Ikhramm hausa novels 4

 Ikhram~  By Khaleesat Haiydar

    53......

 Karfe daya saura Mami ta shigo dakin Khaleel tana kwada ma Ikram kira, farkawarta knn daga bacci bata ga ikram gefenta ba, Khaleel na xaune kan gado yana ta faman solve din mata assignment na Maths, ita kuma tana kwance gefensa duk ta takure kanta sbda sanyin AC tana bacci, Mami tace "Meye hka Khaleel" rufe littafin yyi da sauri yana kallon agogo yace "Mami baki yi bacci ba" tayi masa mugun kallo tace "nan ne wajen kwaciyarta Khaleel, ni fa bana son shashanci da rainin hankali, snn da ka bude mata AC hka kana da maganin da xaka bata ne idan ta tashi tana tari" mikewa yyi da sauri yace "wllh Mami ita ta kunna, kuma ni assignment muke yi tayi bacci" Mami tace "assignment din kke rubuta mata ynxu?" yace "No naga tayi bacci ne...." fixge buk din Mami tayi daga hannunsa tace "kar ka sake yi mata rubutu daga yau tunda bakai ke biya mata kudin mkrntr ba" bae ce komai ba ta isa kusa da Ikram ta dago ta tace "tashi muje ki kwanta Ikram" cikin magagin bacci take cewa "yaya Khaleel ni  ka dinga yi min bacci nake ji, anjima xan tashi" Mami tayi tsaki ta shiga tattara sauran buks dinta da sch bag snn tace "ka kai min ita daki idan ka gama tsayuwar" tana kai wa nn ta fice, yyi murmushi ya bi ta da kallo snn ya juya yana kallon Ikram da tayi ruf da ciki tana bacci, ya karasa kusa da ita ya dagota, kwace kanta ta shiga yi ta bude ido a hankali tana cewa "oowh yaya Khaleel ni bacci nake ji wlh" kan kafadarsa ya daurata ya fita daga dakin, ko da ya shiga dakin Mami tana bathroom, ya kwantar da Ita yana kallon dan karamin bakin rashin kunyarta da murgude murgude, hannu yasa ya dan buge bakin ta bude ido da sauri tana kallonsa, ya juya ya fice daga dakin da sauri, murguda masa bakin tayi ta juya ta ci gaba da baccinta.  Ranar friday da daddare Ikram na xaune dinnin tana karanta literature book din da suke amfani da a sch mai suna without a silver spoon, Aliyu da Khaleel suka shigo gidan, ta mike da sauri tayi gun Aliyu ta rungumesa tace "yayana nayi missn dinka jiya baka xo ba" yyi peck din goshinta yace "Mami ce ta bar min aiki da yawa a office shiyasa ban xo ba" hanyar stairs Khaleel ya nufa, Aliyu yace "baki gaida Khaleel ba Ikram" ta murguda baki tace "ae nasani" murmushi yyi yace "to me kike yi a dinnin" tace "literature nake karantawa kasan gobe muna da literature" yace "gud, my Ikram je ki ci gaba da karatun ki" ba musu ta koma dinnin din ya haura sama, dakin Mami ya nufa, ya tarda ta xaune tana rubutu Khaleel na kwance kan gadonta, ya xauna ya gaida ta ta amsa snn tace "ya aka yi a Meetn din da kuka je" ya shafa kansa yace "Mami ni ban je ba su Dr Ibrahim ne suka je" tace "ok, Momy ta baka sako ka kawo min" yace "A'a Mujaheed ta ba bani ba" Mami bata kuma cewa komai ba, Aliyu ya dauki remote ya shiga canxa tasha, Khaleel yace "Mami wae fa ran sunday yake son kai Ikram gidansu" Mami ta juya tana kallonsa tace "to shi bae da baki?" Khaleel yyi murmushi yace "to nayi shiru" Aliyu ya juya yana kallonta yace "Mami nayi xaton Momy ta gaya maki ne" Mami tace "to idan ta gaya min fa" ya dan yi shiru snn yace "to kiyi hkuri" bata tanka sa ba, bayan kmr minti biyar tace "da ranar lahadin nake so Khaleel ya kai ta gida, but gobe sae su tafi, ran lahadi sae ka kai ta gidan naku" kai kawae Aliyu ya gyada mata Khaleel ya hade rae ya mike xaune yace "Mami ni wani waje fa xani gobe," Mami tace "idan ku ka dawo sae ka je inda xaka" bae ce komai ba ya mike ya fita daga dakin, Aliyu ya bi bayansa. Suna xaune daki suna cin abinci Khaleel yace "wae in tambayeka Aliyu" ba tare da Aliyu ya kallesa ba yace "m ol earz" Khaleel yyi murmushi yace "emm dama abinda ka gani jikin Ikram ya burgeka har kke son aurenta nake so ka gaya min" Aliyu ya dago yana kallonsa, Khaleel ya ci gaba da cin abincinsa yana murmushi yace "yes ina jin ka, don ni abun na daure min kai, nd Beside me kaga ta iya, yarinyar da ko hankalin kirki bata da shi, bbu abinda ya cika kanta sae shegen wasa da rashin kunya, common gyaran daki bata iya ba bare shara, uwa uba axo ga girki, ban tsamman ma ta iya kunna gas din ba, wnn burden babba kawae kke son daura ma kanka, yarinyar da bata wuce ka shiga da ita bayi kayi mata wanka ba ka sa ma kaya" dariya ssae Khaleel ya fashe da har da kyakyatawa, Aliyu ya jefa cokalin hannunsa cikin abincin gabansu ya mike yana kallon Khaleel.

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikraam~  By Khaleesat Haiydar      54.....  Juyawa Aliyu yyi ya fice daga dakin ba tare da yace masa komai ba, Khaleel ya bisa da kallo yana ci gaba da dariyarsa ya girgixa kai yace "naga ta ynda xa'ayi wnn abun dae" Washegari karfe tara Khaleel ya shigo dakin Mami cikin farar shaddarsa ya xauna yana kallon Mami yace "Mami ta gama shiryawa ne, ina son mu dawo da wuri don akwae inda xa ni" Ikram dake daure da towel tana shafa mai tace "ni dae sae na gama kallon Shaun the sheep kafin mu tafi, kaga an kusa farawa" ya galla mata harara yace "wa xae jira ki ki kalla wani shaun the sheep" ta murguda masa baki tace "kai" ya juya yana kallon Mami yace "Mami ki gaya mata ta daina murguda min baki watarana xan cire mata hakori idan tana min hka" Ikram tace "sannunka ba sae ka cire min ba" Mami tace "ban hana ki rashin kunya ba Ikram" kmr xata yi kuka tace "shi ya fara min fa Mami" Mami tace "da'alla rufe min baki ki rufe min maina ki ajiye" Ikram ta rufe man kmr xata yi kuka ta mike tana kallon kayan da Mami ta ciro mata ta sa, riga da skirt ne na atamfa sae Hijab, ta rungume hannayenta ta juya masu baya tace "ni ba wnn kayan xan sa ba Mami, ni wando da riga xan sa wnda yayana ya siya min" Mami tace "baxa ki sa ba," hawaye ne ya cika idonta ta jawo vest dinta xata sa, Mami tace "shiga bayi kisa kayan" daukan sauran kayan nata tayi ta shiga bathroom ta sa ta fito. Khaleel ya rufe bakinsa da hannu yana kallonta, ta fashe da kuka tana kallon Mami tace "wllh nasan dariya yake yi Mami, ni yake wa dariya" Mami ta daka mata tsawa "fita ki ban waje, jarababbiya kawae ihu yyi maki ba dariya ba" ta fice daga dakin da gudu ta sauka kasa ta dinga rusa kuka, jummai ta fito daga kitchen da sauri tana tambayarta me ya faru, ko kallonta bata yi ba sae kukanta take kmr xata shide, Khaleel ne ya sakko rike da makullin mota da hijabinta ya karaso kusa da ita cikin falon yana murmushi ya xauna yana kallonta yace "ni dae ban maki dariya ba wllh" hararansa tayi ta mike xata bar wajen ya riko hannunta da sauri yace "to srry xan jiraki ki gama kallon cartoon din ki wllh" komawa tayi ta xauna tana share hawayenta, karfe goma suka bar gida suka kama hanyar suleja bayan Mami ta rakosu har bakin mota, surutu kawae Ikram ke masa cikin motar shi dae sae um um yake ce mata, ta gaji don kanta tayi shiru, can kuma tace "ae yayana yace min yana xuwa gidanmu Allah yasa mu gansa yau" ya juyo da sauri yana kallonta yace "wani yayanki" tace "yaya Aliyu mana" ya gyada kai snn yace "yaushe ya gaya maki yana xuwa gidan ku?" tace "kullum yana ce min ya je" Khaleel ya tabe baki bae ce kmae ba, sha daya suka isa gida, yana gama parkin ta bude mota ta fice tayi cikin gidansu da sauri, wanke wanke ta tarar Ammi ke yi ta rungumeta tana cewa "Ammina gani na xo" Ammi ta mike tsaye tana murmushi tana kallon yar tata tace "ke dawa kuka xo da safe hka" Ikram tace "ni da yaya Khaleel muka xo, Mami na gida, Ammi ina Abbana?" Ammi tace "ya fita kasuwa, je ki kice masa ya shigo mana" Ikram tace "to" snn ta juya ta fita, Ammi ta bi ta da kallo a sanyaye, ssae ta lura Ikram ta nutsu ynxu, tabarma ta dauko ma Khaleel ta shimfida masa, suka shigo gidan a tare da Ikram ya xauna kan tabarma snn ya dukar da kansa ya gaida Ammi, ta amsa da fara'arta tana tambayarsa Mami, yace "tana nn lfya, Mama" Ammi tace "shekaran jiya ma wan ka ya xo nn" Ikram tace "bana ce maka yana xuwa ba" murmushi kawae yyi bae ce komai ba, awansa daya a gidan yace xae tafi gun wani abokinsa dake wajajen anjima da yamma xae xo daukar Ikram, Ikram ta rakasa bakin xaure tace "yaya Khaleel kar kaxo da wuri fa" "to" kawae yace mata ya wuce, snn ta dawo cikin gida, Ammi ta sa ta taje ta gaida su baba Habu, da maman altine ta dawo, ko minti goma ba'ayi ba ta dawo gidan tace ta gaishesu, Ammi tace "da sauri hka Ikram, to ki tafi gun Abbanki ki gaishesa, daga nn sae ki shiga gidansu Mmn Shafa ki gaishesu tunda ba nisa, idan kina dawowa sae ki shiga gidan yakumbo ma ki gaisheta" Ikram tace "ni baxan je gidansu Shafa ba" Ammi tace "sbda me" tace "sbda xagina mama shatu da kawu Na lado xa suyi idan na je, hka ma ranar da naje take ce min karuwa, kuma da na tambayi Mami meye karuwa tace min prostitute ce" Ammi tace "meyasa kika tambayeta Ikram" Ikram bata ce komai ba, Ammi tayi shiru na wani lkci snn tace "to tashi maxa kije ki dawo" Ikram ta mike ta sa takalminta tace "to amma dae baxan je gidansu shafa ba" Ammi bata ce komai ba ta bita da kallo har ta fita daga gidan.  Karfe biyar da rabi na yamma Khaleel ya xo tafiya da ita, sae taji kmr kar ta rabu da Amminta, Khaleel ya ba Ammi sakon da Mami ta bada a kawo mata snn suka bar gidan da Ikram wajajen karfe shidda.

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~ By Khaleesat Haiydar 55...... Sae da

suka yi nisa snn Khaleel yyi parkn ya juya yana

kallon Ikram da ta hakikance a baya ya galla

mata harara yace "waye drivern ki, c'mon dawo

nn" ta bata fuska tace "to ni nan nake son in

xauna" yace "Allah baki isa ba, ki dawo gaba

idan ba hka ba in sauke ki a titi" dawowa gaba

tayi tana murgude baki ta xauna, snn ya ja motar

suka bar wajen, bakwae saura suka shigo Abuja

amma basu shigo cikin gari ba sae kusan takwas

sbda traffic, wani gida daban ta ga suka shiga da

ba nasu ba, tabi tsakar gidan dake cike da

motoci da kallo, ga dai daitun mutane dake xaune

tsakar gida wasu na shan lemo wasu kuma na

xaune ne kawae tace "ha'a yaya Khaleel ina ne

nn muka xo, ae ba nn bane gidanmu" bae ce

komai ba ya gama parkn snn ya bude mota ya

fito, ita ma hka, ya xagayo ta inda take yace

"kika kuskura kika ce ma Mami mun je wani guri

dake baxan sake wasa dake ba wllh, kuma baxan

dinga siya maki ice-creams ba" tace "to ina ne

nn" ya kama hannunta suka nufi balconyn dake

bayan gidan, yana bude kofar ta riga sa shigewa

tana kalle kalle, fixgota yyi da sauri yace "kee

nace ki shiga" bata damu da ihun da yyi mata ba

hankalinta na kan mutanen da ta gani cikin falon,

both maxa da mata suna ta ciye ciye da shaye

shaye wasu ma rawa suke, ta juya tana kallon

Khaleel baki bude tace "lah gun party muka xo

yaya Khaleel" bae tanka ta ba ya ja ta suka

shiga falon, ssae aka yi decoratin din falon, da

dae alamar birthday ake, muzic sae tashi yake ta

ko ina, gaba daya aka maida hankali gun Khaleel

da Ikram, Khaleel yace "don Allah ku rage vlme

din wnn wakar taku, its 2 much " wani guy dake

kwance yana cin nama ya mike xaune da sauri

yace "baka ce baxaka xo ba karyar bnxa kawae,

wacece wnn kuma Khaleel, ko ita ce babe din

taka?" Khaleel ya juya ya kalli Ikram snn yyi

masa mugun kallo yace "babe dina?? u re vry

crazy" duk suka kwashe da dariya, shima yyi

dariyan yace "ita ce matar da Aliyu ke shirin aure

wllh is'nt it astonishin, kawo maku ita nayi

kawae ku ganta naji cmmnt dinku" duk suka

tsaya kallon Ikram baki bude, har da matan falon,

dariya ya dinga yi ssae har da dafe kai, can yyi

tsit yana kalle kallen falon yace "hope Mujaheed

baya nn?" wani guy ya fashe da dariya yace

"amma lallai Aliyu ya samu brain touch, wnn ita

ce yarinyar da ya ishe mutane da boast, wnn yar

cikin tasa?" duk yan falon suka kwashe da dariya

har da Khaleel, Ikram ta juya tana kallon Khaleel,

ta duka ta dangwali tiles din falon da yatsan ta

snn ta mike ta manna yatsan a harshenta ta

daga yatsan sama tace "wllh sae na gaya ka da

Mami kaga na rantse" dariya ssae yan falon ke

yi, tayi tsaki tana murguda baki tace "barbarians

kawae" snn ta juya xata bar falon, fixgota

Khaleel yyi yana dariya ta gatsara masa cixo tare

da kwace kanta, wata yarinya ce ta sauko daga

stairs da gudu da wasu yan mata biye da ita a

baya, ta hade cikin kananun kaya masu dan

bnxan kyau, tana nuna Ikram da mmki tace

"dama sbda wnn yar cikin tawa Aliyu ke

walakantani yana ci min mutunci, Abormination,

dama tun ba yau ba nasan wllh Aliyu na da tabun

hankali" dariya ssae Khaleel ke yi ya kamo

hannun Ikram, ta fixge tana kallon saleema, daga

ta sama yyi, suka fita daga falon ana ta dariya,

cikin mota ya saka ta suka bar gidan. Eatry ya

tafi da ita ya siya mata abubuwa da yawa, nn da

nn ta fara washe hakora suka kama hanyar gida

bayan tace baxata gaya ma kowa inda suka je

ba, bbu irin jaraban da Mami batai ma Khaleel ba

kan daren da suka yi, shi dae dukar da kansa yyi

bae ce komai ba, ta gama ta ja Ikram suka wuce

sama suka bar sa nn tsaye. Karfe tara da rabi

Aliyu ya shigo gidan, direct dakin Khaleel ya nufa

bae samesa ciki ba, ya fito ya shiga dakin Mami,

xaune ya tadda shi kusa da Mami suna mgna,

Aliyu ya karasa kusa da shi a fusace ya

cakumosa cikin tsawa yace "ka gaya min dalilin

da yasa ka kai Ikram gidansu saleema yau, idan

ba hka ba wllh baxae mana kyau ba a dakin nn

ynxun nn"

Like · 1 · Reply

[2/25, 08:35] Zjy: Khaleesat Haiydar

~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 56...... Khaleel ya juya yana

kallon Mami da ta ajiye abinda take tana kallonsu ganin taki

cewa komai yasa ya mike a fusace shi ma ya shakesa yace

"do ur worst, kuma don me ba ka xo da imbecile din da ya

gaya maka ba" Aliyu ya kafa masa ido na kusan minti biyar

xuciyarsa harbawa, sake sa yyi ya ya juya xae bar dakin Mami

tace "dawo nn" tsayawa yyi daga inda yake yaki dawowa, tace

"magana nake maka" dawowa yyi ya tsaya ba tare da ya kalleta

ba, Khaleel yyi tsaki yace "nnsense" ya juya xae fita daga

dakin, ta daka masa tsawa "nace ka fita? Don uwarka " ya

dawo yyi xamansa, Mami na kallon Aliyu tace "me ya faru" kin

cewa komai yyi ya kauda kansa, tace "mgna fa nake maka" ba

tare da ya kalleta ba yace "bkm" tasan baxae gaya mata ba

knn, ta juya tana kallon Khaleel tace "me ya faru" Khaleel yace

"nima ban gane abinda yake nufi ba Mami" Mami na masa

mugun kallo tace "ko?" yyi shiru, Ikram Mami ta fita ta kira a

gun Jummai suka shigo dakin a tare Ikram na cewa "Mami na

gama duka Assignment dina fa kawae basic science ya rage

kuma yayana xae koya min" Mami bata tanka mata ba ta

xauna tana kallonta tace "ina Khaleel ya kai ki yau" Ikram ta

xaro ido a tsorace ta daga hannu biyu sama tace "wllh bae kai

ni ko ina ba Mami, gurin Ammi kawae muka je muka dawo"

cikin tsawa Mami tace "yhu re tellin me lies uhh, i will flog yhu

mercilessly if i find out d truth get out" Ikram tayi narai narai

da ido ta juya tana kallon Khaleel da ya kauda kai ya daure

fuska, Mami ta daka mata wani tsawan "fice min a daki nace"

hawaye ya cika idon Ikram tace "Mami he said i shudnt say

anythin about it, gashi nn ki tambayesa" Mami tace "wuce ki

ban waje" juyawa Aliyu yyi ya fice daga dakin, Mami ta mike

tana kallon Khaleel da kyau tace "ina ka kai Ikram yau bayan

suleja" Ikram ta juya sui sui ta bi bayan Aliyu da gudu tana

hawaye, Ganin jiran amsan sa Mami take yasa ba tare da ya

kalleta ba yace "gun birthday din Saleema na kai ta, na nuna

ma frndx dinsa ita a matsayin matar da xae aura, dats ol

Mami" Mami ta kafa masa ido xuciyarta na tafarfasa, ta kasa

cewa komai. Washegari sunday Ikram na tashi daga bacci

bayan ta wanke baki wajen karfe takwas ta sakko kasa yin

breakfst, xaune ta tadda Khaleel a dinnin ga break dinsa

gabansa yaki cin komai ya tallabi habarsa da hannunsa biyu da

ya harde fuskarsa a daure, kujera ta ja a hankali ta xauna

opposite shi ta dan marairaice tace "yaya Khaleel ae kasan

bani bace na gaya ma Mami ko, kayi hkuri kaji" wani mugun

kallo ya watsa mata cikin daga murya yace "xan sa ki kuka

idan baki bar nn ba, get out" hararansa tayi ta mike ta mayarda

kujeran tace "to nice nayi maka fada, ni ina ruwana" tsaki tayi

ta koma sama abun ta tana murguda baki, yyi kwafa ya mike

ya fice daga falon. Karfe hudu saura na yamma Aliyu ya xo

gidan tafiya da Ikram gidansu, tana xaune tana kallon Cartoon

bata ma san ya shigo ba ya karaso cikin falon ya xauna

gefenta yana kallonta, ta mike da sauri tace "lah yayana yaushe

ka shigo" yyi murmushi yace "ynxun nn" ta xauna tana kallonsa

tace "kasan mene wae har ynxu yaya Khaleel fushi yake dani

sae kace ni nayi masa masifa, nd i was'nt d 1 dat told Mami

where he took me to, ji fa tun daxu yana garden yaki shigowa,

Mami tace kar in je wajensa ma" Aliyu bae ce komai ba mike

ya nufi stairs don xuwa dakin Mami, Jummai ce ta sakko tace

"mu je ki kara wanka ki canxa kaya Ikram, xaku fita da yayanki

ne" Ikram ta mike da sauri tace "da gske Mama jummai"

jummai tace "gashi nn ya xo tafiya dake" da sauri ta bi jummai

sama tana cewa "amma ae bae gaya min ba to" a dakin

Jummai tayi wanka snn Jummai ta nufi dakin Mami da ita tana

daure da towel, Mami kadae ce xaune dakin, wani hadadden

gown na shadda brown colour ta gani kan gado da

dankwalinsa, murna ta shiga yi Mami ta galla mata harara tace

"idan baki nutsu ba xan bata maki rae, bana son shashanci" ba

shiri ta nutsu Mami ta bata vest tasa bayan ta gama shafa mai,

snn ta dauki gown din ta sa mata da kanta, ido Mami ta tsura

mata gnin wani bala'e'en kyau da shaddar tayi mata dama

gata fara ssae, Mami tayi murmushi ta shiga kwance mata

manyan kalaban da jummai tayi mata, cikin lkci kankani ta

gama kunce su, don tsantsi gare gashin nata ssae, Mam ita

shafa mata man kanta snn ta shiga sharce gashin a hankali

don tasan tana iya saka kuka, ko kadan Ikram bata son a taba

gashinta, tana babbata fuska kmr xata yi kuka har Mami ta

gama bata dae yi ba, Mami ta gama gyara mata gashin ynda

yyi suit dinta snn ta jawo kayan make up dinta ta shiga gyara

mata fuska a nutse.

Like · Reply · Report · Just now

Daiyyiba Muhammad Nabayi

[2/25, 08:35] Zjy: Khaleesat Haiydar ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 57.... Light make up Mami tayi mata snn ta dan goga mata wet lip a lebbanta, ta mike ta dauko dan kunne na fashion da sarka sae bangles masu kyau ta saka mata su, snn ta dauki dankwalinta tayi mata dauri me kyau kmr headtie, ya xauna das das a kanta gwanin sha'awa, Mami tayi murmushi tana kallonta tace "Masha Allah my dota" Ikram ta wara manyan idonta tace "nayi kyau ko Mami" Mami ta rungumeta tace "ssae ma dota, amma kin san me nake so da ke" ikram ta girgixa mata kai Mami ta dafa ta tace "kinga anguwa xaku ikram, kar ki kuskura kiyi magana da kowa kawae gaishe da mutanen da kika gani xaki yi, snn kar ki xauna masu kan kujera a kasa xaki xauna sae ance ki hau kujera kin ji ko, kuma bance kiyi kallo ba idan kika je don na sanki da shegen kallo kmr bakauyiya, kar ki kuskura ki kallan masu TV, lemo ma idan aka baki kar ki sha sae ance ki sha" Ikram ta bata fuska tace "sbda me Mami" Mami tace "kice min to kawae dota" Ikram ta dan marairaice tace "to Mami" turarurruka kala kala Mami ta dauka ta feshe ta da snn ta dauko mata takalmi mai dan tudu don doguwa ce Ikram don ma bata gana girma ba, kalan shaddar jikinta ne takalmin amma light, tayi fasten din mata belt din takalmin da igiya snn ta dauko mayafi kalar takalmin ta daura mata a kafada ssae Ikram tayi kyau kmr wata ba indiya, Mami ta kasa daina kallonta don ita kam mmkin irin kyan Ikram take yi tun kan ba aje ko ina ba, kyakkyawa ce ikram ta karshe da ka ganta ka ga asalin fulani, wayarta ta dauka ta shiga daukarta hotuna snn tace "je ki ki kira min Aliyu" Ikram ta fita da sauri kmr jira take, dakin jummai ta fara shiga ta na juye juye tace "Mama jummai nayi kyau?" sakin baki jummai tayi tana kallonta, Ikram ta bata fuska tace "banyi kyau bane Mama," jummai ta rike haba baki bude tace "ikram" Ikram tayi kmr xata yi kuka tace "kice nayi kyau mana" Jummai ta girgixa kai tace "Masha Allah yar mami, kin ganki kmr balarabiya kuwa" dama abinda Ikram ke jiran ji knn ta fice da gudu tana dariya, kasa ta sauka ta tadda Aliyu xaune falo ya dafe kansa, ta karaso kusa da shi da sauri ta dafa shi tace "yayana" dagowa yyi yana kallonta, tayi murmushi tace "nayi kyau yayana?" kasa ce mata komai yyi ya tsura mata ido sae kallonta yake, ta bata fuska tace "kace nayi kyau mana yayana" nn ma bae ce komai ba, idonsa na cikin nata yana mata wani irin kallo, jijjigasa tayi tace "yayana" sae a snn ya dawo, ta bata fuska ta mike xata bar wajen ya riko hannunta a hankali yace "kinyi kyau kanwata" murmushi tayi tace "to ngdd yayana, mami tace in kiraka, bari in je in tambayi yaya Khaleel ko nayi kyau" kallonta kawae Aliyu ke yi kmr bae taba ganinta ba, ta juya da sauri tayi waje snn ya sauke ajiyar xuciya ya lumshi idonsa, a hankali take tafiyar nata cikin sanda kar yaji karan kon kon shoe dinta, yana xaune yana danna wayarsa, ta rungumosa ta baya hade da yin yar kara da nufin ta tsorata shi, tura ta yyi a fusace yace "wae ni abokin wasan ki ne aka ce maki" rigijib ta xube kasa ta mike tsaye da sauri tana kakkabe jikinta ya juya yana kallonta xae yi mgna ta makale a throat dinsa, cikin muryar kuka tace "kuma Allah ya isa na, dama ba xuwa nayi in tambayeka ko nayi kyau bne" tana fadin hka ta fashe da kuka, ta juya xata bar wajen ya kamo hannunta da sauri, har lkcn yana kallon fuskarta a hankali yace "srry, kin yi kyau" handkerchief ya ciro yana goge mata hawayen fuskarta yace "Aliyu ya xo knn" ta murguda masa baki tace "eh" yyi murmushi yace "idan kun je can sae kiyi ta murguda masu kaxamin bakin nn naki da ba kya brush" ta mike da sauri tana xare ido cikin muryar kuka tace "wllh ina brush kullum da safe da daddare, sae dae idan kai ne baka yi" tana kai wa nn ta juya ta bar garden din, ya bi ta da kallo yana murmushi har tayi corner snn ya mike ya bi bayanta. Har bakin mota Mami ta rakosu bayan ta gama yi ma Aliyu mgnr da xata yi masa a daki, Ikram ta xauna gaban mota tana daga ma Mami hannu baki har kunne, Khaleel ya xagayo ta inda take don tare suka fito yana kallonta yace "saura kije kiyi ta washe masu hakora, ko kuma ki je kina murguda masu katon bakin ki kiga idan baxa su koro ki ba" fitowa tayi daga cikin motar da sauri har tana neman faduwa cikin muryar kuka tace "Mami kina ganinsa ko" da sauri ya shige gida yana dariya, Mami ta bi sa da kallo snn tayi kwafa tace "kyaleni da shi Ikram, shiga mota ku tafi, kuma karki yi misbehave kinji dota, kin dae ji abinda na gaya maki daxu ko" Ikram ta gyada mata kai snn Aliyu ya tada motar suka bar gidan Ikram na daga ma Mami hannu. Like · 9 · Reply · Report · 1 hour

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikram~  By Khaleesat Haiydar     58.....  Karfe hudu Aliyu ya shigo compound dinsu yyi parkn, Ikram ta bata fuska tace "yayana ae gidansu Momy ne nn" ba tare da ya kalleta ba yace "eh" tace "ni bana son gidan nn ka maida ni gida, ashe ba anguwa xamu ba dama" ya kamo hannunta yace "ba dde wa xa muyi ba Ikram, daga nn xamu tafi anguwarmu" tayi shiru tana kallonsa, yyi murmushi ya fito ita ma hka, bbu kowa cikin falon sae TV dake ta aiki shi daya, tayi hanyar stairs ya rikota yace "ina xaki?" tace "xan je gaida Momy da su Seeyama mana" ya girgixa mata kai yace "xaki gaida da su amma ba ynxu ba, ynxu dae ki xauna ki jira ni a nn" ba musu ta koma ta xauna, ya haura sama ba, Dad dinsa ne ya fara sakko wa ya shigo falon ya xauna yana kallon Ikram da hankalinta ke gun kallo, juyawa tayi da sauri tana kallonsa tace "ina yini" yyi murmushi yace "lfya lau" Momy ta sakko tare da Aliyu, ikram na ganinta taje ta rungumeta, Momy tayi murmshi kawae suka shigo cikin falon a tare, har ta xauna kan kujera ta tuna abinda Mami tace mata ta koma kasa da sauri, sae ga Hajiya da su Farida, duk suka xaxxauna a falon, Ikram dae ta mayar da hankalinta gun kallon da take, Abba ne yace "to ina yarinyar take, kasa na bar abinda nake kuma na sauko" Hajiya dake ta kalle kallen inda xata ga matar da Aliyu ke son aure duk da taga Ikram, amma a tunaninta Mami ce ta xo gidan ta bar ta, tace "to nima kalle kallen da nake knn Alhaji, ina yarinyar take" Momy ta dafa Ikram dake kasa kusa da ita tace "ga ta kuwa kuna gani" bude baki Hajiya tayi da mugun mmki tana kallon Ikram, Abba ya kauda kansa yana murmushi, Hajiya ta mike ta saka kuka tace "amma Allah ya isa wllh, me xan gani hka Aliyu, wnn ita ce matar da ka kawo mana mu gani" Abba dae ya kasa juyowa bare yace kmai, har lkcn bae daina murmushin da yake ba, warce ake don ta ma bata sani ba, sae kallonta take, Momy tace "meye abun Allah ya isa a nn Hajiya"

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar

59.....

Ganin ynda take kuka yasa Aliyu ya dago kanta a hankali yana kallon cikin idonta a sanyaye, ya rumtse idonsa don bae son jin sautin kukan nata yace "ya isa hka Ikram" kin daina kukan tayi, hkn yasa ya bude idonsa ya shiga share mata hawayen fuskarta a hankali yace "ya isa Ikram kar ki sake kuka, kinji " kai kawae ta gyada masa tana kallonsa, ya mike yana rike da hannunta, suka fita daga falon, garden ya nufa da ita ya xauna, ita ma ta xauna gefensa, ya kamo hannunta yana kallon cikin idonta a hankali yace "Ikram" tayi shiru tana kallonsa, ya lumshe idonsa yace "promise me ko me xae faru baxa ki barni ba Ikram we wil alwayz b 2geda" shiru tayi tana kallonsa bata ce komai ba, ya ci gaba a hankali kmr me shirin mata kuka "kiyi min alkawarin baxa ki aura kowa ba sae ni Ikram" Khaleel dake xaune balconyn dakinsa yana kallonsu yyi murmushi ya kauda kansa, wae Ikram Aliyu yasa gaba yake ma wnn mgnr, Muryar Ikram yaji tana cewa "i promise yayana baxan aura kowa ba sae kai ni kai kadae nake so yayana" juyowa yyi yana kallonta da mmki, sae abun ya basa dariya, Aliyu ya rumtse idonsa ya rungumeta yace "i luv yhu more Ikram" kai kawae ta gyada masa, Khaleel ya tabe baki ya mike ya shiga dakinsa, xobe karami me kyau Aliyu ya ciro ya saka mata a hannunta tayi murmushi tace "ngd yayana" kasa ce mata kmai yyi ya tsura mata ido. Ranar wednesday Ikram na dawowa daga sch tace ma Mami ita gun Ammi xata yi Mid term Break dinta, Mami tayi shiru tana kallonta don ita kam ta rasa me ke damunta, duk ta xama wata silent kmr ba Ikram, Mami bata mata musu ba tace "to bari Khaleel ya dawo ya kai ki, but kinsan kun kusa fara junior waec Ikram ki tafi da buks dinki da xaki karanta a can" Ikram tace "to" snn ta wuce sama Mami ta bita da kallo tana mmkin sauyawanta lkci daya, ikram dae yarinyace bare tace abu tasa a rae. karfe biyar Khaleel ya shigo gidan bayan Mami ta kirasa ya kai Ikram gida, Mami ta hada mata few kayanta da text buks ta sa su a jaka snn ta mika ma Khaleel ya kai cikin mota, juyowa tayi tana kallon Ikram tace "dota ban fa ce ki ba ma Ammi lbrin abinda ya faru ba kar ki kuskura ki ce mata komai kin ji," Ikram ta gyada mata kai snn suka fito xuwa gun mota, Mami ta buda mata front seat ta xauna, Khaleel ya shiga driver sit ya tada motar suka bar gidan Ikram na daga ma Mami hannu, har suka isa suleja be ce mata ba bata ce masa ba. Ya gama parkin karfe shidda dai dai, ta bude motar ta fita ta buda bck seat ta ciro jakar kayanta snn ta juya tana kallonsa tace "bye" ta juya tayi cikin gidansu, binta yyi da kallo har ta shiga snn ya tabe baki ya buda mota ya fito ya shiga gidan shi ma, Ammi na share tsakar gida ta mike tana kallon Ikram da mmki, Ikram tayi murmushi ta rungumeta, dae dae nn khaleel ya shigo gidan, Ikram tayi cikin dakinta da jakarta, ya xauna suka gaisa da Ammi tana tambayarsa Mami da Aliyu, mintinsa goma a gidan yace xae koma, Ammi tayi masa tayin abinci yace "Alhmdllh" tayi masa Allah ya kiyaye hade da gdya snn ya fita daga gidan. Washegari da safe Ikram na xaune tana cin koko da kosan dake gabanta ita da Amminta, Ammi tace "baki da lfya ne Ikram" Ikram ta dago kai da sauri tace "ni Ammi?? Aa ni lfyata qlau, taba jiki na ki ji" Ammi bata ce komai ba ta ci gaba da cin kosan dake gabanta a hankali, abu daya ne Ammi bata ji ddi game da Ikram ba, kuma shine rashin iya aikinta, sam bata iya komai ba, don kasa wanke kwanukan da ta bata tayi, tsakar gida ma sharan hauka tayi masa, bata dae ce mata komai ba amma ta dauki aniyar yi ma Mami mgna ta dinga barinta tana dan aikace aikacen gida tunda mace take kuma aure xata yi, da yamma Ikram na wanke wanken kwanukan da Ammi ta tara mata ta wanke tana xumbure xumbure, Ammi kuma na tankada gari, suka ji ana sallama a bakin xaure, Ammi ce ta mike ta fita dae dae lkcn da ta ci karo da yaron makwabtansu yace "mmn ikram wae ana sallama a waje" kan Mami tace komai suka shigo gidan sun kai su biyar.


2/25, 08:35] Zjy: Khaleesat Haiydar

~Ikhram~ By Khaleesat Haiydar 60...... Mata biyu

da sojoji uku suka shigo gidan matan na yamutse

fuska, duk suka tsaya cirko cirko a bakin xauren

suna kare ma gidan kallo, dae dae lkcn da Abban

Ikram ya fito xae tafi kasuwa don yana daki

dama, Wani Matsiyacin kallo matan ke ma Ammi

da ke tsaye sokoko tana kallonsu, warce ta turo

dankwali gaba tana taunar cingam tace "ke ce

uwar Ikram, wancan kuma ubanta ko?" kasa

cewa komai Ammi tayi sae kallonsu take a dan

tsorace, hka ma Abba dake ta bin sojojin da kallo,

hango Ikram da Hajiya tayi xaune tsakar gidan

yasa tace "Alhmdllh nan ne, to munxo maku

kashedi kan wancan Matsiyaciyar yar taku ce,"

Ammi ta juya da kyar tana kallon mai gidan nata

xuciyarta na bugawa, hajiyar ta ci gaba cikin

gadara tana kallon Ikram tana nuna masu yatsu

uku tace "kwana uku na baku ku aurar da yar

can," tayi wani murmushin mugunta tace "yess

just three dayz idan ba hka ba wllh wllh sae na

daure ku na daure wanda xae tsaya maku gaba

daya har karshen rayuwarku" ta karasa mgnr

cikin tsawa, dayar matar gefenta me taunar

cingam tace "kwana uku kacal, ko ku sha mmki

wllh, don 'dan mu ba sa'ar yar talakawa

matsiyata bne, yafi karfin wancan shegiyar yar

taku, idan yaga tayi aure ae baxae ce xae aureta

ba" suna kai wa nn hajiya ta juya suka fice daga

gidan sojojin suka rufa masu baya, hawaye ne ya

shiga bin kuncin Ammi kmr famfo, taji kafarta ya

kasa daukarta, to su waye kuma wnn, juyawa

tayi tana kallon Mai gidanta taga wani mugun

kallon da yake mata yana buga kafa, kuka ta

fashe da ta juya tana kallon Ikram, hawaye ta

gani ita ma kwance a fuskarta, ta dawo kusa da

ita ta xauna da kyar tana kallonta tace "su waye

wa ennan Ikram?" a hankali Ikram tace "ita ce

momyn Aliyu" da mmki Ammi tace "momyn Aliyu

kuma, dama ba Mami bace mamarsa" kai kawae

Ikram ta gyada mata, a rude Ammi ta shiga cewa

"na shiga uku to me ya hadaku da Aliyun Ikram"

muryar Abba taji yana cewa "kin dae kusa shiga

uku Aisha baki shiga ba tukun, Alhmdllh dama irin

wnn ranar nake jira, ba ke me kunnan kashi da

shegen kwadayi da son abun duniya ba, to yau ga

daya daga abinda nake gudu nake kuma tsoro ya

faru kuma a kanki xae kare bani ba wllh" mikewa

Ammi tayi da sauri tana kuka ssae tace "ynxu ni

xaka kira me son abun duniya malam, ka min

adalci knn" Abba yyi mata mugun kallo yace "an

kira ki din karya nayi, ba ke karatu kike son yar ki

tayi ba baki son tayi aure, kika tashi kika dauke

min ya ta kika damka ma wasu can kuma kika

boye min har na tsawon wata daya to gashi yau

tayi karatun har ta gama, to Alhmdllh kuma wllh

wllh nn da kwana ukun da suka ce xan aurar da

ita, ae ni abun farin ciki na ma ne wnn Allah ya

dawo mun da 'ya ta lfya, aure kuma kmr na aurar

da ita ne ynxun nn, bari ma inje in samu yaya

dama shekaranjiya jiyan nn ya gama min mgnan

ta, ae ni wnn ba wani abu bne a waje na" bae jira

me Ammi xata ce ba ya saka takalminsa ya fice

daga gidan kmr xae tashi sama, xubewa Ammi

tayi gun tana kuka ssae, Ikram ta hade kanta da

gwiwa ita ma tana rera kukan a hankali aka rasa

me lallashin wani.

1 hr · Khaleesat Haiydar...

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 61...... Ikram na xaune

dakinta da yamma rike da literature book dinta bayan

ta gaji da kukan da take tun safe taji an bude kofar

xaure, mikewa tayi da sauri tayi waje don ganin waye,

ita kadae ce gidan Ammi ta tafi gun yayarta yakumbo,

karo suka kusan ci da Aliyu, ta koma baya da sauri

tana kallonsa, shi ma kallonta yake, murmushin ta mai

kyau tayi tace "yayana" shima yyi murmushi yace

"kanwata" hannunta ya kama suka karasa tsakar gidan

ya xauna kan tabarmar dake shimfide ya xaunar da ita

gabansa yana kallonta yace "Ammi fa" ta dan yi shiru

snn tace "Ammi ta tafi gidan yakumbo" ya daga kanta

yana kallon idonta da ya rine, da mmki yace "me ya sa

ki kuka Ikram?" Ikram tayi shiru tana kallonsa, hannunta

ya kamo yace "kiyi min mgna mana Ikram" kmr xata yi

kuka tace "momynka ce ta xo gidanmu da safe take

ma Ammina da Abbana Masifa," "innalillahi wa'inna

ilaihi raji'un" abinda ya iya furtawa kadae knn ya dafe

kansa, xuciyarsa na bugawa, to wa ya kawo ta gidansu

Ikram, dago kansa yyi da kyar idonsa yyi jajur yana

kallonta, xae yi magana Ammi ta shigo gidan, tana

ganinsa ta hade rae, Ikram ta mike da sauri tana kallon

Amminta tace "Ammi sannu da dawowa" Ammi bata ce

komai ba tayi cikin kitchen da ledan hannunta, tana

fitowa Aliyu ya gaisheta kansa a kasa, ta amsa bbu

yabo bbu fallasa ta shiga dakinta, Ikram ta juya tana

kallonsa snn ta bi ta cikin dakin a sanyaye, ba ajima ba

ta fito ta dan durkusa kusa da shi a hankali tace

"yayana xan je in yi karatu na a daki" kai kawae ya

gyada mata ya mike yace "kice ma Ammi na tafi" ita

ma ta gyada masa kan snn ya fita daga gidan, juyawa

tayi tana kallon kofar dakin Ammi hawaye cike idonta

ta nufi dakinta tana murguda baki. Da daddaren ranan

suna xaune da Amminta a tsakar gida, Ammi ta rafka

uban tagumi, ita ko sae kallon tuwon gabanta take taki

ci, Abbanta ya shigo tare da Kawu na lado, ko gaisuwar

arxiki ba ayi ba Na lado yace "dama na xo da kaina ne

in gaya maki cewar ni Na lado na yanke shawarar hada

'ya ta Rabi aure da dan wajen abokina Dan lami, surajo,

kuma insha Allahu jibi asabar xa a daura auren" yana

kai wa nn ya juya ya fice, Abba ya bi bayansa don

rakasa, kuka Ikram ta fashe da kmr warce tasan meye

aure, Ammi kam bata ce komai ba sae hawaye take

don tasan bbu abinda xata ce a nn da xae shigesu,

Ikram ta mike tana rusa kuka kmr xata tsaga gidan

tana cewa "wllh ni bana son surajo, ni baxan aura kowa

ba sae yayana, ni yayana nake so" Ammi ta dago tana

share hawayenta tace "waye yayanki" cikin kuka tace

"yaya Aliyu mana, ni shi kadae xan aura bana son

kowa, baxan aura kowa ba" Ammi ta fixgota a fusace

tace "to don ubanki ki bisa ki auresa mana, shegiya

kawae, ke har kinsan wanda xaki aura ko" har karfe

sha biyun dare Ikram bata bar kukan da take ita kadae

a daki ba duk da dukan fitar hankalin da Ammi tayi

mata. Da safe idonta duk ya kumbura lebbanta yyi jajur,

alwala kawae ta fito yi ta koma daki, bata kuma fitowa

ba har rana ta fito, Abba bae bi ta kanta ba ya fice

xuwa gun kasuwancinsa don shi har Allah Allah yake

gobe yyi ya aurar da Ikram ya huta, karfe tara Ammi ta

tura mata break fst dinta nn bakin kofa ba tare da ta

ce ta dauka ba tayi gaba, bata ko kalli break din ba ta

ci gaba da kukanta daga inda ta tsaya. Karfe sha daya

saura taji muryan Mami tana sallama bakin xaure da

gudu Ikram ta fito daga dakinta tayi gun Mami ta

rungumeta tare da fasa mata ihu, a rude Mami tace

"subhanallahi, me ya same ki Ikram" cikin kuka tace

"ko ba Ammi da Abba ba ne" Mami ta dago fuskarta da

mmki tana kallonta tace "suka maki me" Ammi na

tsaye bakin kofa fuskarta a daure tana kallonsu, Mami

ta daga kai tana kallonta tace "me ya same ta Mmn

Ikram" kasa mata shiru Ammi tayi don tana ganin

mutuncin Mami ssae, Ammi ta dan kirkiro murmushi da

kyar tace "iskancinta ne kawae Hajiya" Mami ta kamo

hannunta suka kara cikin tsakar gidan ta xauna kan

tabarma ta xaunar da ita ta dago kanta tana kallon

kumburarrun idonta, Ammi ta juya a sanyaye xata koma

daki Mami tace "wajen ki naxo mmn Ikram" ba musu

Ammi ta dawo ta xauna ba tare da ta kalli Mami ba,

Mami tace "kuyi hkuri da abunda ya faru mmn Ikram,

duk ni na ja komai...." Ammi ta dakatar da ita da sauri

tace "dama ba ke kika haifa Aliyu ba Hajiya?" Mami ta

dan yi shiru snn tace "ehh bani na haife Aliyu ba,

kawae dae na rikesa ne kuma na taba auren ubansa

shekaru masu yawa da suka wuce don ina gidan aka

haifesa ma, kuma yana da shekaru biyu na bar gidan

duk da karancin shekaransu kuwa ba karamin shakuwa

yyi da ni ba don uwarsa bata da lkcnsa, matar da ta xo

nn jiya ita ce mahaifiyarsa, kuma kishiyata yrs bck,

bamu yi xaman ddi da ita ba kuma ita ce sillar

rabuwata da Mahaifin Aliyu, kuma har muka rabu bamu

samu haihu da shi ba, ina gama idda Allah ya hada ni

da mahaifin Khaleel, shekaranmu daya na haifi Khaleel,

kuma na ci gaba da karatuna na likita don Mahaifin

Aliyu bae barni na ci gaba ba a gidansa, Khaleel na da

shekaru goma sha biyu Mahaifinsa ya rasu ya b[truncated by WhatsApp]

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikraam~  By Khaleesat Haiydar      62......  Mami tayi shiru na dan lkci snn ta ci gaba "Naji mutuwar mahaifin Khaleel ssae, don Allah ya gani duk iya xamana da shi bamu taba samun matsala ba, mutum ne me saukin kai da kirki ga yawan kyauta, ina gama takaba na koma gun Mahaifiyata da Khaleel, ko kadan yan uwansa basu nuna mana bakin cikin dukiyar da ya mutu ya bar ma Khaleel ko kuma ince ya bar mana me yawa ba don kowa na da nasa, duk family dinsu bbu me karamin karfi, mahaifin Aliyu kuwa ina fita da wata biyu dama ya kuma aure abunsa, kuma kusan a tare muka haihu da amaryar tasa ita ta haifi danta Mujaheed ni kuma Khaleel, makarantar da yaransa maxa ke xuwa na secondary shi Khaleel ma ke xuwa don makaranta ce me kyan gske, lkci daya kwatsan Alhaji ya fara hada sch fees dinsu gaba daya har da na Khaleel ya biya, ni dae ko sau daya ban taba masa gdya ba kuma ban taba nuna na sani ba ma, ana hka dae ya fara xuwa gidanmu yana nuna min Interest dinsa na son na dawo gidansa a matsayin matarsa kuma, har ga Allah ina sonsa, amma ssae nake tsoron xama da matar nn tasa duk da nasan da sabuwar Amaryar da yyi, amma dama Allah ya rubuta dole sae na kuma komawa gidansa, hka kuwa aka yi, ko kadan matan nasa basa shiri da na shiga gidan, amma sae me ina shiga da wata biyu Hajiya ta hade kai da Aishar suka dawo suna shiri ssae, duk suka sani gaba, in takaice maki lbri wllh a daddafe nayi shekara uku a gidan na haifi Seeyama, nn na bukaci ya sallameni bana auren kuma, to dae na wahala kan ya ban takardata, amma kuma yaki bari in tafi da Khaleel da seeyama, ban masa musu ba na bar masa su, na mayar da hankali na ga aikina duk da nasan Khaleel ba jin ddin Hajiya yake a gidan ba, through out stay din yarana a gidan basu yi rashin uwa ba don Mahaifiyar Mujaheed bata taba canxa masu ba, ita ta rike seeyama tun tana karamarta, kuma har yau Seeyama bata sake dani kmr ynda ta sake da ita ba, mun rabu da Alhaji da yan watanni Aliyu ya dawo wajena duk da ba tare da amincewar Mahaifiyarsa ba, ni na rikesa har ya gama karatunsa na likita, su kuma suka rike Khaleel can, to kinji me ya hadani da Aliyu Mmn Ikram, kinga baxan ce maki ba da na bne, ynxu dae abinda nake so daku kuyi hkuri don Allah, iyayensa ne suka takurasa kan aure kuma yace shi Ikram yake so, shine fa ta xo har nn tayi tijarar da ta saba," Ammi tace "bkm Hajiya, Allah yasa mu dace, amma gobe xa'a daura auren Ikram da wani dan uwanta" Mami tace "ban gane ba" ammi ta dan yi shiru snn ta gaya ma Mami ynda suka yi da Hajiya da kuma hukuncin da Abban Ikram da yayansa suka yanke, Mami ta mike da sauri tace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un, anya matar nn xata ga annabi kuwa," ta koma ta xauna da kyar tace "don Allah mmn Ikram kar ku lalata rayuwar yar ku ku bar ta tayi karatu, wllh bata isa aure ba ynxu, irin wnn auren da ake ma yara ke sa xaka ga yarinya na fama da ciwon yoyon fitsari, gasu nn da yawa muna ganin cases irin hka a hsptl " Ammi ta share hawayen dake bin kuncinta tace "to ya xanyi Hajiya, ni ynxu banda abun cewa a nn, ca fa tayi xata daure mu da wnda xae tsaya mana" Mami tayi murmushin takaici tace "ae tana takama mijinta soja ne, yayanta ma hka, amma kyaleni da ita mmn Ikram xan dawo anjima da yamma" Mami na kai wa nn ta fice da sauri, Ikram ta mike da sauri ta fashe da kuka xata bi ta, Ammi ta fixgota ta rungumeta tana kuka ssae.  Mami na isa gida ta kira Khaleel tace ya bar abinda yake ya xo tana nemansa, bae mata musu ba cikin minti sha biyar ya dawo gida, ssae Hankalinsa ya tashi ganin mode din Maminsa, ya xauna yana kallonta cike da damuwa yace "baki da lfya ne Mami?" Mami ta sauke ajiyar xuciya tace "lfyata qlau Khaleel, magana xa muyi ne" ya dawo gefenta ya xauna yace "na me fa Mami, hope lfya?" a hankali Mami ta fara masa mgna ba tare da ta kallesa ba "nasan baka taba min musu ba Khaleel, kuma idan na sa ka abu ko bae maka ddi ba kana respectin dina kayi" Khaleel bae ce komai ba sae kallonta yake, a hankali tace "wnn karan ma baxan so ace ka min musu ba Khaleel" Khaleel ya sunkuyar da kansa bae ce komai ba sae dae gabansa faduwa yake, ganin tayi shiru yasa da kyar yace "me kike son in maki Mami" Mami ta sauke wani ajiyar xuciyar tace "so nake in hada ka aure da Ikram Khaleel......" saukowa kasa yyi da sauri cikin tashin hankali yake girgixa mata kai "no Mami kar ki min hka don kinga bana miki musu Mami plss," nan da nn hawaye ya cika idonsa muryarsa na rawa yace "ki bari plss Mami kar kiyi min hka" Mami tayi shiru tana kallonsa, hawayen dake makale idonsa ya gangaro, ta sauko kasa ta dafa sa tace "y son?" ya daura kansa kan kafadarta cikin rawar murya yace "she is nt meant 4 me, snn ni baxan iya aurenta ba sbda abu biyu, na farko na dauketa a matsayin kanwata na biyu kuma, baxan iya cin amanar brotherna ba, plss Mami karki ce min wnn ba reasons bne consider me" hawaye ssae yake yi, Mami ta shafa kansa tana murmushi tace "ya isa son kar ka sake xubar min da hawayenka, i wont force yhu kuma na gamsu da reasons dinka,"

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~ By Khaleesat Haiydar 63...... Karfe

daya Mami ta isa gidansu Aliyu, tana gama

parkn ta shiga gidan, bata tar da kowa falon ba

kai tsaye ta xarce xuwa dakin Momy, Momy na

ta goge ita daya a daki, tayi mamakin ganin

Mami da rana, Mami ta xauna kan gado ta cire

mayafin jikinta suka gaisa, momy ta xauna kan

kujera tace daga ina kike hka Hajiya, halan baki

je office ba yau, Mami tace "ehh wllh yau ban

je office ba" Mikewa Momy tayi ta bude fridge

ta dauko mata lemo ta dire gabanta, Mami tace

"xauna mgna xa muyi Hajiya" Momy ta xauna

tana kallonta tace "in ji dae lfya Hajiya" Mami

tace "lfyar knn, Mujaheed na gari ne?" Momy

tace "ehh yana nn" Briefly Mami tayi ma Momy

bayanin abinda ya faru, Momy ta saki baki tana

kallonta da mmki, cike da damuwa Mami tace

"to ynxu ni ban san ya xan yi ba Hajiya

Fateema, kuma gobe xasu aurar da ita wae,

shine nace bari na ga ko Mujaheed xae amince

shi" Momy ta girgixa kai cike da takaici tace

"ae Mahaifiyar Aliyu na da matsala, ni har

tausayi yake ban wllh, bari in kira Mujaheed

din" wayarta ta dauka ta kira Mujaheed yana

daga wa tace "maxa ka xo Mujaheed ina neman

ka ynxu" tana gama fadin hka ta katse wayar,

tana kallon Mami tace "Allah ya daura mu

kansa, amma ni wnn reasons din da Khaleel ya

baki ae na hauka ne, wnn bae isa ya hanasa

auren Ikram ba" Mami ta dan yi murmushi tace

"rabu da shi kawae" cikin minti ashirin

Mujaheed ya shigo dakin Momynsa, ya gaida

Mami ta amsa da fara'arta snn ya xauna yana

kallon Mum dinsa yace "gani Momy" Mami ce

ta fara mgna tana kallonsa a nutse tace

"Mujaheed favour daya nake son kayi min don

Allah" Mujaheed ya juya yana kallonta da dan

mmki yace "na me fa Mami" Mami ta dan yi

shiru snn tace "Ikram nake son hada ka da,

Ma'ana ina son ka auri Ikram...." da mmki

yace "Ikram kuma?" Mami ta gyada masa kai

tace "ita" cikin confusion yace "kmr ya Mami,

bn gane ba, ba Aliyu ke son ta ba, in aureta

kmr ya" Mami tace "nasani Mujaheed, ba kuma

ca nayi aure me dorewa xa ku yi ba, A'a ko

nn da sati uku ne sai ka sakar min ita" ganin

duk ya wani daburce yasa Mami tayi masa

bayanin abinda ya faru gaba daya, yyi shiru

yana kallonta snn ya sauke ajiyar xuciya yace

"shknn Mami, wnn ba matsala bane a wajena

dama naga ynda Aliyu ke sonta ne shiyasa abun

ya ban mmki da kika ce in aureta da farko, but

xanyi ynda kuka ce ynxu" Momy tayi murmushi

tace "to Allah maka albarka son" shima yyi

murmushin yace "Ameen Momy" Hankalin Mami

ya kwanta ganin ta sama ma dota dinta

solution, tana idar da sllr Azahar ta koma gida,

kwance ta tarda Khaleel kan doguwar kujera a

falo idonsa a lumshe, ta karasa cikin falon tace

"baka koma office ba son" mikewa yyi da sauri

ya xauna, idonsa ya kada ssae ta xauna gefensa

tace "me ya faru son" girgixa mata kai yyi ya

durkusa gabanta kmr xae mata kuka yace "Mami

gani nake kmr ban kyauta maki ba, yau na maki

musu, plss Mami understand me" Mami tayi

murmushi ta shafa kansa tace "i understand yhu

son, kuma ni ban ji haushi ba coz baka taba kin

jin abinda nace maka ba, ka kwantar da

hankalink na riga da na samu solution" kai

kawae ya gyada mata tace "ka ci abinci ne" ya

girgixa mata kai alamar A'a, ita da kanta ta

mike ta nufi kitchen ta xubo masa abincin ta

ajiye masa gabansa da drink, snn ta haura sama

xuwa yin wanka kafin ta koma suleja.

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~  By Khaleesat Haiydar

     64......

 Mami bata wani sha wahalan shawo kan Na lado ba da yake ya ga kudi, bae ma tsaya binciken ko wa xata hada Ikram da ba yace an basu Ikram, shi dae Abba bae ce komai ba sae kallon yayan nasa yake da mmki ganin ya riga da yyi ma Amininsa alkawarin xae ba dan sa Ikram sae gashi lkci daya ya fasa, cike da farin ciki Mami ta koma gidansu Ikram tayi ma Ammi bayanin duk ynda suka yi da Na lado, ita dae Ammi bata ce komai ba sae tunanin irin halin wan mijin nata take, ynxu ko da ba Mami bne indae ya ga kudi hka xae yi ma yar su, karfe biyar da kusan rabi Mami ta bar gidansu Ikram bayan tace da Ammi gobe dad din Aliyu xae xo a daura auren, bata ma fada ma Ammi da wa xa ayi auren ba Ammi ta rako ta har bakin mota tayi mata gdya ta koma cikin gida ta dauki Hijab dinta ta kama hanyar gidan yayarta yakumbo don can ta kai Ikram da ta isheta da kuka daxu. Mami na komawa gida ta tar da Khaleel xaune balcony yana danna laptop ya mike da sauri ganinta, ta sakar masa murmushi tace "kana nn har ynxu ashe" yace "eh mami ban fita ba," ya karasa ya amshi handbag dinta ta mika masa yace "daga office kike Mami" Mami tace "A'a daga suleja nake gidansu Ikram" bae ce komai ba ya juya da sauri yyi cikin gida ta bi sa a baya, wayarta ta ciro a jaka ta kira Mujaheed tace "Jaheed ka xo ynxu don Allah, akwae abubuwa da yawa da bamu yi mgna a kai ba" yace "to Mami gani nn xuwa" tace "ok" snn ta katse kiran, mikewa tayi tace "bari in je inyi wanka son" ya gyada mata kai ta haura sama.  Washegari saturday dad ya je suleja da Jaheed da frndx dinsa aka daura auren Ikram da son din nasa a kan sadaki dubu hamsin, Ikram bata san wainar da ake toyawa ba tana gidan yakumbo hankalinta kwance don ixuwa lkcn dae ta daina kukan bnxan da take don ssae yakumbo ke riritata komai take so shi take mata, bata da hira da ta wuce ta Aliyu tun yakumbo na jin ddin hirar har ya gundureta, ta daina tanka ta kuma, ba laifi an dan yi taro gidan Ammi su mmn Altine da sauran makwabta da yan uwa, yakumbo bata je ba sbda tana tsare da Ikram kar ta kara gaba tunda ba hankali ya isheta ba,  karfe biyar saura aka fara shirye shiryen wucewa da Amarya Abuja, tana bacci yakumbo ta tada ta taje tayi wanka, ba musu ta je yin wankan don duk ranar bata yi wanka ba tun wnda tayi jiya da daddare, ko da ta fito daga wanka taga su mmn Altine da kawayen Ammi xaxxaune a dakin yakumbo, gaishesu ta shiga yi maimakon su amsa sae taga suna sakin guda, sake baki tayi tana kallonsu, Yakumbo na dariya tace su fita su bar masu dakin ba musu suka fita tsakar gida suna dariya, Ikram ta turo baki tace "me suka xo yi nn yakumbo" yakumbo ta jawo ta ta shiga goge mata jiki tana cewa "gaisheni suka xo yi Ikram" da kanta ta shafa mata mai tana kallon kirjinta, Ikram ta fashe da dariya kmr tababbiya tana kare kirjinta tace "ke yakumbo nono na kike kallo" yakumbo tayi dariya tace "ashe yar tawa ta girma ta fara nono ban sani ba" Ikram ta galla mata harara tace "to shine xaki dinga kallon min, ae Mami tace in dinga sa Hijabi shi yasa nake sawa" vest yakumbo ta bata ta sa snn ta dauko wani tsadaddan less da Alkyabba da Mami ta kawo mata daxu da safe ta sa mata, ssae tayi kyau, da mmki Ikram tace "yakumbo wae ina xani kike sa min sabon kaya" yakumbo na daura mata Alkyabbar a ka tace "gidan Mijinki xaki Ikram" Ikram tace "mijina? Waye mijina, aure aka min?" ganin yakumbo bata ce komai ba yasa ta fasa ihu, yakumbo ta rungumota tace "kai ya hka Ikram" kuka ssae take kmr tasan meye aure, tace "yakumbo ni idan ba yayana bane baxan yi auren ba wllh" da kyar aka fita da ita daga gidan, sbda kukan da take yakumbo tace a tafi da ita Abujan kawae ba sae an kai ta gida ba, uwarta ta riga da ta sa mata albarka hka ma ubanta, kawar Mami daya da na momy daya ne cikin dankareriyar motar da aka kawo na daukar amarya, sae su mmn Altine da makwabciyar yakumbo don yakumbo kin xuwa tayi, ana kiran sllhn Maghrib suka iso makeken gidan sbda traffic da suka samu a hanya, har daki aka kai ta har lkcn bata fasa kukan da take ba tana cewa ita bata son auren, nasiha ssae su mmn Altine suka mata suka bar gidan bayan sllhn isha'i, frndx din Mami da Momy suka kara mata nasu a kai snn suka tafi suka bar ta ita kadae goma saura minti goma bayan sun yi assure dinta cewa ae Aliyu ne mijin nata kuma yana xuwa, sae a snn ta daina kukan da take sae bin dakin take da kallo tana jiran ganin ta ina Aliyu xae shigo dakin don kofofi uku ta gani, goma dae dae taji mota ya shigo gidan, ta kasa mikewa daga inda take sae kalle kalle take kmr munafuka, tana ji aka kulle kofa downstairs, ya shiga haurowa sama a hankali, duk da karancin shekarun Ikram hka kawae gabanta ke faduwa tana kallon bakin kofar da take jin motsi, tana kallo aka murda kofar dakin a hnkali ya shigo dakin kansa a kasa, sae kallonsa take duk da ba ganin fuskarsa tayi ba gabanta na faduwa don dim wuta ne a dakin, dagowa yyi a hnkali yana kallon kan gadon, ido hudu suka yi da shi, ta xaro ido ta mike da sauri tana kallonsa tace "yaya Khaleel"

[


[2/25, 08:35] Zjy: Khaleesat Haiydar

~Ikhram~ By Khaleesat Haiydar 65..... Khaleel yyi shiru

yana kallonta, ita ma kallnsa take tana xaxxaro ido, wani

shegen Ihu ta fasa ta cire Alkyabbar jikinta ta jefar ta shiga

xagaye dakin kmr mahaukaciya tana kuka tana cewa "ni

wllh bana sonka, ni baxan aure ka ba, ka fitar min daga

dakina, ni yayana nake so, wayyo ni ba kai nake so ba" ajiye

ledan hannunsa yyi ya jingina jikin kofa ya harde

kafafuwansa daga tsaye ya rungume hannayensa yana

kallnta, gnin ba ta da niyyar daina haukan da take yasa ya

tabe baki ya karaso cikin dakin ya cire farar rigar shaddar

jikinsa snn ya bude wani drawer ya dauki jallabiyarsa, sae

binsa da kallo take daga durkushen da take tana rusa kuka

kmr ranta xae fita, bae ko kalleta ba ya shiga bathroom, har

ya fito sanye da jallabiyarsa Ikram bata bar kuka ba, ya

xauna gefen gado yna kallnta a nutse yace "kina jin yunwa?"

wani harara ta watsa masa kmr jira take tana murguda

masa baki cikin tsawa tace "to ina ruwanka" mikewa yyi ya

dauko ledan da ya ajiye ya dire gabanta, ta dauka tayi wurgi

da shi, bae ka kalleta ba ya haye kan gado abinsa ya kashe

wutan dakin, mikewa tayi da sauri tayi gunsa cikin kuka

take cewa "ni wllh ka kunna min wutana wa yace ka kashe

min" fixgota yyi ta fado kansa ya rungumeta yace "rufe min

baki kar in cilla ki ta window gun karnukan can dake haushi

a waje" shiru tayi a dan tsorace, tayi lamo a jikinsa yana jin

bugun xuciyarta, a hankali bayan kmr minti takwas yaji

breathin dinta ya dawo nml, ya kunna bedside lamp yana

kallon fuskarta yaga bacci tayi, kashe wutan yyi ya kwantar

da ita ya rufa ta da bargo snn ya juya mata baya yyi

kwanciyarsa, cikin dare ta tashi sae kiran Mami take tana

lalube lalube, ya mike xaune ya kunna bedside lamp yana

kallonta yace "me xata maki" kmr xata yi kuka tace "ni

fitsari xanyi" ya mike tsaye yace "mu je" ta tashi tana kiran

Mami cikin muryar kuka suka nufi bathroom shi dae bae ce

mata komai ba amma Allah ya gani danna xuciyarsa kawae

yake, daga nn bakin kofa ya jira ta ta fito, ya koma yyi

kwanciyarsa ganin taki xuwa ta kwanta yasa yace "baxa ki

xo ki kwanta ba" tace "ehh din" bae kuma ce mata komai ba

ya kashe wutan dakin yyi kwanciyarsa da gudu ta xo ta

kwanta, shi dae bae ce mata komai ba. Ringin din wayarsa

ya farkar da shi da Asuba ya bude idonsa da kyar ya sauke

kan Ikram dake kwance kusa da shi kmr xata shige jikinsa

ta dukunkune kanta waje daya alamar sanyi take ji, janye

jikinsa yyi a hankali daga nata, ya jawo bargo ya rufa ta da

shi snn ya dauko wayarsa a bedside drawer yana kallon me

kiransa da Asuba hka, Mami ya gani a screen din kan yyi

wani tunani tuni wayar ya katse ya jira ko xata kuma kira

bata kira ba, hkn yasa ya ajiye wayar ya mike da kyar ya

nufi bathroom don lkcn sllh yyi, karfe shidda da rabi ya

shigo gida daga masallaci, ya nufi gun wayarsa ya dauka ya

ga Mami ta kuma kira har sau biyu, kiranta ya shiga yi, tana

dagawa tace "ina ka shiga hka Khaleel" ya dan shafa kansa

yace "na tafi masallaci ne Mami, ina kwana" bata amsa

gaisuwar tasa ba tace "ina dota na" ya juya yana kallon

Ikram yace "bata tashi ba" tace "ok kar ka tashe ta, jummai

na nn xuwa tana hanya ma ynxu" tana kai wa nn ta katse

kiran, ya dan yi murmushi yana shafa sajensa, ko amsa

gaisuwarsa ba yi ba ma, wanka ya shiga kawae, har ya fito

Ikram bata tashi ba ya kalli agogo yaga bakwae dae dae,

kararrawar gidan yaji ana dannawa, ya dauki jallabiyarsa ya

xura ya sauka kasa don bude ma jummai kofa, kulolin

breakfst da flsk ne a hannunta, ya gaisheta ta amsa tana

washe hakora tace "sannu babana, ina Ikhram din" ya juya

yana kallon sama yace "bata tashi ba" Jummai ta shigo

falon tana cewa "ehh ka barta kawae tayi baccinta ta huta"

bin ta yyi da kallo a xuciyarsa yana cewa "wnn tsohuwar

kuma me take nufi" girgixa kai yyi ya koma sama ya bude

daki ya shiga, juye juye take kan gadon lkci daya firgit ta

mike xaune tana kalle kallen dakin, tana ganinsa tsaye ta

galla masa harara tace "me kke yi a nn" shima ya galla

mata hararan ya juya ya fice daga dakin, kuka ta saki

amma ba hawaye, dae dae nn jummai ta shigo dakin, Ikram

ta mike da gudu ta rungumeta ta fashe da kukan gske.

Karfe sha daya jummai ta je dafo abinci a gida ta kawo na

rana, Ikram ta dinga kuka wae ita sae ta bi ta, jummai na

isa gida ta gaya ma Mami irin kukan da Ikram ke yi, ba shiri

Mami ta kira Khaleel tace su taho gida, karfe sha biyu suka

isa gidan ta bude mota tayi cikin gida da gudu ta xube jikin

Mami dake falo tana kuka, a rude Mami ke tambayarta me

ya faru cikin kuka tace "ba ance min yayana bne Mijina,

kuma ban gansa ba har ynxu" Mami ta rungumeta tana

shafa kanta tace "ya isa dota na bana son kina kuka hka

kinji" ko minti sha biyar ba suyi a gidan ba Aliyu ya shigo,

Khaleel na xaune dinnin yana shan tea, Ikram kuwa na jikin

Mami har lkcn idonta a rufe kmr me bacci bata ma san ya

shigo ba, a sanyaye ya karaso cikin falon ya durkushe

gaban Mami da ta kasa kallonsa, yana girgixa kai hawaye

cike idonsa yace "don ba ke kika haifeni ba yasa kika min

hka ko Mami"

Like · 1 · Reply · Report · 2 minutes ago


[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 66..... Ikram ta bude ido da

sauri jin muryar Aliyu, sae ta fashe da kuka ta sakko kasa ita

ma ta durkusa gabansa, tana kallonsa tace "yayana ance min

kai ne mijina, amma ban ganka ba sai yaya Khaleel" kasa daga

kai ya kalleta Aliyu yyi, hawaye kawae yake, Mami ta dafa sa ta

dago kansa tana kallonsa cike da tausayi tace "kar ka kuma

cewa hka son, kai ma kasan i luv yhu more den abinda na

haifa, its nt my fault Aliyu, mum dinka ce tasa nayi hkn, but ka

kwantar da hankalinka in'sha Allahu xaka auri Ikram, don ynxu

ba aure tayi ba, at anytime xan karbi takardarta hannun

Khaleel, dan he is nt meant 4 her, nd she's meant 4 only yhu

son," Khaleel ya ajiye kofin hannunsa ya kauda kansa yana

murmushi, kasa ce mata komai Aliyu yyi har lkcn kansa na

kasa, Mami ta mike a sanyaye ta haura sama, Aliyu ya dago da

kyar yana kallon Ikram, Ikram ta matso kusa da shi tana goge

masa hawayen fuskarsa tace "ka daina kuka kaji yayana, ni ina

sonka wllh" a sanyaye yake gyada mata kai, ta rungumesa ta

fashe da kuka, ya rumtse ido duk da yasan bae kamata ba

amma ya kasa cireta daga jikinsa, a hankali yaji tana cewa

"yayana ka manta promise din da nayi maka baxan aura kowa

sae kai ba" dagowa yyi yana kallonta, ya sakar mata murmushi

yana kallon cikin idonta yace "na tuna kanwata" ita ma tayi

murmushin tace "to har ynxu ni banyi aure ba, kai kadae xan

aura ka ji" ya gyada mata kai a sanyaye, a hankali yace "to kiyi

min promise cewar baxa ki bari kowa ya taba min jikin ki ba

Ikram" ta xaro ido tace "to dama ae baxan bar kowa ya taba ni

ba yayana sae kai" yyi murmushi yace "to ngdd kanwata, Allah

yasa ki rike min promise dina kanwata" tace "wllh xan rike

yayana" mikewa Khaleel yyi yana murmushi ya nufi stairs ya

haura sama, Aliyu ya bisa da kallo snn ya Mike da kyar ba tare

da ya kalli Ikram ba yace "na tafi kanwata" binsa tayi da kallo

har ya isa bakin kofa snn tace "to ina xaka yayana" ba tare da

Aliyu ya juyo ba yace "gidan xani" ya bude kofar ya fice ransa a

dagule. Karfe takwas na dare Mami tace ma Khaleel ya dauki

Ikram su tafi can gida Dad na son ganinsu, bayan ya gama

shiryawa ya shigo dakin Mami yi mata sallama, mami tace "kar

ka sake ka gaya ma dad dinka deal dinmu, ko me xae ce maka

kaji kawae ka tashi, snn da seeyama xaku je can gidan" yace

"to Mami" Mami ta juya tana kallon Ikram dake kallo tace

"tashi ku je dota" Ikram ta bata fuska tace "ina xa mu Mami"

Mami tace "can gidansu Momy xaku je, ku dauko seeyama"

Ikram tace "amma ae gidan nn xamu dawo ko" Mami ta gyada

mata kai, snn ta mike ta sa Hijab dinta ta fita, Khaleel ya dauki

jakar uniform dinta da wasu kayanta da Mami ta shirya mata

xae fita Mami tace "kar ka bar min yara su makara xasu

makaranta gobe, da asuba jummai xata kawo maku breakfst,

idan abubuwa suka dawo min nml, xata koma can ita ma

jumman" yace "to sae da safe Mami, but sch bag dinta fa"

Mami tace "jummai xata kawo gobe" ya juya ya fita daga

dakin, bakin mota ya tar da Ikram, ya bude mota ya shiga ita

ma ta bude ta shiga suka bar gidan, har suka isa gidansu Aliyu

bae ce mata ba bata ce masa ba, yana gama parkin ta bude

mota ta fice tayi cikin gidan, fitowa yyi ya bi bayanta, basu

wani dde ba a gidan, Daddy yyi masu nasiha ssae ita dae

Ikram bata ma san me yake cewa ba don hankalinta gaba

daya na gun kallon da take, Khaleel ya mike ya nufi sama

bayan Dady ya sallamesu ya shiga dakin Momy ya fadi mata

sakon Mami na cewa ta basu seeyama, Momy tace "tab,

seeyama ma bata nn wllh, tana can gidan kanwata kuma

karatun fa" yace "ae daga can xata dinga xuwa" Momy tace "to

sae ta dawo" tare suka fito da momy xata rakasu, suka hadu

da Hajiya a corridor, Hajiya na yar murmushi tace "A'a ango ne

a gidan namu yau, sannu ango ina Amaryar taka" dariya ta

basa, ya dae yi murmushi ya gaisheta yyi gaba, Momy tayi

tsaki ta sauka ita ma, har bakin mota ta rakosu snn suka bar

gidan, sha daya saura suka isa gida, ya juya yana kallon Ikram

yaga bacci take, bude motar yyi ya fito snn ya xagayo ta inda

take ya bude motar yana kallonta, bakinta ya dan buge, ta

farka a dan tsorace ta fito da sauri daga motar tana hararansa

tace "meyasa xaka taba ni" tsaki tayi ta shiga kalle kallen inda

suke, ta bata fuska xata yi kuka tace "meyasa ka kawo ni gidan

nn kuma, ni wllh ka mayar dani gidan Mamina" rufe motar yyi,

ya nufi hanyar shiga gidan, ta bisa da gudu tana kuka, suka

shiga falon ya kunna wuta snn ya haura sama tana biye da shi

a baya tana kiran Mami, yana shiga daki ya shiga bathroom ya

canxa kayan jikinsa xuwa na bacci snn ya fito yyi kwanciyarsa

don yyi wanka a gida, ta tsaya daga bakin kofa tana rera kuka

tana kallonsa, kashe wutan dakin da yyi yasa tayi gunsa da

gudu tana cewa "ni ka kunna min wuta in dinga ganin haske"

fixgota yyi kmr jiya ta fado jikinsa, ya rungumeta, a hankali

yace "shiiii" shiru tayi kmr jiya yana jin bugun xuciyarta, gashin

kanta ya shiga gyarawa a hankali yaji ta xamo daga jikinsa

bayan kmr minti biyar ta juya masa baya, ya juya yana kallonta.

Like · 5 · Reply · R

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~  By Khaleesat Haiydar

   67......

 Ikram ce tsaye kitchen kusa da gas tana hawaye tana kallon talgin semo dake kan gas yana ta dahuwa, ita kam bata ji ddin gama junior waec da suka yi ba da ynxu tana sch duk da ba holiday aka basu ba kawae tana xaman gida ne tunda bbu abinda suke a sch ynxu, Jummai ce ta shigo kitchen din rike da ledan cefanen da taje tayi, tace "lah baki fara ba Ikram" cikin muryar kuka tace "to ni ban iya ba kona ni xae yi wllh" muryar Mami taji tana cewa "au tsayuwa kika yi a kitchen din dama, ae wllh sae kin tuka tuwon nn sae dae yyi ta kona kin, shashashar yarinya kawae, ni ban san irin yarinyar nn ba, da na kasa ne da kinsan ynda kika tuke shi kika kwashe, maxa bar mata kitchen din jummai ki fito, mate dinki a kauye har miya suna yi ba tuwo ba" jummai ta fito tana dariya, Khaleel dake kwance falo yana kallo yace "Mami kar ta bata maki gas, ta fito kawae, idan Allah yyi kwakwalwarta xae budu ta iya xata iya" Mami ta watsa masa mugun kallo bata ce kmai ba, ya dauke kansa yana murmushi, yau watanni biyar knn da hada auren Khaleel da Ikram, satinsu uku da xama a gidan Khaleel mami tace su dawo gida amma ba da sanin daddy ba don ta dinga koya ma Ikram abubuwan da ya kamata tun daga kan girki xuwa aikace aikacen gida don bbu abinda ta iya, ssae ta ba Khaleel wahala sati ukun da suka yi a tare don bbu abinda ta iya sae kallo da bacci, dawowarsu gida ya ba Aliyu damar xuwa yana ganinta kullum, ko kadan Mami bata hanasa ba sae dae bata cika son suna xama wuri daya tare ba, shakuwarsu da Aliyu ya karu fiye da na da don ssae take ji da shi, komae sae tace yayana, shi dae Khaleel ba ruwansa don dariya ma kawae suke basa, sae dae fa dawowansu gida ya daina toleratin rashin kunyar da Ikram ke yi masa don da tayi xae maketa sae dae Mami tayi fadan ta tayi shiru, hkn yasa dan shirin da suke yi da ma suka daina kwata kwata da ta gansa sae ta murguda masa baki tayi tsaki, lkci daya girma ya fara bayyana jikin Ikram, kirjinta ya dan ciko nml as a fifteen yr old gal, Mami jira kawae take Ikram ta kai ss2 ta karbi takardarta gun Khaleel ta ci gaba da karatunta kawae, don ranar ca tayi ma Aliyu sae ta shiga higher institution xata basa ita kafin nn ta xama mace sae ta ga ta inda Hajiyarsa xata rainata, shi dae bae ce komai ba amma hankalinsa ba a kwance yake ba har sae ya ga Khaleel ya bata takardarta, a watanni biyar din nn sau shidda suka je suleja gun Ammi, Mami kuma ta kawo Ammi nn gidanta sau uku, Muryar Mami Ikram taji daga bakin kofa cikin fada take cewa "ooh har ynxu a tsaye kike knn ko" Ikram ta dauki muciyar tuwon da sauri tana share hawayenta, ta saka cikin talgin Mami tayi kwafa ta fice daga kitchen din tayi hanyar stairs, ko minti uku ba'ayi da barin Mami wajen ba Ikram ta fasa wani shegen ihu, Khaleel dake kwance ya mike da sauri ya nufi kitchen din a rude, hka ma Mami da ta sakko kasa da sauri, tsaye ya ganta tana yarfe hannu, ya galla mata harara cikin tsawa yace "meye" ta bata fuska tace "abun yana tsalle sae ya taba ni a hannu" ya juya ya fice daga kitchen din Mami ta sauke ajiyar xuciya tace "xo ki fita" da sauri ta fice daga kitchen din jummai na dariya. Ana saura sati biyu Ikram ta fara senior sch Mami tace Khaleel ya kaita su je gaida Daddy, bayan isha ya shigo dakin Mami don Ikram na ciki taki fitowa har lkcn, tana tsaye gaban Madubi daure da towel sae shafe shafe take don shegen son kwalliya ke gareta, ya rungume hannayensa yana kallonta daga sama xuwa kasa ta madubi, ta juya tana hararansa xata yi mgna yyi murmushi yana gyada kai ya fice daga dakin, garin da hadari ssae suka bar gidan bayan Mami tace kar su dde sbda hadarin, suna isa gidan aka fara ruwa, daddy yaji ddin ganinsu ssae don har lkcn bae san a gidan Mami suke ba, Hajiya dae sae hararar Ikram take, Ikram bata ma san tana yi ba sae waige waigen inda xata ga Aliyu take amma bata gnsa ba, shi ko yana daki yaki fitowa, karfe goma saura Mami ta kirasa tace "wae baku fito bane har ynxu Khaleel" yace "ynxu xa mu fito mami" momy tace "A'a ku kwana kawae a nn Khaleel ina xaku cikin ruwan nn" Khaleel yyi murmushi yace "bakomai Momy xamu tafi a hka" har daddy sae da yace su kwana amma Khaleel yaki, ita ma Ikram ba so take ba don hka seeyama ta rakaso su da umbrella xuwa mota suka shiga suka bar gidan snn ta koma ciki, Khaleel yasan Momy fushi tayi shi yasa bata rakosu ba, gidansa ya nufa direct, Ikram ta hade rae tace "ina xa ka kai ni" yyi bnxa da ita yana ta tafiya yana murmushi, kuka ta fashe da bae ko kalleta ba har suka isa gidan ya gama parkn dae dae nn kiran Mami ya shigo wayarsa ya dan yi jim snn ya fita don kar taji kukan Ikram ya daga kiran, a fusace tace "wae wnn wani irin wlknci ne Khaleel" yace "Mami mun taho nn gida ne, kinsan bana son drivin ana ruwa" shiru yyi yana sauraren masifar Mami, har ta gama snn yyi murmushi ya mayar da wayar cikin aljihunsa, ya bude motar yana kallon Ikram ya galla mata harara yace "baxa ki fito ba" cikin tsawa tace "ehh din" murmushi  yyi yace "ae yau xnyi magnin wnn tsiwar taki"

[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~  By Khaleesat Haiydar       68...... Ikram ta fashe da kuka tace "ni wllh baxan fito ba, ka kaini gidanmu" ya xaga ta inda take ya bude mota ya fixgota ta fito tana harararsa, rufe motarsa yyi snn ya ciro makullin gidan cikin aljihunsa ya nufi balcony ta bi baynsa da gudu tana kuka, yana bude gidan ya shiga ya kunna wutan falon ya juya ya gnta a bayansa yyi murmushi, hannunta ya kama suka kuma fitowa balcony suka xaga ta bayan gidan, ynxu kam ruwan ya dan tsaigaita sae yayyafi ssae, kusa da wani cage ya kai ta yana kallnta yce "kinga nn?" bata ce kmai ba sae lekan abnda ke cikin cage din take taga karnuka biyu, suna gninta suka fara haushi da gudu ta koma bayansa gabnta na faduwa tana xare ido, yace "to nn xaki kwana yau ki yi gadinsu baxa ki shigar min gida ba" yana kai wa nn ya juya yyi gaba ta bisa da gudu tana rusa kuka tana cewa "wayyo Mamina, wllh sae na gaya ka da ita" bae ko kalleta ba ya rufe karfen balcony tun kan ta karaso ya shige falo ya rufe kofa, kuka ssae take tana kiran sunansa ya bude mata kofa ga karnukan sae haushi suke da karfi, ruwa ya kuma sakkowa kmr daxu nn da nn ta jike, yana kwance falo yana jin ihunta tana yi tana basa hkri, bbu wnda bata kira ba tun daga kan yayanta mami seeyama, Momy har Amminta, duk yana jinta sae dariyar jin ddi yake, ta kai kusan minti talatin cikin ruwa tana kuka tana kiran sunansa, lkci daya tayi shiru, da sauri ya mike ya nufi kofar ya bude ya gnta xaune ta jingina da bango tana kukan a hnkali, duk ta jike jagab, komawa yyi ya dauko umbrella don baxae iya shiga ruwan ba, ya fito yana kallnta yana murmushi, ta hade kai da gwiwa tana rera kuka, ya karaso gabanta yace "xaki sake yi min rashin kunya" a fusace ta dago kanta cikin tsawa tace "ehh" yace "to" snn ya juya xae bar wajen, ta mike da sauri tayi kusa da shi tana kuka tace "wllh baxan sake ba yaya Khaleel don Allah kayi hkuri" ya juya yana kallnta yace "da gske" cikin kuka tace "ehh" yace "to Allah ya taimake ki" ya kama hannunta suka shiga cikin gidan, daki ya wuce da ita sae rawan sanyi take, ya bata towel ta shiga bathroom ta cire kayan jikinta, fuskarta a daure ta karba ta shiga bathroom din ta daura ta fito, ko da ta fito baya cikin dakin, ta rakube gefen gado tana rawan snyi tana hawaye, rike da kofin tea ya shigo dakin, ya xauna gefenta yana kallnta yace "ga tea kisha sae ki daina jin sanyi" kauda kai tayi cikin kuka tace "bana so" ya ajiye tean ya jawota jikinsa a hankali yace "sbda me baki so" turasa ta shiga yi da karfi, yyi mata mugun kallo yace "au rashin kunyar xaki fara min" girgixa masa kai tayi da sauri tayi lamo jikinsa tace "A'a, amma ka daina taba ni" yace "sbda me" tana kkrin kwace kanta tace "sbda kai ba mijina bne, yayana xan...." buge bakinta yyi ya turata yace "to ki auresa mu ga" ta koma baya tana kallnsa kmr xata yi kuka ba daman yi masa rashin kunya, kofin teansa ya dauka ya shanye snn ya ajiye kofin ya haye gado ya rufa da bargo, tana murguda baki tace "to ni ka tashi ka nemo min kayan da xan sa" kashe wutan dakin yyi, ta dan yi tsaki ta kwanta can karshen gadon don ynxu ta daina tsoro, a hankali ya birgino kusa da ita ya jawo ta jikinsa, ta turasa da karfi tace "ha'a meye hka yaya Khaleel, ni ka matsa..." hannu ya sa ya rufe bakinta yace "shiii, cire min towel dina ki bani na fasa ara maki " ta xaro ido cikin duhun xata yi mgna, taji yana kkrin cire mata towel din, ta fasa kuka tana cewa "don Allah ka bari ni ban sa kaya ba, wllh xan cire maka da kaina" wayarsa ya shiga ring ya turata da sauri ya fada kan gadon, da kyar ya mike xaune yana kallon wayar, nmbr Mami ya gani, ya rumtse ido yaki daga kiran har ya katse, ya mayar da wayar silent snn ya koma can side dinsa ya kwanta ya rufe da bargo ya barta nn xaune tana kuka, har karfe daya idonsa biyu yana jin Ikram ta gama kukanta ta kwanta bacci ya dauketa 30 mins ago, ya mike xaune da kyar ya kunna wutan dakin ya juya yana kallnta, tana kwance ta takure kanta sbda sanyi towel din jikinta ma na kwance gefenta, ya tsura mata ido yana kallnta na kusan minti goma snn ya sauke ajiyar xuciya ya koma kusa da ita ya rungumeta ya rufa masu bargo ya daura kansa a kirjinta, wajen karfe biyu da rabi Ikram ta farka tana juye juye, Khaleel ya mike xaune da sauri yna tambayrta menene, tace "cikina ne ya fara min ciwo" ya dagota yace "cikin ki" ta gyada masa kai kmr xata yi kuka, duk kwanan nn hka take fama da ciwon ciki dama kmr ynda ta kirasa, rungumeta yyi yace "kiyi hkuri xae daina kinji" shiru tayi bata ce kmai ba, bayan minti biyar ta saka masa kuka ssae, ya kunna wutan dakin yace "wae ssae yake maki ciwon" cikin kuka tace "ehh" lallashinta ya shiga yi tana ta juye juye, har kusan asuba basu yi bacci ba sae kuka take masa tana kiran Mami, duk ta daga masa hankali, jikinta yyi xafi, cikin kuka take ce masa ita amai take ji, ya mike yace yana xuwa ya fita xuwa dakinsa ya dauko mata paracetamol, ihu ta fasa ya dawo dakin da sauri yace "menene" kalln jikinta yaga tana yi, ya karaso da sauri ya ga jini jikinta da xanin gadon.


Post a Comment

0 Comments