AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Aysha A bagudo
Page 3-4
Sai da tagama kallonta tsab Sannan ta canza Chennal hade da tashige kitchen dan daura abinci abincin dare
bakin kofar kitchen din ta dawo Tayi tsaye abunta tana cigaba da kallonta Chennal data canza, ajima ajima tana zuwa tana duba abinda ta daura.
Karar bell taji ba kaukautawa shiyasa da sauri taje ta bude gudun maseefar DEENi dan tasan muddin yana gida baya son yawan hayaniya , yanzu ne zai gama daita, Maryam tagani tsaye da wasu en school dinsu su biyu tuni murna yakama zeenat ,ta rungume su daya bayan daya tana musu sannu da zuwa hade da basu hanya "suka shigo har cikin main parlour din hade da Sallamar su .
waje ta nuna musu da hunnu kuzauna mana suka zauna ita kuma takoma kitchen ta duba abinda ta daura taga yayi ta kashe gas din sannan ta dawo inda tabarsu hade da kawo musu drunks mai tsanyi da snacks ta ajiye agabasun .
gabadaya hayaniyya ce ta barke a atsakaninsu da murna ganin juna ,zeenat ta kalli su Sumy hade dayin kasa kasa da muryata tace kuyi magana ahankali fa sannan tace kun kyauta sai yau kuka ga damar zuwar mana , Sumy tace ba gara mu ba muna zuwa time to time.
kufa sai aikin sa rana kullum, hira suka shiga .
a inda Maryam ta dube zeenat tace wai nan fa IV suka kawo mana na birth din rukky, zeenat ta zaro idanu waje I ....me Maryam tace IV .
zeenat Tayi dariya hade da cewa uhmm badani ba" kema kinsa sarai baza'a taba barinmu zuwa wani birthday party ba " Sumy Tayi murmushi sannan tace ai sai da nagaya rukky Amman tace ga zance ga magana " gashi nan, ni ai nasan bazakuyi attending birthday party dinta ba ,da day itace sarkin shishigi da neman suna , zeenat tace kmr kinsani ,duk abinda ya wuce cikin gidan nan namu "ta girgiza kanta baza'a taba barinmu ba ,ki bata hakuri kawai Amman wlh har ga Allah naso zuwa ko dan rukky Sumy tace to why nut ku sace hanya kuje a boye batare da kowa yasani ba ... zeenat ta kalli Sumy fuskarta a hade tace kefa kin cika matsala fa wlh.
kmr bada hausa nake miki magana ba.
ta bude bakinta kennan da niyar sake balbale summy.
sai ga DEENi ya sake fitowa parlour jikinsa sanye da jallabiya marun colour may maseefar kyau sai kyalli take zuwa ga kamshin turarensa mai mugun sanyi dadi wanda tun tasowar zeenat ta sanshi da auren Hamilton har yanzu fuskarsa a daure take tam .. kmr koda yaushe " take ta hadiye maganarta batare da tasan Tayi hakan ba ,ta zuba masa idanu tana kallon kwayar idanunshi, sai data ya hararata, sannan ta dauke idanunta ,ta maida kallonta da hankalinta kacukam a kansu Sumy dake zaune surusuru. Yayinda gabadaya Maryam duk ta fisu tsurewa ko dan ita Yar gidan ce oho..
cikin wata irin murya mai sanyi dadi tamkar ba soja ba yace ke......ta juyo ta ahankali ta sake zuba masa idanunta dan tasan dai daita yake dan haka tabada duk attention dinta garesa.
bakisan kibawa mutun abinci bane ? Dan iskanci sai an roka ,zatayi magana ya katseta a fusace , ai ba tun yanzu nasan ke muguwar rowa ce dake ba Tayi surusuru da idanu ,da sauri tace kayi hakuri dan Allah nayi zaton ko kana azumi ne "naga kullum kana yi "
yace "oh "dama kinsa min ido ne har kinsa cewa azumi nake kullum ?
Jikin Maryam har rawa yake ,a hankali tace wayoo Allah ashe ya dawo ,bari in gudu tun bai gama daita ya da kanmu ba , zeenat tayi shr har sanda ya sake maimaita tambayarsa hade da cewa dan ubanki bada ke nake ba kike bina da idanu kmr zaki cinyeni" ta sake girgiza masa kai,. Tana bashi hakuri
marowaciyace banza kawai mai mugun gado. shiru yayi na dan wani lokaci hade da sauke numfashi .
Sannan can kuma yace ai idan bakiyi rowa ba sai Allah ya tambayeki" km baza'asan ke...Yar uncle Habib bace .
kin taba ganin barewa Tayi gudu danta yakasa rarrafe" zeenat ta sake girgiza kai da sauri ,yace OK ashe dai kema kinsa gaskiya dole kiyi gadon rowa.
Ganin haka yasa su sumy suka nemi sulalewa duk yana kallonsu sai daya ga Maryam na shirin gudu itama dan har summy ta daura hannuta kan handle din kofar ,ya dakatar dasu da hannusa , sannan yacigaba duban zeenat yace barikiji da kyau yana mai nuna da yatsansa" nan ba gidan marowata bane gidan masu bayarwa ne aci . yace menace ? Da sauri tace gidan masu bayarwa ne.
yace gud daga yau bama ni ba ,ko wani ki kaga yazo gidan nan ki bashi ruwa da abinci yaci dan ba naki bane.
ya sake jiho mata wata tambayar yace ko abincin naki ne?, da sauri ta girgiza masa kai dan gabadaya ta sure ta kasa kwakwaran motsi sai ajiye zuciya kawai take yi , yace" baki da baki ne kike kadawa mutane kai , tace naji kayi hakuri dan Allah. Sannan ya juya kan Maryam da kadan ya rage ta fashe da kuka , ya zuba musu ritattun idanunsa da suka fi kama da mage masu saurin raunana mutun kai tsaye , yace ku kuma en iskanci banza kun wani cikawa mutane kunne da hayaniya tamkar kuna club ,kallo daya yayi musu kowace tabawa kafarta iska yaja tsaki ya juya ya nufi dakinsa.
ahankali zeenat take sauke ajiyar zuciya hade da dafe kirjinta , batasan meyasa ba ,idan har Yaya DEENI yana guri Sam bata samun cikakkiyar natsuwa "sai tarinka ganin duk yacika guri ga tsananin tsoransa da take ji yana mamaye zuciyarta . Maryam har da kuka tayi byn sun fita dan daman can ita haka take ,shegen tsoro gareta aiko, su sumy suka ce mezasu ba dariya ba dariya suka dinga yi har da rike ciki suna nuna ta aiko tace yau sai da suyi ta zama a estate din dan bazata rakasu gun securities ba sai da sukayi ta bata hakuri sannan suka jera suna hirar abunda ya faru.
Ko lokacin da ummi tadawo tuni murna da farinciki Ganin tilon "dan " nata yamamayeta zuciyarta nan suka zauna a parlour suna hira cikin hirar ne ummi take masa maganar aure in da tace masa yakamata yanemi mata yayi aure kasan shekararka nawa kuwa yanzu ?yayi murmushi ai dole nasan shekaruna ,muke nan kullum cikin rubuta date of birth ,talatin da biyu ne kawai fa ummi Tayi dariya 32 din ne kawai kusan duk sa'annin haihuwar ka duk sunyi aure acikin estate din nan gasu yasir nan ma duk ansa musu rana dan haka kaima ka fidda mata kafin azumi DEENI yazaro idannu yana bin ummi da kallo a shagwabe yace haba first love dan sunan da yake kiranta dashi kennan tun tasowarsa .... ni din guda nawa nake da zakice inyi wani aure yanzu. Dan Allah kiyi hakuri my first lov zuwa wani lokaci ,duk hirar da suke zeenat na zaune tana jinsu haka kawai taji gabanta na faduwa lokacin da taji abinda ummi tace ,Amma jin amsar da yaya DEENI yabata yasa taji wani irin sanyi na ratsa zuciyarta .
kmr ance ya dago idanunsa suka sauka cikin nata harararta yayi yace kallon fa kin wani tsare mutun da idanu, ummi tace uhmm kafa dawo kennan karka takuramin yarinya ,
ya langwabar da kansa yana maida idanunsa kan ummi cikin sanyi murya yace haba first lov baki ga irin kallon da take bin mutune dashi bane, kmr bata san mutun ba , ummi tace kai da wani idanu ka kalleta har kasan tana kallonka. kuma ma ni banga komai ba kai dai ta kurace kawai dakai indai kana gida baka barin yarinya nan ta huta ta sarara , ya dubi ummi ya tabe baki , Sannan yace ke....kawo min coffee ,ta mike taje ta hado coffee din takawo masa gabanta na wani irin faduwa ta durkusa har kasa ta ajiye masa .
Adaidai wannan lokacin ne zeenat ta kammala karatunta na secondary school , ta fito da sakamakon mai kyau domin tasamu almost 7 credit masu kyau .
shi kansa DEENI yaji dadi Sosai sanda ummi ta nuna masa Amman dayake miskili ne, sai cewa yayi Sam shi bai ga wani kokari da Tayi ba tunda bata cinye duka ba .
ummi Tayi murmushin tace kai ne dai bakaga kokarin ta ba. Amman ni nagani km nasan Tayi kokarin Sosai .
Ina laifi duk cikin wayanda suka rubuta jarabawa tare bbu wanda yakaita marks ,.
yace ok inda ta cinye duka ne zan iya cewa Tayi kokarin ai wayanda suke cinye 9 credit ba finta brain sukayi ba.
Ita dai wasa da kallace kallacen banza tasa a gaba.
ummi ta hade fuska tana harararsa yacigaba da zagin zeenat ganin yadda ummi Ta canza fuska ne ,yasa yabar maganar , ummi ta sake duba result din tana shafawa hade da kwallawa zeenat data tashi tun sanda taji DEENi yasoma zaginta kira ,takaraso tazo ta tsaya kusa da ummi DEENi ya dauki wayarsa yana daddannawa ba ko kalli inda take ba ummi ta mika mata slip din tana murmushin tace kinyi kokari sosai , zeenat ta karba ta juya ta bar gurin dan bazata iya zama a duk inda yake ba .
ummi ta dubi DEENI tace yanzu kuma sai aure zanwa zanwa yarinyata .
DEENI ya juyo a sukwane yace wani irin aure kuma first lov da rana tsaka , kudai Bari yarinya tacigaba da karatu kawai" dan yanzu kai yawaye , an daina irin wannan auren, ballanantana mata marasa illimi "ummi ta dubesa da kyau ta numfasa Sannan tace ni tawa iya secondary zan aurar daita dan ma taki sauraran masu sonta . itama shegen iyayi ne daita kuma dai kasan matan wannan family din basa wuce secondary ake musu aure .
kuma kasan baza'a fara karatun jami'a daga kanta ba, uhm nima nafi son na aurar da abita. DEENI ya tabe baki Sannan yace Allah ya kyauta ni ko zanyi aure bazan auren Yar secondary ba wlh sai wacce tagama jami'a mai tarin illimi ,kuma ba auren family zanyi ba dan baya birgeni. yakarasa maganar yana dan murmushi ,ummi tace to Allah yabaka sa'a. amman ni tawa aure zan mata da wuri .
kai kasan halin big dady bazai taba barinka kayi aure a waje ba .
Wlh nasoma a hada aurenka dana su yasir yace uhmmmm su dai yi nasu ni sai nan gaba .
A wata yammacin DEENI zaune akan dadduma awajen shakatawa shi da abokansa wayanda duk kusan , family ne zagaye dashi gefe guda kuma flasks ne cike da ruwan zafi da kananan cups , hira suke sosai atsakaninsu Amman banda DEENI dan gabadaya daukar hirar tasu yake shirme dan duk zance nasu akan maganar aurene wanda shi kuma Sam baya kaunar ji , dan haka ya sharesu yacigaba da lasalasar wayarsa ya yinda ya kai hannunsa daya ya dauki cup din coffee wanda orready fk ya tsiyaya masa ya kai bakinsa yasha hade da rufe rikitattun idanunshi wanda yazame masa jiki fk ya kalli yasir da faysal dake tawowa inda suke, ya kwashe da dariya har suka karaso bai bar musu dariya ba fk yace sannuku da karasowa Mayan angwane kunsha kamshin kunsha kamshin ,faysal yace kai dai anyi dan iskan yaro , kai baka tsaya ruwan ido ba kana biyewa wannan ya nuna DEENI da yatsa fk yayi murmushi yace yayi an gwanen bana wannan karon gabadaya suka dara hannu suka bawa juna suka gaigaisa har DEENI.
yasir ya dube fk yace ai gara muyi aurenmu tunda muna son juna kai ka zauna kar kayi har mahdi ya bayyana ,fk yace A'a nifa bance saboda me zakuyi aurenku ba . Amman gaskiya zaku takura kanku ne kawai yanzu da wani aure wayannan kananan bbys din.
DEENI ya tabe baki Sannan ya dube fk yace shiyasa rawar kan yaran ke kara yawa ba . dukkansu suka sa dariya suna cikin dariyar ne fk har da rike ciki sai gasu zeenat da suka taso daga islamiyya su biyar suka jero kowace sanye da hijab dinta raudat da shemah da samiha da Maryam sai zeenat dake tsakiyar su dukkansu kyawawane .
da hannut fk yake nuna musu inda suke Sannan ya dakata dariyarsa ya kalli inda DEENi ke zaune tamkar bai san abinda ake ciki ba , ko kallon inda suke bai yi ba, yacigaba daddannawa da sarrafa wayarsa .
fk yace kai gaskiya bbys din nan fa su hadu dayawa fa , nima ko zan dan shiga daga ciki ne.
yasir yace dako ka huta , kabar wannan ya nuna DEENi fk ya cigaba A'a ina ai bazan barsa ba tare zamuyi namu auren , ko yakace mutumina kaga Shikenan mun huta da surutu jama'a DEENi ya kallesa a kaikaice yace A'a ku dai da kuka ji zaku iya kuje kuyi Tayi .
Amman ni ya nuna kansa da yatsansa hade da tabe baki, ba yanzu ba" har sanda su zeenat suka zo suka wuce . Suna hirarsu suna dariya Maryam ce ke basu labarin abinda ya faru jiya bbu wanda bai dara ba har ita zeenat din raudat tacewa zeenat ai ke kika daukar masa wlh kuma yarinka yi miki kennan ina ma nice daya gane kuresan suka sake yin dariya .
Tun lokacin daya dawo zance sa da ummi bai wuce DEENI kayi aure fito da mata cikin yan,uwanka kayi aure hirar kennan sai dai idan basu zauna ba .
Yau takama walimarsu zeenat ta saukar alqur'ani mai girma wanda aka shirya musu anan islamiyyarsu dake cikin estate din ,su kusan goma anyi taro walima lfy yayinda zeenat ta karbi kyaututtuka da dama saboda kokarinta har kuka ummi Tayi sakamakon tunowa datayi da er'uwarta taro ya watse lfy kowa yakama gabansa ,byn sun gama hirarsu da ya zame musu jiki suka fara hada kujerun da akayi walimar dasu . sun fito kennan suka ga Yaya DEENI da wani abokinsa zaune akan kujera biyu suna hira ,take suka ja birki samiha tacewa zeenat jeki amso wadan can kujerun, cikin zolaya tayi mata maganar dan tasan yadda take jin tsoronsa zeenat tace uhmmmm ku dai kuje "suka sa mata dariya ke wlh muguwar matsoraciyace wlh ki rage tsoransa shiyasa yabi duk ya renaki ,Tayi sororo tana kallonsu , Sannan tace to bari naje amso Tayi tafiya kmr zata isa gurinsa sai kuna ta juyo da sauri" aiko suka sake kwashe mata da dariya .
muryashi ce ta katse musu dariyar tasu lokacin daya suke kallonsa a frigice" yayinda gaban zeenat yasoma faduwa yace ke....da hannu ya nuna musu alamun suzo 's suka nufo inda
Yake cike da tsoro ya zuba musu rikitattun idanunsa yana kallonsu daya byn daya yana nazarinsu Sannan yace da ganinku akwai alamun rashin gaskiya atare daku ? ya nuna su da dan yatsansa zeenat Tayi saurin cewa A'a cikin inda inda uhm bbu komai fa Tayi gudun Kar wata cikinsu tafada masa shiyasa Tayi saurin yin magana ,to menene na inda inda wama ya tambayeki ?Tayi shiru tamkar ruwa yacinyeta. Sannan ya juya ya kalli abokin nasa da ya zubawa zeenat idanu yana kallonta kafarsa yasa ya take kafar manir dashi ,sannan ya dawo natsuwarsa ya mai da hankalinsa kan DEENi , DEENi ya nuna su zeenat da samiha hade da shemah da Maryam yace gasu nan bansa inda sauran suka nufa ba, manir yace ina tayaku murna walima saukar alqur'ani mai girma, Allah yasa na tsoron Allah ne ,suka hada baki wajen cewa Ameen , kallonsu kawai DEENi yayi jikinsu har rawa yake suka bar wajen.
manir yabi bayansu da kallo yace kai sisters din nan naka fa akwai kyau DEENi ya kallesa yana watsa masa harara ok iskancin naka kuma yau agidanmu zai Kare.
manir yayi murmushi yace Allah barin ma wace ta tsakiyarsu gaskiya duk tafiso haduwa DEENi ya kalli inda ya nuna sai yaga zeenat yake nufi take yaja tsaki manir yace dama ita ka zaba wlh dan nasan karshe ma auren zumunci za'a maka DEENi ya sake jan tsaki dan Allah malam karka dameni da wannan shirme bazan ,manir bai daddara ba ya sake cewa Allah dama tsayawa kayi akayi Yar gida tunda duk tarin matan dake sonka baka kallonsu , a fusace DEENi yayi magana dan me zan kallesu alhalin banda abinyi dasu.
manir yayi murmushi ina ma ni ne kai wlh tsayawa zanyi na kwashi gara son raina har sai nagaji in more kuriciyata , DEENi yace ai kai dan iskanci ne lamba daya , wlh ka guji abinda kakewa ya'yan mutane "ko dan gaba .
ka dauki neman mata tamkar wani abinci, manir ya dan daki kafadar DEENi yace ai sun fi abinci dadi ,.
Amman Allah koni ina son na daina bin matan bazan ,wlh abun ne da kmr wuya Amma kacigaba da yimin addu'a . DEENi ya nuna sa kai zanwa addu'a saboda banda abinda zan roka Allah , manir ya dage masa gira daya yes meye dan kamin addu'a kaga idan Allah ya shiryani sai kabani wacce Yar dimadimar sister din taka na aura , bai kulasa ba sai canza zance da yayi nan dai suka cigaba da hirarsu har zuwa sanda sukayi sallama da juna .
Abinda zai daure maka kai bai wuce yadda ummi ke sake bawa zeenat kulawa ta musamman ba ,ta kowani part tana iya kokarin ganin ta fito da diyarta ta tsab, zeenat bata rasa komai ba tun daga dangin sutura da mayuka shafe masu tsada zuwa kayan kwalliya ana cikin haka tafiya takama ummi zuwa India dan haka ta tasa diyarta gaba suka tafi zeenat taji dadin zuwansu India tamkar karta dawo ,watan su daya suka tattaro suka diro Nigeria saboda bikin family dinsu yakusa koda ta dawo ma su Maryam sun dinka mata duk anco din da aka fidda tunda damar suna da telarsu ce da yake zuwa har gida ya karba dinki,.
biki akayi sosai bakama hannu yaro an kashe kudi tamkar ba'asan ciwonsu ba bidia iri kuma a duk anan cikin estate din akayi komai, daga karshe akayi walima washegari ranar Sunday aka daura auren en mata biyar haka ma samarin aka dan kowace gidan mijinta, ya saura mutun uku ne cal suka rage da basu aure ba, Maryam da shemah sai zeena amaza kuma fk da DEENi sai kamil .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Aysha A bagudo
Page 5-6
Zeenat na da kyau sai dai ba can ba" fara ce Sol Amman batada dagon hanci wannan bai sa fuskarta muni ba" haka idanunta matsakaita ne ita mutun ce mai tsananin son kwalliya wanda ko alwala Tayi sai ta sake yin wata sabuwar kwalliya, haka nan ummi bata gajiya da siya mata kayan kwalliya iri iri sannan bata ganin aibunta a duk lokacin da zata bata a gurin yin kwalliyar .
abinda kawai bata so kuma bata yarda dashi ba, shine a yimata dinkin da zai bayyana surar jikinta ,nan nefa tace bazata bada goyon baya gurin bata kamasho yada zina ba , dan a cewarta shigar da yawancin ena'mata keyi a wannan zamani itace ke sake haifar da fashadi a doron kasa.
zeenat akwaita da saurin sabo da mutane sannan km tana da son kawaye ita da Maryam dan ko yanzu suka san mutun ko km kuka hadu dasu sanadin wata kawar, Shikenan sun zama kawaye , shiyasa suka fi dukkan sauran en'uwansu jama'a dan daga waje ma zuwa ake gurinsu sabanin sauran" kullum kaga ana rikinci a bakin get da sune , gurin shigo da baki most especially ma na school dinsu. abinda ummi tafi tsana kennan daga gareta yawan tara kawaye gata da matukar son gayu ,da son kallace kallacen film muddin tana gida kuwa bata da aikin yi sai na kallo ,daga wannan Chennal zuwa wata ,sai dai duk da wannan halin nata Allah yabata illimi sosai both arabic & school.
Daidai misali Allah yayi mata farin jinin samari masu sonta daga waje ma biyota akeyi, sai dai bata fita dan ma ummi taki yarda tafara zance da wuri sai data kai ss2 kuma duk masu zuwa gurinta da aure suke sonta "amman matsalar dai daya ce family dinsu basa yarda da macce Tayi auren wajen Amman sukan bar namiji.
kana duk masu son nata bataji son su har cikin ranta 'har wani lokacin ummi kesata gaba da fada "tace maza ki tsaya ruwan ido daga karshe kirasa kowa kizo kina nema yawan yi mata fadan da ummi keyi ne yasa ta tsaida kamil dan gwaggonta" yayar mahaifinta da suke uwa guda uba guda .
shima bakowa yasan suna tare dashi ba , dan bata gama tantancewa aurensa ba" kuma shi bai fiyye zama a garin ba yana aiki ne a abuja ". haka kawai taji idan bata samu wanda yafi ba , zata iya aurensa dan shima ba laifi .
Jiki da jini wata safiya ummi ta tashi da ciwon ciki , wasa wasa tun tana daurewa har abun yafi karfinta gabadaya tafita haiyacinta' hankalin zeenat yayi mugun tashi dan bazata manta yawan labarin da ummi ke yawan bata na mahaifiyarta da irin wahalar da batasha kafin mutuwarta ,ciki har da cewa mata Tayi ta bude ido ta zabi miji wanda zai san mutuncinta kar taje gurin ruwan idonta ta kwashi gaibu ,shiyasa take massefar jin tsoron haihuwa da mutuwa dan ta kudircewa ranta, ta amince da mutuwa tunda tasan muddin kwanakinta suka Kare Shikenan "amman ita kam bazata yarda da haihuwa ba ganinta garata tasha wahala daya .
wunin ranar da ciwo ummi ta wuni can kuma tasamu sauki dare nayi ciwo ya sake dawo zeenat taso zuwa ta sanar da DEENi Amman ummi taki .
washegari DEENi yashigo da shirin fita aiki dan bai san bata da lafiya ba koda yashigo dakin yayi matukar girgiza da ganinta kwance cikin bargo da kyar take iya magana a rude yakaraso inda take ya tambayar ba lafiya ne ? Ummi tace eh tun jiya yace meyasa baki sa an tashe ni ba ,ya kalli inda zeenat ke rukube kusa da ummi duk tazama wata kalar tausayi.
ke....Wace irin" sakariyace da baza ki iya zuwa kisanar min ba da kyar ummi ta iya bude baki ,tace ni na hanata ya furzar da huci ta bakinsa hade da cire hular kansa yayi wurgi dashi gefe ,take ya Ciro waya cikin aljihun bayan wandonsa yakira family doctor dinsu wanda side dinsu kawai yake dubawa.
mintina kadan sai gashi likinta dayake bai da Nisa dasu cikin sauri yashiga duba ummi sosai har drip aka sawa ummi a ranar DEENi kasa fita yayi koina byn likinta ya wuce ne, ya kirasu ya Mahmoud ya sanar masu da ummi fa ba lfy , idanunta ta zuba mashi tana kallon bakinsa yadda yake maganar ne tamkar wata mace shi yafi daukar hankalinta,
ba taba jin DEENi ya birgeta ba irin na yau.
duk wunin ranar kusan shi yayiwa ummi komai hatta magani da abinci a baki yabata sai gurin la'asar su Yaya Mahmood sukazo tare da matansu sai zuwansu ne ma yasa mutane cikin estate din suka sani dan DEENi bai sanar da kowa ba, shi dai ta mahaifiyarsa kawai yake.
Ai kafin kace me tuni side din ummi yacika da jama'a, haka suka dinga shigowa duba ummi har dare DEENi na tare da ummi yana bata kulawa. duk yayi wani iri cikin lokaci kadan yafita haiyacinsa zeenat na zaune a gefe guda tana jiyo hirarsu rokonsa ummi take akan yayi aure ahankali takira sunansa NASURULDEEN ....abinda yasake tada ma DEENi hankali kennan yaushe rabon dayaji ummi takira complete name dinsa , tacigaba ban rasa komai na rayuwar duniya ba inada tarin dukiya da kadaroro wanda ni kaina basan iyakarsu ba ,burina da muradina ahalin yanzu bai wuce inga aurenka ba, Amman na fuskanci kafi son sai na mutu sannan zakayi aure . Jikin DEENi ya dauki rawa hankalinsa ya sake tashi matuka ta sake kiransa cikin tattausar muryar hade da rarrashi DEENi banida kowa daga kai sai zeenat sai kuma dan uwana wanda yake wata uwa duniya ,idan bakayi aure ka taramin jikoki masu albarka ba mezakayi min naji dadi , ina ji ajikina sai na mutu zakayi aure a rude yace first lov ki daina cewa haka zanyi inshallahu kina raye Tayi murmushin karfin hali tace kullun haka kake cewa, ni tuni na fidda raina ka tashi katafi Allah ya maka albarka ... Amman yarinyar nan zeenat na rokeka dan Allah ko ban tashi ba kada kabari ta koma hannun mahaifinta, na damka amanarta a hannunka ,bata da kowa duk duniyar nan daga ni sai kai ,karikemin ita a hannunka har zuwa lokacin da zata samu miji . DEENi yakamo tafin hannun ummi cikin nasa ahankali yasoma magana muryasa cike da rauni da fargaba, yace haba first lov ki daina maganar mutuwa nan kece zaki aurar daita da hannuki kuma kina raye inshallahu ta girgiza kai ita kadai tasan abinda take ji cikin muryarta irinta marasa lfy tace Shikenan tashi kaje ka kwanta , hankalinsa a tashe ya fice daga dakin..
zeenat ta mike daga inda take idanunta na zubda hawaye ta taimaka mata suka kwanta tana kuka kasa kasa ummi tace lfy zeenat ummi . .... ummi..... cikin sheshekar kuka tace banason naji kina cewa zaki mutu kibarni dan Allah ,ummi tace nafa da kar na fada mutuwa ta zamemin dole sai dai idan ajalina bai zo ba . zeenat ta saki kuka hade da kamkameta ummi a jikinta , tacigaba da kuka mai cin rai hade da cewa ummi bazaki mutu ba inshallahu da kanki zaki aurar dani ni ga duk wanda kike so da kyar bacci ya dauketa yayinda ummi Tayi nisa a bacci .
Shi kuwa DEENi tunda ya koma dakinsa ya kasa zaune ya kasa tsaye sai zariya yake daga farkon dakin zuwa karshe kafin daga baya ya nemi gurin ya zauna.
yayi tagumi da duka hannuwansa yayi zurfi cikin tunanin yadda zai yi lallai ya zama dole ya nemo mata domin cikawa umminsa burinta. sai dai shi matsalar sa bai san ta ina zai fara ba ? Bai taba yin buduwar ba ballanantana wata aba soyayya, shi duk a tunaninsa raini hakan zai jawo masa idan yaje yace yana son budurwar .
ya kamo gefen lips dinsa ya dan cizawa a hankali har daga karshe ya yanke shawara zai nemi fk da zance anan ya sulale ya kwanta rigingine idanunsa na kallon celling dakin .
yayinda ya rungume hannushi a saman kirjinsa yana aiyana irin type din maccen dayake son ta mallakesa,kuma wacce ya dace ya aura cikin sanyi ya runtse idanunsa gam take yasoma zaiyano irin type dinsa kyakkyawa dogowa mai dirin jiki , choculate colour, mai dara daran idanu sannan educated mai wushiryar haka dai ya rinka yi har dare ya sula bai samu wani ishashen bacci ba. koda asuba kafin ya tafi masallaci sai da ya fara shiga Bedroom din ummi ya sameta tana sallah ya sauke ajiyar zuciya sannan ya wuce ganinta tsaye tana sallah yasan Allah yakawo mata sauki .
A masallaci DEENi suka hadu da fk byn an idar da sallah "yajashi gefe guda da idanu fk yake binsa da kallo "abinda bai taba faruwa ba saboda DEENi daya idar da sallah yayi yan addu'oinsa yake wuce wa gida .
fk ya dube sa da kyau yana nazarinsa kafin daga baya yace lfy kuwa naganka haka ? Gabadaya fk yagama tsurewa da ganin yanayinsa sai da ya sake maimaita tambayarsa sannan DEENi yace ina fa lfy jiya ummi kwana Tayi ba lfy har tana barmin wasiya burinta da muradinta yanzu bai wuce nayi aure ba.
fk yayi shr yana jin DEENi har sanda yagama bayaninsa sannan yace baita kadai ba har big dady ma burinsa kennan dan ko jiya sai daya min maganar nida kai Amman tunda kai ummi ta damu ta tsananta gara kayi kawai kurabu lfy .
DEENi yace ai bakasan inda zan nemi matar ba nifa gabadaya en,mata family din nan basu min ba sannan kuma sun min kankanta da aure ,fk yace A'a bawani kankanta" mace na kankanta da aure ne ? kaine dai kawai kake ganin haka ,ni yanzu na yanke shawarar zan tsaida shemah kawai tunda na dade ina sonta nida zakaji shawarata ma da zeenat ka aura DEENi ya mishi wani irin kallon bakada hankali sannan yaja tsaki yace haba dai zeenat , fk yacigaba yarinyar akwai hankali wlh ,ba kmr wancan banzar ubannata ba, dayake duk sun tsani halinsa.
kaga kawai sai a hada bikinka da nawa kawai kaga zeenat batada matsalar, km ko bakomai ummi zata ji dadin Sosai da wannan hadin.
DEENi yace Amma ban taba jin koda alamar digon sonta ba, kuma ni gaskiya ina ganin tamin yarinta dayawa duk fa shekarunta sha tara zuwa sha ashirin ne fa. nafison mutual girl wace ta mallaki hankalin kanta tasan yadda zata kula dani akan bed ,amman wannan Yar bbyn maimakon ta kula dani ,ni ne zan koma renonta.
fk ya dubesa a kaikaice yace lallai yaran zamanin da kasani Amman banda na yanzu, sai su maka abinda manyan matan baza su iya ba, kana rai nata ne kawai , sai kaga mararta ta daukeka tsab, DEENi yaja tsarki kai ban son iskanci shawara nake so, ba wani shirme ka can na bazan ba .
fk ya kada kafada yace well tunda kaga bata maka ba kana iya duba wasu acikin gari .
DEENi ya kalleshi yana watsamasa harara "kaifa dan iskane dan kaga nazo maka da maganata shine zaka rainawa kanka hankali " sai kuma yayi kasa kasa da murya yace kasan Allah ni fa ko a waje ba wai ina kallon mata bane, fk yace to katsaya akan zeenat din kawai, duk inda ake neman macce mai natsuwa yarinyar nan takai ,DEENi ya sake jan tsaki yace ai inda takaicin yake kennan sai kuma nakirata ince ina sonta ...ya fada yana tabe baki "hade jin takaici da haushin shawarar da fk yakawo masa " fk yace inda bazaka iya ba kabi ta sama , ma'ana kasamu big dady da maganar kawai, kasanar dashi kana sonta nasan zai ji dadi Sosai .
DEENi ya sake watsamasa wata harara yace dan Allah malam ka dameni , ina ganin fa kmr kafara samun tabin hankali , wa yace dakai ina sonta "zan dai yi aure badan ina so ba ,ya juya yabar fk nan tsaye yana binsa da kallon mamaki sannan kuma yace ai kaine babban mahaukacin dan iskan kawai , sai iskanci fall ciki ,shi bai ga laifinsa da yace bazata ya saukarsa a bed sai nawa sai kuma ya kwashe da dariya .
0 Comments