kiran ta.
Duk wannan tarin tambayoyin ba ta da amsar su.
Mai yasa yaya Faruk ke burge ni? ta tambayi kan ta.
Zuciyar ta ce ta ba ta amsa akan saboda yana da irin qualities d’in da kike so a gurin namiji, shi yasa kika ji yana burge ki...
Ganin tunanin da ta fara bai da wani amfani yasa ta d’auki wayarta ta kunna cool music tana saurare, a haka bacci ya d’auke ta.
*KADUNA*
Karatun mu ya ci gaba da tafiya da dad’i da ba dad’i saboda matsalolin high institution da ba za a rasa ba.
Yau sanye nake da cotton material kalar pink, yayin da nake sanye da white hijab & flat shoe, jakar dake hannu na kalar pink rik’e a hannu na.
Magana na fara ma Halima wacce ta maida hankalin ta ga rubutun da take yi na ce "Halima bari in lek’a cikin asibiti, kwana biyu ba na jin dad’in jiki na".
Tsayar da rubutun da take yi ta maida hankalin ta gare ni tace "Ayya Sorry Fatima, ki jira in k’arasa rubutun da nake yi sai in raka ki".
"kar ki damu Halima, ki ci ga ba da rubutun ki, nima ba dad’e wa zanyi ba".
"Sai kin dawo, Allah ya k’ara sauki".
"Amin" na amsa mata kana na fita daga class d’in.
Ko da na k’arasa asibitin, ba da kati na nayi a record room, ba a d’au wani lokaci ba naji an kira suna na, bayan naje ne ta tura ni room 5.
Ko da na isa gurin, ba wasu mutane, dan haka ba a d’au lokaci ba aka kira suna na.
Yau sanye yake da wani tsadadden yadi kalar ruwan madara sa’banin ran nan da na ganshi da shigar likitoci, yana sanye da d’an k’aramin medicated glass a fuskar shi, sai k’amshi dake tashi a room d’in.
Zama nayi a kujerar da marasa lafiya ke zama, yau ma rubutu yake yi ba tare da ya d’ago ya kalle ni ba.
Ganin bai ce min komai ba yasa nace "Ina wuni Dr".
"lfy lau, me yake damun ki".
Har a wannan lokacin bai d’ago ya kalle ni ba.
"fever nake fama dashi kusan 1 week kenan".
Sai a lokacin ya dakatar da rubutun da yake yi ya kalle ni.
Kin ce kin kai kusan 1 week kenan kina fama da fever, bayan shi ba inda yake miki ciwo?" Ya tambaye ni.
"gaskiya babu" na amsa masa a tak’aice.
Hannun shi yasa a kan wuya na don jin yanayin temperature d’ina.
Wani irin shock na ji san da ya ta’ba ni, ko dan shi ba muharrami na ba ne yasa naji haka? na tambayi kaina.
Wata farar takarda yayi rubutu a jiki ya mik’o min yace "ga wannan takardar sai ki je lab a miki test duk da nafi tsammanin malaria ce ke damun ki, in kin yi test d’in sai ki kawo min result d’in in gani".
"na gode Dr".
"aikin mu ne, kar ki damu".
Sallama na masa na tafi.
Hakan ta kasance, washegari nayi sammakon zuwa aka d’ebi jini na a laboratory suka ce an jima in dawo, na tafi class, muna gama lectures na first period na koma.
Da na amshi result d’in a laboratory na wuce na kai kati na a record room, tambayar su nayi Dr Abubakar nake son gani, sun fad’a min cewa yau sai da rana yake da aiki, dan haka na koma class da niyyar in in mun gama lectures kan in tafi gida sai in zo in ganshi.
Muna gama lectures d’in na je na musu Magana kasantuwar sun d’auko folder na tun da safe, dan haka suka ce in wuce room 4 yau a nan zai ga patient.
Ina zuwa ban samu mutane ba kasancewar rana ne, hakan yasa na wuce d’akin direct.
Sallama nayi na nemi guri na zuna
Amsa min yayi da murmushi a fuskar shi.
"Fatima ko? ya tambaye ni.
Mamaki ne ya kama ni yadda aka yi har ya rik’e suna na.
Folder na ya d’akko ya ajiye a gaban shi, tambaya ta yayi na yi test d’in da ya ba ni?
Mik’a masa takardar nayi nace "eh nayi".
Sai da ya gama nazarin takardar sannan ya fara rubutu yace "Maleria ce ke damun ki, zan rubuta miki magani".
Takadar ya mik’o min yace in amsa maganin a pharmacy.
"Allah ya k’ara sauk’i student"
"Amin Dr".
Sallama na mishi na bar office d’in.
Tun daga wannan lokacin in ban da lafiya ya zamana gurin shi nake zuwa ya duba ni, sai dai in ba ya nan ne nake ganin wani likitan.
Lokaci na ta tafiya in da muka cinye zangon karatun mu na farko muka fara rubuta jarabawar mu ta farko.
Muna chat da yaya Faruk amma ba sosai ba, kasancewar ya ce min in da suke ba network mai kyau.
Duk san da muka had’u a chat yana k’ara jaddada min irin son da yake min.
A can ‘bangaren yaya Faruk sai ya zama sun fara sabawa da Nana Khadijah kasancewar yana lek’a wa gidan su Mus’ab in kad’aici ya dame shi.
Duk da in yaje ba wata hira suke yi ba kasancewar ita ma Magana ba ta dame ta ba amma yana yabawa da natsuwar ta da kamun kan ta.
A haka har ran tafiyar su tazo suka tafi garin Adamawa.
0 Comments