AZUMIN ILU*
😂😂😂😂😂😂
*peg 21*
*MAMAN MAMY*.....✍
```allah yasa mudace duniya da lahira Allah kasa muna cikin intattun bayi```🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻
*barkanku da shan ruwa masoyan ILU🍷🍷🍗
Nasan dai da yawa sun hadewa kajin maigari miyau duk da dai kunsan ILU da Rowa🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣
Gaskiya na yarda asabe ta samun iya ta fada tana kara kallon kofa... Har asabe zatayi magana ILU ya shigo buguzun buguzun tsayawa yayi yana masu murmyshin nan nasa..... Sai kuma yayi wucewarsa yana fadin duk Wanda ya zauna ai yaga zama ....
Iya CE ta dubi ledar dake hannun ILU sai mai ke diga.... Aa ILU andawo kiwon toya gajiya nasan dai baa rasa gajiya ba......
Dawowa yayi ya zauna bisa kujera yar zukunne ...bari kadai iya ai dawa tayi nama kiwo alhamdulilah hukuncin nan yayi min dadi saboda in zaayi wata ina zuwa kiwon nan banjin komai ya fada yana kara daga ledar dake hannun shi .....
Asabe ce ta dubeshi sosai ...uhm ILU kenan ai nasan ruwa baya tsami banza to meye kasamo acikin ledar nan ....
Yawwah tayani gani asabe nima abinda nikeson tambaya kenan kika rigani iya ta fada tana kara leka ledar ....
Mikewa tsaye ILU yayi yana fadin shi kenan iya asabe ta koyamaki ganin kwaf yanzu daga kuganni da Leda sai akama a like sai ansan ko meye ciki eh amma da ya malam ne ya shigo da Leda ko kwano bamai cewa meye ciki saini da aka raina ...
Dariya iya tasa oh! Ni salame na godewa Allah to ILU kaida malam daya ne .....hhhhhhh haka yake gani tunda ya girma asabe ta fada tana to she baki ....
Harara ya galla mata oho kodai me zakice sai dai kice wannan da kike gani ya daga ledar naman... Kazar daji CE gasassa kuma kwalelenku karma kusa rai kunji na fada maku .....
Kazar daji ...iya ta maimaita nidai tunda Nike ban taba ganin ko jin wani yace kazar daji ba sai yau ...ILU nuna min ita in gani....
Barta basai kin gani ba tunda baki Santa ba shi kenan Ku dama tsaffi haka kuke koni watarana cewa zakiyi baki sanni ba ....ya nufi dakinsa yana fadin saura kuce Baku dakamin yajin da nace ba wllh yau inhana ayi koko da kosai gidannan ya shige tare da banko kofa yadda zaaji dadin boye kaza ....
Asabe CE ta dubi iya a firgice ...Allah dai yasa kin daka masa yajin kinsan halin ILU abinda ya fada zai iya aikata shi ...wah! Ai tuni na daka shi ai ni nasan halin ILU kamar yunwar cikina ...
Dariya suka sa gaba daya asabe na fadin ILU balai ne amma ni ban yarda da ledar can ba dagani akwai wani ciki.... Yi shirunki iya ta katse ta intayi wari munji sanya masa I do kawai...
Shiru sukayi ganin ya fito yanata kakaniyar rufe kofa ...
Saida ya rufe yabi da tsumma ya kulle sannan ya dawo ya dubi asabe ....saura ki bude min daki wllh na lahira sai yafi ki jin dadi bare na lura kwannan haye min kike ke kin girma ko??
Ya fada yana girgiza kafa ..
Kaga ILU banson Neman fitina yama zaayi ina gani ta bude maka daki ...da wannan babatun Naka ga ruwa can bayi nakai maka ka watsa kaji sanyi tun dazu nakai maka su ,...
Wuce wa yayi bay in yana fadin ato nidai na fadi duk Wanda ya bude dakin can yau ya budowa kansa kema iya kijama bunsurunki kunne naga alamar yana yawan shigar min daki banna rannan sauran tuwona ya cinye to yau ya bude min daki Allah saina targada shi tunda ni ba abokin wasansa bane yawwah ....ya ida shigewa bayi wanka...
Asabe CE ta dubi iya yaufa ya karo wulakanci ji yadda yake wani cika yana batsewa sai kace wani yace zai bude dakin in wani yaji saiya dauka buhun kudi ne ya aje ....
Kedai ba ruwanki ....dole yayi wannan fitinar ga azumi ga kiwo aini nayi tunanin abinda zaiyi ma sai yafi haka iya ta fada tana kokarin tashi ...
Tunda ni fito wankan yake takalar fada ba Wanda ya biye masa dama yafi Jan asabe itakam kwanciyarta tayi kamar mai bacci tana jinsa hadda fadin asabe in tana bacci wai minshari take kamar bijimin sa ita kuma iya intana tafiya kamar ana koyawa yaro tata ....da daidai yaga ba Wanda ya kula shi saiya yayi awallahr laasar ya fita yana fadin tumakan gidannan duk asabe ta koya maku kilbibi ...
Yana fita suka hau dariya tare da fadin morewa ILU kenan in yana fitinarsa ai banza a kyaleshi ....
*bayan sallar magriba*
Can nesa dasu iya ILU yayi shimfida don karma wani yaga abinda ke cikin ledar a hankali yake yagar abinsa yanaci ga tashhinsa gefe yana dangwalawa ....
Malam ne ya dubeshi aa wai yau ILU me aka samu ne ??
Bakomai ya malam kazar daji CEdazu. Da mukaje kiwo muka kama shine muka gasa ko zakaci???
Aa ILU aci lfy kasan bandamu da irin wadanan abubuwan ba ...
Shi kenan ya kara afki ILU ya fada yana tura tsokar nama baki...
Aiba ya kara affki ba bazaka yanma su asabe ba ko kamanta I do guba inji malam...
Hmmmmm yanzu ina iya basu suci suce maka kamar kazar gida kasan su da. Santi shiyasa na hanasu...
*09031711711 for comment Muje zuwa labarin ILU*
[6/20, 18:42] Maryam Muhammad Hassan Ce: *BRRILAINT WRITER'S ASSOCIATION*⚜
😂😂😂😂😂😂
*AZUMIN ILU*
😂😂😂😂😂😂
*Peg 22*
*MAMAN MAMY*....✍
🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻🤵🏻
*ILU a BIRNI na nan zuwa soon labari mai cike da ban dariya yazo da salon nishadantar da masoya yazo da tsare tsare iri iri ina mai tabbatar maku Cewar azumin ILU somin tabi ne akan ILU a BIRNI*
😂😂😂kada kubari abaku labari yana zuwa after sallah🤝🏻💘
*gaisuwar ban girma ga yan brrilaint hantsi leka gidan kowa⚜allah ne ka tafiyantar da alaamurranmu Allah ya karayimana jagora ameeen*👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻
Murmushi malam yayi kaidai ka basu koma me zasuce ....
ILU ne ya dubi iya ..zakici kazar daji ...
Ai ko kazar dawace inaci ..iya ta bashi amsa ...
Yar dariya yayi sannan ya yago nama mai Dan yawa ya mika ma asabe.. Ungo Ku raba in kuma kun raina Ku bani abuna ...da sauri asabe ta karbe ina mu ina raina wa ....
Shiru iya tayi tana taunar nama ita dai taji kamar kaza wannan data sani ...kasa daurewa tayi ...
Kazar daji kece ko ILU to gaskiya wannan kazar ta gari CE ....eh wllh da nima haka zance asabe ta fada tana kara taunar naman ...
Dariya malam yasa ...dama ILU ya fadi santi yayi maku yawa gashi tun kafin aje koina kun fara ...to dama bai Baku ba yaci abinsa ...
Ato ba said a na fada maka ba ya malam ai nan dagewa za suyi da tsiya kaza ce irin ta gari ...ILU ya fada yana taunar kashi. ...
Aa malam ayi batun gaskiya anshi ci kaji naman nan sai ace wannan ba kaza bace ta sosai iya ta fada tare da mikawa malam sauran naman dake hannunta ....
Ina ni bazan karba ba can tsakaninku dama kun saba ...mikewa yayi tsaye ni kunga wurin maigari zani inbashi hakuri hukuncin daya yankewa yarannan yayi tsauri sosai ya sasasauta masu albarkacin watan Ramadan ....
Da sauri ILU ya durkusa gaban malam yana sude hannu ba kadan yaji dadin kazar nan ba ...don Allah ya malam ka kyaleshi wllh hukuncin ba tsanani sosai ciki ka barshi kawai duka fa kwana ukku ne kacal zamuyi kuma koma ba don haka ba ai maigari uba ne garemu zamu iya yimasa ...
Shiru malam yayi cikeda mamakin ILU sai dai duk iya hasashensa bai gano komai ba ....amma tabbas yasan akwai wani Abu akasa saboda yasan halin kayansa...
Ajiyar zuciya malam ya saukar shi kenan ILU Allah ya kyauta gaba bari inyi alwallah in fita sallah kayi maza ka kammla ka fito...
To ya malam ILU ya fada cike da farin ciki ...
Malam na fita asabe ta kalleshi ..tsakaninka ga Allah INA kasamu kaza ILU...
Yar dariya yayi kwantar da hankalinki yanzu zan fada maku saura Ku gayama malam ai kunsan sauran basai na fada maku ba ..
Said a ya kara yagar masu naman ya basu... Iya kau sai was he baki ake ana cin kaza..
Said a ya bari takai masu karo sannan ya fara koro masu bayani ...sukuti sukayi suna kallonsa naman dake bakin asabe kasa ida tamnawa tayi itako iya sauran na hannunta ta rike ta kasa kaishi ga baki ....
Yana basu labarin yana dariya sannan ya kara da cewa ..kuma wllh naji maganar nan ga malam CE masa zanyi tare muka hada baki daku kune ma kuka soya ta ya ida kecewa da dariya...
Innalillahi wainna ilaihir rajuun ..ni salame iya ta fada tare da sakin sauran naman dake hannunta ...na shiga ukku yanzu ILU fitinar daka jajubo mana kenan kajin maigari ILU ...lahailahailal lahu sallalhu alaihi wa sallam asabe kina jin wannan bakin labari ....
Dariya asabe tahau yi hadda tafa hannuwa ...inajinshi iya ai wllh saida raina ya bani bakiga da malam yace zaije ba maigari hakuri ba wani kukan kura da ILU yayi gaban malam ...ai tun nan nasan akwai abinda yake aikatawa ...
Dubanta iya tayi shine kuma kike dariya ...ato iya kuka zanyi ai gara ma inyi dariyar in rage zafi kin dai San halin ILU.. Nikam ko give ya kawo nama ci zanyi ba ruwana ehee ....
Mikewa ILU yayi tare da sakin wata katuwar gyatsa ...alhamdulilah ya fada tare da daukar Dan tsinke ya fara sakace... To shawara dai ta rage gamai shiga rijiya ko kuyi shirunku kuci nama ko Ku fadawa malam duk daya garama kuyi shiru ku kuci nama shine zai fiye maku..ni kunga tafiya ta ya buga katuwar rigarsa yayi waje yana fadin waye yace damu ba muba ...
Oh! Ni salame iya ta fada tare da dunan asabe dake dariya ahaka sukaci gaba da tattaunawa akan lamarin ...iyace ke fadin shiyasa naga ya zunbula waccan katuwar rigar Ashe da aika aikar da zaiyi ...
To kedai bakin ki alaikum kar malam yaji... Wa ni na isa ai bama zan fara ba iya ta fada tana rike haba alamar mamaki...
ILU kam na fita ya hade dasu basiru... Tafawa suka hauyi suna dariya kowa na fadin yadda yasha perty da tasa kazar ...mudi ne ke fadin harna ka gara gobe tayi inga yadda zamuci akuya .....
Suna nan zaune kafin afara sallah suka hango maigari buguzun buguzun da babbar Riga ...ILU ne ya kece da dariya dubeshi da Allah shifa in da balai mai wayo ne...
Gaba daya sukasa dariya wane wsyau anata dibar kaji...
Ahaka aka gama sallah kowa ya watse ...
Da sahur ma bawani abinci karki ILU yaci ba saboda wannan dankwaleliyar kaza da ILU ya tada sai ruwa da yasha sosai .......
Washegari da lillimi aka tashi kauyen taba daya ba rana hakan yasa ILU kara shirin fita kiwo ...
Yana fitowa ya dubi iya dake zukkune tana ba dabbobi abinci asabe kuma na shara ...Toni zan wuce hajiya iya adaka tasshhin da yafi bani jiya dadi ....to adawo lfy iya ta fada atakaice ....
Ba girin garin ba tayi mai inji asabe ..bakuda Matsala ILU ya fada sannan yayi waje ...
Batare da bata lokaci ba suka kora tumakai daji yau baa Debi kaji ba ...
Saida ya kama kosassa akuyan nan sannan yasa suka saki sauran ...mikewa mudi ita yayi ..yanzu zan ruga inkira maigari da kunga munkusa isowa Ku taushe akuayar Ku rika fadin saura kadan ta ida mutuwa majine ya sareta Ku barni da sauran aikin ...dariya suka hau yi to ilun malam angama ..
Da gudu n gaske ILU ya nufi cikin gari yana fadin maigari akuya zata mutu a taimaka maigari!!!
Rigar nan tasa sai sama take iska na kadata
*hhh Muje dai zuwa labarin ILU*
0 Comments