AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 7-8
Har DEENi yazo gida tunanin yake akan shawarar da fk ya bashi" anya kuwa zai iya amince da auren zeenat ?
Lokacin da yashigo yayi daidai da zeenat ta tabare magani tana mikawa ummi ,ta amsa ta apa zeenat ta Mika mata ruwa ,yayinda shi km yake tsaye jingine da jikin kofa rungume da hannuwansa duka a kirjinsa yana kallonsu, take zuciyarsa ta dinga ingizashi akan lallai bbu wace ta dace ya aura sama da zeenat bisa ga hujarsa tacewa ,bazai taba samun matsala daita gurin kula da mahaifinsa saboda irin soyayyar dake tsakaninsu "
yasan ko yana nan ko baya nan zata kula daita, umminsa zata zamo a karkashin kukawarta tunda zeenat bata da wata uwar da wuce ummi tunaninsa ya katse lokacin da ummi takira sunansa' tace son karaso mana yayi frigigit ya dawo natsuwarsa ahankali yashiga takowa har inda ummi take ,ya zauna zeenat ta gaidashi ta mike zata fice daga dakin bai amsa mata gaisuwar data masa sai dai yabi bayanta da kallo" ummi ta kalleshi ta kauda kanta, yace first lov yajikin naki ummi ta danyi murmushi hade daura hannuta kan sumar kansa tace naji sauki sosai , ahankali sauke ajiyar zuciya ko bai ce komai ummi ta fahimci yaji dadin yadda yaganta ,yana nan zaune , Sam yakasa yiwa ummi zance yana ya auren zeenat din ,daga karshe ma tunani yayi kawai gara yasamu ya mahamud da zance dan gaskiya kunya yake ji yayiwa ummi maganar da kansa .
Da yammacin ranar byn ya dawo daga office yaje har gida yasamu ya mahamud da maganar ya ji dadi kwarai da gaske, har yarasa inda zai sa DEENi dan farinciki dan shima da kansa ya matsu yaga DEENi ya ajiye iyali kmr kowani magidanci , yace Shikenan sai kasamu yarinyar da zance, ku daidaita kanku DEENi yace A'a ina ganin basai na sameta ba in dai first lov ta amince ai Shikenan .
yaya mahamud yace ummi bazata taki ba Amman dai kasan kaidar auren gidanmu kennan bbu dole a ciki "muddin kuka daidaita kanku na iyayenmu may sauki ne idan Kuma ita ummi ta amince ita yarinyar tace bata sonka fa? DEENi yaji haushi da takaici sunkamasa alokaci guda yace ai nima ba wai ina sonta bane kawai dai zan aureta ne.
Yaya mahamud yace shirme bazan kennan kai yanzu idan anzo meeting cewa zakayi basonta kake yi ba ,zadai ka aureta ne ?DEENi yayi murmushin gefen baki har dimple dinsa ya lotsa sannan yace cewa kurum zanyi ina son zan aure zeenat ne ' Yaya mahamud yace to Allah ya mana zabi na alkhari kabari zanje gurin ummi tukun duk yadda mukayi daita zakaji DEENi yace Shikenan ya mike fice ,a office ma koda yaje aikinsa kawai yasa gaba .
dan shi gabadaya ya manta da wani zance aure can .
Mahamud yasamu ummi cike da karfin gwiwa" ganinsa ba wanda zai kai ummi murna tunda daman burinta kennan naganin auren DEENi, Amman ga mamakinsa yana gama labarta mata abinda yakawo shi, sai yaga ummi tayi kicin kicni da ranta tamkar bata taba sanin wani abu farinciki ba "sai da gaban Yaya mahamud ya fadi dan ganin yadda ummi tayi da fuska tamkar yazo mata da zance mugun abu " tace kai ne kaga sun dace kaba shi shawara ya nemi aurenta ko Kuma shi da kansa ya sameka da zance ?
Da sauri yaya mahamud yace A'a shine dai yazo min da zance ummi ta sake daure fuska, sannan tace ka koma ka fada masa ban amince ba ,kace masa akwai sauran mata a gidan nan yana da damar zabar duk wacce tayi masa, idan ma ya canza ra,ayinsa nakin auren family' to yaje waje ya nemi matarsa can itama Allah zai bata nata mijin, Amman Sam ni ban yarda da wannan hadin ba " tayi shiru na wani lokacin kana zubawa Mahmud idanunta tana kallon yanayin daya shiga ,ahankali ta numfasa sannan tace kana iya wucewa idan kana da abinyi ka manta da wannan shirme na DEENi .
Yaya mahamud yayi kasa da kansa Sosai cikin muryasa can kasa kasa da alamun km rarrashi yace dan Allah ummi ki amince da auren nan bazan iya tunkarar DEENi da maganar ba.
duk da bansa dalilinki nakin amincewa ba" ummi ta dan saki fuskanta ba kmr dazu ba tana mugun son mahamud tamkar dan da ta haifa acikinta tana jinsa har cikin zuciyarta .
tace bawai ina kin hadin bane duk duniya idan akwai wanda zai so auren DEENi da zeenat a bayana yake ,na farko dai kaima kasan halin DEENi da dan bazar zuciya , ga saurin fushi ga maseefar miskilanci tsiya ga jin kai sannan da bakinsa yasha gayamin cewar shi bazai taba yin auren family ba sannan shi mai digiri yake so ya aura ,shine km yanzu zai zowa mutane da wani salo.
ni da tawa iya secondary kadai ta tsaya" ai kai da jin zancensa ma kasan akwai wani makirci daya shirya "dan nace yayi aure ai bance lallai sai ya aure tawa yarinyar ba , Muhamud yace ummi ki duba lamarin abun tunda shi da kansa ya furta cewa ita ta masa ba za'a samu wata matsala ba ,.
ummi tace Sam bata yarda da wannan tsarin ba " ita dai yaje gaba ya nema hakurin duniya nan bbu wanda yaya Muhamud bai bawa ummi ba amman taki amincewa ,duk ta inda ya bullo mata sai itama tabiyo masa ta wata hanyar, har ran yaya mahamud yasoma baci ,yaji haushin abinda ummi tayi dan haka ya hakura ya fice ransa abace .
DEENi zaune a office dinsa ya dukufa wajen tura sakwanni a yanar gizo ,hankalinsa kwance yake bin komai daki daki , yaji daya daga cikin wayoyinsa ,daya ta dauki karar sauti mai dadi ,ya dauke idanunsa daga kallon system din yasa hannu ya dauki wayar yana dubawa ganin sunan dake yawo akan screen din ne" yasa yayi sauri dagawa yakara a kunnenshi hade da yin sallama" kana ina muryar Yaya mahamud yaji ta daki dodon kunnenshi cikin sanyi murya DEENi yace ina office yace ok idan katashi kabiyo inason ganinka sannan ya kashe wayar .
DEENi zaune a gaban Yaya mahamud kansa sunkuye a kasa yayinda idanunshi ke kallon zarazaran yatsun kafafunsa yana sauraron sakonshi da ummi tabayar a sanar dashi.
a gurin Yaya mahamud sam bai tsammaci jin haka daga umminsa ba ,ga mamakin Yaya mahamud sai yaji deeni yace Shikenan babu komai Allah yasa haka shine mafi alkhari .
ya mahamud yace ka hakura kennan? Nashi ganin bazai damu dan ummi ta hanashi auren zeenat , dan haka Yace eh "tunda daman ba wai yana sonta bane" nan dai suka bar zance aure suka shiga wata hirar daban a inda Yaya mahamud ya tashi yaje ya kwaso wasu takardu da file files ya zubesu nan a gaban DEENi yace yasa masa hannu ciki " kai tsaye DEENi ya zaro wani hadadden Biro daga gaban aljihun rigarsa yasoma cike gurraren da akeso yayi sign, dan gabadaya dukiyar DEENi , sulaiman da Muhamud ne akai su suke kula daita kuma komai na tafiya daidai " domin dukkannisu abu guda ne a gurin ummi dan ma idan ba'agaya maka ba…
zaka dauka duk ummi ce ta haife su .
Sai da DEENi yagama sign din ,sannan yaya mahamud hada da mishi bayanin companies din da suke son budewa a kasar American, sun turo musu da sako akan suna da bukatar mutun daya daga cikin masu company din " yazo interview dan haka shi ya wakilta sulaiman yaje , DEENi yayi murmushin yace Shikenan bbu komai duk yadda kukayi ,daidai ne Allah ya taimaka .
To byn DEENi yakoma gida ya dingawa ummi wani irin kallon, wanda shi kansa yakasa gane dalilin yin haka, yana son yi mata magana Amman yayi shr ,yayinda zuciyarsa ke kwabarsa akan ya share kawai ai baita kadai bace mace a duniya" daman ai dan ita yake son ya aure zeenat din ,da yaje waje ya aure wata wacce bai san halinta na boye ba ai gara zeenat din Amman tunda bata so shima ya hakura .
Da misalin karfe goma na dare DEENi sanye da rigar wanka dan fitawarsa kennan daga bathroom ,ya tsaya gaban dress mirrow yana karewa jikinsa hade da zare rigar wanka dake jikinsa" ya saura daga shi sai boxer , yabi koina a jikinsa da turaren Hamilton 27, sai daya kammala da komai na al'adarsa da yasaba yi kafin ya kwanta sannan ya hau kan royal bed din ya lumshe rikitattun idanunshi, alamun yana son yayi bacci' sai dai baccin yaki zuwa kawai ya tsinci kansa da tunanin zeenat.ya rinka jinta ajikinsa , yadda yake jinta a halin yanzu bai tsammaci abin har ya zai haka ba ,,
Sosai ya tsinci kansa cikin damuwa ko baya son yarinyar hakika ya tsananta da son aurenta yayi shr yana tambayar kansa abinda ummi take nufi da kin amincewa datayi,shi ya guji big dady da maganar a tunaninsa sai umminsa tafi kowa murna da jin dadi 'ya dauki tsawon lokacin kwance kafin bacci barawo yayi gaba dashi .
Byn kwanaki , DEENi yakasa hakuri da maganar zeenat din kmr yadda yaso shima ta share da zance kawai ya manta dasu "
Amman yakasa, ya samu ummi da kansa a wata safiya dayazo gaisheta byn yayi shirinsa na zuwa aiki cikin kakinsa dake kara masa kyau tamkar dan shi kadai akayi" sai kamshin yake zubawa ta koina "gashin kan nan nasa kwance luf luf luf dasu , duk da bacika yawa sukayi ba ,saboda yanayin aiki "Amman dayake Allah yayi mishi suma takoina ajikinsa ko yayi askin ma baya wani dadewa" gashin zai sake fitowa" sosai yayi kyau matuka ,ita kanta ummi satar kallonsa take har ya tagota ya sakar mata murmushi tace son kayi kyau sosai fa, uniform din nan nakara maka kyau ,ya dage mata girarsa daya yace Allah first lov yace ai daman can nj may kyau ne sannan duk maccen datayi dacen samuna , ta gama samun duniyarta sai dai ta nemi lahirarta kawai " ummi tayi dariya sosai ya kamo hannun umminsa cikin nasa muryasa a shagwabe hade da dan karyar da wuyansa, yace first lov da kanki ma kin yaba dani "tace uhmm yabon gwani yazama dole "yace to meyasa bazaki bani auren zeenat ba ?
Ta lissafomasa dalilinta kmr yadda ta sanarwa Muhammad ta Kuma sake jaddada masa yaje gaba ya nemi mata Amman banda diyarta ranshi ya baci Amman ya share take Yar fara'a dake fuskarsa ta dauke " sai dai bai nuna ba , cikin sanyi murya yace to Shikenan ummi na hakura" Amman bazan taba zuwa koina neman aure ba" saboda banida nagartar daza'a soni Kuma bani aure" ummi tace ba fa haka nake nufi ba yace haka ne mana first lov" ina da munanan halayen da ban cancanci abani mata aure ba. ummi tayi murmushi tace nifa bance haka ba yace haba first lov kince mana gashin nan kema da kanki kin hanani taki Yar , to waye zai amince yabani yana kaiwa nan ya cire hannun umminsa cikin nasa ya mike cikin sanyi jiki tamkar bai damu ba ,.
gabadaya jikin ummi yayi tsanyi ita bawai auren ne bata so ba halinsa take gudu ta yaya zata yarda ta aura masa marainiyar Allah yazo yana cutar mata da yarinya .
Abin mamaki duk a tunanin DEENi na bazai shiga damuwa ba akan kin amincewar ummi ,
sai gashi dumu dumu cikin tashin hankali kullun sai yayiwa umminsa naci da magiya akan tabashi auren zeenat ,ita kuwa ummi duk lokacin dataga ya dauko mata zance sai share hade da bata fuska .
Please kumin uziri , may be zaku dan jini shiri sakamakon matsalar rashin wuta naso narinka muku type akai akai batare da westing time ba Amman kuyi hakuri ana kyawun tare🤝🏻🤝🏻
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 9-10
Zeenat kwance a bedroom din ummi hannuta rike da wani English novel face to face tayi zurfi cikin karatun novel din saboda yadda take enjoy din novel din ya .
Yaya DEENI ne yashigo gaishe da ummi kafin yafita aiki ,byn sun gaisa ne ummi tace har ka shirya fita kennan ? Yace mata eh sannan yaja ya tsaya yayi shr ya zubawa ummi idanunshi .
ummi ta dubeshi tace da magana ne ? Tunda tarigada tasan muddin yayi shr irin haka to da magana a bakinsa.
koda yake tasan dai zance nasa bai wuce maganar zeenat bane " Kuma daman tana son zeenat din tajima kunneta idan ta amince ruwanta "
dan haka ummi kalleshi da kyau tana nazarinsa ta numfasa sannan tace masa kayi shr alhalin nasan da magana abakinka .
, muryasa a shagwabe yace first lov kan dai maganar zeenat ne ,dan Allah first lov, ba yabon kai ba "ina da qualities din da za'a bani auren kowace irin mata nake so" Kuma ko Yar gidan waye ,.
Yar taki ma daba wani kyau ne daita ba" dan ma zan taimaka mata "ya fadi haka fuskarsa a hade ,.
ummi tace duk da haka day bazan bada diyata ba kaje waje ka gwada sa'a r ka" wai ma in tambayeka DEENi yamaida hankalinsa sosai ga umminsa" tace kai da kake ta damun kanka da zance nan kullum. kasamu ita yarinya da maganar ,kun daidaita kanku ne ?
DEENI yace uhmm kece dai zaki sanar mata, ummi ta nuna kanta da dan yatsanta, nice ma zan tayaka yakin nemar maka soyayyarta" lallai ma bason auren nata kakeyi ba" kashare zance kawai tunda baka shiriya neman aure ba. yace to ni first lov in na fada sai naga tamkar Raina ne zatayi, ummi tace kunji girman kan ba a hassale ummi tace dan Allah kayi hakuri kabar zance nan. haba duk kabi katadda hankalinka da nawa. yarda ne dai bazanyi .
dan haka kayi hakuri kabar zancen nan kwata kwata dan ba yarda zanyi ba .
DEENI daya gaji dayiwa ummi magiya ya hakura ya ficewarsa ,yana jin takaici kansa, tunda daga lokacin da zeenat taji DEENi ya ambaci sunanta ta mike zubur zaune daga kwanciyar datayi, hankalinta a tashe jikinta har rawa yake tsabar rudewa" ita zeenat din yaya DEENi yake nufi ko wata daban.
ahankali ta furta in ko ita yake nufi dakuwa ta more a rayuwarta, dan gaskiya yaya DEENi ba irin namijin da mace zatace bataso bane , ahankali ta sake furta A'a dan Allah ummi kada kimin bakinciki mana.
tana jin fitarsa ta fito da sauri daga dakin tana kallon ummi dake zaune tana jan carbi, zatonta ko ummi zata mata maganar ne. Amman sai taga sabanin haka .
dan kuwa ummi ko kallon inda zeena take tsaye batayi ba.
dan tarigada tasan taji komai" to Kuma bayanin me zata tsaya yi mata. Ta dai yi shr ne taga yadda zata dauki lamarin .
Can kuma, ummi ta dago tana duban zeenat din tana nazarinta" yayinda zeenat din itama ummi take kallo" har zuwa lokacin ummi batace komai ba .
sai ma kau da kanta gefe datayi , ganin ummi bada niyyar ce mata komai ,yasa zeenat kira sunan ummi" ta juyo tana duban zeenat din da kyau".
ahankali cikin sanyi murya tace ummi wai wata zeenat din yaya DEENi keso ?
Ummi ta dan tabe baki sannan tace dan Allah rabu dashi wai ke yake nufi "da sauri zeenat tasa hannuwanta duka ta dafe kirjinta dasu tana zaro idanu waje "tace da gaske ni yake so ?
ummi tace zan miki karya ne" zeenat ta marairaice murya tace shine Kuma ummi zakice masa baki yarda ba.
ummi tace to may kike nufi ,kina son kice min kina son DEENi kennan ? Zeenat Tayi shr dan bata da amsar bawa ummi dan gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bai dauki rawa ba.
ummi ta sake yin magana daman kina son DEENi ne naga duk kin tada hankalinki haka ?zeenat tace nifa bance ina son shi ba Amman ke meyasa zakice A'a Kuma ma mayye dalilin dayasa kika ki amincewa ,ummi tace ok tutseni zakiyi" kan naki yarda ko yaya , zeenat tace ba haka bane" ummi tace tsaya ma kiji abinda yasa naki yarda, DEENi "da" nane' ni haife shi da cikina sannan ke ma kinsa halinsa sarai da shege miskilanci da saurin jin haushi mutun ,abu kankani ke hassalashi ga tarin girman kan tsiya, zeenat ta tsugunna nan gaban ummi hade kamo hannuwan ummi duka cikin nata muryarta sanyaye tace haba ummi dan day kawai saboda wannan halin nasa ne "zai sa kike amincewa , in dai dan haka ne' ni na amince da aurensa kinji .
ummi tace duk kinbi kin koma kalar tausayi wai ma meyye birgeki da DEENi ne naga duk jikinki ya dauki rawa haka ?.
Zeenat tace ai gaskiya yaya ba irin mutunmin da za'a tsaya cewa ba,aso bane ni dai na amince ,ummi tace ko kin amince, ni nace A'a ban yarda ba ,.
Zeenat ta mike cikin fushi tayi bedroom din ummi .
da kallo ummi tabi bayanta dashi ummi taji matukar mamakin ganin reaction dinta musamman da tasan zeenat din ,bata fiyye nuna fushinta akan abu ba .
Koda tashiga dakin ma waje tasamu ta zauna abunta tayi tagumi batayi aune ba, kawai taji hawaye na silalowa mata.
ita kanta tasha mamakin ganin hawayen na zuba a idanunta "ta tambayi kanta to daman can tana son DEENI ko yaya? domin abun itama yayi maseefar daure mata kai ".
kuka takeyi " iya karfinta hade da ganin laifin ummi din ,to meyyesa ummi zatace batason aurenta da ya'ya DEENi byn ita tasha kisma haka a ranta .
taci kukanta sosai har sai da taji alamun kanta ya fara mata ciwo ta runtse idanunta sannan ta kwanta "nan a gefen bed din ummi tacigaba rera kukanta kasa kasa .
Yinin ranar tayi shi ne cikin daki hade da tunanin DEENi da kitsima kalar rayuwar da zatayi a gidan DEENi.
Da zarar taga ummi kuwa take hade fuskarta saboda jin haushin abinda tayi " .
kusan zuwa Maryam uku gidan "Amman zeenat taki saukowa kasa" dan gabadaya takasa samun sukuni gabadaya haushin kowa take ji.
,ita kuwa ummi sai binta take da idanu dan ma kasa magana tayi , gashi ranar Sam DEENi ma kin dawowa yayi da wuri sai wajen shabiyu , .
haka ma washegari tun asubar fari yabar gida ya dai shigo ya gaida umminsa a tsaitsaye.
,byn ummi ta idar da sallah ne kafin ta soma lazimi , yayinda zeenat ke kwance akan bed , idanunta a runtse tamkar may bacci Amman Kuma ba baccin take ba .
ummi takira sunanta kusan sau uku Amman tayi mata shr alhalin tana jinta.
ummi ta sake kiran sunanta tace zeenat nasan kina jina Kuma idanunki biyu Amman kika min banza , hade da ganin laifina .
bakomai yasa kika ga naki yarda da maganarki da DEENi ba" nasan halin DEENi ciki da bai bashida dadin sha'ani kwata kwata gashi da bakar zuciya tsiya azo ayi auren nan yazo yana gana miki azaba, .
ni.. nasan abinda nake gudar miki Amman inda kinkiji ke kika sani , kije Allah yabada sa'a .
Amman ki sani idan akwai wanda zai ji dadin aurenki da DEENi a bayana yake, Amman duk da hakan bazai hanani fadar gaskiya ba idan tazo.
Kuma shawarata gareki ki rage rawar kai dan idan ya fahimci haka zaki sha wulakancin, da karshe km mutuncinki ya zube a gurinsa.
ga zaton ummi zata ji zeenat din tace ta hakura da auren DEENi din ne Amman sai ganinta tayi ta duro daga kan gado ta zube gabanta durkushe.
, taji tace idan dai har kin amince ummi inshallahu bbu abinda zai faru .
Ummi tayi shr ta tsura mata idanu tana kallonta ummi tace kina nufin kin amince zaki auri DEENi kennan ? Zeenat tayi shi shr takasa cewa komai ba sai karyar da wuya datayi , ummi ta sake duban tace ke..bafa zan yarda da auren nan ba . take zeenat ta fashe da wani irin kuka tana bawa ummi hakuri ta amince dan Allah abin ma ya daina bawa ummi mamaki , yadawo bata tsoro ,.
Cikin kuka zeenat ,tace ai shi yace yana sona " to ta yaya ke zakice A'a ummi tabita da wani irin kallo tausayi , aranta kuma tace ya'yan yanzu sam basu da kunya . wani irin son zeenat din ne taji yana ratsa ko wani part na jikinta.
ga tarin tausayin yarinyar dake matukar damunta ,Amman hakan ba zai sa taji zata iya amincewa da muradinsu ba .
ta kau da tausayin yarinyar a ranta ta hade fuskarta tamau ,sannan tace ke dan ubanki akan na hana aurenki DEENi ne zaki ,ta sani gaba da kuka "dan bakisan ciwon kakin ba ,danma ke shashace ko shi dayace yana son naki" bawai damuwa yayi dake ba.
tunda har zuwa yanzu bai kawo kansa gareki ba.
sai kece zaki wani damu mutane da kuka akanshi ,cikin wani irin sabon kukan zeenat tace bagashi ke yayi miki maganar ba .
Ummi tace OK dan yayi min maganar shine may . ni zai aura ko ke ,da kyar ta iya sausauta kukanta sannan tace ummi dan Allah ki amince mana tunda day har shi ya furta da kanshi".
ummi taja tsaki ta mike tsaye tace ni masa, ban waje tun banyi ball dake ba shashar bazan kawai.ta wuce parlour
tavarta zeenat nan durkushe.
aiko zeenat naganin haka ta fashe da wani kukan har da shesheka .
Da daddare misalin karfe tara ,DEENi zaune a parlour shida ummi suna kallo Amman jifa jifa take sako masa hirar duniya " shi dai jinta kawai yake , yayi tamkar bbu abinda ke damunsa Amman shi kadai yasan abinda yake ji aransa' zeenat ta hado masa coffee tazo har inda yake zaune ta ajiye masa nan kusa dashi ta juya zata bar gurin ko kallo bata ishe shi ba ballanantana yasan ko ita wacce, hakan da yayi ne yasa ummi taji ba'adadi aranta . muryasa a kwasashe yace ke.....ta juyo ahankali hade da zuba masa idanunta shima ita yake kallo da ritattun idanunsa ,yace dawo ki dauki abinki konace miki ina bukatane" da sauri ta zeenat ta girgiza kai, ya kau fuskarsa kmr bashi yayi maganar ba .
bai sake cewa komai ba ,km bai kalli inda ummi ke zaune ba, ya mike kan three site yayi kwanciyarsa " aransa yace akanki zan dinga huci takaici abinda ummi tamin" tunda tace bazata auramin ke ba.
nima na hakura da auren naki" sai ta jikaki tay tasha .
kunya ne hade da tsoro suka taru sukama zeenat rubdugu , taji gabadaya kakafunta sun Gaza daukarta " ana cikin haka shemah tashigo da sallamarta "kai tsaye wajen ummi ta nufa ta zauna tana gaishe da ummi "ta amsata cikin sakin fuska , .
,sai sannan ta juyo tana kallon inda zeenat ke tsaye kikam tamkar an dasata' km sai a lokacin idanun shemah yaKai ga DEENi,dake kwance idanunshi a lumshe. itama idanu ta zuba masa tana kallonsa , tana jin wani irin ajikinta yayinda gefe daya zuciyarta ke wani irin dokawa da sau da sauri " shi km kwata kwata bai ma san Allah yayi ruwan mutun a gurinba " ahankali ya mike tsaye yana wa ummi sai da safe "a ciki ta amsa masa dan takaici abinda yayiwa zeenat " suna hada ido da ummi yasakar mata murmushin gefen baki hade da yakashe mata idanunsa daya wanda ita kadai tagani " da sauri ya haye step ,.
yana barin wajen atare suka sauke ajiyar zuciya daga zeenat din har shemah " .
dan har gara shemah ma akan zeenat din dan ita gabadaya a frigice take "idanunta ta dan juya da niyar satar kallon inda ummi take , ai ko take suka hada ido daita ummi kalli zeenat din tana watsa mata harara dan gabadaya tagama bata haushi .
yana shiga dakinsa ya fada kan bed dinsa ya jawo system dinsa kennan idanunsa yaKai ga phone dinshi dayaga almost 12 miss cul da sauri yasa hannu ya dauki wayar yayi dealing number daya Gani bugu daya biyu "fk ya dauka yace ka kyauta angon zeenat" bukatarka ,ta biya ai dole kashare mutane. DEENi yaja tsaki mtssss sannan yace dan Allah ni rabani da wannan zancen naka na banza" haka kurum kasa mutun a one chance,.
gashi kaja wa mutun wulakancin kawai ,fk yace wulakancin Kuma a gurinwa DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa sannan yace a gurin ummi mana.
to meyya faru inji cewar fk.
sai da DEENi ya jima bai yi magana ba kafin daga baya ,yaja wani irin numfashi yace ummi fa taki amincewa da shawarka ,sai ma wani yawo ake min da hankali kmr za'a bani gold.
fk ya kwashe da dariya yace mutumina kodai ka zurma ne, irin wannan jin haushi haka.
DEENi yace kai nifa na hakura da yarinyar nan wlh ,dan gaskiya bazan jura wannan wulakancin ba .
ga mata nan dayawa a waje suna bina kmr su lashe ne " fk yace tsaya ranka ya dade ba haka za'a yi ba, bari zamu samu big dady da zance nasan komai zaizo da sauki .
ko Kuma kai me zai hana kasa zeenat din da kanka.
DEENi ya sake jan tsaki yace maganar bazan kennan ai inda takaicin yake kennan haba ai kauyancine a wajena na tsaya ina gayawa wannan yar karamar yarinyar kalmar so .
fk yace kaji irin ta ko kana son yarinya Amman girman kanka na neman cutar dakai "DEENi ya katseshi " hade da cewa kai fa dan matsala ne , nasha gaya maka ka daina cewa ina son yarinyar nan, zan dai aureta ne kawai fk yace Shikenan ajiye wannan zance.
bari gobe inshaallahu zanzo muje gurin big dady DEENi baice komai ba ya katse wayarsa .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 11-12
Washegari bai tashi da wuri ba sai wajejen shabiyu na safe yatashi. yashiga, bathroom byn ya fito ne yayi tsaye gaban mirrow yana kallon every part of him ,tsawon lokacin yana tsaye yana kallon kansa ta mirrow kafin daga baya ya janyo wata karamar stood dake gefe ya zauna .
hannushi ya dora a saman fadaden kirjinsa yana shafa kwantaccen gashin kirjinsa hade da lumshe idanunsa "shi kansa yasan duk matar data mallakesa matsayin mijinta bakaramin Lucky Tayi ba .
cikin sanyi jiki tamkar macce yasoma shafe jikinsa da body lotion " DEENi na kashewa kanshi kudi fiyye da tunanin may karatu ,
mikewa yayi cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufi cikin bedroom din shi dan saka kayan " har ya nufi kofar dazata kaishi parlour" sai ya tuna ana jiransa dan haka yaja tsaki mtssss sannan ya nufe kofar bedroom dinshi byn yashige tare da cewa koma waye zai tafi idan yagaji da zama dan yanzu baida lokacin kowa .
Shiryawa yayi cikin wasu hadadun kananan kaya wando blue jeans da riga longslive" wani irin kyau Allah yayi masa na daukar hankali" ya isa kan durowa ya kwashi wayoyinsa ya zuba cikin aljihun wandonsa "ya sanya takalmansa mai sawun ciki ya zura hannushi daya cikin dayan aljihun .
Shemah ce zaune a parlour DEENi take zaman jiransa "wacce tun karfe tara na safiyar ranar ta dako samamko son ganin DEENI din.
da farko bedroom din ummi ta nufa , sanin datayi dole zai shigo gurin ummi ,ganin har ummi tagama abinda take tadawo main parlour dinta yasa itama tabiyo bayanta , .
Ganin tagaji da zama kusan 1 hour tana zaune zaman jiransa Amman bata ga alamun. fitowarsa ba yasa tacewa ummi dan Allah takira mata shi .
Ummi takirasa tasanar dashi bai ce da ummi komai ba dan kusan da haushi yatashi . Ita Kuma ganin yayi shr yasa tace mata taje part dinsa .
Koda ya yafito falonsa yaga mutun zaune shi duk tunaninsa FK ne ko cikin abokan aikinsa kallo daya Yayi mata ya dauke idanunsa daga kanta "yi yayi tamkar bai ganta ya nufi hanyar fita. ta taso da sauri tana kiran sunanshi " cigaba yayi da tafiyarsa danshi a ganinsa bai ga abinda zai sa ya tsaya ba ,.
ganin saurin bazai mata ba , dan haka ta kara da dan gudu da sassarfa har ta cimmasa ,a daidai cona da zata kai mutun main parlour din gidan tasha gabansa da sauri tana sauke ajiyar zuciya hade da cewa dan Allah yaya katsaya magana nake son yi dakai .
dubanta yayi tamkar bazaiyi magana sai Kuma yace meyye matsalarki dani ? Dan ji Yayi kmr ya dauketa da maruka " Kalmar daya fada ne yasa taji zuciyarta ta tsinke " Tayi wani irin tsalle kmr zata tafasa kirjinta ,.
Tayi shiru tana tattaro kalmar dazatayi amfani wajen fahimtar dashi abinda ke ranta .
cikin sanyi murya yace ina zaton kin manta ko ni wanene shiyasa kika tareni , sai da ta saita kanta sosai, ta'aro jarumta takara akan wanda take da" sannan tasamu kwarin gwiwa. cikin marairaicewa murya irin ta masu neman taimako tace dan Allah yaya" kadan bani aron lokacin uziri ne dani.
yamata wani irin duban dayasa yanhanji cikinta kadawa sannan yace uhmm ina jinki kuma ki tabbatar da uzirinnaki mai ma'ana ne .
"da idanunta ta amsa masa dan gabadaya ilahirin jikinta kirma yake tsabar rudewa datayi har wani gumi take fitarwa na wahala.
tun ba yau ba DEENi yasan shemah nason furta wani abu gareshi Amman rashin ganin fuskarsa yasa taki tunkarsa shi bema san dalilinsa na tsayawa ba .
Shi kansa yasan dole wannan ranar zata zo komai daren dadewa ".
ahankali take sauke ajiyar zuciya saboda fargaban da tashin hankali , abinda zai biyo baya " numfashi taja hade dayin kasa da kanta dan sam bazata iya kallon kwayar idanunshi a wannan lokacin .
Ahankali tasoma magana muryata kasa kasa cikin in...inna ,tace daman ..daman..ina son sanar dakai " ina..ina so.....da hannushi ya dakatar daita" tun bata kai ga karasa maganarta ba tare da buga mata wata irin razananniyar tsawa wanda yasa ba shemah ba ,har zeenat dake kokarin fitowa daga dakin ummi zuwa parlour "ta koma cikin daki da sauri " ta manne da jikin kofar hade da cewa wayyo... Allahna me Kuma yasame sa haka cikin tashin hankali ta sake mannewa da jikin kofar . , hatta ummi dake zaune a falo say da taji amon muryasa ,wani irin kallo yake jifarta dashi yace kina.... me uhmm repeat what u say , lip's dinshi cikin bakinsa yana cizawa sannna yace what ar u try to say ,ya sake jiho mata wata tambaya, still shr kake jin shemah ba bakin magana Amman gabadaya ilahirin jikinta ya dauki kirma .
Cikin isa da takama yace u better keep what'ever you won't say before I sikater you now jikin shemah yacigaba rawa kafafuwanta suka Gaza daukarta dana sani kuwa tayishi yafi cikin buhu , ya tsareta da mayatattun idanunsa " murya a kwasashe yace na sake jin kin Kuma furtamin wannan bazar kalmar wlh azim zakiga yadda zanyi da namanki stupid girl kawai.
ya ja tsaki ya wuce abinsa ta tsaya nan tana bin bayansa da kallo ranta a bace batasan lokacin da Hawaye yasoma zubo mata tana tunanin yaushe ne zata daina kuka akan son DEENi mutumin da take matukar so tamkar ranta mutumin da mata ke rububin son shi mutumin dayake jama mata aji ga shegen kyau da kwarjini " nan ta zube kasa ta risgar kuka ahankali hade da sa hunnta duka ta toshe bakinta dasu .
Zeenat dake tsaye jikin byn kofar dakin ,banda kirma bbu abinda jikinta keyi , tsabar frigice jin abinda shemah ke kokarin yi' domin taji duk abinda ya faru tsakanin yaya DEENi da shemah tsabar tsoro ne ya hanata fitowa ,wani irin kishi ne taji yana taso mata tun daga kan tsintsiyar kafarta yana bin ilahirin jikinta hade da kashe mata duk wani gabobin dake jikinta , taji a ranta da tana iya fitowa,. tabbas da ita kadai tasan yadda zatayi da shemah, tsinuwa kuwa iri iri bbu wanda zeenat bata aikawa shemah ba .
, ahankali zeenat ta sulale kasa ta dora hannuwanta duka bisa kanta.cikin kuka take cewa Shikenan ummi tacuce ni zata kai ni tabaro "gashi taki yarda da aurena ,da yaya DEENi ga wasu can suna neman farautarsa .
,ba tasan tana shirin jefa diyarta cikin halaka bane akan tilon danta.
dan ita yanzu ji take zata iya yin komai akan DEENI .
Ahankali Tace ita yanzu yazatayi da ranta , idan Kuma yace hakura daita fa ? Taji gabanta fadi
Da sauri tasoma girgiza kanta tace hakan ma bazai taba faruwa ba inshallahu sai ta aure yaya DEENi mijinta ne ita kadai , .
dan ita yanzu wani irin son DEENi din ne yashigeta na farat daya ,kmr kar taji ya furta yana sonta ...itama taji tana maseefar kaunarsa , Ita taji ta Gani zata iya rayuwa dashi akowani irin hali.
kawai,a hankali ta sake ta saki wani irin marayar kuka mai ban tausayi tana furta ummi karkimin haka dan Allah ..kar min haka ummi ke uwace gareni har da rabi .
dan Allah karki rabani yaya DEENi wlh zan iya zama dashi a haka , duk munin halinsa ina son shi " tunda harshi ne ya furta yana sona ...
gabadaya ta rikece da wani sabon kuka tana sambatu .
kuka tayi sosai har da shesheka ahankali ta sauko da hannuta bisa kirjinta" ta dafe kirjinta dataji yana mata wani irin ciwo zuciyarta na dokowa da sauri da sauri zeenat ta runtse idanunta dan ita kadai tasan yadda take ji.....
ta ciki dakin zeenat ke rizgar nata kukan ,yayinda shemah da ke waje durkushe ta nata .
Taku yake cikin izza da jin kai da jin shi wani ne yake takunsa har yakaraso ya zauna kujerar da umminsa ke zaune ya dora kansa kan cinyarta "ita Kuma ta'ajiye jaridar dake hannuta tun soma jin amon muryasa ta daina karatu datake "ya sakar mata murmushi gafen baki tamkar bbu abinda ke damunsa ,yace gud morning my first lov ....
ta daura hannuta bisa sumar kansa tare da fadin morning my son yakatashi lfy , ya dan tabe baki sannan yace nut bad ....
tace ya'akayi ne son me kakeson cine akwai dinshi iri iri akan darning wanda orready zeenat tashirya komai .
turo baki yayi cike shagwaba har zaiyi magana " kome ya tuna sai Kuma ya fasa cewa komai " ummi ta tsurawa fusharshi idanu tace kayi shr ya lumshe idanunsa muje kayi breakfast din ina lura da kai tunda kasoma zancen yarinyar nan bakason zama ma a gidan ballanantana Kaci abinci ahankali ya ware idanunshi akan umminsa sannan yace first lov na koshi fita ma zanyi yanzu ....
0 Comments