INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar
®NWA
xarahbukar.wordpress.com
36 - 40
K'ashe gari da k'arfinta ta tashi, fuskar ta dauke da murmushi dan kuwa tayi alwashin daina zubda tsad'addan hawayen ta kan matsiyacin nan, ranar kin dillanci kadai take jira.
Kayan jinkinta ta cire ta dauro zanin wanka ta fito tsakar gidan, bayin ta leka taga babu ruwan balle famfo sai bukitin k"arfe marar hannu dake ajiye, tsaki taja aranta tanai tir da talauci, kofar Inna kulu ta nufa ta tsaya, babu ko gaisuwa tace "Tsohuwa xanyi wanka".
Daka cikin k'uryar dakin Inna tace.
"nazo na mike ne ?
Mikewa tayi hade da sunkutan redionta ta fito tana kara maimaita abunda ta fadi.
Cike da tsiwa Batul ke kollanta, "ruwa zaki ban nayi wanka"
Yar tsugunno dake gurin Inna ta dasa mazaunin ta akai sannan tace "ayyo ainan babu ruwa, waje zaki je akwai burtsatsan unguwa saiki dibo"
Kallon rainin Batul takai mata, tayama xata fita waje diban ruwan kamar wata buduwar k'auye, agidama Hassan ke jamata ruwa a rijiya balle kuma nan daba zama taxo ba.
"Ba girma na bane, saidai jikanki ya fita ya debo min"
"Toh saiki jirasa yaxo" Inna ta fadi cikin ko ta kula da kallon da take mana.
"Ina ya fita da safan nan" Batul ta tambaya .
Banxa da ita Inna tayi, saima redio data kunna jin labaran karfe takwas. Tsayuwar mintinu ashiri Bayul tayi, Inna bata tanka taba, wanka kadai takeson yi danji dadin jikinta, ganin tsayuwar ba amfani yasan ta komai daki tasanya hijb ta fito, bokitin dake bayin ta dauka ta fice waje.
Sai yanxu ta karewa unguwar kallo, jama'an cikin ta ba abun kallo akara bane, gaba da gidansu kadan butsatsan yake, mutane kusan ashirin data ganin bisa layi yasata jan mugun tsaki, itakam bada ita zaai haukar nan ba, dole nema subarta ta diba dan ita ba kalar subace. Karasawa tayi tanai ma kowa kallon wulakanci, su dinma ita suke kallo, dire bokitinta kusa da wanda tagani yana diba, jira kaidai take ya cire tasanata, yana cirewa kuwa ta sanya, murmushi tayi ya kusa cika babu wanda ya tanka ta, saima kallon ta da kadai suke, kadan ya rage ya cika, wata yarinya dake can baya ta karaso tasa hannu tayi wurgi da bokitin ruwan ya kelaye gurin.
"Ke kin isa, wa kika fi gashin tsuliya anan dahar zaki raina mana wayo kizo ki ganmu alayi dan iskanci shine zakiyi babakere" yarinya mai suna Dija ke magana cikin karaji da zare idanu.
Murtukewa Batul tayi, ta nunata da yatsa, "ke bakauyiya, ki kiyaye ne, kinsa dawa kike magana kuwa "
"Nasani mana, da mutum nake bada dabba ba, layi kuwa sai kinbi tunda ba ubanki ya kafa famfam ba" kallon sama da kasa Dija ke mata ayayinda take maganar.
Dariya yan gurin su kwashe dashi, daya dake gurin tace "kalle tafa damu da ita banga bammaci ba, sai felekan tsiya harda wani ansan dawa take magana, kaji ja'iri, mukam nan saidai kici na jaki"
Ruwan ne ya cinye Batul tayi tsit, tayi underestimating dinsu, batayi expecting zasuyi magana ba yadda tayi masu kallon yan primitive society, cike da kunya tadau bokitin ta koma baya ta tsaya, dariya kuwa basu fasa ba, ignoring kadai Batul tayi har layi yaxo kanta, bisa kai ta aza ta koma gida cike da tausayin kanta. Wanka ta shiga sharp shrp ta fito, sauri take tana da lecture by 10.
Kwalliya sosai tayi cikin atamfa riga da skirt ta fito ta riske Inna hartai wanka tana zauna bisa tabarma tana shan shayi da buredi da fried kwai, mamaki karara tayi yaushe Inna ta debo ruwan waima yaushe ta kunna murhu aza ruwan zafi da soya kwai, gadai murhu babu alamun an taba, tsaye tayi kan Inna, "kudin mota, xan wuce makaranta"
Cikin fara'ar Inna ta kalleta tace "mijinki zaki tambaya bani ba, kuma ai kyaci abinci kafin ki fiti ko".
Kaman jiran take tace toh xan ci" wazai ga kwai da biredi ya kyale, dama yunwa takeji ba kadan.
"Gashi" inna ta fadi hade da mika mata bakar leda
Budewa tayi da azama, saidai abunda tagani yasata yamutse fuska, taliyar hausa ce danya da manja da kulli gishiri da yaji, "Tsohuwa miye wannan"
"Abincin ki mana, dare da rana, ga murhu can ki dafa asawake, ga langar samira xan ara miki tunda baki kawo tukunya daga gidan kuba"
Kuka ne ya rage Batul batai ba, daurewa kadai tayi ta ajiye ledar ba tare datace uffan ba, tunanin kawai take ta tashi ta gudu ne ko yaya, toh idan ta gudu taje ina, shi wanda take muradin so baima san da zaman taba, fuskar sama ba sani tayi ba, ance he is rich & simple, amm toh ina zata ganshi, burinta daya taga tazama matar mai kudi ba matar matsiyaci ba.
Zaman kusan awa biyu tayi gurin Mamuda bai zoba, yunwa na nema illata ta, mikewa tayi tahau aza murhu, abunda bata taba yiba saidai Hajjo tayi, ba karamin wahala tasha ba sannan wutan ya kama, karamar bokiti datagani tadau ta debo ruwa ciki tahau kikirkiri din daura taliyar.
Bayan ta sauke, ko tayi batama Inna ba tahau ci. Sai bayan Sallah azahar Rasheed ya shigo gidan, tana ganin sa tahau surfa masifan yaja mata bataje makaranta ba, gaisawa da Inna yayi kafin ya zaune yace mata "banda halin ciyar dake da biya miki na makaranta, hakuri xakiyi idan Allah ya hore nan gaba kyaje, rayuwa saida manaji, ina abinci na ?
Ya gama soka mata kibiya azuciya, daskerwa tayi tana sauraran sa sannan tace "duk inda kudi suke dole ka nemo su, uwarka ma tayi kadan ta hanani zuwa balle kai karan kadan miya, abinci kuma ban dafa dakai ba"
Kallonta kawai yake bai ce uffan ba, aransa fadi yake bakisan uwata ba dole kice haka, duk randa kika shigo hannuta zaki gane ruwan ba sa'a kwando bane.
Masifa sosai da fitsara tayi tamai, wata zuciyar nace mata toh idan kinje makarata kicewa su Billy mene, ai da kunya ma, kila ma sun gama yada ta aduniya, hakura kadai zatayi tayi da batun makaratta kafin tasan abunyi nan gaba.
****
Sati biyu zani bata canxa ba, halin Batul sai wanda ya karu, akullum Rasheed xaije gidan amma maganar arziki bata hadasu, iya kaci susha hira da Inna da dare ya koma gida, dadi sosai Batul takeji aganinta a kekensa yake kwana waje ita ta kame a daki, wanka da cin abinci duk bayayi agidan, atunaninta tsoronta ya hanasa sakat.
Ta bangaran Inna kuwa ta rasa daga ina ake kawo mata abinci mai rai da lafiya, saida taga tanaci amma ita an barta da manja da yaji, ba abunda ya shafe ta, opportunity kadai take jira ta fece.
Yau ya jima a gidan suna hira da Inna, sai kusan tara yamata sallama, rai bace yabar gida, yafara gajiya da cin mutunci Batula, sakinta zaiyi ya shafawa kansa lapia tunda ba sonta yake ba. Inyaso taje can ta karata da karyar ta, shidai Rmd ya mata nisa saidai ta nemi wani can daban.
Agajiye likis ya dawo gida bayan ya tsaftace jikinsa, Mom ya tarar tsaye tsakiyar palon tana kai komo, kafin yakai ga isa gareta ta tunkaro sa, cike damuwa tace "my boy daga ina kake by this tym
Agogon hannusa ya kalla, goma dayan mintinu amma ji yadda take interrogating dinsa kaman karamin yaro ,rabawa gefenta yayi ya zauna kan kujera,
"Ancemin kwanan biyu bakaje office ba, idan kasa wasa asset dinmu xai iya dropping" ta fada tana kai mazaunin ta dayan kujerar dake gefensa.
Takaici ne ya cikasa, matan biyun duk sun dauramai zafi, ya dawo gida bai tsira ba, Mom dinsa mai kudi amma sai shegen son kudi alway seeking for more, dayar can kuma talaka but desperate to be rich by all mean, kodayake baima san inda ta dosa ba, karyata kadai ya isheshi bugun zuciya.
Nisawa yayi yace " Mom gayamin make tsakanin ki da Hajiya safara"
Gabanta ne ya fadi, wace irin tambaye ce wannan, ta fadi aranta, afili tace "babu komai, kawata ce tun muna yammata, miyasa ka tambaya ?.
Kawar da tambayar yayi dacewa, "na yadda xan aure Mardiyya"
Dariya mai dauke da farin ciki tayi, "ka fara sonta kenan ?
Kai y girgiza, "a'a, xan bata chance ne, you once said kwarya tabi kwarya, shiyaaa nayi deciding auranta"
Dadin sosai Mom taji, atleast xata huta da threat din Hajiya safara, saidai wani hanzari ba gudu ba, zusa katsina ya kamata, amma da wana ido zata dubi kawu Habibu, kusan shekarau sama da ashiri ta yayesu a ababin rayuwar ta, saukin abun ma My boy yakan kai masu ziyara. Mikewa Rasheed yanai mata Sai da safe, bai jira cewarta ba yayi gaba, tuni ya gano ta lula duniyar tunanin dabai san ta miye ba.
Bayan kwana biyu ba inda yake zuwa sai office, da wuri yau ya shirya ya fice office, aiki sosai ya wuni yana yi, charles ne ya shigo yace Mardiyya keson ganinsa it urgent, izini ya mai data shigo, sanna ya fice.
Da sallama ta shigo, hannun ta rike da files, amsawa yayi yanai sakar mata murmushi, karfin gwiwa ta samu ta karasa ta hade da mika mai, bai karba ba ya mata nuni da ta ajiye,
"Ki zauna mana" ya fada ganin tana shirin fita.
Akunyace ta zauna, yace "Momcy bata gaya maki good news ba ?.
Sunne kai tayi danta gane inda xancen ya dosa,
"Ya preparation"
Nisawa tayi, dakyar tace "babu wani shiri, am sure kaima you aint interested da wani grand Preparations".
Murmushi yayi yana cigaba da kallonta, duk lokacin nan yarasa miyasa bai gano good side of her ba sai yanxu, koda yake Batula ta sanya shi gano hakan, sau da dama akance yaran masu kudi basu da tarbiyya ashe ba duka aka taru aka zama daya ba, guntun tsaki yaja aranshi, bai taba cin karo da bad girl irin Batula ba, wani mugun tsanar ta yakeji aranshi.
"Marfiyya inason auran nan yaxama grand weedding, wanda kowa a duniya saiya san ni Rmd nayi aure".
Tsuru tayi tana kallonsa, ita mamaki ma yabata all of a sudden ya yadda da auranta kuma big wedding yakeso, kodayake itama hakan takeso, halinsa yasa ta kama kanta.
Hira sosai sukayi kaman masoyan asali, tun tana kame kanta harta saki jiki tana dariya.
*Katsina*
Wedding Bells 💃💃💃💃💃💃💃💃💃
[10:00PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar
®NWA
xarahbukar.wordpress.com
41 - 45
Katsina..
K'arfe sha biyu na rana direban Mom yayi horn gaban kataferan gate din gidan Kawu Habibu, bude gate mai gadi yayi da azama kansancewar ubangidansa ya sheda mai zuwa su.
Parking yayi ya fito ya bude mata kofar b'angaranta, cikin isa ta fito tanai karewa gidan saman kallo sannan ta taka zuwa tangameman palon.
Ajiyar zuciya kawu Habibu ya sauke, tun shigowarsu yake tsaye bakin window benan yanai kallonta, hali da bazai canza ba abunda kadai ya furta sannan ya juyo saukowa.
Hajiya Suwaiba matar sa ta fito daga kitchen, kicibis tayi da ita tanai ma palon mugun kallo, "hajiya Fati harkin karaso ashe, sannu da zuwa" Hajiya Suwaiba ta fada cik'e da fara'a.
Ayatsine tace "sauri nake kice wa Kawu na iso"
Gyaran murya kawu Habibu yayi yana saukowa.
Kunya ne ya kamata batayi tunanin zai jita ba, mazewa tayi tace "Kawu ashe kana kusa, ina wuni".
"Lapia lau Fatima",ya amsa hade da zama kan kujera, itama zaman tayi, hajiya Suwaiba ta koma kitchen nema mata abun sha.
Gaisuwa sukayi mai tsawo kafin Mom ta gabatar da abun da ya kawo ta, Jinjina kai kawu yayi, yasan tabbas rana irin tayau zataxo, matar da bata daukesu abakin komai ba shine yau ta tako taxo dan danta xaiyi aure, ashe dai komai nada ranarsa.
Nisawa yayi yace "naji dadi matika, Abdulrasheed zaiyi aure, naso ace na hadashi da diyata Hafsat saidai hakan bai yuyu ba".
"Gaskia ne" Mom ta fadi tana murmushi dabai kai zuci ba, yaushe ma zata yadda Hafsat ta auri Rasheed, mai kawu yake dashi ma, mutumin da rabin dunkiyar sama Ubanta ne basa, dan lecturing da yakeyi nawa yasamu, shima dai xance kawai yage, bazata yuyuba, Mardiyya ce daidai da Boy dinta.
Tattaunawa sukayi da kawu, sannan ta gayamai sun riga sun tsayar da rana sati daya kacal, farin ciki sosai Kawu yayi, yanaji da Rasheed tamkar dansa, halin uwarsa kadai yasa yake maintaining distance. Sun dade suna magana daga bisani Mom ta masu sallama ta kamo hanyar Kd.
Gidan Hajia Safara ta nufa, nanma sun dade suna tattauna yadda buki zata kasance, daga bisani ta mike zata wuce suka hadu da Abban Mardiyya ya shigo, gaisawa sukayi da Mom yana zolayarta ya shirye shirye, dariyar kawai tayi bata amsa baima ta wuce waje Hajiya safara ta rakata bakin motar ta. Murmushi Abban Mardiya ya saki aransa yana fadin "ku gama shirin bukin ku kafin nima nawa buki yaxo" darawa yayi ya karasa wuce warsa ciki.
***
Bikin ya kusanto gadan gadan, kwana biyu kadai ya rage, pre-wedding picture kusan ashirin suka dauka da differnt photographers, sunyi matukar kyau, matured style sukayi wanda bai sabawa addinin musulunci ba, Duk inda ka shiga xancen kadai ke ruruwa, Iv din bukin da picx sai yawo suke a social media, daga masu murna sai masu ihu ganinsa, wasu dan shishigi ma har watapp name dinsu Rmd suka maida.
Tun bayan datayi sallar azahar Batul take jin jikinta amace, gabadaya ta rasa make mata dadi, shi matsiyacin can kusan sati bata gansa ba, hajjo da Baba da yan kannanta ne suka fado mata arai tahau lalubar wayarta da tunga aka kawota bata bi takan shiba, dauka tayi taga yaki kunnuwa, tsaki taja sanin cewa rashin caji yahana ta kunnu, gashi kuma gidan ko wuta babu balle soket.
Fitowa tayi tadau bokiti tace, "Inna na fita dibo ruwa"
"Kar dai ki dade"Inna tafada daga cikin daki.
Dire bokitin tayi ahankali bakin karga sannan ta fito tsakayir unguwar dubawa tayi ko zata samu masu cajin haya, wayam babu ko alamun su, wani gidan siminti tagani can gaba dasu da wutar lantarki awaje, da azama ta taka ta shiga gida, Kwakwasawa tayi, yarinya mai suna Hafsat Rano ta bude,
"ina wuni, dan Allah caji nakeso asamin, ga gidan mu can" Batul ta fada tana mata nuni da gidansu.
Shigo, amma maman mu ta fita" acewar Hafsat.
Godiya Batul tayi ta shiga ciki, yammata biyu zaune tagani kusa da socket suna cajin wayoyinsu suna chating, kaman munafuka ta gaidasu sanna ta sakala nata cajin, gefe guda taja ta zauna hade da tagumi.
Dariya daya cikin yammatan mai suna Baby nurse tayi tana fadin "nashige su mistakely na tura pre wedding picx din Rmd da matarsa group, yaukam nasan dole xarah ta cireni".
Dayar mai suna Dija Waziri tace "maiya kaiki kinsan dai Xarah bata bari aturo abunda bai shafi littafi ba, turomin hoton Iv dinsu, zakije Dinner din ?.
Ihu murna Baby Nurse tayi tace "invited or no invited we must be there,".
shewa sukayi hade da tafawa, (ni xarah nace gayyar sode)
Sauraran su Batul take amma tarasa inda xancen su ya dosa, kalmar Rmd kadai hankalinta yafi karkata akai, kasa daurewa tayi ta kunna wayarta, gashi kuma bata watsapp balle su turo mata hoton, karfin hali tayi tace "sis dan Allah turonin picx din Rmd ta Bluetooth".
Kallon banza Baby nurse takai mata, abun mamaki wai ta bluetooth, har yanxu ana yayin sane ta fadi aranta.
Cikin rawar jiki Dija waziri ta kunna Bluetooth tahau tura mata, godiya sosai Batul tayi bata tsaya jiran wayar ta cika ba ta cire ta koma gida, dakinta ta shige da gudu batare data tsaya sauraran Inna dake magana ba.
Addua takeyi wayar na bisa kirjinta, so take ta kalli pic din amma tana tsoro karya zamana Rmd da take muradin samu bai hadu ba, dakyar dai tasamu courage ta kalli pic din, kur tayi tana kallon kyakyawan fuskar sa mai dauke da murmushi, saidai kuma kaman taso tasan fuskar wani guri, a iya tunanin ta bata gano ba, sanin ya mata nisa inama zata ganshi, wani irin sonshi da begansa ne ya mamaye zuciya ta, ware idanu tayi adaidai lokacin da suka sauka a fuska Mardiyya, tsaf tagane ta kwanaki sun hadu a ostrich bakery, last tym da taganta ba karamin burgeta tayi ba amma yau duk sai taji wani irin haushi da kishinta....dafe kai tayi tana fadin innalilahi wa inna'ilaihi rajun, Mamuda ka cuceni,, adalilinka wata ta maye gurbin wanda nake muradi arayuwata, Allah ya isa tsakanin dakai, na tsane ka, banza matsiyaci dan tasha" kuka sosai ne ya kufce mata, su baba da hajjo da tayi niyan kira fasawa tayi, wurga wayan tayi gefe cike dajin haushin su, koma miya faru sune suka caza mata.
******
Buki Budiri ya kankama💃, duk wata shagali na bukin hausa, turawa dana India gabadaya an kwatanta, duk fadin duniya zancen su ake, BBc, cnn, aljazeera, channels, nta tashoshi da dama ka kune hirar auran Rmd Da Mardiyyah ke wanzuwa, manyan mutane ,yayan sarakuna da gwamnoni duk sun hallara ranar daurin auren su.
Karfe 3 na rana aka mika amaryan gidansu Rmd nan inda suke zama da Mom, Hajiya safara baki yaki ruhuwa sai murna take yarta tayi goshi, guraran 8pm aka fara shirin tafiya haddaddiyar Dinner da xaa ayi a fountain Mansion...ni xarah nace bara na leka Batula nasan za ayi african time kafin afara.
**
"Yaunxu Batula baza ki bar kukan nan ba, abu yakici yaki cinye wa tun shekaranjiya kina abu daya" Inna ta fada tana tsaye bakin kofar dakin.
cikin shesheka tace "Inna dan Allah kice wa Mamudu ya dawo ya sakeni, bana sonshi, ki taimaka ya sakeni na auri wanda naso" karasa maganar tayi cikin kuka mai tsuma zuciya.
Ba karamin tausayin ta Inna taji ba, karasa shiga dakin tayi ta zauna gefen ta tana fadin "karki damu very soon xai sakeki,
"Dagaske Inna" ta fada in cool voice.
Kai kadai Inna ta taga mata alamu eh, hankalinta na kan fuskar wayar Batul, hoton Rmd din ke kan screen saver ta wanda tuni tayi croping ta cire fuskar Mardiyya, "kaico yarinya kishe ke dawainiya dake," inna tace aranta
Lallashi sosai Inna tahau yi mata amma kamar zugata take kara sautin kukan ta take.
Tamkar an tsigare ta mikewa tayi tana zara idanu sannan ta janyo ghana must go din ta, budewa tayi tadau yar dubu daya rak data mallaka arayuwarta sannan tadau jan gyale ta yafa bisa kodaddiyar goriyar atamfa dake jikinta, "Ina xaki adaran nan" Inna ta fadi tana kallonta.
Cikin saurin tace "bazan dade ba" ficewa tayi da azama ba tare da ta jira cewarta ba.
Sauke numfashi Inna tayi ta mike tsaye tana kai komo adakin, yazamata dole tama Rasheed magana, lokaci yayi dazai fito ya nuna mata shine wanda takeso tun kafin ciwon zuciya ya kamata, yadda taga Batul na kuka ta yadda cewa lailai tayi sanyi kuma ta saduda, dakinta ta nufa tahau lalubar wayarta dan kiran Rasheed.
Babban titin unguwar ta tako tanai sak'a da warwara a zuciyan ta, Iv data gani ya nuna mata a fountain Mansion xaai Dinner saidai kuma batasan gurin ba, amma kuma idan taje ya xatayi, nuna kanta garesa xatati ko miye ?, gigiza kai tayi hakan bazai yuyyba, zataje ne kawai taganshi ido da ido.
Napep data tsada ba wanda ya dauke ta acewarsu gurin district area ne da napep ko achaba basa zuwa, dakyar dai tasamu taxi sukayi ciniki ya kaitaa naira dari shida dan ba karamin nisa ne da inda ya dauke taba, can farkon hanya ya sauketa ta tafara takowa toward the gate, Kasa karasawa tayi bakin gate din, sojijin kusan 20 ke tsaye bakin gate din, sai manyan motoci da suke artawa ciki a guje, daga gurin da take tana jiyo sautin wak'a dake dashi.
Tsuru tsuru tayi, bugun gabanta na tsananta, shahada tayi ta nufa gate din, daya daga cikin soja ya dakatar da ita yana tamvayar ta Iv, ba'a bata ba tace dashi, tuni ya kuma daure fuska, dan kuwa babu mai shiga sai da Iv, dinner din is strictly on invitation.
"Oga dan Allah ka barni na shiga " ta fada amarairace. bai tanka taba saima kallon gefe sa da yake, Mom ke takowa cikin takun kasaita, sanye take cikin tsadaddiyar leshe kanta daure da gele wanda Oshewa beauty suka mata tieing, kallonta Batul tayi aranta tana adduaa Allah sa matar ta barta ta shiga.
Karasowa tayi.
"Julius make sure ku tsaya postion dinku, gasu nan isowa" ta fada tana kallon julius bata ma lura da Batul dake tsaye ba, juyawa tayi zata tafi sai kuma ta juyowa kallon Batul, dauke kai tayi da sauri ta kalli julius tace "miya kawo almajirai gurin nan ?
"Hajiya ayi hajuri, yanxu zata tafi"
Harara takaimai taja tsaki ta wuce.
"Yarinyar kibar gurin nan, kafin nasa a wulla ki titi"
"Dan Allah ka barni na shiga, it very urgent" kuka ta sanya tana magana.
D'ayan soja dake tsaye yace "yunwa take ji, bara atura kodan snack ne abata ta tafi"
Gefe Batul tayi ta tsaya tana sharar kwalla.
Covony na mayan motoci guda ashirin sukayi, motar amarya da ango ne a tsakiya, suka karaso gaban gate din basu shiga ba, duk motocin suka tsaya, Zaune suke a motar babu mai magana tsakanin, jifa jifa ne Mardiyya ke kallonsa ta saki murmushi, shima murmushi yake sakar, gabadaya hankalin sa baya jikin sa, maganar su da Inna a waya kadai ke yawan mai a kai, ita so take ya nunawa Batul kansa, saidai bazai iyaba dan kuwa ba sonta yake kuma bai yadda ta saduda ba, nan gaba tana samu wani oppurtunity halin karyar ta xai dawo, asalima he is planing of sakinta idan Baba ya dawo daga tafiyar kauye da sukayi.
Numfasawa yayi ya jingine kansa cikin seat hade da kawar da kansa gefe yana duban waje da hasken lantarki ya gwauraye, gabansa ne ya fadi ganinta can nesa tsaye tana zubda hawaye, idanuwan na kallon motarsa tasu da tasha decoration, motar kadai take gani banda mutane dake ciki kansancewar tinted glass dinta.
Kallon ta kawai yake yana mamakin abunda ya kawota gurin nan, Inna tacemai ta fita amma baiyi tsammanin nan tazo ba, gashi yanxu sha daya na dare yayi baisan ma yadda zata koma gida ba dan babu abun haya gurin. Hannu yasa da niyya bude bangaransa xai fito tayi sauri daura hannunta daya sha lalle bisa nasa, kallonta yayi ta sakar mai murmushi, tace 'it time" murmushin dabai kai zuci ba yayi yace "okay'
Fara tafiya motocin sukayi suka shiga ciki.
Bangaran Batul kuwa kuka kawai take ba kagauta, snacks da soja ya kawo mata fir taki karbar, dakyar da sudin koshi tabar gurin bayan Julius ya sama mata lift a motar wata da zata koma gida.
Karshe haduwa Hall din ya hadu, Fadin haduwar Hall din kauyanci ne, jama'a masu hannu da shuni ke zaune gurin, daka ga couple din kasan suna cikin farin cikin, dukda cikin damuwa yadda xata koma gida yake bai hanashi sakin fuska ba.
Budirin kadai ake ana ciye ciye cikin jin dadi da annashuwa, can na hango members na *xarah Bukar novel 1, 2, & 3, Home of novel, Pherty novel, Musha karatu, Qurratul-Ayn Novel, Mom fatu Novel*, mamakin ina suka samo Iv nake, ban gama mamaki ba sai ganin su *Miss xoxo Ummee Agoss, Sadiya Jegal, Mom fatu, Queen Miemee, Rookie kazxx, Ramalurv, Hafsat Rano, Dija Waziri, Waliyyah* hakince nagansu suna kwasar loma, nima baa barni baya ba, ledar dake boye cikin jakata na fiddo na kwashi varieties of abincin dake gurin dan kaiwa kawayena su *Mrx Ay, Naja wali, Faty so, fati Imam, Aysha Gajo, Aisha Magasa*😋😋😋😋
Kusan 3am taro ya watse, kowa ya tattara yayi gida, couple ma suka koma gidansu.
*****
Bayan kwana uku.
Mom ta wuce Abuja huta da gajiya, Zaman Rasheed da mardiyyah ba yabo ba fallasa, sosai Mardiyya ke kokarin faran tamai, ba laifi shima yakan kokarin faranta mata dukda bata gabansa, sunyi waya da Innaa ya yanke shawara zuwa dauko Batul ya dawo da ita gidansa, dukda haushinta yakeji zai yi kokarin sanyata farin ciki dan ya lura her case is critical.
Bayan Sallah Isha Mardiyyah ta taimaka mai yayi shurin sa tsaf cikin kananun kaya daya kara fiddo da azahirin kyau sa, har bakin mota ta rakasa ya fice daga gidan sannan ta koma cikin gida cike da shaukin sanshi.
Kwalliyarta tayi cikin dogowar bakar abaya. Tsakar gidan ta fito rike da empty Ghanar ta tana kakkabewa, Inna dake zaune tayi dariya ganin tabar kukan da takeyi tun safe, jira take Rasheed ya iso taga reaction dinta, gashi kuwa tayi kwalliya abunta tayi kyau, komawa daki Batul tayi tana maida kayanta cikin ghanar sannan ta zuge ta fito rike dashi,
Cike da tsiwa ta tsaya kan Inna "tsohuwa Allah kaddara saduwa, idan jikanki ya dawo ki tabbata ya sakeni, idan ms bai sakeni ba xan dawo dakaina na amshi takarda ta".
Mikewa Inna tayi da azama, tace "Batul ina zaki adaran nan ?
Yake da yafi kuka cuwo tayi, tace "Babu ruwanki, na riga na yake shawarar fita duniya dan cinma burin rayuwata, babu wanda ya isa ya hanani"
Kwantar da murya Inna tayi tace "tabbas ba wanda ya isa ya hanaki, amma dan Allah kiyi hakuri ki tsaya kona minti 20 ne, i promise you won't regret it".
"Sai kiyi ai" Batul ta fada tana hararar Inna, juyawa tayi zata fita, Inna tayi saurin rike Ghanar tanai rokonta karta fita, fir Batul taki hakura ganin Inna zata bata mata lokaci yasa ta saka mata Ghanar ta fice waje tanai tsinewa matsiyacin gidan. Da gudu Inna tabita waje amma ina Batul ta riga ta tsare, gudu kadai take batare data waiwayo ba, Hannu Inna ta aza akanta tana fadin "Batul kinwa kanki, opportunity daya rage maki kikai shuri dashi", haushin kanta sosai Inna tayi, da tasan mai hali bazai canxa ba da bata tsaya lallaba Rasheed ya bata chance ba. Komawa tayi gida ttadau waya ta kira Rasheed, driving yake kan titi, kadan ya rage ya karaso unguwar, daukar wayar yayi Inna ta shaida mai abunda ke faruwa cike da damuwa, kwantar mata da hankali yayi yace zasuyi magana idan ya karaso.
Gudu take harta karaso titi, batama ankara da kokarin tsallaka titin da take ba, sai ganin hasken mota tayi ya kusan to da gudu, cike da kidema tayi baya dan kauce mata amma tuni tayi latti motar sa dage dayan lane dince ta faso aguje, wani mugun burki yaja adaidai lokacin da ta kwalla ihu ta fadi kasa sumammiya.
Hankali tashe yayi parking ya fiso, Addua kadai yake Allah yasa bata ji ciwo wa, karasawa yayi gareta yana haska fuskatar, wazai ganni inba Batula ba, wani mugun tsaki yaja cike da tsanarta, ji yake kaman ya barta gurin yayi tafiyarsa saidai bazai iya ba kodan darajan mahaifin ta.
Daukata yayi yasata bayan mota sannan yaja komawa Gidansa da ita, yana parking farfajiyan Mardiyya ta fito da fara'arta, bude motar yaya ya fito da ita kwance bisa hannunsa, da azama Mardiyyah ta nufesa hankali tashe, magana take bai saurare taba banda saurin da yake yaje ya direta, babbab daki mai shegen kyau ya nufa da ita sannan ya kwantar da ita bisa lausassan gado.
"Sweetie wace wanan" Mardiyya ta fadi arude, dan kuwa ta fisa tsorota, atunanin ta macacciya ce.
"Accident tayi, ki kula da ita" ya fadi ya fice daga dakin, dakinsa ya nufa ya zauna cike da taikici sannan kuma ya kunna karamin Tv dake manna a bangon dakin, Tv ne mai dauke da connection footage na gidan gabadaya, part kusan goma na gidan ya nuna, yasa remote yayi zooming part din dakin da ya kwantar da Batul, jira yake kadai ta farka yaga reaction dinta.
Toilet Mardiyya ta shiga ta dibo ruwa a bowl hade da hand towel sannan ta dawo kusa gareta tahau goge mata fuska inda ya kwarzane, bayan ta gama mikewa tayi ta sauka kasa kiran altine ta hada ruwan zafi a flask.
Bayan mintuna biyu Batul ta farka a gigice, tsorata tayi ganin ta a wagegen daki, zaburewa tayi ta mike tana karewa dakin kallo, ina ne nan kadai take tambaya aranta, tasan dai moto ya kusa bige ta ta fadi daganan kuma sai gata anan, "kodai wanda suka kusa kade tane suka kawo ta" ta fadi aranta.
Tsoro da mamaki ne ya kamata, da sauri ta fice daga dakin, bin tangameme stairs din tayi da kallo tana adduaa neman tsari, atunaninta gidan yankan kai aka kawo ta, dago da idanuwanta tayi taga hadaddudun frames mai dauke da picx din Rmd da Matarsa kusan shida anyi decor dasu ajikin bagon, rike baki tayi kam tamkar wace tayi niyyan ihu, jin motsin zaa hawo yasata rugawa dakin da gudu, kwanciyar tayi tana neman mafita, dan kuwa indai gidan Rmd Allah ya kawota bazata fita ba, mafita kawai take nema, can kuma dabara ta fado mata ta saki murmushi hade da runtse idanunta.
Kallonta Rmd yake ta Tv, saidai baisan dalilin komawar ta cikin dakin da gudu ba.
Murmushin gefen baki yasaki, yasan definitely she is up to somtin, kashewa yayi ya fice zuwa dakin.
Ahankali Mardiyya ta shigo dakin ta karasa kan gadon ta zauna, bude idanu Batul tayi tana lumshe su kaman wace yanxu ta farfado, mikewa tayi zaune tana kallon mardiyya da itama kallonta take.
"Wace ce ke ? Batul ta tambaya tanai mata kallon rashin sani.
Murnushi mardiyya tayi ta matso da ita tana fadin "ya jikin naki ".
Kallon rashin fahimta Batul tayi mata, "banda lafiya ne ?
"sweetie ya kawo ki dazu, wai kin samu accident"
Tsurewa Batul tayi tahau kuka karya, "accident when n how, i cnt remember anything".
Mardiyya sarkin tsoro, tashin hankaline ya bayyana karara a fuskarta, atunanin ko Batul tayi loosing memories dinta.
Rikota tayi tace "baiwar Allah ya sunanki
"Na manta" batul ta fada cikin muryan kuka.
Cike da tausayi Mardiya tace "plz try to remember wace ce ke, koda ma garin da kika fito ne, kiyi kokari ki tuna"
Shuru batul tayi kaman mai tunani can kuma tace "abu daya na iya tunawa
Mardiyya tace "Gayamin "
"Nasan dai ni yar sarki ce, it seems someone is plotting to kill me" karashe maganar tayi tana juya kanta as if she is trying to recall wasu abubuwan.
"Kill you " mardiyya ta fada in shock.
Yes" abunda na sani kenan, kuka sosai Batul ta fashe dashi hade da fadawa kafadar mardiya, lallashin ta Mardiyya tahau yi.
Duk drama da Batul take akan idonsa, basu lura daya shigo ba, gyarar murya yayi duk suka dago suna kallon sa, mikewa Mardiyya tayi ta karasa garesa, tana fadin "mutune abun tsoro, i wonder mai beautiful princess tayi suke son kasheta" cike da tausayi tayi maganar.
Kasa magana yayi tsananin tsanar Batul da yakeji aransa, kallonta yake, aransa yana fadin "she will never change......
0 Comments