Azumin ilu hausa novels 7

 AZUMIN ILU*

😂😂😂😂😂😂


        *peg 23*


*MAMAN MAMY*......✍


🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻

   *ILU a BIRNI*

Hhhhhhh kardai kubari abaku labari ILU ya zabure ya shiga binni acan ne zaiyi suna saboda shakiyancinsa da   hikimarsa ....uhm badai a cewa komai👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻😂





Hankali tashe maigari ya fito daga gida shida wasu mutane ukku da suke magana .....yadda ILU yayi wata faduwa gaban maigari saika rantse da Allah wani mugun tashin hankali ne ta tun karo kauyen ...


Lfy ILU maigari ya fada afurgice ...inafa lafiya ga akuya can zata mutu maciji ya sareta ILU ya fada yana fitar da numfashi ....


Eyeee na bani ni uwaisu yanzu akuyar tawace zata mutu tashi Muje inganta yau naga ta kaina saiga maigari na Neman fashewa da kuka...


Cikin mutanen nan ne daya ke fadin haba maigari akan akuya daya zaka tayar da hankalinka duk yawan dukiyar dabbobi da kake da ita ....

Haba kafin su farga maigari ya nade babbar rigar shi ya sheka aguje yana fadin ta ina kukayi ILU ....ILU ne ya Mara masa baya yana fadin kara wuta dai maigari saura kadan Allah yayi mata cikawa ....oh! Jamaakuzo kuga yadda maigari ke sheka gudu kamar Wanda akace gaba dayan awakan zasu mutu....



Mutanen da ya bari ne dayan ya dubi gudan... Aminu tsayawa zamuyi bazamu bishi ba ...nima tunanin da Nike kenan ai basu tsaya wata shawara ba suka bisu aguje......


Tun daga nesa maigari ya hango yadda akuya ke bultse bultse taji maza ...ai maigari baisan sadda ya sauke rawanin dake kansa ba ya rike a hannu ...shi kenan ai wannan tana daya daga cikin manyan garke yau na shiga ukku ni uwaisu..


Uwaisu!! Mudi da basiru suka maimaita sunan suna kumshe dariya wai Ashe sunan maigari kenan basiru ya fada kasa kasa da kyar suka kumshe dariyar dake Neman tona masu asiri ....


Maigari ne ya dubi ILU ...ILU ya akai wannan alamari ya faru ...ILU ne ya fara matse kwallan karya dai dai lokacin mutanen maigari suka karaso sunata kallon akuya na shure shure kamar da gaske ...


Bari ya maigari tunda Nike ban taba ganin tashin hankali irin na yau ba... Kawai muna zaune sai dai mukaji akuya ta kwala ihu irin ihun da tumakai basu taba yin irin shi ba.... Mu duba haka sai mukaga katon majici tunda Nike bantaba ganin mai irin girmansa ba idanuwan sa guda ukku reras... Ukku kace ILU maigari ya fada yana zare idanu tare da marmatsawa alamun tsoro ....



Kwarai kuwa ukku kansa kuwa ko bai kai na mudi ba to kadan ya rage ..eyee mutanen nan suka fada suna kara kallon mudi .....sosai kuwa inji basiru ai inaga wannan macijin shine sarkin macizzai na nan yanki ....tuni jikin maigari ya dauki rawa cikin in ina yake fadin yanzu ya zaayi da ita ILU ba maganin da zamu bata ta warke.....





Afirgice ILU ya dubeshi magani... Tab Ashe kanaso mu mutu waya fadamaka irin wadannan macizan nayin Sara abaada magani ai sai dai a yankata kawai a cire dai dai inda ya sareta a zubar shi kenan kawai....


Yankawa! Maigari ya maimaita hankalinsa tashe saboda in akwai abinda yaki jini to asara ce.... Eh sosai kuwa mudi ya bashi amsa baima wuce yan mintoci ta karasa ba ...daya daga cikin jamaarsa ne ya dubeshi hakuri zakayi ranka ya Dade wani ganin ga Allah baiwa ne...



To shi kenan a yanka maigari ya fada yana matse yan kwallansa ....kici kaca aka danne akuya basiru ya danna mata wuka aka yanke ..maigari sai share zufa yake...



Da yake cikin mutanen sa akwai barinji cikin kankanin lokaci aka fede ta tas.... Maigari ne ya dubi ILU saika amshi wuka ka yanki inda macijin ya sareta a matsa can karshen gari a zubar ...da sauri ILU ya karbi wuka ya fara yanko cinyar akuya yana fadin daga nan dafin ya fara ....in taka ice maku saida ILU ya wafce Rabin akuya da kwatarta wai duk dafin ya shiga ciki ......



Ajiyar zuciya maigari ya saukar ganin uban tulin nama amma ance dafin maciji na ciki ....girgiza kai kawai yayi ya dubesu to Ku tabbar kun zubar da naman nan bayan gari kar wani ya ciyowa kansa ajamani balai ....yar dariya mudi yayi sha kuruminka maigari ai inda baka taba tsammani ba can zamu kai wannan nama ....


Yawwah to shi kenan sawa yayi mutanensa suka dauki sauran naman dayan sai kallon tulin naman nan yake cikeda mamaki ...ILU ne ya gallara masa harara to ko abaka kaci ne... Aa ILU nibance ba kawai INA takaicin zubar da nama maiyawan gaske ...uhm kaga aminu Muje bari kara daga min hankali maigari ya fada tare dayin gaba yana fadin maza Ku tattaro kiwon Ku dawo ILU ...




Baijira amsarsu ba suka wuce zuwa cikin gari da sauran naman daya rage ...



Saida suka bari sun kule sannan suka fara babbaka dariya mudi hadda faduwa kasa shi kanshi basiru dafe ciki yayi saboda dariyar ta fara motsa masa ciki ....ILU ma dariyar yake yana kallon naman...





Kai wllh ILU balai ne mudi ya fada kaga maigari buguzun buguzun dashi aakuyarsa zata mutu har kuka yayi fa h...


 Wai uwaisu! Inji basiru dariya sukasa gaba daya ...sunan yayi min dadi tunda Nike ban taba jin sunan maigari na gaskiya ba sai yau da dalili yayi dalili ILU ya fada yana dariya ...



Aikam yau naga uwaisu wai kunga yadda keyar maigari take haba shiyasa kullum kai cikin hula basiru ya fada yana kara gyara zama...



Sunyi dariya sosai har yadda maigari yayi saida ILU ya maimaita sannan suka fara yima nama gashin tsire ...ILU na fadin zaiga zubarwa ...






*09031711711 for comment* maman mamy ke cewa da fatan kowa yasha ruwa lfy

[6/20, 18:42] Maryam Muhammad Hassan Ce: *BRRLIANT WRITER'S ASSOCIATION*⚜




😂😂😂😂😂😂

*AZUMIN ILU*

😂😂😂😂😂😂


  *peg 24*

*MAMAN MAMY*.....✍


*yeeee barkanku da sallah masoya ina fata kowa yayi sallah lfy tare da fatan zakuji dadin kara kasan cewa tare dani acikin wannan novel ngd*



👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻jinjina ta musamman ga yan group dina the top Hausa novel gaskiya inajin dadin yadda kuke kula dani akoda yaushe Allah yabar zumunci ameen🙏🏻🙏🏻


      *sokon barka da sallah ga yan BRRILAINT hantsi leka gidan kowa💃💃💃*



Bayan sun kammala gashe naman ne basiru ya dubi ILU dake ta zabga murmushi kamar sabon ango...


Gobe kuma me zamuci mutumen ..yar dariya ILU yayi  sha kuruminka nawan ai gobe bazamu zoba saboda maigari ya kara mana kwana kan cin kaji ...dariya mudi ya sa yana kokarin kashe wutar da sukayi gashin... Uhm kace garken uwaisu ya bani kenan ...



Sai da suka raba naman dai dai sannan suka kado awakai gida suna tafe ILU na dariya yana baje bajejiyar rigarshi ....


Bayan sun sakasu gidan ne ILU ya basu ajiyar naman shi ya shiga kaiwa maigari makulli ...zaune ya sameshi ya buga uban tagumi kamar wadda uwarshi ta mutu ...

Sai da ILU ya gyara fuskarshi sannan yace... Ya maigari ga makullin angama aiki ...jiki sanyaye maigari ya karbi makullin tare da fadin ...gobe kuzo fa don duk Wanda bai zoba saina kara masa kwana kai ...yar dariya ILU yayi ba damuwa zamuzo ...



Yana fitowa suka tafa da basiru sannan suka hau hanyar gida ...



Yauma zaune ya iske su tsakar gida asabe CE ta tashi ta nufi ILU tana kallon ledar dake hannun sa tare da fadin ga ILU ga ILU kawo ledar in kai maka daki ....


Janye ledar ILU yayi tare da gallara mata harara ...oh ni ILU asabe yaushe kika koyi sa I do ne ina ruwanki da Leda ta ....


Kumshe dariya asabe tayi ..ILU laifi ne don danuwa ya tari  danuwa sa ...eh laifi ne matsa in wuce ko inbigeki wllh tunda Baku gaji da zama ba ai kunga zama  ....wucewa yayi tare da kallon iya dake kallon su tana dariya....


Iya iya iya baiwar Allah ana nan zaune ko wai Ku meyasa bazaku tashi Ku nemi na kanku ba kullum sai dai kuyi zaune kuyi ta zare idanuwa kamar mage....


Asabe CE ta kalleshi sannu mai Neman na kai ...duka yaushe ka fara fita ko yanzu da kake fitar ai akwai dalili da ba sai dai kayi kwance ba kana mana raki kamar wani karamin yaro ....


Matsawa tayi tasan ba karamin aikinsa bane ya kai mata bugu ..dariya iya tayi sosai tana kare masa kallo da bajejejiyar rigarshi da iska ke kadawa ...uhm gane hanya asabe ai ni bazansa ILU cikin masu Neman na Kansu ba zan dai iya sashi cikin layin yan Neman rigima ....



Murmushi ILU yayi sannan ya wuce da ledar sa yana fadin iya lafazinka iya kason kason ka ehee...


Aa yi hakuri ILU abin bai kai nan ba asabe ta fada tana dariya ....iya ma dariyar take tare da fadin ato duk ranar dai da maigari ya gane ba ruwa na  kuma aka bani ci zanyi tunda bani na aiki mutum ba.... Sosai kuwa iya ai koni ci zanyi wallahi yo in ruwana asabe ta fada tana gyara zama...



Shidai ILU baice kanzil ba ya shige dakinsa yana murmushi ...



     *bayan magrib*


Yauma gefe ILU ya koma da ledar sa ya fara cin naman shi yana dangwala yaji yau kam ko kosan da koko bai kalla ba ga lemunsa mai sanyi gefe yana korawa...



Malam ne ya dubeshi ...ILU yau ma kazar dajin CE ka samo ..nifa na kasa gane maka .....anya lamarinka akwai kamshin gaskiya ciki?? 



Nama ILU ya tura bakinshi ba wani Abu ya malam ka yarda dani ...ko akwai wani Abu asabe ??


ILU ya dubi asabe ...da sauri asabe ke fadin aa ba komai malam ba komai... Tasan halin ILU ta fada ta fadi wani Abu Allah kadai yasan tsiyar da zaya kulla mata ...


Yar dariya ILU yayi ..kefa iya akwai wani Abu ...hmmm kaga ILU in ka tashi zuwa kabar jirana shaaninka ai sai kai wa ya isa yasan halin da kake ciki ...



Dariya malam yasa tabbas yasan akwai wata akasa kawai dai suna tsoron ILU ne shima yasan halin yan kayan sa...







*barkanmu da sallah all inajiran ILU yazo mu zagaya mu gaida masoya*


Post a Comment

0 Comments