ALAKA 9-10 BEST HAUSA NOVELS

 ALAKA 

9-10

     ***  ***  ******

Bayan sun tashi, Sun koma hostel, tayi wanka, ta Dauki kaya, zata sa,

Zariyar wandon ya cukwikwiye, sai janshi take, yaki warwarewa, ta fara kokarin fizgewa, Harda hawayenta, 

Tana ja, ni wallahi na gaji, bana son zaman makarantan nan, suwaiba ta shigo, tace lubabatu ya akayi? 

Tana hawaye, tace bakomai, ta amshi wandon dake hannunta, ta zauna, ta gyara mata, tace lubabatu kiyi hakuri kinji, tana hawaye, 

Tace yaushe za ayi hutu? 

Suwaiba tayi dan murmushi, tace nan da kwana goma sha tara, Lubabatu ta jawo jakanta, ta Dauki paper da biro, ta rubuta kwanakin da ya rage, tace kinga kullum zan rinka cancel din daya, 

Suwaiba tace yafi maki ko? Ta daga mata kai, Tun daga ranar, data tashi da safe, sai tayi cancel din daya. 

ta shirya suka fita, tana zaune, can hanyar gate ita fa Amina, Amina tace kizo mu tafi, 

Lubabatu tace nafi so inta gani mota da masu fita, Amina tace shikenan, 

Lubabatu tace sunji dadi, amma mu anzo nan an yasar damu, sai kace marasa galihu, nide wallahi Allah ya tsine ma wanda ya kirkiro boarding, daria ma ta ba ma Amina. 

Da sauri lubabatu ta mike, tace kai kalli motan gidanmu, ta ruga da gudu, tana tsaidasu, suka tsaya, 

Bala yace ya akayi 'yar gidan yaya sultan, 

Sai kuma ta fara hawaye, duka suka fito, 

Yaya fatima tace kai lubabatu duka yau kwananki biyar, amma jibi har kin rame, tace ba dole in rame ba, 

Amina ta karaso, zainab ta rike lubabatu, tace da ba kya nan, gidan ba dadi, 

Tace kai ni kawai burina in bar makarantar nan, bana sonshi, Yaya salma tace kiyi hakuri, hawaye ya zubo mata, Yaya fatima tace bari mu tafi, tunda kuka zaki rinka yi, ta dauko food flask, 

Ta mika mata, tace gashi mommy tace a kawo maki, tasan kina son farfesun kifi, shiyasa ta maki. 

Lubabatu tace bana so, ko miyan da aka min ma ban shanye ba har yanzu, 

Yaya fatima tayi daria, tace duk cinki yanzu, ba kya cin abinci? Lubabatu tace idan kun san bata min rai zakuyi, kawai ku tafi, Yaya salma tace kiyi hakuri, ta kalli zainab, tace ke ko magana, sai wani faman kallona kike,Kamar baki sanni ba, 

zainab ta danyi daria,Yaya fatima tace ga kawa ma kin samu, 

Amina tayi murmushi, tace ai taki ta saba, 

Ita dama take cikin gari, Yaya salma tace wane gari kike? Tace ni 'yar zaria ce, Lubabatu tace kuma kika yarda aka kawoki? Amina tace ai ni dama nafi son boarding school. 

Lubabatu tace lalle, 

Bala yace kuzo mu tafi, magriba ta kusa, 

Lubabatu na hawaye, tace ku gaida min dasu ammi, da mommy, da affan dina, tana kallo suka tafi, sai hawaye take, Amina ta dauki flask din sukayi hostel, 

Amina tace kima ji dadi, gashi 'yan gidanku sunzo kin gansu, amma ki rinka damuwa, 

Ki saki jikinki. 

Amina da kanta ta sa masu, suka hada da bread suka ci, 

Suka bar ma suwaiba sauran. 


      Suma suna komawa gida, abba yaji labarin sunje wurin lubabatu, 

Yace duka yaushe aka kaita, da zaku je, salan ku sa taki karatu, in ba visiting ba, kada in kara ganin wani yaje, ko ba tana bukatan wani abu ba. 


      **********

Kwanaki sun tafi, gashi gobe za suyi hutu, in banda dadi ba abinda lubabatu take ji, sai murna take,

Ta zauna tayi packing din komai nata, 

Dede da ledar indomie da duk wani abu da tazo dashi, saida ta hada dashi, ta fara nade katifa, suwaiba tace ina zaki dashi? Lubabatu tace gida, dan bana son in bar komai nawa a school din nan. 

Suwaiba tace ki barshi, ba abinda ze faru dashi, Sannan ta barshi. 

Washegari kuwa, tunda sassafe ta baro hostel, 

Sai murna take, Amina tace dama kina daria haka? Lubabatu tace gashi kuwa kin gani. 


   Ana bude gate gaba daya duk wasu sun fara tafiya, tana ganin 'yan gidansu, sai murna take yaya fatima tace yau ba kika kenan? 

Amina sai daria take mata, Lubabatu ta kalli Amina, tace to mu zamu tafi, sai nazo daukanki kenan? 

Ta shiga mota, sai daga mata hannu suke,

Suna fita, taji iskan waje ya ratsata, 

Harda lumshe idanu, da sakin ajiyar zuciya, 

Suna isa gida, da gudu da shige, Sede ta bari, suka shigo mata da kayan. 

Ammi tace to 'yan boarding an dawo? 

Da murnarta ta daga affan, sai murna shima yake. 

Ta zauna, Ammi tace ya naga kinyi baki, 

Lubabatu ta bata rai, tace ba dole inyi baki ba, 

Kunje kun kaini inda mutum zeta wahala, Tun asuba idan mutum ya tashi, shida barci sai dare, sai akai har sha daya ba ayi barci ba, 

Ta fara hawaye,Ammi tayi daria, tace to miye abin kuka, tashi kije kiyi wanka, 

Ki dirza jikinki sosai fa, ta mike, Ranar lubabatu tayi wankan jin dadi. 

Tana fitowa, aka zauna, aka yi makeup, 

Ammi ta dauko mata sabon kaya, tace gashi kisa, tace Ammi na gode, 

Saida ta yi break, Sannan tayi gidan mommy, tana shiga, ta fada jikinta, mommy na daria, tace 'yan boarding, naga duk kin rame? 

Tace ba dole ba, Ai boarding bala'i ne. 

Nan ta zauna tayi ta basu labari, 

   Sukaita daria, idan suka ji wani, 

Bayan sun koma gida, ta bude jakanta, 

Ammi tace to ke ai duk baki wani  ci komai ba, 

Tana ta fiddo kayan ciki, taga sai ciro ledojin indomie, Na biscuit duk gasu nan, Ammi tace wannan bolar da da kika kawo mana? Wannan takardar fa? 

Lubabatu tace kwanakin da ya rage, Na rubuta, shine nake cancel kullum, suka yi daria, Sannan tace wadannan ledojin abinda yasa na dawo dasu, saboda ba zan baro komi nawa ba, 

Shine mu kika kawo mana, Ai bola ne, Yaya fatima tace ai ke lubabatu, har yanzu baki da hankali. 

Ammi tace to Kwashe ki kai bola, ta kwashe ta fita dasu, 

Ammi tace naga ko abbanki baki tambaya ba? 

Tace tunda ya kaini boarding ba ruwana dashi, 

Bani waya in kira yaya sultan dina, 

Ammi tace sede ki nemi wayan da zaki kirashi, 

Tunda kin nuna baki damu da mijina ba, 

Lubabatu na daria, tace to Ammi ya hakuri, ki bani inji muryanshi, Ammi ta mika mata, yana dauka, Kamar Zata fasa mashi kunne, tace yaya sultan  shima cikin murna yace lubna kin dawo? 

Bani labarin boarding, nan tayi ta bashi, suna fira, tace yaushe zaka dawo? 

Yace na kusa kada ki damu. 

Sun dade suna fira, Sannan sukayi sallama. 

Koda abba ya dawo, bayan sun gaisa, 

Cewa tayi abba dan Allah ka cireni, ni ba zan koma ba, Yace hakanan zaki yi hakuri, ki koma, tace abba kasan me? Yace a'a, tace akwai 'yan secret code a school din, idan baka cireni ba, zan shiga kungiyarsu nima, daria ma tasa abba, Yace to idan kika shiga kungiyar sai mu bada ke sadaka kawai, 

Tace abba yanzu na gane baka kaunata,

Bakomai, tayi shiru, daga karshe ma ta mike, tayi daki, tayi kwanciyarta. 

Barci nan ya dauketa, dan akwai barci a idonta.

Haka taci gaba da zaman hutu, tana jin kamar ba zata koma ba, ranar ko da aka koma school, harda zawo, 

Haka tayi tayi, harda kwanciya ciwo. 

Yaya fatima tace ammi wallahi ba wani ciwo da take yi, duk pretending ne, Lubabatu ko tanka mata ba tayi ba, dan ita cikin tashin hankalin komawa take, 

Abba yace a bari wani satin sai ta koma. 

Ana gobe zata koma kuwa, ba wanda ba tayi fada dashi ba, dan bata son kowa ya tanka mata, Ranar ko da zata koma, haka ta rinka tima, tana ihu, yanda kasan ana dukanta, 

Da abin ya bama ammi haushi, ta dauketa da mari, ta kara dauketa da mari, tace ni na kaiki makarantar, da zaki nemi ki rinka daga min hankali? 

Ta kara kai mata duka, kara wage bakin tayi tana ihu, tana fadin ni wallahi ba zan koma ba, meyasa sai ni kadai za a kai, saboda ba a kaunata, in ba ku kuka haifeni ba, ku kaini wurin wadanda suka haifeni, ammi tace au ni kike fada ma haka? Dukanta taci gaba dayi, mommy ta shigo gidan, tace haba wai me yake faruwa hakane? 

Ta rike lubabatu, tace duk komawan ne haka? 

Tace mommy bana so, ba dadi, bana jin dadin zaman can, dan idan ba a cireni ba, ba karatun da zanyi, 

Ta fashe da kuka, mommy tace kiyi hakuri, 

Kafin ki dawo, zansa abbanki ya cireki kinji, ki koma din, Kada ki damu. 

Yanzu me kike so? 

Tace bana son komai, mommy tace a'a fada min inda abinda kike so, 

Cikin kuka, tace ki bani tarugu kawai inta ci, har in mutu, dan da inci gaba da makarantar nan, gara na mutu, 

Mommy ta kara riketa, tace haba lubabatu, bani nace zansa a cireki ba, 

Kada ki damu, ko baki yarda dani bane? 

Tace a'a, mommy tace to gama shiryawa, a maidaki ko, ta saketa, 

Lubabatu tayi cikin daki, mommy tace ma ammi, ki dena dukanta, lallabata ya kamata ayi, ammi tace ita kullum 'Yar lallabawa ce? 

Bafa tada hankali har yanzu, Lubabatu na shiga daki, wasu kaya ta dauka, na gida, tasa a leda, 

Ta fito, ta taddasu tsaye duk zasu rakata, 

Ta kallesu, tace duk bana son rakiyar kowa,. Ta fice, ko kallon inda bala yake, ba tayi ba, sai magana yake mata, haka ta fice, ammi ta biyota, tace ke ina zaki? 

Nan waje ta tsaya tarar machine, tana hawa, Yaya fatima, tazo ta riketa, tace ma me machine din tsaya ta sauka, Lubabatu tace ki kyaleni ba ruwanki dani, tace ki sauko, 

Lubabatu tace ba zan sauko ba, Yaya fatima tace to haka zaki koma ba abinci? 

Lubabatu tace ina ruwanki, haka ta dage ta ture yaya fatima, tace ma me machine din, wuce mu tafi, F. G. C zaka kaini, ya tada suka wuce, 

Ammi ta kalli mommy tace kinga halinta ko? 

Mommy tace kyaleta, bala yaje ya kai mata, 

Ammi tace haba yarinya, zaki gane kuranki, se kici abinda zaki ci ai. 

Suna isa, ta sauka, ta sallameshi, ta shige cikin school din, nan ta hadu da wata ta dawo, suka jera, tace mata, dan Allah kwana nawa zamuyi ayi hutu? 

Yarinyar tace mata, Kin san zamu dade, tunda third term muke, 

Sai munyi kusan 3 months, shiru kawai tayi,

Hawaye ya zubo mata, har ta isa hostel, 

Amina na ganinta, da gudu, ta rugo ta tareta, 

Tace sai yau kika dawo ko? 

Tace banma yi niyyar dawowa ba, 

Dan ba yanda zanyi ne, Amina tace to ya na ganki haka, ina sauran kayanki? 

Naga daga ke sai school bag, Lubabatu tace can na barosu, Amina ba zan taba son boarding school ba, 

Na tsaneta, har yanzu ina tsine ma, 

Wanda Ya kirkiro boarding school. 

Allah ya tsine mashi, dan ina jin na tsine mashi, yakai sau chasa'in da tara, cikon na darin, sai randa na bar makarantar, daria ma taba ma Amina, tace kai Lubabatu, boarding school fa yana da dadi, kinki natsuwa ne ki lura, 

Anfi karatu ma sosai, Lubabatu tace ke kika ga haka, dan ni ba karatun da zanyi, Wai da gaske zamu kai wata uku a nan? 

Amina tace eh mana, mu da gida sai august, Lubabatu tace ai yakai wata hudu ma, taf lalle kuwa, 

Amina tace kin san ai third term ne, 

Su aunty suwaiba kuma, zasu gama su tafi su barmu, Lubabatu de bata kara cewa komai ba, suka isa daki, suwaiba ta ganta, tace Lubabatu sai yau? 

Ta gaidata, ta aje jakanta, ta rafka tagumi, ita de suwaiba ta bita da kallo.


            ***************

Haka yaci gaba da Zama cikin school din, 

Taki ta saki, kayan provisions dinta kuwa, haka ta rinka barna dashi, 

Ta hada wannan, ta wancan, Amina tace lubabatu ki dena almuzaranci, zafa a dade, Lubabatu tace bade sun kawoni ba, 

Amina tace kafin ki ga na gida, zafa kisha wahala, 

KO dan kina ganin a garin kike ko? 

Lubabatu tace ko daya, kudinsu ne ze gaya masu, bade sun kawoni boarding ba, mu zuba ni dasu, 

Amina tayi daria, tace lubabatu wani zubin kina bani daria, 

Tafe suke, zasu school area, ta Dauki dutse tana jefe jefe, can wani malami yazo wucewa, tana jefa dutsen, ta jefa a kanshi, da sauri ya juyo, Lubabatu ta kauda kanta. 

Yace kai waye ya jefeni a cikinku? 

Amina tace sir bamu bane, kayi hakuri dan Allah, 

Lubabatu ya kauda kanta, tana wasa da wani dutsen a hannunta, ya jawota, Yace ke kika jefeni ko? Tace bafa da gangan na maka ba, haka ya kaimu har staff room, Yace zaki sani, tace mallam nafa ce maka ba da gangan nayi ba, Yace Amma ai yanda kika nuna, yasa naga da gangan kika yi, dan haka sai na zaneki, tace mallam kada ka bigeni, Amina kallonta ta tsaya yi, 

Dan tasan yanda ake tsoron malamin, amma taga ba alamar tsoro a idon lubabatu, saboda ya haddaci mugunta, 

Haka ya dauki bulala ya zaneta, Yace tashi ki bace min da gani, useless girl. 

Suka fito, 

Lubabatu tace wallahi Amina kinga dukan nan, bashi ya dauka, dan ba zan kyaleshi ba, Amina tace to me zaki mashi? Lubabatu tayi murmushin mugunta, tace kede kisa ido ki gani, Amina tace ni dukan da ya maki ma, tausayi kika bani, amma naga ke baki damu ba, 

Tace ai ba zan damu ba, nide burina kawai in rama abinda yamin, 

Kuma sai na rama, ze san ya taba Lubabatu. 

Suka wuce.

Amina tace dan Allah lubabatu kiyi hakuri, 

Bana so wannan malamin ya sa maki ido, 

Lubabatu tace taf aiko zamu sa ma junanmu kuwa, dan idan yanzu na mashi, yamin wani fa zan kara mashi, 

Amina baki san halina bane, wallahi idan kinga ban rama ba, sai de in mutuwa nayi, Amina tace to yanzu ya zakiyi? 

Lubabatu tayi murmushi, tace kisa min ido ki gani, 

Tun daga ranar idonta yake a kan mallam shamsu, 

     Sun shiga class, taje kujeran malamai, 

Ta tsira allura guda uku a kai, ta samu sit din gaba, wurin rabi'atu ta zauna. 

Rabi'atu na zuwa, tace dan tashi min a wuri, 

Lubabatu tace ba zan tashi ba, rabi'atu tace aiko sai kin tashi, Lubabatu ta kalleta, tace ke ba zan tashi ba, 

Rabi'atu tace oh har kin gama kukan makarantar ne, zaki shigo mana da naki salon rashin mutuncin? 

   Lubabatu tace sosai kuwa, rabi'atu tace to tashi min a wuri, Lubabatu tace wai in tambayeki mana, 

Lokacin da aka kawoki ubanki da kujera ya kawoki school din? Tambayarki nake, ashe ba dashi ya kawoki ba, to ba zan tashi ba, 


   Form master dinsu ya shigo, Yace kai ku kuma lafia? 

Rabi'atu tace sit dina ta zauna, yace ke lubabatu koma naki, tace mallam nifa ba na zauna a nan bane, 

Dan in dauwama, wani dan abu kawai zan aiwatar in tashi in bar mata wurinta,saboda a nan din zefi min dadin gani. 

Yace to rabi'atu ki koma nata idan ta gama, sai ki dawo, rabi'atu ta wuce kusa da Amina ta zauna, 

Amina tace kiyi hakuri, rabi'atu tace ba damuwa, 

Daga ganinta tana da taurin kai gaskia. 

Suna nan zaune ko ya shigo, Lubabatu sai faman murmushi take, 

Bayan sun gaidashi, gaba daya yaki zama, 

Ya kake a tsaye, Lubabatu cikin magana, kasa kasa, tace ka zauna mana. 

Ya Kalli lubabatu yace ke ina hankalinki yake? 

Ana lesson hankalinki na wani wuri, 

Ta kura mashi ido, Wai me ma ya dawo dake gaba? 

Tace ra'ayi.binta kawai yayi da kallo, yana mamakin halinta, 

Yaje zai zauna, Lubabatu ta fara murmushi, 

Wata a class din ta mashi magana, 

Ya dawo, Lubabatu harda cije lebe, 

Taji haushi, 

Bayan ya gama, Yace yauwa na tuna, 

Kowacce ta shirya, test zamuyi, 

Ya gama rubuta masu a kan board, 

Yace ten minutes na baku, 

Kowa ya jawo paper, 

Itade Lubabatu burinta taga ta rama. 

Amina se rokon Allah take, Kada Lubabatu tayi wani abin, 

Bayan sun fara, 

Ya koma ze zauna,yana dosana jikinshi, 

Ya zauna da karfi, da sauri ya mike, 

Yana duba kujerar, 

Ga daya alamun ta shigeshi ya makale a jikinshi, 

Yace uban me kuka sa a kujerar nan? . 

Lubabatu daria kawai take, ta samu ta daure, tace mallam ai gashi nan makale a wandonka, yasa hannu ya jawo, wurin cirewa ya kara jin zafi,Yace uban wa ya min haka? 

Lubabatu tace mallam ya za ayi muyi maka haka? 

Yace ku fiddo min da wanda ya samin allura, 

Rabi'atu tace mallam sede in Lubabatu ta maka haka, tunda gashi ma ba sit dinta ta zauna ba, 

Lubabatu tace akan me zan maka haka, 

Tunda itace taje ta zauna min a wuri, 

Oh se yanzu na gane, ashe shiyasa kika zauna min a wuri, saboda kin san munafuncin da kika hada, to mallam rabi'atu ce, 

Ta bita da harara, Harda murguda baki, shide sai faman murza wuri yake, 

Ranshi a bace, 

Yace dan kunga na tsaya ina sauraranku, every body kneel down, 

Duka sukayi, 

Yace rise up your hand, Lubabatu tace sunan uwar, Close your eyes, 

Tace sunan uban. 

Yace ke me kike cewa? 

Ta bude idonta, tace ni? 

Kasa ce mata komai yayi, ta maida idonta ta rufe, 

Suka fara bashi hakuri, 

Saida ya gaji dan kanshi, Ya kyalesu, 

Tare da zanesu, 

Yana zuwa kan lubabatu taki tsayawa, 

Sai zagaye class din suke, 

Gaba daya class din mamakinta suke, 

Can ya rikota, ta makaleshi, taki bari ya bigeta, 

Sai cukwikwiyeshi take, 

Amina duk hankalinta ya tashi,Lubabatu tace mallam kada ka bigeni,wanda ka samu ma yayi ai, 

Ya samu ya kai mata duka, ya riketa, 

Yace ban yarda dake ba, ke kika aikata min haka, 

Ya kara zura mata bulala, ta rike bulalan, 

Ya kai mata mari, 

Saboda har yanzu abin na damunshi, 

Gani yake raini zai shiga tsakaninshi da students, idan ya kyaleta. 

Ya dinga kai mata duka, ta tureshi ta fice, 

Ya kallesu ranshi a bace, ya fice class din, 

Ta dawo class din tana daria, mamaki ma ta basu, yanda suka ga bata damu ba, 

Ta dawo wurinta tace tashi rabi'atu ki koma wurinki, ta mike, 

Duka sai fadi suke wanda yasa aka bigemu Allah ya isa, Lubabatu tace kude kuka sani, 

Ta zauna, 

Amina tace lubabatu ki dena, tayi daria tace, ke ba wanda ya taba dukana na kyaleshi, sai iyayena, 

Dan haka ni dashi mu zuba, sai naga wanda ze saki a cikinmu, Amina tace lubabatu malaminki ne fa. 

Lubabatu tayi murmushi tace Amina kenan, 

Amina tace yanzu kuma me zaki mashi? 

Lubabatu tace ki kara sa ido ki gani. 

Amina tace idan ko zaki rinka sa ana hadawa da 'yan class, zaki ta shan Allah ya isa, 

Lubabatu tace akwai ranar da Zan rokesu gafara, 

Amina tace to shikenan, amma ni shawarata, da kin hakura, kina gani fa mun kusa yin exams fa,ze iya yaki barinki a class din, bare har kiyi exams din, gashi promotion exam zamuyi,yasa a maki repeating, dan ba mutunci gareshi ba, Lubabatu tace ai sai kiyi, yanzu naji na kyaleshi, har suka tashi, tana tunanin abinda zata aikata mashi na gaba, 

Gaba daya malamai da students sunji abinda tama mallam shamsu, 

Tunda an riga an gano ita tayi. 


Post a Comment

0 Comments