MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽
*INA SANE DAKU*
_Masoya littafin SILAR KAYAN SALLAH, ina k’ara ba da ku hak’uri akan shirun da kuka ji ni na kwana biyu na rashin posting da wuri, hakan ya faru ne na yadda abubuwa suka yi min yawa, insha Allah zan muku typing d’in shi_.
*QUESTION OF THE DAY*
_Su wa K’urayshawa suka aika lokacin yana mushuriki a lokacin Sulhun Hudaibiyya, da yaga irin son da sahabbai suke ma (S.A.W) ya koma zuwa ga k’urayshawan yace musu ‘Ya ku mutane na, Wallahi hakika na bak’unci sarakuna, na bak’unci Kaisar da Kisra da Najjashi, wallahi ban ga wani sarki shugaba daya da mutanen sa suke girmama shi kamar yadda sahabban Muhammad suke yi ga Muhammadu ba_.
63-64
Yana shiga ya fara ma Anty Jiddah fad’a akan me yasa za ta bar ni in fita gurin Dr, bayan tasan an kusa biki na.
Tabbatar mishi tayi da ba ta san shine yazo guri na ba, da ba ta barni na fita ba.
A lokacin na shigo falon da sallama ta.
Anty Jiddah ce ta amsa min ciki-ciki, da alama ita ma ranta a ‘bace yake.
Yaya Aminu kuwa sai watso min banzan kallo yake yi.
Hakan yasa jiki na yayi sanyi duk da ban san me nayi ba nayi k’arfin halin yi mishi sannu da gida.
Maimakon ya amsa min sai ma nufo ni da yayi.
Ban yi tunanin wani abu zai min ba shi yasa ban gudu ba.
"Daga ina kike" yaya Aminu ya tambaye ni cikin d’aure fuska.
"Abokin yaya Faruk ne yazo, shine ya turo shi guri na ya ba ni sak’o ya kawo min".
Wani irin kallo ya watsa min mai nuna alamar tambaya kana ya ce "Ina sak’on da ya bayar".
Cikin daburce wa na ce "ya… ce… zai…dawo…anjima…yana…sauri…ne…ya …bar…shi…a…".
Ban gama fad’a mai abin da zan ce ya d’auke ni da wani lafiyayyen mari.
Cikin fad’a ya ce "Uban wa za ki raina ma hankali, kina sha ban gane wannan Dr bane, za ki ce min abokin Faruk ne, ban fad’a miki ki rabu dashi kina da wanda zaki aura ba, yau ba gobe ba su Abbu za su ji wannan maganar, na gaji da rufa miki asiri, dama Faruk nasan hak’uri yake yi dake akan abin da kike mai saboda wannan Dr, tun da shi so ya rufe mai ido ba zai iya hukunta ki ba, yau za ki ji a jikin ki, kije ki d’akko jakar ki mu tafi gida".
Kuka na fara yi ina bashi hak’uri akan yayi hak’uri kar ya fad’a ma su Abbu amma bai saurare ni ba.
Ita kanta Anty Jiddah na ba ta haushi, amma ganin kukan da nake yi ne ya karyar mata da zuciya yasa ta fara ba yaya Aminu hak’uri akan ya min hak’uri, ko sauraren ta bai yi ba.
Ganin ban da alamar tashi in d’akko kaya na yasa ya janyo hannu na ya kaini mota ya kulle ya shiga side d’in driver ya ja muka tafi.
Muna zuwa gida ma ya rik’o hannu na kamar wacce ake ma jagora.
Main parlour muka nufa yana ci gaba da min fad’a, yana d’aura laifin ga Dr, wanda ya ce in dai suka had’u sai ya ci mishi mutunci tun da shi yake hure min kunne.
Jin yadda yake aibata Sadik yasa nayi k’arfin halin duk da tsoron dake raina nace Yaya Aminu ka daina ganin laifin Dr Sadik da ni, Allah ne ya jarrabe mu da son junan mu, abu ne mai wuya a ce lokaci guda in cire son shi…".
Maganganun da yaji ina fad’a mai ne yasa shi harzuk’owa ya ficiko AV wire dake manne a jikin DVD ya fara zuga min ita a jiki na.
Dukan da yake min ne yasa na sa kururuwa ina ta kuka, jin kuka na yasa Ummu da Abbu suka fito daga side d’in su suka nufo falon, shi kanshi yaya Khalil yana cikin d’akin shi yana jiyo ihu na, shima a lokaci d’aya suka shigo falon don ganin me yake faruwa.
Yaya Khalil kuwa tun da ya ga dukan da yaya Aminu yake min ya zargi akwai abin da nayi wanda yasa na tunzura yaya Aminu yake min irin wannan dukan, shi yasa bai samu k’arfin zuwa ya cece ni duk kuwa da tausayin da na bashi.
Dukan da suka ga yana min ne yasa Ummu ta daka mishi tsawa.
"Aminu miye haka, wani irin laifi ta maka haka kake mata wannan dukan, so kake yi ka ji mata ciwo".
Jin hakan da yaya Aminu yaji Ummu tayi magana yasa ya dakatar da dukan da yake min ya wurgar da AV d’in, sai faman huci yake yi.
Sai a lokacin Abbu yayi magana ya ce "Ku same ni a falo na".
Gaba d’ayan mu muka nufi falon Abbu, jiki na kuwa ba inda bai min rad’ad’i.
Abbu ne ya kalli yaya Aminu ya ce "Aminu ban ji dad’in irin dukan da kayi ma Fatima ba kasancewar ta mace, kai babba ne, ka fi ta hankali".
Cikin ladabi yaya Aminu ya ce "Kayi hak’uri Abbu, Ummu kema ki yi hak’uri".
Abbu ne ya ce "Ba komai Aminu, dama ba laifi kayi ba, sai dai ina son kasan ita mace a hankali ake bin ta, yanzu fad’a min me tayi".
Yaya Aminu ne ya nisa kana ya ce "Abbu akwai abin da yake faruwa wanda ban fad’a muku ba, ina sha matsalar k’arama ce da ni kaina zan iya shawo kan matsalar ba tare da na sanar daku ba, sai a yanzu nake ganin matsalar ta fi k’arfi na da ya zama dole in sanar daku ita…".
Ummu ce ta katse shi da cewa "Wai wace matsala ce daka ke ta mana kwana-kwana, ka fito ka fad’a mana".
Tun da naji yaya Aminu da gaske ya keyi fad’a musu zai yi, jiki na ya k’ara yin sanyi, ban san yadda za su d’auki maganar a gun su ba, hukuncin da za su yanke min shi yafi tsaya min a rai.
Nan yaya Aminu ya gyara zama ya kwashe duk iya abin da ya sani tsakani na da yaya Faruk da kuma Dr Sadik, da abin da yanzu na fad’a mishi akan Dr.
Shiru d’akin ya d’auka kamar ba kowa a ciki, kowa da irin abin da yake sak’awa a zuciyar sa game dani.
Ni kuwa ina can a ra’be kamar wacce tayi ma sarki k’arya, ba abin da nake yi sai aikin k’ifta idanuwa da nake yi.
Abbu ne ya ja gauron numfashi kafin ya juyo da kallon shi zuwa guri ni ya ce "Fatima, abin da Aminu ya fad’a min gaskiya ne?".
Nasan ko wani abu nake sha bazan kalli idon Abbu in ce mai bana son yaya Faruk ba, na za’bi ba re akan shi, nasan abin da zai min sai ya fi na kowa muni ganin yadda ya d’auki yaya Faruk kamar yaya Aminu, shiru na a wannan lokacin sai ya fi min amfani.
Ummu ce ta daka min tsawa ta ce "Ba dake ake magana ba Fatima kika yi wa mutane shiru, ko mu ma za ki fara gwada mana fitsarar da kika koya ne".
Har yanzu na kasa bud’e baki na in yi magana sai hawaye da ya fara zuba a fuska ta.
Tun san da abin nan ya faru, yaya Khalil bai yi magana ba sai bi na yake da ido.
Abbu ne ya ci gaba da cewa "Fatima ke nake saurare".
Ba ni da wata sauran dabara da ya wuce in fito in fad’a ma Abbu da Ummu abin da yake raina, watak’ila su duba uzuri na su fuskance ni su bar ni da wanda nake so, da wannan na samu karsashin yin magana.
"Abbu kayi hak’uri, nima ba laifi na ba ne, nayi duk wani k’ok’ari akan in sa son yaya Faruk a raina don in faranta muku dashi kan shi yaya Faruk da ya nuna min soyayyar shi har ya zuwa yanzu da ake maganar bikin mu, amma zuciya ta tak’i amsar tayin siyayyar sa, zuciya ta tayi nisa a son Dr Sadik, Abbu da Ummu dan Allah ku tausaya min ku fahimtar da yaya Faruk, nasan zai fahimce ku…" Na k’arasa maganar cikin kuka.
Abbu ne ya kalle ni ya ce "Ina sauraren ki Fatima, yanzu me kike so in miki".
Ba tare da jin tsoron hukuncin da zai biyo daga baya ba na ce "Abbu so nake yi ka ba yaya Faruk hak’uri ya hak’uri ya hak’ura da aure na, Dr Sadik na ke so".
Kowa a d’akin ni yake bi da kallo, a yadda na fahimci kallon da suke min yana nuni da ban san abin da nake yi ba.
Ummu kuwa da ‘bacin ranta ya kasa ‘boyuwa tashi tayi tazo ta tsinka min kyawawan mari lafiyayyu guda biyu, wanda hakan ya haddasa min ganin taurari a fuska ta.
Rabon da Ummu ta kai hannu ta a jikina na manta, bare har ya kai ga ta mare ni.
Yau nasan ran Ummu ya ‘baci kasancewar ta mai hak’uri da sanyin hali, nasan za ta iya min abin da yafi haka in dai akan yaya Faruk ne.
Cike da ‘bacin rai ta ce "In da nasan akan haka Aminu ya dake ki, da ko fito wa bazan yi ba har in mishi magana, Fatima ban ta’ba tunanin hakan daga gare ki ba, ki d’auka wannan maganganun da kike fad’a kamar guguwa ce dan in ta kad’a ta tafi ta riga ta tafi kenan, ci gaba da wannan maganganun zai iya sa ki fuskanci mummunan hukunci daga gare ni, ki kiyaye ni".
Abbu ne ya katse ta daga fad’an da take min "Hajiya k’yale ta ki zo ki zauna".
Ba ta musa mishi ba ta dawo gurin zamanta ta zauna ba tare da ta k’ara cewa wani abu ba.
Kowa idan ka duba yanayin da yake ciki ransu a ‘bace yake.
Abbu ne ya saki murmushin takaici wanda bai kai ciki ba ya ce "Na ji bayanin ki Fatima, ina so ki saurare abin da zan fad’a miki da kyau, wannan maganganun da kike fad’a min wai ba kya son Faruk kina da wanda kike so na d’auke shi shirme ne, Fatima abin da kike so a miki ba mai yiwuwa ba ne, ba na magana biyu, ba ni na had’a ki da Faruk ba bare ki ce za a miki auran dole, hasalima ba ki ta’ba nuna mana ba kya son shi ba sai yanzu da kika ga komai yazo k’arshe sannan za ki bijiro da wata magana mara amfani, ina so ki sani ko da basaid amincewar ki sai kin auri Faruk, ina so ki sani ba ki da wani miji bayan Faruk, zan iya nemar ma Faruk aure a ko ina ne bare ke mallakina, ba ki isa ki lalata mana zumuncin dake tsakani na da d’an uwana da kowa yake sha’awar mu ba wanda tun kan a san za a haife ki muke yin shi, sai ke a rana d’aya da kike so ki wargaza mana shi a lokaci guda, wannan su ne maganganun da zan fad’a miki, shawara ta rage naki, abu na k’arshe da zan fad’a miki shine ban yarda ki k’ara fita daga gidan nan ba sai in ni na umarce ki" Yana gama fad’ar haka ya mik’e ya shiga cikin bedroom d’in shi.
Wani irin kuka na fashe dashi, a lokacin zuciya ta wani irin zafi take min da irin hukuncin da Abbu ya yanke a kaina.
Ummu ce ta d’aura da cewa "Fatima kin bani mamaki, ina ganin ki yarinya mai hankali, ashe ban sani ba kin riga kin canza da yadda na sanki, ki rasa wanda zaki yi ma butulci sai Faruk wanda yake dazumunci da ganin girman manya, za ki nuna kin fifita wani a kanshi, tun yaushe Abbun ki ya raba ki da wannan Dr yace ki bashi hak’uri kina da wanda za ki aura, shine ki ke so ki nuna mishi bai isa dake ba, ki ka ci gaba da soyayya dashi, ko a fuska ki ka nuna ma Faruk wani abu sai nayi mugun sa’ba miki".
Tana gama fad’ar haka ta bar gurin.
Yaya Aminu mik’ewa yayi ya tafi, ko kallon in da nake bai yi ba.
Ya rage daga ni sai yaya Khalil a falon, ina tunanin zai ce min wani abu, ga mamaki na bai ce min komai ba, a fuskar shi na gane shima bai ji dad’in abin da nayi ba.
Tashi yayi ya koma side d’in shi, a raina ina k’ara mamakin canzawar yaya Khalil, in da a da ne yaga an min wannan dukan a gaban shi, ya dinga bani hak’uri kenan, amma yanzu ko magana bai yi min bare in sa ran zai ba ni hak’uri.
Ganin ni kad’ai nayi saura yasa na tashi na tafi d’aki na dan in gasa jiki na, saboda ko ina a jiki na ba in da bai min ciwo.
Tun daga wannan lokacin na rage fito wa falo, ba kuma wanda ya damu da fitowar tawa tun da fushi suke yi dani.
Yaya Faruk na kira na a waya, sai dai hirar tamu ba ta yin wani armashi, saboda komai ya min magana sai na gadama nake bashi amsa, da ya tambaye ni dame-dame nake so ya sa min a akwati, k’in fad’a nayi, da ya matsa min ne nace duk abin da ranshi yake so, size d’ina kawai na fad’a mai, ba yadda bai yi ba akan mu tattauna akan bik’in, amma nak’i, ganin hakan da nake mai ne yasa yayi fushi ya rage kira na sai ya kama yake kira na.
Nana Khadijah kuwa yanzu shak’uwar su sai k’ara gaba take yi da yaya Faruk, yanzu sukan zauna da ita yana jan ta hira, yawancin hirar tasu yana fad’a mata yadda yake so na, hakan yana ba ta mamaki ganin yaya Faruk miskili wanda bai damu da kula mata ba a yanda ta ji yaya Mus’ab na yawan fad’a sai take mamakin yadda yake fad’a mata yanda yake so na, lallai ta tabbatar da son da yake min ba k’aramin so ba ne, ba ta san bikin yaya Faruk ya kusa ba, sai da taje gidan su yaya Mus’ab ne taji suna maganar bikin da Anty Maryam, tun san da taji maganar bikin ta rasa yadda za ta fassara yadda take ji a ranta, ganin abin zai dame ta yasa ta watsar da tunanin da yake so ya zamar mata matsala.
Lokacin da suka had’u da yaya Faruk ne take mishi fatan alkhairi a auran da zai yi, ta kuma mishi k’orafin me yasa bai fad’a mata bikin shi ya kusa ba, ya bata hak’uri akan mantawa yayi, shi kanshi yaya Faruk yana ganin mutuncin Nana Khadija saboda yadda ta d’auke shi kamar yayan ta, sannan natsuwar ta da kamun kanta da rashin hayaniyar ta na d’aya daga cikin abin da yasa yake ganin mutuncin ta, shima sai yake jin ta kamar k’anwar shi, ko su yaya Mus’ab da Anty Maryam suna mamakin yadda yake zama yana hira da ita duk da dukan su ba ma’abota surutu ba ne.
Yau ina zaune a d’aki na kamar yadda na sabar ma kaina, yaya Khalil ne ya shigo da sallamar shi.
Amsa mishi nayi na kau da fuska, saboda shima yanzu ya shiga cikin sahun wanda ba su damu dani ba.
Murmushi kawai yayi ganin yadda nayi.
"Fatima zuwa nayi in baki shawara a matsayina na d’an uwanki, wanda ya damu da damuwar ki, wanda kuma bai son ki sa kan ki a wani hali".
Jin ban ce komai ba yasa yaci gaba da cewa "Fatima, abubuwan da kike yi sam bai kamata ba a matsayin ki na ‘ya mace, da nayi niyyar in zuba miki ido kamar yadda kike so a k’yale ki, sai na ga bazan iya ba, yanzu har kin manta sharad’in da na gindaya miki in dai kina so mu shirya shine ki so yaya Faruk, ko da yake na lura dake za ki iya ‘bata wa da kowa in dai akan Dr ne, tun da yanzu gashi kin za’bi ki zauna a d’aki ke kad’ai kina ganin in kika yi hakan za a gane kina fushi, to bari in fad’a miki ki ji, ki hak’ura da Dr Sadik tun da su Abbu da Ummu sun nuna sun fi son ki auri d’an uwan ki, ni da yaya Aminu ma mun fi son ki auri yaya Faruk d’in, me zai sa ba za ki duban hakan shi zai fi miki zama alkhairi tun da kowa shi yake so ki aura, duk abin da kika ga yawan mutane nak’i to ya kamata ka hak’ura dashi duk kuwa da son da kake mishi, zai iya yiwuwa abin ba alkhairi ba ne a gurin ka, ko da yake ke kin yi nisa a makauniyar soyayyar da ba za ki fahimci hakan ba, wannan shawarar ina baki ita ne a matsayina na yayan ki, nasan komin daren dad’e wa zaki tuna da shawarar da na baki, nasan a yanzu ba lallai ki d’auki hakan da mahimmanci ba, ki zauna ki yi karatun ta natsu ko dan gudun ‘bacin ran iyayen mu da kuma zumuncin mu da zaki ja ya samu rauni ta dalilin ki, ina fatan za ki yi amfani da shawarar da na baki, na barki lafiya" yana gama fad’ar haka ya bar d’akin ba tare da yaji nawa jawabin ba.
Tabbas nasan duk abin da yaya Khalil ya fad’a gaskiya ne, ni kaina da zan iya amfani da shawarar da suke bani da na bi, sai dai matsalar zuciyata da ta riga ta daina d’aukar shawarar kowa a dalilin son Dr.
Kasancewar takunkumin da Abbu yasa min na hana ni fita, ba k’aramin takura min yayi ba, yanzu ba ni da halin had’uwa da Dr sai dai a waya, na fad’a mishi duk halin da ake ciki, ya nuna min da kar in damu da duk abin da za’a min in dai zamu cin ma burin mu.
Son da nake ma Sadik bai sa na hango illar abin da nake yi ba, ni ko da yaushe shine in kasance da son Dr a raina.
Da wannan nake samun k’arfin gwiwa amma a maganar gaskiya halin da ‘yan gidan mu ke nuna min a yanzu na damu na, dan duk wanda yasan ni a da yasan na canza dan har wata ‘yar rama nayi.
Duk wata kulawa da Ummu da su Abbu har ma da yaya Khalil suke nuna min a da, yanzu babu wannan.
Gashi yanzu shirin mu da Anisa yaja baya, ba wani cika zuwa tayi ba tun san da tazo gidan mu muka samu sa’bani da ita akan maganar yaya Faruk, duk da ina kewar ta kasancewar yadda muka shak’u tun muna yara, hakan ba zai sa in rabu da burin zuciya ta dan in faranta mata, muna waya da ita jefi-jefi.
Ranaku na ta wuce wa inda bikin mu ya kasance yau saura sati uku, a ranar kuma aka kawo akwatina Set biyu aka kawo, dana Abbu da ya had’a da na yaya Faruk, kowane set akwatuna uku ne da kit, haka ma na yaya Faruk, kowane set da kalar sa, kaya ne na gani na fad’a, akwatunan kad’ai abin kallo ne bare aje ga kayan dake ciki, baki ba zai iya fasalta kayan da ke ciki ba, sai dai gani da ido.
A ranar ne na samu na rok’i Abbu akan ya barni in je gidan su Halima, jin inda zani yasa Abbu yasa yaya Khalil ya kaini ya d’akko ni.
Ko da muka je gidan su Halima, da k’yar yaya Khalil na rok’e shi akan yaje ya dawo, da cewa yayi sai ya jira ni.
Ina shiga muka gaisa da Maman su kana muka wuce d’akin ta.
Hira muka dasa ta yaushe gamo, mai aikin su ce ta kawo min kayan abin sha da abinci.
Ko kallon abincin ban yi ba saboda a halin damuwar da nake ciki, nafi buk’atar mai kwantar min da hankali akan wani abinci.
Drinks kad’ai na d’auka na sha.
Halima ce ta matsa min da tambayar dalilin ramar da nayi, ganin abokin kuka ake fad’a ma mutuwa yasa na kwashe komai na fad’a mata har ya zuwa yanzu halin da nake ciki.
Halima ce ta numfasa kana ta ce "Gaskiya Fatima kina cikin wani hali, dole ne a tausaya ma halin da kike ciki, sai dai gaskiya ni ban goyi bayan ki akan ki tafi wani gurin ba, gwara ki ta ba su Abbu hak’uri akan su baki wanda kike so, ki ci gaba da nuna musu yadda kike jin Dr a ranki da halin da za ki iya shiga idan bashi kika aura ba, nasan za su fahimce ki, ko kuma kije ki samu Dadin su yaya Faruk d’in ki mishi bayani, nasan shi zai son farin cikin d’an shi dan ba zai so d’an shi ya auri wacce ba ta son shi, haka kuma ba zai so zumuncin su ya samu rauni saboda wannan auren ba".
Girgiza mata kai nayi kana na ce "Halima ba wata dubarar da zan bi wadda ta fi min sauk’i shine in yi tafiyar, gurin da zani ba mai cutar wa bane, da kunya in tunkari Dadin su yaya Faruk da wannan maganar, gaskiya ba zan iya ba, Dadi da Momi sun nuna min soyayya, su Abbu ba za su saurare ni ba, dan ba ki ga yadda suka nuna ‘bacin ransu akan maganar nan ba ne, yaya Faruk ma ba zan iya tunkarar shi da wannan maganar ba dan ba zan so ya shiga wani hali sabo dani ba, kawai dai ki taya ni da addu’a, Allah yasa komai yazo cikin sauk’i".
Cikin tausayawa Halima tace "Amin dai Fatima, insha Allahu zan dinga sa ki a addu’a ta".
Da k’yar Halima ta tilasta min na ci abincin da mai aikin su ta kawo min, ba laifi na ci abincin dan na dad’e ban ci abinci mai yawa irin shi ba.
Haka Halima taci gaba da bani shawarwari, hak’ik’a na ji dad’in shawarwarin da ta bani.
Kiran yaya Khalil ne ya katse mana hirar da muke yi, sanar da ni yayi ya na k’ofar gida yana jira ma, sallama muka yi da ita, mun yi da ita akan sai mun had’u da ita ta waya.
Ko da muka koma gida ban nuna musu komai ba, Falo nazo aka yi ta hira dani.
A fuskar su kad’ai da na kalla na gane sun yi farin ciki da yadda na sake, da alama na hak’ura da k’udiri na.
Jin dad’in hakan ne yasa bayan na koma d’aki Ummu ta shigo ta k’ara min nasiha tare da bani magungunan da za su gyara ni.
Saboda ban son tayi fushi dani yasa na amshi magungunan nashi ba wai magungunan na da dad’i ba, hasalima wasu da nashi ji nake yi kamar in yi amai.
Abbu ma ya kira ni ya k’ara min nasiha, na nunar mishi da ba komai na hak’ura.
San da Ummu ta ce in zo in ga kayan akwati ban mata musu ba, dan bana son ta zargi ko har yanzu ban hak’ura ba, gaskiya iya had’uwa akwatunan nan ya burge ni, kai da gani kasan mai tsada ne, kayan ciki kuwa nasan kud’i yayi kuka, nasan ko Dadi da Momi kad’ai Allah kad’ai yasan kayan nawa suka zuba a ciki, bare har da na yaya Faruk da yace zai k’ara min.
Ko ni idan na ce kayan bai min ba na fad’i son raina ne, gaskiya sun yi bajinta a akwatinan da aka kawo.
Haka Ummu tasa mai gyaran jiki ta zo ta fara min gyaran jiki.
Anisa ma tazo dan mu tattauna akan yadda bikin zai gudana, na sanar da ita da cewa ba wani event da zanyi sai walima, da ta matsa min ne na ce na bar mata wuk’a da nama, ta tsara duk yadda take so bikin ya gudana, hakan da na ce mata taji dad’i.
Yau bikin mu ya rage saura kwana goma, sai shirye-shirye ake yi ko ta ina kasancewar abin na gida ne, a yau ne kuma muka shirya tafiyar da zanyi ni da Dr.
Kayana na h’ada a irin jakar matafiya, na d’ebi abin da zan buk’ata.
Sai da fito falo na ga ba kowa, dan gudun a sami matsala sai da na je d’akin Ummu na ga tana bacci, dama nasan Iya Talatu ba ta nan Ummu ta aike ta, haka na k’ara fita parking space na ga ba motar yaya Khalil, daman nasan Abbu baya nan.
Da wannan na samu k’arfin gwiwa na d’akko jaka ta na fito cikin sand’a dan kar wani yaji takun tafiya ta.
Cikin sa’a san da nazo bakin gate ba kowa, dan haka da sauri na bud’e k’ofar a hankali na fita.
San da na fito daga gidan ne naji wasu hawaye sun zubo min masu zafi, zuciya ta na k’wa’ba ta akan abin da zan aikata ba mai kyau ba ne, zuciya ta na umarta ta da na koma, abin da nake shirin aikata wa zai iya janyo min fushi a gurin iyaye na da ‘yan uwa na, idan na tuna da in da za ni bai da wani matsala, zan dawo idan lokacin bikin ya wuce, da wannan na samu k’arfin gwiwar tafiya.
Can bayan layin mu maka had’u da Dr kasancewar dashi zamu yi tafiyar.
Ina zuwa ya bud’e min mota na shiga muka d’au hanyar barin garin.
[6/30, 21:10] Maryam Ahmad: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*FATAN ALKHAIRI*
_Atika Bashir_
_Khadijat Ahmad_
_Murjanatu Bukhari_
_Ameenat Umar Abdullahi_
_Aisha Ibrahim_
_Da sauran fans na Kainuwa Writers Association na Facebook group_
_Amsar question of the day shine Urwatu bn Mas’ud As-Sakafiy (RA) shine wanda k’urayshawa suka aika lokacin yana mushiriki a lokacin Hudaibiyya_.
65-66
Muna fara tafiya na cire sim d’in dake waya ta nasa sabon sim d’in da Dr ya kawo min wanda zamu dinga waya dashi.
Tun da muka d’auki hanya na kasa yin magana, in ban da hawayen da ke ta zubowa a ido na ba abin da nake yi, tunanin gida kawai nake yi da halin da zasu shiga idan suka san ba na nan, danasani na fara yi akan wannan shawarar da muka kawo na tafiya ta.
Dr ne ya lura da halin da nake ciki ya fara lallashi na da kwantar min da hankali, hakan yasa na d’an saki jiki na duk da abin na damu na a raina.
Ba mu sauka a ko ina ba sai a garin Wagini.
Ni na dinga nuna ma Dr hanya har muka kai gidan Hajiyan Wagini.
Bayan yayi parking ne ya kalle ni yace "Pls Zarah kar kisa kan ki a damuwa, ni kaina ba zan so in gan ki cikin damuwa ba, hakan da muka yi shine mafita a gare mu, kuma kin ga ba wani bak’on guri za ki zauna ba, gurin kakar ku ce, komai zai zama normal, za mu dinga waya, kin ga ba hali in dinga zuwa ina duba ki saboda kar a samu matsala amma in na samu sauk’in aikin zan yi k’ok’ari in lek’o ki, sai dai in nazo in fad’a miki in da za mu had’u don gudun samun matsala".
Narai-narai nayi da ido, ji nake yi kamar in fashe da kuka saboda halin da nake ji na a yanzu.
Girgiza min kai Sadik yayi alamar kar in yi kuka.
Kasa daurewa nayi na fashe da wani irin kuka mai tsuma rai.
Kallo na kawai Dr yake yi, da alama shima jikin shi yayi sanyi da halin da nake ciki.
Cikin tattausan lafazi Dr ya fara magana "Zarah in har hankalin ki bai kwanta da wannan hukunci da muka yanke ba gwara in maida ke gida ki auri d’an uwan ki, ni sai in hak’ura, tun da muka tawo kike cikin wani yanayi har muka kawo, gashi kuma tun kan a je ko ina kin fara kuka, ba zan so ta dalili na ki shiga wani hali ba".
Ina jin Sadik ya fara maganar sai ya hak’ura da ni in auri yaya Faruk tun da zan sa kaina a damuwa nayi saurin dawowa da natsuwa, nasan in har na koma gida ba abin da zai hana Abbu aura min yaya Faruk, hakan na nuna cewa nayi bankwana da Dr kenan.
Murmushi na sakar ma Dr duk da iya le’be na ya tsaya na ce "Dr in na tuno halin da su Ummu za su shiga ne sai hankali na in ji ya tashi, zan yi k’ok’ari in ga na rage damuwa, fatana mu kasance a tare dakai".
"Yawwa Zarah ina so in koma, kin ga yamma tayi, ba na son yin tafiyar dare".
Jiki na ne ya k’ara yin sanyi na tafiyar da Dr zai yi, yanzu ganin shi zai min wuya tun da ban san lokacin da zai sake zuwa ba.
Kamar ya san abin da nake tunani kenan ya ce "Haba Princess Zarah, don’t put yourself in worry, ai za mu dinga waya kuma insha Allah zan samu time in zo in duba ki".
Wayar shi da ya fara ringing ne ya katse me mai maganar da yake yi, ya kalli Screen d’in wayar kafin ya juyo ga kallon shi gare ni ya ce "Zarah bari in k’arasa, Dr Kamal ne yake kira na, ina jin ana nema na a asibiti ne".
Karyar da kai na nayi cikin muryar shagwa’ba na ce "Dr ka tsaya ko ruwa ne ka sha, yanzu in na shiga cikin gida sai Hajiyan Wagini ta tambayi waye ya kawo ni, in na ce direban gidan su Momi ne ya kawo ni, sai ta ce a kai mishi abinci da abin sha, kaga in har ka tafi zata iya d’ago ni, bari in shiga ciki in fito".
Fita nayi daga motar na d’auki ‘yar jaka ta na shiga cikin gidan.
Samun Hajiyan Wagini nayi zaune a falon ta.
Ina sallama na fad’a jikin ta ina murna.
Itama dariya ta fara yi ta amsa min sallamar tana cewa "Ja’ira d’aga ni kar ki k’arasa min k’afar tawa".
K’ara lafewa nayi a jikin ta ina dariya na ce ‘Ke Hajiya dan ma kin samu na hau wannan k’afar taki, yaushe rabon da ki samu wanda ya hau".
"Ai yanzu wannan k’afar tawa ta fi k’arfin ki, sai dai kuma ki bar ma ‘ya’yan ku da za ki haifa min ke da Soja marmari daga nesa, Allah sarki ina mai gidana na kaina, kwana biyu ba mu yi waya dashi ba…".
Katse ta nayi da cewa "Kai Hajiya yanzu in kika fara zaro zancen nan ba tsayawa za ki yi ba, ni na manta da direba a waje, ko ruwa ban kai mai ba".
"Au Allah sarki, Malam Lawal ne ya kawo ki, shine dan shashanci baki ce ya shigo mu gaisa ba, maza jeki ki ce ya shigo ciki, sai ki bud’e mai d’akin bak’i, akwai abinci a kitchen kije ki d’akko mai".
Jin Hajiyan Wagini za ta iya gano wanda ya kawo ni in har na shigo dashi yasa na ce mata "Hajiya sauri yake yi, bai so ya yi tafiyar dare, ruwa kawai yace in kai mai ya sha".
Ko iska zai bi k’arewar sauri da yake yi, ai dai ma gaisa ko’ tana gama fad’ar haka naga ta d’akko wani mayafi dake kan hannun kujerar ta.
Jin Hajiyan Wagini za ta bod’e min yasa na ce mata "To bari in je in ce ya shigo ku gaisa Hajiyan mu ba sai kin fita ba, tun da k’afar taki ta zama a lalla’ba" Na k’arasa maganar da wasa.
Ita ma cikin wasa Hajiyan Wagini ta ce "Ki yi addu’a ma k’afar ki tayi k’warin irin tawa".
Kitchen na shiga na d’akko drinks da ruwa, na zuba a d’an madaidaicin tray na nufi k’ofar gida.
Bud’e bayan k’ofar motar nayi na zauna, ganin haka yasa shima Dr ya fito daga gaban motar ya dawo baya.
"Sorry Dr, na barka kai kad’ai ko" na fad’a cikin siririyar murya.
Wani kallo ya jefo min mai isar da sak’wanni da dama ya ce "kar ki damu Zarah".
Tsiyaya mishi ruwa nayi a glass cup na mik’a shi, amsa yayi ya sha kad’an ya ajiye yayin da ya d’auki Viju milk yana sipping.
Mun d’an ta’ba hira dashi kana muka yi sallama da Dr ina d’aga mishi hannu shima yana d’aga min, tunanin kewar shi da zanyi kawai nake yi.
Sai da naga tafiyar shi kafin na koma cikin gida.
Hajiya ce ta kalle ni ta ce "Ina kuma Malam Lawal d’in na ga kin shigo ke kad’ai".
"ya tafi, yace in gaishe ki".
"Au yanzu sai da ya tafi bai shigo mun gaisa ba, ai shi kenan".
Sanin in na zauna Hajiya ce zata dame ni da tambayoyin ta, shi yasa na wuce d’aki na barta a falo.
A can ‘bangare su Ummu kuwa, bayan ta tashi daga bacci ne ta fito falo, ta dad’e a zaune ba ta ji motsi na ba, hakan yasa ta tashi ta tawo d’aki na dan ta duba ni.
Ganin ba ta ganni ba yasa ta duba cikin band’aki na amma ba ta ganni ba, haka ta dinga duba ko ina a gidan ba ta ganni ba.
Mamaki ne ya kama ta dan ita tasan ba muyi da ita zan fita ba.
Fito wa tayi harabar gidan, sunan wanda yake musu gadi ta dinga kira.
"Malam Musa! "Malam Musa!
Jin kiran da Ummu ke mai ne yasa ya fito daga d’an d’akin shi dake can gefen gate ya tawo da gudu.
"Hajiya gani" Malam Musa ya fad’a cikin ladabi.
Ummu ce ta ce "Daman tambayar ka zanyi, ba ka ga fitar Fatima daga gidan nan ba, na tashi daga bacci ne na ga ban ganta ba".
"Gaskiya ban ga fitar ta ba, ina jin ko lokacin da na shiga band’aki a lokacin ta fita".
"Ba komai Malam Musa, za ka iya tafiya" tana gama fad’ar haka ta juya cikin falo.
D’akko wayar ta tayi ta kira Anty Jiddah ta tambaye ta ko na zo gidan ta, nan Anty Jiddah ke sanar da ita ban zo ba.
Haka Ummu ta kira Anisa ta k’ara tambayar ta ko na zo gidan, ita ma sanar da ita tayi ban zo ba.
Duk inda Ummu take tunanin zanje, ta kira ta tambaya an tabbatar mata da ban zo ba.
Gashi tana ta kiran numba ta ba ta shiga ba, ganin haka yasa Ummu ta kira Abbu ta sanar dashi halin da ake ciki.
Ko minti ishirin ba a d’auka ba sai ga Abbu da yaya Khalil sun shigo a tare.
Abbu ne ya kalli Ummu wanda hankalin ta ya fara tashi ya ce "Hajiya ya aka yi Fatima ta fita ba ki sani ba, kuma ba gidan k’awayenta ta tafi ba?" ya k’arasa maganar da tambayar ta.
Ummu ce ta nisa ta ce "Na tashi daga bacci sai na ji ban ji motsin ta ba, na shiga d’akin ta ma ba ta nan, na kira gidan su Jiddah da Anisa ba taje can ba, har k’awar ta d’in nan Aisha ita ma na kira ta tace min ba ta je can ba, na kuma tambayi Malam Musa yace bai ga fitar ta ba, sai dai Khalil yaje gidan wannan k’awar ta Halima yaga ko can taje".
Abbu ne ya kalli yaya Khalil ya ce "Khalil je ka gidan k’awar Fatiman ka ga ko tana can".
"Toh Abbu, bari inje in gani" yaya Khalil ya amsa kana ya juya ya bar falon.
Abbu ne ya nisa ya ce "Kar ki damu Hajiya, insha Allahu ba nisa tayi ba".
Ummu ta ja gauron numfashi ta ce "Allah dai yasa Alhaji".
"Amin".
ya fad’a a tak’aice.
*************************
Yaya Khalil ya je gidan su Halima ya tambaye ta ko na zo gidan, ita ma ta tabbatar mishi da ban zo ba.
Ganin yanayin yaya Khalil yasa taji tausayin shi, tasan suna cikin wani hali gurin nema na, matsalar da aka samu shine ban fad’a mata inda za ni ba, dama tun farko ita ba ta bada goyon baya na wajen yin tafiyar nan ba, da haka suka yi sallama da yaya Khalil ya dawo gida jiki a sanyaye.
Tun da na shiga d’akin Hajiyan Wagini na ajiye kaya na, cire kaya na nayi na shiga band’aki na watsa ruwa, na nemi kaya marasa nauyi nasa na fito na nufi kitchen na d’ebo abinci da ruwa na dawo falo.
Zama nayi kusa da Hajiyan Wagini na fara cin abinci muna d’an yin hira da ita.
Cikin hirar ne Hajiya ta kalle ni ta ce "Fatima lafiya na ganki a garin nan ke kad’ai alhalin bikin ki ya kusa, mu da muke shirin zuwa biki sai kuma in gan ki kinzo" ta k’arasa maganar tana kallo na.
Ban so Hajiya ta fahimci plan d’ina da wuri, na fiso sai ta tashi tafiya Kaduna in bijire mata in k’i bin ta, zan fito in fad’a mata k’udiri na akan fasa auren yaya Faruk, nasan ba k’aramin rigima za mu yi da ita ba, zanyi duk iya yi na in shawo kanta akan tasa su Abbu su fasa auran mu.
Murmushi nayi na ce "Hajiya zuwa fa nayi in miki sallama, shine kuma yanzu za ki tsare ni da tambayoyin ki, sai in ma yi zuciya in koma".
Hajiya ce ta ce "Ka ji ni da ja’irar yarinya, to koma mana, ba dole in tambaye ki ba, na ganki kwatsam ke kad’ai kuma nasan a Kadunan ana can ana ta shirye-shirye".
Shiru na mata taci gaba da maganganun ta, nasan ci gaba da tanka mata zai iya jawowa ta wargaza min shiri na, gwara in samu mu rabu da ita lafiya.
Ina gama cin abincin na kai plate d’in kitchen, ban dawo falo ba na wuce cikin d’aki don muyi waya da Dr.
Ido na ne yakai kan wayar Hajiyan Wagini, tashi nayi da sauri na sa ta a flight mode yadda in an kira za aji ta a kashe alhalin a kunne take, nasan za ta iya kiran Abbu ko Dadi taji dalilin zuwa na ko kuma su za su iya kiranta su tambaye ta ko na zo Waginin.
Waya na zauna muka sha da Dr kamar kar mu rabu, lallai na yadda ba abin da yakai soyayya dad’i musamman in ka had’u da wanda kuke so junan ku, sanar dani yayi yana hanya, idan ya k’arasa Kadunan zai kira ni, sallama muka yi dashi akan sai ya kira ni.
Yaya Khalil haka ya dawo ya sanar dasu cewa ban je gidan k’awa ta ba.
Haka aka ci gaba da kira na amma ba a samu na, wayar a kashe take, Ummu najin haka ta soma kuka tana cewa "Oh ni Aisha, Allah kasa yarinyar nan ba wani gurin ta tafi ba".
Abbu ne yaci gaba da lallashin Ummu akan ta daina kuka, a zuba ido a gani zuwa anjima, idan ban dawo ba sai a san matakin da za a d’auka.
Su kansu idan ka ga gansu, kasan suna cikin wani hali na tashin hankali.
Abu wasa-wasa sai gashi har dare ba a ganni ba, hakan yasa yaya Aminu wanda yazo gidan tun san da ya koma gida Anty Jiddah ta sanar dashi halin da ake ciki ya tawo gidan yace ko za a je a tambayi Dr ne ko yasan inda nake.
Abbu ne ya hana yaya Aminu zuwa, yace in aka yi hakan ba a kyauta ma Dr ba, tunda ba a da tabbacin ko yasan inda nake, kuma hakan zai iya jawo wata matsala, ni ai ba yarinya ba ce, a dakata a gani ko zan dawo.
Har dare ban dawo ba, shi kanshi Abbu ya rasa wace hanya zai bi ya shawo kan matsalar, gashi ya kasa d’aukar waya ya kira Dadi da Hajiyan Wagini ya fad’a masu halin da ake ciki, ganin dare yayi ne Abbu yasa kowa ya tafi ya kwanta, ko a ranar a nan yaya Aminu ya kwana, sai kiran Anty Jiddah yayi ya fad’a mata ba zai samu dawowa ba, a gidan su Ummu zai kwana.
Haka kowa a ranar yayi kwanan k’unci da fargaba, ba wanda yayi barcin kirki a cikin su.
Ummu kuwa da Abbu ba a san wanda yafi shiga tashin hankali ba, ba wanda ya rintsa a cikin su.
Dukkan su tunanin su yazo d’aya akan cewa na gudu ne ba ‘bata nayi ba, shi yasa Abbu bai samu k’arfin gwiwar kai report police station ba.
Washegari ne Abbu ya kira Dadi akan yana neman shi, wata ‘yar matsala ce ta taso.
Ba a d’au wani lokaci ba sai ga Dadi ya zo gidan.
Abbu ne yake sanar da Dadi ba a ganni ba, basa tunanin ‘bata nayi, sun fi tunanin guduwa nayi dan ra’ayin kaina.
Tun da Dadi yaji wannan labarin ya dinga ma Ummu da Abbu fad’a akan ya hakan ta faru.
Abbu na ganin babu wani dalili da zai ‘boye ma Dadi abin da yake faruwa tun da na riga na tona musu asiri, gwara ya fito ya fad’a mishi komai, hakan yasa bai ‘boye ma Dadi halin da ake ciki ba game da halin da muke ciki tsakani na da yaya Faruk da kuma Dr, har zuwa rashin gani na da ba ayi ba.
Abbu ne ya d’aura da cewa "yaya ina neman afuwar ka akan ‘boye maka halin da ake ciki da nayi, ina ganin na isa da Fatima da zan ba ta umarni tabi, ashe abin ba haka yake ba, soyayyar wani ta fini mahimmanci a gurin ta da har ta za’be shi akan bin umarni na, A yau da a ce ina da wata ‘ya macen ban da Fatima da na ba Faruk ita, ina rok’on alfarma a gurin ka yaya kar ka hana ni, ina so in nuna ma Fatima ni na haife ta ba ita ta haife ni ba, zan aura mata aure da Faruk a rananr da aka tsara ba tare da an fasa ba, sai dai in ta mutu da auran shi a kanta, zan nuna wa Fatima ni ba irin uban nan ba ne da zasu bi son ransu su faranta ma ‘ya’yan su akan abin da suke so" ya k’arasa maganar cikin takaici.
Dadi ne yaja gauron numfashi kana ya ce "Ibrahim ba ka kyauta min ba na ‘boye min halin da ake ciki na tsakanin Fatima da Faruk, dukkan su ‘ya’yan mu ne kuma ba za a tauye ma kowa hak’k’in shi dan mu faranta ma d’aya daga cikin su ba, ita soyayya Allah ne yake sa ta a zuciyar mutum, ba a tilasta wa d’an adam sai ya so wani, in Allah bai nufa yaso wanin ba zai ta’ba son shi ba duk kuwa da kusancin su, nasan Fatima ba ta kyauta ba da ta za’bi hanyar guduwa akan tana ganin shine maslaha a gare ta, da ni ta zo ta sama ta fad’a min halin da take ciki da abin bai kai ga haka ba, yanzu abin da yafi mahimmanci shine a samu a san inda Fatiman take, in yaso daga baya a samu mafita akan wannnan al’amarin.
Abbu cikin ‘bacin rai yace "yaya kayi hak’uri da abin da zance, ni dai da kaina ba zan sha wahalar neman Fatima ba, bayan nasan guduwa tayi, taje duk inda zata tun da tana ganin hakan shi yafi mata".
Ummu ce cikin kuka ta ce "Alhaji kayi hak’uri da abin da ya faru, yaro ne ka haife shi ba ka haifi halin shi ba, menene amfanin neman yarinyar da ba za tayi wa iyayen ta biyayya ba, abin da kake ji yana faruwa ko ka kalla a talabijin shine yau ‘yar ciki na ta aikata, abin da bai ta’ba faruwa a dangin mu ba amma ta sanadiyyar yarinyar da na haifa sai gashi ta aikata".
Murmushi kawai Dadi yayi ya ce "Kar ki damu Aisha, komai zai zo da sauk’i insha Allah, ni zan koma, da yardar Allah za a ganta".
Sallama ya ma su Ummu yayin da suka jera da Abbu suna ci gaba da tattauna matsalar, Dadi ne yake ta ba Abbu baki akan ya d’auki komai da sauk’i, kar ‘bacin rai yasa ya d’auki mummunan mataki.
Yaya Faruk tun da ya koma Abuja ya ci gaba da ayyukan shi, sai dai matsalar da muke samu dashi na yawan fad’o mishi a rai, yana ganin komai ya kusa zuwa k’arshe tsakanin shi dani in har aka yi auren shi kenan, yasan wuyar ta ayi auran mu, yasan yadda zai yi ya shawo kaina in fad’a cikin zazzafar soyayyar shi, yana da hanyoyi da dama da zai bi da ni in kamu da son shi cikin sauk’i, da irin wannan tunanin yake jin sauk’i a ranshi.
Yau yana zaune a falon yaya Muhsin suna hira, yayin da Nana Khadijah ke zaune a d’aya daga cikin kujerun dake falo tana karanta wani hausa novel mai suna *SANADIN KADDARA* tattauna wa suke yi akan yadda bikin zai gudana, hankalin ta ya kasu kashi biyu, d’aya yana ga littafin da take karantawa, d’ayan yana ga tattaunawar da su yaya Faruk ke yi akan bikin shi, ba tasan me yasa in dai aka yi maganar bikin yaya Faruk take jin wani iri a ranta ba, ta rasa yadda za ta fassara wannan lamarin da yake damun ta, ba kuma wanda take ganin za ta iya fad’a ma wa dan kar a canza mata manufar ta, ita dai abin da ta sani shine yanzu sun yi sabo da yaya Faruk wanda ita kanta take mamaki, sai dai a yanzu jikin ta nayin sanyi in ta tuno da auran da zai yi, tasan dole ne ta ja jikin ta daga gareshi a dalilin auran da zai yi.
Yaya Faruk ne ya kira sunan ta "Khadijah!
Kiran sunan ta da yaya Faruk yayi shi ya katse mata tunanin da take yi.
"Na’am yaya Faruk" Nana ta amsa mishi cikin sanyin ta.
"Ina fatan normal, naji kin yi shiru ne ba ki ce komai ba".
Tsadadden Murmushi tayi kana ta ce "Ba komai yaya Faruk, novel d’in nan ne ya d’auke min hankali".
"Ok hakan na da kyau" shima ya fad’a yana murmushi.
Ta’be baki Mus’ab yaya ya ce "Kaima ai kasan wannan miskilar ba lallai ne kaji maganar ta ba, ko da yake naga ai taku tazo d’aya kuna hira, ko dan jirgin miskilancin tare ya d’ebo ku ya ajiye ku a airport d’aya ban sani ba".
Dariya yaya Faruk yayi wanda hakan ya k’ara fito da kyawun shi ya ce "Kai fa Mus’ab iskancin ka yawa gare shi, yanzu ina ruwan ka a cikin maganr mu, ko kai na tambaya".
Dariya shima Mus’ab yayi ya ce "Sorry Bregadier Faruk angon Fatima".
Murmushi kawai yaya Faruk yayi bai ce komai ba.
Wayar Mus’ab ce tayi k’ara alamar kira ya shigo.
Bayan ya gama amsa kiran ne ya kalli yaya Faruk ya ce "Ka ga ina da appointment da Birgedier Aminu na manta, shine ya kira ni yana jira na, bari in je in dawo, pls ka jira ni".
"Kawai dai ka same ni a Block d’ina tun da ban san time d’in da za ka dawo ba, idan muka gama hira da Khadija zan tafi" cewar yaya Faruk.
"Ba matsala, sai mun had’u a can kenan".
"Ok sai mun had’u" yaya Faruk ya amsa a tak’aice.
Muhsin ya juya kallon shi ga Nana Khadijah ya ce "In Maryam ta tashi daga bacci, kya fad’a mata na d’an fita".
"Sai ka dawo".
Nan suka yi musabaha da yaya Faruk ya fita daga falon.
Jefi-jefi suke yin hirar kasancewar su mara sa son surutu, lokaci d’aya kuma yaya Faruk na kara wayar shi a kunne da alama akwai wanda yake son kira bai samu ba.
Gajeren tsaki ya ja kafin ya ajiye wayar shi a kan jikin shi.
Shiru ne ya biyo baya kafin ya mik’e da niyar tafiya.
Sallama ya mata ya fara tafiya.
Kiran sunan shi da Nana tayi yasa shi juyowa.
Itama tashi tayi ta tako tazo kusa dashi.
Cikin marairaicewa ta ce "yaya Faruk what’s wrong".
Cikin basarwa ya ce "Me kika gani".
"Gani nayi yanayin ka ya canza a lokaci guda, kamar akwai abin da yake damun ka".
Lallausan murmushi yayi ya ce "No don’t mind Khadijah, ba wani abu bane, just ina ta trying d’in number Teemah ne ya k’i shiga, sai a ce a kashe take, ni kuma ban cika son takura wa mutane in ce ai kai mata waya za mu yi waya da ita".
Murmushi kawai tayi ta ce "Gaskiya amarya ba ta kyauta ma angon ta ba, tasan zai nema ta sai kuma ta kama ta kashe wayar" ta k’arasa maganar cikin zolaya.
"lallai Khadija kin ga gadon barci na, yanzu ni ki ke tsokana".
Dariya tayi ta ce "Sorry yaya Faruk, na ga Amaryar tamu ce za ta sa yayan mu a network".
Girgiza kai kawai yayi ya mata sallama ya tafi.
Yau kwana na biyu a Wagini, ina cikin d’aki ina waya da Dr.
Jin Hajiya ta shigo tana sababi yasa nayi saurin yi yi mishi sallama.
Cikin tsokana na ce "Hajiya wai ke da waye naji kina fad’a, wa ya ta’ba min ke".
Cikin fad’a Hajiya ta ce "Ban sani ba, dan jakar uban ki, me kika sa min a waya ta na kasa kiran mutane, gashi kwana biyu kenan bamu yi waya da ‘ya’ya na ba, nasan haka kawai ba za su k’i kirana ba, sai dai in da dalili".
Zagin da Hajiya ta min ne yasa na fara dariya.
Ran Hajiyan Wagini ne ya k’ara ‘baci jin dariyar da nake mata ta ce "Au ‘yar jakar uba dariya ma na baki ko, ba zaki fad’a min me kika yi ma wayar nake ganin wani d’an jirgi a saman wayar ba, nasan ba wanda zai min aika-aikar nan sai ke".
Kasa daure dariyar nayi saboda wani zagin da Hajiyan Wagini ta k’ara min.
Ganin dariyar da nake mata yasa taci gaba da sababi ta ce "Ki yi dariyar ki da kyau, zan rama ne, dan ni da iyayen ki zan had’a ki, kwanciyar hankalin ki shine ki gyara min waya ta, ai nasan Soja sai yayi hak’uri dake, ko da yake shi ba ragon namiji ba ne" tana gama fad’ar haka ta fita daga d’akin tana ci gaba da fad’an ta.
Ni kuwa cewa nayi "yaushe zan bar wayar ki a geneneral mode sanandin su Abbu su kira ki su tambaye ki, ki fad’a musu ina nan ko ke ki kira su".
Dadi tun da ya bar gidan su Abbu tunani ne ya addabe shi, yanzu abin da yafi damun shi shine halin da yaya Faruk zai shiga idan ya riski wannan labarin, ga kuma rashin gani na da ba ayi ba, ya zama dole ya sanar da yaya Faruk halin da ake ciki dan barin kashi a ciki baya maganin yunwa, shi kanshi shaida ne da irin son da yaya Faruk yake yi min, ashe shi bai sani ba d’an shi son maso wani yake yi wanda yafi ciwo, da irin wannan tunanin yayi tayi har ya k’arasa gida.
Samun Momi yayi da Anisa suna ta hira akan bikin, jikin shi ne ya k’ara sanyin ganin yadda kowa yake maganar yadda bikin zai kasance.
Guri ya samu ya zauna yayin da Momi da Anisa suka mishi sannu da zuwa.
Momi ce ta tashi ta nufi kitchen ta d’akko coconut juice wanda yaji madarar peak a ciki, k’anshi flavour ne kawai yake tashi a ciki.
Tsiyaya mishi tayi a glass cup ta mik’a mishi.
Amsa yayi ya sakar mata murmushi duk da damuwar da yake ciki amma ba lallai ne ka gane hakan a fuskar shi ba, kad’an ya sha ya ajiye ya maida kallon sa ga Momi ya ce "Rukaiyya ina so muyi wata magana dake, ina so ki yi wa maganar kyakkyawan fahimta".
Jin haka ya sa ta tattara natsuwar ta ga Dadi dan jin mai zai fad’a mata.
Anisa ce ta mik’e da niyar fita daga falon, Abbu ne ya dakatar da ita akan ta zauna.
Dadi ne ya fara maganar da cewa "Rukaiyya kowani d’an adam da kike gani da k’addarar sa, Allah na iya jarabtar bayin sa ta hanyoyi da dama dan ya gwada imanin su yaga ko za su iya cinye jarabawar su, to hakan ce ta faru ga Faruk…".
Momi ba ta gama jin zancen ba ta katse Dadi da cewa "Me ya same shi Alhaji, pls ka fad’a min abin da ya samu Faruk d’in".
Dadi ne yaci gaba da cewa "Ba abin da ya sami lafiyar shi, sai dai wata jarrabawa da take niyar samun shi ko ma in ce ta same shi, nan Dadi ya sanar da Momi halin da ake ciki kamar yadda Abbu ya sanar dashi.
Ran Momi ne yayi masifar ‘baci da abin da nayi, ita a ganin ta wannan wani rainin hankali ne aka zo musu dashi, sai da biki ya kusa za a ce na gudu kuma akwai wanda nake so, shi yasa tun san da Faruk ya fad’a mata yana so na ta yi mamaki dan tasan akwai wanda Anisa tace mata muna soyayya, abin da yasa ta bar maganar ganin Faruk bai fad’a mata wata matsala daga gare ni ba, ashe kuwa matsalar tana nan za ta ‘bullo.
Cikin fad’a Momi ta ce "Alhaji lallai Fatima ta ci mutuncin mu, yanzu akan Faruk ta gudu dan ni ban kawo ‘bata tayi ba tun da ba kaza ba ce ita da za a ce a gida an zo an d’auke ta, duk yadda yake nuna mata so shine za ta saka mishi da haka a lokacin da bikin su bai wuce sati biyu ba, sakayyar da za ta mana kenan na irin son da muka nuna mata tamkar yarinyar da muka haifa da cikin mu haka muka d’auke ta, shine za ta nuna mana na butulci irin na d’an adam, me yasa tun farko ba ta fad’a bashi take so ba, da tuni ban bashi hak’uri ya hak’ura da ita ba, to tun da abin haka ne Anisa ma ta hak’ura da Khalil duk da shi na san bai da matsala, tun da k’anwar shi ta guji jinin ta itama me za tayi dashi".
Ganin yadda ran Momi ya ‘baci yasa Dadi ya mata shiru, sai da ta gama fad’an sannan yaci gaba da cewa "Rukaiyya a matsayin ki na babba fushi bai kamace ki ba duk da nasan ke aka ‘bata mawa, maganar Anisa ta rabu da Khalil bai taso ba tun da su ba ruwan su a ciki, in za a ga mai laifi to bai wuce Fatima ba, laifin ta da na gani shine guduwar da tayi amma dan ta ce ba ta son Faruk ba laifi bane duk da ta wani ‘bangaren in aka duba yaci a ce ta so shi ko dan son da yake mata da kuma alak’ar zumunci dake tsakanin su, sai dai shi so ba ya duba wannan, ni yanzu abin nafi buk’ata shine a ga ita Fatiman".
Momi ce tayi saurin katse shi da cewa "Anya Alhaji kana son Faruk kuwa, wato kai ba halin da d’an ka zai shiga ka ke tunani ba, kafi buk’atar dawowar Fatiman, yanzu duk yaudarar da yarinyar nan tayi ma Faruk duk ba abin duba wa bane".
Murmushi Dadi yayi jin Momi na tambayar shi wai anya yana son Faruk kuwa.
"Hajiya ina ganin tambayar ki ba ta buk’atar amsa na tambaya ta akan wai ina son Faruk kuwa, nasan za ki fi kowa sanin irin son da nake ma Faruk, kar ‘bacin rai yasa shaid’an yayi tasiri a zuciyar ki, duk wannan maganganun ba su ba ne maslaha a gare mu, sanar da Faruk shi yafi".
Yana gama fad’ar haka ya d’akko wayar shi ya kira layin Faruk d’in, cikin sa’a ya samu numbar shi.
Bayan ya d’auka ne Dadi ya umarce shi da yazo Kaduna yana neman shi, yaya Faruk ya amsa mishi da yana nan zuwa insha Allah.
Ita kuwa Anisa mamaki ne ya kamata da jin abin da na aikata, ba ta zaci zan iya aikata kwatankwacin abin da na aika ta ba, tuni ta fara tausaya ma halin da yaya Faruk zai shiga, ita shaida ce a irin son da yake min.
Itama ta k’udurce a ranta za ta rabu da yaya Khalil ko da Momi ba ta fad’i hakan ba duk kuwa da irin son da take mai saboda a dalilin k’anwar shi yayan ta zai shiga wani hali.
Dadi ne ya kalli Momi ya ce "Kin dai ji munyi waya da Faruk d’in zai zo, ban ce ke ko Anisa ku kira shi a waya ku fad’a mishi abin da yake faruwa ba" yana gama fad’ar haka ya nufi side d’in shi.
Momi cikin damuwa ta kalli Anisa ta ce "Anisa kin ji abin da Fatima tayi ko? amma kina gani Dadin ku bai ganin laifin ta, kema kina da laifin ki Anisa, nasan baza ki rasa sanin wani abu dake tsakanin Faruk da Fatiman amma ba ki fad’a min ba, da nasan matakin da zan d’auka da wuri, yanzu ai gashi har dake za a jefa d’an uwanki cikin wani hali" Momi ta k’arasa maganar cikin takaici.
Ita kanta Anisa jikin ta yayi sanyi, tana ganin ba amfanin ‘boye ma Momi komai tun da yanzu tasan halin da ake ciki, dan haka ta zayyane ma Momi komai na tsakanin yaya Faruk dani, da irin matsalar da shi yaya Faruk yake fuskanta a guri na akan Dr Sadik, da kuma damuwar da yake shiga akan haka.
Jin wannan labarin da Momi tayi ya k’ara sa mata ‘bacin rai akan wanda take ciki, nan Momi taci gaba da fad’an ta da irin matakin da za ta d’auka akan wannan al’amarin.
[7/3, 23:16] Maryam Ahmad: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞
🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀🤦🏽♀
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*MARYAM AHMAD PAKI*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽
*TA’AZIYYA*
_Ina mik’a sak’on ta’aziyya ta ga family d’in Murjanatu Alhassan wacce Allah ya ma rasuwa a ‘Yar aduwa University a sanadiyar rashin lafiyan da tayi_.
_Allah nake rok’o ya jik’an ki ya gafarta miki, Allah yasa aljanna ce makomar ki_.
_San da naji labarin rasuwar ki ba k’aramin tashin hankali na shiga ba, nasan nayi rashi, ke k’awa ce ta gari da bazan mantaD dake ba_
😭😭😭
_Ina mik’a sak’on ta’aziyya ta ga Hussaina wacce Allah yayi wa mijin ta rasuwa_.
_Halima Mk ina k’ara mik’a sak’on ta’aziyyata gare ki na rasa mijin ki da kika yi_.
_Allah nake rok’o ya jik’an su baki d’aya ya kyautata makwancin su, ya sa aljanna ce makomar su, Allah mu ma ka kyautata k’arshen mu_
_Ina rok’on duk wanda ya karanta wannan page d’in yasa su a addu’a_
*QUESTION OF THE DAY*
_Wace surah ce take karantar da cewa duka abubuwan duniya suna da dangantaka da junansu, dangantaka bayyananna ko’boyayya, Kuma zumuntarsu na gudana gwargwadon dangantakarsu da juna_
67-68
Su Abbu kuwa ba k’aramin fushi suka yi dani ba, yaya Khalil ma ya fisu shiga damuwa saboda yadda muka fi shak’uwa dashi, ba wani mai walwala a cikin su tun san da na bar gidan mu.
Dadin su Faruk ya bada cigiya ta a kafafen yad’a labarai, sannan ya kai report police station amma har yanzu shiru ba wani bayani a kaina.
Tsakanin Dadi da Abbu an rasa mai k’arfin gwiwar da zai iya tunkarar Hajiyan Wagini akan rashin gani na da ba ayi ba, tunanin fad’an da za tayi da halin da za ta shiga yasa suka ‘boye mata, sun barshi akan sai an ganni za a sanar mata da komai, a cikin su ba wanda tunanin shi ya kawo can zan tafi.
Yau kwana biyu kenan da wayar da yaya Faruk suka yi da Dadi sai gashi a Kaduna.
Tun san da Dadi ya kira shi yake tunanin dalilin kiran da Dadi ya mishi, yasan in akan biki ne zai sanar dashi a waya, ba sai yace yazo ba.
Bayan ya huta ne Dadi ya kira shi side d’in shi.
Samun shi yayi da Momi a zaune, alamun dake fuskar su na nuna kowa da abin dake damun shi.
Sallama ya musu ya nemi guri ya zauna.
Dadi ne yayi k’arfin halin amsa masa sallama.
Cikin ladabi yaya Faruk ya ce "Gani Dadi".
Dadi sai da saki ya gauron numfashi saboda tunanin abin da zai fad’a ma yaya Faruk ba mai dad’in ji ba ne kana ya kira sunan sa "Umar!
Cikin sanyi ya amsa "Na’am Dadi".
A ranshi kuwa jinjina abin da Dadi zai fad’a mishi mai matuk’ar mahimmanci ne tun da ya kira ainihin sunan shi.
Dadi ne ya nisa kafin yaci gaba da cewa "Faruk, dalilin da yasa na ce kazo Kaduna shine akan wata k’addara da ta faru bayan tafiyar ka wanda yake da alak’a da kai, ka ga kenan ‘boye maka bai da wani fa’ida".
Tun kan Dadi ya fad’a mishi maganar da yake son fad’a mai, yaji jikinshi yayi sanyi, yanzu jikin shi ya fara bashi ba abu mai dad’i Dadi zai fad’a mai ba.
"Faruk abin da nake son fad’a maka shine yau kwana hud’u kenan ba a ga Fatima ba, ba a kuma san inda ta tafi ba, hakan kuma na da nasaba ne da auren da za a muku da kuma wanda take so shi wannan Dr d’in, ina son ka d’au hakan a matsayin jarabawar ka, shi Ibrahim saboda ranshi a ‘bace yake ya ce ko da ba ta dawo ba zai d’aura mata aure dakai, kuma ni na fahimci dan ya faranta maka zai yi, ni kaina nasan Ibrahim da Aisha suna nuna maka so kamar d’an da suka haifa,sun kansu yanzu suna cikin damuwa da abin da Fatima ta aikata, maganar a d’aura aure ba a ga Fatima bai taso ba, za a k’ara ‘bata Al’amarin ne, gwara in ta dawo a san yadda za ayi, ba na so ka sa wannan matsalar a ranka dan guje ma kamuwa da wata cutar, kayi hak’uri Faruk, nasan Fatima ba ta kyauta maka ba" ya k’arasa maganar cikin lallashi.
Tun san da lokacin da Dadi ya fara labarta mishi wannan mummunan labarin kan shi yake a sunkuye ba tare da ya d’ago kai ba.
Duk wannan maganganun da Dadi yake ma yaya Faruk ji yake kamar ana watsa mishi tafasasshen ruwan zafi ne a zuciyar shi, ran shi ba k’aramin ‘baci yayi da jin wannan labarin ba, jijiyoyin kanshi duk sun tashi, idanun shi duk sun canza launi zuwa ‘bacin rai, bai ta’ba kawo wa a ranshi wannan mummunan labarin Dadi zai sanar dashi, ji yake ina ma mafarki yake yi ya samu ya farkar daga wannan mummunan mafarkin wanda bai fatan ya k’ara yin irin shi, sai dai kash! Wannan mummunan labarin a zahiri Dadi yake sanar dashi, yau ya k’ara tabbatar da maganar da Hausawa ke cewa idan wani yak’i ka wani sai yaso ka, shi da ‘yan mata ke son shi yana ja musu aji, nan ya tuno da Binafa yadda take mishi magiya akan ya so ta saboda yadda ta kamu da son shi, ya samu ya ba ta hak’uri ta hak’ura da sauran ‘yan matan da suka fad’a mishi suna son shi bai kula su, sai gashi an samu a kanshi na gudu saboda kar na aure shi duk kuwa da irin son da ya nuna min amma ni ban ga hakan ba, na za’bi bare a kanshi, ba abin da yafi tsaya mishi a ranshi shine yadda na dinga mishi yawo da hankalin shi na k’in fitowa a fili na fad’a mishi ba na son shi da wuri, sai daga baya da ya sakankance da cewa ina son shi sannan na nuna mishi da ban yi na’am dashi ba, yanzu ba abin da yake mishi yawo a k’wak’walwar shi shine guduwar da nayi wanda ba a san inda na tafi ba, a yanzu yana ganin ba abin da zai fi mai sauk’i illah ya samar wa kanshi mafita kafin dawowa ta, shi kad’ai yasan matakin da zuciyar shi ke fad’a mishi ya d’auka akan wannan curkud’ad’d’en al’amarin, yana ganin ba wanda yafi cancanta da ya nemo ni dan zartar min da hukuncin da ranshi ke ayyana mishi da ya yanke wanda yake ganin shi kad’ai ne zai kawo k’arshen wannan abun da yake faruwa tsakani na dashi.
Momi da Dadi jikin su ne ya k’ara yin sanyi ganin halin da yaya Faruk ya shiga tun a yanzu wanda ke nuna tsantsar tashin hankalin da yake ciki da kuma ‘bacin rai da ya mishi dabaibayi a lokaci guda.
Falon ne ya d’auki shiru ba tare da kowa ya sake magana ba, kowa da irin tunanin da yake ayyanawa a ransa.
Jin shirun da yayi yawa ne yasa Dadi ya kira sunan yaya Faruk cikin tattausan harshe.
Yaya Faruk ne ya d’ago kan shi wanda yake mishi wani matsanancin ciwo, wani irin nauyi kan yake mishi saboda tsabar ciwon da yake yi mishi.
"Come close to me my son" Dadi ya fad’a cikin lallashi.
Ba abin da yaya Faruk yafi buk’ata a yanzu da ya wuce yaji shi a kwance ko ya samu sauk’in rad’ad’in da yake ji a zuciyar shi da kuma kan shi da yake mishi matsanancin ciwo.
Ba tare da musu ba ya matso ya kwanta a jikin Dadi, a lokacin ne yaji wani irin zazzafan hawaye na fita daga idanun shi, sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi kamar wanda yaci kuka ya k’oshi, k’arshe ma runtse idon shi yayi ko ya samu sauk’in halin da yake ciki, sai faman karanta *Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un* da *Allahumma ajirni fih musibatih, wa aklifni khairan minha* wannan addu’o’in su yake ta faman maimaitawa a cikin ranshi, a hankali yaji natsuwa ta fara shigar shi, ‘bacin ran da yake tare dashi ya fara raguwa.
Momi na ganin halin da yaya Faruk ke ciki ita ma ta fara zubar da hawayen tausayin shi, tasan daman hakan za ta faru, yaushe rabon da ta ga hawayen yaya Faruk, amma yau a dalili na yaya Faruk na zubar da hawaye.
Dadi na lura da hawayen da Momi ke yi, yasan dole ta shiga wannan halin in dai ta ga yaya Faruk a cikin wannan halin, shi kanshi kawai dauriya yake yi ba wai dana bun bai dame shi ba, a yanzu ba wanda yafi buk’atar lallashi sama da yaya Faruk.
Dadi ba abin da yake faman yi sai shafa kan yaya Faruk yake yi kamar yadda ake lallashin k’ananun yara, a lokaci d’aya yana fad’a mishi sweet words masu kwantar da hankali.
Jikin shi da yaji ya d’au zafi wanda hakan ke nuna zazza’bi ne ya kama shi mai zafi.
Janyen jikin shi yayi daga jikin Dadi, hannun shi yasa ya rik’e kan shi wanda yake ji kamar zai tsage saboda ciwon da yake mai.
Tashi yayi da niyar tafiya, ya fara tafiya kenan, hannun shi na dafe da kanshi, jirin da yaji yana d’ibar shi, nan ya fara tangad’i zai fad’i, da sauri Dadi ya taso dan ya rik’e shi kafin ya fad’i, ko kan Dadi ya k’arasa yaya Faruk ya fad’i a k’asa.
Momi ce ta taso da gudu tana kuka tazo tana jijjiga yaya Faruk.
Anisa ma wanda shigowar ta yayi daidai da fad’uwar yaya Farud da gudu ita ma ta k’araso gurin yaya Faruk wanda yake kwance a k’asa.
Momi kuwa cikin kuka cewa take yi "Faruk ka tashi, ku kad’ai gare ni, daga kai sai Anisa, ku kad’ai Allah ya ba ni, kar ka mutu saboda ‘ya mace, idan ka mutu ban san halin da zan shi ga ba".
Anisa ma cikin kuka ta kwanta a jikin yaya Faruk tana cewa "yaya Faruk dan girman Allah ka tashi, kai kad’ai ne d’an uwana da nake kalla na ji sanyi a raina, kar ka tafi ka barni da maraicin ka, rashin ka zai sa in shiga cikin wani mawuyacin hali, yaya Faruk kaji tausayin mu ka tashi dan Allah…" nan ta k’ara fashe wa da wani irin kuka.
Cikin Momi da Dadi an rasa mai lallashin wani a cikin su.
Dadi ne ya ta’ba yaya Faruk yaji yana motsi, hakan yasa ya fahimci suma yayi.
Da sauri ya wuce gurin d’an k’aramin fridge d’in shi ya d’akko faro water mai sanyi yazo ya yayyafa mishi a jikin shi.
Saukar ruwan da yaji a jikin shi yasa ya saki wata ajiyar zuciya.
Dadi ne da Momi suka samu suka kama shi suka kai shi side d’in shi.
Wayar shi Dadi ya d’akko ya kira family Dr d’in su ya fad’a mishi halin da yaya Faruk ke ciki.
Ba a d’au wani tsawon lokaci ba sai ga Dr yazo da kayan aikin shi.
Bayan gwaje-gwajen da Dr ya mai ne ya kalli Dadi ya ce "Alhaji a gwaje-gwajen da nayi na gano Faruk yana yawan tunani duba da yanda BP d’in shi ya hau, yawan tunanin da ya fara yi mishi yawa ne ya jawo mishi ciwon kai mai tsanani wanda hakan yasa temperature d’in jikin shi ya canza, ciwon kai da jirin ne ya hadassa mishi suma, sannan Alhaji pls a kiyaye fad’a mishi abin da zai sa ranshi ya ‘baci don kiyaye lafiyar shi, yanzu zan mishi allurar da zai sakko mai da zazza’bin, zan kuma sa mishi drip da yaji k’arfin jikin shi, sannan zan ba da maganin da za a bashi yasha, in da hali a barshi ya huta don a yanzu bai buk’atar hayaniya".
"Za mu kiyaye insha Allah" Momi ta fad’a.
Bayan ya mishi allura ne yasa mishi drip kana ya musu sallama suka fita da Dadi.
Tun da aka sa ma yaya Faruk drip yake ta faman barci kasancewar har da allurar bacci Dr d’in yasa mai.
Momi ce ta koma side d’inta dan dafa wa yaya Faruk abincin da zai ci in ya tashi.
Anisa kuwa zama tayi a kusa dashi tana kallon yadda yaya Faruk ya koma a lokaci guda.
Ba abin da take furta wa sai "Fatima why, me yasa za ki sa yaya Faruk a wannan halin da yake ciki" a lokaci d’aya hawaye na ci gaba da zubowa a idanun ta.
Yaya Faruk sai da ya kwashe fiye da awa uku yana bacci kafin ya tashi daga baccin.
A hankali ya dinga bud’e idon shi, Anisa ya gani a gefen shi tana rik’e da d’ayan hannun shi wanda ba a sa ma drip ba, yayin da hawaye ke zubowa a idanun ta.
Ganin yaya Faruk ya farka yasa ta saki murmushi ta ce "yaya Faruk ka tashi, sannu ya jikin, yanzu ina yake maka ciwo, akwai abin da ka ke so ne, ko in kira Momi ne?".
Jin wannan jerin tambayoyin da Anisa ke jero mishi yasa ya girgiza mata kai.
K’ara rik’e hannun ta yayi yana kallon ta, idanun ta da ya gani ya canza kala ya tabbatar mishi da tayi kuka, hannun shi yasa yana goge mata hawayen.
Kwanciyar da ya ji ya gaji da ita ne yasa a hankali ya tashi ya zauna.
Da sauri Anisa ta kara mishi pillow a bayan shi ya jingina da gadon.
Drip d’in da taga ya k’are ne yasa ta cire mishi ta koma ta zauna.
"Me yasa ki kuka?" yaya Faruk ya tambaye ta.
Kamar jira take yi ta k’ara sa wani kukan, cikin kukan take cewa ‘yaya Faruk dan Allah ka daina sa tunani ni a ranka, likita yace BP d’in ka ya hau kuma duk a dalilin tunani, plss ka cire tunanin Fatima a ranka".
A hankali ya ce "Kar ki damu Anisa, komai ya kusan zuwa k’arshe insha Allahu, ki daina kuka kin ji my lovely sister".
"Na daina yaya Faruk".
Momi ce ta shigo da foodflask a hannun ta da flask.
Ajiye wa tayi a kan centre table ta nufi yaya Faruk cikin fara’a ta ce "Ka tashi Faruk, sannu ya jikin".
"Da sauk’i Momi".
"To Allah ya k’ara sauk’i".
"Amin Momi".
Niyar mik’ewa yayi da niyar tashi amma har yau jikin shi ba k’arfi.
Momi ce ta ce "Ina zaka kuma".
Cikin muryar marasa lafiya ya ce "Ina so in je in watsa ruwa ne, jiki na ne nake jin shi ba k’arfi, ga shi ina so in yi sallah la’asar da ban yi ba".
Cikin tausayawa Momi ta ce "Ka bari kaci abinci zaka ji dad’in jikin ka, in yaso sai ka watsa ruwan kayi sallah".
"Bari in je in yi brush in dawo".
"Ok" Momi ta amsa mishi.
Tashi yayi a hankali yake takawa, da alama har yanzu bai gama jin k’arfin jikin shi ba.
Band’aki ya shiga ya d’auraye fuskar shi kana yayi brush ya fito.
Dawowa yayi ya jingina da gadon.
Momi ce ta kalli Anisa tace "Je ki kan fridge ki d’akko plate da cup a zuba mishi ya ci".
Anisa ce ta had’a mishi kakkauran Tea wanda yaji madara a ciki, d’ayan plate d’in kuma farfesun kayan cikin ne a ciki.
Momi ce ta amshi tea d’in da plate d’in ta matsa kusa da yaya Faruk d’in.
Tea d’in take bashi a baki wanda yake shan shi kamar mad’aci hakan yake jin shi a bakin shi, kad’an yasha tea d’in y ace ya k’oshi, ajiyewa Momi tayi ta fara bashi farfesun, yana shan farfesun ne ba wai dan yana jin taste d’in shi a bakin shi ba, sai don kar ran Momi ya ‘baci yasa yake sha.
Dadi ne ya shigo d’akin yayi don ganin jikin yaya Faruk.
Samun shi da yayi ya farka har yana d’an cin abinci yasa yaji dad’i a ranshi.
A hankali ya k’araso gurin su yana Murmushi ya kalli yaya Faruk ya ce "Jiki yayi sauk’i kenan Faruk, Allah ya k’ara afuwa da sauk’i".
Amsawa yayi da "Amin".
Bayan ya gama cin abincin ne ya mik’e yaje ya watsa ruwa yayi alwala yazo ya rama sallolin da ake bin shi kana ya koma ya kwanta.
Dadi ne ya kira su Abbu ya sanar dasu rashin lafiyar yaya Faruk.
Da daddare sai gasu Abbu, Ummu da yaya Khalil sun zo duba shi.
Jikin Ummu ne yayi sanyi ganin da Momi take amsa musu maganar su kamar ba ta so, tasan hakan bai rasa nasaba da halin da yaya Faruk yake ciki wanda a dalili na hakan ya faru dashi, ko waye aka yi wa d’anta haka dole ne ranta ba zai mata dad’i ba.
Anisa kuwa tun bayan gaishe dasu da tayi ta tashi ta bar d’akin.
Shi kanshi yaya Faruk bai ji dad’in yadda Momi tayi ma su Ummu, da yadda yaga Anisa na share yaya Khalil, yana ganin wannan abin da ya faru tsakanin shi da ni ne, bai kamata su ‘bullo da wannan matsalar ba duk da yasan dan saboda shi suke yin haka, suna jin haushin abin da na mishi.
Yaya Khalil ne ya tashi ya bi ta d’akin ta amma ta k’i sauraren shi, a iya nazarin da yayi yasan ba abin da ya had’a shi da ita bare yace fushi take yi dashi, duk wasu kalamai na lallashi da ya kamata ya fad’a mata ta saurare shi amma tak’i, sai ma kuka da ta sa mishi.
Jikin shi ne yayi sanyi da kukan da yaga Anisa ta na yi, shi kanshi yanzu dauriya ce yake yi irin ta namiji, gashi kuma Anisa na so ta d’aga mishi hankali da kukan ta.
Cikin kukan take cewa "yaya Khalil ina rok’onka ka k’yale ni, ka barni na ji da halin da nake na halin da d’an uwa na yake ciki a yanzu wanda ‘yar uwarka ce silar shi shiga wannan halin, yaya Khalil tun da Fatima ta nuna ba ta son d’an uwa na to nima ina ganin babu wani fa’ida a ci gaba da soyayyar mu, nima ina kishin d’an uwa na kuma ina son sa, yaya Khalil ka fita na ce" ta k’arasa maganar cikin kuka.
Sai yanzu yasan akan abin da yasa Anisa take k’in kula shi, tana mishi haka ne saboda ta rama abin da Fatima ta yi ma d’an uwan ta, yasan ko mai zai fad’a mata ba za ta saurare shi ba, abin da ya fi shine ya bari ta sakko, hakan zai fi sa su fi fahimtar junan su.
Kallon ta kawai yayi ya girgiza kai ya fita daga d’akin.
Yana fita ta sake fashewa da wani kukan, wannan lokacin akan abu biyu take kukan, na son yaya Khalil da ke d’awainiya da ita a cikin zuciyar da rashin yi mishi adalci na hukunta shi da laifin da ba nashi da kuma tausayin halin da yaya Faruk yake ciki.
Haka su Ummu suka yi sallama da su Momi kowa da abin da yake damun shi a ranshi.
Ranar haka yaya Faruk ya kwana da tunanin in da na tafi.
Washegari jikin yaya Faruk yayi sauk’i dan ya samu ya fito falo ya zauna, ganin yadda kowa ke nuna mishi kulawa yasa ya saki jikin shi duk kuwa da yadda yake jin zafi a cikin zuciyar shi na abin da na mishi.
Yaya Aminu ma yazo da Anty Jiddah sun zo sun duba shi, yaya Aminu haka ya ci gaba da kwantar mishi da hankali, ya nuna mishi shi kanshi halin da yake ciki na abin da na aikata.
Sun d’an jima a gidan kana suka koma gurin Momi suka mata sallama suka tafi.
Yau kwanan yaya Faruk biyu da zuwan shi Kaduna ya shirya zuwa Wagini gaishe ta, kiran ta da yayi a waya haka ma Dadi ya sanar dashi shima bai samun ta a wayar, hakan yasa ya shirya tafiyar.
Fito wa yayi cikin shigar wani yadi mai laushi kalar ash, in ban da k’amshin turare da yake tashi ba abin da falon yake yi.
Sallama yayi ma su Momi akan ya tafi Waginin, may be zai kwana a can ko ya dawo yau.
Fatan a dawo lafiya suka mishi.
Kasancewar ya sa wa motar speed yasa ya isa Wagini a da wuri.
Hajiya na zaune a tsakar gida tana sauraren radio taji shigowar yaya Faruk.
Sallama yayi yazo ya zauna kusa da ita akan tabarmar da take zaune.
Amsa masa sallamar tayi da fara’a a fuskar ta.
Hajiya ce ta ce "Maraba da mai gidana Soja na kaina, sannu da zuwa".
"Yawwa Hajiya, mun same ku lafiya".
"lafiya lau, ya aiki, ya wajen iyayen naka"
"lafiyar su lau, suna gaishe ki".
"Hajiya lafiya wai ba a samun wayar ki, su Dadi suna kiran ki ba sa samu, nima na kira ba ta shiga sai a ce min a kashe take".
Hajiya dama kamar jira take yi ta fara fad’a "Rashin samu na da ake yi ba zai rasa nasaba da wannan ‘yar buhun ubar ba, ba yadda banyi da ita ta gyara min wayar nan amma yarinyar nan tak’i, idan na ce ta kira min ku a wayar sai ta ce ba ta shiga, haka na gaji na k’yale ta".
Murmushi kawai yayi yace "Wai wace yarinyar ce ki ke magana Hajiya".
"Au kai duk bayanin nan da nake yi ba ka gane wacce nake nufi ba, to amaryar ka nake nufi Fatima…".
Da sauri ya katse da cewa "Wace Fatiman wai Hajiya".
Hajiya ce ta mishi dak’uwa tace "Ungo naka, kaji ni da shak’iyin yaro, yau Fatiman ce ba ka gane ba".
"Hajiya kina nufin Fatiman Abbu, dama tana nan ne".
"Yau kwanan ta kusan shida kenan, na ji kana tambayar dama tana nan ne, kana nufin ba a san tana nan ba ne".
"Tana ina ne Hajiya?".
"Tana can cikin d’aki, hala tana can ta kunna kururuwar shed’an tana saurara, yarinya ba ta da aiki sai kunna wak’ok’in soyayya kamar a kanta aka fara".
Bai tsaya sauraren abin jin bayanin da Hajiyan Wagini ta ke mishi ba ya mik’e ya nufi d’akin.
Duk yadda na ‘bata mishi hakan ba zai hana shi jin dad’in tawowa ta nan Wagini ba, kowa tunanin shi bai kawo nan na tawo ba.
Ni kuwa ina kwance akan gado, earpiece ne a kunne na ina sauraren wak’ar Hussaini Danko, sauraron wak’ar na ke yi sannu a hankali kamar ni na raira ta, mai taken _SOYAYYA TA_
Bin wak’ar na fara yi inda mai amshin take cewa _nima soyayya ta zan furta_
_ba a saka ni rana d’aya in yi gudun ka_, _so d’ammara nayi ko za ya saka min hauka_, _ko mutuwa nai zan so a dalilin son ka , _so ajiya nayi ranar shi tazo zan d’auka_, _idan tafiya nayi an ce da gwani amsar ka_, _nace kai na za’ba_, _har zuci bazan canza ba_, _ba kuma zan k’osa ba…_, _ni kaine burina ba a hana ni zuwa gurin ka_, _so ne jagora na shi ya dasa min k’imarka_, _amsar tambihi na je ka rabe min hujjar ka_, _ya zan yi in k’yale ka in ta zama a cikin cuta_, _so so soyay…_
Sauran baitin ne ya tsaya a iya baki na saboda idanuna da suka sauka akan wanda na gani a bakin k’ofa yana kallo na.
A hankali ya tako ya k’araso inda nake ya tsaya yana ci gaba da kallo na, a yanayin shi bazan iya gane halin da yake ciki ba.
Wata irin kunyar yaya Faruk ne ya kama ni da tsoron shi a lokaci guda, daskarewa nayi a zaune ba tare da na iya motsa ko da d’an yatsa na ba.
Wani irin murmushi ya min wanda na kasa fasalta mai murmushin yake nufi a gurin shi.
"Fatima kenan, ashe nan ki ka tawo a na ta neman ki a gida" ya k’arasa maganar yana min wani irin kallo.
A halin da nake ciki na firgici ba zai bani damar in iya bud’e baki na in amsa wa yaya Faruk tambayar shi ba.
A yadda na lura ma bai da buk’atar amsawa ta a yanzu.
Ci gaba yayi da cewa "Fatima kamar yadda kike buk’atar in barki da masoyin ki wanda ku ke son junan ku ina ganin lokacin yayi, na yarda ke jaruma ce a soyayya da zaki iya fad’i tashi a kanta, in da kika ban kunya a soyayyar taki shine tsoron da kika sa a ranki har yakai ki ga barin iyayen ki wanda ki ka sa su a cikin halin damuwa, a matsayi kin a ‘ya mace ina ganin ba mutunci ki ba ne barin gari dan ba kowa yasan nan za ki zo ba, hakan da kika yi zai sa mutuncin ki ya zube a idanun mutane, anyway ba dogon zance zanyi dake ba illa in sanar dake *FATIMA NI UMAR FARUK NA HAK’URA DA AURAN KI, FATIMA NA HAK’URA DA SOYAYYAR KI DUK KUWA DA SON DA NA KE MIKI*.
Sauri nayi na d’ago kaina na kalle shi, banyi zaton jin wannan kalamen daga bakin yaya Faruk ba sanin son da yaya Faruk yake min ban yi zaton zai yi saurin yanke hukunci irin wannan ba na hak’ura dani amma sanin halin yaya Faruk in ranshi ya ‘baci zai iya yanke kowane hukunci dan samar ma kanshi mafita yasa ya zartar da hukunci, bai duba halin da zai shiga ba, Kalamen da ya yi amfani dasu wajen yi min magana shi ya bi duk sassan jiki na ya katse min kuzari na da nake tare dashi a wannan lokacin.
A lokacin wani irin tausayin yaya Faruk ne ya kama ni wanda ban san lokacin da hawaye ya fara sintiri a idanu na ba.
Ci gaba yayi da cewa "Fatima ina da power da zan iya auran ki in kuma koya miki so na ko da ba kya so, ba wai wannan abin da kika aikata ne yasa naji tsoro na hak’ura da auran ki, sai dan ni ba mai son shiga rayuwar wani ba ne, ina son ba wa mutum right d’in shi ne a matsayin shi na d’an adam, kin fad’a min wannan Dr ki ke so ban d’au hakan a komai ba, sai yanzu da kika d’auki matakin fara guduwa daga gaban iyayen ki, na ji tsoron a matsayin ki na ‘ya mace kar ki je ki aikata wani abin da bai dace ba duk a dalilin aure na da zaki ko bayan anyi aure na da ke ki je ku ci gaba da soyayyar ku kuna cin amana ta, kin ga kenan zan iya d’aukan ko wai mataki da ya zo min idan hakan ta kasance, hakan yasa na fasa auren ki, Fatima nayi niyar nuna miki kuskuren ki na yaudara ta da kika min, da tozarta ni da kika yi niyar yi a lokacin da bikin mu bai kai sati biyu ba kika tawo nan da niyar guje ma aure na, na so in nuna miki ba kowane namiji ne ake yaudarar shi a zauna lafiya ba, sai dai k’udurin da nake dashi na miki hukuncin na fasa dan ke ‘yar uwa tace, hannun ka ba zai ru’be ba ka yanke ka yar, shi yasa zan barki da halin ki".
Maganganun da yaya Faruk yayi amfani dasu wajen yi min magana sun min tsaurin da zuciya ta ba za ta iya amsar su ba, nasan maganganu ne yake fad’a min a k’aik’aice masu isar da sak’onnin da yake son isar wa wanda Hausawa ke cewa "kukan kurciya jawabi ne".
Wani irin kuka na saka a lokacin, in ban da shasshek’ar kuka na da ya cika d’akin ba abin da ke tashi.
Murmushin takaici yayi ya kalle ni ya ce "Fatima ba ki yi wa kan ki adalci ba da kike yin kuka alhalin ni ban miki wani abu ba, ina ganin in akwai wanda ya dace yayi kuka bai wuce ni ba saboda halin da kika sa ni a ciki, Fatima ni kukan zuciya nake yi wanda yafi na fili ciwo, ni a gani na murna ya kamata ki yi yau na cika miki burin kin a barin ki da wanda kike muradi".
Ni dai ba abin da nake yi sai ci gaba da kuka na da nake yi, wannan maganganun da yaya Faruk yake fad’a min zai fi min sauk’i akan yasa bulala ya zane da wannan maganganun da yake fad’a min.
Ganin Hajiyan Wagini kawai muka yi ta shigo cikin d’akin tana cewa "Haba Soja me kuma kayi ma amaryar taka, ko me ta maka ai kamata yayi kayi hak’uri da ita dan nasan dama ita ce da laifi, ni kaina tun da tazo take sa ni magana, dama ina jin haushin ta’ba min waya da tayi".
Ci gaba nayi da kuka na ba tare da na tsagaita ba, hakan yasa Hajiyan Wagini ce ma yaya Faruk "Mai gida na wai me ka mata ne ta cika mana kunne da kuka".
Wani irin banzan kallo ya watsa min kana ya kalli Hajiya ya ce "Hajiya kukan jin dad’i take yi dan ni ba abin da nayi mata".
Hajiya cikin lallashi ta ce "Wai me aka miki ne ki ke kukan nan".
Cikin kuka na ce "Hajiya dan girman Allah ki ba ma yaya Faruk hak’uri, na mishi laifi ne".
"Me kika mishi?".
Hajiya ta tambaye ni tana kallo na.
Shiru nayi wannan karan ban bata amsa ba, hakan yasa Hajiya fusata ta fara fad’a tana cewa "Ka ga ja’iran yara, kowa sai tambayar shi nake yi me yake faruwa kun k’i fad’a min sai tamaula ku ke yi dani".
Yaya Faruk ne ya rik’o hannun Hajiya ya ce "Hajiya mu je falo zan fad’a miki abin da yake faruwa" yana gama fad’ar haka suka bar d’akin.
Samun guri yayi ya zauna ya zayyane ma Hajiyan Wagini abun da yake faruwa da hukuncin da ya yanke yanzu.
Hajiyan Wagini na gama jin labarin ta sa kuka tana cewa "Yanzu dama abin da Fatima tayi kenan, shi yasa ta tawo nan, ba yadda ban yi ba akan ta fa’da min dalilin zuwan ta tak’i ta kuma d’au waya ta tayi min wani surkullen da ban da damar in kira mutane ko a kira ni, wannan wace irin hatsabibiyar yarinya ce, yaushe soyayyar zamani ta canza Fatima ta koma haka, to wallahi ba ta isa ba sai ta aure ka ko tana so ko ba ta so, anya Fatima tana da rabo kuwa a duiya tun da ta k’i ka, shi yasa ta ke kunna min wak’ar soyayya ni ina sha duk cikin son ka ne ashe wani barbad’ad’d’en take so ba kai ba".
Duk da ranshi ba ya mishi dad’i amma hakan bai hana shi murmusa wa ba jin Hajiya na cewa wai anya Fatima na da rabo a duniya kuwa?
Jin fad’an Hajiya yayi yawa yasa ya ce "Hajiya kar ranki ya ‘baci akan wannan maganar, ni na riga da na hak’ura da Fatima, kin ga kar a zo ayi abin da zumunci zai ‘baci".
Wani kallo ta mai na anya kasan abin da ka ke fad’a kafin taci gaba da cewa "Anya Soja kana cikin hankalin ka kuwa, ko dai shi wannan Dr d’in da ka ce yana son ta ya maka wani surkulen da zaka hak’ura da Fatiman, in ba haka ba ya za ayi bikin ku bai wuce sati biyu ba kace ka hak’ura da ita, ina ganin ka gwarzon namiji ashe ba haka ba ne, ko da yake bazan yi mamaki ba tun da son da kake ma Fatiman ba zai barka ka d’au hukunci akan ta ba, abin kunya yarinyar da ka ga k’uruciyar ta amma wai shakkar ta ka ke yi, to in kai ka hak’ura ni ban hak’ura ba, ba wanda ya isa ya kawo min matsala a cikin iyali na in dai ina raye".
Lallashin ta yaya Faruk ya fara yi amma kamar k’ara zuga ta ake yi, maimakon tayi shiru sai ma mik’e wa da tayi ta nufi d’akin da nake ciki.
Tun san da suka fita suka bar ni na ci gaba da kuka na har na gaji, sai faman ajiyar zuciya na ke yi, ba kalar tunanin da bai zo min a raina ba a wannan lokacin.
Fad’an Hajiya ne ya katse min tunanin da nake yi.
"Sannu Fatima, na ji abin da kika aikata, bari in fad’a miki babu wanda ya isa ya lalata min zumuncin da yara na suka dad’e suna yi, a yadda soja yake fad’a min nima za ki iya fad’a min magana in dai akan wannan Dr ne, to ko ke Laila-Majnun ce k’arewar soyayya sai kin hak’ura da shi wannan shed’anin yaron da yake zuga ki, ke ba ki isa ki kunya ta ‘ya’ya na ba, ke in banda sharrin so ai kin san Soja yafi k’arfin ki a komai ma".
Duk fad’an da Hajiyan Wagini take min kaina a sunkuye yake, nasan Hajiya za ta iya min abin da ya fi haka kasancewar duk cikin familin mu tafi son shi da shak’uwa dashi sannan sunan kakan mu ne wanda ya rasu, shi yasa duk wanda ya ta’ba yaya Faruk sai inda k’arfin ta sai ya k’are.
Yaya Faruk ne ya shigo ya ga fad’an da Hajiyan Wagini ta ke min, magana ya mata a kan ta k’yale ni tun da ya hak’ura, jin hakan ya k’ara tunzura HajiyanWagini ta dawo da fad’an kanshi "Rufe min baki, na ga akan Fatima za ka iya dawowa Sallamame sai yadda tayi dakai, kai in ban da ba ka da zuciya har za ka iya sa bakin ka har ka bani hak’uri duk da abin da ta maka, to in kai kana tsoron ta ni ba tsoron ta nake ji ba".
Duk wannan fad’an da Hajiya ke mai bai ce mata komai ba sai ma wayar shi da ya ciro yana daddanawa.
Ganin wayar da yake dannawa yasa Hajiya ta ce "Yanzu Soja duk wannan fad’an da nake yi akan ka shine za ka bad’a min k’asa a ido, maimakon kaima ka nuna ‘bacin ranka ka taya ni yi mata fad’a sai ma wayar ka da ka d’akko kana dannawa, ai shi kenan" nan Hajiya ta k’ara sa wani kukan.
Sanin rikicin Hajiyan Wagini yasa ya maida wayar shi gaban aljihun shi ya ce "Hajiya ki yi hak’uri, ban cika son d’aura ma kaina damuwa ba, likita ya min gargad’i akan haka saboda kiyaye lafiya ta kuma kin san ni ban cika son hayani ba".
Wannan maganar da yaya Faruk ya fad’a ne yasa Hajiya yin shiru daga fad’an da yake min.
Hajiya ce ta fara fita a falon, har ya fara tafiya kana ya juyo cikin d’aurewar fuska ya ce min "Ki shirya yau za mu koma Kaduna in kin gadama, in kuma za ki kira wannan Dr d’in ne ya zo ya d’auke ki ku tafi wani gurin, kina da damar yin haka, za’bin ya rage naki" yana gama fad’ar hakan ya bar d’akin.
Samun Hajiya yayi akan zai koma Kaduna dani, Hajiya na jin haka ta ce itama da ita za a tafi a yi komai a gaban ta.
Yaya Faruk bai mata musu ba ya ce ta shirya zuwa anjima za su tafi.
Abinci Hajiya ta shirya ma yaya Faruk wanda na dafa.
Tun da Hajiya ta zubo mishi abincin yaji bai marmarin shi dan yasan ni na dafa, ba yadda Hajiya ba tayi dashi ba akan yaci amma yak’i, sai ma ce mata da yayi bai jin dad’in bakin shi ne, ruwa kawai yasha da dambun naman da Hajiya ta kawo mai wanda ba ta rabo dashi yaci kad’an.
Haka na zauna a d’aki ba tare da na fito ko falo ba, abincin da na dafa ma kasa fitowa nayi na ci, ko sallah a band’akin ciki nayi alwalata, na san in dai na kuskura na fito falo ba abin da zan fuskanta sai ‘bacin rai, fad’an Hajiya kawai ya ishe ni bare a je ga kallon da yaya Faruk yake min a yanzu, A yanzu ina ganin yaya Faruk ya dawo kamar yaya Faruk d’in da na sani a da, yanzu ga wani tsoron shi da ya sake shiga na a karo na biyu.
San da za mu tafi yaya Faruk ne ya shigo d’akin ya ce in fito mu tafi.
Ko da zan shiga motar tunani na fara yi akan gaba zan zauna ko a baya, had’a idon da muka yi da yaya Faruk ne ya watsa min wani banzan kallo yasa ba shiri na bud’e baya na shiga, Hajiya ma baya ta shiga yaya Faruk ya ja mu muka tafi.
0 Comments