AGOLA 2

 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani 

NABILA RABI,U ZANGO

( Nabeelert Lady)


@ ( H,O,N,A)


Part 20.....25


Da sallama suka shiga cikin gidan, cike dasauri Zarah tafito tayi kyau se kamshi takeyi zuwa tayi ta rungume megidanta tana dariya, shima dariyar yakeyi.

   Janshi tayi zuwa daki, su Hajjo suna tsaye bakin kofa, Jalila ce tajasu zuwa wani daki, bandaki ta nuna masu sannan tashimfida masu abun sallah tafita domin kawo masu abinci da ruwa, bayan sunyi sallah sukaci abincin da Jalila takawo masu.


Atare suka fito bayan yayi wanka, yafito cin abinci, zuba mashi tafarayi, saurin tashi yayi yana kiran Jidda da Jalila, bayan sunzo yace ina bakin da mukazo tare? Jalila tace suna dakin baki sunyi sallah suna cin abinci, ajiyar zuciya yayi yace yau Jalila nagode.

    Ya mutsa fuska Zarah tayi tace Alh, wane irin baki ne suka shigomun gida bansan da zuwansu ba, zama yayi yafara cin abincin shi yana murmushi. Zamatayi kamar zatayi kuka tace ina magana amma kayi shiru, haba hajiya, ai komenene kinbari ingama cin abinci ko.


Zaune suke afalo suduka, ayayin da su Hajjo suke zaune kasa. Zarah se cika take tana batsewa, Hajjo duk jikinta yafara sanyi ganin irin kallon da Zarah take yimasu, ko gaisuwarsu da kyar ta amsa, dama Zarah batason mutane, bare kuma dataga kyawawan mutane suzo tare da mijinta.


Gyaran murya Alh, yayi anan yayi masu bayani akan su Hajjo, har labarinsu seda yabasu. Jalila se kuka takeyi, gaba daya tausayinsu yakamata. Jidda da Zarah kuwa yatsuna fuska sukayi, zuciyar Zarah kamar zata fashe dan haushi.


Alh, yace sbd haka nakawosu gidan nan inafatan kuma zaku rikesu tamkar yan uwanku.... Zarah tace dan Allah Alh, dakata, kayi mani bayani yanda zanfahimta, idan ma masu aiki ne ka kawomun ni banida bukatarsu, inada me aiki, dan gaskiya wadan nan sadakar yallan bazasu zauna mun agida ba, idan ma temakonsu zakayi kabasu kudi sukama gabansu.


Murmushi Alh, yayi yace Zarah ai baki tsaya kika gama jin abinda zance ba ko, kinrufeni da fada kamar kinsami wata Jidda ko Jalila, kuma dan rashin mutunci agaban mutane zaki rufe ido kina fadamun abinda kikaga dama.

   Ina fatan acikin bayani na danayi bakiji nace zan ajesu agidanki ba. Agidana nace zan ajesu ko? Dan haka ki kula da kalamanki. Kuma wannan dakike gani Hajjo, insha Allahu cikin satin nan za,a daura mana aure, Falak kuma zanriketa kamar yanda zanrike Jalila ko Jidda.

    Bana son inkara jin wata magana kuma Jidda ku kiyaye, dan haka wancen part din acan zasu zauna, bance ku hada girki ba, kowa nashi zeyi, abinda nakeso asamu zaman lafiya acikin gidana, kinfi kowa sanin halina banason tashin hankali ahakan yasa bamu taba samun sabani nida ke ba, seyanzu. Dan haka ki kiyaye.


Jalila ga key din wancan part din nan zanyi magana da megadi kuje keda Mairo ku tsaya ya gyara idan nafita zansa akawo kaya azuba aciki dan yau nakeso su koma.


Murmushi tayi tace angama Dady, tashi yayi yace Hajjo kutaso muje. Fita sukayi suka shiga mota. Kasuwa yanufa dasu.


   Wasu irin zafafan hawaye ne suke zarya afuskar Zarah, tunda take da Alh, betaba yimata koda tsawa bace bare fada. Amma yau gashi sbd wasu banzaye yana fadi mata maganganu. Jidda tamatso kusa da ita tace haba Ummi meyasa sbd wannan maganar zaki daga hankalinki, tunda nataso agidan nan bantaba ganin kukanki ba seyau, tayama za,ayi inso wadan nan mutanen masu kama da aljanu.

   Wlh Ummi kinfi karfin yin kishi da fillo, ki kyalesu zaman gidan nan seya gagaresu, naso ace acikin part dimmu zasu zauna wlh damun samu. Masu aiki, amma bakomai idan sunsan wata basusan wata ba.


Jalila tace haba Yaya Jidda, da bakinki kike fadin wannan maganar, kada kimanta fa suma mutane ne kamar kowa, kuma ko ba komai duk abinda Dady yakawo gidan nan ai yakamata mudaukeshi da daraja, kuma ai...... saukar marin dataji ne yahanata karasa maganar datakeyi.

     Zarah tace dama batun yauba nasan bakida kishi akaina, nadauka kune masu goyamun baya aduk halin danake ciki, amma segashi dabakinki kike fadin wannan maganar. Wlh idan kinaso mushirya kifita aharkar wadannan mutanen, idan bahaka ba, kuma zamusa kafar wando daya dake. Tashi tayi tashige daki taci gaba da kuka, aduniya babu abinda ta tsana kamar kishiya, seyanzu take ganin wautar ta narashin mallake Alh, tuntuni ta biyema shawarar Karima, gashi nan duk irin kissar datakeyi mashi be hanata yimata kishiya ba. Lallai wannan tafiya ni akaimawa, kuma nasamu tsaraba me tsoka. Amma wlh duk yanda zanyi matar nan bazata dade agidana ba.


Kafin sudawo har angama gyaran part dinsu, masu kaya sunkawo ansaka aciki, komai yayi dede tun daga labule , kujeru, gadaje da kayan kitchen babu abinda ba,a saba, dakin Falak kadai ya isa ya burgeku, komai na bukata seda aka saka aciki sannan driver yashigo da kayan abinci yasaka a store ya kulle gidan, yatafi.


Se yamma suka gama siyayya lefe sosai yahada mata. Itama Falak babu abinda be saya mata ba, Hajjo har kuka tayi sbd murna, gidan abokinshi yawuce dasu, anan yayi mashi bayanin komai, matarshi Zainab mace me kirki ta tausaya masu sosai. Alh, yace inaso kuje muje gurin telanki domin abashi dinku nansu dan dawuri nakesonsu.

    

Farouk yace bakomai Dauko hijabinki muje nima inyi rakiya, abokina kace nanda kwana 5 zaka angwance, lallai wannan tafiya tayi riba. 

     Seda ya gwadasu sannan Alh, yabashi kudin dinkinshi yace nan da kwana 2 azo akarbi kala 5 na amarya kala 3 na Falak zeyi kokarin kara wasu kafin biki, idan yaso sauran zuwa bayan biki se azo akarba. Godiya sosai, suka yimashi suka tafi. Basune suka koma gida ba se karfe 7 na dare, makulli ya amsa gurin driver suka nufi part dinsu yabude. 

    

Mamaki ne yakama su ganin irin kayan da aka zuba agidan, duk da ba baki bane aganin irin kayan amma sunji dadi sosai. Bayan sunzauna. Hajjo tace Alh, bansan dawane irin. Baki zanmaka godiya ba, kagama mana komai arayuwa sede inroki Allah yabamu ikon saka maka da mafificin alkhairin daka yimana.


Murmushi yayi yace Hajjo basekin godemun ba, domin kingama mun komai tunda kika amsa zaki aureni, nima Allah yabani ikon kamanta gaskiya atsakaninku. Abinda nakeso dake ki kasance me hakuri, banason tashin hankali, kuma nasan baki dashi, kiyi hakuri da duk abinda zaki gani, daga gurin Zarah, nasani sarai bata da son mutane, shiyasa ma na ajeku anan, koda banida wannan part din bazan iya hadaku agida daya ba, dan haka kuyi hakuri dasu.

    Kuma insha Allah bayan biki Falak zaki cigaba dazuwa makarantar su Jalila. Nasan aji daya za,a saka ku tunda kince a ss 2 take , itama Jalila haka. Kome kukeso akwaishi akitchen, Falak inaso kidaukeni kamar mahaifinki, kada kiboyemun damuwarki dan Allah, kuma kizauna da yarana kamar yan uwanki. Godiya suka kara mashi sannan yayi masu seda safe yace su kulle kofar,


Adaki yasamu Zarah kwance, kusa da ita yaje yajawota yana fadin haba my luv yau kuma ni ake sharewa haka. Kinsan fa bamuyin haka dake, dan Allah kada kibari shedan yashiga zuciyarki yabata mana zaman lafiyar damukeyi na tsawon shekaru da dama.

    Murmushi tayi data tuna shawarar da Karima tabata, dazu fasuka gama waya, tace Zarah maza yan lallashine, idan harkinaso kimallake zuciyar namiji kozakiyi mashi asiri dole sekin hada da biyayya da kuma kissa, idan bahaka ba, kina zaune wata zatazo ta kwace maki miji, kawai ki kwantar da hnklinki ayi biki agama idan yaso da kssa ki koreta, amma idan kina tada hankalinki kome yafaru da ita ke za,a ce.


Kara rungumeshi tayi tasaka kukan kissa, tana fadin dan Allah Alh, kayi hakuri nayi nadamar yimaka abunda bantaba yimaka arayuwata ba se yau, kuma agaban ,ya,yanka da bakinka. Allah yasa haka yazama alkhairi, nide fatana kayi adalci atsakaninmu.


Sosai yaji dadin abinda tafada, dama yasan kishine yasata fadin abinda tfada dazu, goge mata hawayen idonta yayi yace nagode sosai matata, Allah yabiyaki, insha Allahu zaki sameni mecika alkawari, bazan taba juya maki baya ba, kema kinsan aduk duniya kece mace ta farko dana fara so, kece uwar yara na, babu abinda ze rabamu. Tashi sukayi tarakashi zuwa bandaki yyi wanka sannan suka kwanta.


Washe gari bayan yashiga sun gaisa dasu Hajjo yanufi gidan kawunshi, anan yafada mashi abinda ke tafe dashi, sosai kawunshi yaji dadin maganarshi, dan suma sungaji da halin matarshi narashin son mutane, yace bakomai Allah yakaimu asabar din, amma waye ze zama waliyinta? Yace abokina Farouk shine yace ze zama waliyinta. Yace to Allah yakaimu, kuma sekayi kokarin rike amanar marayun Allah daka dauko, yace insha Allahu kawu, anan yayi mashi godiya yatafi.


Ana saura kwana 2 biki komai ya kan kama har dinkunansu ankawo saura wadanda ba,a dinka ba, sosai sukayi kyau acikin kwanakin dasukayi, bakamar Falak, kyawunta yakara fitowa, Jalila kadai take shigowa part dinsu dan ita hakanan takeson Falak, amma Jidda da Zarah tunda sukazo basu kara sakasu aido ba, dan Hajjo macece wadda batason wulakanci shiyasa ta tsorata da irin abinda Zarah tayi masu, hakan yasa bata kara shiga part dinsu ba. Duk yanda Alh, yaso tashiga amma tace itade tsoro takeji yabari bayan biki tashiga.


Sallama aketa kwadawa acikin falon, da kyar Zarah tafito tana yatsina ta amsa sallamar. Ahankali tace tofa yau kuma Inna Asabe ce agidanmu, washe baki tayi tace wlh Babanki ne yace kwana 2 bakizo ba, shine yace inzo inga ko lfy. Zama tayi tace tokema Inna banda abunki tunda kukaji shiru ai kunsan lafiya ko, amma kinwani kwaso kafa kintaho.


Ran Inna yabaci dajin maganar Zarah, amma dayake ita Allah yayita da shegen kwadayi yasa tace ayi hakuri hajiya. Anan tasa Mairo takawo mata abinci da lemu, zama tayi tanata zubi tana zuba surutu.


Zarah tace Inna namanta banfada maku ba, Alh, aure zeyi fa. Cike da mamaki tace haba Hajiya wace irin magana kike fadi haka, kamarki ace wai za,ayi maki kishiya kuma kizauna kina fada ma mutane, aini atunanina mutanen kauye wadanda basu waye ba, sune akema kishiya, yanzu duk cikin kawayenki wakika gani da kishiya? Gaskiya bazata sabuba ayima yata haka. 

   Matsowa Zarah tayi jin irin maganar da Inna take fada. Asabe tace wlh na dauka tuni kingama da Alh, seyanda kikace yakeyi shiyasa bandamu davkawo maki maganin mallaka ba, kina tunanin duk son dayake maki idan matarshi tafara haifa mashi namiji agida baze manta dake ba. Gaskiya bazata yuwu ba.


Zarah tace yauwa Innata dan Allah kifadamun abinda yakamata inyi, dama neman abunyi nake, segashi Allah yakawoki, wlh konawa zan iya kashewa inde za,a fitarmun da wannan fulanin agida na. Murmushi Asabe tayi aranta tace anzo gurin, tunda baki badawa dan Allah yanzu kam lokacina yayi nima dazanyi arziki, wlh sena ta tseki kamar me.


Asabe tace kada kidamu acan zariya kinsan munada manyan bokaye, dan haka akwai kawata Dije tana da wani hamshakin boka, inaso bayan biki kizo muje gurinshi kome kikeso za,ayi maki. Godiya sosai Zarah tayima Asabe harta manta da irin abunda takeyimata dazu, Zarah tace yauwa Innata ainasan koda nayi rashin Uwa bazanyi kuka ba tunda ina dake, amma de anan zaki kwana zuwa gobe se insa driver yamaida ke ko. Mamaki sosai Asabe tayi jin yau tasamu matsayin kwana agidan Zarah. Anan suka cigaba da firarsu


Urs 

NABILA RABI,U ZANGO

( Nabeelert Lady)

08028525

: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)


@ (H,O,N,A)


Part 25.....30


Ayau asabar aka daura auren Alhaji Abba da Hajara akan sadaki naira dubu 30, mutane dayawa sunsami halartar daurin aure.


   Acikin gida kuwa babu wanda yazo ta bangaren Zarah daga Karima se Inna Asabe, dan yanzu sosai Zarah take mutunta ta, sbd zata kawo mata mafita amatsalarta. Tare da kawarta tazo wato Dije, sunci sun sha sunkuma kwashi ganima.


Jidda kuwa alokacin bikin ma bata kwana gida ba, tana can gidan kawarta Ameera bayan sundawo daga party suka wuce gidansu Ameera acan suka kwana.

   Jalila ce itada mairo me aikinsu suka shiga bangaren su Falak suka tayasu aiki, matar farouk ma tazo, sekuma yan uwan Alhaji.

   Hajjo tayi kyau sosai, idan kaganta bazaka ce Hajjo daga sani bace a wata 5 dasuka wuce, ita kanta tasan rabonta da farinciki irin na yau tunkafin mutuwar mijinta.


Haka akayi biki kowa ya watse aka bar amarya da diyarta agida, Jalila ce ita da Falak zaune adain Falak. Jalila tace wlh Falak nakosa asakaki makaranta nima insamu abokiyar tafiya, musammamma islamiyya, banida kawar tafiya, dan Yaya Jidda tadena zuwa kuma Ummi tahanani infadama Dady. Falak tace ai gara kada kifada mashi, addu,a kawai zaki tayata, kinsan kowa da irin tashi kaddarar. Jalila tace haba Falak, ko kinsan jiya ba,a gida yaya ta kwana ba, wlh ina matukar jin bakincikin halin da yaya tasa kanta, wlh ko sallah ba sosai takeyi ba, idan namata magana karshe zagine zebiyo baya.

    Falak tace tabbas Yaya Jidda tana cikin jarabawar ubangiji, sede muyi ta mata addu,a Allah yashiryeta, kuma kada kibari Dady yafara jin maganarta abakinki tunda kinsan abinda Ummi tace. Jalila tace nagode Falak bara intafi kada Ummi tanemeni.


Zaune suke gaba dayansu a falon Alhaji, Zarah tana zaune akusa dashi, bakaramin dauriya tayi ba, wajen boye damuwar dake zuciyarta. Hajjo ko gaba daya tsoro yahanata sakewa ta kosa takoma part dinta.

   Alhaji yayi gyaran murya yace, Alhamdulillahi, Allah yanuna mana wannan rana damuke fatan zuwanta.

Zarah takanki zanfara, kece Babba, inaso dan Allah, kamar yanda nasanki bakida fitina acikin gidan nan, haka nakeso kicigaba dazama ayanda nasanki, ku hada kanku, kidauki Hajjo tamkar kanwarki, kuma kirike Falak tamkar Jidda ko Jalila, abanson kubari wasu suzo susamu damar tarwatsa farin cikin damuka gina shekara da shekaru acikin gidan nan. Allah yabaki hakuri akan wanda kikeyi, banyi auren nan dan bana sonki ba, ko kuma da niyar in wulakanta kiba,nayi ne domin ina bukatar hakan, kuma dan inraya sunnar Manzon mu.


Kema Hajjo, inaso ki saki jikinki acikin gidan nan, kidauki Zarah kamar yar uwarki, da yayanta amatsayin naki, banason wata fitina, duk abunda baki ganeba nacikin gidan nan zaki iya samun Zarah ki tambayeta, ko kuma ni kitambayeni.

    Maganar girki kuma dama nafada maku, kowa nata zata rikayi, Hajjo idan kina bukatar me aiki Zarah kisa Mairo tasamo mata, ko kuma idan zata iya tarika yimaku ku biyu, ko ya kikace Hajjo? A,a bakomai Alhaji, ai aikin ma bawani meyawa bane, zan iya yi nidaya, tacigaba dayima Umminsu Jalila, idan ina bukatar wani abu zansa mairo tayimun.


Zarah tace haba Alhaji ai base anakara kawo wata me aiki ba, Mairo ma ta ishemu, Fatana Allah yabamu zaman lafiya, kuma Hajjo dan Allah kiyi hakuri da abinda nayi maku farkon zuwanku, sharrin shedan ne. Hajjo tace lah, ai babu komai.

    Muemushin jindadi Alhaji yayi yace, to Zarah yakike ganin za,a yi gurin raba girki? Zarah tace bayan kagama kwana 3 ina ganin muyi kwana 2 ko hajjo? E duk yanda kikace yayi hakan. Alhji yace to Allah yabani ikon kwatanta adalci atsakaninku. Bara muje mukwanta naga dare yayi, tashi Hajjo tayi tamata seda safe tawuce, jawo Zarah yayi ya rungume, kwallar data ke boyewa ce tazubo, saurin kifa kanta tayi bisa kirjinshi. Kara rungumeta yayi yana lallashinta, da kyar yasamu tabarshi yatafi.



Haka rayuwa tacigaba datafiya cike da kwanciyar hankali, ansaka Falak makarantar su Jalila,inda aka sata a ajinsu Jalila SS 2, alokacin su Jidda suna shirin gamawa, sosai take gane karatun, dama Falak bade kokari ba, cikin lokaci kadan tazama zakaran ajin, hatta da malamai sun santa. Babu abinda ke hadata da Jidda, dan bakaramin Tsanarta Jidda tayi ba, sbd kyan datake dashi, ko magana tayi mata bata amsawa, amakaranta idan akaje daukarsu tarinka fadama kawayenta ga AGOLAR gidansu nan, abun yana matukar damun Falak, kullum sede Jalila tarika bata hakuri, duk irin cin mutuncin da Jidda takeyi mata bata taba fadama Ummanta ba, sbd tasan Ummanta dasaurin damuwa.


Zaman gidansu Zarah zamane na kissa, domin baka taba gane Zarah batason Hajjo, duk da bawani shiga part din juna suke sosai ba, amma tana nuna mata so.kuma Alh, yana iya kokarinshi akansu, babu abinda suka nema suka rasa, duk irin kudin da yake basu Hajjo bata siyan komai, sbd acewarta babu abinda suke bukata. Hakan yasa taroki Alh, dasuje ta duba account din Falak, tanaso ayi mata ATM, sannan tacigaba da ajiyar kudi aciki.

     Tare sukaje akayi mata komai, sannan tasaka dukan kudin datasamu abiki da kuma wanda yake basu, 



Bayan wata daya da bikinsu, Hajjo tafara laulayi, zazzabi me zafi takeyi, hakan yasa Alh, yaduketa suka tafi asibiti, suna zuwa awon farko akace tana da shigar ciki na sati 3. Murna agurin Alh, kamar ba,a taba yimashi haihuwa ba, bayan sundawo gida yawuce part din Zarah. Anan yake fada mata cikin Hajjo, Da kyar Zarah ta dedeta kanta sbd wata irin faduwar gaba ce tazo mata jin Hajjo tana da ciki, murmushi tayi tace kai amma naji dadi, ai gara mukara samun yara agidan, amma wadan nan ,yan matan dasunyi aure shikenan gidan ze koma shiru. Alh, yace wlh kuwa, Allah de yasa tahaifa mana aboki. Dif murmushin fuskarta yadauke, shi bema kula da yanayin data shiga ba, haka yayi ta zuba, daga karshe yakoma part din Hajjo.


Wata irin zufa taketo mata, daki tashiga, tarasa abunyi kawai tasaka kuka. Lallai namiji ba abin riko bane, wai yau Alh, dakanshi yake maganar ahaifa mashi yaro, wato sbd yaga niban haifa mashi ba. Wlh dole gobe inje Zariya, nadena kaima Karima kuka na, dan naga idan nabiye mata zata kaini tabaroni, yanzu lokacin kissa da biyayya sunkare dole se boka yashigo cikin al,amarin nan. Allah yakaimu gobe da safe.


Washe gari dasafe ko abinci Zarah kasa ci tayi, haka su Jalila suka gama shiri sukayi mata sallama, tace masu zataje zariya kilama ta kwana. Sukansu sunyi mamakin jin kalmar zuwa zariya abakin umminsu, kuma ma har maganar kwana takeyi, ganin kamar suna yimata wani kallo yasa tace masu Inna ce bata da lafiya. Sukace Allah yabata lafiya, idan kinje kiduba ta.


Segurin karfe 9 Alh, yashigo, alokacin Zarah harta shirya jiranshi kawai takeyi, sanin Alh, bame hana zuwa unguwa bane shiyasa bata damu da seyanzu zata fada mashi ba.


Bayan sungaisa yace waini Zarah ina zuwa naga kinfito da jaka da gyale? Murmushi tayi tace wlh jiya bayan kafita akamun waya daga gida cewar Inna batada lafiya, to ganin dare yayi shiyasa banfada maka yau zanje ba.


Ashsha, meyasa meta? Tace gsky basu fadamun abinda kedamunta ba, amma idan naje zanji,sede gobe nakeso nadawo. Mamaki ne yakama Alh, sede yaboyeshi dan bakaramin dadi yaji ba, dayaji Zata kwana agidansu, acewarshi kila tafara canza halinta ne. Shikenan babu damuwa Allah yakiyaye hanya, kinga akwai inda zanje aida muntafi tare, amma idan nasamu lokaci zanje indubota. Zarah tace ai bakomai idan najema yawadatar, zanhadaku awaya. Yajikin Hajjon? Murmushi yayi yace jikinta dasauki ai tasha magunguna. Daki yashiga yadauko mata kudin naira dubu 100 yace tarikesu ahannunta ko za,anemi wani abu, godiya tayi mashi, yawuce yafita, tace gata nan zuwa ta duba Hajjo. Mairo ta kwala ma kira kasancewar anan take kwana, dan dattijuwa ce. Bayan tazo tafada mata zataje gida se gobe zata dawo. Ita kanta mairo tayi mamaki, duk abinda zasu bukata ta bata sannan tawuce part din Hajjo.


Bayan ta dubata ta tashi zata tafi, Hajjo tashiga daki tadebo sabulan wanka dana wanki masu yawa tace akaima Inna, godiya Zarah tayi mata sannan tafita aranta tana fadin abanza wlh, babu abinda zesa naji tausayinki, haka nan daga zuwanki keda waccan shegiyar AGOLAR taki kunaso ku mallakemun miji.


Murna duk tacika Inna da Baban Zarah ganin yau Zarah ce agidansu kuma harma zata kwana, Inna tace Malan ai yakamata ka koma kasuwa hakanan kazo ka tsaya acikinmu kamar mace, jiki na rawa yace wai da zama zanyi mugaisa da Zarah ta, tunda taxo ai yau babu batun kasuwa kuma. Zarah tace Baba kaje kawai ai anan zan kwana yanzu akwai inda zanje. Inna tace idamma kazauna mezaka bata, yace shikenan to sekun dawo, haka yafita Inna tana binshi da harara aboye, abinda baku sani ba, Asabe tadade da mallake Baban Zarah, dama kuma tahanyar asiri tashigo gidan, dan Asabe muguwar yar tasha ce dan ba,a cikin Zariya take ba,yawon iskancinta ne yakawoya zariya harta hadu da Baban Zarah, Kawarta Dije ta tsaya mata har ta aureshi, kuma tayi sanadiyar mutuwar uwar Zarah ta mallakeshi take zaune agidan, ko Zarah tarasa yanda zatayi da ita ne shiyasa take zaune da ita, dayake ta iya kissa, hakan yasa mutanen gari suke ganinta kamar ta kirki. Ganin Zarah ta auri me kudi yasa ta saduda tamaida kanta sakarai agurinta saboda itama tayagi rabonta

Se gashi Allah yakawo mata hanyar sauki dazata ci kudinta aruwan sanyi. 

   Bayan Zarah tabata sabulan da Hajjo tabada akawo mata, Asabe tace kinga irin kissar tata ko, ina nan dake idan alh, yazo seta fada mashi abinda tabada aka kawomun,tashi muje gidan Dije, wannan bazesa mukyaleta ba. Alh, baze kara haihuwa da kowa ba, sede ke. Murmushin jindadi Zarah tayi tace shiyasa nake sonki Innata, yauwa ga waya ma nataho maki da ita, nasaka maki layi aciki sbd idan inason wani abu basena nataso nazo ba, banason Alh, yafara zargin wani abu, tunda yasan bazuwa nakeyi sosai ba. Asabe tace dama Hajiya tunda kinada mu agari ai kinwuce kije gurin boka da kanki, aisede kibamu umarni muyi, godiya tayi mata, sannan suka nufi gidan Dije, daga can suka wuce gurin boka, dama Dije ba miji gareta ba.


Abakin bukkar bokan Dije tace sujirata tashiga akwai maganar dazasuyi dashi, kashe ma Asabe ido tayi sannan tashiga, dayake boka natane, anan tayi mashi bayanin abinda takeso yacaji Zarah, dakuma kasanshi idan tabayar, da abinda zasu dauka ita da Asabe.


Fita tayi suka shigo tare. Bayan Zarah tagama yimashi bayani, Boka yayi dariya yace cikin kikeso alalata ko kuma akasheta gaba daya? Fiddo ido tayi, tace boka bazan iya kashe mutum ba, kawai a lalata cikin, idan yaso daga baya da kaina, nasan yanda zanyi inkoreta. Boka yace aikinki yana da tsada, amma sbd wadan nan zanyi maki sauki. Zarah tace boka kudi badamuwata bane, konawa zanbiya inde za,a cire cikin. Boka yace kije can kidaga wancan kwaryar kisaka dubu 150. Tashi tayi jiki na rawa taciro kudin tasaka. Wata diyar roba yadauko hannunshi yasa abisa cikinta yarika wasu surutai, yana murza cikin, wata kara sukaji anyi, Zarah takama Asabe tarike, aje diyar robar yayi yace matso nan ki gani, wata kwarya me ruwa aciki yadauko nan take hoton Hajjo yafito, tana kwance se juyi takeyi akasa, kafafunta kuma jini yana fita. Boka yace cikinne yake fita, angama da wannan matsalar, se nakara ganinki. Tashi sukayi suna mashi godiya.zasu fita boka yace Dije ke kitsaya. 

   Bayan sunfita, boka yace gaky Dije kun kawomun matar dazan ci kudi kuma kuci, lallai bayanzu zan sallami wannan matar ba, semunci kudinta, sosai, kudin yadauko yadauki dubu yadauki dubu 80 yabasu 70, godiya Dije tayi mashi tace semun sake dawowa.


Urs,

NABILA RABI,U ZANGO

( Nabeelert Lady)

08028525263


[7/8, 4:02 PM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani

NABILA RABI,U ZANGO

( Nabeelert Lady)


@( H,O,N,A)


Part 30..... 35


Falak ce tayi sallama tadawo daga makaranta, kaitsaye dakin Ummanta tanufa, cikin sauri ta ajiye jakarta takarasa gurin Ummanta, ganinta kwance cikin jini tana nishi.

   Kiran sunanta tafarayi tana kuka, ganin takasa amsa mata tayi waje da gudu domin kiran driver, fitar ta yayi dede dashigowar Alh, tsaya wa tayi haryayi parking, dasauri ta isa gurinshi, tana kuka.

   Fitowa yayi yana tambayarta lfy? Tace Umma ce batada lafiya. Ai bejira ta idasa ba, yayi hanyar part dinsu. Yana zuwa yaga halin datake ciki , hijabinta yasa mata yadauketa, Falak tana biye dasu, mota yasata, Falak na kokarin shiga sega Jalila. Alh, yace yauwa Jalila zamuje asibiti Hajjo ba lfy, ku kula da gidan. Shiga yayi yaja suka tafi.


Suna zuwa aka wuce emergency da ita, Alh, se zagaye zagaye yakeyi, Falak ko se kuka takeyi, shikan shi Alh, tabashi tausayi. Seda suka dauki minti 30 sannan aka fito da ita abisa gado aka nufi, dakin da aka bata da ita, bin bayanta Falak tayi, shikuma yabi bayan likitan.


Zaune suke a office, Dr, yace Alh, sede kayi hkr cikin dake jikinta yazube. Sede bamu samu wani dalilin daze nuna mana abinda yayi sanadiyar zubar cikin ba. Amma alhamdulillahi, babu wata matsala atare da ita, anyi mata wankin mahaifa, kuma anyi mata allurai, insha Allahu zuwa dare ma zaku iya tafiya, semunce Allah yakawo wani me amfani. Zufar data fitoma Alh, agoshi yagoge, sannan yace ameen, Dr, nagode. Sosai yaji ciwon zubewar cikin sede babu yanda zeyi dole yayi hkr da hukuncin Allah, tashi yayi yanufi dakin da suke.


Zauns suke adakin Asabe, Zarah tace gaskiya Inna nagode maki, yanzu nakara tabbatarwa banida sama dake, dana tsaya bin shawarar Karima dayanzu ina can ina tagumi. Kome kenan idan akwai wata matsala, zanyi maki waya sekuje gurin bokan, basena zoba, idan kuma takama dole senazo se inzo din.

Wayarta ce tayi kara, ganin Alh, ne yake kira yasata saurin dagawa, jin muryarshi cikin sanyi, yasa tace lfy de Alh, naji kamar wani abu yana damunka, naji muryar kasa kasa.

   Anan yafada mata abinda yafaru, salati tafarayi cike da damuwa kamar zatayi kuka tace Alh, gani nan tahowa, tunda ko la,asar ba,ayi ba. Yace aa kibari se gobe, tunda itama Inna bata da lafiya. Tace a,a ai taji sauki, nide bazan iya zama ba, Hajjo tana da bukatata akusa yanzu, kasan su Falak yara ne, dole asamu wata babba akusa da ita, tunda Mairo aiki yayi mata yawa . Sosai yaji dadin yanda Zarah ta nuna kulawarta akan Hajjo.

    Bayan sunyi sallama tayi murmushi tace lallai aikin boka na kyau, Asabe tace meyafaru? Dije tace ai base an fada maki ba, kema kinsan cikin yabi ruwa. Dariya suka sa suduka. Zarah tace dani kike magana Hajjo. Bara intashi intafi, kada yamma tayi. Kudi tafiddo dubu 2000 tamika masu tace ga wannan asayi magi, godiya sukayi mata, suka rakata har mota, tazo shiga kenan Babanta yadawo, yace a,a Zarah ina kuma zaki? Tace wlh yanzu Alh, yamun waya abokiyar zamana tana asibiti, shine nace gara intafi. Baba yace wayyo Allah yabata lafiya, amma kin kyauta. Allah ya kiyaye hanya kidubata idan kinje. Dubu 1 tamika mashi tace Baba ga wannan anyi cefane, godiya yayi mata yanata shimata albarka, har ta tafi. Asabe tace malam kawo indauki kudina najiya, kasande ai baka baniba ko? Kamar zeyi kuka yace haba Asabe wlh koda naje kasuwa babu abinda nasamo, kuma idan nabaki dari 500 dama kuma meshago yana bina dari 300, kinga kudin sunkare, dan Allah kiyi hkr zanbaki. Dije tace a haba malam kabarshi wasa take maka bakomai tabar maka. Godiya yashiga yimata, anan yawuce masallaci, sukuma suka nufi gida.


Dije tace wlh wani lokacin bakida tausayi Asabe, duk irin kudin da kika samu yau, wanda rabon da ki rike irinsu harkin manta amma saboda dari 500 kinemi sama dan bawan Allah hawan jini. Asabe tace kinsanni akan kudi banida mutunci wlh, tunda harna iya kashe mazajena 2 saboda kudi, kinsan banida mutunci akan kudi, shiyasa bazan daga ma Zarah kafa akan kudi ba wlh, kina ganin sabida tsabar rowa dubu 2 tabamu duk irin wahalar damukasha, amma dayake biyan bukatar tane 150 taba boka. Dije tace ki kwantar da hankalinki, ai tunda de zata iya bada ko nawa ne ayimata aiki, mukam kakarmu ta yanke saka. Kinsan konawa boka yadauka yabamu sauran?  80 yadauka wlh, dariya Asabe tayi tace kai amma wannan boka yanada kirki, gaskiya naji dadi, dauko kibani kasona in adana.


Tunda Zarah ta isa gida wanka kawai tayi, taci abinci tawuce asibiti, lokacin dataje, har Hajjo ta farfado. Tea ta hada mata, takamata suka je bandaki. Seda tayi wanka tagyara jikinta sannan, Zarah tamika mata kayan da Alh, yakawo mata, sawa tayi tafito. Falak ce tashiga bandakin domin wanke kayan data cire.

   Bayan tasha tea taci abinci sannan tasha magungunanta. Zarah tace sannu Hajjo, Allah yabaki lfy, ya kuma kawo wani me amfani. Hajjo tace ameen. Zarah tajuya taga Falak bata nan, kuma Alh, yaje yin sallah. Tace amma Hajjo meze hana kibari sekin warke sosai sannan ki kara samun ciki, ina nufin kizo inraka ki gurin likitana asa maki robar hana daukar ciki, amma kada kibari Alh, yasani kinga seki huta sosai, daga baya se acire maki, nasan Alh, beda hkr ko baki warke ba, yana iya zuwa karbar hakkinshi, kinga niyanzu na huta. Hajjo takurama Zarah, ido harseda ta tsargu.

    Zarah tace kinyi shiru, murmushi tayi tace ai likita ma yace kozan kara samun ciki senan da shekaru sbd barin dana samu. Ajiyar zuciya Zarah tayi, batasan lokacin da murmushi ya kwace mata ba, tace wayyo gaskiya na tausaya maki, amma ai bakomai wata rana zaki samu. Kallonta kawai Hajjo takeyi, aranta tace ai idan mutum yanuna baya sonka daga farko, koyazo daga baya yace yana sonka kada kayarda dashi.


Segurin karfe 8 aka sallamesu. Bayan sunkoma gida, Alh, yace mairo tarika shiga tana taya Hajjo aiki kafin tasamu sauki. Zarah tace ai bakomai ma taje tayi mata sati 2 harta warke, Hajjo tace a,a Ummin Jalila ai za,a barki da aiki, idan tagama maki tunda nawa babu yawa setazo tamun. Alh, yace shikenan hakan ma yayi.


Tundaga wannan ranar Mairo take shiga part din Hajjo tana taya ta aiki, sosai mairo takejin dadin aiki agurin Hajjo, sbd tana da kirki, kuma bata kyamarta kamar Zarah, gashi tanayi mata alkhairi akai akai, harcewa takeyi dama Alh, yasamoma Zarah wata ita abarta anan, idan ta tuna aikin sati 2 kawai zatayi takoma can dazama batajin dadi, Sosai suke zama da Hajjo suyi ta fira, shiyasa ma seta gama aikin Zarah take tahowa gurin Hajjo. Duk wani labari na Hajjo babu wanda bata sani ba, sbd hakanan Hajjo taji mairo ta kwanta, mata gatade dattijuwa, amma tana bata girma, shiyasa ma bata iya kiranta da mairo sede tace mata Baba mairo, hakan bakaramin dadi yakema Mairo ba, Falak da Jalila ma haka suke cemata, amma banda Jidda.


Jidda ce kwance adakin saurayinta Al,amin, bayan sungama aikata masha,arsu, Al,amin yace Dear nah yakamata fa kitashi kiyi wanka inmaida ke gida, kinga ankusa tashi daga islamiyya, tunda nagama dora maki nawa karatun. Murmushi tayi tace wlh, dande Dady yana gari da anan zan kwana, banason tafiya inbarka. Al,amin yace nafiki son haka Jidda, shiyasa naso ace kinbari nazo gidanku muyi aurenmu mu huta kikace bakison aure yanzu. Jidda tace wlh, Al,amin rayuwar aure takura ce, duka yanzu shekarata nawa dazanyi aure, ai gara inbarai sena kai irin 27 ko 28 haka, yauwa lokacin nakara girma. Amma kawai yanzu da kuruciyata inshiga sahun manya. Murmushi Al,amin yayi yace shikenan ai nima bawai auren ne yadameni ba, tunda de inada kudi na nasan bazan rasa yan mata ba, duka Jidda ta kaimashi yana dariya yace, kemafa bani kadai kike kulawa ba, abinda nasani de nida ke muna son junanmu sosai, amma kowa yana kula duk wanda yasamu, ko kin manta da kaina ina hadaki da aboka naina masu kudi, kuma ni seki hanani kula wasu, aikinsan harakar bariki kowa yanada yanci. Jidda tace naji de amma aikasan kai na dabanne tunda kaine kafara sanina ,ya mace, yace wlh Jidda akanki nafara wannan sana,ar. Shiyasa nake bala,in sonki Jidda na. Murmushi tayi tace bara inyi wanka.


Haka rayuwarsu tacigaba datafiya, hanakalin Zarah bakaramin kwanciya yayi ba jin Hajjo bazata haihu yanzu ba, arizikin mijinsu sehabaka yakeyi, shiyasa yabiya ma Hajjo da Falak da su Jalila hajji, yace ma Zarah tabari tunda ita taje wata shekarar se sukara tafiya tare, baya son abrshi shi kadai. Bakaramin dadi taji ba, za,a barmata mijinta.


Lokacin da Mairo tacika sati 2 tana aiki agurin hajjo, ranar data dawo bangaren Zarah sallama takeyi amma jin shiru yasa tawuce dakin Zarah, taje zata kwan kwasa taji Zarah kamar tana waya, har zata juya taji Zarah tana dariya tana cewa, ai wlh, Inna Asabe, yanzu hankalina akwance yake, tunda mukayi nasarar zubar da waccan cikin na hajjo likita yace kozata kara haihuwa senan da shekaru, shiyasa nace dole inyima boka babbar kyauta sabida yabiyani, yanzu Alh, yabiya mata hajji ita da yara, harda wannan AGOLAR banzar akabiya mawa, narasa meyasa Alh, yake son maidata kamar kowa agidan nan. Ai kede kibari da sannu zankoresu subar gidan nan, toshikenan sekinjini. Mamaki ne yakama mairo jin abinda Zarah take fadi, saurin komawa tayi tanufi dakinta, tana tunanin hanyar dazata bi domin. Kare Hajjo daga sharrin Zarah.


Urs,

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)

08028525263

[7/8, 4:02 PM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)


@ (  H,O,N,A)


Fita Mairo  tayi tashiga kitchen tacigaba da aikinta, tana tunanin maganganun Zarah, hakade ta barma cikinta, danbazata so afara jin wata magana abakinta ba, amma tayi alkawarin zata sa ido sosai aharkar Zarah, tunda tagano tacanza halinta.


Haka rayuwa tacigaba da tafiya, harsu Hajjo sunje hajji sundawo, sosai tayima Zarah da Baba mairo tsaraba, bayan kwana biyu suka shirya zuwa Abuja ita da Alh, domin kaima matar farouk abokin Alh, tsara barsu, dan bayan bikinsu akayima Faruok transfer yakoma can. Kwanansu 2 acan, bakaramin bacin rai Zarah tashiga ba, anyi tafiya banda ita.


Bayan dawowarsu, Mairo tashiga part din Hajjo, tana zuwa ta isketa abandakin falo tana ta amai, temaka mata tayi, bayan tagama suka dawo falo, mairo tace sannu Hajiya, amma inaganin kamar ciki ne dake ko? Hajjo tace nima haka nake tunani, dan tunkafin muje hajji nadena ganin al,ada ta, sede yaune nafara amai. Mairo tace aikinsan yanzu ba cikin farko bane, kila ma yayi wata 2 shiyasa baki fara laulayi dawuri ba.


Amma zankawo maki wani magani, inde kinsha zaki dena amai kuma zakiji kwarin jikinki. Hajjo tace aiko nagode Baba mairo, wlh bansan da abunda zan saka maki ba, Allah yasani nayi rashin uwa, amma gashi yanzu Allah yabani ke, inajinki tamkar uwata, babu abinda zan iya boye maki. Kwallan da mairo take boyewa suka zubo mata, Hajjo tace Baba mairo meyafaru kuma?  Mairo tace bakomai, kawai naji dadin kalamanki yata, tunda nake bantaba haihuwa ba, banida me kirana mana, segashi yau kinbani babban matsayi wanda bakowa ne yake amsa shiba. Hakika yau ina cikin farin ciki wanda. Nadade banji ba. Allah yayi maki albarka keda diyarki Falak.


Sede inaso infada maki wata magana, ada ina shakkun infada maki, sbd bansan yazaki daukeni ba, kila bazaki yarda da maganata ba. Amma ayanzu dakika bani matsayin uwa agareki, nasan zaki yarda da abunda zan fada maki, dan kinsan uwa bazata fadama yarta karya ba.


Inaso kiboye cikin dake jikinki har lokacin da zaki haifeshi, ko Alh, banaso kifada mashi kina da ciki harse yayi girma, nasan shi baza,a iya boyemashi ba. Hajjo tace meyasa kikace haka Baba mairo, nasan dole akwai dalilin dayasa kikace haka, dan Allah kifadamun koma menene, nayi maki alkawarin bazan bafadama kowa ba.


Anan mairo tafadama Hajjo duk abunda taji Zarah tana fadama Asabe awaya. Hajjo tagoge kwallan idonta, tace wlh jikina yabani Zarah ba sona take ba, kawaide tana yimun fuska 2, lokacin da aka kwantar dani asibiti take cemun wai inzo tarakani asakamun robar hana daukar ciki.


Anan jikina yabani wani mugun nufi take nufi dani, kawai sena fada mata likita yace kozan haihu senan da shekaru, wlh Baba mairo ina gama fada mata bakiga wani murmushi datayi ba. Tun daga nan nagane abinda take nufi dani.


Kuma insha Allah Zarah bazatasan ina da ciki ba sede taji haihuwa ta. Shima Alh, bazan fada mashi ba harse yayi kwari, shima sena rokeshi kada yabari kowa yaji, Mairo tace bara inje inkawo maki maganin.


Haka Hajjo tacigaba da renon cikinta babu wanda yasani daga mairo se Falak, su Jidda anyi graduation duk da bawani kokari tayi ajarabawarsu ba, su Falak kuma sunshiga ss3 karatu sukeyi sosai dan sunaso sucigaba da karatunsu idan sungama.


Jidda yanzu duk inda Al,amin zeje tare suke zuwa, ko da kwana nawa zeyi tunda Alh, baya zama gida yanzu sosai, Zarah kuwa tunda Jidda tana wadata ta da kudi babu abinda yadameta, abinda Jidda tagane ma Zariya tamaida gurin zuwanta, tunda taga Asabe bata kwaba mata duk inda taje kotayi dare bata cemata komai, kuma Baba bashida katabus agidan, hakan yasata yanzu tafi zama Zariya akan gidansu, koda Alh, yaji tana zuwa Zariya dadi yaji saboda yaga umminsu ita bata zuwa.


Lokacin da cikin Hajjo yacika wata 7 aranar Alh, yagane tana da ciki, yace lallai ma Hajjo yanzu nikike boyema abun farin ciki?  Dariya tayi tace wlh banso kagane ba, naso kawai kazo kaga jariri ko jaririya, shiyasa ko zanje awo nake cemaka zanje wankin kai. Amma kayafemun da karyar danayi maka. Jawota yayi yace bakomai, aikinsan dama ni ina baku damar fita duk lokacin da kukeso koda bana nan.


Amma gaskiya naji dadi sosai,  Allah yasa rayayyene, tace ameen. Amma dan Allah banaso kafadama Kowa har ummin Jalila, nafiso inbata mamaki tunda kai kaganoni.

    Yace shikenan angama daukarta yayi suka nufi daki.


Su Falak suna third term a ss3 Hajjo ta haifi yaronta me kyan gaske, babu wanda yasan tahaihu, dan cikin dare nafara nakuda kuma taci sa,a Alh, agurinta yake, haka suka hada kaya suka nufi asibiti, Falak kawai tasan suntafi, gurin karfe 8 suka dawo, bayan ya kaita part dinta yawuce part din Zarah, yanashiga yahadu da Mairo, yace tabar abinda takeyi taje Hajjo ta haihu, sosai mairo taji dadi, tace me aka haifa, yace namiji, barka tayi mashi sannan tawuce part dinsu.


Farin ciki kawai Alh, yakeyi, dakin su.  Jalila yaje yace tafito tacigaba da aikin da mairo takeyi, dan taje gurin Hajjo ta temaka mata ta haihu. Jalila cike da murna tace Dady meta haifa?  Yace kunsamu kani Jalila bakaramin dadi taji ba, fita tayi tawuce kitchen. Dakin Zarah yashiga, ganin yana cikin farin ciki ga bakinshi yaki rufuwa, tace Alh, yaude lafiya kake kamr wanda aka yima bushara da gidan, aljanna? Yace aidole kiganni haka, Hajjo ta haihu kuma tasami namiji me bala,in kama dani. Dariya Zarah tayi tace amafarkin yau ne kaga haka? Yace wlh da gaske nakeyi, tun dare muna asibiti. Zarah tace karbo yaron kukayi kome, nide nasan Hajjo bata da ciki. Ganin zata bata mashi lokaci yajata zuwa part din Hajjo.


Mutuwar tsaye Zarah tayi ganin Alh, yamiko mata yaro me bala,in kama dashi, kamar an tsaga kara, wata irin zufa ce tarika keto mata ta ko ina, tama rasa mezatayi, takasa karbar yaron, hawayene suka taho mata tayi saurin juyawa takoma. Falo, mamaki ne yakama Alh, ganin abinda Zarah tayi, amma su Hajjo sun harbo jirginta.


Urs,

 NABILA RABI,U ZANGO

(  Nabeelert Lady)

08028525263

Copied By

YAYA HAYAT 

        (admin 

   Hayat hausa novels

Hausa novels and fashion

Cool novel, makeup and kitchen1⃣

Cool novel, makeup and kitchen2⃣

                   AND 

Cool novel, makeup and kitchen3⃣) 



      WHATSAPP NO:

   +2347039625239

[7/13, 09:39] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)


@ (  H,O,N,A)


Fita Mairo  tayi tashiga kitchen tacigaba da aikinta, tana tunanin maganganun Zarah, hakade ta barma cikinta, danbazata so afara jin wata magana abakinta ba, amma tayi alkawarin zata sa ido sosai aharkar Zarah, tunda tagano tacanza halinta.


Haka rayuwa tacigaba da tafiya, harsu Hajjo sunje hajji sundawo, sosai tayima Zarah da Baba mairo tsaraba, bayan kwana biyu suka shirya zuwa Abuja ita da Alh, domin kaima matar farouk abokin Alh, tsara barsu, dan bayan bikinsu akayima Faruok transfer yakoma can. Kwanansu 2 acan, bakaramin bacin rai Zarah tashiga ba, anyi tafiya banda ita.


Bayan dawowarsu, Mairo tashiga part din Hajjo, tana zuwa ta isketa abandakin falo tana ta amai, temaka mata tayi, bayan tagama suka dawo falo, mairo tace sannu Hajiya, amma inaganin kamar ciki ne dake ko? Hajjo tace nima haka nake tunani, dan tunkafin muje hajji nadena ganin al,ada ta, sede yaune nafara amai. Mairo tace aikinsan yanzu ba cikin farko bane, kila ma yayi wata 2 shiyasa baki fara laulayi dawuri ba.


Amma zankawo maki wani magani, inde kinsha zaki dena amai kuma zakiji kwarin jikinki. Hajjo tace aiko nagode Baba mairo, wlh bansan da abunda zan saka maki ba, Allah yasani nayi rashin uwa, amma gashi yanzu Allah yabani ke, inajinki tamkar uwata, babu abinda zan iya boye maki. Kwallan da mairo take boyewa suka zubo mata, Hajjo tace Baba mairo meyafaru kuma?  Mairo tace bakomai, kawai naji dadin kalamanki yata, tunda nake bantaba haihuwa ba, banida me kirana mana, segashi yau kinbani babban matsayi wanda bakowa ne yake amsa shiba. Hakika yau ina cikin farin ciki wanda. Nadade banji ba. Allah yayi maki albarka keda diyarki Falak.


Sede inaso infada maki wata magana, ada ina shakkun infada maki, sbd bansan yazaki daukeni ba, kila bazaki yarda da maganata ba. Amma ayanzu dakika bani matsayin uwa agareki, nasan zaki yarda da abunda zan fada maki, dan kinsan uwa bazata fadama yarta karya ba.


Inaso kiboye cikin dake jikinki har lokacin da zaki haifeshi, ko Alh, banaso kifada mashi kina da ciki harse yayi girma, nasan shi baza,a iya boyemashi ba. Hajjo tace meyasa kikace haka Baba mairo, nasan dole akwai dalilin dayasa kikace haka, dan Allah kifadamun koma menene, nayi maki alkawarin bazan bafadama kowa ba.


Anan mairo tafadama Hajjo duk abunda taji Zarah tana fadama Asabe awaya. Hajjo tagoge kwallan idonta, tace wlh jikina yabani Zarah ba sona take ba, kawaide tana yimun fuska 2, lokacin da aka kwantar dani asibiti take cemun wai inzo tarakani asakamun robar hana daukar ciki.


Anan jikina yabani wani mugun nufi take nufi dani, kawai sena fada mata likita yace kozan haihu senan da shekaru, wlh Baba mairo ina gama fada mata bakiga wani murmushi datayi ba. Tun daga nan nagane abinda take nufi dani.


Kuma insha Allah Zarah bazatasan ina da ciki ba sede taji haihuwa ta. Shima Alh, bazan fada mashi ba harse yayi kwari, shima sena rokeshi kada yabari kowa yaji, Mairo tace bara inje inkawo maki maganin.


Haka Hajjo tacigaba da renon cikinta babu wanda yasani daga mairo se Falak, su Jidda anyi graduation duk da bawani kokari tayi ajarabawarsu ba, su Falak kuma sunshiga ss3 karatu sukeyi sosai dan sunaso sucigaba da karatunsu idan sungama.


Jidda yanzu duk inda Al,amin zeje tare suke zuwa, ko da kwana nawa zeyi tunda Alh, baya zama gida yanzu sosai, Zarah kuwa tunda Jidda tana wadata ta da kudi babu abinda yadameta, abinda Jidda tagane ma Zariya tamaida gurin zuwanta, tunda taga Asabe bata kwaba mata duk inda taje kotayi dare bata cemata komai, kuma Baba bashida katabus agidan, hakan yasata yanzu tafi zama Zariya akan gidansu, koda Alh, yaji tana zuwa Zariya dadi yaji saboda yaga umminsu ita bata zuwa.


Lokacin da cikin Hajjo yacika wata 7 aranar Alh, yagane tana da ciki, yace lallai ma Hajjo yanzu nikike boyema abun farin ciki?  Dariya tayi tace wlh banso kagane ba, naso kawai kazo kaga jariri ko jaririya, shiyasa ko zanje awo nake cemaka zanje wankin kai. Amma kayafemun da karyar danayi maka. Jawota yayi yace bakomai, aikinsan dama ni ina baku damar fita duk lokacin da kukeso koda bana nan.


Amma gaskiya naji dadi sosai,  Allah yasa rayayyene, tace ameen. Amma dan Allah banaso kafadama Kowa har ummin Jalila, nafiso inbata mamaki tunda kai kaganoni.

    Yace shikenan angama daukarta yayi suka nufi daki.


Su Falak suna third term a ss3 Hajjo ta haifi yaronta me kyan gaske, babu wanda yasan tahaihu, dan cikin dare nafara nakuda kuma taci sa,a Alh, agurinta yake, haka suka hada kaya suka nufi asibiti, Falak kawai tasan suntafi, gurin karfe 8 suka dawo, bayan ya kaita part dinta yawuce part din Zarah, yanashiga yahadu da Mairo, yace tabar abinda takeyi taje Hajjo ta haihu, sosai mairo taji dadi, tace me aka haifa, yace namiji, barka tayi mashi sannan tawuce part dinsu.


Farin ciki kawai Alh, yakeyi, dakin su.  Jalila yaje yace tafito tacigaba da aikin da mairo takeyi, dan taje gurin Hajjo ta temaka mata ta haihu. Jalila cike da murna tace Dady meta haifa?  Yace kunsamu kani Jalila bakaramin dadi taji ba, fita tayi tawuce kitchen. Dakin Zarah yashiga, ganin yana cikin farin ciki ga bakinshi yaki rufuwa, tace Alh, yaude lafiya kake kamr wanda aka yima bushara da gidan, aljanna? Yace aidole kiganni haka, Hajjo ta haihu kuma tasami namiji me bala,in kama dani. Dariya Zarah tayi tace amafarkin yau ne kaga haka? Yace wlh da gaske nakeyi, tun dare muna asibiti. Zarah tace karbo yaron kukayi kome, nide nasan Hajjo bata da ciki. Ganin zata bata mashi lokaci yajata zuwa part din Hajjo.


Mutuwar tsaye Zarah tayi ganin Alh, yamiko mata yaro me bala,in kama dashi, kamar an tsaga kara, wata irin zufa ce tarika keto mata ta ko ina, tama rasa mezatayi, takasa karbar yaron, hawayene suka taho mata tayi saurin juyawa takoma. Falo, mamaki ne yakama Alh, ganin abinda Zarah tayi, amma su Hajjo sun harbo jirginta.


Urs,

 NABILA RABI,U ZANGO

(  Nabeelert Lady)

08028525263

[7/13, 09:40] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani 

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)


@( H,O,N,A)


Part 40.....45


Afalo yasamu Zarah tana goge kwallan idonta, Zarah meyafaru haka? Fitowa Hajjo da Mairo sukayi suna kallonta domin jin abinda zata ce. Haba Alh, ai wlh bekamata ma indauki yaron nan ba, me kuka daukeni acikin gidan nan, ni na dauki Hajjo kamar kanwa agurina amma ashe ita ba haka bane, 


Kaima kabiye mata kun maidani agefe guda, wai yanzu ace har Hajjo tayi renon ciki agidan nan amma bansani ba, wlh da ace yaron nan baya kama da kai bazan taba yarda Hajjo ta haifeshi ba. Kuma har ace ina gidan nan nakuda takama Hajjo ai komin rashin matsayina amatsayina na ,ya mace za,a iya kirana inrakaku asibiti amma kai me mata zaka dauketa kutafi ku biyu.


Gaskiya baku kyauta mun ba, kuma yau nagane matsayina agurinku, kuyawa tayi tafashe da kuka zata tafi, jikin Alh, yayi sanyi sosai, seyanzu yake ganin rashin wayon dayayi daya biyema Hajjo akan kada afada ma Zarah tana da ciki, gaskiya shima beji dadi ba.


Aje yaron yayi yafita yabi bayanta, Hajjo tayi murmushi tace Xarah kenan, tabbas dan kyautawa bamu kyauta ba, amma Allah yaga nufinmu, dan haka ko kinyi fushima nide tunda nakare lfyr yarona ai shikenan. Mairo tace kukan munafunci ne takeyi, tasan idan bahaka tayi ba, Alh, ze iya gano bata farin ciki da wannan yaron, ki kyaleta tunda ba akan gaskiya take fushin ba, zata sauko, kema kije kiyi mata ta ,yan duniya.


Adaki yasameta tana ta kuka, wanda azahirin gaskiya kukan bakin cikin haihuwar yaron da akayi ne, na 2 kuma rashin sanin Hajjo tana da ciki, da taje an zubar dashi.


Jawota yayi yarungumeta yafara aikin lallashi, shima kamar zeyi kukan, dan har ga Allah beji dadin abinda akayi mata ba, shi sam beyi tunanin zataji haushi ba. Sallamar dasukaji abakin kofa ne yasashi tashi yaduba ko waye, tare da Hajjo suka shigo, zama tayi abisa gefen gadon,


Ahankali tace. Ummin Jalila dan Allah kiyi hakuri, nasan ban kyauta maki ba, amma atunanina keda Alh,naso inbaku mamaki, naso ace kuduka Jariri kawai kuka gani, sede shi yafara ganewa, shiyasa narokeshi akan kada yafada maki, nafiso inbaki mamaki kawai kiga yaro,


Nasan zakifi kowa murnar hakan, saboda irin damuwar danaga kinshiga danayi bari, amma kiyi hakuri, ga yaron nan, nabaki dama kiyi mashi huduba da duk sunan dakika ga yayi maki, domin danki ne.


Murmushin dayafi kuka ciwo tayi ta tashi zaune, tace shikenan Hajjo na hakura, amma kada kisake, kuma nahakura ne, saboda wannan damar da,aka bani. Alh, ka amince inyi mashi huduba?


Dariya yayi yana mejin dadin irin hadin kan da matanshi sukeyi, yace ni na isa inshiga tsakanin yaya da kanwarta, gashi kiyi mashi huduba muji abinda kika sa mashi


Karbarshi tayi acikin kunnenshi tarika dura mashi zaki tana fadin nice ajalinka, magana takeyi tana murmushi, kamar gaske. Dagowa tayi tacenayi masa huduba da sunan marigayi Bashir, ( mijin Hajjo baban Falak).  Za,a rika kiranshi da Amir, inafatan Alh, ban bata maka raiba, kada kace nasaka sunan abokin tarayyar ka? Matsowa yayi ya rungumeta yace gaskiya Zarah kina da tunani me kyau, wlh naji dadi sosai, kuma nagode daya kasance kece kikayi wannan hudubar, dan dani nayita da sunan mahaifina zansa, amma hakan da kikayi, naji dadi sosai, domin anyima Falak da Hajjo kara, idan Allah yasa takara haihuwa zasa sunan Babana.


Wani shu,umin murmushi Zarah tayi aranta tace nima naji dadi da aka bani damar zaben suna nasan dama sunan Babanka zaka sa, wlh, bazaka taba saka sunan Babanka akan ya,yanta ba.


Matsowa Hajjo tayi, ta rungume Zarah tana yimata godiya. Duk da aranta takasa yarda da wannan abun da Zarah tayi, kuma murmushin dataga tayi yakara tabbatar mata da akwai wani abu azuciyarta. Amma koma menene Allah yamaida maki nufin ki.


Tashi sukayi suka fita, bayan taje tafada ma, Mairo abinda yafaru. Mairo tace dole sekin dage da addu,a domin Allah ne kadai yasan irin mugun nufinta akanki, Allah yamana tsari da sharrinta. Ameen.


Haka akayita hidimar zuwa barka, yan unguwa, kudi sosai Alh, yakashe a haihuwar yaron, Zarah hakuri kawai takeyi, dan tace bazataje Zariya ba, sebayan suna, damma dadin datakeji Alh, yabata kudi masu shegen yawa, Yara ma duk yabasu, kasancewar Jidda bata nan, sede yabama Zarah nata.


Su Falak sunata hidima, ranar suna yaro yaci sunanda Zarah tasa mashi.


Fadi irin kudin da aka kashe bata lokacine. Harsu Asabe da Dije seda suka zo suna, wani filin Alh, daya zagaye yayima Ameer kyauta, sede be bari Zarah taji ba, saboda yasan halin mata.


Zaune suke adakin Zarah suna magana. Zarah tace wlh sena sa boka ya korar mun wannan matar, ita da yayan ta acikin gidan nan. Dije tace ai kinyi mata me sauki, baki tunanin idan kika koreta wata rana asiri yakare yasake maido ta? Ai kawai idan zakasha giya kasha ta dubu.


Ina baki shawara ki kasheta kawai, Zarah tace ni nafijin zafin yaron wlh. Asabe tace lallai bakida wayo, idan kika kashe maciji mabi sare kan ba ai kinyi aikin banza. 


Kawai kifara kashe Hajjo daga baya seki kashe yaron, idan kinsamu nutsuwa kizo muje gurin boka.

Haka suka ci gaba da tattaunawa,


Urs,

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)

08028525263

[7/13, 09:40] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah

Marubuciyar Zamani

NABILA RABI,U ZANGO

(Nabeelert Lady)


@ ( H,O,N,A)


Part 45.....50


Bayan suna da sati daya, Zarah tashirya tanufi zariya, tana zuwa suka tafi gurin boka, bayan tagama yimashi bayani akan tanaso akashe mata Hajjo da yaronta, hada ido Dije tayi da boka ta kyafta mashi ido.

Dariya yayi yace Hajiya ni banayin aiki 2 alokaci guda, musamman idan yakasance na kisa ne, sede zanyi maki wani temako daya, nafarko dole kizabi wanda za,akashe acikinsu,


Zarah tace akashe yaron, Asabe tace lallai bakida wayau, idan aka kashe yaron ai zata iya kara haifar wani. Zarah tace hakane afara kashe Hajjon, dariya boka yayi yace bazamu kasheta lokaci guda ba, dole zamu samata ciwo nawani lokaci gudun kar azargi wani abu.

Shikuma yaron zanmaidashi dolo, kafin shima yabi uwarshi.


Amma wannan aikin naki zeci kudi, tace kamar nawa za,a bada? Naira dubu dari 200 zaki bada, anan take tadauko ta ajesu a inda tasaba ajewa,


Wani allon karfe yadauko yayi wani rubutu akai, sannan ya hura wuta yadora allon asaman wutar, yace yanda allon nan zeyi zafi haka jikinta zerika zafi, ko wane irin magani aka bata bazata taba jinsaukin zafin jikinta ba.


Dasannu zata mutu, garin magani yabata yace ta murzashi ahannunta alokacin data dauki yaron seta shafa hannunta akan yaron, shima idan uwar tamutu ki aiko su Dije suzo sukar ba maki maganin da akashe shi dashi. Godiya sukayi mashi suka tashi suka fita. Dije kuma ta tsaya karbar masu kason su, dubo 60 yabasu, tayi godiya tace naji dadi dabaka bata maganin duka ba, nafiso karika raba aikin yanda za,afi samun kudi. Dariya yayi yace Dije naga alama kinfini son kudi.


Kwance Hajjo take tana bama Ameer nono, kamar daga sama taji antsikareta, tashi tayi, se kuma taji jikinta wani irin sanyi yana shigarta, tashi tayi tajawo bargo, duk da lokacin zafine, amma haka takejin wani irin sanyi, shiga tayi cikin bargon, kafin minti 20 kuma gabadaya jikinta da bargon sunyi wani irin zafi.


Cire bargon tayi tarasa inda zata sa kanta, rigar jikinta tacire shima de basauki, tashi tayi da kyar tanufi bandaki, wanka tayi, sede data zuba ruwa ajikinta kamar ruwan zafi tazuba, haka tafito tasamu riga marar hannu tasaka.


Falo ta fito ta kunna A,C ta kwanta, duk da haka zafi takeji ajikinta, wasu irin hawaye ne sukarika zubo mata saboda ciwon kan datakeyi, ga Falak tana makaranta sunfara waec bata dawowa da wuri.


Kamar daga sama taji sallamar Mairo, kasa amsawa tayi, dasauri mairo tashigo jin Ameer na kuka amma bata daukeshi ba.

     Daukarshi tayi tana fadin Hajiya lfy, kasa magana tayi sede kwalla, kusa da ita tamatsa,ta dora hannunta ajikin Hajjo, saurin cirewa tayi jin wani irin zafi kamar ze kona mata hannu, tace Hajiya ai zazzabi kikeyi, bara inkira driver yazo yakaimu asibiti tunda Hajiya bata nan,


Suna zuwa asibiti aka karbesu domin anriga da ansan Alh, wayar Hajjo mairo tadauka takira Alh, anan take fada mashi suna asibiti, yace gashi nan zuwa, goye take da Ameer yana ta kuka tana jijjigashi, da kyar yayi bacci.


Alh, ne zaune a office din Dr, yace mashi zazzabi ne kawai me zafi takeyi amma anyi mata allura kuma ansa mata karin ruwa insha Allahu zata samu sauki. Godiya yayi mashi ya amshi takardar maganin daze siyo yafita.


Zaune suke duka gidan har Zarah domin ta dawo, Jidda ce kawai bata nan, dan suna Abuja ita da Al,amin. Zarah tace oh, sannu Hajjo, wannan irin zazzabi haka, ace tundazu yaki yasauka, sema kara hawa yakeyi.


Alhaji yace gaskiya nima nafara tsorata da wannan zazzabin, Allah de yabaki lfiya, Hajjo. Zarah tace Mairo kawo Ameer kije gida keda su Falak da Jalila kushiryo abinci ko, naga dare haryafara yi, Falak da tun dazu take kuka tace. Ummi da kinje kin huta yanzu kika dawo daga unguwa fa, ni zan zauna agurinta.


Zarah tace a,a kuje kuda kuka dawo daga jarabawa, ai yakamata kuje kuyi wanka kuci abinci, bakomai nizan zauna, idan kundawo anjima senaje ni. Alh, yace kuje kawai idan kundawo taje.


Suna fita Alh, yace bara yaje yadawo, Ameer na hannuna Zarah, ita kuma Hajjo tana bacci, Saurin fiddo magani tayi ajakarta tashafa a hannunta takama Ameer tashafa mashi akai, wata irin kara yayi wadda har Zarah seda ta tsorata tayi saurin mikewa, Hajjo datake bacci seda tafarka.


Turo kofar dakin akayi, wasu nurse ne 2 suka shigo, ganin Ameer yana wani irin abu farin miyau yanata fito mashi, yasa sukayi saurin karbarshi suka fita, Hajjo tace mekika yimashi Zarah?


Akideme tace wa ni? Nima bansan abinda yafaruba, kina bacci inason inshiga bandaki sena ajeshi kusa dake,nashiga bangama abinda nakeba naji kararshi, ina fitowa naganshi akasa kwance. Wasu hawayene suka fitoma Hajjo, ido kawai ta rufe tanajin wani irin zafi ajikinta.


Bin bayansu Zarah tayi, tana sauke ajiyar zuciya, karo taci da Alh, yana kokarin shiga dakin, yace lafiya de? Anan tafada mashi abinda yafaru, shima binta yayi, koda sukaje Ameer haryayi bacci, nurse tace wai meyafaru dashine? Zarah tafada masu abinda tace ma Hajjo, suka ce Allah yakara sauki, sunyi mashi allura zejisauki, dauko shi tayi suka fita.


Bayan su Mairo da Falak sundawo, Jalila kawai suka bari agida, da kyar suka samu Hajjo taci abinci, se alokacin Ameer yatashi, tunda yatashi yake zubar da miyau abakinshi, ga kanshi yawani langabe,


Karbarshi mairo tayi tana kare mashi kallo, Zarah tace tunda kunzo nizan wuce, dare yayi, Allah yakara sauki.

Alh, yace nima anjima zantaho, tace to. Hajjo tace anya yaron nan faduwar dayayi beji ciwo ba kuwa, kalli yanda yakeyi Alh, karbarshi yayi yace bara inkaim likita shi yaduba shi.


Bayan Dr, yagama dubashi yace aini Alh, banga wata alama data nuna mani faduwa yayi ba, kuma naduba jikinshi lafiy lau babu wani abunda ke damunshi, da faduwa yayi dayatashi da kuka, kasan dama ba,a raba jarirai da miyau abaki, kanshi kuma dayake langabewa dama kasan ai jikinshi beda kwari, tunda ko sati 2 beyiba. Kada kudamu bawata matsala bace, godiya yayi mashi yafita.


Bayanin abinda likita yace yayi masu, itade Hajjo jikinta yakasa yarda da abunda akace, dan kawai tana kunyar Alh, yasa tayi shiru dan ita macece me kauda kai akan abu, yadade har gurin karfe 11 sannan yayi masu sallama yatafi.


Mairo tace Hajiya wai meyafaru har Hajiya tace Ameer faduwa yayi? Anan tafada mata duk abinda yafaru. Mairo tace wlh hajiya batada gaskiya, nikam yanzu tsoronta nakeji, amma bakomai Allah yafita, ni tunda tace zataje Zariya jikina yake bani wani mugun abun zekaita.


Mucigaba da addu,a insha Allahu bazatayi nasara akanki ba, Falak tagoge kwallan dake idonta tace Umma gobe idan naje islamiyya zan tambayi malam wace irin addu,a zanrika tofa maki, dan wannan zazzabin yayi yawa. Mairo tace gaskiya kam nima naga alamar dole semun hada da addu,a.


Washe gari ciwon Hajjo kamar karashi akeyi, sukansu likitocin sunyi mamakin irin zafin zazzabinta, duk wani test anyi mata amma babu koda maleria ce ajikinta, duk wani temako sunyi mata amma zafin jikin yaki sauki, haka suka cigaba dayi mata allurai da magunguna.


Bayan Falak tadawo daga islamiyya tadauko ruwa akofi tayi addu,oin da malaminsu malam Sameer yabata, tayi, tabama Mairo kama Hajjo tayi tace tayi bismilla tasha, tana gama sha tarika atishawa , karbar rowar ruwan tayi ta wanke mata fuska zuwa wuyanta, sannan ta kwanta.


Cikin mintuna kadan zafin jikinta yakoma sanyi, jitayi kamar ancire mata kaya ajiki, Hamdala sukayi, Mairo tace aini nasani wannan ciwon naki akwai aikin asiri aciki, Alh, yazo mukoma gida kawai acigaba dayi maki addu,a. Falak tace shima Malam Sameer haka yace idan har tasha kuma zazzabin yasauka to tabbas akwai sihiri ajikinta. Mairo tace ke duniya, anya mutane suna tsoron Allah kuwa?


Bayan Alh, da Zarah sunzo suka sami Hajjo azaune tana bama Ameer nono, Alh, cike da jindadi yashigo yazauna kusa da Hajjo yana fadin jiki yayi sauki kenan, tace gaskiya Kam jikinta yataba, yaji sanyi yace Alhamdulillah bara inje Dr, yabamu sallama, Mairo tace nimade haka nace, dan suma sunkasa saukar da zafin zazzabin amma Falak tana amso addu,a agurin malaminsu aka bata tasha ko minti 10 ba,ayiba yasauka.

     Kwarewa Zarah tayi, nan take zufa tafara fito mata, tagefen ido suke kallonta, da kyar ta dede ta kanta tace Alh, gara de abarta takara samun sauki, yace A,a suma kansu sunkasa yimata magani tunda addu,a tanayi mata, fita yayi Zarah tabishi dakallo.


Hajjo tace Ummin Jalila yagajiyar jiya? Murmushi tayi tace haba ai gajiya tabi lafiya, yajikinki? Tace dasauki.

   Tare sukazo da Dr, yakara duba jikinta, shima yayi mamakin saukar da zazzabin yayi lokaci guda, shima shawara yabasu akan sucigaba dayimata addu,a. Sallama yabasu suka nufi gida,


Hankalin Zarah bakaramin tashi yayi ba ganin Hajjo tawarke, sede Ameer da haryanzu yana zubar da miyau, kuma kanshi baya tsayawa, shima addu,a sukeyi mashi. Waya Zarah tayima Asabe tace taje gurin boka tafada mashi abinda yafaru, idan zata turama Jidda kudi a account tunda  kince jiya tadawo ko,


Falak ce tare da Jalila suntaso daga islamiyya, sallama sukaji abayansu, juyawa Falak tayi, murmushi tasaki sannan ta amsa sallamar, jalila tace lah Malam Sameer ashe kaine? Yace wlh, kuwa inata sauri naga harkun taho, dama tambayarku zanyi yamejiki, Falak dasauki Malam dan tunda nayi mata wannan addu,ar shikenan bata kara zazzabi ba. Yace Alhamdulillahi kicigaba dayi mata addu,ar dakinga tafara irin zazzabin, tace to malam mungode, tare suka tafi harseda yakaisu kofar gida Jalila tayi mashi sallama tashige, Falak tace nagode sosai malam, bansan da mezan gode maka ba, Murmushi yayi yace dan wannan ai bawani abu bane, Allah yakara bata lafiya. Ya Exam dinku? Tace dasauki ai mungama Waec ma ranar monday zamufara Neco, yace to Allah yatemaka adage ayi karatu, nima dama hutu nasamu kuma yakusa karewa zankoma last semister dina.

Falak tace lah Malam ashe baka gama karatu ba, yace emana, tace wace makaranta kake to, yace a A,B,U Zariya nake, Falak tace amma baka dade dafara zuwa makarantar nan bako? Yace na dade mana, amma aikinsan makarantar 2 ce akwai ta yara data manya, toni da nafison koyama yara, shiyasa nake acan, to shugaban makarantar ne yace indawo nan, amma nibanaso, 


Tace meyasa malam? Yace kinsan halin yanmatan yanzu basuda kunya shiyasa nafison yara, kuma gashi makarantar ba,a dukan manya kinga dole su raina malamai ko, Falak tace to aide ajinmu basa raina ka, ko? Murmushi yayi yace mace daya ce tagama rai nani , zaro ido tayi tace wacece? Yace Falak ce, da gudu yashige gida tana dariya. Shima dariyar yakeyi, shide harga Allah yanason Falak, sede yana tsoron yafada mata abinda ke ranshi taki amincewa.


Wanene SAMEER? 


Sameer dan asalin garin kaduna ne, suna zaune a tundun wada, shi kadai Allah yabama iyayenshi, tunda yagama secondary school mahaifinshi yarasu, daga shi se ummanshi Halima suke zaune agidan, yan uwan babanshi bawani karfi garesu ba, hakan yasa suka kasa daukar nauyin karatunshi tunda result dinshi yafito, duk da mahaifinshi bawani kudi gareshi ba, amma yanada rufin asiri, tunda yanada gidan kanshi, dan karami, aciki suke zaune da Ummanshi, tanayin kosan saidawa da kuma markade, dahaka ta tara kudi tabiyama Sameer kudin makarantar dayasamu A Zariya, cikin ikon Allah yafara karatu cikin sa,a hankalinshi kwance, yake karatunshi, domin Sameer beda hayaniya,mutum ne me natsuwa, ga kokari.


Idan anyi hutu yana koyawa a islamiyya kuma yana zuwa shagon wani abokin babanshi yana aiki, da haka yake tara kudin komawa, Ummanshi tahada mashi da nata.


Dahaka haryakusa gama karatunshi, yanzu haryana shekarar karshe a jami,a wannan karin ne daya dawo bangaren yanmata da koyawa aka bashi ajinsu Falak, tunda yadora idonshi akanta yaji yana sonta sosai, sede ganin daga gidan fatake fitowa yasan tafi karfinshi, amma duk da haka yakasa cire sonta aranshi, Sameer kyakkyawane nakarshe yanmatan makarantar dayawa suna nuna suna sonshi, sede yaki basu fuska, baya magana da kowa, dalilin fara maganarsu da falak akan ciwon Ummanta ne, tundaga nan yasamu damar yimata magana.


Wannan kenan.


Bayan sati biyu da samun saukin Hajjo takara tashi da wani zazzabin, haka kullum Falak take yimata addu,a data sha ciwon yake sauki, bayan kwana 2 kuma yadawo, Ameer kullum ciwonshi kara fitiwa fili yake yanzu kowa yagane Abnormal ne, Hajjo duk tarame tayi baki, Falak ma tarame saboda abu 2 yahade mata, ga ciwon Ummanta ga Exam, damma sunkusa gamawa, 


Alh, yarasa yanda zeyi gaba daya beda nutsuwa, sbd ciwon Hajjo, Zarah ma afuska kullum cikin damuwa take, hakan yasa tace ma Mairo takoma gurin Hajjo harseta warke, koda yaushe cikin turama Asabe kudi take domin akaima boka.


Ameer ma yarame saboda baya shan nono sosai, hakan yasa Alh, yace adena bashi nonon sbd zafin zazzabin datakeyi, madara yasiyo mashi Mairo tana bashi, abin yayima Fakak yawa ga malam Sameer takoma makaranta, ko no wayanshu batada.

    Ahaka ciwo yayita cin Hajjo addu,a kam tana shanta, Aranar da su Falak zasu zana jarabawar karshe, dasafe tafito cikinshirinta, tashiga dakin Hajjo, kwance taganta, sede ayau setaga tayi haske, sosai.


Zama tayi akusa da ita tace Umma zantafi, kuma yau zamu gama makaranta, kinga se indawo inrika kula dake sosai, kinga Baba mairo aiki yayi mata yawa. Murmushi Hajjo tayi, kamo hannun Falak tayi ahankali tace, Falak bazan dena fada maki akowane hali kika tsinci kanki kiyi hakuri da irin rayuwar da tasameki, kuma inaso duk rintsi kada kijuyama Alh, baya, kome zeyi maki kidaukeshi tamkar mahaifinki, kamar yanda ba,a iya canza uba, haka nakeso kirike Alh, ko bana gidan nan banbaki ikon kibar gudan nan ba, sede aure ko mutuwa, ki kula da kaninki, banaso koda wasa rashin kunya tashiga tsakaninki da Zarah, ko Jidda, nasan aduk gidan nan sune basa sommu, amma Jalila Allah yayi mata albarka, banaso kirabu da ita, itace kawarki kuma yar uwarki.


Kiyi hakuri da rayuwa Falak, zakici ribarta wata rana, inaso kirike Baba mairo, domin nadauketa amatsayin uwa, banida abokin shawara se ita, kema inaso kidauketa haka, nasan bazata iya cutar dake ba. Allah yayi maki albarka, tashi kije kada ki makara.

   Hawayen dasuka zuboma Falak tagoge tace Umma insha Allahu zanyi aiki da duk abinda kika ce, kuma zaki samu lafiya kidena fadar haka. Hajjo tace bani biro da takarda, bayan ta aje mata tajuya harta kai bakin kofa takara juyowa, kallonta daga Hajjo nayi, kwalla nafita daga idonta. Shigowar Jalila yasa Hajjo tagoge idonta, Jalila tace Umma yajikin, tace dasauki, Harzakutafi? Tace E, to Allah yabada sa,a.


Kama hannun falak tayi suka fita, biro tadauka tacigaba da rubutu a takardar, tana gamawa mairo tashigo. Hajjo tace Baba mairo duba cikin drowar can zakiga wata zaka baka kimiko mun.


Bayan tabata ne tamika mata takardar data rubuta tace tasaka ciki. Baba mairo, inaji ajikina ciwon nan bana tashi bane, zantafi inbar yarana 2 agurinki, duk da nasan kema bakida karfin rikesu, sede inaso Ameer da Falak sucigaba daza agidan nan, matukar ba, Alh, ya koreta ba, dan Allah ki kularmun da Falak marainiya ce, inaso wannan jakar kiajemun ita harse ranar da aka kai Falak dakin mijinta sannan kibata, idan Allah yasa tayi dacen miji kice kada tazama meboye sirrinta agurinshi.


Duk abinda Zarah zatayima Falak Kibata hkr, tashi kilekamun ko Alh, yashigo, goge kwallan idonta mairo tayi tace Allah yabaki lafiya Hajiya ciwo ba mutuwa bace, tashi tayi tafita.

    Tare suka dawo da Alh, danshigowar shi kenan gidan. Kwance suka sameta tana  kallon silin bakinta dauke da murmushi, kusa da ita Alh, ya matsa, hannunta yakamo gani yayi yakoma, dasauri yadora kanshi bisa kirjinta, nan ma babu numfashi, jijjigata yashiga yi yana kiran sunanta, amma ina rai yayi halinshi.

Kuka yasa kamar karamin yaro, mairo ma kukan takeyi tana fadin shikenan Hajiya wayyo. Yadade ahaka, kafin yadauki waya yafara kiran kawunshi sannan yakira Farouk da sauran mutane, fita yayi domin kiran Zarah.


Tunda driver yakaryo kwanar gidan taji faduwar gabanta ta karu, tunaninta ne yatsaya alokacin dasuka tsaya kofar gidan taga taron mutane, wasu sunata alwala, da gudu tafito tanufi cikin gidansu, ita da Jalila.



Post a Comment

0 Comments