ALAKA 13-14 BEST HAUSA NOVELS


 ALAKA. 13-14 

       *************

Abba ya maidata makarantar da take, taci gaba dayi, idan an koma hutu, zata ci gaba da zuwa. 

Zaune suke, Lubabatu tace Ammi wai ina akuyata? Tunda nazo ban ganta ba, Ammi tace ai yanzu ba naki bane, tunda baki jin magana, 

Lubabatu tace dan Allah Ammi kiyi hakuri, 

Kisa yaya fatima ta rakani in gani, 

Ammi ta kalli yaya fatima, tace rakata,

Daga nan gidan, ban yarda ki barta tayi magana da wasu a waje ba, 

Bare har ta saba da wasu,ta samu wurin zuwa a unguwar, Yaya fatima tace to Ammi, ta mike suka tafi, 

Suna shiga, suka gaidata, ta kallesu, 

Tace ya gida? Suka ce lafia lau, Yaya fatima tace dama lubabatu ce tazo ganin akuyarta, maman sadiq tace au itace lubabatu? Lubabatu tace eh, suka isa wurin akuya, 

Ta rikota, tace la ciki ma gareta tsoho, 

Maman sadiq tace ai da yake me ciki aka samar maki, Lubabatu tayi daria. 

Maman sadiq tace an maki bayani haihuwar farko name kiwo ne ko? 

Lubabatu tace a'a sede ki bari se ta kara haihuwa, Sannan in baki, amma wannan nawa ne, tayi daria, 

Tace Lubabatu kenan, Kada ki damu ai haka akeyi, Yaya fatima tace tunda kin ganta kizo mu koma gida, 

Suka fito, sukayi gida, Lubabatu tace Ammi wai kiji matar nan, Wai haihuwar farko wai nata ne, Ammi tace eh mana, Lubabatu tace nide ba zan bar mata ba, Ammi tace idan ba kiyi wasa ba, duka zan bar mata harda uwar, gara ma kiyi shiru, bata kara cewa komai ba. 


       *************

Kwance take, tana waya da yaya sultan, cikin jin dadi, sai daria take, 

Can tace, Ai akuyata ma ta kusa haihuwa, Yace kai dan Allah, tace da gaske.


Yace to idan ta haihu ni zaki bar mawa ko? 

Tace ai har an bada kyautar 'Yar da zata haifa, 

Wai haihuwan farko ba tawa bace, kuma ba zan yarda ba, Yace a'a kiyi hakuri, idan na dawo, zan sai maki wata, ni da kaina zan maki kiwon ma, kinga bame dauke maki, na haihuwar farko, Sede ki rike abinki ke kadai, tace yauwa yayana, shiyasa nake sonka, yayi daria.


      Sun dade suna fira, tana bashi labari, 

Yana daria, saboda dariyar da take bashi, 

Sannan sukayi sallama. 


       *********

Kwanaki na Kara ja, har sun koma hutu, an maidata, school din da take, 

Dan a cikin hutu ne su kan dan yin waya suna gaisawa. 


     Zaune suke, maman sadiq ta shigo, 

Suka gaisa da ammi, tace to akuya ta haihu, ta samu mace da na miji, 

Ammi tace to ikon Allah, Lubabatu akuya ta haihu, yau mun huta, 

Tayi daria, maman sadiq tace tunda biyu ne, Na dauki akuyar ita sai ta dauki bunsuru, Lubabatu tace bunsuru kuma? Ammi tace au da kika samu ta baki, 

Ai naso ta dauka duka, idan ta kara haihuwa, sai ki dauka, Lubabatu ta zumbura baki, maman sadiq tace lubabatu kenan, 

Ta mike tace to na gode, sai anjima. 

Ta tafi, 

Lubabatu tace ni wai Ammi nida akuyata se ace in tashi da bunsuru, 

Me zanyi da bunsuru? Ammi tace to ki bar mata duka, 

Ta zauna ran nan a bace, bata tanka ma kowa ba, aunty jamila da ummi, suka shigo, da gudu lubabatu taje ta taresu, aunty jamila tayi daria tace, Lubabatu ba a girma, tayi daria, tace aunty duka shekaruna nawa? 

Ta kalli ummi tace kin boye, Ummi tace ina nan, kune baku son zuwa gidanmu, Shiyasa na dena zuwa, 

Lubabatu tace me zamu zo muyi, tunda aunty bata nan, Ummi tace tunda mu ba mutane bane a gidan, 

Bayan sun gaisa, 

Ammi tace aiki ya boyeki, aunty tace kede bari, mutum naso yayi zumunci be isa ba, nan suka dan taba fira, 

Tace bari na shiga ciki, sauri nake, 

Ammi tace baki bari yayyan naki su dawo, 

Aunty tace zaria nake so na wuce yau, 

Bana so nayi dare, tunda na gaisa daku, naga Yara, Ai kamar na gansu ne, 

Ammi tace hakane, 

Tare suka shiga wurin mommy, nan ma bata jima ba, suka fito, Lubabatu wurin rakiya, tace ma ummi ban baki labari ba, akuyata ta haihu, dan de kuna sauri, 

Dana kaiki kin gansu, Ummi tace ai zan dawo, Lubabatu tace shikenan. 

Suka tafi. 


Daga nan ita kuma gidan maman sadiq ta shige, da wayan Ammi a hannunta, 

Haka ta yi ta daukarsu, tana masu hoto, tana yi tare dasu, 

Maman sadiq de se daria take mata, 

Seda ta gama ganinsu, Sannan ta dawo gida, ta kira yaya sultan, tace akuyata ta haihu, mace da namiji, Yace iye, Kinga data haihu mun samu wasu, tayi daria, 

Tace bari ma na turo maka ka gansu, 

Haka ta shiga whatsapp din Ammi, 

Duk ta tura mashi, Bayan ya gani, 

Ya kirata, Yace na gansu, kema kinyi kyau, 

Haka kika kara kyau, daria kawai tayi, 

Seda lokacin islamiyya yayi, Sannan suka yi sallama, ita kuma ta yi sallah, tayi shirin islamiyya, Sannan suka tafi.

Gaba daya sun zauna gaban ammi suna bata hakuri, Lubabatu tace ammi ki dena kuka, 

Ammi tace to ya zanyi, shi muke kallo muji dadi, 

Abba ya shigo, Yace kiyi hakuri addu'a yake bukata, 

Ammi ta share hawayenta, Yace yanzu ki tashi kiyi hakuri, ki kwanta. 

  Kinga gobe da wuri zakiyi sammako. 

Tace ko na kwanta ba barcin zanyi ba. 

Abba yace daurewa zaki yi, ta mike ta shiga dakinta. 

Abba ya bita, 

Lubabatu tace kiga ammi fa, kanin babanta ne fa ya rasu. 

Amma take wannan kukan. 

Babanta ma ya rasu ta hakura, bare wannan. 

Sai ta bari 'ya'yanshi suyi kukan. 

   Yaya fatima ta kalleta, tace ni dadina dake har yanzu baki da hankali. 

Kamar fa baba yake a wurinta. 

Lubabatu tace amma ai bashi ya haifeta ba. 

Yaya fatima ta mike, ta shige daki, 

Ta barta nan zaune, ita da affan, itama daukanshi tayi, suka bi yaya fatima ciki. 


       *************

Washegari kuwa, Tun asuba, ammi ta gama shirinta, 

Mommy ce ta shigo gidan, tana kara mata gaisuwa. 

Har mota ta rakata, tace insha Allahu ina nan zuwa. 

Da yake ita da abba da daddy zasu tafi. 

   Ita kuma ta kula da gida. 

     Su kuma komawa gida sukayi, suka ci gaba da shirin tafiya school. 


        ************

Bayan sun dawo, da yamma suna shirin tafiya islamiyya. 

Lubabatu ta kalli yaya fatima, tace yaya fatima, 

Dan Allah ki temaka min, ban Iya haddar yau ba. 

Yaya fatima tace au duk baki tashi yi ba, 

Sai yanzu da lokacin islamiyyar yayi, 

Zaki ce wani baki iya ba. 

Ni ba abinda zan iya maki a yanzu. 

Sede kije duk abinda ze maki ya maki. 

Tunda ke ba zaki taba zama ki koyi abu da wuri ba, wasa yaci karfinki. 

Lubabatu tace to naji, tunda ba zaka koya min ba, se kiyi shiru, baki zauna ba kina fada min magana. 

Shirinta taci gaba dayi, 

Ta shirya affan suka fita. 


     Bayan sun isa islamiyya, mallam ya shigo, yana amsar hadda. 

Tun kan yazo kanta, ta fara kuka, Bayan ta mike, Yace lubabatu ya akayi ne? 

Cikin kuka tace baban ammi ne ya rasu, 

Ta tafi maiduguri yau, kuma bata je dani ba. 

Yace Allah sarki, Kiyi hakuri, Allah yaji kanshi. 

Yanzu zaki iya karantawa? 

Cikin kuka, tace eh. 

Yace to ina sauraranki, Bayan ta fara. 

Ko aya biyar ba tayi ba. 

Ta kara fashewa da kuka, Yace kiyi hakuri, zauna, gobe kya karanta min. 

Zama tayi, ta hada kanta da gwiwa. 

Tana murmushi, zainab dake zaune kusa da ita. Tace lubabatu nafa sani haddar ce baki iya ba, Shiyasa kika yi haka. 

Nasan baki ma mutuwa kuka. 

   Lubabatu tace to naji kiyi shiru de. 

Nasan halinki, Murmushi kawai zainab tayi. 

Bayan sun tashi, a hanya, haka zainab tayi ta basu labari. 

Yaya fatima tayi daria, tace wallahi ba ta iya karatun bane, Shiyasa tayi haka. 

Zainab tayi daria, tace ni nasan haka ai. 

   Yaya fatima tace kede kika sani, wallahi inde ba zaki girma ba, kina tare da wahala. 

Lubabatu tace eh din naji, ba ruwanku dani. 

Kuma akan abinda nayi, duk wanda yaci gaba da tada maganar, duk rashin mutuncin da na mashi, shi ya siya da kudinshi. 

Gaba daya daria suka ci gaba dayi mata. 

Suna isa gida, saida zainab ta bama mommy labari. 

Mommy daria harda hawaye, tace kai Lubabatu, da abin daria kike. 

To yanzu ai sai ki zauna, ki koya, tunda yana nan yana jiranki gobe. 

In ba kukan zaki ci gaba da mashi ba. 

Lubabatu ta kara daure fuska, tace mommy karya fa take yi, mommy tace ai ni na sani, Lubabatu ba zatayi haka ba. 

Yanzu tashi kuyi alwala, idan kuka gama, sai ki zauna kiyi karatunki ko? 

    Ta mike tayi alwalanta, Bayan ta idar da sallah, mommy tace yanzu zo muje dakina, ki zauna kiyi karatunki tsanake ko. 

Taja hannunta, suka wuce dakinta. 

Tace kiyi zamanki nan, dana gama hada ma su daddy abincinsu zanzo muyi tare ko. 

Bari inje, saboda suna hanya. 

  Haka ta zauna taci gaba da karatunta. 

Har mommy ta gama hada komai. 

Ta dawo dakin, tace yauwa 'yar albarka. 

Yaya kin iya ko? 

Haka suka yi ta yi tare da mommy, 

Har seda taga ta iya, Sannan ta kyaleta. 

Tana yin sallan isha'i, nan ta kwanta dakin mommy, rayuwar Lubabatu tana son mommy, dan ita da yaya sultan ne kawai suke binta a hankali a gidan nan. 

Duk abinda tayi ba daidai ba, Sede su gyara mata cikin kwanciyar hankali, ba tare da fada ba. 


Shiyasa tana son mommy sosai. 


     *************

Sai misalin karfe sha daya na dare, Sannan  suka iso garin. 

    Nan lubabatu taci gaba da zama gidan mommy, haka affan ma. 

Dan duk inda lubabatu tasa kafa, shima nan yake sa nashi. 


 Ranar sadakan uku, mommy ta shirya tabi jirgi, ta ta isa maiduguri. 

Kwananta daya, suka juyo tare da ammi.


  ************


Rayuwa taja, shekarun sunja, yanzu ba laifi, Lubabatu na daukan kanta budurwa. 

  A lokacin gashi har su yaya fatima sun gama secondary, had sun daura karatunsu, ita da salma, 

Inda suka samu admission a ABU zaria. 

Ita de lubabatu yanzu suna ss3,tace ammi nide idan na gama secondary school, gaskia ba zan ci gaba da karatu ba, aure zanyi. 

Ammi tace ke lubabatu ni kike fada ma haka? 

Lubabatu ta zumburo baki, tace nide Ammi gaskia na fada, dan ba zan iya yin karatu ba, nafi so nayi aure. 

Ammi ta kai mata duka, tace tashi ki fita ki bani wuri, ta mike ta koma daki, 

Tace nide koma me zakuyi, aurena zanyi. 


    **************

Duk abinda aka sa mashi rana sai yazo, 

Yau gashi su yaya sultan nata shirye shiryen dawowa gida nigeria. 

Inda suka dage tun zuwansu basu waiyayi gida ba, sai da suka had'a har masters dinsu. 

Yau gida cike yake da murna, Tun ba lubabatu ba, baki yaki rufuwa. 

Abin alfaharinta, farin cikinta, zai dawo gida, 

Kusan shekaranta nawa, rabonta dashi. 

Sai dai suyi waya. 

Dede da abinda zasu ci, ita ta zauna ta shirya masu, dan duk abinta. 

Wurin girki, dole ka bata lambar yabo. 

Ranar haka ta zauna ta tsantsara kwalliya. 

Yanda kasan wadda zata gasar kwalliya. 

Mommy na kallonta, tayi daria, tace gaskia lubabatu kinyi kyau sosai. 

Tayi murmushi, tace mommy da gaske? 

Tace sosai kuwa, yau yayanki baze ganeki ba gaskia. 

Daria ta kara yi, 

Komai seda ta shirya masu, lokacin har a tafi taho dasu. 

Lubabatu saboda zumudi, komawa kofar gida tayi, tana jiran dawowarsu. 

Tana nan tsaye, mota ta danno kai. 

Gaba daya Washe bakin tayi, tana kallon motar, nan aka bude gate din suka shiga. 

Itama shigowa tayi, 

Suna fitowa, da gudu ta ruga, ta rungume yaya sultan, tana fadin yayana nayi missing dinka, shi kuma sai daria yake, 

Ya dan cireta daga jikinshi, ya rike mata hannu, Yace nima nayi missing dinki sosai. 

   Tayi murmushi, Yace lubna ta ce ta koma haka? 

Daria ta kara yi, yana rike da hannunta, suka shiga cikin gida, dan shi yaya aliyu har ya shige, ya barsu nan. 

Yace ina rashin ji? Tace yanzu babu. 

Yayi Daria, Yace ai na fara ganin alama, ya ragu. 

Suka idasa daki. 

Mommy kanta bakinta yaki rufuwa. 

Su zainab suka fara gaidashi, Yace bana amsawa, tunda baku damu dani ba. 

Wadda ta damu dani, waje na tarad da ita, tana jiranmu, suka ce yaya kayi hakuri. 

Nan suka gaisa. 

Lubabatu ta kalli yaya aliyu tace yaya aliyu an dawo lafia? Kallonta yayi, Yace lafiya lau. 

Nan de suka mike, suka shiga ciki. 

Saida suka gama shiryawa, Sannan suka fito. 

Nan suka zauna, duka gidan, Su Ammi, dasu abba, duk ana sashin daddy. 

Yaya sultan yace ina fatima fa da salma? 

Lubabatu tace ka manta suna school. 

Yace au na manta, nan suka fara cin abinci. 

Yaya sultan yace kai wannan irin dadi haka, wa ya girka mana? Mommy tace gata nan lubabatu, ta hana kowa ya taba komi, duk ita tayi. 

Yaya sultan yace gaskia kanwata wannan abinci yayi dadi, Yaya aliyu yace ina fa dadi, ta jagwalgwala girki. Ai sede aci dan kar a mutu.

Daria wurin sukayi, Lubabatu ta zumburo baki, tace yaya sultan kaji abinda yace fa. 

Yaya sultan yace kyaleshi,yasan girkin yayi dadi, kawai miskilancinshi ne baze bari ya fadi haka ba. 

Ai wannan abincin, ko wadda tayi degree ne akan girke girke, ba zata gwada maki iya girki ba. 

  Lubabatu tayi daria, tace shiyasa nake sonka yayana. 

Daria sukayi. 

Saida suka gama cin abincin sannan yaya aliyu ya mike, Yace to nide zan dan shiga daga ciki in kwanta, dan na gaji. 

Idan wannan yarinyar na wurin nan. 

B zata bari mutum ya huta ba. Mommy tace kai de ka sani, Murmushi kawai yayi, ya fice abinshi. 

Lubabatu ta bishi da kallo, ta dawo da kallonta wurin yaya sultan. 

Tace kalleshi idan da ba dadi, Ai da ya aje be ci ba, amma kalli yanda yaci da yawa. 

Yaya sultan yace ki kyaleshi ai gulms ce. 

Abba yace kude kuka sani, kaima yanzu ka tashi ka wuce kaje ka huta. 

Yayi Daria, Yace to abba ya mike, Tare da lubabatu suka fito, har daki ta rakashi. 

Ya kalleta yace in baki tsarabarki? 

Ko zaki bari sai na tashi barci? Tace to Ka kwanta, idan ka tashi sai ka bani. 

Yace to shikenan, taja masu kofar ta fita. 

Ta koma daki, tayi zaune sai murmushi take, kome take aiyanawa a ranta oho. 

Dan yanzu kara jin yaya sultan take a ranta.


Da lubabatu aka bud'e tsaraba, haka ya kawo mata, " 'katuwar wayarta." 


    Banda kaya da ya siyo mata. 

   Kowa an bashi tsarabarshi. "


Tun dawowar su yaya sultan. 

"shakuwa ta kara shiga tsakanin lubabatu da yaya sultan."

  "sede yanda da yake janta a jiki, baya janta yanzu."

Gashi ita kuma har yanzu ganin 'karama take ma kanta."



Ko ta shige mashi,' kokari yake yaga ya cireta daga jikinshi." 


     *************

"lubabatu ce tafe d'akin su yaya sultan."

d'auke da "jug d'in kunun" gyad'a "a hannunta." 

Tana shiga d'akin,"ta zauna kusa dashi."

"tace yaya sultan, gashi na gama. 

"yace yauwa kanwata."

Ya zuba a cup,"yasha. 

Seda yasha kunun nan sosai. 

"sannan ya kalleta,"yace sannu ko..!

"wai lubabatu," wa ya koya maki wannan girki haka?"

"ta kashe mashi ido," da yanzu ya zame mata jiki."

Tace haba yaya sultan,"da gaske kake,"wai na "iya girki sosai?" 

Yace gaskia kam ina jin "dad'in girkin ki."

"tayi daria..!

Tace yaya sultan," da "kwamacala, na " iya girki  fa."

     "akwai ranar da ammi ta sani girki, na cika masu yaji, ya waro idanunshi..! 

Yace kai dan Allah?" 

"tace da gaske."

Aiko duk suka kasa cin abincin."

Tayi daria."

Tace kasan ma da suna ci me nace masu?"

    "yace "a'a", tace seda na d'aga masu gira."

Na d'anyi daria."

Sannan nace masu ya kuka ji girkin?"

Yayi dad'i ko?"

Ammi ta harareni,"tace idan na tashi zaki ga yanda zanyi dake,"girkin da ba dad'in" gaba, bare na baya."

"kuka kasan ni kaina,"nasan abincin beyi dad'i ba."

Yaya sultan yayi daria. 

Yace kai "lubabatu", har yanzu de, kina nan yanda kike."

Tace kai yaya sultan."

   "yaya aliyu ne ya shigo. 

Ya kallesu," yace kuna  nan kuna shirman da kuka saba? 

Ka zauna kayi ta biye ma yarinya."

   

   "lubabatu ta bishi da harara. 

Y d'auki abinda zai d'auka, ya fita," ya bar masu "d'akin."



    **************

" yaya sultan," yace yauwa lubabatu."

"baki bani labarin "akuyarki ba." 


    tace "uhum,"  bari kawai yaya sultan..! 

"ai idan na baka labarin nan, sai ka tausaya min."

Ya "gyara zamanshi, Yace kice labari ne mai tsawo?" 

Tace sosai kuwa. 


   Bana baka labarin akuyata ta farko ba.“

Har na fad'a maka matsalar dana samu,"da wasu ma duk da aka siyo."


Yace eh."

Tace to ai ta mutu.! Yace innalillahi.! 

Yaushe?"

Tace bata dad'e ba, Yace duka ko wata biyu ba ayi ba, kika ce min ta haihu."

Tace kaide bari," ai ka bari in baka labarin tun daga akuyar farko. 

Har zuwa kan ta 'karshe."

Yace to ina jinki."


Tace to bayan an bar min bunsuru, Kasan na riga na nuna bana so."

Sai abba, Yace inyi hakuri, idan ya tashi ze 'kara siyan min wani. 

 Sai in had'a guda biyu."

Sai na bar mata, ita kuma uwar," daga baya, sai ta gaza, abba yasa aka yanka aka soya."

Kaga na tashi banda ko d'aya kenan."

Ya 'kara gyara zama, Yace tofa.!"

Labari mi'ka'k'ka."

   Tace yaya sultan sede fa idan na fita, inga bunsurun nan, ya gitta ta kofar gidanmu ya wuce," nida abina."

ina ji ina gani, bunsurun da na raina. 

Da christmas,"akayi cinikinshi dubu biyar."

    Abba da ya tashi ya 'kara siyan min wata akuyar."

Da tafiya tayi nisa,"

Itama akuyar nan sai ta haifi' yan biyu."

Mace da namiji," aka ce sede Kiwon farko in bar mata."

Banda wancan dana bar mata. "

  Da aka ga na'ki yarda, sai aka' kara bani bunsuru," 

Kaji fa rainin wayau."

Yaya sultan daria ya fara yi, Harda kwanciya 'kasa."

   "lubabatu tace ka bari in gama maka mana." 

Ni kuma nace aiko ba a isa ba,"ya za ayi nida akuyata, sai ace in rin'ka tashi da bunsuru.! 

   Tafiya tayi tafiya,"sai kakar ta mutu."

Nan na tada balli, nace ni kuma wallahi, Sede in ta d'auki bunsuru, ni kuma na d'auki akuyar."

Kan haka, abba har dukana ya kusa yi."

Dan kasan Allah."har yanzu ban ha'kura ba, 

Dan sai ya biyani."

Shi aka ja mawa."

Yaya sultan yace idan na baki shawara, zaki d'auka?"

Ta d'aga mashi kai. 

Yace ki ha'kura da Kiwon nan, dan be amsheki ba."

Tace kai yaya sultan! 

Ya d'aga mata gira."

   Tace to naji amma ba zan ha'kura ba,"

Sai ya sai min wani abu."yace ki bari ni zan baki wani abu."

   

  Tade yi shiru, ba tare da tace komai ba."


      Yace kinga da boarding dinki kika zauna. 

Da yanzu kin kusa gamawa."

Ta kalleshi."

Tare da waro ido.! 

Tace taf.! 

Yaya sultan baka san boarding bane,"

Bashi da "dad'i, gashi duk rashin rowan mutum sai ya koya." 

  

   Idan ba haka ba, baka yi loma biyu ba, sai de kaga plate."


   Shiyasa idan na had'a abinci zanci."

Idan zan masu tayi, Sai in d'aure fuska. "

In d'anja kwanon, in ri'keshi, Sannan in bismillah.! 


  Idan naga mutum ya cika hannu, ince d'an rage."

Banda 'katuwar loma."


Yaya sultan ya hau daria," harda rike ciki."


Yace kai lubabatu" baki da dama."

    Kice malamai ba 'karamin fama suka yi dake ba."


Tace ai shiyasa principal ta'ki amsata."


  Yace yau de kin bani daria, Kinga tashi ki tafi ki kwanta, dare yayi."

Ga bros ma naji muryarshi ze shigo d'akin,"


   Kinga gobe ma akwai abinda nake so na fad'a maki,"

Tace to Ka fad'a" min yanzu, Yace kiyi hakurin gobe, 

Zan fad'a maki ai."


   "kinga dare yayi yanzu, muje in rakaki."

Tare suka fito, Yaya aliyu ya kallesu,"

Yace sai yanzu shirman naku ya 'kare?! 

Allah ya kyauta."

Ya shige ya barsu nan."


 "lubabatu koda ta koma d'aki," tana kwanciya. "

Barci ya d'auketa." 


  Burinta.! Safiya tayi, taji me yaya sultan ze fad'a mata."


Washegari kuwa, tunda taje suka gaisa da yaya sultan,take tambayarshi me ze fad'a mata!? 

Yace  "yanzu ba makaranta zaki ba, 

To ki bari idan kika dawo, zan fada maki, bani nace zan fada maki ba. 

Da haka ya lallabata ta tafi. 


    ************

Aiko tana dawowa d'akinsu ta wuce. 

Yana kwance ta samu kusa dashi ta zauna. 

Ya Kalleta, Yace "yace har kin dawo?" 

Ta d'aga mashi kai.

Sannan tace  "nazo inji me zaka fad'a min." 


   Yace   "kai ba zaki bari sai kinci abinci ba, kinyi wanka kin huta."

Ta d'an kalleshi, tace "abinda zaka fad'a min yafi duka wad'annan." 

Kai kawai nake saurare. 


   Daria yayi, Sannan yace  "lubabatu inaso zamuyi magana, sai de ban sani ba a irin shekarunki, ko zaki fuskanceni." 


Tace  "yaya sultan wane irin magana?" 


Ya kalleta, gami da furzar da iska daga bakinshi. 


Tace   "yaya sultan kai nake jira."


Binta yayi da kallo, Yace "lubabatu ban san ya zaki d'auki maganata ba.

Ina tsoron fad'a maki." 


Tace  "kada ka damu, koma miye, ka fad'a min, ba wani abin tsoro bane."


" yaya sultan ka manta yanda muke da ne?"

Bafa nida aboki sama dakai, to me ze gagareka da zaka kasa fad'a min. "

Kallonta, yayi yaga yanda ta natsu tana magana. 

Yace "hakane."


"lubabatu tun kina k'arama, kika shiga raina,nake biye ma duk wata shirmanki, har zuwa girmanki."


"lubabatu ina sonki.! 


Tayi dariya, tace "kaji yaya sultan." 

Nima ai ina sonka. 

Dama nace baka sona ne. 

Shima dariyan yayi, Yace  "bari in fahimtar dake, Lubabatu ina sonki, 

Inaso na aureki.!


    Waro idanunta waje tayi, sai kuma ta mik'e, ta fice d'akin da gudu. 

Dariya ya hau yi mata. 


Haka ta shiga d'aki, sai faman maida numfashi take. 


Ammi ta shigo, tace "ke kuma lafia?" 

Tun dazun kuka dawo, amma baki ga daman shigowa gida da wuri ba."

Nishin me kike haka?"


Tace   "bakomai."

Ammi tace "Allah ya kyauta."


Ta fice a d'akin. 


Lubabatu ta fad'a kan gado, sai faman murmushi take,tana juyi, sai faman juya idanu take. 


Wayanta ya fara k'ara, tana dubawa, taga yaya sultan, sai ta tsinci kanta da kasa d'aukan wayan. 

Har ta katse, ya k'ara kira, saida ta kusa katsewa, Sannan ta d'auka. 


Ta kasa magana, dariya yayi, Yace  "yau kuma ni ake jin kunya?" 


Dan na fad'i abinda ke raina. 


Ta kasa magana, sai de murmushi. 


Yace  "yaya sultan d'inki ne fa, da kike yawan fad'in baki da miji sai shi, gashi kuma zan cika miki burinki, kina min wulak'anci."


"tunda baki sona, Na janye."


Da sauri, tace "a'a yaya sultan."

Dariya yayi, duk ta kasa magana, sai kace bashi bane abokin firanta. 


Post a Comment

0 Comments