ALAKA.
11-12
*****************
Kwanaki na ja, tana nan, tana tunanin abinda zata aikata mashi,
Cikin school din malamai da students ba wanda be san lubabatu ba, yanda suka ga abinda takeyi, jss2 amma ta addabesu, dede da seniors basu son tabata,
Sun san halinta, tunda ko an mata, bata damuwa, ita de burinta, ta rama, shiyasa suke lallabata, idan suna so ta masu abu.
Gashi kwanaki kadan ya rage su suwaiba su gama,
Yau take visiting, 'yan gidansu Amina sunzo, taje suka gaisa,haka ta zauna suna ta fira dasu, har karfe biyar lubabatu bata ga yan gidansu ba, Gaba daya, ranta ya gama baci,
Sai can sai gasu sunzo, Harda abba,
Tana ganinsu ta bisu da kallo, tace shine sai yanzu zaku zo, abba yace ke ko gaisuwa babu, baki ga yanda kowa ke taro iyayensu cikin murna ba,
Tace ai baku zo da wuri ba, mommy na daria, tace to yi hakuri,
Suka samu wuri suka zauna,
Tace to meyasa baku zo da wuri ba?
Abba yace yau muka koma sabon gidanmu,
Mun manta da visiting, shiyasa muka tare a yau, Lubabatu tace ai dama dole ku manta, tunda baku damu dani ba,
Abba yace kai lubabatu kenan, ta Dauki affan, tace naga ka kara nauyi ne, me kake ci?
Yayi daria, nan suka yi ta fira, ta kira Amina suka gaisa, da yake har 'yan gidansu sun tafi,
Can cikin fira, tace abba dan Allah akuya nake so ka sai min, Yace lubabatu me kuma zaki yi da akuya?
Tace kawai kiwo nake so inyi, Yace to shikenan kada ki damu,
Wa za a samu da ze maki kiwon?
Tace ka samu wata haka, ammi tace naga nan layin akwai wata mata, da take kiwo, sosai,sai in bata ta maki, Lubabatu tace yauwa ammina,
Abba yace lubabatu rigima, Yaya fatima tace ai ita de ta samu abinda za a kashe kudi shikenan, Yaya salma tace ai lubabatu daban ce,
Tace eh naji, nan suka yi ta fira,
Sai da aka fara kiran sallan magriba, Sannan suka tafi.
************
Kwanaki sun kara ja, gashi yau ss3 suke candy, sabo turken wawa,
Lokacin da suwaiba zata tafi, haka lubabatu ta rinka kuka, sai kace wadda uwarta ta mutu, ta bata Phone number dinta, haka ta koma kamar mara lafia.
Daga karshe ta saki jikinta, taci gaba da hidimanta, tunda gashi har suma, Sun fara exams,
Bayan sun gama, Sun zauna zaman jiran hutu,
Tafe suke tare da Amina, sai faman daria take, Amina tace banfa yarda dake ba, daga dukkan alamu, kina son aikata wani abu ne, Lubabatu tayi daria, tace kamar me fa? Amina tace nafa sanki fa, wa ya tabaki? Kike shirin daukan fansa? Lubabatu tayi murmushi, tace ba wanda ya tabani,
Har suka karasa.
Ganin taga mallam shamsu, yasa ta kara sakin daria,
Amina tace kai lubabatu anya kuwa?
Lubabatu tace bari ki gani, waye wancan?
Tace mallam shamsu,
Tace yau yaushe? Amina ta kara cewa friday.
Lubabatu tace kuma gashi yayi shirin juma'a,
To kin san Allah, Sede ya koma gida, ya canza wata shigar.
Ta dubi kashin shanu da basu dade da sakinshi ba, Murmushin mugunta tayi,
Haka tasa hannunta a ciki ta debo,
Yana zuwa ta watsa mashi,
Jikinshi ya kalla, ya kalleta, wanda kashin har saman fuskanshi,
Ga duk mutane a wurin.
Da wasu malaman dake saurin tafiya masallaci,
Mallam shamsu yace wai ke wace irin mara mutunci ce?
Me na maki?
Takaici yasa harda hawayenshi, wani malamin da suke tare, yace ka bari muje ka canza kaya mu wuce,
Kada mu rasa sallah,
Idan muka dawo, yau sai kin raina kanki.
Tana tsaye, rike da kugu, ta tabe baki.
Suka wuce, mallam shamsu yana tunanin abinda ze mata,
Amina sakin baki tayi tana kallonta.
Can tace lubabatu meyasa kika yi haka?
Tace au wani abu nayi? Ai ya gode ma Allah ma, da ba kashin mutum na zuba mashi ba, Kin fa sanni, idan aka min bana kyalewa.
Tayi gaba, Amina ta bita a baya,maganar har ya kai wurin principal,
Suna komawa hostel,da sauri lubabatu ta dauki kayan da tazo dashi,
Ta zira, tasa hijabi, Amina tace ke ina zaki?
Tace gida, da sauri ta fice, tana isa bakin gate, Allah ya temaketa, ba kowa wurin,
Da sauri ta fice, machine kawai ta tara.
Tana hawa, ta tuna bata san gidan da suka koma ba, Tace kaini u/shanu.
Tana isa, seda ta samu kudin machine a nan, tunda dama can ta baro komai nata, Bayan ta sallameshi,
Ta fada gidansu jamila, mamanta na ganinta, tace ya akayi yan boarding, yaushe kika dawo? Ta zauna, ta gaidasu, tace gida nazo, Sede ban san gidan da muka koma ba, maman jamila tace to ki bari jamila ta dawo, na aiketa ne, sai ta rakaki, tana nan jamila ta dawo, da gudu jamila tazo suka rungume juna, mamanta tace to tashi ki rakata gidansu.
Ta basu kudin machine, suka Fita suna fira,
Har suka samu machine, suka tafi.
Suna isa gidan,suka sauka, jamila ta sallamesu, suka isa gidan, suna shiga, ammi dake zaune kan kujera,
Tace ke daga ina kike haka? Ta zauna, itama jamila ta zauna, ta gaidata,
Ta mike tace zan tafi, dama lubabatu na rako gida.
Ammi tace shine zaki tafi tun yanzu?
Tace akwai abinda zanyi ne, Ammi ta dauko kudi ta bata, tace ki gaida mamanku, nan kofar gida lubabatu ta rakata, ta dawo, Ammi tace tambayarki nake, ya na ganki alhalin ba ayi hutu ba? Fatima data fito daga wanka, ta leko,
Tace kai lubabatu sneaking kika yo?
Lubabatu tace to ai wani malami ne yake yawan dukana, Na rasa me na mashi,
Ammi tace shine kika dawo gida?
To ta ina ma kika biyo, Lubabatu ba tare da ta lura da hakan da tayi laifi bane, tace ta gate na biyo,
Seda na koma hostel na cire uniform dina, dama naje da kayan nan,
Shine nasa, na fito, Allah ya temakeni, ba megadi a wurin, kawai na fito na hawo machine, ta Ammi ta dauketa da mari, tace wato baki ga laifin da kika aikata ba ko?
Tashi Ki fita ki koma, ta inda kika fito.
Lubabatu ta fara kuka, tana cewa dan Allah Ammi ki kyaleni, ba zan koma ba, wallahi idan na koma, wannan malamin, kasheni ne kawai, baze yi ba, Ammi tace sai kin koma koda ze kasheki din, Ai kinsan abinda kika mashi, bare ma karya kike yi, zaki tashi ki wuce tun kafin babanki ya dawo, ko kuwa, Lubabatu ta duka har kasa, tana kuka, tace Ammi dan Allah ku rufa min asiri ku cireni a makarantar nan, wallahi ba zan taba so ba, idan kuma kuka matsa min sai na koma, zanta aikata koma miye a makarantar, har 'yan secret code, sena nema na shiga, taci gaba da kukanta,
Yaya fatima tazo, ta kama mata hannu, tayi ciki da ita, ta zaunar da ita,
Lubabatu sai faman ajiyar zuciya take, tana share hawayenta, Yaya fatima tace kiyi hakuri, yanzu meyasa kika gudo?
Ta bata labarin duk abinda ya faru, tsakaninta da mallam shamsu,
Yaya fatima tace kai lubabatu meya ja maki, koma me ya maki, ke komi ba zakiyi hakuri ba, sai kice sai kin rama, abinda baki yi a school din da kika bari ba, sai a wannan,
Meyasa? Lubabatu tace saboda bana so.
Yaya fatima da kanta ta shiga kitchen ta zubo mata abinci, ta amsa, ta fara ce, tace ina affan? Yaya fatima tace yana barci. Taci gaba da cin abincinta.
***********
Abba ne ya shigo, Ya samu wuri ya zauna,
Yace kinga abinda lubabatu tayi kuwa,
Yanzu principal dinsu ta kirani, ta fada min duk abinda tayi, nan ya kwashe komi ya fada mata, Yace tace yanzu haka nemanta suke, basu ganta ba,
Tace bata girmama kowa, duk wanda ya mata seta rama, Harda zagi,
Dama nasan halinta ne ramuwa, amma meyasa take ma malamai? Ammi tace ni ban san irin halin yarinyar nan ba, zuwanta boarding dinma, be haifar da komai ba, tunda wasu sabon abubuwan ta karo,
An kaita dan ta gyaru, amma ba canji a lamuranta, yanzu haka maganar da nake maka, tana cikin gidan nan,
Abba ya mike a fusace, yayi dakin nasu, rikota yayi, ya fara dukanta,
Ta fara ihu, tana fadin dan Allah kayi hakuri ba zan kara ba, mommy dake zaune, tace kai kamar kukan lubabatu nake ji? Da sauri ta fito gidan, ta shigo nan.
Ta tadda abba nata dukanta, ta dauketa,
Lubabatu tace lafe jikin mommy, mommy tace haba wannan duka haka?
Yace dan baki san abinda tayi bane,
Nan ya kwashe komi ya fada mata,
Mommy tace dama kun san halin lubabatu,
Be kamata a kaita boarding school ba, a gida ya kamata a barta,
A gyarata, amma kuka dauketa, kuka kaita boarding, seda ta nuna bata so,
Dan haka ku kyaleta ta zauna cikin 'yanuwanta.
Lubabatu cikin kuka tace dan Allah abba kada ka maidani, inba haka ba, mallam shamsu baze kyaleni ba.
Abba yace ai gara ki koma ya maki duk abinda ze maki, tunda ke baki jin magana,
Dan haka tashi yanzu a maidaki, kara kankame mommy tayi, tana kuka,
Tace Allah abba idan na koma, zan iya aikata abinda yafi haka, tunda bana so, mommy ta fita da ita.
Suka yi gidansu, sai kuka take, duk su zainab suka kewayeta.
Mommy tace to kukan ya isa haka,
Lubabatu tace nide mommy bana son komawa,
Mommy tace ki kyaleshi, Ai ba zaki koma ba, nide shawarata dake,
Ki zauna ki natsu, ko haka kika ga 'yan uwanki nayi ne? Tace a'a, mommy tace to ina so ki zama kamar su dan Allah, cikin kuka tace to, mommy tace yauwa ko ke fa.
Lubabatu tace to dan Allah mommy kada ko bari abba ya maidani,
Wallahi bana so, ban taba jin dadi a school din ba,
Yaya salma tace to ke lubabatu kyaje ki rinka ma malamai rashin mutunci, Lubabatu ta harareta,
Tace dan baki san abinda yamin bane,
Shiyasa zaki ce haka.
Ta kauda kanta, mommy tace to ya isa.
Ranar de lubabatu taki komawa cikin gidansu,
Sai Washegari, Sannan ta shiga, ammi kallonta kawai tayi, Lubabatu ta rakube jikin bango, sai kace wata marainiya, abba ya fito,
Yace to tashi ki wuce in maidaki, ta Duka, cikin kuka tace abba kamin rai, ka kyaleni, wallahi bana son boarding,
Ka barni cikin 'yanuwana, zan zama kamar yanda sauran suke, ya daure fuska, Yace mike mu tafi,
Ina da abin yi, yaga bata da niyyar tashi, ya daka mata tsawa, zaki tashi ko sai na zaneki, da sauri ta mike,
Suka Fita, sai share hawaye take, Yaya fatima ta kalli ammi tace Allah sarki ammi wallahi na fara tausaya ma lubabatu, da kun kyaleta a gabanku, tunda tana nan din ma ta ta kare, se wasu abin ma, data kara daura ma kanta.
Ammi tace ni kaina yanzu nafi so inga tana kusa dani din, amma da ya zanyi.
Fatima tace hakane, dan yanda ta nuna bata so taga din, zata iya yin abinda ta ambata din, zata iya hadewa da Yara na banza, kinga kenan ba ayi gyaran ba, dan haka ammi ki kara rokonshi ya kyaleta din,
Ammi tace zanyi haka din,
**************
Suna isa cikin school din, gidan principal din suka zarce shida ita,
Da yake ranar weekend ne, sai share hawaye take, principal na ganinsu, ta gaisa da abba, ta kalli lubabatu tace sannu, daki ka san baki da gaskia, sai kika gudu gida ko?
Ta sunkuyar da kanta kasa, principal ta kalli abba, tace kaga yarinyar nan, ba karamar shedaniya bace, hatta malamai, zamanta school din nan, tsoron tabata suke,
'yan watannin kawai da tayi a ciki, ba wanda be santa ba, inde a fage ne na rashin kunya, abba yace kuyi hakuri, ina bakin kokarina a kanta,
Bade ta jin magana ne, principal tace kayi hakuri, amma de ka dauketa, ka maidata gida ta zauna kusa dakai, dan ba zan iya da ita ba,
Nan gaba kaina zata dawo, abba yace da kinyi hakuri, tace dan Allah kayi hakuri, Allah ba zan iya barinta cikin nan ba, gara tana tare daku, Zaku fi sa mata ido,
Nan ko gani za tayi ai ba haihuwanta mukayi ba, bamu da iko da ita,
Abba yace shikenan, ya kalli lubabatu yace burinki ya cika ko?
Sai kizo mu wuce, Yace ma principal na gode, tace ba damuwa kayi hakuri fa, Yace a'a ba matsala,
Tace wuce muje hostel din ki kwashe kayanki,
Abba yace to me zata yi dasu?
Principal tace ko tana da wanda zata ba mawa,
Bari muje,
Tare suka jera, suna tafiya, principal tace, Ai banso ba, zaki bar makarantar nan, ba tare da na zaneki ba, tunda baki ji, ita de lubabatu bata ce komai ba, tunda burinta ya cika, ta bar makarantar.
Har suka isa,abba ya tsaya, ba tare da ya shiga ba, suka shiga, principal sai fada taje mata,
Amina na ganinta, ta taho da sauri,
Tare duk suka fito da kayan, ta mika ma Amina, tace gashi na bar maki su duka,
Principal tace ba zan zauna mata a school ba,
Amina tace dama ai abinda kike so kenan.
Banji dadi ba, Na saba dake, Lubabatu tace kada ki damu, zaki rinka ganina, zan dan rinka visiting naki, tunda bamu da nisa, yanzu bani number din da Zan rinka samunki, idan anyi hutu,
Amina ta bata.
Suka fito, principal tace ina kayan naki?
Tace na bar ma Amina su, principal tace to yayi kyau sai ki wuce mu tafi, Tare da Amina suka jera, sai hawaye take,
Suna tafiya, ita kanta lubabatu ta fara hawaye,
Har suka isa wurin abba,
Abba ya kalleta a daure, cikin fada, Yace ina kayan?
Tace na bar ma Amina, ta nunata, Amina ta gaidashi, ya amsa.
Yace se ki wuce mu tafi, yasa hannu a aljihu, ya ciro kudi, ya mika ma Amina, ta amsa, tana mashi godiya,
Suka wuce, Lubabatu duk taji bata son rabuwa da Amina, duk ta bata tausayi,
A mota kuwa, abba sai fada yake ma lubabatu, Yace yanzu yarinyar nan, bata birgeki ba, gata ta zauna tana karatunta lafia,
Yarinya mai natsuwa, ke kuwa rashin jinki, da rashin kunya baze bari, ki zauna da mutane lafia ba,
Sai fada yake mata, har suka isa gida.
Suna shiga, ammi ta gansu, tace ya naga haka?
Yace principal din taki amsarta, ammi tace ai kin kyauta, zaman gida ko ki zauna ki tayi, idan ma karatun ne ba zakiyi ba, gaba daya sai ki zauna, da jahilcinki, sakarya kawai.
Tashi Ki bace min da gani, ta mike ta shige dakinsu, lokacin fatima na kwance tana barci, bata tadata ba, Ta zauna kawai,
***************
Ammi ta kalli abba, tace halin lubabatu fa sai ita, bame jurewa da halinta, sai mu data zaman ma dole,
Dan haka dole mu zauna tare da ita.
Abba yace hakane, Ai ita ta sani, Na rasa meke mata yawo a kanta.
Ita kuwa kaya kawai ta canza, ta dare gado, bata wani dade ba, Barci ya dauketa.
Dan yanzu ji tayi hankalinta ya kwanta, tunda an rabata da kaya, duk fushin da zasuyi, zama su sauko ne.
Ita dama duk bacin ran mutum ba damunta yake ba, hidimanta zata yi abinta.
Kai kayi ta fama da bacin ranka kai daya.
*********,,
Fatima ta farka, ta ga lubabatu kwance,
Ta tadata, tace ya haka? Lubabatu ta juya, tace ai principal taki amsata, Yaya fatima tace abba ya kyaleki? Tace eh.
Yaya fatima tace kede ki samu ki natsu,
In ba haka ba, ba zaku dedeta da abba ba,
Lubabatu tace to.
************
Ta gama shiryawa ta fito, tayi hanyar fita,
Ammi dake zaune, tace ina zaki? Tace wurin mommy zani, ta kira min yaya sultan,
Ammi tace ba zaki ba, Lubabatu tace kai ammi dan Allah ki temaka min.
Ammi tace nace ba zaki ba, idan kuma zaki fita, ban isa dake ba, ki fita.
Ta samu wuri ta zauna, rai a bace,
Tayi shiru,
Ammi tace bade baki jin magana ba,
Idan na Kara ganinki a waje, ko kin fita,
Sai na mugun saba maki a gidan nan.
Ita de tayi shiru ba tare da tace komai ba.
0 Comments