auren sirri hausa novels 3

 AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page  7-8



Har DEENi yazo gida tunanin yake akan shawarar da fk ya bashi" anya kuwa zai iya amince da auren zeenat ? 

Lokacin da yashigo yayi daidai da zeenat ta tabare magani tana mikawa ummi ,ta amsa ta apa zeenat ta Mika mata ruwa  ,yayinda shi km yake tsaye jingine da jikin kofa rungume da hannuwansa duka a kirjinsa yana kallonsu, take zuciyarsa ta dinga ingizashi akan lallai bbu wace ta dace ya aura sama da zeenat bisa ga hujarsa tacewa ,bazai taba samun matsala daita gurin kula da mahaifinsa saboda irin soyayyar dake tsakaninsu "

yasan ko yana nan ko baya nan zata   kula daita, umminsa zata zamo a karkashin kukawarta tunda zeenat bata da wata uwar da wuce ummi tunaninsa ya katse lokacin da ummi takira sunansa' tace son karaso mana yayi frigigit ya dawo natsuwarsa ahankali yashiga takowa har inda ummi take ,ya zauna zeenat ta gaidashi ta mike zata fice daga dakin bai amsa mata gaisuwar data masa sai dai yabi bayanta da kallo" ummi ta kalleshi  ta kauda kanta,  yace first lov yajikin naki ummi ta danyi murmushi hade daura hannuta kan sumar kansa  tace naji sauki sosai , ahankali sauke ajiyar zuciya ko bai ce komai ummi ta fahimci yaji dadin yadda yaganta ,yana nan zaune , Sam yakasa  yiwa ummi zance yana ya   auren zeenat din  ,daga  karshe ma tunani yayi kawai gara yasamu ya mahamud  da zance dan gaskiya kunya yake ji yayiwa ummi maganar da kansa .


Da yammacin ranar byn ya dawo daga office yaje har gida yasamu ya mahamud da maganar ya ji dadi kwarai da gaske, har yarasa inda zai sa DEENi dan farinciki dan shima da kansa  ya matsu yaga DEENi  ya ajiye iyali kmr kowani magidanci , yace Shikenan sai kasamu yarinyar da zance, ku daidaita kanku DEENi yace A'a ina ganin  basai na sameta ba in dai first lov ta amince ai Shikenan .

yaya mahamud  yace ummi bazata taki ba Amman dai kasan kaidar auren gidanmu kennan  bbu dole a ciki "muddin kuka daidaita kanku na iyayenmu may sauki ne idan Kuma ita ummi ta amince ita yarinyar  tace bata sonka fa? DEENi yaji haushi da takaici  sunkamasa alokaci guda yace ai nima ba wai ina sonta bane kawai dai zan aureta ne.

 Yaya mahamud yace  shirme bazan kennan kai yanzu idan anzo meeting cewa zakayi basonta kake yi ba ,zadai ka aureta ne ?DEENi yayi murmushin gefen baki har dimple dinsa ya lotsa sannan yace  cewa kurum zanyi ina son zan aure zeenat ne ' Yaya mahamud yace to Allah ya mana zabi na alkhari kabari zanje gurin ummi tukun  duk yadda mukayi daita  zakaji   DEENi yace Shikenan ya mike fice ,a office ma koda yaje  aikinsa kawai yasa gaba  .

 dan shi gabadaya ya manta da wani zance aure can .



Mahamud yasamu ummi cike da karfin gwiwa" ganinsa ba wanda zai kai ummi murna tunda daman burinta kennan  naganin auren DEENi, Amman ga mamakinsa yana gama labarta mata abinda yakawo shi, sai yaga ummi tayi kicin kicni da ranta tamkar bata taba sanin wani abu  farinciki ba "sai da gaban Yaya mahamud ya fadi dan  ganin yadda ummi tayi da fuska tamkar yazo mata da zance mugun abu " tace kai ne kaga sun dace kaba shi shawara  ya nemi aurenta ko Kuma shi da kansa ya sameka da zance ?

 Da sauri yaya mahamud yace A'a shine dai yazo min da zance ummi ta sake daure fuska, sannan tace ka koma ka fada masa ban amince ba ,kace masa akwai sauran mata  a gidan nan  yana da damar zabar duk wacce tayi masa, idan ma ya canza ra,ayinsa nakin auren family'  to yaje waje ya nemi matarsa can itama Allah zai bata nata mijin, Amman Sam ni ban yarda da wannan hadin ba " tayi shiru  na wani lokacin kana zubawa Mahmud idanunta tana kallon yanayin daya shiga ,ahankali ta numfasa sannan tace kana iya  wucewa idan kana da abinyi ka manta da wannan shirme na DEENi .

 Yaya mahamud yayi kasa da kansa Sosai cikin muryasa can kasa kasa  da alamun km  rarrashi yace dan Allah ummi ki amince da auren nan bazan iya tunkarar DEENi da maganar ba.

  duk da bansa dalilinki nakin amincewa ba" ummi ta dan saki fuskanta ba kmr dazu ba tana mugun son mahamud tamkar dan da ta haifa acikinta tana jinsa har cikin zuciyarta .


 tace bawai ina kin hadin bane duk duniya idan akwai wanda zai so auren DEENi da zeenat a bayana yake ,na farko dai kaima kasan halin DEENi  da dan bazar zuciya , ga saurin fushi ga maseefar miskilanci tsiya ga jin kai sannan da bakinsa yasha gayamin cewar shi bazai taba yin auren family ba sannan shi mai digiri yake so ya aura ,shine km yanzu  zai zowa mutane  da wani salo.

 ni da tawa iya secondary kadai ta tsaya" ai kai da jin zancensa ma kasan akwai wani makirci daya shirya "dan nace yayi aure ai bance lallai sai ya aure tawa yarinyar ba , Muhamud yace ummi ki duba  lamarin abun  tunda shi da kansa ya furta cewa ita ta masa ba za'a samu wata  matsala ba ,.

  ummi tace Sam bata yarda da wannan tsarin ba " ita dai yaje gaba ya nema hakurin duniya nan  bbu wanda yaya Muhamud bai bawa ummi ba amman taki amincewa ,duk ta inda ya bullo mata sai itama tabiyo masa ta wata hanyar, har ran  yaya mahamud yasoma baci ,yaji haushin abinda ummi tayi dan haka ya hakura ya fice ransa abace .



DEENi zaune a office dinsa  ya dukufa wajen tura sakwanni a yanar gizo ,hankalinsa kwance yake bin komai daki daki , yaji daya daga cikin wayoyinsa ,daya ta dauki karar sauti mai dadi ,ya dauke idanunsa  daga kallon system din yasa hannu ya dauki wayar yana dubawa ganin sunan dake yawo akan screen din ne" yasa yayi sauri dagawa yakara a kunnenshi hade da yin sallama"  kana ina muryar Yaya mahamud yaji ta daki dodon kunnenshi cikin sanyi murya DEENi yace ina office yace ok idan katashi kabiyo  inason ganinka sannan ya kashe wayar .


DEENi zaune a gaban Yaya mahamud kansa sunkuye a kasa yayinda  idanunshi ke  kallon zarazaran yatsun kafafunsa yana sauraron sakonshi da ummi tabayar a sanar dashi.

 a gurin Yaya mahamud sam bai tsammaci jin haka daga umminsa ba ,ga mamakin Yaya mahamud sai yaji deeni yace Shikenan babu komai Allah yasa haka shine mafi alkhari .

ya mahamud yace ka hakura kennan? Nashi ganin bazai damu dan ummi ta hanashi auren zeenat , dan haka Yace  eh "tunda daman ba wai yana sonta bane" nan dai suka bar zance  aure suka shiga wata hirar daban a inda Yaya mahamud ya tashi yaje  ya kwaso wasu takardu da file files ya zubesu nan  a gaban DEENi yace yasa masa hannu ciki " kai tsaye DEENi  ya zaro wani hadadden Biro daga gaban aljihun  rigarsa yasoma cike  gurraren da akeso yayi sign, dan gabadaya dukiyar DEENi , sulaiman da Muhamud ne akai su suke kula daita  kuma komai na tafiya daidai " domin dukkannisu abu guda ne a gurin ummi  dan ma idan ba'agaya maka ba…

 zaka dauka duk ummi ce ta haife su . 


Sai da DEENi yagama sign din ,sannan yaya mahamud hada da mishi bayanin companies din da suke son budewa a  kasar  American, sun turo musu da sako akan suna da bukatar mutun daya daga cikin masu company din " yazo interview dan haka shi ya wakilta sulaiman yaje , DEENi yayi murmushin yace Shikenan bbu komai duk yadda kukayi ,daidai ne  Allah ya taimaka .



To byn DEENi yakoma gida ya dingawa ummi wani irin kallon, wanda shi kansa yakasa gane dalilin yin haka, yana son yi mata magana Amman yayi shr    ,yayinda  zuciyarsa ke kwabarsa akan ya share kawai ai baita kadai bace mace a duniya" daman ai dan ita yake son ya aure zeenat din ,da yaje waje ya aure wata wacce bai san halinta na boye ba ai gara zeenat din Amman tunda  bata so shima ya hakura .



Da misalin karfe goma na dare DEENi sanye da rigar wanka dan fitawarsa kennan daga bathroom ,ya tsaya gaban dress mirrow yana karewa jikinsa hade da  zare rigar wanka dake jikinsa" ya saura  daga shi sai boxer   , yabi koina a jikinsa da turaren Hamilton 27, sai daya kammala da  komai na al'adarsa da yasaba yi kafin ya kwanta   sannan ya hau kan royal bed din ya lumshe rikitattun idanunshi, alamun yana son yayi bacci' sai dai baccin yaki zuwa  kawai ya tsinci kansa da tunanin zeenat.ya rinka jinta ajikinsa , yadda yake jinta a halin yanzu bai tsammaci abin har ya zai  haka ba ,,

Sosai ya tsinci kansa cikin damuwa ko baya son yarinyar hakika ya tsananta da son aurenta yayi shr yana tambayar kansa abinda ummi take nufi da kin amincewa datayi,shi  ya guji big dady da  maganar a tunaninsa sai umminsa tafi kowa murna da jin dadi 'ya dauki tsawon lokacin kwance kafin bacci barawo yayi gaba dashi .


Byn kwanaki , DEENi yakasa hakuri da maganar zeenat din kmr yadda yaso shima ta share da zance kawai  ya manta dasu "

 Amman yakasa, ya samu ummi da kansa a wata safiya dayazo gaisheta byn yayi shirinsa na zuwa aiki cikin kakinsa dake kara masa kyau tamkar dan shi kadai akayi" sai kamshin yake zubawa ta koina "gashin kan nan nasa kwance luf luf luf dasu , duk da bacika yawa sukayi ba ,saboda yanayin aiki "Amman dayake Allah yayi mishi suma  takoina ajikinsa ko yayi askin ma baya wani dadewa" gashin zai sake fitowa" sosai yayi  kyau  matuka ,ita kanta ummi satar kallonsa take har ya tagota ya sakar mata murmushi tace son kayi kyau sosai fa, uniform din nan  nakara maka kyau ,ya dage mata girarsa daya yace Allah first lov  yace ai daman can nj  may kyau ne   sannan duk maccen datayi dacen samuna , ta gama samun duniyarta  sai dai ta nemi lahirarta kawai " ummi tayi dariya sosai ya kamo hannun umminsa cikin nasa muryasa a shagwabe hade da dan karyar da wuyansa, yace first lov  da kanki ma kin yaba dani "tace uhmm  yabon gwani yazama dole "yace to meyasa bazaki bani auren zeenat ba ? 

Ta lissafomasa dalilinta kmr yadda ta sanarwa Muhammad ta Kuma sake jaddada masa yaje gaba ya nemi mata Amman banda diyarta ranshi ya baci Amman ya share take Yar fara'a dake fuskarsa  ta dauke "  sai dai bai nuna ba , cikin sanyi murya yace to Shikenan ummi na hakura" Amman bazan taba zuwa koina neman aure ba" saboda banida nagartar  daza'a soni Kuma  bani aure"  ummi tace ba fa haka nake nufi ba yace haka ne mana first lov" ina da munanan halayen da ban cancanci abani mata aure  ba. ummi tayi murmushi tace nifa bance haka ba yace haba first lov kince mana  gashin nan kema da kanki kin hanani taki Yar , to waye zai amince yabani yana kaiwa nan ya cire hannun umminsa cikin nasa ya mike cikin sanyi jiki tamkar bai damu ba ,.

gabadaya jikin ummi yayi tsanyi ita bawai auren ne bata so ba halinsa take gudu ta yaya zata yarda ta aura masa marainiyar Allah yazo yana cutar mata da yarinya .


Abin mamaki duk a tunanin DEENi na bazai shiga damuwa ba akan kin amincewar ummi ,

sai gashi dumu dumu cikin tashin hankali kullun sai yayiwa umminsa naci da magiya akan tabashi auren zeenat ,ita kuwa ummi duk lokacin dataga ya dauko mata zance sai share hade da bata fuska  .




Please kumin uziri , may be zaku dan jini shiri sakamakon matsalar rashin wuta naso narinka muku type akai akai batare da westing time ba Amman kuyi hakuri ana kyawun tare🤝🏻🤝🏻




MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗

  AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 9-10



Zeenat kwance a  bedroom din ummi hannuta rike da  wani English novel   face to face tayi zurfi cikin karatun novel din saboda yadda  take enjoy din novel din ya .


Yaya DEENI ne yashigo gaishe da ummi    kafin yafita aiki  ,byn sun gaisa ne ummi  tace har ka shirya   fita kennan ? Yace mata eh sannan yaja ya tsaya yayi  shr ya zubawa ummi idanunshi .

ummi ta dubeshi tace da magana ne ?   Tunda tarigada tasan muddin yayi shr irin haka to da magana a bakinsa.


 koda yake tasan dai zance nasa bai wuce maganar zeenat bane " Kuma daman tana son zeenat din tajima kunneta idan ta amince ruwanta "

dan haka ummi kalleshi da kyau tana nazarinsa ta numfasa sannan tace masa kayi shr alhalin nasan da magana abakinka   .

, muryasa a shagwabe yace first lov kan dai maganar zeenat ne ,dan Allah first lov, ba yabon kai ba  "ina da qualities  din da za'a bani auren  kowace irin mata nake so" Kuma ko Yar gidan waye ,.

Yar taki ma daba wani kyau ne daita ba" dan ma zan taimaka mata "ya fadi haka fuskarsa a hade ,.


ummi tace duk da haka day bazan bada diyata ba kaje waje ka gwada sa'a r ka" wai ma in tambayeka DEENi yamaida hankalinsa sosai  ga umminsa" tace   kai da kake ta damun kanka da zance nan  kullum. kasamu ita yarinya da maganar ,kun daidaita kanku  ne ? 

DEENI yace uhmm kece dai zaki sanar mata, ummi ta nuna kanta  da dan yatsanta,  nice ma zan tayaka  yakin nemar maka soyayyarta" lallai ma bason auren nata kakeyi ba"  kashare zance kawai tunda baka shiriya neman aure ba. yace to ni first lov in na fada   sai  naga tamkar Raina ne zatayi, ummi tace kunji girman kan ba  a hassale ummi tace dan Allah kayi hakuri kabar zance nan. haba duk kabi katadda hankalinka da nawa. yarda ne dai bazanyi .

dan haka   kayi hakuri kabar zancen nan kwata kwata dan ba yarda zanyi ba .


DEENI daya gaji  dayiwa ummi magiya ya hakura ya ficewarsa ,yana jin takaici kansa, tunda daga lokacin da zeenat taji DEENi ya ambaci sunanta ta mike zubur zaune daga kwanciyar datayi, hankalinta a tashe jikinta har rawa yake tsabar rudewa"   ita zeenat din yaya DEENi  yake nufi ko wata daban.

 ahankali ta furta in ko ita yake nufi dakuwa ta more a rayuwarta, dan gaskiya  yaya DEENi ba irin namijin da mace zatace bataso bane , ahankali ta sake furta A'a dan Allah ummi kada kimin bakinciki mana.


 tana jin fitarsa ta fito da sauri daga dakin tana kallon ummi dake zaune tana jan carbi,  zatonta ko ummi zata mata maganar ne. Amman sai taga sabanin haka .

  dan kuwa ummi  ko kallon inda zeena take tsaye batayi ba.

 dan tarigada tasan taji komai" to Kuma bayanin me zata tsaya yi mata. Ta dai yi shr ne  taga yadda zata dauki lamarin .

Can kuma, ummi ta dago tana duban zeenat din tana nazarinta" yayinda zeenat din itama ummi take kallo" har zuwa lokacin  ummi batace komai ba .

sai ma  kau da kanta gefe datayi  , ganin ummi bada niyyar ce mata komai  ,yasa zeenat kira sunan ummi"  ta juyo tana duban zeenat din da kyau".

 ahankali cikin sanyi murya tace ummi wai wata zeenat din yaya DEENi keso ?

Ummi ta dan tabe baki sannan tace dan Allah rabu dashi  wai ke yake nufi "da sauri zeenat tasa hannuwanta duka ta dafe kirjinta dasu tana zaro idanu waje "tace  da gaske  ni yake so ?

ummi tace zan miki karya ne"  zeenat ta marairaice murya tace shine Kuma ummi zakice  masa baki yarda ba.


 ummi tace to may kike nufi ,kina son kice min kina son DEENi kennan ? Zeenat Tayi shr dan bata da amsar bawa ummi dan  gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bai dauki rawa ba.

 ummi ta sake yin magana daman kina son DEENi ne naga duk kin tada hankalinki  haka ?zeenat tace nifa bance ina son shi ba Amman ke meyasa zakice A'a Kuma ma mayye dalilin dayasa kika ki amincewa ,ummi tace ok tutseni zakiyi" kan naki yarda ko yaya , zeenat tace ba haka bane" ummi tace tsaya ma kiji  abinda yasa naki yarda, DEENi "da" nane' ni haife shi da cikina sannan ke ma kinsa halinsa sarai da shege miskilanci da saurin jin haushi  mutun ,abu kankani ke hassalashi ga tarin  girman kan tsiya, zeenat ta tsugunna nan gaban ummi  hade kamo hannuwan ummi  duka cikin nata muryarta sanyaye tace  haba  ummi dan day kawai saboda wannan halin nasa ne "zai sa kike amincewa  , in dai dan haka ne' ni na amince da aurensa  kinji .

ummi tace duk kinbi kin koma kalar tausayi wai ma  meyye birgeki   da DEENi  ne naga duk jikinki ya dauki  rawa haka ?.

 Zeenat tace ai gaskiya yaya ba irin mutunmin da za'a tsaya cewa ba,aso bane ni dai na amince ,ummi tace ko kin amince, ni nace A'a ban yarda ba ,.


Zeenat ta mike  cikin fushi tayi bedroom din ummi .

da kallo ummi tabi bayanta dashi ummi taji matukar mamakin ganin reaction dinta musamman da tasan zeenat din ,bata fiyye nuna fushinta akan abu ba .


Koda tashiga dakin ma waje tasamu ta zauna abunta tayi tagumi batayi aune ba, kawai taji  hawaye na silalowa mata.

 ita kanta tasha mamakin ganin hawayen  na zuba a idanunta "ta tambayi kanta  to  daman can tana son DEENI ko yaya? domin abun itama yayi maseefar  daure mata kai ".

kuka takeyi " iya karfinta hade da ganin laifin ummi din ,to meyyesa ummi zatace batason aurenta da ya'ya DEENi  byn ita tasha kisma haka a ranta .

taci  kukanta sosai har sai da taji alamun kanta ya fara mata ciwo ta runtse idanunta  sannan ta kwanta "nan a gefen   bed din ummi tacigaba rera kukanta kasa kasa .


Yinin  ranar tayi shi ne cikin daki hade da  tunanin  DEENi  da kitsima kalar    rayuwar da zatayi a gidan DEENi.

 Da zarar taga  ummi kuwa  take hade fuskarta saboda jin haushin abinda tayi " .

kusan zuwa Maryam uku gidan "Amman zeenat taki saukowa kasa" dan gabadaya takasa samun  sukuni  gabadaya haushin kowa take ji.

,ita kuwa ummi sai binta take da idanu dan ma kasa magana tayi ,  gashi  ranar Sam DEENi ma kin dawowa yayi da wuri sai wajen shabiyu , .



haka ma washegari tun asubar fari yabar gida  ya dai shigo ya gaida umminsa a tsaitsaye.


 ,byn ummi ta idar da sallah ne kafin ta soma lazimi ,  yayinda zeenat ke kwance akan bed , idanunta a runtse tamkar  may  bacci Amman Kuma ba  baccin take ba .

ummi takira sunanta kusan sau uku Amman tayi mata shr alhalin tana jinta.

 ummi ta sake kiran sunanta  tace zeenat nasan kina jina Kuma idanunki biyu Amman kika min banza , hade da ganin laifina .

bakomai yasa kika ga naki yarda da maganarki da DEENi  ba" nasan halin DEENi ciki da bai bashida dadin sha'ani kwata kwata gashi da bakar zuciya tsiya azo ayi auren nan yazo yana  gana miki azaba, .


ni.. nasan abinda nake gudar miki Amman inda kinkiji  ke kika sani , kije Allah yabada sa'a .

Amman ki sani idan akwai wanda zai ji dadin aurenki da DEENi a bayana yake, Amman duk da hakan bazai hanani fadar gaskiya ba idan tazo.

 Kuma shawarata gareki ki rage rawar kai dan idan ya  fahimci haka  zaki sha wulakancin, da karshe  km mutuncinki ya zube a gurinsa.


 ga zaton ummi  zata ji zeenat din tace ta hakura da auren DEENi din ne  Amman sai ganinta tayi ta duro daga kan gado ta zube gabanta  durkushe.

 , taji tace idan dai har kin amince ummi  inshallahu bbu abinda zai faru .


Ummi tayi shr ta tsura mata idanu tana kallonta  ummi tace kina nufin kin amince zaki auri DEENi kennan ? Zeenat tayi shi shr  takasa cewa komai ba sai karyar da wuya datayi , ummi ta sake duban  tace ke..bafa zan yarda da auren nan ba  . take zeenat ta fashe da wani irin  kuka tana bawa ummi hakuri ta amince dan Allah abin ma ya daina bawa ummi mamaki , yadawo bata  tsoro ,.

Cikin kuka  zeenat ,tace ai shi yace yana sona " to ta yaya ke zakice A'a ummi tabita da wani irin kallo tausayi , aranta kuma  tace ya'yan yanzu sam basu da kunya   . wani irin son zeenat din ne taji yana  ratsa ko wani part  na jikinta.

 ga tarin tausayin yarinyar dake matukar damunta ,Amman hakan ba zai sa taji zata iya amincewa da muradinsu ba .

 ta kau da tausayin yarinyar a ranta ta hade fuskarta tamau ,sannan  tace ke dan ubanki akan na hana aurenki DEENi ne zaki ,ta sani gaba da kuka "dan bakisan ciwon kakin ba  ,danma ke shashace ko shi dayace yana son naki" bawai damuwa yayi dake ba.

 tunda har  zuwa yanzu bai kawo kansa gareki ba.

   sai kece zaki wani damu mutane  da kuka akanshi ,cikin wani irin sabon kukan zeenat tace bagashi ke yayi miki maganar ba .

Ummi tace  OK dan yayi min maganar shine may . ni zai aura ko ke  ,da kyar ta iya sausauta kukanta sannan tace ummi  dan Allah  ki amince mana  tunda day har shi ya furta da kanshi".

 ummi taja tsaki ta mike  tsaye tace ni masa, ban waje tun banyi ball dake ba shashar bazan kawai.ta wuce parlour 

tavarta zeenat nan durkushe.

 aiko zeenat naganin haka ta fashe da wani kukan har da shesheka .


Da daddare misalin karfe tara ,DEENi zaune a parlour shida ummi  suna kallo Amman jifa jifa take sako masa  hirar duniya "    shi dai  jinta kawai yake , yayi tamkar bbu abinda ke damunsa Amman shi kadai yasan abinda yake ji aransa' zeenat ta hado masa coffee   tazo har inda yake zaune ta ajiye masa nan kusa dashi ta juya zata bar gurin  ko kallo bata ishe shi ba ballanantana yasan ko ita wacce, hakan da yayi  ne yasa  ummi  taji ba'adadi  aranta . muryasa a kwasashe yace ke.....ta juyo ahankali hade da zuba masa idanunta  shima ita yake kallo da ritattun idanunsa ,yace dawo ki dauki abinki  konace miki  ina bukatane" da sauri  ta zeenat ta girgiza kai, ya kau fuskarsa kmr bashi yayi maganar ba .

 bai sake cewa komai ba ,km  bai  kalli inda ummi ke zaune ba, ya mike kan three site yayi kwanciyarsa " aransa yace akanki zan dinga huci  takaici abinda ummi tamin" tunda tace bazata auramin ke ba.

 nima na hakura da auren naki" sai ta jikaki tay tasha .

kunya ne  hade da tsoro suka taru sukama zeenat rubdugu , taji gabadaya kakafunta sun Gaza daukarta "  ana cikin haka shemah tashigo da sallamarta "kai tsaye wajen ummi ta nufa ta zauna tana gaishe da ummi "ta amsata cikin sakin fuska , .

,sai sannan ta juyo tana kallon  inda zeenat ke tsaye kikam  tamkar an dasata' km sai a lokacin idanun shemah yaKai ga DEENi,dake kwance idanunshi a lumshe.  itama idanu ta zuba masa tana kallonsa  , tana jin wani irin ajikinta  yayinda  gefe daya zuciyarta ke wani irin dokawa da sau da sauri "  shi  km kwata kwata   bai  ma san Allah yayi ruwan mutun  a gurinba " ahankali ya mike  tsaye yana wa ummi sai da safe "a ciki ta amsa masa  dan takaici abinda yayiwa zeenat  " suna hada ido da ummi yasakar mata murmushin gefen baki hade da yakashe mata idanunsa daya  wanda ita kadai tagani   "  da sauri ya haye step  ,.

 yana barin wajen atare suka sauke ajiyar zuciya daga zeenat din har shemah " .

dan har gara shemah ma akan  zeenat din dan ita gabadaya a frigice take "idanunta ta dan juya da niyar satar kallon inda  ummi take  , ai ko take suka hada ido daita ummi kalli zeenat din tana watsa mata harara dan gabadaya tagama  bata haushi .


yana shiga  dakinsa ya fada kan bed dinsa ya jawo system dinsa kennan idanunsa yaKai ga phone dinshi  dayaga almost 12 miss cul da sauri  yasa hannu ya dauki wayar yayi dealing number  daya Gani bugu daya biyu "fk ya dauka   yace ka kyauta angon zeenat"  bukatarka ,ta biya ai dole  kashare mutane. DEENi yaja tsaki mtssss sannan  yace dan Allah  ni rabani da wannan zancen naka na banza" haka kurum kasa mutun a one chance,.

gashi   kaja wa mutun  wulakancin kawai ,fk yace wulakancin Kuma a gurinwa DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa sannan yace a gurin ummi mana.

 to meyya faru inji cewar fk.

 sai da DEENi ya jima  bai yi magana ba kafin daga baya ,yaja wani irin  numfashi  yace ummi fa taki amincewa da shawarka ,sai ma  wani yawo ake min da hankali kmr za'a bani gold.

 fk ya kwashe da dariya yace mutumina kodai ka zurma ne, irin wannan jin haushi haka.

  DEENi yace kai nifa na hakura da yarinyar nan wlh  ,dan gaskiya bazan jura wannan wulakancin ba  .

ga mata nan dayawa a waje suna bina kmr su lashe ne "  fk yace tsaya ranka ya dade ba haka za'a yi ba, bari zamu samu big dady da zance nasan komai zaizo da sauki .

ko Kuma kai me zai hana kasa zeenat din da kanka.

   DEENi ya sake jan tsaki yace maganar bazan  kennan ai inda takaicin yake kennan haba ai kauyancine a wajena    na tsaya  ina gayawa wannan yar karamar yarinyar kalmar  so .

fk yace kaji irin ta ko kana son yarinya Amman girman kanka na neman cutar dakai "DEENi ya katseshi " hade da cewa kai fa dan matsala ne , nasha gaya maka ka daina cewa ina son yarinyar nan, zan dai aureta ne kawai  fk yace Shikenan ajiye wannan zance.

 bari gobe  inshaallahu zanzo muje gurin big dady DEENi baice komai ba ya katse wayarsa .




MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗

  AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 11-12



Washegari bai tashi da wuri ba sai wajejen shabiyu na safe yatashi. yashiga, bathroom byn ya fito ne yayi tsaye gaban mirrow yana kallon every part of him ,tsawon lokacin yana tsaye yana kallon kansa ta mirrow kafin daga baya ya janyo wata karamar   stood dake gefe  ya zauna . 

hannushi ya dora a saman fadaden kirjinsa yana shafa kwantaccen gashin kirjinsa  hade da lumshe idanunsa "shi kansa yasan duk matar data mallakesa  matsayin mijinta bakaramin Lucky Tayi ba .


cikin sanyi jiki tamkar macce yasoma    shafe jikinsa da body lotion "  DEENi na kashewa kanshi kudi fiyye da tunanin may karatu , 

 mikewa yayi cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufi cikin bedroom din shi dan saka kayan " har  ya nufi kofar dazata kaishi parlour" sai ya tuna ana jiransa dan haka yaja  tsaki  mtssss sannan ya nufe kofar bedroom dinshi  byn yashige tare da cewa koma waye zai tafi idan yagaji da zama dan yanzu baida lokacin kowa  .



Shiryawa yayi cikin wasu hadadun kananan kaya wando blue jeans da  riga longslive" wani irin kyau Allah yayi masa na daukar hankali"  ya isa kan durowa ya kwashi wayoyinsa ya zuba cikin aljihun wandonsa "ya sanya takalmansa mai sawun ciki  ya zura hannushi daya  cikin dayan aljihun .



Shemah ce zaune  a parlour DEENi  take  zaman jiransa "wacce     tun karfe  tara na safiyar ranar   ta dako samamko son ganin DEENI din.


  da farko bedroom din ummi ta nufa , sanin datayi dole zai shigo gurin ummi ,ganin har ummi tagama abinda take  tadawo main  parlour dinta yasa itama tabiyo bayanta , .

Ganin tagaji da zama   kusan 1 hour tana  zaune  zaman jiransa  Amman bata ga alamun. fitowarsa ba  yasa tacewa ummi dan Allah takira mata shi .


 Ummi takirasa  tasanar dashi bai ce  da ummi  komai ba dan kusan  da haushi yatashi . Ita Kuma ganin yayi shr yasa tace mata taje part dinsa .



Koda ya yafito falonsa yaga mutun zaune shi duk tunaninsa FK ne ko cikin abokan aikinsa kallo daya Yayi mata ya dauke idanunsa daga kanta "yi yayi tamkar bai ganta  ya nufi hanyar fita. ta taso da sauri tana kiran sunanshi " cigaba yayi da tafiyarsa danshi a ganinsa bai ga abinda zai sa ya tsaya ba ,.

 ganin saurin bazai mata ba , dan  haka ta kara da dan  gudu da sassarfa har ta cimmasa  ,a  daidai cona da zata kai mutun main parlour din gidan tasha gabansa da sauri  tana sauke ajiyar zuciya hade da cewa dan Allah yaya katsaya magana nake son yi dakai .

 dubanta yayi tamkar bazaiyi magana  sai Kuma yace  meyye matsalarki dani ? Dan ji Yayi kmr ya dauketa da maruka " Kalmar daya fada ne yasa taji zuciyarta ta tsinke "  Tayi wani irin tsalle kmr zata tafasa kirjinta ,.

Tayi shiru tana tattaro kalmar dazatayi amfani  wajen fahimtar dashi abinda ke ranta . 

  cikin sanyi murya yace ina zaton kin manta ko ni wanene shiyasa kika tareni , sai da  ta saita kanta sosai, ta'aro jarumta takara akan wanda take da"  sannan tasamu kwarin gwiwa. cikin marairaicewa murya irin ta masu neman taimako tace dan Allah yaya" kadan bani aron  lokacin uziri ne dani.

 yamata wani irin duban dayasa yanhanji cikinta kadawa sannan yace uhmm ina jinki kuma ki tabbatar da uzirinnaki mai ma'ana ne .

"da idanunta ta amsa masa dan gabadaya  ilahirin jikinta  kirma yake tsabar rudewa datayi har wani gumi take fitarwa na wahala.

 tun ba yau  ba DEENi  yasan shemah nason furta wani abu gareshi Amman rashin ganin fuskarsa yasa taki tunkarsa shi bema san dalilinsa na tsayawa ba  .

 Shi kansa yasan  dole wannan ranar zata zo komai daren dadewa  ".


 ahankali take sauke ajiyar zuciya saboda fargaban da tashin hankali , abinda  zai biyo baya " numfashi taja hade dayin   kasa da kanta dan sam bazata iya kallon kwayar idanunshi a wannan lokacin .

Ahankali    tasoma magana muryata  kasa kasa  cikin in...inna ,tace  daman ..daman..ina son sanar dakai   " ina..ina so.....da hannushi ya dakatar  daita" tun bata kai ga karasa maganarta ba  tare da buga mata wata irin razananniyar  tsawa  wanda yasa ba shemah ba ,har zeenat dake kokarin  fitowa daga dakin ummi zuwa parlour "ta   koma cikin daki da sauri " ta manne da jikin kofar  hade da cewa wayyo... Allahna me Kuma yasame sa  haka cikin tashin hankali ta sake mannewa da jikin kofar .   , hatta ummi dake zaune a falo  say da taji amon muryasa  ,wani irin kallo yake jifarta dashi   yace kina.... me uhmm repeat what u say   ,  lip's dinshi  cikin bakinsa yana cizawa sannna yace  what ar u try to  say ,ya sake jiho mata wata  tambaya, still shr kake jin shemah  ba bakin magana Amman gabadaya ilahirin jikinta ya dauki kirma .

 Cikin isa da takama yace u better keep what'ever you won't say before I sikater you now  jikin  shemah yacigaba   rawa kafafuwanta suka Gaza daukarta dana sani kuwa tayishi yafi cikin buhu ,  ya tsareta da mayatattun idanunsa " murya a kwasashe yace     na sake jin kin Kuma furtamin  wannan bazar kalmar wlh azim  zakiga yadda zanyi da namanki stupid girl kawai.

 ya ja tsaki  ya wuce abinsa ta tsaya nan tana bin bayansa da kallo  ranta a bace  batasan lokacin da Hawaye yasoma zubo mata   tana tunanin yaushe ne zata daina kuka akan son DEENi mutumin da take matukar so tamkar ranta  mutumin da mata ke rububin son shi  mutumin dayake jama mata aji ga shegen kyau da kwarjini " nan ta zube kasa  ta risgar kuka  ahankali hade da sa hunnta duka ta toshe bakinta dasu .


Zeenat dake tsaye jikin byn kofar  dakin ,banda kirma  bbu abinda jikinta keyi , tsabar frigice jin abinda shemah ke kokarin yi' domin taji  duk abinda ya faru tsakanin yaya DEENi da shemah tsabar  tsoro ne ya hanata fitowa ,wani irin kishi ne taji yana taso mata tun daga kan tsintsiyar kafarta  yana bin ilahirin jikinta hade da kashe mata duk wani  gabobin dake jikinta ,  taji a ranta  da tana iya fitowa,. tabbas  da ita kadai tasan  yadda zatayi da shemah, tsinuwa kuwa iri iri  bbu wanda zeenat bata aikawa shemah ba .


 , ahankali zeenat ta sulale   kasa ta dora hannuwanta duka bisa kanta.cikin kuka take cewa  Shikenan ummi tacuce ni  zata kai ni  tabaro "gashi taki yarda da aurena ,da yaya DEENi ga wasu can suna neman   farautarsa .

,ba tasan tana shirin jefa diyarta cikin halaka bane akan tilon danta.

  dan ita yanzu ji take zata iya yin komai akan DEENI  .

Ahankali  Tace ita yanzu yazatayi da ranta , idan Kuma  yace hakura daita fa ?  Taji gabanta fadi 

Da sauri tasoma girgiza kanta tace hakan ma  bazai taba faruwa  ba inshallahu sai ta aure yaya DEENi  mijinta ne ita kadai , .

dan ita yanzu wani irin son DEENi din ne yashigeta na  farat daya ,kmr kar taji ya furta yana sonta ...itama  taji tana maseefar kaunarsa ,  Ita taji ta Gani zata iya rayuwa dashi  akowani irin  hali.

 kawai,a hankali ta sake  ta saki  wani irin  marayar kuka mai ban tausayi  tana furta ummi karkimin haka dan Allah  ..kar min haka ummi ke uwace gareni har da rabi .

dan Allah karki rabani yaya DEENi  wlh zan iya zama dashi a haka , duk munin halinsa ina son shi  " tunda harshi  ne ya furta yana sona ...

 gabadaya  ta rikece da wani sabon  kuka tana sambatu .

 kuka tayi sosai har da shesheka ahankali ta sauko da hannuta bisa kirjinta" ta dafe kirjinta dataji yana mata  wani irin ciwo zuciyarta na  dokowa da sauri da sauri  zeenat ta runtse idanunta dan ita kadai tasan yadda take ji.....


  ta ciki  dakin zeenat ke rizgar  nata kukan ,yayinda shemah da ke  waje durkushe ta nata   .



 Taku yake cikin izza da jin kai da jin shi wani ne yake takunsa har yakaraso ya zauna kujerar da umminsa ke zaune ya dora kansa kan cinyarta "ita Kuma ta'ajiye jaridar dake hannuta tun  soma jin amon muryasa ta daina karatu  datake "ya sakar mata murmushi  gafen baki tamkar bbu abinda ke damunsa ,yace gud morning my first lov ....

ta daura hannuta bisa sumar kansa tare da fadin morning my son yakatashi lfy , ya dan tabe baki sannan yace nut bad  ....

 tace ya'akayi ne son  me kakeson cine akwai dinshi iri iri akan darning wanda   orready zeenat tashirya komai  .

 turo baki yayi cike shagwaba har zaiyi magana " kome ya tuna sai Kuma ya fasa cewa komai " ummi ta tsurawa fusharshi idanu tace kayi shr ya lumshe idanunsa  muje kayi breakfast din ina lura da kai tunda kasoma zancen yarinyar nan bakason zama  ma a gidan  ballanantana Kaci abinci  ahankali ya ware idanunshi akan umminsa sannan yace first lov  na koshi fita ma zanyi yanzu ....


Post a Comment

0 Comments