MAIMOON BEST HAUSA NOVELS

 Maimooon


Episode Twenty Two: Efisowa


Ina zuwa class Hafsat ta taso take tambayata "well, what did he said?" Na kalleta da jajayen ido nace "it's none of your business" ta jima tsaye a kaina sannan ta daga kafada tace "OK, in tayi tsami maji" da ace ana sayar da maganin sa ido da saina sayo na bawa Hafsat. Two days suka wuce, zuciya ta fara sanyi amma har yanzu ban huce ba. Ibrahim duk ya gama rikicewa saboda silent treatment da nake bashi. Amira kuma ta ja baya da komai, ta zama wata irin silent ba ta yiwa kowa magana, musamman ma ni. On the third day muna aji a zaune sai ga Ibrahim nan yazo, ya taho direct gurina ya tsaya a gabana yace da karfi yadda kowa a class din zaiji "nace miki I don't love her, what more do you want from me?" Gabadaya ajin kowa yayi shiru yana kallon mu ballantana su Hafsat sa ido. Nayi kasa da murya nace "what are you doing?" Ya kara daga murya yace "am telling everyone bana son ta ni ke nake so, ke kadai nake so" Wata jamila tace "sir wacece? A ajin nan take? Cewa tayi tana sonka?" Na dan saci kallon amira sai naga ta juya ma class din baya tana kallon waje, sai kawai naji zuciya ta ta karye, na dauki wani katon textbook na fara dukan Ibrahim da shi ina korar sa waje, amma yaki tafiya yace lallai saina fada masa cewa maganar ta wuce sannan zai fita, su kuwa 'yan aji sai kara tambayarsa suke ya basu labari. Da naga dai Ibrahim da gaske yake so yake yayi wa Amira tonon silili sai nace masa na yarda, maganar ta wuce, yace "kinyi alkawarin ba zaki kara tayar da maganar ba?" Nace "I promise" sannan ya juya ya fita. Yana fita Hafsat tace "well3, dama nace in tayi tsami zanji, 'yan class din nan duk mai son yaji wacece yazo in gaya masa" nan da nan duk suka tafi gurin Hafsat, na kalli Amira naga alamar tsoro a fuskarta, nayi sauri naje gurin Hafsat nace "Hafsat dan Allah ki bar maganar nan" tace "sai kinyi min alkawarin daga yau anti Hafsat zaki ke ce min" nace "done, anti Hafsat from today".


Sai da muka je hostel sannan Hafsat tace "ni daga ke har Amira kun bani mamaki wallahi, ni banga abin so a jikin wannan dogon mutumin ba" nayi dariya kawai ba rabu da ita, amma maganar ta ta tsaya min a rai. A lokuta da dama mutum ba shi yake zabar wanda zuciyarsa zata so ba, kawai haka kawai zakaji kana son mutum, wani lokacin kuma daga kaga mutum sai kaji baka son sa, ba tare da yayi maka komai ba. Kamar yadda lokaci daya na ji zuciya ta tana son Ibrahim duk da irin banbancin da yake tsakanin mu, babu wani dalili da zance saboda abu kaza nake sonsa, kawai dai nasan ina son sa. Da nayi considering Amira sai naga itama haka ne a wurinta, kawai taji tana sonsa ne amma saboda kusancina da ita ya saka ta boye a ranta har sai yanzu da suke spending time together sannan ta fara nuna masa, it must be hard on her, especially yanzu da yayi declaring a gaban kowa cewa baya sonta, sannan gashi gandantakar mu ta shekaru kusan shida tana so ta baci saboda kawai ta kasa controlling zuciyar ta. She deserves a break from me. Ina yin wanka na shirya sai na tafi dakinsu Amira, na tarar da ita a kwance idonta a rufe kamar mai bacci amma kana ganinta kasan ba baccin take yi ba. Na daka mata duka a cinya nace "sleepy heads, ki tashi mu tafi karatu" ta bude idonta tana kallona da mamaki. Ita tasan na sani. A hankali tace "bana jin dadi ne" nace "yeah right, in kika fita zaki warke" a haka na takura ta tayi wanka muka fita. Tun daga nan muka cigaba da kawancen mu da Amira, amma duk abinda muke yi da Ibrahim yazo gurin zata tashi, ni ma kuma bana cewa ta tsaya saboda ta ciki na ciki daurewa kawai nake yi. 


Soyayya sabowa muke shimfidawa da Ibrahim. Gani nake tunda na shiga SS3 ai I am old enough, shima kuma dama kiris yake jira. Sam Ibrahim baya kunyar nuna min soyayya ko a gaban waye ma kuwa, ni dai duk sai kunya ta rufe ni. Rannan a class ya zo yana cewa wai ya kasa bacci jiya kawai sai yaji muryata yake so yaji, wai saura kadan ya taho hostel, su kuma 'yan ajin sai su biye masa suyi ta tsokana ta, inna ga sun dame ni sai in tashi in bar musu ajin. 


Anan nake so inja hankalin iyayen yara musamman 'yan mata akan mu kula da tarbiyyar 'ya'yan mu. Yanzu makarantu sun baci, da yawa malamai suna soyayya da daliban su mata. Kuma da yawa daga cikin su basa nufin alkhairi, musamman a boarding schools. Kuma school management suna basa kula tunda shi kansa principal din ko vice ba zai rasa budurwa ba, musamman a private school inda yaran suke da budaddan ido. Mu tabbatar mun bawa yaran mu tarbiyya sannan kullum muke yi musu addu'ah dan babu abinda yafi addu'ah iyaye kariya a gurin 'ya'yansu. Allah yayi wa zuri'ar mu albarka baki daya. 


Rannan muna a gaban chemistry lab muna duba past questions and answers na WAEC sai muka hango Ibrahim da wasu mata su biyu a gaban staff room, Hasiya ce ta taba ni tace "kinga mutumin ki can, ko suwa ya samu kuma" ina dubawa naga mata ne su biyu da kaya a hannun daya, dayar daga gani babbar macece dayar kuma budurwa, budurwar da hijab matar kuma da babban mayafi, sun jima a tsaye suna magana sai naga ya karbi kayan hannun budurwar ya wuce gaba suna binsa a baya suka tafi staff quarters. Har dare ban kuma ganinsa ba kuma ina ta tunanin ko su waye wadan nan? Washe gari da safe sai gashi yazo yace min inzo, muna fita waje sai yace "there is someone here that wants to see you" gaba na ya fadi nace "who?" Yace "my mother" nan da nan naji wani tashin hankali yazo min, he wants me to meet his mother, this is serious. To ni yanzu da wacce fuskar zan je mata? Kuma me zance mata? Nace masa "Ibrahim am sorry, I can't" ya bata fuska yace "why can't you?" Nace "tsoro nake ji" dariya yayi yace "tsoron me kuma? Bata cin mutane, besides tare zamu je, just ku gaisa shikenan" na kalli kayan jikina, uniform ne a wanke a goge, hijab dina ya rufe har bom2 dina, fuskata babu kwalliya, dama ba kwalliyar nake yi ba. Na sake kallonsa har yanzu da dariya a fuskarsa. Yace "you look great, let's go" yana fadin haka ya shige gaba, na bishi a baya kamar wadda kwai ya fashewa a ciki. Direct visitors room muka je, ya dan tsaya yana kallona yace "are u ready" na girgiza kaina alamar no, yayi dariya kawai ya bude kofar da sallama. Nima nayi sallama na shiga. Su biyu ne kamar jiya da babba da karama. Ina kallon babbar nasan ita ta haifi Ibrahim sai dai bata kaishi tsaho ba, karamar kuma sam basa kama dan ta fishi hasken fata sosai, dan da kadan zan nuna mata fari, sai dai ita fuskarta duk kuraje yayin da tawa take tas. Kana ganin maman su Ibrahim kaga typical yaroba woman. Da daurin zanin ta akan riga, da goggoron akan ta. Ibrahim ya zauna a kusa da ita ni kuma na durkusa daga nesa a kasa na gaisheta da turanci. Ta amsa min amma daga gani turancin na isar ta yayi ba. A raina nace oho dai ni ba iya yarabanci nayi ba sai dai mu tsaya daga gaisuwar. Na gaishe da dayar tunda daga ganinta nasan ta girme ni. Ta amsa tana dariya, na dago kai sai naga Ibrahim ne yake hararar ta, ya wani dora kafa daya akan daya. Maman su kuwa idonta yana kaina. Sai da muka dan jima a haka sannan Ibrahim yace "Maimunatu this is my mother, and that girl over there is my sister" da saurin ta tace "his step sister" na dago kai na kalleta sai naga idonta a kansa, bansan dalili ba sai naji hankali na bai kwanta ba da kallon da take masa. Mamansu naji ta fara magana da gurbataccen turancinta "kullum na kira Ibrahim zancen sa Maimunatu tace kaza maimunatu tayi kaza, inna yi masa complain akan baya zuwa mana weekend sai yace ai muna karatu da Maimunatu sun kusa fara exams, kullum zancen kenan, shine nace bara inzo inga maimunatun nan dai da ido na" naja hijab dina na rufe fuskata, inaji tana masa magana da yarabanci, naji dai tace fulani a ciki, sai naji yace "mu fa yaroba ba'a wani kunyar suruka, in zaki bude ido ki bude, dan duk randa kika haihu ita zata yi miki wanka" na kara dunkule wa a guri daya a raina ina cewa kai Ibrahim mai ya kawo zancen haihuwa kuma? Gaba daya suka yi dariya. 'Yar budurwar ce tayi magana tace "let me introduce myself properly, ni step sister dinsa ce, ma'ana babana ne mijin mamansa, sunana Efisowa amma zaki iya kira na Efi, nazo in taya shi assessing sabida nasan ba iya zabe yayi ba. Dama tunda naji mama tace Fulani nace sai nazo nagani da kaina, gashi kuma naga kinyi kankanta da yawa" Ibrahim yace mata "shut off" sannan yayi mata magana da yarabanci itama ta mayar masa, sai maman tayi musu magana duk sukayi shiru. A hankali maman tace min "ina parents dinki?" Nace mata "suna cikin garin abuja" tace "ku 'yan Abuja ne" nace "'yan jigawa ne mu" kawai sai naji matar tayi min, yadda take magana a hankali irin maganar Ibrahim. Efi ce dai hankali na bai kwanta da ita ba, duk na damu ganin ta kasa dauke idonta daga kan Ibrahim. Ibrahim ne yace zai mayar dani class dan muna karatu, Efi ta sake yin magana da yarabanci shi kuma ya sake ce mata shut off maman tayi tsaki tana kallon efi alamar warning. Tunda muka fito bamu yi magana ba sai da muka dan yi nisa sannan yace "how do you like my mother" nace "she is OK, you look like her but taller" yace "no, she always say da baban mu nake kama" Har nayi tunanin kar in tambayeshi akan efi amma sai zuciya ta ta kasa jurewa, nace "Your sister doesn't like me" yayi dariya yace "yours doesn't like me either" nima nayi dariya sannan nace "but this is different, i feel like there is some tension between you two" yayi shiru bai bani amsa ba, wannan ya tabbatar min da zargina. Nan take naji raina yana kuna. Sai da muka kusa zuwa class sannan yace "koma menene da a tsakanina da efi is over tun tuni, abinda yake tsakanin mu sam bashi da dangantaka da efi. A mincewar mama da baba kawai nake bukata. Please Maimunatu don't screw this thing off. Mama tazo takanas saboda ta ganki, please show her your best behavior yadda in taje zata bawa baba labari shima zai yaba dake, please don't let Efi get in your head, that is exactly what she wants" muna zuwa gaban class din mu nayi shigewa ta ba tare da nace masa komai ba. Har na zauna yana tsaye a gaban class din ya rungume hannayensa fuskarsa da alamar damuwa. 


Bayan na zauna sai nayi tunanin ban kyauta wa Ibrahim ba, kuma gaskiya ya fada cewa this is our chance, ya kamata inyi kokari inyi probing to his mother cewa I am good enough, inna bari kishin Efi ya shiga raina tun yanzu to ina da problem. 


Anan zan tsaya inja hankalin 'yammata har ma da matan auren, idan mace ta nuna tana son mijin ki, musamman idan shi mijin ko saurayin baya son ta, don't make an enemy out of her, ki jata a jikin ki kiyi mata kirki sosai, make sure duk sanda saurayin ko mijin yake around kun nuna mata irin soyayyar da kuke yiwa junan ku, ita da kanta zata ji kunya ta ja baya, amma idan kika kama fishi da fada kamar kina tura shi gurinta ne. Ke kuma budurwa da kike neman miji, kar kiga wata da nata kiyi sha'awa kice lallai sai kin raba. In dai har soyayyar tsakani da Allah yake yi mata to ba zasu rabu bafa. 


Washe gari da yamma muna kofar library da Amira da wasu kawayen mu sai ga Ibrahim sun taho gurin mu shida Efi, tun daga nesa nake kallon yadda take ta shishshige masa, gaba daya kowa ya tsaya yana kallon su har suka kara so. Kallo daya nayi masa nasan ransa a bace yake. Suna zuwa yayi introducing dinta generally, sannan yace "she said she wants to look around the school" nayi sauri nace "she is welcome" tare da miko mata hannu, ta kalle ni sannan ta kalli Ibrahim kamar me neman izni shi kuma ya dauke kansa ya juya ya tafi, tayi masa magana da yarabanci bai amsa mata ba, ya saka hannayensa a aljihun wandon sa yayi tafiyarsa. Yana tafiya na fara yi mata hira, nayi mata introducing duk friends dina da suke gurin. Amira ko kallon ta bata yi ba. Daga nan nace tazo in showing her around, tun daga classes, labs, kitchen, dining hall duk sai da na kaita, sannan na kaita hostel. 

Hafsat tana kwance muka shiga, ta bimu da kallo, sannan tace min da fulatanci "wannan kuma a ina kika samota?" Na amsa mata da turanci "she is Ibrahim's step sister" sannan na kalli Efi nace "this is my Sister, Hafsat" Efi tace "oh my God she is so beautiful, nice to meet you" ta mika wa Hafsat hannu, kirikiri Hafsat ta ki bata hannu tace da fulatanci "ni bazan taba hannunki ba, kurwata kur" nayi dariya, Efi tace "what did she said?" Nace mata cewa tayi "ai kin fita kyau ma" nan da nan ta washe baki tace "thank u" Hafsat ta harare ni. Nan da nan Efi ta fara santin dakin mu, wai wannan ai ko a gida sai haka, ita in tana nan ai ba zata so ayi hutu bama. Nan da nan na chika mata gabanta da kayan chiye2 muka zauna muka yi ta hira, tana bani labarin gidan su. Amma ni bance mata komai ba akan namu gidan. Har akayi sallar magrib muna tare can sai Ibrahim ya kira ta yace ta fito su koma gida, haka kawai sai na samu kaina da jin babu dadi saboda ya kira ta a waya. Na dauko wani set din toiletries na mu na dove na saka mata a keda na bata. Tayi ta mamaki wai ina student har nake kyautar kaya?  


Washe gari Ibrahim yace min zasu tafi, na hado sweets da biscuits madu yawa a leda na boye a hijab dina saboda 'yan sa ido, yazo ya kira ni muyi sallama da mama. Ina shiga na gaishe ta, ta amsa min da sakakkiyar fuska sosai tayi min fada akan karatu, naji dadi har raina, na dauko leda ta na bata nace a kaiwa Abdullahi da Abdulrahman, kananan kannen Ibrahim. Taki karba na ajiye mata a gabanta na tafi. 


Da daddare Ibrahim yazo yana ta fada wai me yasa na kashe kudi na sayo kaya? In ina son in basu basai inyi masa magana shi ya sayo musu ba? Shi ya dauka siyowa nayi. Bayan kwana biyu sai gashi da kaya niki niki ya kawo min. 


Sanda muka fara SSCE kullum in mun shiga exam Ibrahim zai zauna a kofar hall din ya jira ni, har sai na fito ya tambayeni ya paper sannan zai tafi. A lokacin ya koya min jin kida, zai kunna slow music ya saka ear piece a kunne daya ni ma in saka kunne daya muna ji tare. Shakuwa ce sosai kullum take kara shiga tsakanin mu. Har tararradin ranar da zamu gama paper nake yi. A week to gama papers din mu PC ta kira ni tace federal government ta aiko a bada sunan best student za' a biya mata scholarship zuwa university of her choice. Dan haka tana sanar min cewa sunana zasu bayar. Nayi shiru ina tunani. I don't need the scholarship, daddy zai iya biya min karatu zuwa kowacce kasa nake so. Scholarship is meant for bright students din da iyayensu ba zasu iya biya musu school fees ba. Kawai sai Amira ta fado min a rai. Nan take nace da pc na barwa Amira, asaka sunan ta instead of sunana. PC ta nuna bata ji dadi ba, I am the best student that they ever had a school din. Nace mata to tayi contacting daddy ta sanar masa, duk abinda yace shikenan. 


Ana gobe zamu yi graduating Ibrahim ya kira ni yace zamuyi magana. Muna zama na lura he is serious. Yace "Maimunatu in kunje gida ina so zanzo in nemi iznin neman auren ki a gurin daddyn ku" zuciya ta ta buga da karfi na kalle yace "yes, ina so in samu permission dinsu saboda insan in da na dosa, just pray for us" 


I hope you enjoy this episode. Put on your seat belts because the next episode is going to blow u away. 


Maimoon

Episode Twenty three: The Break up 💔


Alright this is another long episode, nayi deciding zan ke yi da yawa ne saboda we have a long way to go. 


Na yi shiru na zuba mishi idanu kamar yadda shima ya zuba min. Can ya dan yi murmushi yace "are you scared?" Na gyada kaina alamar eh. Yayi dariya yace "I am scared too, amma dole muyi haka, saboda inaso in kun koma gida in ke zuwa gurin ki kuma kinga bazan ke zuwa bada iznin daddy ba, it's not right" na sunkuyar da kaina nace Allah ya kai mu. 


Washe gari har mukamuka fitar da kayan mu bakin gate banga Ibrahim ba, mun dawo hostel muna sallama da mutane sai gashi yazo bakin gate, daga ganin sa nasan cewa he is not OK. Hafsat ce ta tambaye shi "sir, baka da lafiya ne?" Yace mata "wallahi kwana nayi da zazzabi" nan Hafsat ta saka shi a gaba da tsokana wai dan zamu tafi ne, nima kaina zazzabin nake ji. Muka je bakin gate yace shi ba zai karasa ba, wai ko wanka bai yi ba baya son ya shiga gurin mutane. Nan Hafsat ta barmu ta karasa gate. Tana tafiya ya matso kusa dani yace a hankali "so, finally dai zaki tafi ki barni" nace "ba kace zaka ke zuwa ba" yace "ba dole in zo ba, dan ke fa nake zaune a garin nan, only for you, yanzu ma tunanin yadda zanke yin spending days with out you nake yi." Nace masa "ai zamu ke yin waya" yace "bayan ke baki da waya? Kuma in kinje gidan bakya kirana da wata wayar" nace "ai zan kira ka yanzu" "ban yarda ba, ki bani number mommy kawai" "laa to in ka kira ta me zaka ce mata?' "Sai ince mata son in law dinta ne" nayi dariya, a raina nace lallai wannan bai san wacece mommy ba. A fili kuma nace "Allah da gaske nake zan kira ka" ya marairaice fuska "yanzu tafiya zaki yi ki barni?" Nayi dariya ganin yadda yayi da fuskarsa, yace "au dariya ma kike yi min ko? Duk sanda daddy ya bani permission kullum sai nazo" nace "Allah ya kaimu lokacin" Hafsat naji tana kwala min kira, naga tana dago min hannu, nasan anzo daukar mu kenan. Naki tafiya, sai gata tazo tace in ba zaki tafi ba zanyi tafiya ta wallahi, na kalle ta na dauke kai. Sai tace au kuka zakuyi? Bani phone dinka inyi muku hoton tarihi, kawai sai ya fito da phone din ya mika mata, ta karba ta bude camera ta dauke mu. Na dan kwantar da kaina a kafadarsa shi kuma ya juyo da kansa yana kallona. Hoton yayi kyau sosai. Daga haka Hafsat ta figi hannuna muka tafi, ina jinshi a hankali yace "Maimunatu" amma ban juyo ba ballantana in amsa masa. 


Muna zuwa gida muka tarar daddy da mommy sun shirya mana surprise party na graduation, duk kowa yana nan har neighbours an gayyato, ga cake kato da hotunan mu a jiki ni da Hafsat. Nan da nan muka chanja kaya zuwa dogayen rigunan da mommy ta bamu as gift din ta, ta Hafsat pink tawa red. Munyi kyau ba kadan ba, mommy tayi mana light make up. Muka fito muka yanka cake tare da daukar hotuna, nan take naji duk na manta da wani rabuwa da Ibrahim. Muna gamawa daddy ya kawo mana nashi gift din. Muna unwrapping muka ga wayoyi ne sababbi fil kirar Samsung galaxy edge ta Hafsat pink tawa red. Ai ji nayi kamar daddy ya saka ni a aljanna. Muka rungume shi muna murna tare da cewa "thank you daddy". Bayan an tashi daga party muka dawo main palo muka dasa sabuwar hira, muna ta basu labarin makaranta su kuma suna bamu labarin abubuwan da suka faro sanda bama nan. Hafiz ya samu admission shima a Oxford inda zai karanci accounting. Anan daddy yake ce min sunyi waya da PC din mu akan scholarship dina, "is that what you really want" nace eh, yace "to shikenan zance a bata din, Allah yasa haka ya zamar miki sadaqatujjariya" nace "amin daddy" nan ya kara yi mana nasiha akan tausayawa na kasa damu da duk wanda muka ga yana bukatar taimako, wanda duk ya taimaki wani Allah zai taimake shi. 


Muna komawa daki da daddare mu ka dauko wayoyin mu muka kunna, dama already an saka mana sim cards a ciki. Hafsat ta dauko address book din da muka karbi numbers din friends din mu ta fara saving a wayar ta, ni kuma number da nake so inyi saving tana cikin kaina. Na zauna nayi dialing, bugu daya ya dauka, sai kuma na kasa magana, yayi ta hello3 can yace "maimunatu talk now, ko so kike zuciya ta ta buga ne" da mamaki nace "ya akayi kasan ni ce?" Yayi dariya yace "nasan babu wanda zai kira ni yayi shiru, wato wayo zaki yi min ko?  Ke kina jin murya ta amma ni kinyi min rowar taki ko?" Nace "a'a ba haka bane ba fa. Dama so nake ince maka daddy ya saya min waya" da sauri yace "haba? Amma daddy ya gama yi min komai" nace "ya jikin naka?" Yace "na warke yanzu tunda naji muryarki" na lumshe ido na ina jin dadin kalamansa. Dama Ibrahim da magana a hankali balle kuma ana tsara budurwa a waya. Na kwanta lamo a kan gado na rungume pillow, ina ganin Hafsat tana harara ta ni kuma na murguda mata baki. Kalamai Ibrahim yayi ta tsaro min wadanda nake jin su har 'yan yatsun kafata. A haka har bacci ya dauke ni. Da assuba karar waya ta tashe ni, da kyar na bude ido na na duba naga number Ibrahim, tunda banyi saving ba. Ina dagawa yace "a tashi ayi sallah sleepy head" cikin bacci nace "na tashi ai" yace "aa, ban yarda ba, ki shiga toilet ki kunna ruwa inji tikunna" na tashi na shiga toilet na daga sink sannan ya kashe wayar. 


Haka rayuwa tacigaba da kasance mana ni da Ibrahim, kullum muna makale a waya. Wannan yasa na rage zaman falo sai bedroom. Da naji mommy ta taho kuwa sai in kashe wayar. Babu abinda Ibrahim bai tsara min ba, ya gama tsara mana rayuwar mu kaf, tun daga design din gidan da zamu zauna, 'ya'yan da zamu haifa, yace duk so yake su yi kama dani amma mazan suyi tsahon sa. Ni dai sai dai inyi dariya ko ince masa to. Wani lokacin yakan sakj layi ya koma bedroom secrets ni kuma da naji haka sai in kashe wayar. 


Munyi three weeks da dawowa Ibrahim yace yana son zuwa, yana son in gaya masa ranar da zai samu daddy a gida. Na gaya masa yace to in jira shi. 


Ranar da zaizo tun safe na tashi da mutuwar jiki. Muka yi waya da Ibrahim na ce masa ya bari sai yamma tunda yanzu daddy baya gida. Nayi masa text din address. Allah ya soni mommy tana office tun safe, dan haka na shiga kitchen na gaya wa cook abinda nake so ta hada min zanyi bako. Tana dariya take tsokana ta "it is about time, ya kamata mu fara ganin samari a gidan nan" nima nayi dariya nace "asma'u ba fa saurayi na bane, just nace miki zanyi bako sai kice saurayi?" Ta tabe baki tace "ai ku 'yan boko haka kuke, sai kuce baku isa aure ba" da naga dai magana take nema sai na fice na bata guri, dan banajin dadi sosai. Nayi wanka na na saka wata blue din atamfa mai pink flowers, riga da skirt, na gyara fuskata da powder da wet lips, na fesa turaruka na masu dadin kamshi. Hafsat tana kwance tana kallona tace "finally yau zai zo gidannan, I salute his courage" na ce mata "shut your mouth, saidinawa masu bacci da ido daya" na fita na kira wani daga cikin yaran gidan nace ya saka min kujeru a garden. Na dawo falo na zauna nayi folding hannuna zuciyata tana bugawa. 


Har five daddy bai dawo ba, Ibrahim bai zo ba. Hafsat ta sauko tana kallona tace "you look pale moon, relax" nace mata "baki san mai nake ji ba Hafsat" waya ta ce tayi kara na duba naga Ibrahim ne, na dauka yace "Am here, ina gate, your security won't let me in" tun daga muryarsa na gane he is somehow not happy" nayi sauri na dauki gale na pink na fita, ina jin Hafsat tana cewa "good luck". Ina fita wani security ya karaso guri na yana min bayanin wani yazo gurina, nace masa su bude masa gate, nima na yi hanyar gate din da sauri. Yana shigowa wani security ya zo da bomb detector yana shafa masa, da sauri na daga masa hannu nayi masa alama da ya matsa daga gurin. Na karasa da sauri ina kakaro murmushi, shima murmushin yayi min da side daya, da alamar bacin rai a fuskarsa. Complete yaroba attire ya saka. Riga bubu three quater da wando mai fadi, sai hula da aka dinka da yadin shaddar, ya lankwasa hular zuwa side din fuskarsa. Nayi masa sannu da zuwa na wuce gaba da dan sauri shi kuma ya biyo bayana. Kamar daga sama naji ance "hey!! Where are u going?" Na juyo naga chief security din gidan ne yake wa Ibrahim tsawa. Zuciya ta naji ta buga da karfi. Na juyo a fusace na kama yi masa masifa shi kuma yana bani hakuri cewa bai san tare muke ba. Yadda yake kallon Ibrahim kadai zaka gane assessing kayan jikin sa yake yi. Banyi aune ba sai ji nayi gate ya bude, lokaci daya Royce Rossey din daddy ta danno kai harabar gidan. Ji nayi kamar kafata ba zata dauke ni ba, ni kame kam a gurin da nake haka ma Ibrahim. A hankali motar take gangarowa har tazo dai dai saitin mu sannan glass din ya fara sauka kasa. Innalillahi wa inna ilaihir raji'un kawai nake ambata a zuciya ta dan bakina bazai iya furta komai ba. Fuskar daddy ce ta baiyana cike da kwarjini da kyau da kasaita irin na fulani. A hankali ya chire glass din idonsa yana kallona sannan ya mayar da kallonsa kan Ibrahim. Daga ni har Ibrahim babu wanda yace komai. Ya mayar da glass din idonsa sannan glass din motar shima yayi sama a hankali har ya rufe sannan motar ta mirgina tayi gaba. Ajiyar zuciya mai karfi na sauke, sannan na fara jin wanj sanyi yana shigata alamar zazzabi. 


Na juya na kalli Ibrahim wanda har yanzu motar yake kallo. Nasan idan ba a movie ba Ibrahim bai taba ganin RR ba, dan very few people ne suke da ita a Nigeria. Nace masa "let's go" amma bai motsa ba. A hankali yace "I guess that is your father, the man I am suppose to meet today" kaina a kasa nace yes. Da haka na juya na nufi hanyar garden. Sai da nayi nisa sannan ya biyo bayana muka karasa tare. Muna zuwa na nuna masa kujera amma sai ya tsaya ya fara safa da marwa. Ni dai na zauna na zuba masa ido. Dan kansa kuma yazo ya zauna yace "why didn't you tell me" nace "me fa?" Ya kalleni bacin rai karara a fuskarsa yace "you clearly know what" nace "me kaso ace na gaya maka? Cewa babana ambassador ne? Muna da katon gida mai cike da securities?" Ya katse ni da cewa "hell yes!! Exactly like that, da kin gaya min haka da nasan mai zan fuskanta ai" nace "it doesn't change anything" yace "it changes everything, ni maimunatun da na sani is a simple daliba, wannan kuwa is a princess living in a castle guided by a bunch of dragons" ta gefen ido na na hango driver yana fito da motar yaya Walid daga garage, da alama fita zai yi. Na dawo da hankali na kan Ibrahim nace masa "I am still me" ya mike tsaye ya cigaba ba safa da marwa "ta yaya kike tsammanin mutun kamar ni zaije gurin mutun kamar babanki yace masa yana neman auren 'yarsa? Daya kalleni abinda zai gani shine some stupid yaroba parasite da zaiyi feeding on his daughter, he will take one look at me and ask his security to throw me out" zafin zuciyata naji ya karo, na mike tsaye ni ma "don't talk about my father that way, baka san shiba, ba haka yake ba. Don't judge him without knowing him" gani yayi da gaske raina ya baci, sai ya tsaya yace "am sorry maimunatu, am just not myself" na zauna shima ya zauna. Ta gefen idona na hango Ya Walid ya fito daga gida ya nufi motarsa. A cikin zuciya ta nake cewa "karka juyo, karka juyo" amma kamar wanda na takarkare na kwalla masa kira sai gani nayi ya juyo din kuwa, ya dan dakata yana kallon mu, har da saka hannunsa ya kare hasken rana. Har ya bude kofar motarsa sai kuma ya rufe ya sake kallon inda muke, na kalli Ibrahim naga shima shi yake kallo. Kawai sai naga ya nufo inda muke zaune. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai nake ta maimaitawa a raina. Ibrahim yace "I guess this is your brother" nace "yes". Duk gidan mu Ya Walid ya fi mu hasken fata, fari ne tas dan har yalo fatarsa take yi. A kyau kuwa ba daga nan ba. Dan gayu ne na ajin karshe, ballantana kuma yau kamar fitar musamman za'ayi. Shirt da wando a jikinsa 'yan gaske, kansa babu hula sai gyaran da gashin sa ya sha sai daukan ido yake, takalminsa da agogon hannunsa kadai abin kallo ne. Ya karaso gurin mu idonsa a kaina, sannan ya kalli Ibrahim da alamar tambaya a fuskarsa. Ya bawa Ibrahim hannu suka gaisa. Da fulatanci ya ce min "Moon a inda za'a kare kenan?" Na bata fuska yayi dariya, sannan yace da turanci "idan mommy ta dawo kice mata na fita" sai a lokacin na tuno cewa mommy tana iya shigowa a kowanne lokaci. Na gyada masa kai kawai. Ya juya yayi taku biyu sai yayi juyi 180 ya dawo yace "baki yi introducing din mu ba kuma" nayi murmushin yake nace "Ibrahim wannan shine yaya Walid, babban yayan mu, Ya Walid wannan shine Ibrahim my.... " Ibrahim yayi sauri yace "her former teacher" nayi sauri na kalleshi amma sai naga bani yake kallo ba. Ya Walid ya dan jinjina kai yana dan turo baki, sai kuma ya juya zai tafi, two steps ya sake tsayawa a raina nace "oh dear God, what now" ya juyo fuskarsa da alamar tambaya ya sake kallon Ibrahim sannan yace min da turanci "Ohh ko shine wanda kwanan baya kika sa daddy ya samo wa aiki?" Zuciya ta naji ta bug sau biyu a tare sai kuma ta tsaya chak, jini yayi draining daga fuskata. Ya Walid ya lura da chanzawar yanayi na sai ya daga kafada yace "what did I said?" Daga haka ya juya ya nufi motarsa kirar Ferrari wacce ba'a dadr da saya masa ba. Ta bata wuta, ya kunna kida ya figa a guje a fice. 


Tunda ya bar gurin babu wanda yayi magana a tsakanin mu. Can Ibrahim yace "you really are a genius maimunatu, you played me like a fool, and like the fool I am I am madly in love with you. What a foolish fool am I" a hankali nace "I am sorry" ya sake mikewa, "sorry? Do u just say u are sorry? Wato kina ganin bazan iya samarwa kaina aiki ba shine kika je ki ka gayawa daddy ya samomin?" Nima na mike tsaye "ni bance ba zaka iya samarwa kanka aiki ba, ka riga ka kai takardunka ka nemi aikin ka da kanka... " ya katse ni yace "amma ni da ke munsan da baiyi magana ba baza'a bani ba" yayi shiru sannan ya cigaba "PC tace min wani ambassador ne yayi endorsing dina, I should have known, amma da yake I am a fool sai na karba ina murna" magana yake yi da karfi cikin bacin rai. Out of no where naga chief security yazo gurin "ma'am is this man bothering you?" ban san sanda na rufe shi da masifa ba nace idan bai bar gurin ba saina saka ya bar aiki. Bashiri ya bar gurin. Na sake cewa da Ibrahim "am sorry, ban dauka ranka zai baci har haka ba, naga kana son aikin kuma I didn't want to loose you. I love you" na fada ba tare da realizing cewa na fadi L word ba. Murmushi Ibrahim yayi sannan a hankali yace "and I love you too, only too much" ya karaso inda nake tsaye ya saka hannayensa biyu ya riko fuskata yana kallon jajayen idanuna, ya cigaba da cewa "I am going maimunatu, zan dawo in ga daddy amma sai na zama worthy of u, sai na zama worthy of meeting your daddy, sai na zama someone da zaki nuna wa family dinki. Please wait for me, I will come back for you, I promise you" i dona a cikin nasa nace "you are already worthy enough to me" ya dora lips dinsa akan goshina for what seems like eternity sannan ya juya bayansa ya kama hanyar gate. Kamar hadin baki sai ruwan sama ya tsuge. Ina tsaye ina kallonsa har ya isa bakin gate sai kuma na tafi da gudu na shiga gida, direct sama na hau, na wuce dakin mu na bude kofar balcony na fita na hangoshi ya fita daga get din ya dau hanyar fita daga quarters din, hannayensa a cikin aljihun rigarsa, yana tafiya a hankali yayin da ruwan sama ya ke sauka a kansa. 


Anan zan dakata inja hankalin samari da 'yan mata a harkar neman aure, in kaga budurwa kana sonta itama tana sonka, in dai har kana da halin yin aure, ma'ana kana da aiki ko sana'a wadda kasan zai iya rike ku to kar kace sai kayi kudi zakayi aure, hakan bashi da ma'ana. Maybe baka da rabon yin kudin. Maybe arzikin ka is linked with her. Fadin ubangiji ne cewa kowacce rai da arzikinta take zuwa duniya, idan baka da arziki sai kaga a sanadiyyar auren da kayi, ko haihuwar da matarka tayi Allah ya baku arziki. Kuma abinda mutanen mu har yanzu bamu gane ba shine, idan kayi aure baka da arziki, kukazo kukayi arzikin tare da matarka to kun fi mutunta juna, ku sha wahala tare kuji dadi tare. Indai har yrinya tace tana sonka, indai har soyayyar Allah da annabi take maka to bata damu da kudinka ko rashin kudinka ba. Wannan wait for me shiriritar bata da ma'ana, kana can kana neman kudin wani zaizo wanda ya fika komai kuma she may fall in love with him, kaga kayi losing kenan, biyu babu. 


Next thing da nake so inyi magana akansa, duk da dai sai a next chapter za'a fi fahimtata sosai shine akan judging mutun ba tare da kasan sa ba. Never judge a book by its cover. Yawancin mutane suna da kirki, no matter the tribe, you just need to know them. Masu kudi da masu sarauta, in kaga wulakanci a tare dasu mostly daga gurin na kasansu ne ba daga su bane. You just need to take a deep breath and talk to them...


Next thing shine secrets in a relationship. In kuna so relationship din ku ya dore, never ever keep a secret from each other, never lie to each other. 


Ga 'yammata da samarin da suke tsoron relationship dinsu ba zai dore ba saboda banbancin yare, ko social status, do u try to make it work ko kuma a boye kuke yi? Just take a deep breath ku tunkari iyayenku da maganar, it may turn out easier than you imagine. Ita zuciya an halicceta da son wanda yake kyautata mata, ko wanne kabila ne shi, indai har zai juri kyautatawa iyayenki, yana nuna musu best behavior dinsa, ke kuma kullum kina nuna musu how much you love him, insha Allahu zaku ga chanji a gurinsu. But most importantly pray.



Post a Comment

0 Comments