AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 25- 26
Bai ko kalli inda take ba hasali ma operating din system dinsa yacigaba dayi.
" tayi kusan minti goma tsugunne a gabansa batare daya dago idanunshi ya kalleta ba .
Shr Tayi tare da" sunkuyar da kanta kasa .
Yayinda zuciyarta ke tsananta bugawa .
cikin daddaden muryarsa may cike da dadin sauraro "fiyye da komai datafi kauna .
Yace tun yaushe kike tare da wance sakaran Dana ganku shekaranjiya ?
Batasan sanda ta zauna ba ,dan tsabar frigice da tsoron daya shigeta na lokaci guda .
,zuciyarta ce tasoma rawa...rawa tare dokawa .tarasa yadda me za tace.
cikin ya'n sakanni nan hankalinta yayi matukar mugun tashi. kwakwaluwarta "tashiga tariyo mata abinda ya faru a shekaranjiya din .
gabadaya tagama
frigita da tmbyr daya jiho mata, tunaninta ya ta'alaka ne akan ya manta da abinda yagani din .
dan ganin ya share Bai nuna koda a fuskarsa ba .
da kyar ta iya bude bakita tare da son nuna masa , itama batasan inda zancesa ya nufa ba.
, muryarta cike da rudani tace wa kenan ?
Sai Lokacin ne ya dago rikitattun idanunshi ya dubeta dasu .
,tare da zabgamata wata uwar harara .
cikin sanyayyayiyar muryarsa, ta isa ya sake yin magana Yace wawa ..... .ni zaki waskewa ya nuna kirjinsa da yatsansa
bakaramin laifi zaki karawa kanki wajen nuna min bakisan abinda nake nufi ba .
Domin bana bukatar
rainin hankali ko karyata min abinda idanuna suka gane me .
Amsa tmbyta kawai nake da bukata .
take muryarta tasoma rawa alamun kuka keson kufce mata.
,ahankali ya daura yatsan hannunshi akan lip's dinshi " shiiiiiiiiiii....... karki kuskura naga Tear's dinki ko rawar murya .
dan banida bukatar su .
I said tun yaushe kuke tare , that's ol ....
A boye ya dinga sauke ajiyar zuciya sannan ya"
yacigaba ko duk dadewarku bakisan tun lokacin da kuke tare ba ?
Lokacin daya taji maganarsa na neman birkita mata Brain dinta. to up side down" wani irin rudewa da gigicewa ta sake yi .
Ba bakinta kadai ke rawa ba ,yanzu kam har gangar jikinta rawa yake .
Ta dawo tamkar wata zautacciya Da kyar tasamu ta iya hadeye abinda taji ya tsaya mata a makoshi .
tare da zubda hawayen da suka taru a idanunta, cikin rawar murya tace shekara biyu kennan.
Tana gama fadar haka
, tayi saurin sunkuyar da kanta kasa dan gudun jin saukar mari .
yayinda hawayen tausayin kanta suka cigaba da bin kuncinta.
a hankali ya dinga girgiza kanshi shekara biyu kennan ya sake maimaitawa kansa.
Cikin sanyi ya maida jikinsa" ya kwanta rigingine ya Kuma cigaba da operating din system dinsa batare da ya sake ce mata komai ba .
,Take yaji zuciyarsa ya dauki beating ,wanda yarasa dalilin jin haka .
Kusan minti shabiyar kennan idanunshi na kan system dinshi yana cigaba da aikinsa .
, wanda mutun zai iya dauka aikin ne kawai a gabansa"
amman a zahirin gaskiya hankalinsa ya rabu gida biyu ne . kan aikinsa da nazarinta yanayinta " maganarta ba iya kunnenshi kadai ta tsaya ba " har gangar jikinsa takaiwa farmaki . ahankali ya dinga furzar da iskar mai zafi daga bakinsa . gashi dai magana yake son yi amman taki fitowa sakamakon zuciyarsa dake bugawa .
,da kyar yasamu iya bude bakinsa .
yace kina nufin shima sonki yake yi kennan ?
Tsoro da faduwar gaba ne suka taru suka mamaye zuciyarta.
cikin in..inna ..tace wai wai haka yace "amman , dan Allah kayi hakuri .
da sauri DEENi dake rigingine ya mike zaune cikin daga murya yace mene ? Nayi hakuri ubanki "
Da sadakin nawa akanki idan da kuna kula juna ,I don't care .
Amman yanzu iskanci ne yasa kika, cigaba sauraran wancen sakaran dan tsabar kin raina min hankali.
Bakinta na rawa tace Ai shima yasani" shiyasa ma yace ya hakura dani .
, ok da shi m...
sai km yayi shr yakoma ya kwanta . hade da runtse idanunshi . Lips dinshi na kasa yakamo yana cizawa a hankali ahankali " cikin zafin rai da kunar zuciya ya nuna mata kofa da yatsansa alamun ta bar masa dakin .
,kasa Mikewa tayi tsabar tsoro gabanta yacigaba da faduwa ,muryarta na rawa" ta sake yunkurin bashi hakuri dan Allah yaya kayi hakuri wlh mun rabu dashi tun ba ya...
Wata irin tsawa ya daka mata take maganar ta makale "tun batakai ga karasa yin ta ba .
wanda hakan yasa ta mike tsaye da sauri batare da tashirya yin hakan ba.
jikinta yacigaba da kirma .
Ahankali ya bude rikitattun idanunshi "kasa kasa yake kallonta ji yake tamkar ya tashi ya shakota" tare da yaryarfa mata maruka" ko zai dan samu ya ragewa kansa tension din daya addabe shi tun shekaranjiya.
amman ina baya ji zai iyayi haka.
kodan "
,sanin halin Umminsa.
yasa muddin yayi haka ranta zai baci ,hakan kadai ne yasashi kasa aiwatar da komai akanta.
idanunshi ya watsa mata yana mai sake kafeta dasu wani irin kwarjini ya sake yi mata wanda hakan shi ya kawo katsewar duk wani kuzarin dake tattare daita .
Muryasa a sarke yace live dis room now before I skater you .Ai Bai kai ga rufe bakinshi ta kwasa "
da sauri ta soma kokarin barin dakin.
Hade da tabe baki a ranta Tace matsefafe banza kawai "anya zan iya daukar wulakancin nan naka kuwa ?
ta fice tana goge gumi duk da ba lokacin zafi bane jikinta sharkaf yake da gumi .
Tana fita ta dinga fidda numfashi sama sama tamkar mai cutar asma.
sai data goge gumin daya cigaba tsatsafo mata sannan ta shiga daki .
Zaune ta samu Ummi. Tana balle magani zata sha .
Ummi tabita da wani irin kallo tace ke km daga ina haka ? Tace yaya DEENi ne yakirani" Ummi tace yashigo ne ta girgiza mata kai" kawai " alamun Eh " to yana ganki duk a frigice kmr wacce tayi gudun tsire ,ko wani abun yayi miki.
zeenat tayi narainarai da idanuwa tace A'a Ba abinda ya min .
Ummi ta sake dubanta hade da tabe baki tace ke kika sani ma idan wani abun yayi miki .
,ba kinki tsayawa waje daya ba, sai wani rawar jiki kike yi akansa dan tsabar sakarci irin naki .
Zeenat dake tsaye tana duban Ummi taji tamkar ta zubda kwalla dan jin takaicin abinda Ummi tace mata .
, Tace to ni yanzu Ummi wani rawar kai nayi km ? tmbyta abu kawai yayi fa.
Tace to me Yace miki ko abinci zai ci zeenat ta sake girgizawa Ummi kai.
, baki da bakin ne da zaki dinga amsa minb da ka. cikin rawar murya zeenat tace Allah Ummi tmbyta kawai yayi.
tmby ce kawai zai saki kiyi hujiga hujiga haka kmr an kwatoki a bakin kura .
Ki sanar dani idan wani abu yayi miki.
Tukun na ma , how many hours dana dawo parlour na iske baki nan . Km nasan tun lokacin Kina dakinsa dubi yadda kike fidda gumi dan Allah .
a sanyaye zeenat din Tace to ni Ummi me kike so nace byn .....
sai km hawaye ya balle mata shar shar.
yasoma bin fuskarta . Tayi saurin tare da
sanya byn hannuta tana goge hawayen wasu na sake silalo mata.
Ummi ta zuba mata idanu kawai tana kallonta tare da nazarinta tabbas tasan duk yadda akayi akwai abinda deeni ,yayi mata .
Amman dan sakarci da kafiya irin tata gashi tski fadar gaskiya.
sai da ummi ta numfasa sannan ,tace meyye km na kuka ke da kika ce ba abinda aka miki .
,bakiyi kuka a can inda aka ritsa ki ba sai a nan ,dan kin rai nani ko..
kasa cewa komai zeenat din tayi illa sanya kai datayi cikin bathroom, tashige abunta tana kuka kasa kasa , abubuwan sun taru sun cakude mata .
goma da ashirin ga rashin samun kulawar DEENi gareta .
ga damuwar Ummi akan ta nacewa DEENI .
cikin dare ma sam kasa bacci tayi .
Sai faman juyi kawai take akan gado tare da tunanin iri iri ta jima kwance batare da bacci yayi nasarar dauketa ba .
Wani tunanin ne yazo gara ta tashi takai kukanta gurin mai duka.
dan haka ta mike cikin sanyi jiki " taje tayo alwala .
sallah nafila ta dingayi ba kaukautawa tare da neman zabbi Allah akan aureta da DEENi.
dan ita kanta tasan zuwa yanzu tabbas tayi kuskuren saurin amincewa da aurensa datayi .
Domin shine musababbabin abinda yasa wulakancinsa ya sake nunkuwa gareta. wanda ita kanta tasan hukuncita abinda yafi dacewa daita kennan .
na saurin amincewa datayi da auren DEENi cikin gaggawa batare da ta neman zabin Allah ba .
hankalinta kan tashi.
a duk sanda ta tuna da maganganu ummi. A Ranta tace anya kuwa bazan hakura da auren nan na DEENi na hutawa rayuwata ba .
wai ace mijin da zaka aura ne" ya zame maka tamkar wani ma'alaikan daukar rai ko wani dodo .
Kuka take sosai tana , addu'a neman Zabin Allah a game da auranta dashi .
darajar nafilar data kwana tana yi ne .
yasa washegari ta tashi sakayau daita cikin nishadi da farinciki "
ba kmr ko wace safiya ba .
duk da bata da wani kuzari da walwala. Amman hakan bai hana jin dadi ba.
kitchen ta nufa kai tsaye dan hada masa breakfast kasancewa weekend ce .
" byn wasu yan mintina ta kamla da komai na break tashirya dining . Cikin haka ummi ta iso parlour ta zauna kan dinning table tana yi mata sannu , murmushi tayi tare da koma kusa ummi ta zauna" ta sheida mata ta gama komai .
tana jinsa yashigo yana gaida ummi fuskasa a daure kmr kullum.
Sanye yake cikin dark blue t shirt da wando jeans . ummi ta amsa masa cike da fara'a ka tashi lfy ya dan saki fuska kadan Yace lfy lau na tashi first lov kujera ya zauna . a tsorace itama zeenat din ta gaishe shi ,ya amsa mata a ciki batare daya kalli inda take ba.
,ummi Tace ya..ya .ayi serve din ka ne ? Ya hade rai yaki yin magana .
da kai fa nake a zubo maka abinci ne ta sake maimaita wa ?
Ya dan dubi ummi a shagwabe Yace bana ci.
ummi ta Gane tmbyrta da tayi masa ce ta hassala shi .
dan haka sake bi takansa ba da kanta ,ta zuba mishi komai da'aka girka ta turo plate din gabansa ,tare da dungure masa kai " gashi nan miskilili sarkin zuciya Yace to ni ta yaya za'a tmbye ni ko zanci abinci " byn ansa zanci din "
ummi tayi murmushinsu irin na manya Tace uhmmmm DEENi kennan halinka sai kai "Allah ya canza maka wannan budadden halin naka " Ameen yace tare da kai spoon bakinsa .
parlour ya dauki shr baka jin motsin komai baya ga karar spoon din zeenat .
juyawa spoon din kawai take takasa kai ko loma daya bakinta sakamakon cika wajen da DEENi yayi" duk da tasan hankalinsa da idanunshi ba'akanta suke ba .
tayi shr ta fada cikin duniyar tunanin abinda ya shafeta km yafi damunta.
Wanda a halin yanzun Bai wuce aurenta da DEENi ba .
domin kuwa tana matukar jin tsoron zama dashi ba dan komai ba sai dan tsoron azabar da zai dinga gana mata a gidansa.
hankalinta kan tashi a duk sanda ta tuna da hakan.
Ahankali Ummi ta ajiye spoon din hannuta tare da zuba mata ido kawai tana binta da kallo tarasa meke damun Brain dinta a cikin kwanakin nan .
kusan minti goma ta dauka tana kallonta batare da ita zeenat din tasani ba .
Zeenat .....ummi takira sunanta a frigice ta juyo tana kallon ummi ,ci abinci abinda ummi ta iya cewa kennan .
DEENi dake zaune haushi kmr ya kashe shi tsaki ya dan ja ,ummi ta juyo bangaren sa Tace lfy kai km ?
Fuskarsa a dakune Yace babu , Sai da taga Ummi ta sake dubeta sannan tasoma cin abincin , shima bawani sosai .
Byn sati biyu
Shirye shiryen bikinsu zeenat aka soma sosai ba kama hannu yaro.
,anshirya komai na al'adar hausa kmr sabbabin dinkuna da gyaran jiki komai km tare akeyi musu ita da shemah km iri daya.
musamman ummi ta dauko kwararriyar mai gyaran jikin daga india domin ta gyara mata tilor diyarta da kyau.
duk wani gata da uwa zata yiwa diyarta "ummi tayiwa zeenat shi .
shima mahaifin zeenat din yayi iya bakin kokarin Sosai .
a nyi kamu amare idan aka feshe su da turare masu dadin kamshi na mutune India wanda duk wacce ummi ta dauko ta gyara zeenat din ce tazo dashi.
Anyi musu murzar lalle da kitso .
amman ansha fama da zeenat gurinyin kitso dan cewa tayi ita sam na attachment ,zatayi .
sai da ummi ta bude mata wuta sosai tare da cewa ,zata sanarwa DEENi tukun ta natsu .
Sau ran kwana biyu daurin aure mutane India suka iso , kusan mutum ashirin maza da mata sosai aka shiga hidimar da ,baki.ummi taji dadi Sosai dan kusan duk shakikanta ne suka zo wanda km shine zuwansu na farko Nigeria idan .
,gabadaya gidan nasu cike yake da baki dan haka ba kasafai zeenat din take zama a part dinsu ba ,tana can gidansu shemah .
Zeenat Tace dan Maryam muje kirani part dinmu ina son naga ummi yau duk banganta ba .
, Maryam Tace gaskiya na gaji da yawa wlh kije kawai . zeenat ta ja saki Tace dan Allah muje kiraki ni yanzu zamudawo.
shemah dake kwance ta mike zaune tace muje na rakaki kinsa halin Maryam da maseefar son jikin tsiya.
, Mikewa sukayi har sun fito sai ga Maryam Tace wlh baza kubarni ni kadai ba , zeenat tace ke km kika sani " idan zaki muje .
Tare , suka nufo part dinsu zeenat.
tafe suke suna hira irin tasu ta amare daga nisa zeenat ta hango motar DEENI parke a kofar part dinsu "daga gefe .
" can baya km motar fk ce sai wata motar daban wanda batasan ko ta waye ba .
Jingine yake jikin motar shi yana amsa waya sanye cikin English wear's black jeans da rigar ashi colour "mai gajeren hannu wanda ta fidda ainihin kyaunsa da gargasan gashin jikinsa dake kwance kan Gabar hannushi .
idanunta fes akanshi tana binshi da wani irin kallo saboda yadda taga yakara yi mata kyau. fuskasa har wani shekin annuri take fitarwa kmr ance ya dago idanunshi suka hada idanu.
da sauri ta dauke idanunta wani abu ta dinga ji yana tsirga mata ajikita. sai taga ya fita daban cikinsu fk duk da bawani kallonsa tayi sosai ba .
ta sake dago idanunta da niyar sata kallonsa suka sake hada ido harara ya sakar mata , kallo daya ya sake yi mata ya kau da fuskarsa gefe yacigaba da wayarsa a kallo dayan da Yayi mata yane yadda jikinta ya tsanyi .
kai tsaye zeenat taja hannun Maryam wacce tafi kusa daita ta juya da sauri ta karya cona itama shemah ganin haka yasa tabiyo bayansu da sauri tana jin fk na kiranta . shemah Tace yazaki biyo damu tana km.
zeenat Tace bbu komai mu bi nan di yafi sauki .
ta bayan part dinmsu suka shiga , da ummi tasoma cin karo ta rungume tana sakin ajiyar ,ummi tace meyye haka ?muryata kmr mai shirin yin kuka take Haba ummi yau fa duk banganki ba ,baki ga har wata rama nayi ba " tayi murmushi tace lallai kam kin rame dan ga natsuwa nan suna bikin dariya mutane dake tare da ummi suka shiga yi .
Ummi tayi gaba zeenat nabiye daita tana zuba mata shagwaba.
shape shape tayi abinda zatayi suka bar gidan .
Ranar daurin auren da safe ta nufo gidansu dan dauka kayanta dazata saka .
wanda ta manta bata hadu dashi ba cikin kaya .
,tafe take tana sauri . yayinda su ya faruk da abonkan DEENi ke tsaye duk cikin shirinsu na zuwa daurin aure .
amman banda DEENi wanda dagani shi suke Jira .
Wani irin kunya ce taji takamata dan haka ta dan janyo gefen mayafinta ta rufe fuskarta ,tana jin yaya faruk nacewa amaryamu ki bude idanunta kada ki fadi mana .
amman ina ko waiwayo batayi ba tacigaba da tafiyarta ta kofar baya tabi yauma.
tashigo dogon parlour'nsu ta baya kennan tasoma jiyo kamshin turarensa kafin tayi kokarin bude fuskarta taji sunyi karo da mutun .
da sauri takarasa bude fuskarta "yaya DEENi ne wanda zai fito har wayar dake hannushi ta fadi .
,gabanta ne yayi wani irin faduwa dan har wani juya juya ta dinga ji da sauri ta tsugunna dan miko masa shima ya tsugunna da zai dauka a tare hannunsu yakai kan wayar ,wani irin shock ne yajata " wanda baita kadai ba har shi DEENi yaji abinda taji.
Wani iri shima yaji ajikinsa tamkar an jona masa lantarkin .
. Shine yasoma kokarin janye hannushi daga kan nata ,ahankali ta Miko masa wayar batare da ta mike ba hade da cewa kayi hakuri dan Allah .
komai Bai iya cewa ba baya ga amsar wayar da Yayi ya barta nan tsugunne.
Bayansa tabi da kallo yayi matukar yi mata kyau har batasan yadda zata misalta ba sanye yake cikin shadda fara kal sai kamshin yake zubawa .
gabadaya kamshin turarensa ya gyaraye dogon parlour'n .
Ahankali zuciyarta tasoma bugawa tamkar zata basa kirjinta ..
girgiza kai kawai tayi dan batasan wani irin aure take shirin yi ba haka ta juya cikin sanyi jiki tabar gurin tana shiga ciki.m mutane akama kiranta da amarya amarya kinsha kamshi ita dai bata iya cewa komai ba dan gabadaya jikinta a sanyaye yake .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 27-28
Part din cike yake da abonkan arzikin da en'uwa ,Ummi
Jikinta a sanyaye ta dinga ratsa mutane dake ,zaune a parlour ' har ta iso dakin ummi , da idanun take bin en dakin da kallo .
kozata ga ummi ganin bata alamunta bane , yasa tmbye matar uncle din Inda ummi take.
tace yanzu tashiga bathroom .
Ahankali ta fidda numfashi tare sauke ajiyar zuciya .
cikin haka ummi ta fito tana ganin zeenat din.
ta bata fuskarta "ta zauna tana dubanta"
gefen ummi zeenat tasamu ta zauna fuskarta dauke da murmushi wanda da Gani na karfin hali ne .
Cikin kasa da murya ummi tace yana ganki haka ina kayanki ?
Cikin sanyi jiki zeenat tace shi nazo dauka .
,ummi tace ke dai kin cika shiririta wlh "
komai baza kiyi shi cikin sauri da kazar kazar ba kin dinga jan jiki kennan ,kmr wata mage .
Alhalin kin san halin wanda zaki aura " dan oya oya ne .
jin haka yasa jikin zeenat din sake yin sanye, tare jin wata irin faduwar gaba " zuciyar ta dinga dokawa da sauri tamkar baso kirjinta.
ahankali tasa hannuta ta kamo na ummi
cikin nata jikinta har rawa yake hade da rage murya tamkar mai shirin zubda kwalla tace dan Allah ummi kiyi hakuri kinji karkiyi fushi dani ,zan canza inshallahu Amman " kimin addu'a .
wlh tun sanda aka samo shirin bikin nan nake jin faduwar gaba wanda narasa dalili .
ummi ta tayi shr tare da zuba mata idanu kawai tana kallonta .
tausayinta ne ya sake kamata , ,duk sai taga takara ramewa ba kmr kwanaki ba hakan yasa taji ba dadi aranta.
, ahankali ummi ta mike tare da riko hannuta tayi cikin , bedroom daita. En dakin suka bisu da kallon sha'awa duk da basu ji maganarsu ba Amman sun birgesu .
,Har suka shigo bedroom din Ummi na rike da hannuta Ta zauna daita tana rarrashita kan ta kwantar da hankalinta fargaban aurene kawai ke sata jin faduwar gaba Amman bbu abinda zai faru inshallahu "
Ummi da kanta ta shirya diyatata cikin wata arniyarta geziner ligth blue sai daukar ido take da kamshi tare da fesheta da turaruka kala kala masu sanyi kamshin take zeenat ta fito amarya sak .tayi kyau sosai
Ummi ,ta dauki waya tayi mata hotuna sannan takira Maryam tace tazo ta tafi daita din .
Kwanciyar tayi flat a kan gadon su shemah tana kallo da sauraran duk abinda ke faruwa .
a cikin dakin dake cike da en mata da kawaye
abinka ga mai yawan kawaye " da mutane kala daban daban " yasa dayawa wayan dake cikin dakin kawayen zeenat din ne .
gyara kwanciyarta tayi idanunta na kallon celling dakin hannuwanta duk rungume da kirjinta yayainda zuciyarta ke cigaba tsalle tamkar zata fasa kirjinta ta fito waje.
ahankali ta runtse idanunta sanyi taji yana ratsa koina a jikinta duk da tarin fargaban dake tattare daita hakan bai hanata jin jikinta yayi mata nauyi ba .
Tana ji ajikinta burinta da dokin son auren DEENi .
duk babu shi ahalin yanzu sakamakon fargaba da tsoron kasancewa tare dashi a muhalli daya .
Ta dauki lokacin mai tsawo kwance yayinda ta dinga jin wani iri ajikinta .
Bugun zuciyata na sake karuwa.
ta dinga kokarin ganinta ta cire damuwar dake damunta wanda a zahirance ita ta daurawa kanta .
har yanzu da take kwance jikinta a sanyaye yake takasa tabuka komai.
idanunta ta runtse tana cigaba da sauraron hirar dasuke sama sama .
10:30
Karfe goma da rabi daidai na ranar lahadi Allah ya cika alkawarinsa domin dimbin, jama'a sun shaida daurin auren NASURULDEENI ALIYU BELLO da MUZEENAT HABIB BELLO" daurin auren daya tara manya attajirai da kusoshin gwanati hade da maikata
bakaramin farinciki family din muhd bello suka yi ba ganin sun kara karfafa zumunci a atsakaninsu, .
dan haka farincikisu ya sake karuwa takoina ka juya , family din murna ne cunkushe a fuskokinsu
Zeenat dake kwance har lokacin tana saka da warwara still jikinta a sanyaye yake takasa kwakwaran motse .
zuciyarta fall da fargaba musamman lokacin da taji hayaniyar mutane ta cika gidan alamun an daura aure, en'uwa nata shigowa ana gaisawa , ajiyar zuciya dumin hawaye taji yana bin kuncinta shikennan ta faru takare tana matukar son deeni Amman tana jin tsoron zama dashi hayaniyar mutane take sake jiyowa hakan yasa jikinta ya dauki kirma,kirrrrrr... sam ko kadan bbu wanda ya lura da yanayinta.
Sai ma tashi sukayi suka fita waje km har sanda suka fito tsakar gidan suna ta daukar hotuna bbu wanda ya lura da yanayin da suka barta .
" Maryam ce data karaso wajensu taga suna ta hotuna bbu ita yasa tashiga dakin dan dubota dan kusan tana lura daita tun jiya tamkar mara lfy .
kwance ta tadda ita tana fidda numfashi sama sama .
Da sauri ta karasa inda take bbu abinda jikinta keyi sai fidda hucin zafi, a rude ta dinga takiran sunanta zeenat ... zeenat daman bakida lfy ne?
Kai kawai ta iya girgiza mata alamun eh da sauri Maryam ta mike ta nufi part din ummi tasanar mata .
tare suka dawo gurinta da wasu en'uwa ummi guda biyu .
zuwa yanzu jikinta ya tsananta zafi tare da karkarwa .
ban da salati bbu abinda ummi keyi da sauri takarasa kusa da zeenat din ta zauna tare da riko hannuta" may zan Gani , haka ni fadeela ?
, zeenat kina son ki kashe min kanki ne ?
Ko yaya ,
Alhalin kinsa ke kadai gareni duk duniyan nan km ke kadai debimin kewar er'uwarta dana rasa , bazan iya jurar rashinki ba dan Allah ki tausayi min mamana.
sai km hawaye shar shar daga idanun ummi sosai Ummi ke zubda kwallar tausayi diyarta ganin yadda ta fita haiyacinta cikin lokaci daya .
Ummi tace zahra kamama min ita dan Allah .
su aunty suka mata zeenat sukayi part din Ummi daita .
kai tsaye dakin DEENi ummi tabada umarnin a wuce daita.batare da bata lokaci ba ummi
takira family doctor dinsu .
sannan takira DEENi tace yasameta a dakinshi yanzu yanzu .
Doctor bai dauki wani lokacin ba" sai gashi yana zuwa yasoma duddubata tare dabata taimakon gaggawa .
ummi ta dubi doctor hankalinta a tashe tace doctor meke damunta ?
doctor yace bawani abu bane damuwace kawai tayi mata yawa "amman inshallahu zata. dawo daidai .
A gaugauce DEENi yashigo byn amsa kiran Ummi .
yana shigowa dakin mutane suka dan ragu .
ahankali yakaraso kusa da Ummi ya tsaya yana tmbyrta abinda ke faru sai data ja numfashi sannan ta nuna masa inda zeenat din ke kwance tace zeenat ce ba lfy sai lokacin idanunshi suka kai gareta kwance take akan bed dinshi an lullubeta da bangon rufarsa.
shr yayi tare da zuba mata rikitattun idanunshi.
Daddaden kamshin turarensa tasoma juyowa may matukar sanyi ahankali ta dan lumshe idanunta .
Taku daya zuwa biyu yayi yaja ya sake ya tsaya" sannan ya dubi inda ummi ke tsaye yace me doctor din yace yana damunta?
, doctor din still ya sake mashi bayani kmr dai yadda yayiwa ummi . ahankali ya sake mai idanushin kanta yana cigaba da kallonta wannan shine karo na farko daya tsaya ya Kare mata ,
, sosai kamshin turarensa ke sake kaiwa hancinta farmaki tare da susuta mata duk wata gaba dake jikinta .
.
jikinta da zuciyata suka dauki rawa wani zazzabi mai zafi yayi nasarar sake rufeta sakamakon idanushi dake yawo a gangar jikinta .
Da sauri doctor ya nufo inda take" deeni yasa hannu ya dakatar dashi alamun kada yakarasa gareta" dan wani abu yaji yana taso masa sanda doctor ke masa bayanin abinda ke damunta , tamkar ya auna doctor waje dan takaicin abinda ke cin zuciyarsa.
ganin haka yasa doctor din yace a samo ruwa da towel a goge mata jiki dashi dan tazo daya dubata yaji yadda jikinta ya dau zafi yace zai je ya dauko magani ya dawo cikin sauri ya fice dakin .
A ranta tace doctor dama kayi zamanka dan maganinka kadai ba zai taba min maganin damuwarta ba .
dan ita kadai tasan abinda ke cin ranta .
Wanda tun daga cikin zuciyarta take jin yake taso mata .
tare da haddasa mata tsoro da faduwar gaba.
Tsaye yake har yanzu sai suke hanuwanshi duka da Yayi cikin aljihun wandonsa.
ahankali yasoma takowa zuwa bakin gadon km idanushi akanta.
cikin sanyi ya yaye bargon da aka lullube mata jiki dashi. idanunshi fes akan fuskarta dake lumshe tayi fayu sannan km takara rame sosai ahankali ya daura hannushi saman goshinta .
jin yadda goshinta ya dau zafi da yadda take fidda numfashi sama sama yasanyashi kai hannushi da sauri jikinta.
take yaji abinda ya sake frigitashi .
zafin dake jikinta ya ratsa tafin hannushi" wanda bai san sanda tausayinta ya lullubet shi ba ya dinga jin wani abu na tsigar wa ajikinsa , ya juyo tsaitin Maryam yana harararta yace tsayuwar me kike anan da sauri ta fice daga dakin bata fi minti uku ba Sai gata ta dawo da ruwan ahanunta jikinta na rawa.
azaton zeenat ummi ce ko auntyta zasu goge mata jiki ,amman sai taga DEENi yakarbi robar ruwan a hannu maryam .
Gabadaya suka fita daga dakin har ummi "tare da kulle masu dakin .
Cikin sanyi jiki ya tashi ya dawo gabanta har yanzu sanye yake cikin shadda fara tas sai kamshin turarensa ke tashi a dakin .
ahankali ya cire farar hular shi ya ajiye gefe sannan yasa hannushi duka ya tattarota jikinsa yaja zip din rigar kasa ya zare rigar jikinta ya ajiye gefe ,take jikinta ya sake daukar kirma gabanta yacigaba da faduwa .
tsoro da mamaki suka taru cika zuciyarta. aranta tace wayyo nashiga uku me yaya ke nufi da cire min riga ? yana nufin shi ,zai goge min jiki .
tana ji tana Gani ya cire mata kayan jikinta tsab har bra dinta .
ta rage daga ita sai zani iya cibiya ,sannan ya zauna tare daurata a saman cinyarsa" ya juyo daita suna facing juna taso tasa hannu ta Kare kirjinta amman kasancewar jikinta bbu kwari yasa takasa aiwatar da komai "dan haka ta runtse idanunta gam.
tana jiran taji ruwa ajikinta Amman sai taji shr ahankali ta dan bude idanunta ,DEENi zaune idanunshi kyam akan kirjinta .
da sauri ta maida idanunta ta rufe dan frigice da tsoro ya dauko towel din ya matse sannan yasoma goge mata saman jikinta zuwa kirjinta da fuskarta , ya dimauce da ganin halitatta kirjinta ,hakan yasa yafi goge mata gurin a tare suka dinga sauke ajiyar zuciya .
can yaji ana nouking din dakin yayi sauri ya mayar mata da rigarta sannan yabada izinin shigowa.
doctor ne yashigo da ledar magunguna ahannushi Yace abata abinci taci tukun sannan tasha maganin.
byn tafiyar doctor DEENI yakira ummi Yace akawo tea, en'uwa dayawa suka shigo dakin "ummi da matar uncle din zeenat ,Maryam har ma da shemah . suka dinga jero mata sannu.
byn sun fita ne taji tamkar kar su fita dan bata son abarta daga ita Sai shi.
hakan na sake frigita zuciyarta .
kadan tasha tea din tace takoshi bai wani takurata ba ,ya ballo magani ya Mike mata ba musu tasa hannu ta karba tasha ,dan tasan halinsa ciwonta bazai hana ya jibgeta ba .
Shiya gabadaya a tsorace take dashi.
MMN SUDAIS
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 29-30
Byn tasha magani . komawa tayi ta kwanta lomo ajikinsa' tana sakin numfashi sama sama wani iri taji ajikinta lokacin data tsinci kanta kwance kan tattausan jikinsa .
ga kamshin turaren jikinsa gyaraye dana dakin sun buwayi hancinta .
ji take tamkar sukasance haka har abada.
, ahankali tasoma lumshe idanunta har ta rufe su rufff..
bacci ne may nauyi Yayi nasarar daukarta acikin mintina da basu wuce goma ba .
Kyawawan idanushi masu matukar haske da daukar hankali ya zuba mata.
Tare da Kare mata kallo wani zirrrrrrrr ya dinga ji ajikinsa" lokacin daya jita lefe a saman kirjinsa .
da kyar yake jawo numfashin yana fesarwa.
hannushi ya sake kaiwa wuyanta har lokacin jikinta da sauran hucin zafi.
janyota jikinsa ya sake yi .
Tare da ,yasanya hannuwansa duka ya rungume tsam tsam ajikinsa "yana fidda numfashi .
tare da fatan samun saukin zugin da zuciyarsa ke masa wanda shi kansa yarasa dalilin haka.
" Har lokacin bacci take rungume ajikinsa suna musayar numfashin juna mutuwar da jikinsa yayi ne yasashi sake zuba mata rikitattun idanunshi tsawon lokaci yana kallonta
Da kyar yasamu yayo control din kansa cikin sanyi jiki ya zareta daga jikinsa ya kwantar daita ya sake lullube ta da blanket ,sannan ya Mike tsaye yana karkabe jikinsa.
,rigar jikinsa yasoma cirewa ya saura daga shi Sai farar single da wanda shadda.
Wordrob dinsa ya bude ya dauke wasu kayan da zai canza " tare da yashigewa bathroom .
Dakin ya sake dawo byn yagama shirya kansa , cikin farin yadin voyal may matukar taushi da daukar hankali.
Agabanta ya tsaya yana makale links din gaban rigarsa yayinda idanushi ke kanta yana cigaba da kallon fuskarta.
Ahankali ya dinga jin reaction din jikinsa na sauyawa ,yayinda zuciyarsa ke beating tana tsalle tamkar zata bafa masa kirji . wanda shi kansa yarasa dalilin dayasa shi jin haka.
Ahankali ya dauke idanushi a kanta sakamakon
, ji yayi "ana nouking din dakin "yabada umarnin ashigo batare daya tmbyi kowaye ba .
Maryam ce tashigo da sallmarta .
ta gaidashi ya amsa mata a dake .
Cikin sanyi nan nasa
Yakarasa gaban mirrow ya dauki agogon ya daura a tsintsiyar hannushi tare daukar kwalbar turaren ya feshe ilahirin jikinsa ta cikin mirrow din yake wa Maryam magana cikin dakakiyyar " muryasa ki kula daita idan ta farka .idan kika ji zazzabi bai sauka ba ki sanar da first lov ,a tsorace tace ta amsa masa da to...
yana fita ta bi bayansa da kallo cikin ranta tace wayyo zeenat na tausaya miki auren wannan maseefaffe .
,Sai kinyi hakuri da wannan budadden halin na shi .
gefen gadon takoma ta zauna tana sake jin tausayin zeenat din a ranta .
Sosai zeenat tayi bacci baita ta tashi ba.
Sai gaf da magariba.
ji da Maryam tayi jikin zeenat din bbu zafi ko daya .
yasa ta sanarwa da aunty zahra .
Su Aunty zahra suka sata tayi wanka da sallah .
tana zaune akan prayer mat "duk jikinta a mace taji sunce tunda jinkinta da sauki tashiyar akaita tayi sallama da Ummi.
fuskarta cike da tsoro ta dubi aunty zahra tace dan Allah aunty karku kai ni wani guri wlh bani da lfy ..
aunty zahra tace A'a kiyi hakuri yanzu za'a kai ki gidanki kya ji sauki a can.
tana kuka tana komai aka shiryata cikin wata geziner mai ruwan kasa ,Sai kamshi ke tashi ajikinta kai tsaye gurin ummi aka kaita ta mata nasiha mai ratsa jiki ,sannan takara da ce mata takasance may tsananin tsafta da girki domin sune manyan makamai dake kara karfin aure .
Sai km hakuri ,kiyi hakuri kiyi hakuri mamana da duk abinda zaki Gani.gidan aure bbu komai acikknsa Sai hakuri .
Km hakuri shine jigon zaman aure .
duk wata mata da kika ganta zaune gidan mijinta ,hakuri take yi
dan haka ki kula da kyau kinji mamana .
Zuciyar ummi ta tsinke tayi rauni Sai km hawaye shar shar......suka soma zuba , en'uwa ummi da suka zo daga india sukai taba hakuri suma sunyi mata tasu nasiha Sosai .
, ita dai zeenat bbu abinda ummi ta fada wanda bai shiga kunneta ba .
tare da kukan tausayin kanta .
duk sanda ta tuna yau , za'a kaita gidan deeni hankalinta ne ke sake tashi .kuka sosai take har da majina .
ganin irin kukan da zeenat din ke yi yasa ummi kiran deeni a waya .
Byn yan wasu yan mintina Sai gashi yashigo da sallama ,mutane dake zaune a dakin .
suka fita gabadayansu dan basu waje .
Ahankali yakaraso cikin dakin sosai, ya durkusawa gaban ummi yayi zaman dirshan har da tankwashe kafafunsa. ganin haka yasa itama zeenat tazamo " tayi irin zaman da yayi a gaban ummi" Sai dai ita zuciyarta da gangar jikinta cike suke da rauni.
badan namijin kokarin datakeyi ba da tune zuciyarta ta buga tsabar frigici.
Ummi tayi shr tare da zuba musu idanunta da suka gama canza kala saboda kukan datayi.
Tsawon lokaci tana zaune ta tasa su gaba tana kallonsu kafin daga baya tasoma magana
cikin sanyi muryata ta Kira " sunansa NASURUDEEN...... ahankali ya dago idanunshi yana duban umminsa dasu batare daya amsa ba .
Sai dai yadda takira sunanshi din ya girgiza zuciyarsa domin ya manta when last da yaji takira complete name dinshi haka .
Dan haka ya tattara dukkan hankalinsa da natsuwarsa gareta .
Cikin sanyi murya data sha kuka tace DEENi ga zeenat nan ta sake dawo gareka" a karo na biyu . Sai dai wannan karon yasha bamban da sauran lokuta .
'wanna karon ta dawo gareka ne da matsayi guda biyu ,kawarka km matarka .
zan ji matukar farinciki da kwanciyar hankali idan kuka hada kanku ,kuka zauna lfy.
, zeenat yarinya karama kayi hakuri daita" duk wani abinda ta maka wanda bai yi maka ba , ka sanar min .
Ni Zan fahimtar daita ta hanyar da zata gane .
Ban yarda da duka ko zagi da cin fuska ba .
Kuka zeenat din keyi har lokacin shi kansa ya tsausaya mata matuka
Ga mamakin DEENI Sai ya ga ummi itama ta sauko gabansu hawaye ne ke bin fuskarta wani nabin wani ,a rude deeni yasa hannushi yana share mata hawayen .
Cikin tsananin tashin hankali Yace dan Allah first lov ki daina zubda hawayenki haka , kiyi hakuri "zubda hawayenki bakaramin maseefa bane atattare dani " idan har yanzu bakya son aurena da zeenat ne wlh ashirye nake dana bar miki ita har abada .
Cikin kuka ummi ta girgiza masa kanta ba kukan komai nake ba DEENI facce na tsantsar farinciki .
Farinciki ne yamin yawa har yasani zubda su.
,ta janye garesu byn ta dauke hawayen idanunta.
kama hannun deeni dana zeenat tayi "ta hade su waje guda tare da daura nata hannu saman nasu .
Nagodewa Allah daya nuna min wannan rana may cike tarin farinciki mara misaltuwa , zeenat ga deeni nan nabaki shi amana har abada banida kowa Sai shi.
ki zauna lfy dashi cikin amana "deeni kaima ga amanar zeenat nan naba matukar ka cuceta "ban bazaka ji dadina ba. Dan Allah Ku kula da junanku .
Ku rike min amanar junanku " ku kadai gareni byn Allah banida kowa Sai ku.
abinda tata fada kennan tana sake hade" hannuwansu waje daya .
Duk yadda yaso daurewa zuciyar kasawa yayi sakamakon ,kaunar zeenat din da yake hangowa karara a cikin idanun umminsa.
bai so zeenat din taga kasawarsa " dan haka ya kife kansa kan hannun umminsa ya sumbata cikin dabara ya goge kwallar idanunshi. zuciyarsa ke kwabarsa akan alkawarin da umminsa ke so ya daukar mata " shi kadai yasan abinda ke damun zuciyarsa , aranshi ya dinga ayyana abubuwa masu tarin yawa"anya kuwa zai iya daukar alkawarin nan ....
jikinsa yayi masa nauyi tausayin ummin ya sake mamaye zuciyarsa. muryasa a sanyaye yace ummi ki kwantar da hankalinki inshallahu bbu abinda zai faru zan riketa amana yayinda a cikin zuciyarsa yake sauya kudirin ,ma,anar na karba dan kada Allah ya tuhumeshi gobe kiyama.
Yayinda ta kasa km hannuta dake cikin nashi yake ta murzawa ahankali cikin wani irin salo da yake sa tsagar jikinta tashi .
saboda nata hannu na kife ne cikin nashi tafin hannun.
gabadaya jikinta yayi tsanyi yasoma rawa rawa "dan samun saukin hanyar tsira da son cire hannuta cikin nashi" yasa tayi saurin cewa na karba alkwarin ummi inshallahu ni dai addu'arki kawai nafi bukata "
.cikin sanyi ya sakar mata hannu ..
Allah sarki ummi wani irin farinciki ne gyaraye da tsantsar kaunar ya mamaye zuciyarta . murmushin jin dadi ta dinga yi .sannan ta mikar da zeenat din tsaye ta rungume ajikinta . Tace Mamana ina miki addu'ar km bazan gushe wajen yi muku addu'a ba Allah ya muku albarka ,ya azurtaku da ya'ya masu albarka.
Da kyar su aunty zahra suka rikota sakamakon rukunkume ummi da zeenat din tayi .
sun fito tsakar gidan dake cike da mutane .
Wanda ,Yawancin duk en'uwa ummi ne da kawayenta.
Kai tsaye gidan mahaifinta aka kaita shima nasiha may tsara jiki yayi mata sosai da nuna mata tayi hakuri ta kula da mijinta , tamkar yadda mahaifiyarta tayi. yace naji dadi kwarai da deeni yakasance miji agareki,ina muku fatan alkhari .
Ina da yakini deeni zai rike min ke da amana .'
da baki duk wata kulawar da ta dace.
Ahankali take cigaba da kukanta.. aranta kuwa cewa tayi uhmmmm.
abba bakasan asalin halin deeni bane .
shiya ka fadi haka.
,halinshi na zahiri kawai kasani bakasan na baniba.
yace ta daina kuka duk abinda take da bukata karta zamo may rokon miji ta tmbye shi zai mata .
,har gidan big dady Sai da aka kaita agurguje suka dawo gidan kafin motar daukar amarya tazo.
may gyaran amarya ce ta sake mata sabon gyara na musamman zeenat din ta sake fitowa fes abinta .
Sai sheki take zubawa ga wani irin kamshi na musamman dake tashi ajikinta .
Duk da cikin estate din zata zauna hakan bai hana motocin abokan deeni dana fk cika kofar gidan ummi ba .
Dan daukar amare .
Shemah aka soma saukewa , sannan zeenat aunty zahra ,ke rike da hannuta fuskarta rufe cikin mayafi" har cikin gidan ta umarceta da tashiga da kafar" dama tare da yin Bismillah " tayi kmr yadda aunty'n tace.
sannu ahankali har suka iso dakinta ta zaunar daita akan gado.
nan da nan mutane suka cika gidan dan ganin dakin amarya .
ahankali zeenat ta dan bude idanunta da suke rufe " tana kallon irin dukiyar da Ummi ta narka mata a daki wanda take jin ko mahaifiyarta ce a raye .
bazata iya mata kwatankwacin haka ba , dan ma tsayawa bada labarin irin kayan da Ummi ta zuba mata a dakin ma bata lokaci ne ..
Zaune dake a gefen laulausar zanin gadonta ta cure waje daya sakamakon tsaron daya cika . Ahankali ta kai idanunta kan agogon dake manne da bangon dakin" Karfe goma shada ta buga daidai"atsorace ta saki ajiyar zuciya saboda wani sabon tsoro dataji yana kawo mata ziyara.
A ranta tace kar dai deeni barinni zaiyi in kwana ni kadai.
aiko idan haka ta kasance da nashiga uku dan a gaskiya bazan iya kwanta ni daya acikin gidan ba .
Yan kawota basu minti goma da tafiya ba.
taji saukar yayyafi sama sama wanda ya hadasawa yanayin garin yin tsanyi hade da kamshin kasa.
" ruwa bai yi yawa ba haka nan yayyenfin bai tsaya ba.
Kusan tun lokacin da suka tafi suka barta anan take zaune bata ko motsa ba Sai yanzu datayi tunanin deeni na iya barinta ta kwana ita kada . Hakan yasa ta Mike cikin tsoro ta kulle kofarta ta dawo ta zauna ,zamanta ke da wuya .
Tasoma jiyo Hayaniyar muryoyin maza daban daban" a cika gidan hakan yasa taji tsinkewar zuciya .Tare da faduwar gaba da .
hankali ta runtse idanunta tana jin yadda zuciyarta ke dukan uku uku kmr zatayi tsalle ta fito waje .
Deeni tsaye a parlour'n yayi babbake tare da dakatar da abonkansa .
yace to to....Nagode sosai da kulawarku.
rakiyar ta tsaya iya nan..
ba Sai kunshiga ba.
fahad ne yayi murmushi sannan Yace ko baka fada ba ma anan zamu tsaya.
,muma bashiga zamuyi ba .
,dan an dade da daina wannan .
Shr tayi tare da kamkame jikinta waje daya tsoro ne ke sake kawo mata ziyara .
tun tana jiyo hayaniryasu sama sama har tadaina taji dif...alamun basa cikin gidan sun fice .
Juyawa suka sake yi tare ya raka su , fahad na ta mishi tsiya iri iri
Cikin sauri sauri "gudu gudu yashigo parlour sbd ruwan daya sake yin karfi duk ya jike masa farin yadin dake jikinsa .
Ya tsaya kulle koina .
Ahankali ya murda handle din kofar dakinta yajita a kulle .
Ganin alaum murda kofa yasa ta sake mikewa tayi taje ta bude masa .
Tana may sunkuyar da kanta kasa .
.cikin sanyi jiki ya shigo dakin tare da rungumeta tsam tsam ajikinsa da hannushi daya "sannan ya ajiye tarin ledodin dake hannushi kamshin dake dakin kawai ya isa yasa kagane rana ce ta musamman....
0 Comments