auren sirri 4

 AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 13-14




Bangane fita zakayi  ba byn ko breakfast bakayi  ba ina fa hankalce dakai fa  duk kwanakin nan bakason  cin abinci,  

ina  zaka ma tukun danaji kace fita zakayi   naga week end ce  yau .ta hade fuska ta mau hade da zuba masa idanunta.

Ya dan yi murmushi gefen baki har  dimple dinsa ya lotsa" kyaunsa ya sake bayyana" ya mike daga kan cinyarta ya zauna sosai shima  yana kallon yanayin  umminsa"  yana jin yadda soyayyar Ummi nasa  fiyye da komai nasa  "yana sonta baya son damuwarta itace duniyarsa sannan itace ke  tattare da duk wani farincikinsa  tana tsantsar " son  shi da nuna masa duk wata kulawar da uwa kadai zata iya yin haka  .


Hannuta yakamo duka cikin nasa ganin yadda ta damu muryasa a sanyaye  kmr koda yaushe  yace am so sorry my first lov muje zanci tayi murmushi tace kai ko hade da  dan dungure masa kai "dan bazata iya fushi dashi "shi kadai Allah yabata " batada. Kmr sa  duk duniya  . Cikin dan daga murya  Ummi   tayi kiran  zeenat .

 DEENi ya  yamutsa fuskar sannan ya langwabar da kai   yace kibarta kawai  "first lov .

ki zuba min da kanki nafi son naci dagareki dan ma banson wahalar dake ne ma  da sabon girki zaki min yakarasa fadar  maganar cike da shagwaba " ummi ta dubesa ta sake yin dariya tace  Allah yashirya min kai  yace Ameen  yana kashe mata idansa .


byn yagama cin abinci duk da bawani abin kirki yaci ba "Amman hakan yatiwa ummi dadi ko bakomai ya dan saki ranshi ba kmr  kwanaki ba"  wayarsa ce ta sake  karade parlour da  kara wanda tun soma cin abincinsa  yake jin kukanta  "Amma ya" share.

 ahankali yasa hannu ya  dauki wayar  yana kallon screen din " sunan FK yagani rubuce yana wayo "tabe baki  Yayi kana ya  manna wayar da kunnenshi , , FK najin alamun an daga wayar yace Yayi angon zeenat da girma "kujerarka . DEENi yaja tsaki yace ya'akayi  ne" sarkin matsala.


  bangaren  FK kuwa shekewa Yayi da  dariya    sannan yace ina waje ina jiranka fa dan  banson nashigo muyi westing time dan nasan halinka da son jikin tsiya " shima DEENi  bay wani damu da shigorwasa ba  dan baya son ummi  tasan inda zashi  ,


  'Umminsa yake kallo har sanda yagama" waya sannan yace mata shi zai fita sai ya dawo  tayi masa a dawo lfy  " mikewa  Yayi tsam cikin tafiyarsa ta kaisata ya nufi hanyar kofar fita ya daura hannushi kan handle ummi takira sunansa ya juyo yana dubanta tace kar kade fa  yayi murmushi yace love you mum ya  murda kofar  ya fice  .


Tsaye ya iske FK shi kadai jingine da jikin motar DEENI hannuwansa rungumeta da kirjinsa DEENi  ya Mika masa suka gaisa sannan suka  wuce kai tsaye gidan big dady.


  FK na gaba DEENi na biye dashi a baya har suka karasa cikin gidan  suka nufin  inda suka san zasu  tarar da  big dady .


 zaune suka hango  tsohon mai tarin shekaru da dattako,sai dai" ya dan manyanta kadan  domin shine "dan"  Muhammad bello khaliyal na farko  Kuma shi ke yanke  hukunci ga duk abinda yataso dangane da   komai" na cikin family  .


Zaune yake  idanunshi manner da  medical glass "da Gani kasan nakara lafiyar ido ne.

 suka karaso inda yake da sallarmasu ,da  fararsa yake dubansu.

 ya ajiye   jaridar daily trust  din dake hannushi gefe cikin sakin"  fuskarsa dauke da murmushi ya amsa sallamar sannan suka gaidashi ya amsa yana tambaye aikinsu" suka ce alhmd .

shr yabiyo baya tsawon lokacin kafin da tsohon ya dago ya sake dubansu.

 da  fk, suka hada ido dan DEENi tun byn gaisuwar da Yayi masa Yayi kasa da kansa yana kallon yatsun kafarsa" tsai Yayi yana nazarinsu duka sannan   yace lfy  dai naganku haka duk da yana ganinsu koda yaushe "amman wannan zuwan nasu  da dan banbanci "sai daya sake maimaitawa, tambayarsa sannan fk Yayi gyaran murya yasoma yi masa bayanin abinda ke tafi dasu.

Sannan  yakara danashi maganar tsakaninsa shemah .

  big dady yaji dadi Sosai matuka da jin haka  duk da yasan kusan irin aure da akeyi kennan a family din .

Amman duk da haka yaji dadi fiyye da kowani aure da'akeyi family din.

Yana murmushi  yace har kun daidaita junan ku kennan ?

fk Yayi tsuru tsuru yana kallon big dady" yayinda   shi  DEENi har zuwa yanzu kansa na soke a kasa" yana jin  duk abinda big dady ke cewa. take  yaji karfin gwiwarsa tayi kasa big dady yace    uhmm kun gama daidaita kanku  ?

still fk ne ya sake bashi amsa  yace A'a sai dai shi DEENi ya sanarwa umminsa" amman bata amince da abun ba.

 big dady ya kira sunansu daya byn daya, a tare suka dago, suka zubawa masa ido.

 big dady yace kuje ku nemi amincewarsu ku daidaita tsakaninku  inyaso sai asan abin yi


 DEENi zaune tamkar an dasa shi ji yayi kmr  kasa ya tsage  ya shige  ciki haka yaji " dan wani irin kunya yaji tamasa rubdugu dan haka  da kyar yasamu ya iya Mikewa  tsaye    suka bar part din  jikisu duk  a sanyaye barin ma fk da bai taba tunanin haka ba .


Suna fitowa daga part din big dady" DEENi yasoma zagin fk yana bude masa wuta , yace daman ka kawo ne a sake nuna min iyakata ?

 ,fk yace haba DEENi ka natsu mana musan abinyi  "wlh ko ni kaina bansa haka zata faru ba dan Allah kayi hakuri ka sausauta  wlh na dauka  komai zai zo da sauki shiya gaji nace muje . wani irin duba DEENi ke jifansa dashi " DEENI yace  ok wani sabon  rainin wayon  zaka sake kawo min .

gabadaya fk yakasa cigaba da magana illa idanu daya zubawa DEENi yanzu yace son zeenat  yake" yace masa sam ba haka ba .

 DEENi ya tsaya sosai suna kallon juna shi  da kf  .

a fusace yace kasan Allah kasan yadda zakayi da haukar, damuwar da kaman nami   dan ban ai keka kabani irin wannan gurbataccen shawar ba.

Gabada ka rusa min komai ,  fk dayaga hassala shima  jin zantuttukan da DEENi ke furtawa .

A harzuke yace  ai bani  nace kazo min da shawarar taka ba " iya abinda naga  zan iyayi  ne" na sanar maka.

Kai tsaye ka fito  kace  daman can kana son yarinyar" bancin haka daga baka shawarar , meye naka na damuwa daita .

 DEENi bai san sanda ya  dunkule hannushi" zai kaiwa fk naushi a baki  ba.

Take   fk ya goce yana kallonsa gabadaya  yanayinsa yagama canzawa sai huci yake kmr mayuncin zaki .

Fk  yace wai meke samunka ne ?

 kodai  kasha wani abu  ne yau , a fusace DEENi yace wuta nasha ba wani abu .

Sai daya furzar da huci mai zafi  sannan yace  kasan Allah sai dai kasan yadda zakayi da tashin hankali daka jefani ciki .


fk yace idan ba  haka ba Kuma fa "DEENi Yayi kyacci yace I will finish you....  ya wuce fuuuuuu kmr wani zaki .fk yabi bayansa da sauri yana kiran sunanshi  yayi banza dashi yacigaba da tafiyarsa da sassarfa har yacimasa ya ruko hannushi "da sauri DEENi ya juyo, ya bige masa  hannu " fk yace haba DEENi meyasa kake daukar komai da zafi ? DEENi yace da fetir ne kasan Allah idan har kana son zaman lafiyarka  dani " wlh ka nemo solution ya wuce nan yabashi . 



Cikin tsanyi jiki zeenat ta mike tsaye  byn taci kukanta ta koshi . bathroom tashiga ta wanke fuskarta tukun  sannan  ta fito' ta murda handle din kofar ' daidai lokacin da shemah ta mike tsaye itama " tasa byn hannuta tana  goge fuskarta " yayinda  wasu ke sake silalowa" wani irin kallon zeenat  ke binta dashi  ,kmr takasheta haka take ji wanda kallo daya shemah tayi mata "tarasa dalilin dayasa zeenat ke mata irin wannan kallon  haka  .


Zeenat  tace munafuka ashe zuwan dakike mana gidan" ba dan Allah kikeyi ba.

Shemah tace lfyr kuwa , bangane nufinki ba.


 zeenat tace zaki gane manufakar banza kawai daga karki sake shigo mana gida tunda kinada manufarki ta zuwa .


 jin haka yayi mugun  hassala shemah, gashi daman tana  tare da  haushin abinda DEENi Yayi mata , hannuta  tacire ta dauke zeenat da wani  mari wanda ya frigita zeenat  .

ai kafin ta sauke hannun  zeenat bata tsaya wata wata ba" ta damki makonshi shemah tace ni kika mara.. kika mareni daga bazaki sake marin wata ba ,wani irin nishi shemah ke fitarwa tana mutsu mutsun kwatar kanta har hawayen wahala take fitarwa ,zeenat tace   ba kukan soyayya kikeyi  ba zan aikaki   abarzahu inyaso kya ji dadi yin kukan da tushe .

Km still tana damke da makoshinta  " tace nufinki kice kina  son yaya DEENi ko .


  Wlh yarinya  karyar tasha karya " da kyar shemah tasamu tasa iya karfinta ta kwace kanta  daga rikon da zeenat ta mata .

 Take suka suma kwokuwa da juna gabadaya  hayaniryasu  ta cika gidan ,a tsorace ummi takaraso gurinsu ta shiga tsakanin" zeenat da shemah wacce har shedewa take saboda kukan dayaci karfinta gabadayansu  fuskarsu  tayi jazir,.

 zeenat na kuka shemah na kuka cikin fushi da bacin rai ummi ke tambayar su abinda ya hadasu fada amman cikin bbu wanda yabata amsa har sanda   " DEENi yashigo gidan ya samesu  tsaye cirko cirko , yaja ya tsaya  yana jan tsaki dan tun shigowarsa yake jin hayaniryasu yanzu ma  ganin ummi ne yasa ya tsaya ,  da kallo yabisu dashi " ummi  na  ganinsa tace yauwa gara ma  daka shigo , ta sanar masa abinda faru ummi nagama fada masa takama gabanta  .


   ai yana gama jin abinda umminsa tace ya fara dauke zeenat da wani mahaukacin ,mari dayasa taji dan guntun fitsarin dake makale da mararta zubowa ,  itama shemah bata nata sannan ya gwara  kansu gabadaya  waje daya jikake gum.......  Bbu wacce tayi kokarin yin kuka cikinsu dan sunan halinsa sarai  bakaramin aikinsa bane ya hada musu da punishment.


 tsawa ya daka musu   yace kowace ta takama gabanta  tun bai sabauta musu jiki  ba , hade da cewa yan iskan yaran kawai  .


Dakinsa ya  wuce yasoma  zariya daga farkon daki zuwa karshe  hannuwansa duka yasa yana balbale botura rigarsa" wani irin zafi yake ji  a zuciyarsa tamkar ana zuba masa barkono , gumi ke tsatsafo masa takoina kmr ba dazu yayi wanka ba " sai daya balle botura rigar ya cire yayi jifa daita ya  fada   kan bed   idanunshi na kallon sama  celling dakin ahankali .

Ahankali yasoma runtse idanunshi  har ya rufesu ruf  gabadaya tunani mafuta kawai yake tabbas indai sai ya tunkari yarinyar nan da sunan yana sonta to wlh ya hakura daita har abada kai auran ma yafasa gabadaya  .



MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗

  AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page  15-16



Tare zeenat suka jero da shemah" suna kuka saboda  marin da yaya DEENi yayi musu  yashigi    kowannesu" amman hakan bai hana zeenat aikawa shemah da zagi iri iri  ba" har suka karaso  parlour"  inda ummi ke zaune  tayi xuru ...hade da zubawa sarautar Allah ido abin ya faru Yayi maseefar girgiza zuciyarta .  kirasu ummi tayi tana sake tambayar su"  abinda ya hada su fada  haka" alhalin da can ba haka sukeyi ba,.

   shemah ce  tasoma magana cikin kuka   Allah ummi ni bansan nayi mata wanj abu  ba"  kawai ganinta  nayi tafito daga daki" tana wasu abubuwa   ,daga nan Kuma sai ta hau ni da zagi ,.

zeenat zatayi magana ummi "ta katseta  tace  ya isa   banson jin komai daga bakinki  .

 dan ta fara zargin wani abu dangane da abinda ya faru yanzu " ummi tayi musu fada sosai da nasiha mai ratsa jiki .

     tace karta sake ganin sunyi fada da juna  ,  shemah ce kawai ta iya amsawa  tayi wa Ummi sallama ta wuce Amman it's zeenat kishi tattare da kunar zuci suka taru suka tsaya mata a kirjinta hakan yasa takasa cewa komai  .


Ko byn fitar shemah ma  "zeenat  tsaye tayi tacigaba da kukanta tana jin haushin ummi data hanata yin  magana ,alhalin gaskiya tana Gani  .

   yatsun DEENI ne  kwance a gefen  fuskarta wanda ya haddasa wajen dan tasawa , dan gabadaya fuskarta ta canza kala tayi jazir ".

  tun  Ummi  naji haushin kukanta nata  har ta dawo tausaya mata dan tasan , ta daukar kanta wahala ne  in dai akan DEENi  ne . 

  Ummi na kallon yatsun DEENi  kwance a fuskarta take taji wani abu ya tsarga mata " har cikin zuciyarta taji kmr ta zubda hawayen takaici  kiran sunanta tayi  hade da  nuna mata guri zama kusa daita.

    cikin sanyi jiki zeenat ke daga kafafunta inda take tsaye  har ta isa inda Ummi ke zaune ta zauna "kmr yadda ummi ta umarceta  ,


Ummi ta zuba mata idanu  kawai tana kallonta dan abun nata na neman fin karfinta  "tsawon lokacin zeenat tana risgar  kukanta ,batare da  ummi tace mata komai ba ,

  sai da ummi ta gama nazarinta tsab sannan tace duk wannan kukan   na meye haka  ?   


    Kar kice min duk akan son  DEENI kike neman yin fada da er'uwarki . Saboda Allah Ke ko kunya  abinda kika aikata baki ji ba .

"  zeenat tayi shr takasa  cewa komai dan ita kadai tasan yadda take jin zuciyarta, .

Ummi tace meyasa  zeenat , meyasa bakya jin maganata ne ,irin abinda zaki min kennan ko wannan shine kalar tarbiyar dana baki uhmm ?

    kina ganin haka kawai zanki amincewa da auranki da DEENI " kiyi tunanin mana .

koda yake  baki san ciwon kanki ba shiyasa.

' ballanantana" kisan gata neke miki  .


  mutumin da bai san da zamanki ba, bai damu dake ba" ko kallon  arziki baki isheshi ba" shine zaki  zauna  kina westing din  hawayenki akansa takarasa fadar maganar tana takaicin zeenat,.

"    Ummi ta sake maida dubanta sosai gareta tana mamakin yadda zeenat din  ta canza cikin lokacin kadan . Alhalin ita duk iya lokacin ta dauka tare da yarinyar bata taba ganin irin haka atattare daita ba 

 cikin kuka    zeenat tace   ummi  kinki  amincewa da aurenmu  yaya DEENi .

  ai gashi nan ai ...... sai km tayi shr" dan jin kunyar abinda take kokarin son fadi "dan haka tacigaba da  sheshekar kukanta,.


" Ummi tace uhm Ina jinki kikarasa mana ,   tace wlh  wlh idan kika kuskura" kika bari  yasan kina wannan"  haukar akansa " kin shiga uku  da wulakanciinsa " .


 zeenat  ta zube nan  kasa  tana kuka hade da  kamo kafafun Ummi .

tace  dan Allah  Ummi ki Amince da maganar yaya kinji "wlh ni Ina sonshi a haka " kiyi mana addu'a kawai"  bbu abinda zai faru  inshallahu .

  Ummi ta sake  zuba mata idanun tana kallon  sarautar Allah, da rashin kunya irin ta Zeenat , su fa daman  yayan zamanin nan ba wata  kunyace ta ishe su ba .


 ,ummi tace" da bai ce yana sonki ba fa ? 

Ta jeho mata tmyr " data girgiza zuciyar  Zeenat " din" tayi kasa da kanta tana zubda kwalla ita fa ganinta bbu abinda tayi  .

 a ranta ko cewa tayi  ai shima yana sona tunda ya iya furtawa .


 Ummi  ta sake kiran sunanta tace zeenat idan bakiji kunyata" ta matsayina  ta  mahaifiyarki ba " ,

Ai kya ji kunyata ta ummin DEENI .

amman tunda kin nacewa auren DEENi  km kinji" kin Gani  to wlh duk abinda kika Gani  Shikenan , .

da ma  sharadi kozan  amince da auranki dashi .

   Banda zuwa kawo kara  kum  duk abinda yabiyo baya babu ruwana ciki sai dai ki haye abinki tunda shi kika zaba .

   da sauri zeenat tace to....ummin indai kin amince bbu ma abinda zai faru sai alkhari .

Wani irin    kallo Ummi tabita dashi wanda da Gani kasan na tausayi ne. 

  Dan yanzu ta daina  mamakin duk abinda zatayi  .

da murna ta tashi ta koma bedroom  tayi kwanciyarta tana jin dadi Ummi ta amince da aurenta da yaya DEENi . idanunta ta lumshe"  tana jin Yadda soyayyar   DEENi ke sake huda zuciyarta .


Yinin ranar da murna zeenat tayi shi cike  da tsantsar  farinciki ga tarin  tunanin DEENi dake sake mamaye kowane part na jikinta yau tazo mata da abubuwa masu yawa bacin rai da farinciki  .

duk abinda takeyi Ummi na hankalce daita . kallonta kawai take   tana   binta da idanu   .


 Washegari zeenat" ta zaci ummi zata sanarwa yaya DEENi  cewa ta amince"  sai  kurum taji ummi ta share da zance gabadaya , koda dai  da wuri yake fita ,.


 wasa wasa ummin ta share da maganar kwata kwata garakar gabanta kawai take , .

tana jin lokacin da dama idan yaya DEENi ya dauko mata maganar zata katse shi  tace kar ya dameta ya rabu daita .


sai dai abun yana damun zeenat matuka  yadda kullum yaya DEENi ke sake daure mata fuska da wulakanci iri iri. Amman takan masa uziri ganinta killa sai lokacin da ummi ta amince masa ' sannan zai daina nuna ko in kula dayake ,mata.


 shi kansa yaya DEENi baisan  cewar zeenat din tasan da zance ba. kullum dai ya shigo wajen ummi sai yayi mata nacin ,shifa yana nan yana Jirata.

 ita km tace kar ya dameta bayace yafi son Yar jami'a  ba .

"to yaje ya nema  Amman ita sam bazata bashi diyarta ba , .


yana  fita   zeenat ta  matso sosai kusa da ummi  tace ummi dan Allah bakince ,kin hakura  ki amince  tunda na yarda ba .


sai ummi ta dube tana watsa mata harara tace                  sakariya bazan kawai".

       kalli fa ko kallo arziki baki isheshi ba .Amman duk kinbi jin  tsamgwami kanki .dan fitina tsiya  da jaraba , .

  ni duk abinda nake Ina yi ne "dan Kare matuncinki , ba dan Ina kin   aurenki da DEENi   bane .



 tunda yashiga dakinsa bai sake  fitowa ba" sai dai yatashi" yayi sallah kawai  yakoma gado .

 yasawa ranshi, cewa ya hakura daita kwata kwata dan baiga dalilin  da zai sa shi ya dinga batawa kansa lokaci ba .




Kwance yake akan makeken royal bed dinshi ya rufe kanshi cikin alky  blanket mai matukar taushi ,.

bacci yake Sosai hankalinsa kwance ya rufe  koina na jikinsa banda fuskarsa  saboda yanayin unguwar su mai dauke da sanyin ni'ima ,.


 ahankali ta bude Kofar dakin" kwance ta ganshi, yana sharar  baccinsa ,sai yanzu hankalinta ya kwanta gangar jikinta yasamu natsuwa , kusan kwana biyu kennnn rabon data sashi a idanunta,.


 ahankali take daga kafafunta har ta isa inda yake,. kwance

   idanunta ta   zuba masa" tana kare ma kwakkywan fuskasa  kallo yadda tayi kyau tana fidda annuri na musamman .

Ahankali   ta lumshe idanunta " tana jin wani irin tsanyi nabi jijiyoyon jikinta.

Ahankali ta bude idannuta suka sake sauka akan beautiful face dinshi ,.

  fuskarsa ta kurawa ido  har wani kyalli kyallin  kyauwu take fitarwa  , cikin rawar hannu takai hannuta  gefen fuskasa ta dan  tashafo .  wani irin taushi taji wanda ya  sake dulmiyar daita a duniyar kaunarsa .

Take taji koina na jikinta ya mutu sai wani yammmmuu take ji.

 ita kanta tarasa dalilin dayasa take jin  haka ajikinta .

   ganin bacci yake sosai  yasa ta juya ahankali tabar dakin cike da shaukin soyayyar DEENi  dama Ummi ce "tace ta dubashi    dan har lokacin fitarsa aiki na neman   wuce .


 Koda ta sanar da Ummi cewar  bacci yake har yanzu, yasa ummi ta nufi dakin" dakanta kusa dashi taje" kai DEENI sai data kira sunanshi" kusan sau biyu" sannan  ya dan bude gengerous eyes dinshi ya kalleta dashi "tace  lafiyarka da har yanzu   dabaka tashi ba , .

 tacikin blanket din ya dan yi Mika hade da salati sannna ya dan gyara kwanciyarsa yace lfy first lov ,natashi har nayi sallah " to bazaka aiki bane yace zani.


 Ummi tace Ina jiranka idan kagama.

 ya amsa mata da kai kawai .

a hankali  ya zame jikinsa daga cikin blanket din ,  daga sai dan gareni wando Mika ya sake yi yasa hannunsa ya gyara jijiyarsa dake mike .

Sannan ya shiga bathroom,.

duk da yamakara hakan bai sashin yin sauri ba, wanda normally haka yake da sanyi jiki .

 wanka   yayi, ya fito. ya shirya cikin kakinsa da suka dace da surar jikinsa,  har ya murda handle din  kofar "dazata Kai shi parlour ya tuna Yayi mantuwar wasu files  a dakin baccins" dan haka yakoma ciki daukowa      . 


Tsaye take a bakin kofar dakinsa tafi kusan minti biyar a wajen tana saka dawarwara yadda zata sake  shiga  Bedroom din sa.

 ummi ce tasake aikota .

Ta dubashi dan taji shr  har yanzu .

 tana son tayi nocking Amman tsoro da fargabane  suka hanata .

 daidai wannan lokacin DEENI ke shirin fitowa daga part dinsa . ta daura hannuta kan handle din kofar.

 ai agigice cikin matsanancin tsoro tasaki  wani irin kara  da tasa DEENI , tushe kunnuwanshi " da duka  hannushi "ai batasan sanda  ta fada saman fadaden kirjinsa ba .

hade da runtse idanunta  gam dan tsabar jin  tsoro , batasa abinda zai mata ba Jira kawai take taji saukar mari dan gabadaya tagama frigicewa.

 Amman abin mamaki sai taji sabanin haka.s shiyasa  tasaki jiki ta sake narkewa a fadadden kirjinsa tana shakar dadeden kamshin turarenn jikinsa mai birkita mata tunani "a duk sanda ta Shaka  .


 wani irin ya dinga  ji ajikinsa,  yrrrrrrrrrrrrr.... yrrrrrrrrrrrrr  abinda bai taba faruwa dashi ba  kennan" jikinsa ya hadu da wata macce" shi tunda yake ma  ko hannun macce bai ta ba rikewa ba ballanantana yakai ga hada jiki .

Ya  dinga jin wani irin wani irin  a gangar ajikinsa.

   gabadaya tsigar jikinsa suka mike tsaye , yaji da zai iya " rungume zai yi kawai zaiyi .

 ko zai ragewa zuciyarsa radadi da ciwon dayake ji.

  Amman Ina... Sam bazai  taba iya aikata hakan ba .

ganin yadda tayi lamo ajikinsa ne yasa, cikin takaici  ya bambareta daga kirjinsa cikin tsanyi jiki,

 tsayuwa ce ta gareta , zuciyarta ke neman tarwatse tsabar tsoro da rikincin data tsinci kanta ciki.

,ko ta kanta bai bi ba ya tsuke fuska yana kallonta  ,itama idannuta ta zuba masa  ko kiftawa batayi.

 ga wani irin tsoransa dake lugudar  zuciyarta.


 ahankali muryasa a sanyaye yace malama ki daina min "irin wannan kallon na munafurci .

in ba haka na kwakule idanun rashin kunya tsaki yaja hade da bin   gefenta yazagayeta ya wuce kai tsaye part din umminsa yashiga" sai dai bai ganta ba,.

 dan haka ya wuce main parlour 'dan yasan tunda bata dakinta, tana can .


 zaune yasameta tana yin breakfast fuskarsa a dan sake yakarasa har kusa daita ya zauna   yace gud morning my first lov, ta dubeshi fuskarta dauke da murmushi tace morning dear ,kata tashi lfy girarsa ya dage mata.


 cikin tsnayin jiki  zeenat  takaraso wajen, kallo daya DEENi Yayi mata yasa  ta canza hanya batare da ta sake kallonsa  , kan wasu kujeru dake ajiye a gefe  ummi tabishi da kallo batare da tace masa komai ba  " da kanta tayi savice , din shi ,shi km sai wani zuba mata  shawaba yake , .

  coffee kawai ya iya  yasha, ya mike tsaye  cikin hanzari sakamakon wayarsa data dauki kara yana dubawa yaga  ogansa ne daga wajen  aiki  .

 dan haka yayiwa umminsa sallama  da hannushi ya fice    wayar manne da kunnenshi  .


 Zeenat data  zuba tagumi ,Da hannu biyu  tabi bayansa da kallo har yabar   gurin idanunta na kansa , itama ummi  data dauke idanunta daga kan DEENI "zuru tayi tana kallon Zeenat din , tana girgiza kanta .

 waskewa zeenat tayi hade da sakarwa ummi murmushin dole ummi tayi mata dakuwa da hannu .



Byn DEENi ya gama amsa wayar oganshi ne yana zaune  cikin mota wayar  fk yashigo  " yasa hannu ya dauki wayar ya duba ganin fk ne yasa ya maida wayar ,mazauninta .

Yakirasa yafi sau gomasha daya Amman yaki pic sai  a karo na shabiyu ne  ya danna wani abu "sai ga muryar fk radau  yakarade koina a motar , hello.... hello DEENi kana jina   .... 

Yayi shr  yaki yin magana,sai ma  cigaba da yayi " da direving dinshi .

fk yace haba DEENi ya kana jin zaka min shr. "duk  fa" maganar bata kai haka.

 afusace DEENi ya katse shi  yace maganar tafi haka har ta zarce haka  a waje na.

 km wlh wlh karka kuskura, ka tako inda nake  da sunan kasan ni ai bansa cewar da kungurumin ,dan iska nake zaune ba.

 fk yayi murmushi yace Allah dai ya huci zuciyarka ,dan shi.

 bai fiyye fushi ba" kwata kwata ma bayason duk wani abinda zai kawo masa tashin hankali .

dan haka yayi tabawa DEENi hakuri hade da bashi baki .

 DEENi yaja numfashi  ya sauke ajiyar zuciya . hakan yasa fk ya gane cewar ya sauko kennan fk  yace to yanzu yazamuyi da maganar da  big dady yace.

 DEENi ya tabe baki yace ya dai zakayi dan ni tuni na hakura da wannan yarinyar , karma ka km yimin wannan bazar zance.

 daidai da yakaraso wajen aiki ,ya katse wayar fk batare daya tsaya  ji mai fk din zai km ce masa ba .




MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗

   AUREN SIRRI

      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 17-18



 Wata daya kennan  fk yaji "shiru DEENi bai km yimasa zance maganarsa da Zeenat ba musamman" yazo gurinsa  dan zance daman Kuma sun dade basu ga juna ba" sai dai sukan yi waya lokaci zuwa , lokaci  dama ya kirashi a waya cewa yana nan zuwa .



Byn sun gaisa fk yace friend har yanzu ban sake jin  batunka da yarinyar nan ba .

 deeni ya gyara zama ,hade da  yaja tsaki sannan ya lumshe idanunsa dan takaici da Haushi  maganar .

 ya zubawa fk ido yana kallonsa kawai domin  rasa me zaice masa Yayi   ,tsawon lokacin suna zaune a haka sannan fk yace friend hakuri zakayi dan Allah  ba wai Ina son dawo maka da hannun agogo baya bane .


 Amman idan maganar danayi  akan Zeenat ya bata maka rai, kayi hakuri.


 ahankali deeni ya furzar da iska mai dumi ya miko hannushi ya dafa gwiwar fk , Friend   ban tasamun abinda ya bani matsala kmr maganar yarinyar nan"  abin haushi duk lokacin da nayi kudirin hakura daita sai nakasa .


Kullum addu'a ta Allah yaye min ita daga raina Amman abin ya faskara ko son yarinyar ne yakamani "oho " fk yayi murmushi yace  lallai sonta kakeyi Allah yasa itama ta soka haka .


DEENi ya gintse fuska yace Ina ruwana daita first lov ce kawai damuwata ,data amince da yanzu an wuce gurin Amman tsohuwar nan sai cewa take zan cuci Yar mutane ita bazata bani  Yarinyar karama ba inzo Ina bata wahala fk yace sanin halin ka tayi dan kai din bana wasa bane  kana raina yarinyar ne dayawa shiyasa ummi batason aura maka ita wani lokacin sai inga kmr da gaskiya ummi DEENI yayi masa wani kallo dan ni bason iskanci idan abinda yakawo kennan kana iya tafiya .


Fk yace zanje in sameta da kaina kar damu .

deeni yace dama kabar ta kawai dan ko kaje ba amincewa zatayi ba.

 nasan halin first lov , da zata yarda da tunin ta amince .

na dai fada mata cewar ni na hakura dayin auren gabadaya" inda tagaji da zamana haka tasan abinyi .


Fk yayi ta dariya tare da xolayar DEENI" friend ka dai shiga da yawa da ka'ajiye duk wani girman kai ,ka dinga kiran yarinyar  kana janta ajiki ,idan ummi taga haka zatafi yarda da gaske kakeyi "Amman kai kullum fuskarka a hade  kmr hadari .



DEENi ya tabe baki, kasan Allah bazan taba iya kiran ko wace irin  yarinyar bace, da sunnan zance koba Zeenat ba. kai ma abinda kariga kasani ne "bansa ta Ina zan soma ba   ,nifa bana kawo Zeenat a raina ,in dai  first lov ta yarda " to tayi hakuri ta aureni kawai   dan ni banda wani lokacin ya mace . dan ma taji dadi ta samu miji irina  ,yakarasa fadar  maganar yana jan tsaki fk yayi dariya yace friend banda yabon kai fa , DEENI ya dan yi murmushi gefen baki har dimple dinsa ya lotsa  kai ma  kasan gaskiya fada ne dai kawai  bazakayi cikin  "nida ita wazai taimaka wani ? 


 Bbu abinda zata nuna min " fari ne kawaiya ceceta  "  wanda kai kasan ko man bleaching takara bazata taba kamo nawa ba "fk yace ai shiyasa ka daurawa kanka girman kai al'amarin mata" km duk da kafita kyau ita zuciyarka ta zaba  ,ta zama abokiyar rayuwarka "  zanyi  maka iya bakin kokarina ,.


DEENi yabishi da kallo yace sannan ya maida bayansa ya jingina  da kujera , dama kabar, damun kanka akan zance yarinyar nan , wai dole ne  sai na aureta   ,fk yace tunda nace zanyi kabarni mana ,na gwada sa'a ta ko ummi zata yarda . DEENi  ya daga kafadarsa alamun shi yasani ,sannan yace tunda ka nace  kaje din Amman idan  labarin ba may dadi bane ,karka zomin dashi ba  ,.


 


Kmr yadda fk yayi alkawari   haka ce takasance    yasamu ummi da zance  byn sun gaisa ne   yace daman akan zance deeni ne  da Zeenat" ummi najin haka ta canza fuska " har tasa karfin gwiwar da fk yazo dashi " yayi kasa.


Ahankali yacigaba" dan girman Allah ummi kiyi hakuri ki amince da auren nan "saboda dukkansu naki ne a ganina wannan abin farin ciki ne  .

Ummi ta sake tamke fuskarta Sosai tace  faruk Ina matukar ganin kimarka da mutuncinka  zai fi kyau kabar zance nan" bana jin cewar zan iya amincewa .

  fk yayi shr yana tunanin yadda zai bullo mata  can dabara tazo masa yace to Shikenan Amman naso ki Amince domin deeni yana cikin wani hali  nason yarinyar  nan. daidai lokacin da Zeenat ta dawo daga gidansu Maryam tanac kokarin shigowa  parlour ummi  .

   ,karaf zance ya fada cikin kunneta cak taja ta tsaya jikinta ya dauki kirma .

Fk yace ummi  kin san halinshi baya daga cikin mutane masu magana biyu  ,ya min ransuwa  ba zai tabayin  aure ba ,in ba Zeenat ba ,km duk duniya ita ya Gani yake so.


 zamanshi haka nasan yana damunki ummi tace in duk duniya Zeenat yagani  yake so ita  Zeenat din ya sameta yaji ko tana son shi ? Ko haka kawai dan shi yana sonta" zan dauke  diyata ta nabashi batare da ya nemi amincewarta ba.


Nifa bazanyiwa diyata auren dole ba dan kawai Ina son na faranta masa rai ba .


Daga inda Zeenat ke tsaye tana jin komai" take jikinta ya dauki  yacigaba wara  har wani zazzabi zazzabi taji yana neman rufeta , kafafunta suka Gaza daukarta sakamakon kirmar da suke , nan ta sulale kasa tana jin yadda gabanta yashiga faduwa da sauri da sauri ,  tarasa dalilin ummin nakin aurenta da yaya DEENi .

alhalin tasan yana sonta har haka .

 ,to hakan na nufin ummi tafison yaya yaje waje ya aure wata ,  sabanin ita kennan . 

kawai batayi aune ba taji saukar    hawaye nabin kuncinta .

   Da sauri tasa Hannuta  ta dangwalo hawayen dake bin fuskarta, tana kallo ta girgiza kai  kawai tana jin tamkar an diga mata dalma ne zuciya ,.

Ta runtse idanunta  ahankali muryarta cike da rauni tace meyasa ...

Meyasa ummi kike son ki ruguzamin rayuwa  please ummi ki amince na auri yaya DEENi  , Ina sonshi har bansan iya kar kaunarsa a zuciyata ba " bazan iya rayuwa in bashi ba 


Fk ya fahimci abinda ummi take nufi  shiyasa yace ma DEENi ya dinga kiran yarinyar suna hira. ko km yajata ajikinsa . Ta hakan ne komai zai zo da sauki , fuskasa dauke da murmushi yace ummi idan dan wannan ne ,karki damu , duk wannan me sauki ne zamu tuntubi yarinyar muji , idan bata amince ba Shikenan .



Ummi tace da dai yafiye muku" ba ku tsaya girman kai ba, fk ya sake yin dariya yana girgiza kai  yayi mata godiya ya mike  .


Jin  da Zeenat tayi fk  yayiwa ummi sallama ne  yasa tayi hanzari  mikewa da sauri tashige bathroom din parlour din dake manne da falon nan ta fashe da wani irin kuka ita kam zuwa yanzu tafara jin haushin ummu  .



Fk na fita yakira deeni bugu  biyu ya dauki wayar , fk yace friend kafara da bani goron albishir ,cikin yanayi na ko in kula deeni yace kada kace min first lov ta saurareka ? 


Fk yace ta saurareni km  inshallahu zamuyi nasara da alamun ummi ta amince  ,.

 duk yayi masa bayanin   yadda suka yi da ummi ,

 yakarasa zance  da ummu   ta nuna tanason asamu yarinyar a nemi amincewarta .....

  DEENi yayi shr sannan yace to ai wannan  shine mai wahalar dan bazan taba iyawa ba , fk yace wai kai tsorota kake jine ko yaya ?

 ,ai take deeni ya hassala a fusace ya aiko masa da wata irin uwar ashariya " wanda yasa fk yayi  sauri  cire wayar daga kunnenshi ,ya dan duba  sai daya tabbatar daya yana kan layi. sannan ya mayar yacigaba magana" haba friend meyasa kake saurin daukar zafi akan abinda bai yakawo ba .


 bance dole sai kasameta da kankaba ,ni dakaina zanyi komai.

  sai Kuma ya sausauta yana jan numfashi yace ai kai ne da wani zancen baza.

 naji tsorota akan me ,raini ne kawai banaso , yanzun dai kai kaje kasameta  kuyi magana  da in ni nakirata bafa ra'ayinta zanjira ba. umarni kawai zan bata   fk yace Shikenan sai na nemeka  .


 Zeenat  zaune gaban TV dake manne a parlour su ta hada uban   tagumi ,hade da  zubawa   TV idanun . Kallo daya zaka mata , kasan kwata kwata hankalinta bai kan shirin da'ake gabatarwa .

gabadaya tunaninta ya kashi gida biyu .


ga tashin hankali ummi taki amince wa da aurenta da yaya DEENi. ga kamil  da yasako, gaba da zance yanason kai  maganarsu gurin big dady, .

hankalinta a  matukar tashe yake  .

har ummi   takaraso inda take zaune  taba tasani ba".

 ummi  ta  zuba mata idanu kawai tana nazarinta sannan ta numfasa  sai data kira sunanta tukun ,  Zeenat tayi saurin juyo a frigice tayi firgigib tana duban ummi .

idanunta ta  zubawa ummi kmr wata mara gaskiya " ummi tace wai ke wace irin  sakarriyar yarinyar ce" da kwata kwata baki san ciwon kanki ba "kalli ummi ta nuna jikin Zeenat da dan yatsanta , dube yadda kika dawo ,duk kinbi kin sakama kanki tunanin banza ji yadda kika koma  duk kin tsotse kin rame dan jarabar tsiya ,anason a karemiki mutuncinki ,kinki natsuwa, kisan haka  .

sai kiyi tayi ai.


 cikin haka fk yayi sallama yashigo ya zauna akan kujerar one site  yana   gaida ummi 

Ta amsa masa  fuskarta a gimtse da tasan kwanan zance "  Zeenat ma ta gaisheshi tsam mike taje takawo masa abin sha  .


,ummi ta tabe baki tana hararata dan takaici  sannan ta sake kai dubanta ga fk  din" tace   DEENI fa yana dakinsa .

   Fk yayi murmushi yace ai  ba gurinsa nazo ba ,jin haka yasa  ummi tashare   , ta cigaba da kallonta , gabadaya  parlour ya dauki shr tamkar babu mutane a cikinsa  baka jin motsen  komai sai karar TV .

Zeenat kam kamewa tayi tashiga hankalita dan motsi kadan  , ummi zatace tafiye   rawar kai .

 ganin shr yayi yawa     yasa ummi ta mike tabar gurin ta nufi dakinta . Parlour  ya saura daga Zeenat sai fk .


 yana Ganin  ummi tashiga dakinta yasa ya  juyo  yana fuskantar Zeenat yace sister wajenki nazo fa  .   tace to Allah yasa dai  lfy yace lafiya  nasan zakiyi mamakin zuwa na ?


Tace bawani mamaki killa akwai abinda kake son nayi maka ne .

yace ba wannan bane nazo ne dan nasanar miki da wani abun alkhari koda yake bansan yadda zaki dauki abun ba.

  tsab Zeenat tagane abinda yakawo shi gabanta taji ya tsananta faduwa ,.


fk yace deeni ya duba duk cikin en'mata dake cikin  family din nan.

 yaga bbu wacce tayi masa km tadace dashi sai ke .

Zeenat ta zaro idanu waje kmr da gaske  ta nuna kanta    tace ni fa kace yana so...



Fk yace bawani abin mamaki bane , Dami kika tsinta a kala ,a ranta tace maganar ka gaskiya.

  fk yace yanzu me kika gani idan kin amince , magana zata wuce gurin big dady kai tsaye  batare da bata lokacin ba .

ta tabe bakinta kmr batayi murna dajin zance ba  ,  sannan tace gaskiya kagaya masa kawai yayi hakuri  dan ni  narigada na tsaida wanda zan aura ,.


fk yace waye shi km a ina yake   km kin kai maganar wajen big dady ne ? Duk alokaci yajero mata tambayar ,tace Ko daya muna dai shirin yin haka fk yace yace shi din wanene tace wani ne acikin family dinmu yake humm yace  inbaki shawara ta daga masa kanta" zan so ki dakatar da koma waye.

 dan kowa zaki aura ina tabbatar miki ba zai taba kai kmr DEENI ba .


ke kanki kinsa samun irin su DEENi sai an tona. zakiyi alfahari samun  mijin kmr sa "mata dayawa suna ,sonshi ban sani ba kodan  sun fahimci qualities dinsa ne .

sai km yace amman bazan takura miki ba in kinga bakison shi Shikenan  .

ta kalleshi  a shashance hade da wani irin salo sannan tace nifa bance maka bana son shi ba  na dai kawai kace masa na  tsaida wanda zan aura .

Kaga  yanzu idan na canza raayina da sauri haka shi saurayin nawa  bazai  dadi ba .

ka dai bashi hakuri Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhari .


fk yayi shiru yana cizan yatsa hankalinsa yasoma tashi  "karfa yarinyar nan ta kwafsa masa yazaci yana mata zance zata amsa da murna  ya fadi haka a kasan ranshi.

can km yace to ni yanzu mekike son nace masa ? 


 Ta sake tabe baki yace Kafada masa gaskiya kawai , yace ba za kiyi tunani akai ba kafin ki yanke hukunci ,ko km kuje kisamu wanda kika san kin amince mata km tasan deeni  din sosai tabaki shawara akai, Zeenat  tace naji zanyi tunanin  .


Fk Yace Shikenan zan sake  nemeki zuwa  gobe naji abinda kika yanke akai , tace badamuwa .


Byn ya tafi, ne tashiga dakin ummi  tana murna cike da farincikin burinta yakusan cika ,fitowar ummi kennan daga bathroom aiko tana ganin yanayinta da alamun tace musu ta amince  ,take ta sake daure fuskarta , ta  rufeta  ta fada, ai gashi nan saboda baisan darajarki ,da kimarki ba sannan  bai dauke ki da mahimmanci ba ,yakasa zuwa da kansa sai  abokinsa ya turo miki nasan  jikinki na rawa kika   amincewa ko ?.


 Zeenat taaba fuska tamkar zata saki kuka tace nifa ba wani rawar jikin danayi   .

  ummi tace wlh kiyiwa kanki fada, akan sakarcin da kikeyi ke kmr ba macce ba .

 sam bawani  jan aji irin na sauran mata .

 Zeenat ta sake bata rai sosai .

 ummi tace gaki nan ga deeni ,inda shine nabarki dashi ya isheki wando da riga .



A waya DEENi yaji duk yadda sukayi ya dinga mamaki wai wannan yar yarinyar ce zata ce sai tayi shawara to dawa zatayi ?  Km ita ce wa ?


Fk yace itace mace deeni yace dan Allah  malam imin shiru shiya sa fa kaga bazan iya kai kaina gareta da sunan Ina sonta ba bare tamin salo . Nan km yau zazzagawa fk maseefa yana Ai shi  yaja masa duk wulakancin da'aka masa fk yace kwanta da hankalinka kavarni daita kawai nasan zata yarda ma kawai dai itama so take ta nuna mana itama macce .


Post a Comment

0 Comments