AZUMIN ILU*
😂😂😂😂😂😂
*peg 14*
*MAMAN MAMY*....✍
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
*RAMADAN KAREEM*
*Allah ka karbi ibadunmu ka yafemana zunubanmu ka sadamu da alkharain dake cikin wannan wata mai cike da falala*🙏🏻
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
```tofa jamaa yaufa kawar ILU ba kanta ummuherny 😂😂😂bare kuma asmeenat zeyyan ni kaina jagoran labarin ILU n yau nagane kurena```to Allah yasa mudace😂
Ameeen maryamu karki mana dariya...✍
Tsaye yayi yana kallon asabe dake ta dariya... Aa lafiyarki kuwa asabe kodai kwalwar ta tabu ne ...hhhhhhh haba ILU jibi jikinka duk kumfa sai kace wani kara min yaro
..
Wani Dan guntun tsaki yayi sannan ya nufi dakinsa ...ke asabe wani lokacin baki ganewa ...ai shi kumfa magani ne baki taba jin ance kumfa nasa arziki ba ina sane na barshi ...ki acigaba da dariya duk ranar da nayi arzikin sai kin rains kanki sile bazakici ciki ba dagani sai iya sai ya malam .....yayi gaba yana zare idanu yabar asabe na dariya....
Ranar fa malam sai dai kyale ILU yayi da batun zuwa massalaci salar laasar ..saboda yakai makurar gajiya ko magana ma baiyi sai idanu kamar gyada....
Misalin 6 na yamma su iya na tsakar gida aiki ...sai ganin ILU sukayi ya fito yana fadin Allah! Allah ...yana dafe ciki tare da kakarin amai ...
Da sauri iya ta nufoshi tana fadin yau na shiga ukku ni salame ILU mutuwa zakayi ....girgiza kai ILU yayi a wahalce ..aa iya ba yanzu zan mutu ba kawai dai ina hangen mutuwa ne ....ashha ILU sannu iya ta fada tare da kamashi ya zauna ...
Zaman yaji bazai iya ba yayi kwance lame lame yana bada wassiyya shi ala dole mutuwa zaiyi ....kowa yayi banza dashi sukaci gaba da aikinsu malam ma addua yayi tayi masa saboda abin na ILU ta wuce misali shi kanshi bazai so abarshi ya kara yin dorere ba ....
Ana kiran sallah ..asabe ta Debi ruwa ta watsa mashi ...sai lokacin ne ya mike ya fizgi ruwan sanyi dake hannun asabe said a ya kwankwada son ranshi sannan ya dire kofin yana maids numfashi ....sannu ILU iya ta fada dake tsaye gabanshi ....yawwah ILU ya fada yana hararsu aranshi fadi yake duk zsku ji yadda naji.
..
Bai mayi sallah ba sai da yaci ya koshi yayi gyatsa sannan yayi alwallah ya kabbara sallah.... ILU fa ansha ruwa har wani karatu akeyi da karfi ana gyara tsayuwa kamar bashine ke kiran zai mutu ba ....
Kusa da malam ya zauna yana fadin ....sannu da shan ruwa ya malam don Allah inka rage kabani ...fanken nan ba abinda zaimin...murmushi malam yayi to ILU zan rage maka ...
Bawanda bai rage ma ILU ba ya kuma cinye sannan ya yi wata mahaukaciyar gyatsa yayi alwalla ya nufi hanyar fits yana fadin nidai nayi gaba ya malam .....
Tofa ILU Kaine kayi alwallah zaka massalaci da wuri lallai ansamu acigaba cikin azumin nan Allah mungode maka ....iya ta fada tana murmushi...
Malam ne ya girgiza kai.. Uhm lallai salame Ashe har yanzu baki ida gane halin ILU ba... Ni nasan akwai abinda zai fitar dashi da wuri badai yaci ya koshi ba zakice na gayamaki ....sukuti iya tayi to Allah dai ya shieyamana ILU.... To ameeen inji malam....
Ta bakin malam kuwa saboda ILU na fita shagon sayar da magani ya nufa yana yan wake wakenshi .....halliru barka da shan ruwa da Allah maganin bacci mai karfi zaka bani ....cike da mamaki halliru ya kalleshi ....ILU me zakayi da maganin bacci ana azumi ...uhm bari kaidai ...ni dama in INA bacci ban azumi ban iya bacci shine nace bari in nemi magani....
Wayyo Allah sarki ILU... To gasunan kala biyu ne gadai Wanda kesa bacci sosai nan amma bazan bakashi ba.... Aa halliru bani shi kai dai ba magana r kudi bace nawa yake.... Nera Dari ..to gashi.. Yana halliru kudi ya karbi magani ya saka aljihu ya wuce yana yan wakokinsa cike dajin dadi..
Saura kadan ya isa massalaci suka hade da basiru.. Said a suka gaisa sannan suka jero ILU na fadin.... Da yardar Allah gobe liman da mai gari dore re zasuyi ...cike da mamaki basiru ya kalleshi ta yaya ILU n malam ...
Yar dariya ILU yayi kadai da ido kayi kallo...
*to fans kuma kusa I do kuyi kallo doreren mai gari da liman*
Muje zuwa labarin ILU dani ataskar kungiya msi albarka brrilaint writer's assciaton hantsi leka gidan kowa.......⚜
[6/20, 18:42] Maryam Muhammad Hassan Ce: *B.W.A*
😂😂😂😂😂😂
*AZUMIN ILU*
😂😂😂😂😂😂
*peg 15*
*MAMAN MAMY*....✍
*nace Ku huta*😁
Shiru basiru yayi cike da tunanin abinda ILU zaiyi yau....
Ana gama sallah ...ILU yaja basiru suka nufi wani shago inda ake sayar da lemu kwalba mai sanyin gaske ya say I guda biyu ...suka taho shidai basiru nata kallon ikon Allah... Sun danyi nisa kadanne suka zauna bisa wani Dan dakali....
Lemun ILU ya balle ya jefa magani daya daya aciki ya mayar ya rufe ya dubi basiru ya kwashe da dariya... Wllh basiru har na hango yadda liman zai fara rangaji da wannan rawanin nashi ...shi kuma mai gari nasan sai ya rasa gane hanyar gida...
Zaro idanu basiru yayi kai ILU ko tausayi babu.... Hhhhhhh basiru kenan ai kanka kasan waye ilun malam duk Wanda yaci tuwo dani miya yasha kai dai ka kama bakin ka
Wa ni basiru ya fada... Ai inkaganni lahira kaini akayi... Yawwah basirun inna mai yan kunnuwa.... Tare suka nufi gidan liman...
Kofar gida suka sameshi zaune yana Jan cazbaha ga sauran kayan buds baki gabanshi ...
Sallama sukayi mashi ..suka nemi gefe suka zauna tare da gaidashi day I mashi barka da shan ruwa....
Cike da mamaki liman ke amsawa tare da fadin wa Nike gani kamar ilun malam Allah dai yasa lfy ...murmushi ILU yayi tare da dukar da kanshi kasa irin na ladabin nan ..kai ILU ba karamin jairi bane ...
Aa lfy lau ya liman kawai yau nace dai bari inzo inmaka barka da shan ruwa ....sai kawai liman yahau washe baki yana fadin Allah dai yayi maku albarka yarannan ...basiru kam sai kumshe dariya yake....
Ameeen ya liman ILU ya fada tare da dakko lemu guda ya mika mashi... Ga wannan kadan sha da sanyinshi badai yawa..... Hannu na kyarma liman ya karba yanata was he baki ganin lemu sai zufar sanyi yake ....aa ILU hard a dawainiya
Aa ba komai ya liman ILU ya fada yana kara dukar da kanshi kasa ...
Nan take liman ya bude lemun ya fara sha sanyi na ratsa zuciyarshi ...kai ILU Allah yayi maka albarka ya kara daga lemu ya kwankwada... Ashe haka nan muke maka kallon mashirmanci Ashe kasan abinda kake ...ILU ne ya kalli basiru shima basiru ya kalleshi saura kadan su tuntsire da dariya mussamman basiru ya kara abar wurin ya yi dariyarsa mai Isar shi ....
Said a ya shanye rabi sannan ya kara kallon su... Waini ILU ya batun dorere yau dai karka bari kayi dorere ....nan ma gumtse dariyar ILU yayi... Ai insha Allah gobe bszanyi dorere ba sai wasu kuma....
Yar dariya liman yayi ai dorere ba dadi ILU liman ya fada yana kara shan lemu sanyi na ratsa shi...
Mikewa sukayi to ya liman mu zamu wuce... Inji ILU... A aha har zaku tafi ILU ...to nagode sosai Allah yayi maka albarka ga wani Dan kosai nan Ku tafi dashi ko zakuci anjima ....
Da sauri ILU ya dauka dama sai hararar kwanon yake... Godiya Nike ya liman... Sukayi mashi sallam a suka tafi....
Suna shan kwana basiru ya hau babbaka dariya harda faduwa kasa... Shi kanshi ilun dariya yake tare da fadin ....kai tsohon nan yasan dadi wai kaga yadda yake kurbar lemu yana yamutsa baki kamar an lasawa jariri Zuma .....
Cikin dariyar basiru ke fadin kai wllh ILU kai karshe ne ....
Kaga maza Muje ga maigari tun kafin ya shige gida.... Basiru na dariya suka bar wajen suka nufi gidan maigari...
Liman kau suna tafiya ya kwashe komatsanshi ya shige cikin gida ...yana shiga uwargidan shi talatu ta karbi kayan tare da fadin wannan ragowar namune ko mai gida ...
Fizge robar lemun liman yayi ...kai kudai mata kun cika kwadayi to Dana ILU ya kawomin saboda haka ba Wanda zai shashi.... Buzun buzun ya wuce dakinshi...
Dan murmushi talatu tayi... To liman asha lfy ta wuce kicin ajiye kwanoni...
Lokacin da suka isa gidan maigari har zai rufe gida... Aa wa Nike gani kamar ILU n malam... Eh nine ya maigari barka da shan ruwa ...yawwah ILU lfy dai ko...
Lfy lau maigari dama cewa nayi ya kamata inzo maku barka da shan ruwa.... Kai amma naji dadi sosai ILU ya malam da mutanen gidan....
Suna lfy ga wannan nace bari inkawo maka ba dai yawa...
Cikeda da faraa maigari ya karba ...yaji lemu karara..nagode sosai ILU kamar kasan Abu mai sanyi Nike bukata yanzu ...
Aa ba komai fa ILU ya fada... Mu zamu tafi said a safe.... To Allah ya kaimu ILU ngd sosai ka gaishe da malam...
Zaiji ya fada yana murmushi suka wuce ...tunda suka fito suke dariya har basiru yayi hanyar gida tare da fadin sai goben ILU nasan akwai bidiri garin nan.....
Yar dariya ILU yayi to basiru Allah ya kaimu ....
Tunda ya shiga gida yake dariya har iya da asabe suka fito dagadaki...
Iya ke fadin lafiyarka ILU ....uhm ai tunda kikaga ILU na wannan dariyar to akwai muguntar da zaiyi... Asabe ta fada tana Harar sa.....
*Muje zuwa labarin ILU*
[6/20, 18:42] Maryam Muhammad Hassan Ce: *B.W.A*
😂😂😂😂😂😂
*AZUMIN ILU*
😂😂😂😂😂😂
*peg 16*
*MAMAN MAMY*....✍
```Allah yasa damu da alkhairan dake cikin wannan wata mai albarka```
Dan yake iya tayi ...to Allah yasa ba kanmu muguntar zata kare ba...
To ameeen dai inji asabe tana harararsa....
Shidai ILU baice komai ba sai dariyarsa yake abinsa.... Ya wuce daki ya fara cin kosan daya taho dashi daga gidan liman ....
Tofa jamaa liman fa bacci yake kasarika ...saura yan mintina akira sallah matan suka farka dama shine ke tadasu gaskiya.... Sunyi mamakin baccin liman na yau ...akayi akayi atadashi amma yakasa tashi sai buga minshari yake kamar tsohon sa...haka suka hakura suka kyaleshi ranar ma sai liman yayi sallar asuba...
Hakama bangaren maigari an tadashi an ta dashi yaki tashi haka aka kyaleshi yayita shara baccinshi ....
ILU kam anyi sahur yaci yaci abinci sosai saboda cewa yayi sai anhada mashi hadda na jiya da baiyi sahur ba ...cikeda farin cikin yadda zaiga liman da maigari ...
Tunda suka dawo sallar asuba malam ke mamakin rashin zuwan liman masallaci saboda baiyi mamakin rashin zuwan maigari ba saboda shidai dole liman ya fito ko baijin dadi ...sai dai inya fito yace wani yayi sallar ....
Shidai ILU baice komai ba yana ganin liman bai fito ba yasan cewa aikinshi yayi kyau ....
Sai misalin 10 ILU ya tashi yayi wanka ya fito da cazbaha a hannu ....iya ya duba dake yan share share ...wllh iya yau zaayi rana
Murmushi tayi kwarai kuwa ILU zaayi rana irin mai zafin nan.... Yawwah Allah haka nikeso ILU ya fada yana murmushi sannan yayi waje yana fadin yau akwai kallo kauyen nan ......
Yana fita ya nufi gidan su basiru kafin ma yakai suka hade... Tafawa sukayi tare da fashewa da dariya suka nufi wurin firarsu suna kara zantawa .........
Liman fa Abu ya kankama ko bacci n safe da kyar ya samu yayi ...gashi ana tsala rana irin maisa kishirwannan ....fito wa yayi da niiyar zuwa massalaci kiran sallah azahar duban matan yayi suna aikace aikacen su yaja dogon tsaki...
Yanzu duk cikinku arasa wadda zata tasheni ....wllh yau ukku ukku Nike ganin mutane ji ji nikeyi kamar ba yan hanji cikin cikina rabon da inyi dorere harna mance ....
Wllh wllh liman ba irin tadin da bamuyi maka ba kaki tashi... Uwargidan ce ta mayar masa da amsa tare da dukar da kanta kasa cike da tsoron abinda zai biyo baya ....
Bai kara cewa komai ba ya yi waje yana banbami ...Ashe bai lura ba takalman Kansu daban daban ne rigar kanta daban take da babbar rigarsa ...hatta rawanin ba yadda yake na dashi ya Nada ba ....
Tun daga nesa su ILU suka hangoshi me zasuyi ba dariya ba ILU hard a faduwa kasa.... Duk Wanda ya kalli liman saiya kara kallonshi cike da mamakin yadda ya koma....
Yazo wuce wa ne ILU ya kalli kafafuwanshi ya tintsire da dariya ganin takalma daban daban da alama liman baisan yayi gamin bauta ba .....
Ina yini ya liman ILU ya fada ...cike da galabaita liman ya dubi ILU ...lfy lau ilun n malam...
ILU ne ya kara kallon shi sama da kasa ....ya dai ya liman azumin ne.... Wani Dan nishi liman yayi ..bari kaidai ILU yau dorere Ashe haka kaji rannan wllh dishi dishi Nike gani....
Da kyar ILU ya kumshe dariya ....to ai Matsala r daya ya liman ita yunwa bata da hankali ...hakane ILU wllh na yarda yunwa ba tada hankali... Kaga bari inkarsa nasallaci indan huta kafin in fadi nan.... Buguzun buguzun ya wuce rawanin na Neman faduwa yana taroshi....
Aifa su ILU sai dariya suke suna maimaita yadda liman keyi... Can saiga maigari ya nufo masallacin sai yaken dole yake .....
Nan fa kallo ya koma kanshi ......
0 Comments